﻿[1/9, 7:53 PM] +234 901 554 3771: _*DEEN MARSHALL*_
_Mamuhgee_

*_ZAFAFA BIYAR_* 🔥🔥
_*So Da Zuciya*_
Miss xoxo
_*Halin Girma*_
Hafsat Rano
_*Dabi'ar Zuciya*_
Safiyya huguma
_*Takun Saka*_
Billyn Abdul
_*Deen Marshal*_
Mamuhgee

_Pay @08184017082 Or 09134848107_


*1*

*_BismillahirRahmanir-Raheem_*

Ahankali ta dago kanta dake 'dan Sara Mata ta kalli kofar office din nata da aka kwankwasa batareda ta motsaba ta dauke idonta akan kofar tana sake boyayyan numfashin dake bayyanarda qosawarta da halin ABBAS LAMIDO sbd ko ba'a fada ba tasan koba shi bane to koma waye to al'amarine daya shafi sunan Abaas aciki.
Turo kofar akai tareda shigowa ko Bata dagoba Jin takun takalma yasa ta fahimci Sarah ce Dan Haka ta sake lumshe ido tana dago Kai ahankali tareda dauke hannunta daga kan aikin datakeyi a laptop ta aje gefe tareda gyara zama ta Kai hannu ta dauki ruwan data fitar a fridge tun dazu sbd su huce daga sanyi ta bude robar ruwan Tasha kusan rabi ta ajiye sauran tana cewa"

Sarah akwai wani abune?

Sai alokacin Sarah ta matso ta zauna kan kejerar hutawar dake kallon wadda  *_NAJMA_*  ke zaune tana jiran abinda zata fada,
Saidata Dan sauke numfashi itama kafin Kai tsaye tace"

Naj dazu kafin isowarki zuwan chairman Abaas biyu office dinnan Kuma Banga alamar lafiyaba a yanayinsa
Zan iya cewa dai yanayin da aka Sabane.

Sai alokacin _*NAJMA ABDULLAHI BELA*_ ta dago da fararen idanuwanta dasukai laushi da gajiya tareda damuwar Jin abinda aka fada din ta kalli Sarah tsawon lokaci kafin ta sauke nata numfashin itama ta bude Baki da muryarta me taushi dake kokarin boye damuwarta tace"

Meyene matsalar Abaas Kuma yanzu?

Cikeda kulawa Sarah tana kallonta tace"

A yanda nakega inaga bazai wuce akan maganar jiya bace da Dr Sa'id yazo gurinki sbd zuwansa biyu Ana cewa kunfita tareda Dr Sa'id din.

Sai alokacin ta tuno da zuwan Dr din jiya da fitar da sukai zuwa taron makarantar yaronsa a wata private school dake kusa bama nesa ba.
Ajiyar zuciya ta sauke ahankali tana daukan wayarta Dan kiransa Dan kuwa ma wannan karon yayi kokarin rashin binta gida tun Daren jiyan yayi abinda ya Saba.

Ringing wayar ta ringa yi harta katse Bai daga ba ta sake saka Kiran Bai dagaba har lokacin
kusan Kira uku Tai Masa baya dagawa ta kashe wayar tareda ajewa gefenta ta waiwayo ta kalli Sarah tace"

Bai dagaba
Baya office dinsa ne?

Banajin yafita Dan ko kafin nashigo Naga wucewar secretary dinsa hanyar zuwa office dinsa.

Juyar da fararen idanuwanta tayi ta maidasu kan wayarta da tadau ringing taga sunan Hanifa ne akai ta lumshe idanu ahankali tana sauke ajiyar zuciya tareda Jin sanyi aranta sbd Hanifa Marshal Alfa Bata Bata lokaci komai kankantarsa batareda takirata ba idan taji wani Abu yafaru da ita.
Kallon Sarah tayi da alamar tambayar cewa"
Kinfada Mata yawon da Abaas yayi na nemana yanzu da safe kenan?

'yar dariya Sarah tasaki tana miqewa ta nufi hanyar fita tana cewa"

Sorry ma'am itace takirani da kanta ta tambaya.

Ficewa tayi tareda rufo kofar office din har lokacin da sauran dariya akan fuskarta saidai ta baro jikin kofar sukai kusan Karo da Abaas daya qaraso office din sanye cikin suits ash dasukai Masa kyau matuka kasancewarsa kalar ruwan tarwada Kuma cikakken kyakkyawan namiji meji da lokaci da kuruciya da nera.

Da sauri Sarah ta matsa gefe tana sake sake fuska da tace"

Barka chairman.

Ko kallonta beyiba ya bude kofar office din dake daukeda sunan NAJMA BELA ajiki ya shige tareda rufo kofar.

Tana zaune a inda Sarah ta barta bakuma ta juyoba sbd tariga tagane shine yashigo Dan Haka saima Dan lumshe ido datayi Wanda yake tamkar dabi'a gareta.

Kureta yayi da kallo daga tsayen kyawunta da dabi'unta masu sanyi suke taruwa su sace zuciyar mutum wainda shima sune suke dawo dashi gareta Koda yace ya rabu da ita,
Duk neman matansa yakasa samun wadda tafi Masa Naj kyau da sanyin dabi'u tareda wani irin aji Wanda ko jinin sarauta zai shafa Mata lafiya
Daya samu da tuni ya rabu da Naj sbd gabaki daya tagama Cinna Masa hauka bayan yanada tarin mutunci da dukiyarda yake iya shimfida duk abinda yakeso Amma gashinan yaqare da aiki a ALFA'S sbd ita 'yar  daba 'yar kowaba face wadda ke amatsayin babbar Aminiya ga 'yar Marshal alfa Wanda sbd hakan ne take anan din shikuma yafiso ko ruwa idan zatasha tafada Masa Amma duk yabi yazama wani zararre akanta Wanda abin ke matuqar Kona Masa Rai duk da yasan tana tsananin hkr da dauke ido akan abubuwan dayake Mata Amma shima duk son dayake Mata bazai zauna Yana zuba ido tana yanda takeso ba Dan gwara ta Saba ko bayan aurensu tasan dokarsa baya daukan reni.

Jin shirun yayi yawa yasa ta dago ahankali ta Dan kalli gefensa da idanuwanta ta bude Baki cikin muryarta me taushi da nutsuwa tace"

Akwai wani Abu ne?

Rintse ido yayi wani takaici na taso Masa ya budesu akanta tareda qarasa matsowa gabanta ya fige wayar hannunta ya dangwareta kan kejera da qarfi cikin bacin Rai yace"

Akaro da danban adadiba Ina sake tambayar meye asalin boyayyar alaqarki da wannan likitan sbd bazai yiyu ko yaushe nayi tambayar mu'amalarku kinamun shiru sbd bansan meyake bakiba Wanda Ni bazan iya bakin ba da kinkasa rabuwa dashi,
Kyanki kike rudarsa dashi?
Kokuwa wani abun ne Wanda bansaniba ni......

Kashesa tayi ta hanyar zuba Masa manyan idanuwanta farare dasukai jajir atake da zallar takaicin kalamansa da basuda mutantawa ko darajantata amatsayinta na wadda zai aura din.

Miqewa tayi tsayi tareda daukan wayarta ta batareda tace Masa ko kala ba ta nufi table din office din da Jakarta ke Kai ta dauka ko kallon inda yake bataiba ta nufi kofa ta bude ta fice tabarshi tsaye Yana bin bayanta da kallo zuciyarsa na Kuna Kamar zai cinnawa kansa wuta yakeji.

Tana fitowa Sarah ta taso daga kan table dinta na matsayinta na secretary dinta ta qaraso tun kafin Tai magana ta lura da yanayin Naj din Wanda tasan dama za'ai Haka indai Abaas ne Wanda kullum ne qaida sai sunyi fada da Naj da Abaas din duk da dai kullum fitinar da tashin hankalin na Abaas din ne.

Batareda ta kalletaba da murya me 'dan nauyi tace"

Sarah ki tattara takardun Dana Bari a table da laptop Dina ki kawomun gida idan kintashi.

Ok Naj Allah yatsare hanya.

Tana saukowa qasan building din ta nufi gate zata fita tahau taxi sbd dama Abaas din yawanci ke daukota daga gida Kuma idan sun tashi ya maidata idan Kuma suna fada taxi take hawa wadda dama tafi hawanta shiyasa ma takeda me taxi dinta na musamman Wanda kiransa kawai takeyi yazo Dan kuwa ranaku daddayane basa samun matsala da Abaas Wanda take Jin wani lokacin Kamar zuciyarta zata Gaza bazata iya cigaba da hakuri tana hadiye halayen Abaas ba dan kuwa gabaki daya Babu inda sukai dace da juna dazasu iya rayuwar aure bayan aurenba,
Ta Yaya zata auri mutuminda baisan darajarta,mutuncinta,qimarta ba tareda mutunta alaqarsu,
Tariga tasani tsananin kyawuntane yasa Abaas yake son aurenta Dan tazama tasa abin ado agaresa Wanda Bata saniba ko tsananin zafin ransa da zafin kishinsa zai Bar kyan nata ta tsufa da abunta Dan ita shakkar aurensa yafara mamaye zuciyarta sbd a dukkanin halayensa Babu Wanda baya Bata mamaki.
Ajiyar zuciya ta sauke ahankali tana sake shanye damuwarta Kamar yanda ta Saba akan al'amarin Dan kuwa fasa auran Abaas gareta babbar matsalace dazata sake sako Kai tsakaninta da mahaifiyarta dama Dada kakarta uwa uba Dattijo Wanda yake mijin mahaifiyarta Kuma tawainiyan mahaifinta daya auri mahaifiyarta bayan rasuwar mahaifinsu.
Fasa aurenta da Abaas idan tayi shine zai zama Karo na hudu biyar kenan Ana fasa aurenta...

Mun iso hajiya" me taxi din yafada daidai Yana parking bakin Babbar kofar gidan Marshal Alfa Wanda sojoji  hudu ke zaune kofar gidan suna gadi.

Fitowa tayi ahankali cikin nutsuwa wadda zallar ilimi da wayewartane tareda ajin datake dashine yasa komai nata yake cikin nutsuwa ta bude jeka ta fiddo nera dubu daya ta miqa Masa tana cewa"

Nagode Mal Hafiz.

Juyawa tayi ta nufi gefen gidan daya bangaren dake gefen gidan Alfa wani 'dan madaidaicin gidan gado Wanda yakeda Dan zurfi daga cikinsa sbd 'Dan yawan dasuke dashi a gidan danma kusan duk Yan Matan gidan sunyi aure duk da bawai yawane dasuba sosai.

Cikin sabo sojojin dake zaunen dasukaga dawowarta sukace"

Welcome Ms Naj.

Dan murmushi tasaki tana waiwayowa tace"

Barkanku da aiki da hutawa.

Gidansu ta qarasa Wanda yake gefen da 'yar tazara da gidan Alfa din ta shige Wanda ba gate bane koface irin ta gidan me 'dan rufin asiri.

Gefen Dattijo ne a farko Dan Haka ta wuce Kai tsaye kuryar gidan inda taci Karo da Umma habiba zaune a kofar nata sashen kan kujera tana duba kayan 'yan kananan atampopinta datake saidawa tana waya autarta Asmau na gefenta tana jera kayan cikin qatuwar ledar da aka kawo kayan.

Cikin girmamawa asma'un ta dago tana cewa"

Anty Naj sannu da dawowa.

Yauwa sannu Asmau
Ina yiwa umma sannu idan tagama wayar.

Hannu kawai umma habiban ta daga alamar amsawa tana bin bayan Najma din da kallo tana yamutsa Baki cikeda shaguben Naj din sbd aikin datakeyi Amma aure ya gagara.

Tana Isa sashen mahaifiyarta ta taddata a tsakar gida zaune itama tana lissafin nata kudin na turarukan wuta datake saidawa duk kwalaben turarukan a gabanta baje sai wani irin kamshi Mai qarfi ke tashi ta kalli umman tana nufar dakinta tace"

Ummi sannu da aiki.

Itama Bata wani dagoba tanaci gaba da aikinta gabanta tace"

Yawwa,
Lafiya dai Naga kin dawo yau da wuri.

Tana qarasa shigewa dakin nata tace"

Lafiya kalau hutawa nakeson Yi jiya bansamu bacci sosaiba.

Dama Ina Zaki samu maganar bacci me Dadi bakida abokin Hira acikin gida kowa Yana dakin aurensa,
Dayake Kuma ga wata babbar kwabon Nan kinsamu" taqarasa fada tana kallon gefen Anty Amina dake gefe tana yiwa babbar 'yarta zainab bayanin karatunta da Bata ganeba.

Kallon umman tasu anty Amina tayi tana cewa"

Umma Dan Allah ki daina cewa"

Naqi zaman auren Nan a gaban zainab zata ringa daukan abin aranta tana ajewa da wata fassarar.

Wani mugun kallo ta watsawa Anty aminan kafin tace"

To Yaya kukeson na bayyanarda damuwata da halinda nake ciki akanku?
Ke zaman auren ya gagara kin tattara kindawo gida da budurwar 'ya,
Ita wannan aurenma ya gagareta Yi kwata kwata ta koma ta zama wata ma'aikaciya mutane na qarqashinta ta Yaya zata iya auren
Shiyasa nake sake cewa Hanifa wannan aikin na Najma bazai Bari tayi aureba matuqar tana ganin mazan daidai take dasu..

Lokacin auren ne baiyiba umma" cewar Hanifa data shigo gidan tana qarasowa gurin umman fuskarta daukeda murmushi tace"

Umma Naj zatai aure kamar kowa lokacine kawai Allah Bai kawoba.

Cigaba da aikinta umman tayi tana cewa"

Duk da hakan dai ta rage ganin girman kanta ta sallamawa duk namijin daya samu tayi aure Dan shine mutuncinta da nawa Nima Dan ko Nima na huta da gorin dattijo da Dada dasuke ganin da saka hannuna a  riqewar datai Kamar rake.

Murmushi Hanifa ta saki tana barin gurin umman tana cewa"

Umma Naj zata auri namijin daya kamaceta bawai ko wanne ba gskia
Kumafa ba riqeqa tayiba kawai dai Wanda zai Mana ciki da itane Bai bayyana ba haryanzu
Idan ya bayyana shikenan muma mun huta da damunta da kowa keyi da maganar aure,
Ni wlh bansan meyasa kuka sakamun Naj Dina a gaba ba duk kun damarmun ita.

Qarasawa kofar dakin tayi ta shige tana cewa"

Anty Amina barka da hutawa.

Da 'yar dariya anty Aminar tabi hanifar sbd ganin Kamar ta kunna umma databi kofar dakin da harara kamar zata hadasu su duka Tai musu duka ko zasu fahimci ciwon ranta na rashin auren Naj din wadda ita Sam kamarma abin baya damunta.
#Mamuh#


*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_Ina masoyan Kuma mabiya littaffan zafafa biyar wainda sukai fice gurin kawo muku littafansu masu tsafta da ilimantarwa tareda nishadantarwa,_*
*_Wannan shekarar sun dawo muku da wani sabon salon Kamar kowane zuwan inda suka kawo muku dada'dan labaransu da bazaku taba Dana sanin biya ba,_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107
[1/9, 7:53 PM] +234 901 554 3771: *_DEEN MARSHALL_*
_Mamuhgee_


2
Da wani irin kallo Hanifa kebin Naj dake tsaye bakin wardrobe daure da towel me kauri da girma brown color fuskarta fayau Kamar ko yaushe Babu wata damuwar abubuwan dake addabe da rayuwarta Kamar fitinar ummanta data su dattaji uwa uba ta Abaas datafi ta kowa zama abin baqin ciki da takaici.

Sake kallon fuskarta Hanifa tayi tana zaunawa kan gadon tareda ajiye wayarta gaban madubi tana cewa"

Nayi waya da Sarah dazu.

Batareda ta juyoba tana zare Yan kunnayenta tace"

Kada ki damu da abinda tafada Miki 
Idan Akan Abaas ne zuwa yanzu kema kinsaba da halinsa,
Abinsa ya daina damuna yanzu saidai kawai yanda Naga kamar abin nasa kullum rikidewa yake zuwa ga zargi
Zarginma me muni Wanda nake dannewa Ina sharewa sbd Umma dasu Dattijo...

Sai alokacin Hanifa ta katseta da cewa"

Meyesa Zaki daure sbd su umma bayan su dinma da zasu bude ido da kyau su duba dabi'u da wasu abubuwan tako Ina Abaas Bai cancanta ba bama Haka ba yaushe Kika fara damuwa da abinda ake fada na cewan kece Kika qi aure da har Kika zabi auren Abaas lamido Wanda Ni kwata kwata baima kwantaminba 
Gabaki daya Banga halayen maza masu hakuriba ko iya tattala mace atareda Abaas.

Ajiyar zuciya Naj din ta sauke Jin ran Hanifan yafara baci da zancen ta waiwayo ahankali ta kalleta tareda sakin wani irin lafiyyan murmushi Wanda kusan Arayuwarta tunda tazama budurwa cikakkiya kaf kannenta sukai aure aka sakota gaba tako Ina Hanifan ce kawai take iya ganin murmushinta me fidda asalin kyawunta Wanda yafito daga ainihin cikin zuciyarta sai kuwa Dr sa'id Wanda yake tamkar 'dan uwa Kuma aboki agareta shima idan tana tare dashi takanji nutsuwa da kwanciyar hankali sbd ya fahimceta tareda sanin halayyarta fiyeda 'yan uwanta na jini duk da kuwa Bata hada komai dashi ba face kasancewarsa likitan Hanifa tun suna yara har yanzu dasuka girma.

Zama tayi gefen Hanifan tana kallonta tace"

Ba abun damuwa bane basai kin saka damuwan Abaas ba aranki 
Mubar maganan ma sunan Harya fara sakamun ciwon Kai.

Hanifa Sam ko sunan Abaas din tafi kowa takaicin saurara sbd tun ranar farko da zancen Yana son Naj din ya sauka a kunnenta ta qarewa background dinsa da halayyarsa bincike bataga ta inda ya cancanta Naj ba kafin daga baya taji fara aikinsa da zuba hannun jarinsa a ALFA'S dinsu Wanda Sam bataso hakan ba Amma sbd zagayen da yayi akai Masa Hanya ya bullo ta gurin JALALUDDEEN qaninta Wanda dukiyarsa tafi ta kowa yawa acikin ALFA'S din hadda kuwa mahaifinsu da shine me asalin companies din na Nan portharcourt dama na wajenta.

Miqewa Naj din tayi tana cewa"

Bari nayi wanka nafito zamuyi mgna akan Isma'eel ya kirani dazu akan maganar zuwanki ganin likita A Jamaica.

Kallon kyakkyawar fuskarta Hanifa tayi tana murmushi tace"

Allah sarki Zawj.

Da yanayi na sanyi Naj ta kalleta zuciyarta na yin sanyi da dukkanin wata damuwar Hanifa ko ciwonta.

Toilet din dakin nata ta shige Dan dama wanka zatayi Hanifan ta shigo.
Bayan shigarta wanka miqewa Hanifan tayi ta sauko daga kan gadon ta zura flat slippers dinta na _Jimmy choo_ ta fita dakin ta nufi gurin umma dake zaune har lokacin tana aikin zuba wasu turaren wuta masu tsananin qamshi ta zauna gefen umman tun kafin ta qarasa zama umman tace"

Kun gamo shawaran yanda zaku fuskanci Dattijo da Dadah idan Maganar aurenta da Abbas ta fasu Dan nasan wannan doguwar fuskar da Kika shigo da ita bata lafiya bace Dole akwai abinda yake faruwa tsakaninta da Abbas.

Dan guntun murmushi Hanifa ta sauke tana Taya umman rufe kwalaben turarukan tace"

Umma meyesa kuka kasa gane irin taurin zuciya da qarfin imanin da Naj take dashi sbd ba kowane zai iya hadiyewa ba yakuma danne irin Gori da takura tareda cin fuskan da ake Mata akan rashin yin aure ba?

Umma kowa Yana yiwa Naj kallon taqi aure sbd zurfin ilimi da karatun bokon datayiba a cikin gidan Nan hakama Ana Mata kallon wadda ta Raina maza sbd ganin Kamar matsayinsu da nata daya ne Wanda umma keda Kika haifi Naj kinsan ba Haka takeba kawai dai ita Allah Haka yayita miskila me halin ko oho ga abinda ake fada akanta bayan Haka shi fa aure nufi ne na Allah Kuma ba lallai ne ita lokacin nata auren yayi ba idan lokacin yayi zatayi.

Hmmn Hanifa nagaji da bin bayan Najma akan maganar fasa aurarrakin Nan nata da akeyi kusan Kashi biyar tun Ina yadda da qaddarane a gaskia yanzu na yadda da hadda halinta na miskilanci Wanda kesa mazan ganin Kamar tafi karfinsu ne kokuma tana tuna tafi karfin nasu,
Kunfi kowa sanin yanda Dadah da Dattijo suka sakoni gaba a cikin gidan Nan akan Najma
Kullum fa qara shekaru akeyi ba ragewa ba yanzu ke da Allah yakawo rabo na haihuwa aurenki da yanzu ba kinada yara biyu ko ukuba koma hudu idan anyi haihuwar ritsa Amma Sam Naj ko 'yar damuwar Nan Bata nunawa kullum itace a nutse a kammale saikace wata lissafi ahaka takeson qarewane saidai aiki kawai..
To ku zauna ku dasa sabuwar shawara wannan karon wlh Dattijo rantsuwa ce a bakinsu shida Dadah matuqar aurenta da Abbas ya fasu to wlh bazata rufa sati ba agidan zasu aura Mata duk Wanda ya samu ciki kuwa hadda sojojin dake gadin gidanku yace zai kaiwa tayi idan hakan ta faru Ni kaina danake mahaifiyarta wlh zuciyata zata iya bugawa bare ita Dan Haka ki zaunar da ita kuyi shawara koma menene matsalar su zauna suyi sulhun abarsu itada Abbas din asamu ayi auren Nan ta tafiyarta ta huta Nima na huta da zancen kullum din.

Batasan wane bayani zata yiwa umman ta fahimta ba sbd matsuwar su dattijon tariga tasaka umman itama gajiya tana kasa fahimtar 'yar tata,
Tana tsananin qaunar Naj tamkar 'yar uwarta ta jini dasuka fito ciki daya Dan kuwa tsananin qaunar datake Mata har kasa tantance cikin su biyun tsakanin ita da marshal batasan waye tafiso ba duk da shi din jinintane dasuka fito ciki daya,
Bazata iya Bari Naj ta cutu takowane irin Hanya ba Dan Haka ita da kanta zata nema Ganin Abbas lamido suyi magana idan har yanason Naj da dukkanin zuciyarsa da gaskia to yakamata ya sauya su fuskanci rayuwar aure zasuyi su fahimci juna tun yanzu.
Idan har zai qaunaci Naj da gaskia zaifi Mata ace Dattijo yabada auren Naj wa duk Wanda yasamu.

Wanka ta fito taga Hanifan Bata dakin tasan tana gurin umma ko anty Amina Dan Haka Kai tsaye ta nufi gaban mirror ta zauna ta kalli fuskarta zuwa kirjinta da kafadunta dake bayyane suna wani qyallin haske da samun lafiyar fata ta maida kallonta kan fuskarta datafi komai kyau da daukan ido atare da ita ta lumshe fararen idanuwanta ahankali tareda sauke numfashi kadan kafin ta janyo lotion na jagggins tana shafawa kadan kadan Dan batason Mai da yawa Ta miqe bayan ta shafa turaren POSSES ajikinta tareda mist na Rednight ta zare band din kanta ta gyara daurin gashinta tayisa sako sako sbd Taji dadin kan nata ta nufi wardrobe ta Ciro doguwar riga Mara nauyi zata saka wayar Hanifa data bari kan mirror din nata takawo haske tana vibrating ahankali ba qara sbd Wanda Dabi'arsune rashin sakawa waya qarar ringing Dan kusan itace ta koyawa Hanifan hakan qarar waya na damunta shiyasa Sam wayarta Bata qara idan Ankira saidai vibrating shiyasa itama Hanifan ta koya sbd Naj din.

Ahankali ta waiwayo ta kalla wayar taga sunan dayake Kai _MARSHAL_
 dauke Kai tayi tana cigaba da saka kayanta Dan tunda takeda Hanifa Bata taba daga wayar 'dan uwanta ba idan yakira Wanda shi kadaine kawai Bata daukan wayarta idan shine yakira idan har Bata kusa tun kuwa tasowarsu suna qananu haryanxu.

Sanin baya Kira biyu 'daya yakeyi yasa ta sake waiwayo wayar tana kallon sunan destination dinda caller ID ta rubuto _HAWAII US STATE_ 
Hanifa Babu wani Abu a duniya dayafi Mata qanin nata Wanda su biyu kacal mahaifiyarsu ta Haifa ta bar duniya Wanda tazarar shekara uku ce a tsakaninsu yanayin aikinsa da girman matsayinsa yasa baya tareda ita wayama sai yasamu lokaci suke iya Yi Dan Haka Babu abinda Hanifan Bata Wasa dashi irin waya da marshal din Dan Haka bazata so ta rasa kiranba  takai hannu a natse ta dauka tareda nufar kofa ta bude ta fito ta kalli zainab dake kusa tace"

Miqawa Hanifa wayarta Ana Kiranta.

Karba zainab tayi ta nufi Hanifan da sauri ta miqa Mata cikin sa'a kuwa har lokacin Kiran Bai katseba tana ganin me Kiran ta dauka tana Kiran sunansa cikin tsananin kaunarsa da kowa ya shaida kaunace me girman gaske a tsananinsu.
#MAMUH#




*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_Ina masoyan Kuma mabiya littaffan zafafa biyar wainda sukai fice gurin kawo muku littafansu masu tsafta da ilimantarwa tareda nishadantarwa,_*
*_Wannan shekarar sun dawo muku da wani sabon salon Kamar kowane zuwan inda suka kawo muku dada'dan labaransu da bazaku taba Dana sanin biya ba,_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107
[1/9, 7:53 PM] +234 901 554 3771: *_DEEN MARSHAL_*
_Mamuhgee_



3
Komawa Naj din tayi Dan tayi sallah tana Shiga dakin tun kafin Hanifan ta qaraso dakin ta tayar da sallarta Dan tasan Babu ranar da zasuyi wayan Hanifan Bata hadasu ba suka gaisa Wanda daga ita harshi din basa buqatan gaisawar sbd shi dai Bai taba gaidata ba hakama itama batajin zata iya gaidashi din tun koba komai shine qani Amma gabaki daya matsayi dayake dashi da jin yazama billionaire yasa baya iya gaida mutane kokuma tace wasu mutanen tunda Yana gaida Hanifa da hajjo kakarsu,itadaima gabaki daya Bata wani buqatan shiga rayuwar kowa musamman irin tasa rayuwar wata iri kamar ta Mara kowa komai nasa yawanci kafin suji sunfara gani a labarai kullum koken hajjo da Hanifan rashin dawowarsa akai akai duk da dai taga kamar yafara sauyawa Dan yanzu Yana Dan yin kokari a shekara yazo so uku ko so biyu Haka.

Harta kammala sallar azahar data la'asar da aka gama idarwa lokacin Basu Gama wayarba wadda fiyeda Rabin harshen zancen turanci ne Hanifan keyi Dan Kamar yafi Kama bakinsa yanzu fiyeda hausarsa bugu da qari ma duk rayuwarsa yanzu idan Basu yakira bama baida Wanda zai Kira suyi yaren hausan sbd dad dinsu dai Yafi zama yanzu a Angola sbd tun wasu shekarun aiki da yayi acan bayan rasuwar mahaifiyarsu ya auri wata Yar can wadda gabaki dayama Bata wani Jin hausa Saida tahadu dashi ne ma tafara koya harta iya bayan auren danshi yasa ko dad din yakira sbd duk sun sama zama da yare yanzu Basu wani cika Yin hausar ba sai dai idan sun Kira su Hanifan da hajjon.

Kwashe dadduman tayi ta nade tareda zare milk hijab din datai sallan ta ajesu cikin wardrobe ta juya ta nufa water dispenser dake dakin nata Dan Shan ruwan dumi kawai ta matso ruwan dumi cikin cup tadawo ta zauna kan kujera tareda bude laptop dinta tana Sha tana duba saqon datace Sarah taturo Mata ta email.

Tana cikin aikin wayarta takawo haske tana vibrating ta dan kalla wayar ahankali da idanuwanta dake bayyanarda Bata buqatan Kiran kowa a lokacin taga sunan Dr sa'id ajikin wayar take ta saki ajiyar zuciya siririya sbd bazata iya sharesa ba kokuma nuna qosawarta dashi din sbd tsananin mutuncinsa datake gani dakuma yanda shima yake matuqar mutunta dakuma kulawa da ita.
Kallon Hanifa dake waya har lokacin tayi kafin ta dauki wayar tana amsa Kiran cikin taushin muryarta me zallar daukan hankalinsu sbd nutsuwa wadda sukafi daukanta da Jan aji tace"

Barka Dr sa'id.

Murmushi yasaki me Dan qaramin sauti daga nasa bangaren sbd yasan iya gaisuwarta kenan akoda yaushen 
Ita bame hayaniyar surutu bace Dan Haka cikin taushin murya shima yace"

Kinbar office kokuwa na biyo na kaiki gida?

Ajiye cup din hannunta tayi bayan ta qarasa shanye ruwan tana kallon screen din laptop din gabanta tace"

Nadawo tun kafin time din tashina yayi sbd Ina fama da Dan ciwon Kai
Thank you.

Ajiyar zuciya ya sauke boyayya kafin yace"

Sorry,
Ki huta to idan natashi Zan biyo na dubaki.....

Cikin nutsuwa ta katsesa da cewa"

No kadaka wahalan da kanka gurin zuwa ba stress ne kawai na Dan meeting din danayi Amma yanzu yariga ya wuce.

Ko Naj Bata fadaba yasan damuwan fitanar Abaas ce bataso Dan ya tabbatarda fitarsu jiyan saita kusa zautarda Abaas din Wanda shi tuni ma yake Masa kallon Mara lafiyar qwaqwalwa Dan wasu abubuwan dayakeyi sunfita daga dabiun lafiyayyun mutane,
Kishinsa na hauka ne bana mutanen dasukasan kansu bane,
Fitinarsa ta marasa ilimi da wayewa ne kamar wanda baida ilimin da wayewar,
Shi gabaki dayama ya rasa ta Yaya Macen datake da tsananin aji da sanin darajar Kai tareda wayewa irin Naj ta yadda da auren namiji kaman Abaas lamido,
Ta Yaya Allah yabashi irin wannan sa'ar me girma ta samun Naj amatsayin Mata.,
Shi Yana tsananin son Naj tareda sanin qimarta Dan Haka bazai taba cire Rai ga samunta ba matuqar ba aurenta aka daura din ba da Abaas shiyasa ma duk haukan Abaas din Bata damunsa Dan bayama gabansa shi Naj din ce kawai a gabansa Dan kuwa irin son dayake Mata idan ya aureta zai maidata sarauniyar rayuwarsa Dan kuwa zai tattaleta tamkar ita kadai yakeda ita a duniya.

Kashe wayar tayi tana ajewa daidai itama Hanifa na aje tata wayar ta dawo gurin Naj din ta zauna tana janye laptop din gefe tareda rufewa tana cewa"

Naj zamuyi mgana akan Abaas.

Fararen idanuwanta ta zubawa Hanifan tana cewa"

Wai Ni rayuwata shikenan kullum akan maganar rashin aure yake?

Ahankali Hanifa ta girgiza Mata Kai tana riqo hannayenta duka biyu cikin kulawa da tsananin qaunarta tace"

My beautiful Naj tasan cewa bantaba damuwa da rashin aurenta ba sbd nasan aure lokacine dashi Kamar mutuwa ta yanda idan lokaci yayi Babu mai hanawa ko tarewa,
A zuciyata dakuma adduata kullum shine Allah yasa wannan jingikirin yazamo babban alkhairi agareki,
Wlh banajin dadin yanda su dattijo da su Dadah suka sakomin ke gaba akan rashin auren Nan gashinan umma itama tabisu tana tsangwamanki da rashin aure.

Sai alokacin tasaki wani kyakkyawan murmushi tana kallon kyakkyawar fuskar Hanifan tace"

Bana damuwa da dukkanin zancensu na rashin auren 
Koba komai Baga Abaas Nan ba tunda sun saka auren 4month masu zuwa ai zancen ya mutu yanxu Ina Dan samun sauqinsu.

Bata fuska Hanifa tayi tana cewa"

Abaas lamido bazai taba auren Naj Dina ba matuqar bazai sauya hali ba.

Murmushi me sauti Naj din tayi tana riqota da murmushi akan fuskarta tace"

Kuma Kinga as long as Hanifan Naj bata Aminta dashiba Naj bazata taba aurensa ba.

Dariya suka saki lokaci daya sbd yanda haryanxu suke irin wannan wasar wa junansu
Hanifa tace"

Alqawarine ai kidainma Wasa da zancen,
Inshallah nice Zan tayaki zaban mijin danasan zai darajanta min ke tunda idonsu umma ya rufe Akan kowa Kika samu ki aura nikuma bazan yadda ba taqarasa tana 'yar dariya,
Kinga dama shima Marshal nafada Masa Ni Zan tayasa tantance Matar dazai aura sbd shima shine ya tsaya akan nayi aure da wuri sbd yanayin qarancin lafiyana kema kece Kika tsayawa Isma'eel sbd lokacin amininsa arfat yakawo kudin aurenki Kika ci amanata Kika bi bayansu Saida ya aureni da yanzu lukuman ne mijina ko?
Dariya suka kwashe da ita su biyun suna tunano lokacin musamman yanda Hanifan Bata wani so auren Isma'eel din ba Amma da hajjo da Naj din suka hade Mata Kai gurin Dad dinsu akai auren sbd dama ya dade Yana Sonta tun suna secondary school  sbd 'dan yayar dad din nasu ne 
Shima Marshal Isma'eel din yafi kwanta Masa sbd yasanshi sosai Yasan halayensa ba laifi Kuma shi Dama Wanda zai iya kulada Hanifan da lalurarta yake muradin ta aura din shiyasa.

Dan qaramin mayafi Naj din ta Dora akanta suka fito daga dakin har lokacin Fuskokinsu dauke suke da yanayi na dariyar tuna baya dasuka samu kansu 
Anty Amina ta kallesu tana cewa"

Hanifa ki fadawa hajjo yau ba hirar dare saidai gobe kayan umma dazata aika sako abekuta zamu hada.

 Anty Amina wannan fira taku keda hajjo ai yau kuwa zatayita mitan rashin firar Daren nan dakuke.

Fita sukai umma dai da guntuwar harara tabisu da ita Dan sun kasa gane abinda yake cin ranta,
Tsakani da Allah 'yarta Kamar Naj wadda kaf gidan tafisu ilimin Boko da wayewa tareda abun duniyama ace anyi sadakarta ga duk me rabo idan Batai aureba wlh zata mugun cutatuwa Dan kuwa ciwon zuciyama kamata zaiyi Amma hanifar datakeson ta karkato Mata Naj din tamafi naj din kasa fahimtarta tana ganin Kamar sun takurawa Naj din.

Dakin Dadah suka nufa tun Basu qarasa ba ta tsuke fuska Dan tana zaune kofar dakin kan kujerar roba da qaton farin glass dinta.

Dariya Hanifa tasake tana qarasawa gabanta da cewa"

Dadah my love.

Uwar harara dadar ta sakar Mata tana hararar gefen Naj tace"

Yaudarata za'a kenan?

Da sabuwar dariya Hanifa tace"

Mezaisa na yaudari Dadah me ran qarfe¿
Kawai dai dama......

Cikin hanzari dakuma zallar Kokonto Dadah ta katse Hanifan da cewa"

Wlh idan har kikacemun matsala yarinyar Nan tasamu da Abbas to wlh yau daga ita har uwarta kwanan bacin Rai zasuyi mummuna kuwa 
Kuma wlh gobe zuwa jibi suga 'danyan hukuncin dazansa Dattijo ya yanke Inga qarshen Boko da wayewa...

Zubawa Dadah fararen idanuwanta Naj tayi tana sauraron kalaman bacin Rai na fada na fitowa daga bakin dadar take tahau fada me tsanani Wanda yasa umma yin tsit daga aikin datakeyi Dan tana jiyo fadan Wanda aketa zubawa har ita ba'a ragawa ba qarshe ma korarsu tayi daga gabanta tana tabbatar musu da cewan aure da Abaas anyi angama idan Kuma shiyace yafasa da kanshi wlh auren sadaka zasuyi Mata can ta qarata da kyawun idanma shine take korar maza akansa.

Jiki a mace suka bar gurin suka fice gabaki daya Kai tsaye suka shige gidansu Hanifan Wanda gabaki daya Anguwar Babu kamarsa ga girma da kyau dakuma wani irin tsaro na musamman na sojoji Dan cikin gidan ma gate biyu kafin ka Isa ainihin cikin harabar gidan Wanda ke daukeda motoci na alfarma wainda ake sauyawa akai akai kusan guda shida a ajiye,
Uku na Marshal ne sai guda daya ta Dad dinsu sai daya ta Hanifan ce dayar Kuma ta hajjo ce wadda Bata cika hawa ba sbd Bata fita Sam Sam sai Dole Kuma driver ne yake tuqa ta,
Hanifa ma Sam Bata Jan mota sai Dole sbd yanayinta Wanda yasa dad dinta dashi marshal din suka qarfafa dokan rashin tuqin itama driver ne da ita sai Kuma idan zasu fita da Naj sai Naj din tayi driving.

Suna Shiga qaton palon su ruqayyat da Khadija dake palon suna gyaran yamma Wanda yake kamar Dole koba komai qaida sai sunyi gyaran safe Dana yamma suka Dan durqusa suna musu sannu da shigowo.

Kai tsaye palon dazai isar dasu dakin hajjo suka nufa suna shiga tana zaune makeken palonta me ado na qyallin arzikin duniya da Allah yabasu sanyin ac Dana qamshin turarukan wutan umman Naj daya Gama Kama koina na palon kujeru da curtains duk qamshin sukeyi me Dadi da sanyi 
'yar dattijuwar na zaune fara tas da ita me zubin hasken larabawa tana sanye da doguwar jallabiyar mutanen Kuwait me Fadi tana dagowa ta kallesu tasaki wani irin nutsatsen murmushi tana kallon kyakkyawar fuskar Naj da ako yaushe take sanyata murmushi Dan Kamar yanda take tsananin so da kaunar Jokokinta biyu rak Haka take tsananin so da kaunar Naj din musamman daya zama Naj din tazama tamkar jinin gidan itama danma Naj din taqi dawowa gurinta gabaki daya saidai yau ta kwana gidan jibi Kuma tace gidansu zata kwana danma Allah yasa Hanifa ko bayan datai aure Bata barsuba tana nan gidan saidai idan Isma'eel yazo gari ya dauketa su koma gidansu Yana komawa ta dawo Nan gida sbd duk da akwai Yan aikinta Hanifan hankalinsa Bai kwantaba daya barta ita kadai da masu aiki Dan yanayinta.

Zama gefen hajjo Naj tayi tareda kwantawa ta kwantar da kanta kan cinyar hajjon ta lumshe fararen idanuwanta tana sauke ajiyar zuciya ahankali tace"

Hajjona yau akan shimfidarki zanyi bacci.

Shafa kanta hajjo tayi cikin kulawa tace"

Kiyi hkr NAJMA kinji komai lokacine dashi rashin aure ba wata mummunar kaddara bace idan su dadan sun gaji da zamanki a gidan Ni subani inaso.

Murmushi kawai Naj din tayi tana cewa"

Hajjo idan aka baki Ni kema Zaki gaji da zamana ba aure wataran.

Murmushi kawai hajjon tayi tana kallon Hanifa da duk yanayinta bayada Dadi har lokacin akan fadan Dada Wanda akwai cin zarafi masu 'daci da yawa aciki.
#MAMUH#




*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_Ina masoyan Kuma mabiya littaffan zafafa biyar wainda sukai fice gurin kawo muku littafansu masu tsafta da ilimantarwa tareda nishadantarwa,_*
*_Wannan shekarar sun dawo muku da wani sabon salon Kamar kowane zuwan inda suka kawo muku dada'dan labaransu da bazaku taba Dana sanin biya ba,_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107
[1/9, 7:53 PM] +234 901 554 3771: *_DEEN MARSHAL_*
_Mamuhgee_



4
Anan gurin hajjo tayi niyar kwana Dan Haka Babu wata damuwa Kamar yanda tasaba rayuwarta na rashin riqe damuwan Abu ta sakewarta musamman dayake tanada daki daki me zamanta agidan a cikin babban palon hajjon wanda dakin Babu abin daya rasa najin Dadi da tsari musamman irin na rashin hayaniya da akasan Naj din batada ita Wanda hanifa ma anan dakin take yanzu idan tana gidan sbd tabaro part dinsu Dad dinsu tunda Babu kowa a part din.
Tanada Yan wasu kayan sawa a gidan Dan Haka Kai tsaye bayan sun Gama cin abincin dare Bata tsaya doguwar Hira ba Shirin bacci tayi bayan tayi sallah ta kwanta sai lokacin tabi misscalls din Sarah da Kira cikin nutsuwa tagama sauraran bayananta na aikin data bar Mata kafin ta Dora da cewa"

Ummm Naj dazu bayan tafiyarki Abaas yasake dawowa yasa an fiddo Masa da dukkanin record dinmu na aiki tun na January ya soke wasu daga ciki tareda fidda Kura kuren dazasu Iya bamu matsala Kuma Yana maganar a sauyani daga gurinki.

Dan sanyi muryarta tayi cikin bayyanarda rashin Jin dadinta tace"

Naj kiyi magana dashi please abarni agurinki sbd Ina barin gurinki na tabbatarda korata aikin zaiyi gabaki daya.

Ajiyar zuciya Me sanyi Naj din ta sauke tana tareda bude Baki cikin muryarta me Dadi Kai tsaye tace"

Karki damu zanyi magana dashi gobe
Kawai dai ki ringa kiyaye Masa tunda Kinga yanayin kalar fushinsa baya tunani me kyau idan ransa ya baci.

thank you Naj.

Ok then see you tomorrow"Naj din tafada tana kashe wayar tareda ajewa gefe tana Dan zamewa daga jingine datake akan gadon ta kwanta tana lumshe fararen idanuwanta ta rufe tana Dan yin bacci.

Hanifa dake zaune tana kokarin Kiran wayar mijinta tana sauraron wayar da Naj din keyi ta Dan saki guntin tsokin baqin cikin Abaas din datakeson koyawa zuciyarta Aminta dashi amatsayin mijin 'yar uwar tata tun yanzu.
Kashe wayarta tayi tareda miqewa ta zagayo tahau gadon ta kwanta tunda takasa samun Isma'eel din ga Naj shegen miskilancinta wani lokacin baya barinsu yin wata doguwar fira.


Qarfe 8 na safe ta fito wanka daure da towel me kauri tanaji wayarta na ringing Taki ko kallon inda take ta nufi gaban madubi tafara shafa Mai Wanda dama kusan komai product daya suke amfani dashi itada Hanifan.
Shiryawa tayi cikin doguwar riga maroon ta daura qaramin gyale akanta ta fito tana qamshin turaren Vivian rosalle har lokacin Hanifa na kwance sbd ciwon wuya data tashi dashi Wanda dama kullum cikin ciwuka take sbd sikla ce lafiyarta qarantacciyace sun Saba da rauninta shiyasa qaninta marshal baida wani abinda yafi komai so a duniyarsa bayan ita sai kakarsa tukuna mahaifinsa.

Dakin hajjo tafara zuwa har lokacin hajjon Bata farka ba itama Dan Haka Kai tsaye ta wuce kitchen su ruqayyat na ganinta cikin girmamawa sukace"

Ina kwana Anty.

Lafiya kalau ruqayyat 
Please ku hado breakfast din Hanifa akawo daki batajin dadi.

Fridge ta qarasa ta bude ta dauko madara ta zuba a cup tareda zuba ruwan zafi aciki tayi dumi ta zuba Zuma kadan aciki ta dauka ta shanye ahankali tareda aje cup din ta koma ta  diba dabino uku taci ta fice daga kicin din su ruqayyat suka bita da kallo Kamar dai yanda suka Saba sbd mamakinta har kullum Baya sakinsu na yanda take komai nata cikin wani irin burgewa da qaidojinta da nata ita ta shardantawa kanta su sbd maintaining rayuwarta.

Kalar abincin datake duk da gidansu ba masu halineba ta qayyade abinda take ciwa cikinta Wanda yake kamar dieting ne takewa kanta sbd gabaki daya rayuwarta batason abinci me nauyi tun tana yarinya Haka take idan taci abinci me nauyi sosai Yana wahalar da ita shiyasa data girma ta San yancin kanta tanada abubuwan datake ci kawai da wainda bataci Wanda shima yake qara bayyanarda miskilancinta da burgewarta da wasu ke gani acikin gidansu kuwa suna daukan hakan amatsayin nuna wayewa da nuna kudi Wanda yasa mazan ke ganin tafi karfinsu Ana samun matsalar fasa aurenta Kashi Kashi Kuma Sam Bata nuna damuwar hakan shiyasama ta tabbata dai itace Bata tashi aurenba inji su Dadah da Dattijo.

Cikin kulawa ta taimakawa Hanifa da wuyan ya riqe Mata sosai kamar ba lafiya ta kwanta ba tasamu ta danyi breakfast sai alokacin takira Dr said Wanda shine likitan Hanifan ta sanar dashi.
Dayake yanason ganin Naj din sai yace zaizo yakawowa Hanifan magani kafin ya wuce aiki.

Kafin Dr said din yazo taje dakin hajjo ta gaidata tareda Hado Mata ruwan dumi da Zuma Wanda itace hajjon ta koyawa Naj din Sha kasancewan itama abincin masu nauyi Basu cika Bata lafiyaba.

Bayan ta dan sha ta dago ta kalli Naj din tace"

Zaki tafi office ne?

Da fararen idanuwanta ta Dan kalli hajjon ta maida kallonta kan agogon dake daure a hannunta tana cewa"

Eh Amma ba yanzu ba Ina jiran Dr sa'id ne zai kawo maganin Hanifa wuyanta ya riqe Bata iya motsawa.

Dan numfashi hajjon ta sauke tana Dan jinjina Kai irin na manya tace"

Yau Kuma da riqewan jijiya ta tashi
Allah yabata lafiya.

Amin Naj din tace tana miqewa sbd ganin Kiran Dr sa'id akan wayarta.

Kamar dai yanda yasaba da gidan da dukkanin iyalan gidan tareda farin sani da securities na gidan sukai Masa   amatsayin likitan Hanifan yasa Yana zuwa Kai tsaye aka bude Masa qaton gate din gidan yashigo har ciki da motarsa Amma iyakacinsa gate din farko baqi basa shigowa da motocinsu gate na biyun Dan Haka Yana parking ya fito yasake gaisawa dasu Mike ya wuce ciki Kai tsaye.

A babban palon farko na gidan ya tsaya Wanda yake matsayin na baqi ya zauna bayan su ruqayya sun kawo Masa ruwan black tea suna tiriri sun ajiye Masa kenan saiga Naj din ta fito ta qaraso tareda zama kujeran dake kallon tasa Tai Masa kallo daya ta Dan dauke Kai tana cewa"

Barka da safiya Daddyn Naufal.

Wani irin kyakkyawan murmushi ya sauke sbd a duk lokacinda takirasa da dadyn Naufal zancen na tsumasa sbd hakan na nuni ne da kusanci a tsakaninsu har wani lokacin Jin yake inama ace itace mahaifiyar Naufal din.

Kwarjininta yasa duk yanda mutum yaso baya iya Mata kallon qurulla Wanda shima wani lokacin hakan nasashi Jin fargaban zai iya mallakar Naj din kuwa Dan dai gskian magana bakowane namiji ne zai iya cika idon Naj din ba haryayi Mata irin kallon tsaf kona qurullaba saidai kuwa idan shima nasa kwarjinin ya take nata ne hakan zai iya yiyuwa.

Dan numfashi ya sauke Yana janyo qwazonsa na namijin daya ciki ya sake kallonta yace"

Barka da fitowa Naj.
Ya hajjo ta tashi lfy?
Yasu umma ma?

Alhmdlh" tafada a taqaice tareda sake kallonsa tace"

Maganin Hanifan.¿

Miqa Mata qaramar ledan maganin hannunsa yayi Yana cewa"

Kada a shafa Mata komi agurin Tasha maganin kawai saita gasa jikinta da ruwan dumi shikenan zai sake.

Ok bari nabata maganin yanzu coz tana buqatansa yanzu Nan.

Ta dauka lokaci sosai kusan awa daya kafin tafito cikin shirinta tsaf na zuwa office ta fito daga gidan gabaki daya tashiga gidansu cikin sa'arta Dattijo baya Nan bare maganar fadan jiya na Dadah ya tashi Dan Haka Kai tsaye sassansu ta nufa 
Ummanta na daki tana ayyikanta taje ta gaidata umman ta Gama yimata Gore goren da tariga tasaba dasu ta fito suka hada ido da anty Amina dake zaune tsakar gidan tana waya Ta taso tana kashe wayar suka shiga dakin Naj din tana sake bayyanar Mata da kada kalaman umman su daga Mata hankali tacigaba da rayuwarta cikin salama sbd Haka Allah ya tsaro Mata ba komai bane rashin auren da wuri tunda su ganshinan sunyi sun fito din.

Murmushi kawai Naj tayi tana cewa"

Anty Amina Ni wlh kinmafi bani tausayi sbd fadan umma akan fitowan Nan Taki.

Kiji yarinya ke bakiga tausayin kankiba 
Duk rigimarsu gwarani nayi harna tara yara nafito
Gwara dai kiji tausayin kanki kisamu kiyi shine rufin asirin.

Wani murmushin kawai tasaki tareda daukan abubuwan dazata dauka ta fito ta fice 
Tana fitowa ga mamakinta Dr sa'id na Nan waje Yana jiran fitowarta ya ajeta office Dan batason doguwar hayaniya yasa kawai tashiga suka wuce Amma cikin ranta tana Dan fatan kada su tadda Abaas a ALFA'S din sbd bazata iya daukan hayaniyarsa da fitinarsaba  ciwon Kai kawai zai sakar Mata na Wunin gaba daya.
#MAMUH#




*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_Ina masoyan Kuma mabiya littaffan zafafa biyar wainda sukai fice gurin kawo muku littafansu masu tsafta da ilimantarwa tareda nishadantarwa,_*
*_Wannan shekarar sun dawo muku da wani sabon salon Kamar kowane zuwan inda suka kawo muku dada'dan labaransu da bazaku taba Dana sanin biya ba,_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107
*_DEEN MARSHAL_*
_Mamuhgee_


5
Duk yanda Dr sa'id yaso suyi mgn Bata yiyuba sbd ganin motar Abaas lamido na cikin gurin hakan ke tabbatarda Yana Nan Kuma ko ayanzu Haka yasan Yana iya ganinsu daga sama ta office dinshi
Shi kansa baya buqatan iya zallan wulaqancin Abaas din a bainar jama'a bakuma Dan komai ba sai Dan Naj dayasan tana iya kokarinta gurin tolerating din Abaas din Wanda gabaki daya Bai cancancetaba Kota Ina Sam sam Allah ne kawai ya bashi babbar sa'ar samunta idanma shine ya aurentan kenan Dan shima Bai cire raiba yanama Dan ji a jiki jikinsa Kamar shine ma me sa'ar aureta din kowama ya huta.

Fitowa yayi ya zagayo zai bude Mata ta bude da kanta ta fito da Dan guntun murmushi akan fuskarta tace"

Thanks Dr.

Jinjina Kai yayi Yana kallonta yace"

Atashi lafiya.
Ya juya ya koma cikin motarsa ya tada yabar gurin bayan tuni ta shige alfas din Sarah dake jiran isowarta ko Dama Bata hayeba tana qasa tana Nan reception tana jiranta sbd bazata fara isaba it's kadai Dan shakkar Abaas zai iya Mata komai kafin Naj din taqaraso bazata iya ba gskia Dan yanda ya qware agurin cin zarafin mutum ta yanda duk hakurinka da dannewarka sai ranka yayi mummunan baci zata iya kasa hkr ta maida Masa mgna saidai ya koreta aikin Amma sbd Naj yasa itama take kokari tana hadiyewa tareda jinjinawa jarumta da qarfin zuciya irin na Naj datake hadiye maganganunsa.

Ma'aikatan dake gurin na qasa da Naj din gaidata suka hau yi suna Mata barka da isowa ta amsa musu tana wucewa kaman yanda ta Saba suka wuce Sarah na gefenta tana fada Mata Abaas yariga ya iso yau tunda safe ya iso office din.

Suna Isa cikin office dinta ta ajiye handbag dinta tareda waiwayo ta kalli Sarah dakyau kafin ta bude Baki tace"

Sarah daga yau banason maganar Abaas a office please 
Zuwansa da rashin zuwansa duk bana buqatan sani okay??

Yes ma'am.

Juyawa tayi tana Shirin zaunawa aka turo kofar aka shigo 
Sarah ce kawai ta juya tana ganin Waye ta Dan matsa gefe tana cewa"

Good morning chairman.

Ko kallonta baiyiba ya qaraso ya zauna kan sofa dake office din tana ganin Haka ta sulale ta fice bayan ta ajewa Naj laptop dinta.

Har lokacin Naj dake tsaye Bata juyoba tana hankalinta nakan wasu takardu dake hannunta ta sai qamshinta me sanyi da Dadi dayaketa sake gauraye office din Hadi da sanyin AC Wanda suke qara qona zuciyar Abaas din.

Dagowa yayi ya kalleta tareda zubawa fuskarta dakeda wani irin sanyin kyawu da nutsuwa tareda wani irin fizgar mutum ido kafin ya taso ahankali ya dawo gabanta ya tsaya Kai tsaye yace"

Meyasa Dr sa'id ne kawai zai kawo office?

Dan dagowa tayi ahankali ta kallesa tareda rufe takardun hannunta din ta ajiye ta koma ta zauna a natse tareda fiddo wayarta daga jaka cikin muryarta me kamewa tace"

Yaje duba Hanifa ne ya wuto Dani.

Rintse idanu yayi cikin qoqarin controlling zuciyarsa yace"

Kullum bashida aikine saina zuwa dubata kokuwa itace kullum batada aiki saina kwantawa ciwon dashine zaije Yana dubata ta yanda ke Kuma zai ringa kasancewa dake kokuwa nine da akewa kallon Mara hankali akeson shashantarwa da wannan zancen kullum"" ya qarasa fada Yana Dan daga murya sbd maqura da bacin ran nasa yake qara kaiwa.

Wannan karon kallon mintuna biyu cif tayi Masa tanason fahimtan idan Abaas din Yana lafiya kokuwa sbd kalamansa sun Sosa ranta Dan kuwa kamar Yana cin zarafinsu ne daga ita har Hanifan.

Kamar bazata tankasa ba saita dauke kallonta daga kanshi tace"

Zaifi idan ka tsaya da rashin fahimtanka a iya inda ka Saba kawai.

Cikin fushi yace"

Alaqarki da likitan Nan ta wuce dukkanin hakurina sbd Naga kin sabarwa kanki iya zama cikin motarsa Dan Haka tunda kin yanke zama taxi motar kowa saiki zaba tsakanin Ni ko shi waye Dan bansan ya alqarku zata cigaba da kasancewa ba bayan munyi auren....

Jajir idanuwanta sukai saidai har lokacin Bata dago ta tankasaba saima hakan yaqara qunan zuciyarsa yaci gaba da fada cikin maganganu masu dacin sauraro Amma taqi sake ko dagowa ta kallesa hakan yaqara lalata duk wani sauran hakurinsa ya fice ransa amatuqar bace.

Harya Gama ya fice tana zaune a inda take da wayarta a hannunta tana dubawa,
No Hanifa takira Bata daukaba Dan Haka takira no hajjo taji Yaya Hanifan take hajjon ta sanar da ita cewan wuyan dai Bai sakiba har lokacin.

Sama sama tasamu tayi wasu ayyukan ta tattara tabar office din Takoma gida  sbd hankalinta gabaki daya yakoma kan Hanifa sbd tasan yanayin ciwukanta yanzu a Haka saita share kwanaki wuyan a riqe.

Tana Isa Kai tsaye gidansu Hanifan ta sauka Koda ta iso jikin yadan qara tsanantawa Hanifan Dan Haka kamar dai koyaushe itace tareda ita,itace tasan ciwonta da damuwarta da kulawa da ita bayan hajjo wadda itakuma tsufa yazo Mata bazata iya wani abun ba.,
Tun suna secondary Naj tasaba da kulawa da Hanifa sbd duk gata da tarin dibbin dukiyardasu Hanifan suke dashi basa tareda kulawa ta wani Dan uwa,
Masu aiki sune komai nasu sai hajjo wadda itama dai komai masu aikin ne keyi idan har Hanifa na buqatan kulawa da soyayya irin ta uwa to agurin umman Naj ne take samunta sbd umman da mahaifiyarsu aminai ne Suma tun yarinta shiyasa ma Suma suka taso Kamar umman ce uwarsu,
Umma na tsananin qaunar Hanifa Wanda yasama Hanifan kejin qarancin rashin uwa fiyeda DEEN Wanda shi asalima ko uwar tasa Bai saniba sbd gurin haihuwarsa ta rasu shiyasa ta taso a wani irin miskilallan mutum na qarshe sbd bai taso cikin hayaniyar taron mutane ba tun fara high school dinsa yabar qasar Yana Hawaii acan yayi karatunsa acan yake rayuwarsa ta matsayin babban Navy marshal Wanda zallan iliminsa da yakaisa acikin shekarunsa da basuyi yawa ba hakan Kuma yasa da yawa manyan mutanen Nigeria dake can harma Dana wasu qasar suna kawo sha'awan son hada zuria dashi saidai haryanzu kaman Shirin aure baya gabansa Dan baitaba sha'awan aure yanzu ba duk da hajjo da Hanifa sun fara nuna damuwarsu akan hakan Amma Yana dakatar dasu baya buqatan su takurawa junansu shiyasa ma basa matsa Masa sosai da maganar Dan sanin bayason yawan nanata zance.

Umman Naj itace ta raini Deen din tun bayan rasuwar mahaifiyarsu har Saida ya girma yakai shekaru biyar kafin yafara kwana gidansu ahaka ahaka harya koma gidansu gabaki daya sbd lokacin dad dinsu yayo aure shiyasa a duniyarsa bayan hajjo da Hanifa da dad dinsa umma itace uwa wadda tabashi so da qauna ta uwa duk da itama umman ta Saba sosai da halinsa na ko inkulan tun Yana yaronsa saidai duk yadawo Yana zuwa har cikin dakinta ya zauna tayita kulawa dashi danma yanzu sbd yawan gidan nasu yasa ya daina Shiga idan yazo saidai tayi girkin abincin dayafi so ta aika Masa daga baya taje har palon hajjo acan suke Yar firarsu ta uwa da 'da.


No din Dr sa'id Naj takira saidai Bai daga ba Dan Haka tayi tunanin Yana aikine kokuma yashiga CS Dan yawanci hakan kesashi barin waya office Dan Haka Bata Bata lokaciba tasake hada ruwan dumi ta gasawa Hanifan jikinta tareda sake Bata magani gashi duk yanda taso Hanifan taci abinci takasaci qrshe dai da kanta ta hado Mata ruwan dumi da Madara da Zuma tasamu ta iya Sha tayi bacci.

Saida Hanifan tayi baccin tasamu ta tube tafada toilet tayi wanka tayi sallah tafito palon hajjo ta nufi dining ta zubo spaghetti kadan da salad tadawo ta zauna gurin hajjo suna Yar firarsu akan rashin lafiyan Hanifan da  tuni Dad dinta yafara Kira sbd hajjon data fada Masa 
Shima Isma'eel mijinta tun Naj na office yake Kira sbd Hanifa Bata daukan wayan kowa.

Tana Gama cin abincin kicin kenan saiga ummanta tashigo tareda zainab Yar gaban goshinta ayanzu kenan 'yar anty Amina.

Zama umma tayi ita Kuma zainab Naj ta miqa Mata plate din hannunta tana cewa"

Ki Kai kitchen.

Sosai umma ke girmama hajjo tamkar mahaifiyarta Dan Haka firarsu suka Dora daga nan Naj na gefe tana aiki a laptop dinta saiga Kiran Abaas yashigo wayarta ta dauke ido daga kan wayar tana cigaba da aikinta yasake Kira Bata daukaba har so uku ko kallon wayar Bata sake yiba.

Sai yamma sosai bayan ma Hanifa ta farka su umma suka tafi Takoma gurin Hanifan wadda video call din marshal yashigo wayarta daidai shigowan Naj din.

Qarasowa tayi gurinta tana Kiran sunanta cikin taushin muryarta tana cewa"

Yaya wuyan?

Nuna tayi Mata da wayarta ahankali tana cewa"

Please ki amsa mun Kiran.

Kallon wayar Naj tayi taga sunansa baro baro ajiki takai hannunta ta dauka wayar tana dawowa gefen Hanifan ta zauna ahankali tareda daukan Kiran ahankali kyakkyawar fuskarsa ta bayyana akan wayar Yana zaune palon gidansa dake _Honolulu Hawaii US_ sanye cikin black three quarter da black armless shirt dasuka matuqar bayyanarda hasken fatarsa data Gama renuwa acikin hutu da lafiya sai daukan ido fatar jikinsa takeyi sbd yanayin kayan dake jikinsa dauke Kai Naj tayi tareda miqawa Hanifa wayar tana tashi daga gurin Dan gidansu takeson Shiga Dan Haka Kai tsaye ta fice.

Wayarta ce kawai a hannunta ta fito daga gidan ta nufi kofar gidansu ta shige ta nufi sashensu Kai tsaye saidai tana Shiga ta tadda Dattijo tsaye ga Dadah a zaune hakama ummanta dukkaninsu suka zubo Mata ido Banda ummanta da abun duniya ya taru yayi Mata yawa idanuwanta sun kada sunyi jajir da alama dai ba lafiya ba.

Qarasowa tayi cikin nutsuwa tace"

Dattijo Ina wuni,
Dadah barka da yamma.

Ko kallonta dadan bataiba sbd wannan karon tsaf tagama shirya duk wani rashin arziki da Naj din Bata tunani akan wannan maganar.

Kallonta Dattijo yayi da kyau Yana gyara tsayuwa da gyaran murya yace"

Ki saurareni da kyau kiji abinda Zan fada Miki sbd nafadawa mahaifiyarki kalma bayan kalma Amma Naga kamar ke din kinason watsar da maganar Kamar yanda kike watsi da masu neman aurenki,
Nafada naqara fada wallahi tallahi wannan karon kika Kori abbas da halinki yace yafasa auren Nan wallahi duk Wanda nasamu aura Miki zanyi bazaki maida wata a gidan Nan ba,
Yafara gajiya da halinki yazo ya sameni dazu ransa amatuqar bace na bashi hakuri akan za'a matso da bikin Nanda wata daya ma ayi a huta Dan Haka acikin watan Nan daya Kikai Masa abin dayasa yafasa wannna auren keda mahaifiyarki ku shirya hukuncina dazai biyo baya.

Daga fadar Haka ya juya ya fice Bai qara da komaiba sbd bacin ran al'amarin auren Naj din dayake kaisa maqura.
#MAMUH#



*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_Ina masoyan Kuma mabiya littaffan zafafa biyar wainda sukai fice gurin kawo muku littafansu masu tsafta da ilimantarwa tareda nishadantarwa,_*
*_Wannan shekarar sun dawo muku da wani sabon salon Kamar kowane zuwan inda suka kawo muku dada'dan labaransu da bazaku taba Dana sanin biya ba,_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107[1/14, 3:31 PM] +234 901 771 2720: *_DM 6_*
Shiru ummanta tayi zuciyarta na suya da bacin rai da damuwa hadda sirkin takaicin Naj din wadda take ganin duk itace take qara tsimar da duk wani bacin Rai dake faruwa tsakaninta da Dattijo da Dadah wadda ita kaf duniya Bata ganin laifin kowa akan rashin auren Naj face ita mahaifiyarta sbd ganin suke idan su Naj tana Shure maganarsu ta lalacewar da neman aurarrakinta keyi it's uwarta ta tsaya ta ganar da ita Amma Ina ganin suke itacema take qara daure Mata acewarsu hamshaqin dayayi mugun ci ya tada wuya suke jira Wanda Allan daya halicceta yafita sanin cewan wlh a duniya tafi kowa farin ciki da qaunar ace yau taga 'yarta Naj tayi aure kodan irin daukan ido da fizgar maza datake dashi Amma saigashi qaddara ta Allah tasa duk kyawu datafi Yan zuriar gidan kowa yayi aure yabarta hatta qannenta da dama wainda suke Yan uba dama na dangi sunyi aure sun barta.

Ahankali Naj din ta juyar ta nufi dakinta ta Murda kofar ta bude tashige a Karo na farko dataji zancen Dattijo akan rashin aurenta ya daketa badan komaiba sai Dan yanda ako yaushe ake Dora laifin akan ummanta wanda keda kalamai na cin zarafi.

Bakin gado ta zauna ahankali tareda sauke numfashi tana Dan dafe goshinta ta lumshe ido tana tunanin itafa duk yanda akaso tayi aure da yanda ake ganin kamar taqi auren bazata jawo namiji da aura ba da qarfi Amma meyasa su basa gane hakan?
Shin menene akewa maza su tsaya su aureka Wanda ita Bata saniba ko shine yasa ake fasa auren nata bayan dai tasan acikin wainda sukai neman aurenta suna fasawa kowanne tana Dan iya nata kokarin gurin kulasa da Yar sake fuska tana iya kokarinta gurin aje miskilancinta ta kulasu yanda ya kamata Amma duk da hakan suke fasa aurenta bayan kowannensu Saida ya Aiko magabatansu dayanma har fara bikin anyi aka fasa sakamakon Wai yagano gabaki daya taba sonsa Bata taba sonsaba kawai aurensa zatayi Dan Ana cewa Bata aure.
Wannan shine yafi konawa Dattijo Rai aduk cikin masu neman aurenta suna fasawa sbd har Gama komai anyi Amma zancen ya watse tun akan wannan al'amarinta yaqara baqanta ransa shiyasa yanzu ya dage ya tsayawa Abaas sbd kada shima ya fasan duk da kuwa yagama karantar halayen Abaas sunada matuqar wuyar zama sbd zafin ransa yasa wani lokacin harshi rufe ido yakeyi Yana fada Masa magana musamman daya Gama gano sun Kai maqurar matsuwa a son aurarda Naj dayasa suke lallabashi shiyasa yasamu damar yimata duk kalar abinda yaga dama sbd yasan kome zaiyi baza'a fasa auranba tunda auren akeso ido rufe.

Anty Amina ce tashigo dakin ranta Babu Dadi itama sbd tsakani da Allah suna Jin zafi da 'dacin dukkanin wani fadan cin zarafi da akewa mahaifiyarsu saidai Kuma Babu yanda zasuyi tunda mijine agareta hakama Dadah uwace to Amma Kuma meye laifinka Kai idan anqi aurenka¿

Cikin nutsuwa anty Amina ta zauna kan kujeran madubin dakin ta kalli Naj din a natse tace"

Najma hakuri Zakiyi ki daure ki Kuma qara daurewa da halayen Abbas ayi auren Nan ki huta da wannan fitinar umma ma ta huta da wannan fitinar muma masu gani zuciyoyinmu na daci mu huta,
Idan Kuma kina ganin bazaki iya auren Abbas din ba ki dakatar dashi Kai tsaye saiki bawa Dr sa'id damar fitowa sbd yamafi Abbas din cancanta da mutunci tareda nutsuwar aura tako Ina,
Auren Abbas tabbas idan ba wani rahaman ubangiji babu ta inda zaku samu nutsuwa tako Ina Dan zafinsa yayi yawa kekuma miskilancinki yayi yawa zaku wahala ku duka.

Kallon anty Amina ta dago tayi da fararen idanuwanta dasuka Dan sauya Wanda iya Nan kake iya ganin damuwarta sai Kuma ahankali ta saki Dan guntun murmushi tareda bude Baki tace"

Nagode anty Amina.
 
Shiru sukayi tsawon mintuna biyar kowa kowa da abinda take tunani cikin ransa kafin ta miqe ta fice daga dakin Kai tsaye ta nufi dakin ummansu dake zaune kan kujera shiru da alama damuwace take cinta bakuma yanda zatayi tunda itama tayi iya yinta bazata jawo mijiba ta daurawa Naj din aureba duk abinda sukeji Dole Haka zasuyita daurewa suna hadiyewa har Allah yakawo ranar auren.

Qarasowa tayi gaban umman wadda sai alokacin ta dago a sanyaye ta kalla Naj din ta dauke Kai tana cigaba da tunaninta.

Zama Naj tayi gaban umman tareda riqo hannayenta tana kallon fuskarta ta bude Baki ahankali tace"

Umma kiyi hakuri kadaki saka damuwa aranki,kinada ilimin addini umma kinsan cewa aure lokacine da ubangiji ya dibar maka wlh idan lokacin Nan baiyiba bazakayiba meyasa kike damun kanki da abinda su Dadah ke fada bayan kinsan kinamun addua Kuma insha Allah zanyi auren kila Wanda Allah ya zabarmun ne a mijin Bai bayyana ba kokuma kila lokacin ne haryanxu baiyiba da saura idan Kuma auren ne Allah baice nayiba harna bar duniya Yaya zakuyi da hukuncinsa?
Umma addua kawai Zakiyi Allah yasa hakan shine mafi alkhairi gareni dakuma iyayena.

Kallonta umman tayi idanuwanta na kadawa jajir sbd tabbas su yayanta basusan irin mugun zama da cusgunawa tareda tozarci da hantarar datake samu daga dattijon har Dadah akan wannan al'amarin,
Ta dauka,ta hadiye,ta danne,ta shanye,ta boye duk wani mugun wulaqanci da tozarcin dasuke Mata akan al'amarin Wanda matsi da fitinarsu yasa taji Kota Yaya sotake Naj din tayi auren kowama ya huta kishiyoyi masu Mata dariya su daina Yan gidan masu zundenta su daina,yan matan gidan masu cewa ilimin Boko da aikin office yasa Naj taqi auruwa duk kowa ya daina a zauna lafiya,
Da wanne zataji gata da tsohuwar bazawara a Naj din.

Sake kallon Naj tayi da idanuwanta dake jajir har lokacin ta bude Baki Kai tsaye da sanyin murya tace"

Najma nasan aure lokacine Amma Kuma Allah yakawo Miki mijin meyasa bazaki lallabashiba har ayi auren tunda dai haryanason auren naki¿
Abbas dinnan duk halinsa dakike gani idan anyi auren lallabashi Zakiyi zai sauya shikenan kowa ya zauna lafiya.

Zubawa umma ido tayi akaro na farko tana Jin dacin hukuncin ummanta ahankali ta bude Baki tace"

Umma halayen Abaas ba masu lallabuwa bane.....

Ta Yaya Zaki yanke hukuncin ba masu lallabuwa bane tunda Baki auresan kin gani ba saidai idan shima kinada Shirin sakawa ya fasa auren Dan shima kina ganin bekai bane kaman yanda mutane suke fada.

Da mamaki ta sake zubawa umman ido tace"

Umma idan Kuna tunanin naqi aurene Dan akwai abinda nakeso agurin namijin dazan aura Kuna kuskuren fahimatar halayena da kuka sannu dasu duk da karatun danayi da da wasu cigaban Dana samu hakan Sam bayada alaqa da rashin aurena...

To ki amince da Abbas kawai ayi auren Nan idan ba hakan bane Najma sbd idan dukiya da rayuwa ne Abbas din yanadasu Kuma Yana tsananin sonki idan harkin daukeni mahaifiyarki.....

"Umma kadaki Bari fushi yasa ki lalata rayuwar Naj mana." Anty Amina ce ta fada hakan tana isowa gaban umman Wanda idanuwanta suka rufe gabaki daya.

Naj kasa cewa komai tayi sai idanuwanta dake kan umman sunyi jajir ahankali ta dauke idonta ta bude Baki tace"

Zan aura Abbas idan har hakan Kika zabarmun.
Juyawa tayi ta fice daga dakin gabaki daya tana shiga dakinta wayarta kawai ta dauka ta fito ta fice.

Dadah dake zaune tsakar gidan tana Jin duk hayaniyar tasu farin ciki yacika ranta tunda tasan yanzu Kam Naj din bazata bada matsalaba tunda Zuciyarta ta karye da abinda umman tayi Dan Haka ta tashi Takoma dakinta a Daren zata fadawa Dattijo ya sanarda Abbas ya sanarwa iyayensa za'a matso da bikin Nanda sati uku ko biyu ayi ayi kowa ya huta Dan kaf zuriar gidan Naj din ce kawai ta riqe a gabansu batai aureba da wuri.
#MAMUH#




*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_Ina masoyan Kuma mabiya littaffan zafafa biyar wainda sukai fice gurin kawo muku littafansu masu tsafta da ilimantarwa tareda nishadantarwa,_*
*_Wannan shekarar sun dawo muku da wani sabon salon Kamar kowane zuwan inda suka kawo muku dada'dan labaransu da bazaku taba Dana sanin biya ba,_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107
[1/14, 3:33 PM] +234 901 771 2720: *_DM 7_*


*_GA CHANNEL DIN DAKE YOUTUBE NAN👇🏾_*

https://youtube.com/c/sudaiskura

_Sudais is a young boy who has passion in recitation of the Holy Qur'an at a very young age._

_Please help him grow his YouTube channel by subscribing and liking his videos to encourage the little boy._

_PLEASE SUBSCRIBE_



**********
Kodata dawo Hanifa tasamu komawa bacci Dan Haka Kai tsaye toilet ta Shiga tayo alwala tafito ta tayarda sallah.
Tana idarwa Shirin kwanciya tayi Dan batajin tanajin yunwa har zata kwanta ta fito ta nufi dakin hajjo 
Tana Shiga kallo daya hajjon tayi Mata ta karanto yanayinta cikin kulawa dakuma tsananin qaunar data kewa Naj din tayi Mata hannu datazo ta kwanta kan cinyarta 
Naj din ta qarasa ta kwanta qasa tareda Dora kanta kan qafafun hajjon ta rufe ido ahankali tanajin zuciyarta na samun nutsuwar data kasa samu daga gurin iyayenta.

Saidata fara bacci ahaka kafin hajjon takira sunanta ahankali tace taje ta kwanta a godonta 
Ta bude idanuwanta tareda tashi zaune ahankali ta miqe tana cewa"

No hajjo zanje na kwanta da Hanifa sbd jikinta.

Shikenan kije Saida safe kiyi bacci karki saka damuwan komai aranki Allah ya tashemu lfy.

Amin"tace tana ficewa dakin.

Washe alhmdlh daga ita har Hanifa lafiya kalau suka tashi Hanifa wuyanta ya sake Takoma garau dinta dama Haka take yanzu lafiya yanzu ciwo,kokuma yanzu ciwo yanzu lafiya.
Itama sakayau ta tashi ba wani yanayi na damuwa kokuma dake nuna tana cikin wani hali sbd ta riga ta yarda ta yanke shawaran auran Abbas Dan Haka ta kauda bayyana damuwa a fuska da yanayinta sbd hajjo da Hanifa dasuka samu saqon an saka ranar auren an maida sati uku masu zuwa Wanda dad din Hanifan ne yakira hajjon ya sanar Mata sbd Dattijo ya kirasa ya sanar dashi Dan komai na harkan auren Naj da dad din akeyi sbd suna basa girmansa da matsayi na uba agareta sbd baitaba banbantataba da yarsa Hanifan tun daga karatun primary kuwa har zuwa yanzun.

Ranar bataje aiki bama Koda hajjo ta zaunar da ita akan maganar auren ta tambayeta akan tafada Mata gaskia idan batada ra'ayin auren Abbas din tasa dad yayi mgn dasu Dattijo a fasa 
Tacewa hajjon ta amince da auren Abbas da raayinta ba Dole su dattijon sukai Mata ba.
Hanifa ma tayi tayi akan suyi maganar Amma tace Mata subar maganar ayi auren ahuta.
Dole suka haqura sunaji suna gani aka hau fara shirye shiryen auren gadan gadan.

Tunda aka fara wannan maganar Bataga ko shigowar saqon Abaas dinba a wayarta bare kiransa Wanda Bai wani dameta ba sbd tasan dama za'ai hakan Dan Haka ta tattara dukkanin alamarinsa ta cire akai ko a office Basu hadu ba sbd dama gabaki daya Bata zuwa office dinsa shine me zuwa nata to tunda yaga tagama shigowa hannunsa tunda zata zama matarsa saiyayi watsi da ita shima saima wani basarwa yakeyi a yanda Sarah take fada Mata yasa dokar shigar maza office dinta matuqar ba'a zo anfara tambayarsaba Koda kuwa aikine.
Hakan ya Bata mamaki sbd kaman rashin tunani yashigo al'amarin nashi Dan hakama Ana saura sati biyu bikin tafara hutun bikin auren dazatayi ta daina zuwa office.

Gidansu kuwa sosai da sosai aka hau shirin wani irin gagarumin hidima sbd bikinta kowa yasaka Masa burin holewa tunda sunsan za'a kashe dukiya sbd alaqarta da gidan tsohon marshal Alfa shiyasa suka hau shiri da anko anko na biki kala kala Wanda ita amaryar ma gabaki daya komai baya gabanta mamakinta daya har lokacin Abaas Bai taba kirantaba.

Dadah kuwa farin cikinta da murnarta a bayyane suke ba wani shamaki sai ji takeyi da Naj din tana lallabata hakama Dattijo manyan kudi tako Ina sai shigosa sukeyi sbd Alfa ya sakar Masa kudin hidamar auren fiyeda tsammani ga hajjo ma data tanadarwa Naj dukiyar aure ta musamman shiyasa kowa sai qara rikicewa yakeyi da harkan bikin.

Ummarta tuni tahau aikin gyaran 'yarta sbd dama gyaran amare aikintane Dan Haka yanzu da Abu yake nasu ba kissa ko kadan gyaran Naj din takeyi ta ciki ta waje abinka da kyakkyawar farar mace tuni tafara sauyawa sosai Dan kuwa har wani daukan ido takeyi.

A duniya qawayenta biyu ne daga hanifanta sai Sarah Dan Haka kullum Sarah na gidan sunata shirye shirye Wanda Hanifan ce ke komai itadai nata ido da Kuma Dan murmushin yaqe Wanda babushi ko kadan cikin zuciyarta.

Saida akai saka lallenta kafin aka kawo kayan lefe mota biyu Wanda yasa gidansu yasake daukan bidiri suna sake yadda da Naj dama me kudin ta tsaya jira duk da hakan dai sudai sunyi murna musamman ummanta data ringa sadaka tana ciyar da mabarata sbd Allah yasa wannan karon 'yarta tayi aure.

Ba gidansu Naj din kawaiba ya cika da baqin nesa Dana kusa ba hatta gidan Alfa yasamu saukar isowar Dad Alfa din tareda matarsa da sabbin masu aikinta datazo dasu har guda biyu sai babba 'yar yayarta datake riqo tun tuni wato _HANNA_ Wanda take wata irin wayayyiya datake ji da kanta da Kuma kyau da Allah yayi Mata itama wadda asalin irin son datakewa  Marshal Deen ne yasa tadawo hannun mum Malika saidai hakan be wani taimaka ba sbd takanyi shekara Bata ganshi ba duk da kuwa iyayen nasu sunsan da maganar so a tsakaninta da marshal din Dan Yana kulata ba laifi shiyasa akeda maganar da yiyuwar aurensu gashi Kuma yanzu sun dawo gida gabaki daya da zama tasan yana zuwa Nan akai akai fiyeda can gurinsu sbd Hanifa da hajjo Dan Haka Suma gidan yanzu zai rayu tunda su dad din sun dawo.

Sai yamma sosai Naj tasamu damar fitowa gidansu ta tafi yiwa dad Alfa sannu da zuwa kodata fita mutanen dake waje sai binta da kallo sukeyi sbd yanda tasake wani irin washewa
Tsakani da Allah dai kowa ya kalleta saiyace Abbas yayi dace da kyakkyawar sa'a.

Tare suke da Hanifa dan haka Kai tsaye sashensu dad da mum Malika din suka nufa.

Babban lafiyayyan palon farko suka yadda mum Malika zaune tana waya tana ganinsu ta saki murmushi tana sallama da Wanda take wayar ta miqa musu hannu tana cewa"

Oh our beautiful bride is here
Naj you're looking morethan beautiful.

Murmushi me qayatarwa tasaki tana cewa"

Thank you mum Malika kun iso lafiya?
Ya gajiyan hanya?

Alhmdlh alhmdlh hanya alhmdlh.

Kallon Hanifa tayi dayake ita tunda suka iso tazo tana tareda dad Alfa tace"

Hanifa I'm so happy for Naj 
Allah yasa albarka a wannan auren.

Amin mum.

Congratulations Naj.

Thank you mum Malika.

Hannah ce ta fito sanye cikin doguwar riga Mara dogon hannu kanta daure da wani Dan qaramin scarf da tsadaddiyar wayarta a hannu tana dubawa tana ganinsu ta qaraso da murmushi akan fuskarta tana zama gefen Hanifa tace"

Sister in-law Hanifa barka da shigowa I've been looking for you tun dazu hajjo tace kuna gidansu Naj.

Murmushi Hanifa tayi tana kallonta tace"

Dazu nashigo kina ciki kina wanka 
Ya hanya?

Lafiya kalau sis Hanifa.

Maida kallonta tayi kan Naj dake duba massage din Sarah akan Wai Abaas ya  dakatar da ita daga aiki.

Fuskar Naj din ta zubawa ido tana kallon kyan fuska Dana jiki da Allah yabawa Naj din ta gangara da idonta kan hannayenta dake farare tas kamar Bata aikin komai dasu gashi Tasha gyara tako Ina fatarta sai glowing takeyi 
Dama can Naj na tsananin burgeta sbd tanason Abu me kyau ita shiyasa take tsananin son Marshal dinta ga wani aji da Naj din takedashi kamar ba Yar masu rufin asiri ba Dan Haka ta saki qayataccen murmushi tana kallonta cikin tayata murna tace"

Naj mijinki dinnan yayi sa'a
Congratulations to you Allah yabaku zaman lafiya.

Murmushi Naj tasaki tana kallon Hannah din tace"

Amin nagode Hannah.

Palon dad Alfa suka nufa inda suka samesa zaune Yana waya Dan kusan jama'arsa da yawa zasuzo daurin auren Yana ganinsu yasaki murmushi Yana kallon Naj datake murmushin Dole sbd saqon Sarah yabata matuqar mamaki shiyasa ta yanke shawaran Kiran Abbas din zatayi tana fita taji dalilinsa na korar Mata Sarah.

Zaunawa sukai Banda ita Naj din data zauna a qasa cikin biyayya da farin cikin zuwansa tace"

Dad Alfa barka da zuwa,ya Hanya?

Alhmdlh Najma ya hidiman?
Babu dai matsalar komai ko?

Babu komai Inshallah.

To shikenan Allah yasawa auren albarka yasa agama taron lafiya.

Hanifa ce tace Amin kafin suka Dora da zancen tahowar da Marshal zaiyi Wanda tun kafin suyi nisa Naj ta miqe tana cewa"

Zan Dan karba waya" ta fice.

No Abaas din ta Nemo Kai tsaye tareda Danna Masa kira tahau ringing.
Harta katse Bai dagaba ta sake Danna Masa Kiran sai akaro na uku ya dauka da cewa"

Hello.

Kai tsaye da muryarta me taushi tace"

Maganar office ce zanyi dakai akan Sarah ko Zan iya sanin abindaya faru ka dakatar da ita?

Takaicin zancen nata yaji Dan dama Yana sane yayi hakan Dan kuwa idan ba hakan yayiba yasan wlh har abada Naj bazata taba kiransaba har ayi auren kuwa to Amma yanzun data Kiran sai abin yabasa takaici ko gaidashi bazata iyayiba sai magnar Sarah Dan Haka cikin baqin ciki Kai tsaye yace"

Bana wannan maganar sai a office"

Kashe wayarsa yayi Yana sakin numfashi me zafi tareda komawa jifa da wayar Yana Jin tafasar zuciya.
Jin bazai iya hakura ba yasa ya zari key din motarsa ya fice daga palon mahaifinsa Kota cikin gidansu Bai bi ya fice sbd gidan Suma cikeda jama'ar biki.
Itama akaro na farko dataji bazata dauka wannan wulaqancin nasa ba cikeda takaici ta fasa sake kiransa ta wuce gidansu ranta a Dan jagule.

Washe gari akai gagarumar taron walima kawai sbd gabaki daya Naj din batada raayi na biki sbd komaima yafita kanta har akai waliman aka gama Bata cikin wani dadin zuciya sbd batasan me Abaas din yafadawa Dattijo ba yakirata itada ummanta a Daren yayi musu wani irin fadan cin zarafi duk da ummanta na cikin farin ciki na hidimar bikin Saida tayi kwanan bacin Rai.
##MAMUH#

*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107[1/14, 3:33 PM] +234 901 771 2720: *_DM 8_*
Washe gari kodata tashi miscalls din Dr sa'id biyar tagani a wayarta da text na cewan zaizo yau din yanason Mata fatan Allah ya Sanya alkhairi batai replying nashi ba sbd ganin massage din tun safe yayi Dan Haka ta share akan sai ya zo din.

Yau Bata leqo gidansu ba tunda tatashi tana tareda Hanifa data tashi da ciwon qafafu Dan Haka sai yamma tasamu fitowa ta da dogon hijab har qasa ta mask a fuskarta ta nufi gidansu inda acan tayi wani wankan ta shirya cikin wani brown lace riga da skirt saiga kiran Dr sa'id ta yafa gyale ta fito fuskarta ba kwalliyan komai sai Kohl dake cikin fararen idanuwanta.

Ko data fito Kai tsaye gidansu Hanifa ta shiga sbd tasan Yana ciki baya tsayawa waje musamman irin yanzu da komai zai iya faruwa.
Sabbin qarin securities tagani a waje da cikin gate na farko na gidan tareda ganin sabuwar motar gidan dake rufe a fili da alamun anfita da ita hakan yasa ta fahimci cewan DM na iso kenan ta Dan waiwaya hanyar sashen dayake matsayin nasa acikin gidan kafin ta dauke Kai ta qarasa sashen hajjo daidai shigowar Kiran Abbas tana gani taji bazata daukaba Dan Haka ta kashe wayar gabaki daya tana Shiga palon Kai tsaye.

Hajjo ce zaune a palon sai Dr sa'id shima suna maganar qafafun Hanifan daya duba ta kallesa tana cewa"

Dr barka da zuwa.

Kallon quralla yaso yimata Amma sbd hajjo na gurin yasa ya taqaita kallonsa fuska a sake yace"

Barka Amarya,ya hidima?

Murmushi kawai tayi tana qarasa dakinsu Kai tsaye tashige tana kokarin sake kunna wayarta Bata tsaya koina ba sai bakin gado ta zauna tana Kiran sunan Hanifan batareda ta dagoba.

Dakatawa tayi da abinda takeyi Jin shiru tareda Kuma qamshin turaren _TOM FORD Tobacco Vannile_ daya Gama gauraye dakin sanyin qamshinsa ko Bata dago ba tabbas tasan kodai DM Yana dakin kokuma yashigo ya fita sbd tsadar turaren kawai yasa Babu Wanda zata canka bayan shi Dan Haka ta miqe ahankali tareda juyowa akaro na farko idanuwansu suka shiga cikin na juna a bazata Yana zaune kan sofa gefen Hanifa da farin cikinta yasa ta daina Jin ciwon gabaki daya daga ita har shi Naj din suka zubawa ido
Ta dauke nata idon tana Dan dauke Kai daga kallonsa ta bude Baki Kai tsaye cikin dan sake fuska tace"

Barka da zuwa JALAL.

Dauke idanuwansa yayi daga kanta cikin muryarsa me Kai tsaye yace"

Ya hidima? Allah ya Sanya alkhairi.

Amin" tace Kai tsaye tana juyawa ta fice tana cewa"

Hanifan zanyi magana da Dr sa'id kafin kigama okay.

Tana fitowa palon Dr sa'id ma yagama mgna da hajjo suka fito zuwa harabar gidan inda suka tsaya suna mgna tsawon mintuna suna Shirin fita saiga taga Dr sa'id na kallon bayanta ta waiwaya ahankali daidai qarasowarshi zai wuce zuwa sashensa lafiyayyar fatarsa tana haskawa hakama qaqqarfan jikinsa dayake geaming yagama budewa tako Ina ta yanda duk qwaqwarka bazaka gano shekarunsaba sbd mugun miskilancinsa da kamewarsa dasuka shige da shekarun nasa Dan kuwa ko Dr sa'id daya girmesa da kusan shekaru shida koma fiye Yana ganin tsananin kwarjininsa da cika idonsa Wanda yasa manyansama suna bashi girman hakan.

Dauke Kai tayi suka nufi gate suka fito har jikin motar Dr sa'id din ta rakasa Tai Masa godiya harya wuce ta juya zata shiga gidansu saiga motar Abaas Tasha gabanta tana ganin hakan ta rabe ta shige gidansu sbd akwai jama'a sosai a waje musamman sbd securities din DM dasuka qaru suka cika layin gashi goben ne daurin aure batason hayaniya tasan tsaf Abaas din zai iya Tara musu mutane a wajen.

Cikin soron gidansu ya fincikota a matuqar hasale yace"

Me wancan likitan yazo Yi gurinki a Daren gobe aurenki shiyasa kenan naketa Kira kina qin dauka karshe Kika kashe min waya kokuwa abinda ba'a qarasa bane aka qarasa kokuwa hankalina da Kuka Saba rainawa  wayo keda gidan riqonki dasuka koya Miki rayuwar qarya zaki sake cemun wadda tafi kowa ciwoce yauma batada lafiya yazo.......

Cikin tsananin bacin ran data dau lokaci tana dannewa ta Kira sunansa ta Dan daga murya idanuwanta dasuka sauya akansa tace"

Abaas kasan abinda kake fada sbd tsawon lokaci Ina kokarin daukan jahilcinka a matsayin kuskure da bacin Rai amma abinka Yana yin yawa
Kana qetare iyakarka da yawa
Kaje kawai banason Yin wata magana dakai karka Tarawa kanka mutane anan sbd idan halinka ya bayyana anan banajin iyayen nawa da kake bugun gaban su suka baka aurena zasu aurar maka Dani din so please just leave from here.

Juyawa tayi idanuwanta jajir zata bar gurin ya fizgota da qarfi take rigar jikinta tayi mummunar yagewa saiti da kirjinta Navy blue bra din dake ciki ta ta bayyana gabaki daya tana waiwayowa ta daukesa da wani irin mummunan Mari idanuwanta na cikowa da wasu irin hawayen baqin ciki 
Hanifa dasuka iso tareda DM data janyo Dan zuwa gurin umman sunkirata a waya zata fito soron DM yanason ganinta itama idanuwanta cikeda hawayen bacin Rai ta sake saukewa Abbas din Mari tana daukewa umman Naj din ta sauke Masa nata barin itama hawaye na gangarowa daga idanuwanta.

Marshal kuwa dauke idanuwansa yayi daga gefen sbd jikin Naj din dake bayyane koda Abaas ya dago jikinsa haryana rawa sojojin DM sukai Masa muguwar damqa suka jasa waje Yana fizge fizge suka wuce dashi daidai dawowar Dattijo ya qaraso soron ganinsu cirko cirko 
DM na ganin Haka ya juya ya fice sbd yasan hayaniya za'ayi.

Aikuwa Dattijo da idanuwansa suka Gama rufewa sbd dai ko iya abinda yagani yasan Babu shakka wannan auren sunansa Babu 
Baqin ciki da takaici daya Gama dunqulesa ko magana baiyiba ya kalli ummanta da idanuwanta sukai jajir yace"

Bazance komaiba Amma wallahi tallahi ku sani matuqar gobe tayi Abbas suka fasa auren Nan wlh duk Wanda nasamu daura Miki aure dashi zanyi.

Juyawa yayi ya wuce tsabar bacin Rai idanuwansa ko gani basayi Sosai.
##MAMUH#


*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107
[1/14, 3:34 PM] +234 901 771 2720: https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share




*_DM 9_*


*_MG's SKINCARE_*
*_Ina manyan Mata da manyan yara masu buqatan gyaran jiki da fata akan tabbaci da ingancin kyawu da aikin me kyau kuzo ga mg's skincare inda sukeda nagartattun sabulai da creams masu kyau da aiki,_*
*_mg's skincare nada black soap dasu molato soap hakama akwai gangariyar sabulu na musamman Mixed na Molato/black soap Wanda hadinsa da aikinsa karshene sbd mun gwada mun tabbatar 💯_*

*_Akwai Kuma herbal whitening black soap Wanda shima aikinsa na musamman ne,_*

*_Saikuma beauty kit gbdy nagyaranjiki su cream dakomai ne acikin shi,_*

*_Then akwai bridal kit  shima abu 6 be aciki Wanda sai angwada za'a San kayan MG skincare qarshe ne agurin aiki._*

Chat
08062991549
07046881166
07067210195
Call 
08064532391
Instagram: glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare
Location:kaduna buh we deliver Nationwide
Delivery is not free buh gamasu sari ko wnd yasiya Kaya dayawa kmn 20k above there will be free delivery+ gift


 _*sannan sunada different varieties of frames gamai siyan daya Koh sari*_
_*Sannan muna karban order gamasu hidimar biki kmn dg abinci, snacks,juices nd so on*_
_*Kindly chat with us via 08062991549.*_




************
Rungumeta Hanifa tayi idanuwanta zuciyarta na tafarfasa ta zare gyalen jikinta ta yafawa Naj din ajiki ta Jata ahankali zasu shiga cikin gida ummanta da idanuwanta sukai jajir zuciyarta na Mata wani irin tsananin nauyi Dan Bata buqatan tabbaci tasan auren Naj yasake rushewa kenan da nauyin murya tace"

Kuyi can gidan Hanifa kada kishiga Nan da ita akwai mutane zasu fahimci abin daya faru Kuma komai zai iya faruwa sbd wannan abun daya faru yanzu kuje can kawai tana buqatan kadaici Nima Ina buqatan nutsuwa.

Kallon umman Hanifa tayi cikeda damuwa tace"

Umma ke fa?
Ran Dattijo ya baci kada cikin mutane yayi Miki fada.

Bakomai kuje kawai kuje.

Juyawa tayi ta shige Dan ko kallon Naj takasa sbd tsananin baqin cikin halinda Naj din take ciki.
Sake rufeta Hanifa tayi tajata suka fice tana gani waje kowa ya rabe Yana kallo sojojin DM suka ja Abbas din daga cikin gate na biyu sukai Masa wani irin mugun duka sai gashi Yana ihun ceton Kai Dan azaba gashi me gidan nasu tuni yashige abinsa bare yace su barshi Haka Dan Haka sukai Masa iya Yinsu Saida akaje da gudu aka sanarda Dattijo ya fito cikin tsananin tashin hankali har Yana mugun tuntube zai kife ya ceci Abaas din Wanda baqar zuciyarsa batasa yayi nadamar abin dayayiba saima kallon kawu da yayi da bakinsa fal jini cikin tsananin baqin ciki yace"

Naj ce tasa amun wannan" daga Haka Bai qaraba ya juya ya fada motarsa Yana dafe gefen cikinsa dake Masa mugun ciwo yakasa Jan motar sbd ko gani bayayi sosai Dan take fuskarsa tayi wani irin tashi Kamar burodi Dole jiki na rawa kawu yakirawo jamilu dansa dake cikin gida yazo ya Kama mishi Abbas din suka maida baya jamilu yaja motar kawu na gaba suka nufi asibiti da Abaas din Dan kuwa tuni ya kumbure musamman bakinsa daya baje.

Tunda suka Iso palon hajja Kai tsaye Naj daki ta wuce idanuwanta jajir Bata buqatan komai da kowa a yanzu tunani kawai takeso abarta Dan hakan yasa Hanifa Bata bita dakinba ta zauna Palo tareda sauke wata nannauyan ajiyar zuciya ranta amatuqar jagule itama.

Kallonta hajjo tayi tace"

Meya farune naganku haka? lafiya kuwa?

Kai tsaye Hanifa ta fada Mata abindaya faru tana qarawa da cewa"

Dattijo shi laifin umma yagani 
Ummanma tanacan cikin tsananin damuwa ko wannan karon dai anfasa auren Naj.

Hajjo sosai itama zancen ya mummunan Bata ranta tace"

Ina yiwa Najma adduar alkhairi akan aurenta aduk sallata Dan Haka inaga hakan shine mafi alkhairi gareta Allah yakawo Mata mijin daya fisa.

Amin"Hanifa tace jikinta amatuqar sanyaye idanuwanta sai cikowa sukeyi da hawaye tana maidawa sbd Allah yasani batason Abaas da Naj to Amma Kuma da aka fara hidimar bikin nan bazataji dadin wargajewar auren Naj dinta akaro na maimaci.

Har dare Naj na kwance a daki idanuwanta rufe kaman me bacci saidai ba baccin takeba Dan Babu ta yanda zata iya bacci duk cikin aure aurenta da ake fasawa Babu Wanda ya dasu ta Hanya mafi Muni Kamar wannan.
Har dare Babu me dadin Rai acikinsu anan gidansu Hanifa Abu komawa yayi Kamar na zaman makoki Dan kuwa murna da farin ciki sunkoma damuwa da baqin ciki amma dai lokacin basusan menene zai farun gobe ba yiyuwar auren kokuwa¿
Hajjo data Kira Umma ta Dan Mata maganganun kwantar da hankali tareda sake tunatar da ita daukan qaddara me kyau da sabaninta Yana daga cikin zaman cikakken me mumini me Imani Dan Haka kada ta damu sosai tayi addua kafin safen Allah yasa suji alkhairi idan fasawarce alkhairi idan Kuma yin auren.
Cikin rauni da tsananin damuwa Umma tace"

Na yarda da qaddara hajjo Amma tayaya Dattijo zai lalata rayuwarta ta hanyar aura Mata wani cikin fushi idan ikirarinsa yazama gaskia rayuwarta zata iya lalacewa a qarshe dai auren da aka dage da sai tayin baiyi Rana ba kenan.

Inshallah rayuwar Najma bazata lalace Alfa bazai Bari a lalata rayuwar Najma ba zanyi magana dashi idan har sun fasa auren a hakura Allah zai kawo Mata wani.

Sai alokacin Anty Amina dake dakin Naj da Babu mutane tareda umman taji abin daya faru hankalinta yayi mummunan tashi cikin damuwa da Dan tsoro ta kalla idanuwan umman dake son cikowa da hawaye a raunane tace"

Umma Dan Allah kada kiyi kuka wannan jarabawace Allah kewa Naj Inshallah zata cinye.

Sauke Kai umma tayi tana girgizawa ahankali cikin tsananin baqin ciki da damuwa tace"

Wannan jarabawatace Nima sbd Ina cikin wani hali na tsananin baqin ciki da damuwar rashin auren Naj
Dadah bazata qara Bari nasha ruwa gidan Nan ba cikin kwanciyar hankali 
Ga Dattijo Yana rantsuwar aurar da ita ko duk Wanda yasamu wannan karon tayaya Zan iya kwantar da hankalina da hakan?.

Zama Anty Amina tayi itama tana rafka tagumi cikin tashin hankali da tsoro ta bangare daya tana adduar Allah yasa kada Abbas din yafasa sbd duk halinsa gwarashi an sanshi idan yafasa ba'a San wa dattijo zai aurawa Naj din ba tunda yayi rantsuwa to tabbas kowa yasamu zai iya daura mata Dan Haka ita dai anata gwara Abbas din dai ko yayane.

Ta bangaren Dad Alfa hajjo takirasa yazo tayi Masa bayanin komai ta dora da cewa"

Auren wannan yaro ga yarinya Mara hayaniya da nutsuwa Kamar Naj Sam baiyiba Kuma hakan ya nuna Babu da'ar sanin darajar mace data aure atare dashi Dan Haka idanma su Basu fasa din ba kayi magana da Dattijo a hakura afasa bashi auren.

Shiru Dad Alfa yayi Yana nazarin maganar wadda ta Sosa ransa matuqa shima sbd yanajin Najma tamkar Hanifa Dan Haka Aure Kam kosu Abbas Basu janyeba babushi Dan idan har zai iya yaga Mata rigar mutunci Haka acikin gidan iyayenta tun kafin aure bayan aure al'amarin bazaiyi kyau da dadin ji ba Dan Haka take ya yanke shawarar neman Dattijon tun Daren suyi magana hajjo ma tace"

Idan ka aika kiransa zakuyi magana ka kirani Nima zanyi Masa mgn Dan kada ya qarfafa abin sbd hankalin Fatima umman Najma din ya tashi matuqa da hukuncin dazai yanke.


A asibiti su kawu sai kame kamen zancen ban haquri yakeyiwa mahaifiyar Abbas da qanin babansa Dan mahaifinsa ya rasu Yana Basu hakuri da Basu tabbacin bayan daurin auren gobe za'a zauna ayi magana.
Hajiyar Abbas da ranta yagama mummunan baci ganin yanda kamannin danta ya sauya lokaci guda take ta rufe ido tace wallahi tallahi ko 'yar gwal ce Naj danta bazai auretaba Kuma bazasu yarda ba saisunyi shari'a dasu dattijon akan wannan dukan da akaiwa Abbas dan kuwa zata saki dukiya iya dukiya sai an hukunsu.

Kawu najin Haka wani irin dunqulallen baqin ciki ya tsaya Masa a zuciya ba Dan qarar datace ba sai fasa auren da akai Wanda dama jikinsa yabasa za'ai hakan.
Danne baqin cikinsa yayi yaso qanin mahaifin Abbas din yabashi dama suyi magana ta maza a fahimci juna idan yaso bayan an daura auren ayi maganar wannan Amma Sam shima abin Bai Masa ba ace anyiwa ango duka a gidansu amarya wannan al'amarin babbane.

Kallon Dattijo alhajin yayi a natse yace"

Alhaji Ibrahim katafi kawai maganar Nan bazata yuyuba yanzu sbd halinda shi Abbas din yake ciki maganar auren Kuma a goben dai gskia bazai yiyuba saidai ko kila gaba.

Shiru Dattijo yayi zuciyarsa na quna da tarin baqin ciki,
Shi shikenan kullum cikin gayyata yake Yana Tara mutane Ana fasa aure har sai yakai ya gayyata ba'a zuwa.
To anyi na qarshe da yardar Allah.

Juyowa sukai suka fice daga asibitin suka tari adaidaita sahu suka shiga Babu me cewa qala dagashi har jamilu Wanda shima fasa auren Bai Masa Dadi ba sbd baiga abin fasa aurenba idan an zauna anyi magana Amma sun dauka zafi har suna maganar qara da shari'a Wanda zaice Dan basusan a Ina akai dukan bane da bazasuma fara kawo maganar qara da shari'ar ba Dan kuwa yanasa ran sojojin Marsha ne sukai dukan bama na Alhaji Alfan ba bare ace da sauki.

Koda suka iso gida Saida Dattijo sukai sallar ishai a masallaci kafin yashiga gida dake danqam da hayaniyar Yan biki dasuka zozzo cikinma da yawa zuriar wasu Basu zoba sbd sunsha zuwa bikin Naj din Ana fasawa shiyasa ba kowane yasamu zuwaba.

Gurin Dadah ya aika jamilu yace yakirata sbd zancen bazai yiyu acikin gidanba dayake da mutane ko Ina.

Dadah dake zaune tana Shan radionta cikin kwanciyar hankali ta kalli jamilun daya fada Mata Dattijo na son mgna da ita ta kalli fuskarsa tsaf taga ba wata annushuwa jikinta yabata ba lafiya Allah yasa ba abinda yasaba faruwa bane,ta kashe radiyon tareda miqewa da hijabinta dake jikinta ta nufi kofa tana tafiya ahankali irin ta tsofin da qafafunsu Basu cika wata isashiyar lafiya ba ta nufi waje batareda kowa yasan ta fitar ba.

Dattijo dake tsaye Yana jiran isowarta Kiran alhaji Alfa yashigo wayarsa dama shima gurin nashi suka nufa ayi maganar gabaki dama Dan Haka Dadah na qarasowa yace"

Dadah muje can gurin Alhaji Alfa ayi maganar sbd Nan akwai mutane yanacan Yana jiranmu.

Dadah najin Haka tun Basu qarasaba take cewa"
Ibrahim maganar auren Naj din ce Babu ko?

Shiru yayi zuciyarsa a jagule Bai amsaba har Saida suka Isa cikin babban palon gidan na baqi suka zauna dama Alfa na palon shida hajjo suna Kiran isowarsu.
##MAMUH#




*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107*_DM 10_*

*_MG's SKINCARE_*
*_Ina manyan Mata da manyan yara masu buqatan gyaran jiki da fata akan tabbaci da ingancin kyawu da aikin me kyau kuzo ga mg's skincare inda sukeda nagartattun sabulai da creams masu kyau da aiki,_*
*_mg's skincare nada black soap dasu molato soap hakama akwai gangariyar sabulu na musamman Mixed na Molato/black soap Wanda hadinsa da aikinsa karshene sbd mun gwada mun tabbatar 💯_*

*_Akwai Kuma herbal whitening black soap Wanda shima aikinsa na musamman ne,_*

*_Saikuma beauty kit gbdy nagyaranjiki su cream dakomai ne acikin shi,_*

*_Then akwai bridal kit  shima abu 6 be aciki Wanda sai angwada za'a San kayan MG skincare qarshe ne agurin aiki._*

Chat
08062991549
07046881166
07067210195
Call 
08064532391
Instagram: glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare
Location:kaduna buh we deliver Nationwide
Delivery is not free buh gamasu sari ko wnd yasiya Kaya dayawa kmn 20k above there will be free delivery+ gift

_*sannan sunada different varieties of frames gamai siyan daya Koh sari*_
_*Sannan muna karban order gamasu hidimar biki kmn dg abinci, snacks,juices nd so on*_
_*Kindly chat with us via 08062991549.*_


**********
Cikin girmama Alfa ya kalli Dadah bayan sun zauna a mutunce yace"

Dadah barka da zuwa ansaki fitowar dare ko¿Sannu da kokari.

Ba dole nafitoba Alhaji Alfa tunda dai Haka Allah ya rubuto Dani na tsufa lafiya da 'yayana Amma matsalar jikoki na neman sakamun ciwon damuwa.

Gaisawa sukai da hajjo tana sake Mata sannu da hayaniyar taron jama'a kafin shima Dattijo ya gaida hajjon ya maida kallonsa kan Alhaji Alfa damuwarsa na bayyanuwa gabaki daya yafara magana da cewa"

Alhaji Alfa duk da bansan dalilinka na son magana daniba a a Daren Nan Ni Ina daukeda magana me girma dazan fara fada maka akan daurin auren gobe.
Bansan menene taqamaimai abindaya faruba a dazu Amma dai a yanda nasamu bayani daga bayan Nan shine Najma da mahaifiyarta sun taru sunyiwa yaron Nan Abbas wulaqanci hakama sojojin JALALUDDEEN sukai Masa duka yanzu Haka Yana asibiti a kwance a taqaice zance dai iyayen yaron Nan sun fasa auren Nan.
Naso su fahimceni mu tsaya ayi maganar fahimta Amma ita mahaifiyar yaron ta dauki zafi sosai qarshe dai qanin mahaifin nasa Alhaji Abubakar yace ayi hakuri da maganar auren Nan yanzu Bai sanarwa gaba ba Wanda Ni nasan Babu wata gaba Dan kuwa bazasu taba dawowa ba Dan Haka qarshen maganar zance dai aure babushi ya fasu ba maganar daura aure gobe da Abbas.

Shiru dukkaninsu sukai gurin yadauki tsit na wasu mintuna kowa zuciyarsa ba Dadi musamman shi Dattijo da tasa zuciyar quna takeyi tana 'daci.
Sauke Kai Dadah tayi tareda fashewa da kukan da baya fita sosai tace"

Innalillahi-wainna ilaihirrajiun
Wannan jarabawa nada nauyi ya Allah kabamu ikon cinyewa yasa Allah Fatima da Najman Susan kansu suke cutatarwa tareda mu da Allah ya Dora Mana nauyinsu.

Karkice Haka dadah sbd hakan Suma ba laifinsu bane musamman Fatima zatafi kowa farin cikin ganin 'yarta tayi aure Dan Haka bazata Rusa auren yarta da ganganba musamman da aka kawo wannan gabar ta auren kawai ake jiran daurawa gobe" hajjo ce me bawa Dadah hakuri da wannan kalaman.

Shidai Dattijo shiru yayi yakasa cewa komai sbd tunanin shawarar abinyi goben.

Gyaran murya Alhaji Alfa yayi tareda tattaro nutuwa yace"

Dadah hakurin da aka Saba da tawakkali shi za'a sake dauka sbd shima Abbas din Allah baiyi shine mijinta ba Wanda a hakikanin gaskia harda wasu halayensa dana samu labarinsu yanzu yasa saidai kawai muce Allah yazaba Mata mafi alkhairi,
Sai maganar itace kokuma mahaifiyarta suka lalata auren wannna duk bashine abin dubawaba kawai Allah ne baice yazama mijintaba Dan Haka Dan Allah ayi hakuri a dauka hakan kawai a matsayin wata jarabawar 
Sai maganar taron jama'ar da aka gayyato na nesa Dana kusa na daurin auren goben sai a sanar da cewar an daga auren abawa jama'a hakuri....

Sai alokacin Dattijo ya bude Baki Yana dagowa daga soken da kanshi yake tun dazu yace"

Maganar taron gobe Inshallah za'ai daurin auren tunda Allah Bai qaddari anyi dashi wanda aka tsaro dashiba na yanke goben Zan daura Mata da Mubarak sbd tun farko ma hakan yakamata muyi tunda auren na waje Bai samuba sai ayi na zumunci a rufawa Kai asiri dama shine qarin abinda dayasa nace Zan nemaka a Daren Nan na sanar da kai hukuncin Dana yanke sbd Kota bangarenka idan akai dubi da irin manyan jama'ar qasar nan dazasu zo daurin auren gobe Dominka idan akace anfasa bazasuji dadiba Dan Haka wannan shine nawa hukuncin.

Share hawaye Dadah tayi tana cewa"

Wannan hukuncin yayi gwara ayi Dana gidan Allah yasanyawa abun albarka....

Cikeda bayyanarda damuwa hajjo tace"

Mubarak yaushe akai aurensa da za'a Kuma daura Masa wani auren inace iyakacinsa wata t
Bakwai da aure hakama Najma din gabaki daya Bai kamata ayi Mata aure irin wannan ba Dan ba laifinta bane itama tanason tayi auren Amma Bata hakaba.

Numfashi Dattijo ya sauke Yace"

Mubarak ne me aikin Yi me Dan girma acikin mazan gidan Kuma tunda kamawa tayi Haka zai hadasu su biyun da matarshi ya riqe Amma Kam da yardar Allah Najma tagama zama tana Kore mazan aurenta rantsuwace akaina da alqawari danai Mata daga ita har mahaifiyarta akan wannan karon Inshallah wlh natara jama'a aka fasa aure bazan Bari ayi abanzaba Zan aura Mata duk Wanda ya samu da wannan rantsuwar akaina Amma suka taru suka shure maganata Dan Haka auren Najma gobe da yardar Allah ba fashi za'a daura.

Cikin sanyin murya sbd jikinta daya Gama mutuwa gabaki daya da al'amarin Dadah tace"

Allah yasa hakan shine mafi alkhairi Amma dai banason ayi abinda zai Kuma kawo matsala idan aka fita wannan Dan Haka daga waya ka Kira Mubarak a fara sanar dashi zancen aji ta bakinsa kada ayi abinda zai janyo wata fitinar.

Zallar bacin rai ne da takaici suka Danni zuciyar hajjo ace yarinya Kamar Naj Ana Shirin yimata auren wulaqancinda sai Ankira Mubarak an tambayeshi bayan kowa yasan cewa zaiyi bayaso tunda duka duka yaushe yayi aure da matarsa wadda take yarinyace qanqanuwa sosai bayan cin zarafi da tazarci Babu abinda kishi bazaisa tayiwa Najma wadda take mace me tsananin kamewa da sanin qima da darajar kanta cikin bayyanarda bacin ranta a fili tace"

Basai Ankira Mubarak ba Alfa biyawa JALALUDDEEN sadakinta a daura auren dashi gobe.

Cikin sauke numfashi Alhaji Alfa ya  kalli hajjon wadda kowa yasan ranta yariga yayi mummunan baci akan al'amarin shi kansa Alhaji Alfan ransa  yabaci da hukuncin Dattijon saidai kawai Yana iya kokarinsa gurin dannewane sbd kada ya nuna isarsa da yawa bayan sunfisa iko da Isa akan Najman Kuma shima da hukuncinda yayi niyar yankewa kenan na nemawa Marshal auren amaimakon Mubarak dasukace Dan shikuma aikin Mubarak din ne Bai yarda dashiba Dan harka yakeyi da yan siyasa saikuma maganar Hannah da duk sunsan da maganarta da jalal din saigashi hajjo ta rigasa yanke hukuncin Dan Haka take ya maida kallonsa kan Dattijo dayayi tsit Yana soke Kai sbd ganin ran hajjo ya baci sosai cikin girmamawa ya kalleta zaiyi magana tace"

Aurenta da jalal zai kawo qarshen matsalar komai Inshallah tazarar shekarun ba komai bane tunda duka duka baifi shekaru uku ne tabashi ba dan Haka wannan ba matsala bane.

Wani kukan Dadah takuma fashewa dashi tana cewa"

Ni kulu dame zamu saka mukune da koyaushe kuke binmu da alkhairi¿
Tunda mahaifin yarinyar Nan ya rasu kuka zama gatanta kuka ginata akan kyakkyawar rayuwa yanzu Kuma gashi kun amince da ita adaidai lokacin datake cikin irin wannan tsaka me wuyar ya Allah yasaka muku da mafificin Alkhairinsa Kuma maganar ba ko anbawa jalalu ko ba'a bashiba babuta Dan kuwa Alhaji Alfa kaima mahaifintane Kai tsaye zaka iya cewa kawai kazaba Mata jalalun adaura dashi Kuma ayi hakan sbd ka Isa indai akantane.

Jinjina Kai yayi Yana kallon Dattijo yace"

To Ibrahim me kagani akan hakan??

Jiki mace Dattijo ya girgiza Kai Yana saukewa sbd shi wata irin kunyace ta dabaibayeshi sbd irin qaunar dasu hajjo kewa Najma yasa bazasu iya Bari ayi Mata auren tozarciba daya dage akan sai yayi din Dan Haka kasa kallon hajjo yayi ya kalli Alhaji Alfa yace"

Allah yasa hakan shine alkhairi.

Tashi hajjo tayi tafara ficewa kafin Suma suka fito Dadah hankalinta kwance murna fal cikin ranta tunda damuwarta Bata Kwana da itaba an kaudata Dan kuwa yanzu auren ya sauka inda Babu halin fasawa bare tashiga shakku shidai Dattijo duk ransa har lokacin a jagule yake Dan Haka Babu Wanda yasanda maganar sauyin auren aunbarshi akan sai goben.
##MAMUH#



*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107[1/14, 3:33 PM] +234 901 771 2720: *_DM 11_*
Acikin Daren Koda hajjo tadawo palonta Hanifa na zaune Palo tana waya da Isma'eel dinta dazai qaraso goben tunda safe sbd yasamu daurin auren cikin sanyin jiki Dana murya tareda damuwa tace"

Zawj ko yanzu wannan karon Babu auren Naj.

Subhanallh"yace cikin mamaki da firgici yace"

Meya faru Kuma wannan karon?
Yaya Naj din tana lafiya kuwa?
Innalillahi Wannan labarin bamai Dadi bane.

Kasa cewa komai tayi saima damuwarta akan Naj dake qaruwa sbd wannan karon Naj din abinda Abbas yayi ya daki zuciyarta Dan ba'a taba cin Mata mutunciba kamar Haka yaga Mata sutura a waje dasu Hanifan da ummanta Basu isoba alokacin batasan Yaya zatayiba da jikinta.

Ko palon hajjo Bata zaunaba ta nufi dakinta ruqayyat dake jiran dawowarta tayi Mata gashin qafafunta Wanda ake Mata kullum da daddare kafin ta kwanta sbd nauyin qafafu tana ganin hajjon ta shige taje ta dauko kayan aikin zata nufi dakin Hanifa ta tsayar da ita ta karba kayan tana cewa"

Jeki Zan Mata da kaina.

Karaban kayan tayi ta tura kofar dakin ta shige ta tadda hajjo zaune tasake ajiyar zuciya sai alokacin taji nutsuwa da fushinta ya sauka sbd koba komai shikenan Naj din tazama tasu ta har abada Babu me sake takurawa rayuwarta ta bangare daya Kuma tuno jalal da irin girman miskilancinsa da Kuma yanda girman matsayi yasamesa a cikin shekarunsa na samartaka dan Haka ba lallai hadin nasu yayi ba Dan kuwa shi yanzu yaro da kudine abokin manya itakuma idan ba Allah ya rufa asiriba kallon qani zatamai Wanda zai kawo musu matsala a tarayyar Amma dai koma yayane za'ai auren Kuma Inshallah zai zama alkhairi hakama bazasu takurasuba ko bayan auren za'a barsu ahankali komai zai daidaita Dan Haka ita ko ahakan komai yayi Mata.

Kallon Hanifa tayi tana nuna Mata kusa da ita tace"

Zo ki zauna kusa Dani mu Taya juna murna da Allah ya Sanya alkhairi sbd kema Zakiyi sirika a goben amatsayinki na yayar ango.

Hanifa Bata gane me hajjon ke nufiba ta qaraso ta aje kayan hannunta tana zama gefenta tace"

Naji dadin da auren Abbas da Naj Bai yiyuba Amma hajjo ai bazamuyi murna ba Kuma tunda Naj din na cikin damuwa duk da itama nasan Bata fasa auren bace ta abin daya faru ne.

Tunda safiyar ranar ta waye sai alokacin hajjo ta Dan saki guntun murmushi tana miqar da qafafunta kan qaramin sofa table dake gabanta tana cewa"

Gasamun qafafun ko da Dan sakemin gobe nasamu damar Dan zagayawa dasu cikin gidan kodan jama'a
Gobe Allah yayi damuwarmu akan rashin zuwan Marshal ta qare Dan kuwa yanzu tunda yanada Mata anan taredamu Dole zai ringa zuwa,
Mahaifinki ya nemawa Marshal auren Naj a Daren Nan Dan Haka ankai qarshen duk wata fitina gobe da Marsha za'a daurawa Najma aure Aminyarki ta zama sirikarki yanzu ita din tamuce halak malak.

Ruwan zafin da ba'a sirkaba ta tsunduma qafar hajjon aciki sbd rudewa cikin mamaki dason tabbatarwa tace"

Hajjo Aure tsakanin Naj da marshal??

Zare qafa hajjo tayi tana cewa"

Qonani kike Shirin yine kome?
Bari Naga auren nasu harma da 'yayansu idan Allah yace kafin ki qona qafafun na rasa na zuwa.

Da dai hajjo tayiwa Hanifan bayanin komai Jin tayi wani farin ciki da Bata tabajinsaba anan kusa ya dabaibata tako Ina duk da can qasan zuciyarta tanajin akwai qalubale a tsakanin yardarsu da auren su biyun Dan kuwa Babu me sauqin saukowa wani acikinsu ga maganar aurensa da Hannah gefe daya Amma Kuma tana danne hakan da farin cikin hadin Dan kuwa wannan shine perfect match agurinta ita da Marshal dinta da Naj dinta
Miqewa tayi tana cewa"

Alhamdulillah ya Allah mungode maka da wannan zabi naka.

Ficewa tayi da sauri ta nufa dakinsu da Naj din take kwance tayi sallah ta saka kayan bacci tayi kwanciyarta da gudunta taqarasa ta fada kanta tareda rungumeta tana cewa"

I love you Naj
I love you Naj

Da idanuwanta dasukai laushi ta Dan kalli Hanifan tana maidasu ta lumshe batareda tace komaiba sbd har tafara Jin bacci sai kawai ta maida idanuwan ta rufe da muryarta me taushi tace"

I love you too Amma bacci nakeji barni Dan Allah.

Dariya Hanifan ta Dan sake cikin tsananin farin ciki tace"

Yi baccinki Lafiya MRS DEEN MARSHAL ALFA.

Bataji abinda Hanifan taceba sbd baccin daya fizgeta.
Daganan Hanifa fita tayi dakin Takoma palo ta miqe a kujera ta Danna Kiran mijinta tafada Masa Nan take cikin Daren tafara Dora sabbin shirye shiryen komai danma kamar yanda hajjo tafada Mata a yanke auren kawai za'a daura baza'a daga maganar takurasu tarewaba yanzu sai kowannensu ya Dan nutsu Dan wannan alamari na gaggawar daya riskesu musamman sbd yanayi na yanda suke kallon junansu na tazarar shekarun.

Ta bangaren ummanta da anty Amina kuwa a Daren Basu rintsa ba sbd tsananin damuwa da rashin sanin mezai faru mezai biyo baya ga Dattijo har lokacin umman Bata sake sakashi a ido ba bare tasan da maganar auren a gobe ko babu ga anty Amina zuwanta biyu yinin tana dubo Naj Wanda tunda abun yafaru take daki kwance Bata buqatan ko tada maganar ayi.

Koda akai sallar asuba kusan daga Dadah har Dattijo da Hanifa Basu rintsaba sbd zumudin safiya tayi ta waye a daura auren Nan kada wani abun ya gitta afasa Dan Haka daqyar kowannensu yaga anyi sallar asuba gari ya waye aka hau sabuwar hidima gadan gadan.



***********
Tsaye yake daga bakin qatoton window na cikin geam room dinsa dake cikin flat dinsa Wanda Babu kalar tsadadden lafiyayyan geaming machine dinda Babu aciki Wanda duk inda yake yasaba amfani dasu shiyasa jikinsa kallo daya macen datasan asalin jikin namiji me kyau qaqqarfa bazataji ta mutu a sonsaba take musamman idan tsautsayi yasa kasamu ganinsa ba riga.

Tsaye yake Yana amsa waya sanyeda black three quarter da black armless riga Wanda suka fidda hasken fatarsa sosai dama Kuma black shine kalar kayan dayafi so kila Kiran kalar tana Masa tsananin kyau ne.

Gama wayar yayi daidai knocking kofarsa da akai Wanda hanifa ce kawai yasan tana zuwa ta buga kofarsa Kai tsaye saidai akirasa a waya sbd sanin shi ba mutum bane Mai son hayaniya.

Kashe wayar yayi ya fito daga geam room din ya nufi Palo ya ajiye wayarsa akan kujera ya nufi kofar cikin nutsuwa ya saka hannu ya bude tareda juyawa Yana cewa"

Menene Kuma tunda safe Nan?kinsan bana ganin kowa fa tunda safe is too early now Hanifa.

Muryar Dad Alfa yaji yace"

Munsani Marshal Deen Dan hakan before anything ma we are really sorry to disturb.

Waiwayowa yayi tareda kallon Hanifa dake gefen dad din kafin ya maida kallonsa kan dad din ya na Nuna Masa kujera Yana cewa"

Sorry Dad banyi tunanin ganinkaba Ina tunanin haniface sbd itace tafi iya damuwa musamman da safe.

Zama yayi bayan dad din ya zauna Yana cewa"

Good morning Dad antashi lfy?

Lfy Alhmdlh.

Hanifa ya kalla ahankali yace mata"
 Gud morning madam.

Murmushi tayi tana ajiye kayan data riqowa dad tana miqewa tsaye da farin ciki shimfide kan fuskarta ta kalli qafafunsa dake sanye da slippers na Gucci farare tas kaman baya tafiya dasu sai qafafun Naj dake tsaf fes fes Kamar hakan suka fado mata tace"

Inada aikin Yi Zan tafi Anjima dai nasan zamuyi magana idan kayi lokacina." Ta juya ta fice.

Baibita da kalloba sbd yawan kallo ba dabi'arsa bace ya Dan kalli dad da fararen idanuwansa shima dad din shi ya kalla kafin ya nuna Masa kayan dake ajen da hannu Yana cewa"

As you know yau akwai taron daurin aure So ansamu matsala anfasa daurawa da wancan din saidai za'a daura da Wanda na Isa dashi ga Kaya Nan su babban rigane kayi amfani dashi anjiman sbd mutane zasu taro akwai kuma media you'll more comfortable in it tunda daurin aure ne na hausawa.

Kallon kayan yayi kafin ya kalli dad din Kai tsaye yace"

Thank you.

Gingina masa Kai Dad din yayi Yana cewa"

Ok then see you.

Tashi dad din yayi ya nufi kofa marshal din na bayansa har harabar gidan kafin ya juya zai wuce saiga Hannah Wanda ta fito daga sashensu hajjo data sakawa ranta zuwa gaishesu kowace safiya da Rana da yamma sbd sake samun damar kame zuciyar Marshal tana ganinsa ta qaraso gurinsa tana sake wani irin qayataccen murmushi jikinta sanye da wata doguwar straight English gown ta roba data Dan lafe a jikinta kyakkwan shape dinta a bayyane.

Good morning Marshal" tafada tana tsayuwa agabansa.

Dan kallonta yayi tareda dauke Kai Yana kallon hanyar sashen hajjo da Hanifa ta fito ta koma cikin sauri tana waya da alama dai gabaki daya tama manta da ita din ba wata lafiyayya bace take irin wannan kaida kawon sbd hidiman bikin Naj din.

Juyawa yayi ya wuce Yana cewa Hannah din"

I will talk to you later zankoma bacci yanzu.

Daukeda murmushi a fuskarta tace"

Ok love" tana bin bayansa da kallo Kamar zuciyarta zata narke gabaki daya akansa,
Tana yiwa marshal so me tsanani Dan ita ba Shirin aure gabanta a da Amma yanzu sbd shi aure takeso Kai tsaye ba Jan lokaci shiyasa zata dage da Binsu hajjo ko zata samu a saka ranar bikin nasu tunda ansan da maganar auren nasu.

Alhmdlh Koda Naj ta tashi safiyar lafiya kalau ta tashi kamar koyaushe data Saba tanada qarfin zuciya Kuma tasaba da hakan tunda ba yanzu ne hakan ta taba faruwa da itaba Dan Haka dataga Suma su Hanifa da hajjo dasuke damuwa koyaushe maganar aurenta ta fasu taga wannan karon Suma Basu nuna damuwaba saima farin ciki dasuke da hakan yasa ta qara cire abin a ranta tayi wankanta ta fito sanye da riga da skirt na atampa Maroon data yiwa kalar fatarta kyau tazo palo ta zauna gefen hajjo daketa faman waya tasha ruwan dumi da Zuma da Madara ta koshi ta tashi taje ta dauko qaramin gyale ta yafa kanta ta fito tareda wayarta a hannu tana kunnawa ta nufi gidansu bayan ta biya gurin mum Malika ta gaidata Dad baya Nan jama'arsa nata isowa so baya gida.

Ko data Shiga gidansu Haka ta ringa Dan gaggaisawa da mutane harta Isa dakin Dadah da yau farin cikin duniya tana cikinsa bakinta Sam baya rufuwa sbd farin ciki danma Dattijo ya kwabeta akan kada ta fadawa kowa komai sai sunsamu an daura auren lafiya sunga aure ya dauru tukuna Dan Haka Babu Wanda yasan da maganar bayan ummanta da Dattijon yafadawa yau bayan sallar asuba aikuwa gari na wayewa sadaka me yawa umman ta Tara almajirai tayi tareda duqufa da adduar auren ya dauru taga ya dauru itama Dan har lokacin daga ita har Dattijo gabansu Bai daina faduwaba sai sunga anshafa fatiha aure ya dauru.

Kodata Isa can cikin gida gurin ummanta dasu anty Amina sai hidima akeyi sai hakan yaso Bata mamakinsu saidai Tai musu uzurin basusan Babu maganar aurenba sai anjima idan lokacin daurawan yayi sunji ansanar anfasa Dan Haka batai wani yunqurin maganar da kowannensuba Dan dama ba halinta bane yawan maganganu musamman irin wannan Dan Haka dakinta ta shige tana hada sauran kayayyakin lefen Abbas dake dakin Dan tasan maida Masa za'ayi Allah yasa ko takarmi daya Bata sakaba a kayansa duk aurenta idan za'ayi hajjo ke hada Mata lefe na musamman sbd gudun irin Hakan.  

Har qarfe daya da rabi tana gidan inda tana gamawa Kai tsaye ta fice  Takoma bayan tabar musu kayan shirye tsaf a tsakar dakin ta fito tana waya da Sarah Dake sanar da ita gatanan a Hanya tana zuwa.

A waje Babu kowa maza tsit duk an tafi gurin daurin auren da za'ayi dama a babban masallacin juma'ar da Alhaji Alfan ya Gina acan farkon layinsu jami'an tsaro da securities kuwa koina cikin layin akwaisu 
Sojojin Marshal ne a kofar gida tsatsaye jikin motarsu da alama jiran fitowarta sukeyi ta wuce Kai tsaye ta shige gate suna bude Mata da sauri
Ahankali tace" thank you" tana wucewa hankalinta a waya.
Tana saka Kai a palon hajjo Yana fitowa sanye cikin wata navyblue hilton filtex da rawar da yakeyi kawai zai bayyana kudi me yawa ya lashe
Sai hular daya saka wadda ke nuna Bai Saba sakawaba Dan yanda ya sakatan ta Dan Yi gefe Amma sai hakan yayi wani irin yiwa kyakkyawar fuskarsa dake fidda wani irin qyalli na kwarjini da cika ido ta dauke idanuwanta akansa tana rabewa ya kalli Dan qaramin siririn gyalen dake kanta Wanda iyakacinsa kafadunta ya dauke kai Yana wucewa sbd lokacin daurin auren yayi saura mintuna basufi goma sha uku ba ita Kuma tana shigowa tsakiyar palon hajjo da wasu baqinta da Basu Dade da isowaba sukabi Naj din da idanuwa gabaki dayansu.
##MAMUH#




*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*


*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107
[1/14, 3:34 PM] +234 901 771 2720: *_DM 12_*
Ganin duka idanuwansu akanta yasa ta sauke idanuwanta tareda qarasowa a natsenta cikin taushin murya da rashin karauniya tace"

Ina wuninku Baabah barka da zuwa.

Sake Mata kyallon qiri qiri su baabar keyi wato yanne da qannen mahaifiyarsu Jalal dinne suka qaraso yau sbd tun a Daren jiyan hajjo da Alhaji Alfa suka sanar dasu auren jalal din daya Kama na gaggawa saidai Ba'a sanar dasu yanda akai auren ya yiyuba dakuma girmarsa datai sbd idan ba'a fadaba zakacema ta girmenta sosai Sosai sbd yanayin jikinta datake me kyau da burgewa da nasa jikin daya bude sosai sbd exercise dakuma tsayi daya fita sosai Dan Haka cikeda yabawa suke kallonta fatarta na daukan musu ido sbd zallan gyalan dilka da wasu abubuwan da akaita Bata tana Sha Dana mulkawa.
Baabah tace"

Lafiya kalau alhmdlh,ya hidimar kike 'yar Nan? Ya hidimar jama'a?
Allah ya Sanya alkhairi kinji,
Allah yayiwa wannan auren naku albarka.

Da sauke Kai tayi shiru batareda tace Amin din ba tunda tasan abinda yake Nan ba aure.

Hanifa dake daki tagama shiryawa cikin Ado na shigar alfarma tana qamshi sbd mijinta da tuni ya iso suna gurin daurin auren
Fitowa tayi takama hannun Naj sukai dakin tana cewa"

Naj zo ki sauya shirinki inasa ran yanzu kowane lokaci za'a daura auren 
Zo kiyi ado A ranar farko mijinki ya ganki da ado na musamman.

Zama kan sofa dake dakin Naj tayi tana aje wayarta da kallon Hanifa cikin Dan basarwa tace"

Nasan kinsan anfasa auren Nan just drop your drama.

Murmushi me girma Hanifa tasaki tana cirowa Naj din wani tsadadden navyblue lace me tsananin taushi da rashin ado na hayaniya Wanda yaja kudi sosai gurin siya tareda wani transparent emboidery veil ta aje gabanta tana cewa"

Dan Allah ki shirya kadaki Bari asan abinda yake faruwa musamu Mana a watse lafiya basai kin nuna musu Abbas yafasa aurenki ba ki nuna ko babushi Zaki iya rayuwarki ta walwala da farinki.

Da gangan ta fada hakan Dan Naj din ta shirya da farko qin yadda tayi sai daga baya ta saka kayan ta zauna bakin gado sbd zuciyarta data fara harbawa da sauri da sauri Kamar zata Fado ta Dan dafe kirjinta tana sauraron bugun zuciyarta daya sanyata lumshe fararen idanuwanta ta rufe tanajin kamarma hadda faduwar gaba.

Miqewa tayi ahankali takoma Palo inda hayaniyar baqin gidan take Anata fira 
Tana fitowa dukkanin idanuwansu suka sake dawowa Kanta suna Yana baiwar kyawu da Allah yayiwa Naj din qamshin wani irin fitinannan turaren da ummanta ke Mata gyara dashi daya Gama Kama jikinta Dana kayanta tareda kayanta da aka turara ya gauraya palon cikin nutsuwa da farin ciki a fili hajjo tace"

Masha Allah, Allah na gode maka da ganin wannan Rana Allah kasawa aurensu albarka da farin ciki me dorewa.

Amin Hanifa ta amsa idanuwanta akan Naj da ko itama dasuka taso tun yarinta tare sukai rayuwa tare koyaushe tana yabawa.

Qarasowa tayi gefen Hanifan ta zauna tana duba wayarta hankali kwance ba damuwar komai su Kuma suka cigaba da sha'anin gabansu.

*****
An daura Auren JALALUDDEEN MARSHAL ALFA da NAJMA ABDULLAHI BELA akan sadaki naira dubu dari cif Wanda duban jama'a suka shaidar cikin mamakin sauyi da aka samu ciki harda jama'ar su Abbas da yawa sun halarta sbd basusan cewan an fasaba duk da hakan dai kowa tanata fatan Allah yasanya alkhairi Wanda aketa bawa Marshal hannu Ana tayasa murna shidai bin kowa yake da mayun idanuwansa sai hannu dayake bawa manyan mutanen dasuke miqa Masa hannu Dan tayasa murnar aurenda Saida ya iso gurin yasan nasane.
Isowarsa gurin yasa mahaifinsa daketa dakon jiran isowarsa ya qaraso gabansa Yana kallonsa Kai tsaye yace"

Za'a daura auren Najma dakaine Ina roqon alfarman ka amince da hakan sbd wancan ya fasa adaidai lokacinda Babu wani mafita shiyasa a matsayinsa na mahaifinka Kuma itama Ina matsayin uba gareta na hadaku ta hanyar nema maka aurenta Ina fatan zakamin biyayya.

Fararen mayun idanuwansa ya zubawa Dad din kafin ya Dan sauke Kai cikin miskilar murya yace"

Ok Dad.

Hakan dayace yasa Dad din Jin wani irin sanyi da nutsuwa sbd yanata nazarin yanda zai fahimtar da jalal din hukuncin dasuka yanke Kai tsaye akansa batareda Jin shawararsa ko raayinsaba tunda ba yaro bane yanada iko da yancin zabarwa rayuwarsa abokiyar rayuwarsa da kansa duk da yasan karba Masa Marshal din yayi sbd yariga yazo gurin bazai iya komawaba yasa Dad din kunya Amma yanayinsa kawai ko Bai fadaba Dad yasan anyi Masa shigar sauri Dan kuwa Babu tsarin aure agabansa yanxu musamman da wannan din da za'a daura da ita Dan kuwa a yanda suke dinnan ba lallaiba ta kwantar Masa da Kai shikuma bayasa ran macen dake qarqashin ikonsa zatana Masa kallon qani ko wani Abu Dan kuwa shi mijin macen dazata bisa ne Amma tunda su dad din suka zaba auren dama agurinsu zata zauna so ba damuwarsa bane sosai aciki tunda shi bataredasu zai zaunaba a taqaice ma yaji bazai iya dogon zamaba komawa zaiyi.

Dan Haka Ana gama daurin aure akai gagarumin reception da akai liyafar alfarma shidai ko ruwa Bai Sha ba aka fara watsewa ya zame yayo gida kansa na 'dan sarawa Dan Haka Koda ya iso gida Kai tsaye flat dinsa ya wuce ya zare babbar rigar jikinsa da hula da komaima ya cire ya fada toilet ya sakarwa kansa ruwan dumi ta shower Yana sauke ajiyar zuciya.

Sai dayayi wanka yafito yaji ya Dan samu nutsuwa da saukin ciwon kan ya saka guntayen qananun Kaya yaje fridge yasha ruwa kadan yadawo yashige daki ya kwanta Yana kashe wayarsa cikin nutsuwa bacci ya daukesa.

Saida 'yan daurin aure suka dawo kowa yaji da Wanda aka daura auren zallan mamakin al'amarin yasake yayata gidansu Naj da hayaniya saidai Kuma tunda dai ansamu andaura Mata auren ba'a fasaba gabaki dayaba  a watse a banza yasa aketa sabuwar murna Allah yayi lokaci yayi tayi aure duk da wasu da yawa sun manta da banbancin shekarun sbd matsayinsa da yanayinsa yasama har wainda suka kusan haihuwarsa suna basa tsananin girma sbd matsayi da kamewa shiyasama ake mantawa da wani banbancin shekaru sai murna sukewa umma Allah yabasu Wanda yafi abundama suke buri tako Ina.

Dadah kuwa Banda sadaka da godiyar Allah tana washe bakin babu abinda takeyi yau Jin takeyi wani irin sakat daga ita har Dattijo da sai baza babbar riga yakeyi Yana gaisawa da manyan mutanenda yasan Albarkacin auren Naj da jalal ne yakeci Dan kuwa  ganinsu Koda appointment ne shi bazai samuba Dan Haka sai farin ciki yakeyi Yana baje babbar rigarsa ta tsadaddiyar shaddar da Alhaji Alfan ne yake dinka Masa daman.

Yana dawowa gidan yakira Naj a waya yace maza tadawo gida yanzu.

Da mamaki ta fito zuciyarta ba Dadi sbd dai ga dukkan alamun data gani agun mutane andaura auren kenan 
Ta hadiye wani Abu me daci da nauyi daga maqogoranta Dan kuwa auren Abbas shine mafi mumman al'amari daya sameta a wannan rayuwar.

Ko data shiga gidansu sama sama takejin Ana mata adduar Allah yawa aure albarka Saikuma tafarajin Ana Kiran sunan Jalal da cewan mijinta 
Kanta ne taji ya dauka ciwo sbd komaima ita yanzu a duhu yake Mata Kai tsaye dakin Dadah ta Isa sbd tasan Dattijo daya aika kiranta Yana can tana Isa tashiga da siriryar sallama ta nufi gefen Dadah daketa washe Baki cikin farin ciki ta zauna ahankali tareda bude Baki cikin taushin muryarta tace"

Barka da jumaa Dattijo.

Gaida Dadah tayi itama duk da dazun sun gaisa data shigo.

Kallonta Dattijo yayi dakyau yana Dan  kame fuska yace"

To Najma Kamar dai yanda Kika sani yau ne ranar daurin aurenki da Abbas 
Amma sbd rubutowa ta ubangiji Allah baiyi shine mijin ba Dan kuwa a jiya suka sanarda sun janye sbd abindaya faru a jiyan da safe.

'dan shiru yayi kafin yacigaba da cewa"
Sakamakon hakan yasa Babanki Alhaji Alfa da hajjo suka bayyanarda buqatarsu tason nemawa JALAL aurenki muka amince atake sbd Babu wani zabin kokuma mafita Daman cigaban dayafi hakan Dan Haka dai a taqaice andaura Miki aure da JALAL yanzu ke matarsace halak malak saidai Hajjo ta nema alfarmar kada a takuraki da maganar tarewa gurinsa kokuma wani abun yanzu duba da yanda akai auren Dan Haka Zaki zauna gurinta kafin daga baya idan an natsa Kya koma sashen mijinki kokuma ki bisa can qasar dayake.

Akaro na farko a rayuwarta data kafe Dattijon da ido idanuwan nayi jajir ko qyaftawa batayi zuciyarta ta tsananta dokawa har batasan lokacinda ta bude bakiba tace"

JALAL qanin Hanifa?
An daura auren kokuwa dai za'a daurane yanzu??

Gano inda ta dosa da Aniyar bijirewa auren yasa ya tsuke fuska cikin bori yace"

Andaura Kuma wallahi kibar maganar Nan dakikeson fada acikinki Dan kuwa kisani kikaje Kika dagawa bayin Allahn Nan hankali akan banzan tunaninki na girman Kai suka raba auren Nan dake da mahaifiyarki zaku bar gidan Nan Dan kuwa Banga amfanin rashin godiyar Allah ba,
Dukkanin masu fasa aurenki Babu Wanda yakaisa bare yafisa ba'a ma hadawa ga qauna da mutunci da mahaifinsa da kakarsa dama 'yar uwarsa dasuke Miki har kin Isa kice bakyason auren,
To kiji da kyau Dadah kizama shaida wlh taqi auren Nan bani ba ita Kuma Tak banyarda tasake cewaba.

Miqewa yayi Rai bace ya gyara rigarsa zai fice yace"

Kuma duk abinda kikeyi kiyisa ki hada kayanki anjima Zaki koma gurin hajjon da zama afadawa kowa ba yanzu zata tareba kowa ya watse daga gobe banason zaman tsegumi"
 juyawa yayi ya fice daga dakin Rai bace Dan baiyi tunanin zata musanya din ba yanda yasanta da komai yace hakane sbd rashin iya ja'injarta Amma wannan karon zata iya turjewa shiyasa ya rufe idon yayi Mata me gabaki.

Jajir idanuwanta sukai zuciyarta ta dauki wani irin mummunan 'daci da nauyi dataji tana marmarin mutuwartama Dan kuwa a rayuwa ta Jima tana kunsar baqin cikin maza Dana fashin aure Dana tsangwamar iyaye da 'yan uwa Amma Bata taba Jin an Mata tozarci da baqin ciki irin wannan,
Aure tsakaninta da Wanda ta girma Wanda yake matsayin qanin Aminyarta ta Yaya ake tunanin tayi aure da rayuwar aure da JALAL Wanda bayan sannu ta gaisuwa Babu abindayake hadasu....

Najma karki damu godiya zakiwa Allah jira da zaman gida ya qare Allah yakawo lokaci kema kin aure,
Tsananin Rabon dake tsakaninkine da JALAL din yake Kore waincan aurarrakin naki da ake fasawa,Rabo ne me qarfi na haihuwa kesa irin wannan auren Dan shi Koda aure ko Babu sai ansamu Rabon Dan Haka muke qara godewa Allah da Akai hadin, Allah ya kawo......Wani irin kukan baqin ciki Mai qarfi ta saki sbd maganganun Dadahn dasuka fasa wani qoqon baqin ciki cikin zuciyarta ta miqe tashige kuryar dakin Dadahn tareda zamewa qasa ta zauna tana wani irin kukan da tunda take rayuwarta Bata taba yinsaba.

Tun abun na Wasa Dadah hankalinta ya tashi da halinda Naj din tashiga saitaji murnarta na Shirin komawa ciki Dan kuwa matuqar Najma taje gaban hajjo ko Alhaji Alfa tana wannan kukan na tashin hankali da zallan baqin ciki zasu iya warware auren sbd gudun damuwarta Dan Haka hankali tashe tasa akai Mata Kiran Dattijo da Umma ta fasa musu kuka tana cewa"

Matuqar Najma taqi wannan auren aka warwareshi to Nima barin gidan Nan zanyi bazan zaunaba dan zuciyata harbewa zatayi da kunyar Alhaji Alfa da hajjo Dan Haka gatanan ki fada Mata gwara ta dangana da wannan tashin hankalin ta rungumi auren.

Ko kallon Najman Dattijo baiyiba ya kalli ummanta yace"

Ki saka Mata hankali cikin kanta tadawo tunaninta Dan kema nasan bazaki so auren ya warwareba Dan idanma ya warware na fada Mata hukuncina bazaiyi Mata Dadi ba Dan bazamu zauna da qatuwar budurwaba kamarta muna rarrashinta akan aure bayanma tuntuni yakamata muyi Mata auren Dole mu huta.

Kallon Najman umma tayi tareda miqewa tsaye ta Isa inda take ta janyo hannunta tana cewa"

Inshallah zata fahimta aure Amma yariga ya dauru ma maganar warwarewa tunda ai Dan an Isa da itane akai Mata auren maganar taje gaban hajjo tana wannan kukan Ni kaina bani ba ita Dan Haka Najma ki nutsu kidawo hankalinki rayuwar aure zakiyi a gidan yanzu ba wadda Kika sababa, su din yanzu dangin mijinkine Kuma kinsan son da suke Miki bazasu taba cutatar dakeba hakama jalal ki yadda ko kiqi yadda mijinkine yanzu bashi girma yazama Dole.

Kinga Fatima jeki da ita can kuyi sauran abinda zakuyi na tsakaninku ganinan zuwa na maidata gurin hajjon da kaina shikenan.
##MAMUH#




*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107*_DM 13_*
Zaunar da ita bakin gadon dakinta umma tayi tana kallon yanda fuskarta gabaki daya tayi jajir sbd kukan tashin hankali musamman dogon hancinta yafi yin ja ta zauna gefenta tana tausasa murya cikin kulawa da tausayi tareda kewar rabuwa da ita dazatayi duk da kusa suke tace"

Najma Dan Allah ki daina daga hankalinki akan abindaya kamata kiyi farin ciki akansa,
Farin ciki mukeyi kowama shiyake Dan tayaki murnar aure da Allah yabaki ikon Yi Wanda kinsani auren rahamace tunda kin dau lokaci da gwagwarmaya kafin kisamu kiga hakan.,
A shawarance matsayina na mahaifiyarki Ina Baki shawaran karki watsawasu hajjo da Alhaji Alfa qasa a ido kodan tsananin qaunar dasuke Miki wadda itace ta Sanya hakan,
Hakama Yaya kike tunanin Zaki iya kallon Hanifa kice bakyason Dan uwanta datafi so fiyeda komai a duniya wannan tunanin baiyiba ki ajiyesa Anan gida ki barsa zaman qarqashin ikon mijinki zakije kiyi bakida wani majagorancinki bayansa Dan Haka biyayya da bin umarninsa dole ne....

Wannan kalmar tasa wasu hawayen baqin ciki da ciwo masu zafi suka gangaro Mata tana sake sheshekar kuka ahankali, umma taci gaba da cewa"

A umarni Kuma na matsayina na mahaifiyarki Ina Baki umarnin ki aje maganar Araba aure anan ki barta Dan duk ranarda kikaiwa wani acikin gidan Alfa maganar daga ranar zakisan asalin kalan fushi da bacin Raina Dan Haka Dan Allah Najma na rokeki daki dauka dangana kiyi biyayya kaman yanda Kika Saba yiwa qanin mahaifinki Dattijo daya dauki damuwar tsakani da Allah yasakawa kansa akan al'amarinki,
Qanin mahaifinki ne Kuma Miji gareni Ni mahaifiyarki Dan Haka ya cancanta kiyiwa hukunsa biyayya Koba Dadi sbd baitaba nuna banbanci ko gazawaba a tsakaninku da nasa 'yayan daya Haifa tun bayan rasuwar mahaifinku da wannan biyayyar kawai Zaki iya saka Masa kodan yanda yake Shiga tashin hankali da damuwa ba dare ba Rana aduk lokacinda neman aurenki yasamu matsala Dan Haka kiyi hkr ki dauki dangana Allah ya sanyawa rayuwar auren albarka.

Amin anty Amina tace tana qarawa da nata nasihar da rarrashi Dan kuwa duk Wanda yasan Naj baitaba ganinta a mummunar yanayiba irin yanxu Dan kukan datakeyi harya zama abin kayar da gaba.

Ganin idan aka biyeta sanyi jikin kowa zaiyi yasa aka qyaleta quryar dakin umman ta dunqule a gado cikin mummunan yanayi na qunci da baqin ciki hawaye Kuma sun kasa tsayuwa daga idanuwanta.

Hidimar Wunin biki akaci gaba dayi har dare masu tafiya gida suka tafi akabar baqin nesa kawai wainda Suma washe gari Dattijo yace kowa ya watse yakoma 'dakinsa.

Mummunan yanayin da Naj din take yasa Dadah tacewa Dattijo yaje ya sanarwa Alhaji Alfa abar Naj din ta kwana gida har gobe tadawo sbd sudai duwarsu da tashin hankalinsu kada hajjo ko Alhajin sugan Naj a wannan halin komai zai iya faruwa Ana fadawa Alhajin yace bakomai abarta ta nutsu tukuna tazo Koda fiyeda goben nema zai fadawa mijin nata,da wannan aka barta gidan ta kwana.

Har safe tana dakin umma Nan takwana ko ganinta batason mutane nayi sbd tsananin kunyar kanta da wannan aure ga idanuwanta dasuka kumbura tsabar kukan data kwana tayi a Daren.

Hanifa na sane taqi zuwa sbd tana gidanta tun jiya da daddare mijinta ya dauketa suka tafi takuma qi kira Dan taji labarin kukan da Naj din keta faman Yi a bakin Anty Amina,
Taji tausayinta matuqa hakama tana iya kwatanta jin yanayi na damuwa da Naj din take ciki na auren Kai tsaye da Wanda ko taqamaimai kalma biyar Bata taba shiga tsakaninsu ba duk suka hadu tsawon shekaru kuwa Dan Haka take tausayin Naj din ga sanin halin JALAL datai na tsagwaron kamewa da basarwa Dan kuwa kafin Naj taganewa komai sai anga wuya.

Koda qarfe goma Sha biyun Rana tayi baqi kowa ya hada jakarsa ya kama hanyar komawa gida Dan Haka gidan su anty Amina dasu Khadija da zainab din Anty Amina sai aikin gyaran gidan suke Dan Haka Koda la'asar tayi gidan koina yayi fes fes sai mutan gidan kawai Kamar ba'ai taron biki ba dan ma da Dattijo Bai tsaya akan kowa ya watse yau ba da akwai wainda sai sunqara sati kila kafin su koma.

Bayan sallar isha tayi wanka tareda Shirin bacci tasaka riga da wando masu tsantsi na baccin kalar maroon ta janyo wayarta datun jiya data shiga tashin hankali take kashe ta kunna tareda ajewa gefe batareda tabi takan wayarba ta Haye gadonta tana Shirin kwanciya ummanta tashigo daukeda wani ruwan turaren humra me shegen qarfin qamshi ta ajiye gaban madubi tana zubawa a hannunta tahau shafawa Naj din akoina ajikinta tana cewa"

Sauko Dadah na Kira kutafi gurin hajjo duk da wannan baza'a kirashi da tarewaba Amma dai tafiyar kenan kila sauko ki sauya Kaya Mana.

Bata dago ta kalli ummanba tayi kamar bazata saukoba tsawon mintuna kafin dai ta sauko tana zura slippers dinta dake bakin gadonta ta nufi wardrobe dinta ta bude ta dauko wata sabuwar jallabiyarta me Fadi kalar coffee brown ta warware ahankali ta saka kan kayan baccin Dake jikinta kafin ta jawo qaramin Chantelle veil ta yafa akanta Dan Bata daura ko dankwanlin jallabiya 
Umma kuwa binta tayi tayi tana watsa Mata turaren harya ushers Yana Mata yawa murya a shaqe tace"

Umma Dan Allah ya Isa 
Yana min yawa cikin Kai.

Dainawa umma tayi tana murmushi cikin kulawa tace"

To shikenan ai na barshi Haka Amma bazaki sauya kayaba.....idon da Naj din ta zuba Mata yasa ta waske zancen da sakin murmushi tana cewa"

Ko hakan ba laifi muje ku tafi gobe Amina zata kawo Miki kayanki Dattijo ma na gurin Dadah suna jiranki.

A dakin Dadah abun takaici agareta sabuwar nasiha da lallashi suka Dora Mata da dadin Baki da komai itadai tana jinsu batace komaiba sai sauraro  kawai sai Kuma zuciyarta dake Mata zafi da baqin ciki har lokacin Haka suka Gama ta ta fito itada Dadah da Dattijo Wanda ya fito da Kaya niqi niqi shida Anty Amina da Umma habiba kishiyar ummanta zasu maida gidansu Abbas acikin Daren.

Suna isowa bakin gate da wani irin sauri sojojin Marshal suka taso suka bude Mata kofa suna Mata gaisuwa cikin tsananin girmamawa dayasa Dadah sakin wata sabuwar hamdala cikin ranta abun na Mata Dadi sabanin Naj da "thank you" kawai ta iya bude Baki ahankali tace tana wucewarta kamar ba Amarya ba Kai tsaye gurin sashen hajjo suka nufa gidan tsit Suma duk baqi sun tafiyarsu.

Itace a gaba Dadah na bayanta da kallon ikon Allah da wannan Alamari saidai dayake lallabata sukeson Yi sai batace komaiba suka Isa babban palon gidan dazai isar da ita bangaren hajjo.

Kai tsaye ta shigo palon hajjo idonta dasuka kumbura suna kan kofar dakinta datakeda niyar shigewa ta rufe ta kwanta data shigo Dan Haka Bata lura da mutum dake zaune a palonba Yana cin abinci kan dining ta shige tabar Dadah dake shigowa da zama tana washe Baki ganin Jalal din zaune yanacin abinci tareda hajjo.

Cikin sakewa da farin cikin ganin Naj hajjo ta taso tana yiwa Dadahn barka da zuwa suka zauna suna sake gaisawa.
A 'dan taqaice ya taso yaxo suka gaisa da dadah yakoma dining din Dan baima faraba yanzune zai fara cin.

Hajjo na kallon kofar dakin da Naj tashige tasaki murmushi tana cewa"

Inshallah ahankali zata sake ai tamayi kokari da biyayya ko ahakan Dan Haka baza'a takirata ba zatai zamanta taredani har su daidaita da mijin.

Zare jallabiyar jikinta tayi tabar kayan baccinta har zata kwanta ta fasa ta fito Dan zuwa gurin hajjo Dan Bata Saba fushi da hajjon ba duk kuwa yanzu tanajin kaman antaru an Mata rashin kyautawa da adalci.

Tana fitowa dukkaninsu suka kalleta hajjo na murmushi tace"

Zo ki zauna Nan Najma Babu Mai takuraki akan auren Nan Inshallah,
Zaki zauna Dani har sai lokacinda kikaji da kanki kinason komawa gurin mijinki.... Da sauri Dadah tace"

Ba maganar saita buqata da kanta tunda ba itace me ikon kanta da yanda takeso ba,
Idan Kika biyeta tunda ba tunani cikakke akantaba da Haka zata qare rayuwar auren bare tana ganin cewan ta girmesa Wanda girmewar ta zama ta banza da wofi dankuwa yanzu a qasanshi kike.

Murmushi manya hajjo tayi tana kallon Najman dake gefenta zuru tace"

Bazata tareba saita buqata hakan da kanta inshallah,
Ina Kuma da tabbacin zata buqaci hakan Inshallah.

Kasa wata magana Dadah tayi sbd takaicin Najman datai shiru alamar hakan shine yayi Mata daidai ta miqe tana cewa"

To na tafi Ni Saida safenku Allah ya bamu alheri Dan dai Naga alamar a sashenki kila za'a haif....katseta hajjo tayi da cewa"

Amin ya Allah Dadah Saida safe" saboda sanin Dadah zata iya yanko zancenta tsakani da Allah.
##MAMUH#



*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107*_DM 14_*
Bayan tafiyar dadah hajjo ta kalli Najma da kallo daya zakai Mata kasan Kuka ta kwana ta yini tanayi duk da hakan fuskarta is so fresh sbd wankan da Bata Jima dayiba ga qamshinta tunda tafito ta zauna yake gauraye palon maida kallonta kan hanyar dining da jalal ke gurin har lokacin yanacin abinci Kamar wani sarki Wanda har lokacin Naj batasan da Yana palon ba ta miqe tana nufar hanyar dakinta tace"

Jeki ki kawomin ruwan dumi daki da Zuma zansha na kwanta 'yar gajiya nakeji.
Shigewa dakinta tayi tabar Naj na lumshe ido ahankali cikin sanyin jiki ta miqe ta nufi dining hanyar dining Dan dauko zuman tana tafiya a natse har saidata shiga dining area din da kyau taga Wanda ke tsaye agurin hannuwansa sanye cikin aljihun guntayen qananun kayan dake jikinsa  zai bar gurin tana isowa.

Mayun fararen idanuwansa ya 'dan zuba Mata sbd yaji maganar Dadah ta banbancin shekarunsu data kawo Wanda yasashima 'dan kallon nata Dan ganin abinda ake ikirarin ya girmesa a jikin nata Wanda a iya ganinsa baiga komaiba sai kayan baccin dake jikinta riga da wando ba bra ajikinta sai idanuwanta dasukai nuni da kukan datai ya kalli iya tsayinta da shafaffen cikinta ya dauke Kai ahankali Yana barin gurin yabarta tsaye tanajin wani irin damuwa da 'dacin zuciya me qarfi duba da kallon tsaf sama sama da yayi Mata ya dauke Kai ya wuce yabar gurin da qamshinsa na _Tom Ford, Tobacco vanille_ daya zama Kamar maita tasan qamshim kamar me sbd shikadai tasani me amfani da turaren Dan tsadarsa.

Numfashi me zafi ta sauke tareda shaqaqqen tsokin dabai fitoba taji duk komai ya fice Mata a sukwane ta hadowa hajjo ruwan takai Mata ta fito ta wuce daki ta kwanta tanajin wani Abu toshe a maqogoranta da qyar tasamu bacci ya dauketa.

Qarfe Tara na safe ta fito Palo sanyeda  doguwar straight gown ta atampar super exclusive maroon dataiwa farar fatarta kyau fuskarta fayau ko kwalli Bata sakaba saidai qamshinta daya zama na koyaushe dayake tashi jikinta idan ta kusantoka.
Da slippers a qafarta ta nufi kicin ta hado tea me zafi sosai tadawo Palo ta nufi dakin hajjo tana sha ta zauna kujerar dakin tana cewa"

Ina kwana hajjo.

Amsawa hajjon tayi tana cewa"

Kinyi waya da Hanifa kuwa?
Tun jiya Isma'eel yakira batajin Dadi Wai hannunta na dama ya riqe Yana ciwo kamarma yakira wayarki a kashe yace.

Miqewa tayi tana cewa"

Bari na dauko wayar tun jiya na kunna inaga Banda caji ne Bari nasaka nasamu ko kadan ne saina kirasu kafin na Isa.

Kallonta hajjo tayi tana cewa"

Ki Isa Ina da sabon aurenki akai Najma¿
Kinga hakuri Zakiyi tunda Isma'eel din na Nan Kuma Dr sa'id ma yaje tun jiyan Dan Haka basai kinjeba yanxu Bari a kwana biyu tukuna.

Shiru tayi yanayinta ba Dadi idanuwanta na sauyawa da ciko hawaye kafin Tai magana Hannah tashigo dakin da sallama muryarta a shaqe,hajjo na ganin fuskarta tasan itama kwana tayi kukan Dan kuwa a kumbure idanuwanta suke jajir.

Naj ta qurawa ido zuciyarta na wani irin harbawa da zafin radadin kishinta me qarfi saidai kamar yanda mum Malika ta hudubar da ita akan danne fushi da boye bacin Rai shine matakin nasarar komai tunda dai kowa yasan daga Naj din har marshal ba son juna sukeba aurene kawai na Hadi na huce takaici da fita kunya Dan Haka fushi da qunci ba nasu bane samun zama Matar JALAL da rabuwarsa da Naj ba wani Abune dazai Basu wuyaba ko daga musu hankali Dan Haka dole zasu danne 'dacin zuciyarsu.

Dan yaqen dole tayi tana qarasowa ciki ta zauna kusada Naj tana cewa"

Hajjo Ina kwana?
Ya gajiyan taro?
Allah yasanya alkhairi.

Hawayen datake dannewa suka gangaro ta qarasa gaban hajjo ta durqusa tana sake siririn kuka ahankali tace"

Dan Allah karkiga laifin kukana hajjo zuciyatace ke zafi bansan yazanyiba naji sauki bayan kukan sbd abin yazomin a bazatane.

'dan tausayinta hajjo taji Kuma tasan Kam Dole hannah zataji damuwar abin musamman datasan ayanzu Kam babu ranar auren Hannah din da jalal  sai taga Najmanta tasamu zama dakyau tukuna Dan Hakan takejin tausayin Hannah ta dafa kanta tana cewa"

Kiyi hkr shi aure muqaddarine Kuma Allah yayi itace zata zama Matar ayanzu Amma kadaki daga hankalinki  Matar mutum kabarinsace kema lokacin ne baiyiba ki kwantar da hankalinki kinji.

Shiru tayi tanajin wani qaton takaicin tsohuwar Yana tsaya Mata a maqoshi datake Mata zancen wani lokaci bayan ba Haka takeson ji ba.

Share hawayenta tayi tana miqewa a sanyaye ta juyo gurin Naj datake Shan tea dinta batareda ta maida hankalinta kan zancensuba ta Dan saki yaqen murmushi tace"

Naj Allah ya Sanya alkhairi da fatan bazaki ringa Jin damuwar alaqata da Marshal ba.

'dan kallonta Naj tayi kafin Kai tsaye tace"

Thank you" kawai taci gaba da Shan tea dinta Dan ita abundama zai ringa alaqantata da Marshal din Bata buqata Dan Haka Hannah ma na cikin abinda zata nesa kanta dasu.

Kallon tsaf Hannah taqare Mata tana ayyana wannan shariyar ta Naj datake Kamar wulaqantawa gareta kafin ta juya ta fice idanuwanta na sake kadawa da Jan baqin ciki da takaicin hajjo da Naj din.

Cajin wayarta Takoma daki tayi takira Hanifa sukahau wayarsu duk da taqi Bari Hanifan tayi Mata maganar auren itama Hanifan data fahimci Haka saita bar yimata maganar suka hau zantukansu.

Saida tayi sallar azahar ta 'dan ci abinci kafin taje gurin gaida Dad Alfa datun jiya Basu haduba tafara zuwa gurin mum Malika ta gaidata Kamar yanda suka Saba Babu komai a fuska mum din ta tarbeta suka gaisa Tai Mata addua da fatan alkhairi Hannah na daki tanajinsu taqi fitowa sbd ayanzu kyakkyawan fuskar Naj tafasa zuciyarta yake itakuwa Naj Kai tsaye palon Dad din ta nufa tana duba wayarta ahankali tashiga da sallama ta tura kofar palon tana kashe wayarta Yana zaune kuwa a palon suna magana da jalal dake gefensa sanye cikin farar jallabiyar datasa takasa ganesa sosai Dan kuwa hardasu qaramar farar hular tabani kaji hadisi datai Masa wani irin kyau sbd kayane dabai cika sawaba sai yazo Nan Dan acan kayansa idan ba suit ba sai uniform din aikinsa sai kuwa qananun kayan Shan iska dayafi sakawa idan baya aiki komai Wanda suna cikin kayan dasuke Masa kyau sbd kyan fatar jikinsa.

Dauke Kai tayi daga gefensa tanajin idanuwansa na yawo a jikinta ta qaraso ta zauna a qasa tana gaida Dad din cikin nutsuwa.

Amsawa yayi Yana Mata barka da gajiyar biki cikin farin ciki kafin ya Dora da yimusu nasiha musamman ita akan dole tabi umarni da hukunci  JALAL kowane irine cikin biyayya.

Shiru kawai tayi batareda ta dagoba har yagama ta Dan dago tace"

Nagode Dad" ta miqe ta fice batareda Tama nuna tasan da akwai wanzuwar wani a palonba bayan su.

Bayan fitarta waiwayowa dad yayi ya kallesa batareda yace komaiba ya Dan saki gajeran murmushi Yana mamakin qarfin girman Kai irin nasu su duka biyun Wanda bazai taimakesuba.
##MAMUH#





*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107[1/16, 2:58 PM] +234 808 457 6211: *_DM 15_*
Washe gari sanin a daki ta wuni taqi fitowa sbd fahimtar dai a sashen hajjon yakecin abinci abinda Bata saniba shine baya fitowa zuwa cin abincin Rana acan ake Kai Masa sbd baya fitowa da ranar sai dare yake fitowa cin abincin Daren Dan masallaci kawai yake iya fita cikin Rana Amma bayan sallah Babu abinda yake sakashi fitowa cikin Rana Wanda hakan ne yasa skin dinsa yake fresh koyaushe.

Hajjo na sane da dalilin qin fitowar tata Dan Haka itama Bata damuba tunda lallabata takeson Yi Dan Haka Bata dametaba ta qyaleta,
Sai dare ta fito sanye da riga da wando na bacci farare masu tsantsi kanta sanye da qaramar hular da Bata Gama rufe gashintaba hannunta riqe da waya tana sai qamshi takeyi me sanyi ta nufi kicin ta dauko fresh milk Mara sanyi sosai tafito tanasha ta nufi dining tana shiga idanuwanta suka sauka kansa Yana zaune cikin fararen qananun Kaya hannunsa riqe da cup din ruwa marasa sanyi yanasha ahankali.

Dauke kanta tayi tana kokarin juyawa hajjo dake zaune taredashi tace"

Zoki zauna.

Dakatawa tayi tareda Dan rufe idanuwanta kafin ta bude ta juyo tareda kallon hajjon fuskarta Babu wani sauyi daga straight din datake cikin muryarta me nutsuwa Kai tsaye tace"

Banajin yunwa freshi milk din ya isheni bacci zanyi Dan natashi da wuri gobe zankoma aiki office.

Dan kallon Marshal hajjo tayi taga ko dagowa baiyiba bare yanuna yasan da zuwan wani agurin saidai tasan yanajinsu,
Ta maida kallonta kan Najma cikin kulawa da tausasawa tace"

Wane aiki bayan Baki Gama hutawa daga hidimar biki ba Kuma saikun zauna da mijinki kunyi magana akan aikin idan yaji zai Bari kici gaba.

Dagowa Najma tayi da idanuwanta dasuka sauya Nan take da maganar ta kalli hajjo sai Kuma takasa magana tayi shiru tana hadiye wani daci daya danne zuciyarta ta Dan rufe ido tabude ahankali tace"

Kaina Yana ciwo zanje na kwanta Saida safe hajjo.

Juyawa tayi zata wuce hajjo tace"

Dawo Najma zoki zauna.

Dakatawa tayi tafara sauke numfashi kadan kafin ta juyo tadawo taja kujera ta zauna batareda tace komaiba sbd Jin numfashinta ma takeyi Kamar siqe zamanta agurin da Wanda har lokacin Bai nuna yasan da wanzuwar wata halittar Dan Adam agurinba Wanda Kamar Ana sake sukar martabartane na mace dakuma girmanta.

Ahankali ya dauka tissue yana goge bakinsa Dan yagama cin abincin sai alokacin ya dago ya kalleta Yana kallon hajjo datake lallabata da alama zatai taurin Kai da taurin zuciya 
Ya dauke Kai ahankali tareda miqewa tsaye ya zuba hannuwa a aljihun wandonsa ya bude Baki Kai tsaye a gajarce yace"

Saida safe hajjo" ya juya ya wuce yabar gurin harya fice itama Bata dagoba bare ta nuna tasan dashi,

Kallonta hajjo keyi tana Jin qaunarta da tausayinta tareda jinjina taurin zuciyarta Dan kuwa sosai ta hango tsanar auren da qinsa cikin idanuwan Najma da zuciyarta,
Bataji dadin hakan ba Amma Kuma Dole za'a dubawa Najma din tunda aurene na Babu shiri Babu sanarwa Babu amincewa musamman yanda take yiwa auren jalal din auren ci baya qarara amatsayinsa na qanin qawarta Wanda Kuma takejin bazata iya russunawaba ya juyata kamar yanda maza ke juya matayensu.

Hajjo da kanta ta janyo plate ta zubawa Najman abinci kadan iya Wanda tasan tana iya ci ta turo Mata gabanta cikin kulawa tace"

Ci abinci kafin kije ki kwanta din karki kwanta Babu wani Abu me Dan nauyi a cikinki kinji.

Bata iya gardamaba Sam musamman a yanzu da zuciyarta ke cikin wani hali Dan Haka ahankali tadauki spoon tafara cin abincin hajjo na kallonta tana sake Bata Baki akan karta damu Babu Wanda zai takurata akan komai.

Daqyar tayi spoon shida ta dauki ruwa Tasha ta ajiye ta kalli hajjo cikin nutsuwa tace"

Na koshi zanshiga daga ciki.

Tare suka miqe saidata raka hajjo har dakinta ta sake gyara Mata gadon kwanciyarta kafin Tai Mata Saida safe ta fice.

Tana Shiga daki toilet ta wuce tayi brush tafito ta hau gado ta kwanta tana rufa da bargo wasu hawaye suka gangaro Mata saiga kuka ya kufce Mata ahankali ta rufe idanuwanta tana sakin kukan ahankali tanajin wani irin radadi a zuciyarta,
Bayan qaddarar rashin aure data fasawa qarshe dai qaddarar irin wannan aurence take jiranta,
Auren Wanda ta girma,Wanda ko kallo Bata isarsa bare ya nuna sanin da ita a duk haduwar dazasuyi tayaya zatai rayuwa ahaka a gurin Wanda tafi Amma agurinsa ita ba komai bace face ta qarqashinsa,
Bata buqatar soyayya Amma dai tayi fatar yin aure inda zatai rayuwar 'yanci da mutuntawa tareda Bata kulawa da qaunar data rasa samu tun tashinta,
Batada shaquwa da mahaifiyarta sosai sbd miskilancinta,batada shaquwa da 'yan uwanta da kowa nata face Hanifa wadda itama itace me kokarin riqe shaquwar tasu sbd miskilancinta Dan Haka tayi fatar jinkiranta ya zamar Mata alkhairi tasamu mijin dazai rusa miskilancinta ya cike gurbinsa da soyayyarsa da qaunarsa Amma Haka qaddara tazo Mata Wanda ta gwammaci zamanta Babu me aurenta da wannan auren dazai ringa quntata rayuwarta a zahiri da boye.

Washe gari Haka takuma wuni a daki Bata fito ba a dakin ruqayyat takai Mata abinci Wanda hajjo tasa akai matan.
Koda daddare Bata fitoba saidata tabbatarda ya bar sashen ta fito taje tayiwa hajjo Saida safe Takoma takwanta.

Saidatayi kwanaki tana kiyaye duk wani Abu dazai hadata dashi ko a hanya ne dan ko Dad Alfa idan zataje gurinsa saita Gama tabbatarda Rana tagama tsagowa lokacinda taji baya fitowa kenan a bakin hanifa take zuwa gurin gaidashi su mum Malika ma tana Dan shiga sama sama sbd lurada Hannah Kamar tana Dan Jin zafinta Wanda Sam gabaki daya daga Hannan har Wanda takeyi dominsa basa gabanta Bata Kuma buqatan su shiga gaban nata.

Daqyar taga sati biyu tacika Isma'eel ya koma Hanifa tadawo gidan sai alokacin taji hankalinta yadan dawo Mata musamman yanzu da Bata ganinsa Babu me Mata maganar auren saitake mantawa tana fitar da abin a kanta ta tattara maganar auren ta watsar gefe tafara kokarin son komawa aikinta Amma Kuma Bata buqatan kowa yasake tada mata maganar Saida izinin wani ko damar wani zata fara fita aiki hakan yasa taketa dannewa.

Ta bangaren Marshal kuwa kamar yafita mantawa da maganar auren Dan kuwa gabaki dayama ya daina shigowa ko cin abincin akai akai wani lokacin Hanifa ce ke kaimasa suyo firarsu da maganganunsu dasuka shafesu acan duk da yawanci nasa sauraro ne sai kadan kadan yake saka doguwar magana tanason sako Masa maganar Naj Amma tana Hana kanta kamar yanda suka yanke da hajjo bazasu takuraba akan zancen ahankali komai zai daidaita.

Lokacinda tasamu labarin komawarsa abakin hajjo da Hanifa Sam Bata nunama tajiba Dan ba abune daya shafetaba Dan ita yanzu tabar auren akan hanyar data sauya Mata na uzzurawarsu Dattijo dasu Dadah da ummanta ma hakama dai tana gidane bawai wani gurinba hakama Wanda ake Kira da mijin da auren duk basa gabanta itama Bata gabansu Dan Haka hakanma is okay tunda tasamu yancinta ta wani bangaren.


Yau ciwon baya Hanifa ta tashi dashi me 'dan qarfi Dan Haka bayan zuwan Dr sa'id yadubata yabata wasu magani da wasu treatment dayasa sukai mata na Nan gida tasamu sauki Sosai ba laifi musamman datai bacci Sosai har yamma kodata farka alhmdlh taji sauki saidai Dan sanyin jiki na rashin qwari na wuni datai kwance Dan Haka wanka Naj ta taimakata Mata tayi tayi salloli taci abinci sai alokacin ta dan sakewa ta dauki wayar mijinta dake Kira tun dazu yanajin Yaya jikin.

Sai alokacin Naj tasamu nutsuwa tafito taje taci abinci tadawo tayi sallar ishai da aka Kira tana idarwa ta  tube ta shige toilet wanka Dan bacci takeji Sosai.

Tun safe baya gida Yana gurin wani sabon company da Dad Alfa zai bude rashensa anan Wanda Marshal din zai sake zuba hannun jarinsa me kauri kamar yanda shares dinsa sukafi yawa a wancan company din da Naj take gudanarwa.
Sai kusan magriba suka dawo Dan Haka sallar magriba yayi ya shige Saida ya huta yayi wanka yayi ishai kafin ya nufo sashen hajjon qamshin TF tbc daya Gama Kama jikinsa Yana tashi jikinsa Hannah datakai Masa fruits salad daya 'danci kadan suka fito tare zuwa sashen hajjon tana gefensa tana Masa fira cikin wayewarta da sonsa daya Gama cire Mata kunyar kowa itama sai qamshi takeyi tana sanye da doguwar free grown me guntun hannu dayake bayyanarda tattoo dinta me dauke da sunansa a gefen kafadarta.

Babu kowa a Palo sai qatuwar LG TV dake aiko Dan hajjo na dakinta Kai tsaye suka nufi dakinsu Hanifan hannah na daukeda sauran fruits salad din dazata kawowa Hanifan Dan nuna kulawarta da damuwarta.
##MAMUH#




*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107
[1/16, 2:58 PM] +234 808 457 6211: *_DM 17_*
Koda tagaji da kwanciya da kame fuska taga hakan zai sake cutatar da itane sai kawai ta watsar da al'amarin ta sakewarta taci gaba da abun dayake gabanta tayi wanka ta shirya cikin riga da wando na Shan iska tafito ta nufa kicin ta hado abin datake buqatan ci tadawo dining ta zauna tanaci Hanifa ta fito itama a shirye cikin atampa doguwar riga tayo gurinta tana cewa"

Zanci Nima yunwa nakeji.

Qarasowa tayi ta zauna tana kwada Kiran ruqayyat tace"

Ki kawomin abinci Nima inajin yunwa sosai.

Sunacin abincin tanata jawo fira da zantuka kala kala Wanda dama tasaba itace me janyo Hira a tsakaninsu itace me zancen itace me Hira.
 
Palo suka dawo suka zauna bayan sunyi sallar azahar da akai suka dasa Hira hajjo na daki yau batajin Hira karance karancen Islamic books dinta  takeyi.

Da yamma sosai saiga Sarah takawo Mata wasu files da ake buqatan tayiwa signing Nan ta maida hankali kan takardun tana dubawa Sarah na qara koro Mata sauran bayanan ayyukan dasuke zaman jiranta a office din tanason ta sanar da ita Abbas yadawo aikin da kowa yayi tunanin zai ajiye Amma Kuma ganin Hanifa yasa takasa fadar maganar tunda yanzu Naj din surukarsu ce kawo Mata maganar wani ba daidai bane zata Bari sai Takoma office din zata sanar Mata.

Ganin hankalin Naj yakoma kan aiki gabaki daya dama ita abida yasa takeson aikinta sbd shi kadaine zata zauna tayi batareda wani surutu ko hayaniyaba shirun tana aiki Yana bada nutsuwa Dan Haka Hanifa tabarta Takoma kicin gurinsu ruqayyat suna aikin abincin dare dama ita tana aiki cikinsu lokuta da dama sbd tanada sha'awan girke girken.

Sai bayan magriba tagama duba ayyukan da Sarah din takawo Mata suka tashi sukai sallah kafin Sukaci abinci Sarah tayi shirin tafiya gida suka fito tare ta rakota har waje tareda miqa Mata 10k tace tadauka drp na taxi taje gida.
daidai ta juya zata shige ta hango Hannah tafe tun Bata qarasoba tayi wucewarta Dan bazata iya da sauraren maganganuntaba.

Tana Isa daki ta wuce saidatai sallar ishai kafin tayi wanka tayi Shirin bacci takwanta sbd tana jiyo hirarsu Hanifa har lokacin Hannah na sashen.

Washe gari Haka ta wuni tana aikin wasu takardun data saka Sarah kawo Mata tun tanayi sama sama kwanaki suka Dan fara ja kusan tadawo da aikin office dinta gida takeyi saidai Sarah Dake faman Shan yawo tsakanin office da zuwa gidan kullum.
Hajjo data lura da aikin na Sanya Naj din samun nutsuwa sai tafadawa Dad Alfa akan maganar komawar Naj din aiki duk da Bata wani so Naj din Takoma aikinba Amma Haka ta hakura tabari saidai tasan JALAL zaiyi wuya yabari tunda ita din yanzu matarsace.
Dad alfa dakansa yayiwa Marshal magana cikin nasa mamakin yaji Kai tsaye yace abarta taje 
Shikuma kawai bayason arinqa nanata Masa maganar auren da nauyinta dake kansa Dan tunda ya dawoma yamanta da maganar auren yake aikinsa da rayuwarsa yanda ya Saba ko tunota sai Yana waya dasu hajjo yakeyi idan sun jeho Masa maganarta.

Ta bangarentama tunda aka Bata damar komawa aiki tafisa mantawa da auren musamman da Dad Alfa ya siya Mata lafiyayyar sabuwar motar datake hawa Dan Haka yanzu aiki takeyi cikin nutsuwa da kwanciyar hankali,
Babu damuwa da tunanin fada da gorin dattijo, Dadah da ummanta akan rashin aure saima kulawa da qauna dasuke nuna Mata a yanzu din Wanda yake na lallabawa kada ta bijire auren ya kwabe lissafi yadawo musu sabo,
Ta bangaren office kuwa yanzu girman datake samu gurin ya zarta na kowa dake ALFAS din sbd yanzu tana amatsayin Matar me company dinne sbd sanin da kowa yayi Marshal shikeda 60% shares a company din.

Abbas duk wani Abu dazai hadasu bayan meetings batabi sbd har lokacin Yana sauran 'danyar haukarsa atare dashi Dan kuwa kallo yake Mata harna qurulla wani lokacin Kuma harda 'yan maganganu Amma Bata taba ko kallon inda yakeba Dan dama wannan tun suna tare yasan halinta dabi'artane rashin tankawa da kulawa.
Qarshe sbd nunawa da son nuna rashin gazawarsa da kausar yafara soyayya receptionist dinsu Kuma cikin gaggawa suka fara gabatarda komai lokaci qanqani saigashi Ana sanarwar aurensu Nanda wata biyu masu zuwa.
Duk wannan sha'anin nasane yakeyi shi kadai Dan kuwa ko hankalin saurara Bata badawa idan Sarah na kawo Mata zancen abindayeke faruwa bare ta fahimci menene dinma yake faruwa.

Sosai yanzu takejin dadin rayuwarta Babu takura Babu wani damuwa Haka take gudanarwa,
Kullum zata tashi tayi Shirin office tafito tasa masu aiki suyi Mata abinda takeso taci taredasu hajjo da Hanifa, tafito taje gurin dad Alfa tai Masa gaisuwar safe kafin tafito ta wuce aiki,
Idan tadawo zatai wanka tayi sallah taci abincin tayi baccin yamma kafin tatashi tayi sallar magriba sai suyi firar dare dasu hajjo wani lokacin idan Batai baccin yammaba gidansu take zuwa acan take baccin dakin ummanta kokuma firarta dasu duk da ba itace me firarba Yi akeyi tana Dan amsawa da eh ko aa sai ido datafi sauraron hira dasu.

Ahaka lokaci Mai Dan tsayi yaja tasamu sauyi sosai na jiki da rayuwa Dan kuwa fatarta ayanzu tafi samun qarin hutu da lafiya tareda kyau.
Tayi fresh sosai sbd har wani irin haske take qarawa kullum musamman dayake itama Bata cika Shiga Rana ba Dan rayuwarta bazata iya yaushene zuwanta kasuwaba kokuma siyayya irin gurare masu Rana sosai haka yawanci siyayyarta online shopping takeyi akawo Mata har gida sai idan sunso su fita da Hanifa zuwa manyan malls Haka siyayyan Yan abubuwan amfaninsu kaman su turaruka dasu Mai sai undies da qananun Kaya Haka 
Musamman ita Naj indies basa isarta kullum cikin siyansu take.

Gabaki daya rayuwarta ta manta da auren dake kanta sbd rayuwar data samu kanta aciki ta rashin takura shiyasa ta sake sosai tana gudanar da rayuwar yanda takeso.

Kamar dai yanda Dr said yasake hadawa Hanifa appointment da  Dr Kenneth a Sweden yanzu lokacin zuwanta ya qaraso Dan Haka suke cikin damuwa musamman Hanifan Wanda tasaka ran samun haihuwa sosai a ranta.
A yanda suka bibiyi likitoci tun shekarun aurensu na farko an tabbatar musu da cewa Hanifa bazata iya daukan ciki da kanta ba ma'ana zaiyi wuya saidai ayi Mata dashensa Wanda ta daga hankalinta sosai tashiga damuwa Suma sumshiga damuwa sbd halindata shiga qarshe akai dashen cikin na wata biyu ya fita shima tashiga wani mawuyacin hali na tashin hankali da shiga qunci da addua da komai aka samu ta dangana tayi tawakkali tadawo daidai saidai sun dibar Mata lokacinda zata dawo asake Mata dashen Wanda shine lokacin yayi yanzu saidai Kuma damuwa da tsoron ko zata samu ko bazata samuba ya Hana zuciyarta sukuni duk yanda takeson danne damuwar kasawa takeyi Wanda yake sake sakawa hajjo tausayinta sbd tana cikin jarabawa ta lalurar lafiya yau gobe Babu ga wannan jarabawa ta rashin samun haihuwa Dan ma tanada tawakkaline soda dama Koda damuwar abin ta taso Mata tana dannewa da rokon sassauci gurin ubangiji gashi a zuriar gidan basuda iyali da yawa sune suke fatar su cika gidan da nasu yayan Amma batajin za'a samu daga gareta kila saidai 'dan uwanta JALAL.

Damuwar da Hanifa take ciki tasa gidan kusan kowa damuwar yakeji ita kanta Naj din tunda aka tsaida ranar tafiya Sweden din ta nema hutu office ta daina zuwa koyaushe tana tareda Hanifar wadda damuwa tasaka ciwon  gefen ciki ya kamata cikin lokaci qanqani ya kwantar da ita Nan hankalinsu yakuma tashi ga tafiyar nata sake qarasowa Dan saura Kwana biyu su wuce wannan karon tareda Naj din zasu sbd zasu hade da Isma'eel acan sai Hannah data nace akan zataje itama sbd ta tabbatarda Marshal zaije can daga Hawaii.

Kwana biyu Ana fama da jikin Hanifan ansamu ta 'dan ji sauki ta warware Haka suka lallaba suka tafi tareda Dr sa'id din Wanda yake likitanta.
##MAMUH#



*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*


*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107
[1/16, 2:58 PM] +234 808 457 6211: *_DM 16_*
Hannah ce tayi Dan knocking dakin so biyu kafin ya tura kofar suka shigo tana Dan nuna kulawa ta qarasa gurin hanifan tana ajiye bowl din hannunta kan table tana cewa"

Ohh sister in-law sannu da jiki tun dazu naso shigowa kaina Yana Dan ciwone shiyasa ban shigoba ya jikin?

Gyada Kai Hanifa tayi tana cewa"

Alhmdlh naji sauki thank you.

Dagowa tayi ta kalla Marshal din Yana tsaye da hannu cikin aljihu ganin hanifance kawai a dakin yasashi zaunawa ahankali kan sofa Yana kallonta da fararen idanuwansa ya bude Baki cikin kulawa yace"

Yaya jikin?
Ina tare da dad yau duka sai yamma nasamu kaina,
Dr sa'id yamun bayanin komai Yace hadda sanyi yana Miki yawa meyasa bazaki daina kwana da AC ba?

Murmushi ta 'dan saki tana kallonsa yanda koyaushe yake tamkar shine yayan sbd irin tasa kulawar.

Gyara zama tayi tana kallonsa da sauran rashin kuzari a muryarta tace"

Ina kiyayewa Marshal.

Jeho kanta Hannah tayi cikin zancen da cewa"

Sister in-law Allah yabaki lafiya duk mundamu dake bamason ganinki cikin irin yanayina ciwo musamman Marshal he cares for you so.......katsewa zancenta yayi yawu na neman zubo Mata daga Baki tayi saurin hadiyewa sbd idanuwanta dasuka sauka Kan kofar toilet da aka bude Naj ta fito daureda towel sky blue me haske cinyoyinta dasukafi komai tada hankalin Hannan sai daukan ido sukeyi tayi sama da idanuwanta kan qirjinta dasuka fito Dan fito ta saman koina jikinta daukan ido yakeyi gashinta daure a tsakiyar kanta ta dauresa da Banda gabaki daya Bata lura dasuba Dan batasanda suna dakinba Dan hakan taqarasa fitowa Kai tsaye ta rufo toilet ta nufi closet tana cewa"

Hanifa ruqayyat takawo wankin kayan da aka dauka jiya??

Tsit dakin yayi musamman Hannah data waiwayo da sauri ta kalli marshal din taga idanuwansa basa kan Naj suna kan wayarsane ta kalla Hanifa da ita Kuma Jalal din take kallo Dan kuwa akan idonsa sak Naj ta fito Kuma ta tabbatarda ya qarewa Naj din kallo sak kafin ya basar ya dauke Kai.

Da sauri Hannah ta miqe tana cewa"

Umm Naj Ashe kina ciki bamu saniba sorry Bari mukoma Palo zamu jira ki Gama shiryawa tukuna.

Wuta Naj ta dauke tareda waiwayowa  cikin tsananin mamaki da takaici ga sabon baqin cikinta ba Hannah ce kawaiba akansa idonta ya sauka daidai ya dago zai miqe ya fice idanuwansu suka shiga cikin na juna ta dauke idonta suna sauyawa kin wani irin baqin ciki da kunya da takaici lokaci daya suna taso mata ta juya Kai tsaye Takoma toilet din daukeda kayan barcin data fitar zata saka a hannu.

Kodata Gama shiryawa ta fito basa dakin sun tafi har Hanifa Bata dakin tana dakin hajjo taredashi da hajjon suna magana sbd gobe zai koma duk yanda taso kasa Masa maganar Naj din kasawa tayi ta kalli fuskarsa dake fresh Kamar wani Dan baby hankalinsa nakan hajjo Yana sauraron bayanin datake Masa akan dawowarsa yanzu akan lokaci sbd akwai nauyin iyali akansa.

Marshal bazakai magana da itaba kafin ka wuce?
Kaji koda akwai wani abun datake buqata?

Shiru sukai suna jiran Jin amsarsa saisukaga ya miqe Yana kallon agogon  hannunsa yace"

Zanje na kwanta gobe zantashi da wuri.

Kofa ya nufa hajjo tace"

Goben ka tabbatarda kayi mgn da ita kafin ka wuce.

Da umarni tayi maganar ba wani Wasa acikinta shiyasashi Dan dakatawa batareda ya juyoba kafin ya taka yafice Hanifa na bayansa tana sake Dan saka Baki a maganar.

Sam ba irin wannan auren yasoba Wanda kowa zai ringa shiga tsakanin mu'amalarsa da matarsa sbd yanason yayi nutsatsiyar rayuwar aure Mara hayaniya da soyayyarda baya buqatan  shigan wani zancen,
Ya lura zata ringa hada Masa tarin mutane acikin rayuwar auren Wanda baya buqatan hakan Amma zaiga tsarin dazai dauka.
Koda ya Isa sashensa Saida yakuma wanka da ruwan dumi kafin yayi Shirin bacci ya kwanta.

Bacci me qarfi da dadi itama yau tayi shiyasama tayi lattin tashi sallar asuba Dan sai guraren qarfe bakwai ta bude idanuwanta dake tareda sauran bacci ahankali tana Dan motsawa ta lumshe ido sbd Jin sabon qamshin daya Shiga hancinta ta tashi zaune tana 'yar miqa botiran gaban rigarta uku na sama suna budewa sbd miqar datai ta zuro qafafunta qasa tareda miqewa tsaye idanuwanta suka sauka Kan mutum a tsaye cikin dakin Yana kallonta jikinsa sanye da _Prada-gabardine straight leg trouser _ brown sai White spread collar long sleeves gabaki daya dakin ya gauraya da qamshinsa fararen idanuwansa ya zuba Mata akaro suna yawa ajikinta sbd tunda aka daura Masa aure da ita ake maimaita kalmar girmansa datai Wanda haryau yakasa ganin wani Abu dayake tunanin ya girme Masa 
A taqaicema kallon dayake Mata yasa yake qara ganin zamtowarta qasanshi.

Kallon dayake Mata yasata dakatawa daga wucewar datasoyi ta shige toilet saita nufi kofar ficewa daga dakin zata fice bacin ran dake ranta Yana bayyanuwa kan fuskarta akaro na farko da mace ta wucesa tabarshi tsaye 
Kai tsaye ya damqi hannunta tareda dawowa da ita baya ya tsayar da ita gabansa fuskarsa a hade tsaf ya kalli hannunta datake kokarin fuzgewa a fusace batareda tace komaiba Dan bazata iya bude Baki Tai Masa mgna ba Sam,
Ba wani riqo yayi Mata ba Amma gabaki daya takasa qwacewa ta dago a fusace ta kalli fuskarsa idonsa cikin nata ta janye idonta Kai tsaye tace"

Meye hakan?
Kabar hannuna.
Wannan auren ba wani aureneba kamar kowanne dazai baka Daman tabani so can u get your hands off me.

Sabon kallo yayi Mata Jin abindata fada daya basa mamaki Dan baiyi tunanin zata iya magana Haka ba.
Fizgota yayi ta Fado jikinsa ya dago shanyayun idanuwansa ya zuba Mata Yana kafin ya kalla kirjinsu daya manne Dana juna tana ganin hakan ta qwace da qarfi cikin tsananin bacin rai tareda turesa da iya qarfinta yayi baya ya zube kan gadon dakin kafin ta juya ya janyota tafado jikinsa daidai turo kofar Hanifa data shigo dakin Hannah na bayanta Jin shiru sbd dama itace ta fito din tace yashiga Naj din na ciki Dan wucewa zaiyi.

Da sauri a firgice Naj ta waiwayo kofar tana kokarin tashi daga jikinsa idanuwanta na cikowa da hawayen baqin ciki da bacin Rai
Hanifa kuwa juyawa tayi da sauri tana cewa"

Sorry sorry.
Hannah kuwa da sauri ta qaraso gurin tana Kama Naj dakeson tashi tana cewa"

Bari na taimaka Miki.

Sakinta yayi yana tashi daga kan gadon Kai tsaye ya fice daga dakin Yana duba agogon hannunsa sbd lokaci dayaso shige Masa Bai luraba.

Hajjo Kamar koyaushe idan zai tafi har mota take rakasa itada Hanifan Haka suka fito Hannah na gefensa tana fada Masa irin yanda zatai missing dinsa a can harabar gidan ya tararda Dad Alfa dazasu fita tare tareda mum Malika daketa zuba nata iyayin na zatai kewarsa matsayinta na uwa.

Gidansu Naj yashiga tareda Hanifa yaje yayiwa umma bankwana tareda bar Mata abindaya Saba Bata duk yazo idan zai koma hakama Dadah wannan karon kyautar dataso firgitata yayi Mata kafin yafito tareda Dattijo suna maganar Yana sanar dashi abar Naj din taci gaba da aikinta idan tanada ra'ayin.

Motarsa data sojojinsa lokaci daya suka tashi sukabar kofar gidan wasu na 'yar murnar zasu samu 'yancin unguwa zakai iskancinsa cikin anguwa yanda kaga dama ka tada hayaniya da rigima son ranka tunda sojojin Marshal sun tafi sojojin dake tsoron gidan basuda muguwar fitina da ikon wahala Kamar na Marshal din  matuqar Yana gari ko Rigima da fada andaina a layin Dana bayansa sai Kuma suntafi Dan Haka yau kowa yayi yanda yaga dama.


Toilet tashige saidatai kukan baqin ciki Mai isarta kafin ta iya alwala ta fito baqin ciki da kunyar kanta na kamata tayi sallah tana idarwa tun kafin Hanifa tadawo dakin Takoma tayi kwanciyarta ta rufa tana rufe ido Dan komawa bacci saidai tasan halinda zuciyarta take ciki bazata iyaba.
Hanifa data dawo dakin Bata wani jawo zancen komaiba itama Takoma ta kwanta tana murmushin abinda itace kawai tasan metakeji aranta.



*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107
[1/16, 2:58 PM] +234 808 457 6211: *_DM 18_*
Koda jirginsu ya sauka Ana ruwan sama Dan hakan Isma'eel ne yazo da mota ya daukesu Kai tsaye suka wuce _copperhill mountain Lodge_ inda marshal yake zama matuqar Yana Sweden din,Koda suka Isa room cards din dakunansu suka karba suka wuce 
Dr sa'id gabaki daya ba'a Lodge din ya saukaba nasa masaukin ya nufa Wanda yasaba zama Dan shima Yana Dan zuwa qasar akai akai Dan Haka dakin Isma'eel da matarsa Yana farkon floor din saina Hannah agaba tukuna na Naj acan qarshe Wanda dakin Marshal ne Isma'eel yabata card din batareda yayi tunanin komaiba tunda dai yasan zasu iya zama daki daya.

Dama sai asuba suka sauka qasar Dan Haka Koda suka shiga dakunansu har qarfe Tara na safe ta kusa Dan Haka wanka ajiye luggage dinta tayi cikin wdrp ta tube kayan jikinta ta jefe laundry ta nufi toilet ta sakarwa kanta ruwan zafi tana lumshe ido sbd Jin dadin saukansu a jikinta ta gasa koina nata tafito daureda towel qarami tana goge jikinta sai alokacin take qarewa dakin kallo da irin tsarinsa daya burgeta Dan kuwa komai haduwarsa a tsarance da natse take musamman komai na dakin is white ta nufi wrdrp ta fiddo qaramar akwatinta ta fiddo kayan shafarta ta ajiye gaban mirror ta dauki wasu kayan bacci riga da wando ta dawo gaban mirror sama sama ta shafa body mist ta saka kayan baccin ta dauko wayarta ta duba alkiblan sallah ta Dora jallabiya kan kayanta tayi sallolin da ake Binsu Ana idarwa ta cire jallabiyar ta maida ta Haye gado tashige bargo sbd wani irin bacci da gajiya takeji gabaki daya jikinta ba qarfi,
Wani irin bacci me Dadi da nauyine ya dauketa cikin nutsuwa gashi har lokacin ruwan saman akeyi Bata farkaba sai qarfe biyu da mintuna shima knocking kofan da akeyine ya tada ita ta bude idanuwa ahankali tareda tashi zaune ahankali taji Ana cewa"

Ur Lunch is here Sir.

Saukowa gadon tayi ahankali ta zura slippers din dake dakin masu taushi ta nufi kofar tana Dan mamakin Jin Sir din data ambaya ta bude tana amsa gaisuwar waitress din data kalleta da mamakin ganin mace sbd qarqashin sunan Deen Marshal akai booking dakunan Kuma a iya saninta wannan dinne nasa shigowa tayi ta nufa dining ta jere mata abincin tareda ruwa da drinks masu qarfi ma'ana energy drink Wanda Marshal din Kesha dama sune ake kawo Masa aduk lokacinda za'a kawo Masa abinci indai Yana lodge din ta juya ta fice bayan tagama tunda Babu ruwanta da sanin waye Naj Kuma Ina me dakin.

Brush tayo tafito ta nema wayarta ta zare layinta ta saka layin qasar da tun kafin su iso Isma'eel ya siya Mata dama itace kawai batadashi Amma dukkaninsu suna dashi har Hannah wadda dama tasaba yawon qasashenta da qawayenta ita dinma ta Dan fita wasu qasashen Amma ba dayawaba gurin aikinta da yawon ganin likitocinda Hanifa keyi tun kafin tayi aure Dan Haka itama sosai take waye da harkan qasashen na waje musamman ma dayake tafisu zama a miskilancen dayake bayyanarda ajinta sai hakan yake fin yimata kyau da fitarda wayewarta.

Bayan ta saka layin yahau massage din Isma'eel yashigo Mata akan shida Hanifa sun fita zuwa wani gurin Hannah ma ta fita zuwa gurin friends dinta saisun dawo.

No hajjo tafara Kira suka Dan Jima Suna magana kafin takira ummanta suna Gama magna ta ajiye wayar ta nufa dining din ta zauna tana duba abincin
 duka ba taste dinta bane Amma Haka ta Dan ci kadan Tasha drink dinda Bata tsaya dubawaba sosai tafin ta miqe tabar gurin tana duba chats a wayarta tsawon mintuna saiga room service suka sake gyare gurin aka fitarda kayan abincin sauran drinks din Kuma aka saka a fridge bayan fitarta ta rufe dakin tashiga wanka.

Sai dare Su Hanifa suka dawo Hannah kuwa da alama acan zata kwana 
Koda suka dawo tuni ta kwanta saidai sukai Saida safe a waya sbd ciwon Mara dake damunta yanda Hanifa taji  muryarta yasata zuwa dakin ta dubata saidai ta Dan daure ta nuna Mata ba wani Abu kawai Dan ciwon marane hakanan Hanifa ta tafi tabarta saidai ta tafi da room card din dakin sbd zuwa dubata idan taji shiru da yawa ta fice ta tafi bayan ta rufo Mata dakin,tun yamma yafara yimata ahankali yanzu yafara yimata tsanani Dan kuwa sosai take jinsa gashi tasan lokacin period dinta baiyiba da sauran lokaci.

Daqyar tasake lallabawa tayi wanka da ruwan zafi sosai ta 'dan gasa Marar ta fito ko miqewa tsaye Bata iyayi sosai ta daddafa daqyar ta Isa gadon ko kayan bacci Bata iya sakawaba ta fada gadon ta dunqunqune cikin duvet cover tana rufe idanuwanta dasukai ciki ciki sbd azaba.

Qarfe goma Sha biyu jirginsa ya sauka Bai tsaya jiran Azo daukansa ba yadauka taxi ya qaraso Lodge din tun daga reception aka sanar dashi katin dakinsa Mr Isma'eel Khamis ya karba Baice komaiba ya wuce ma'aikatan gurin na biyedashi da luggage dinsa.

Bangaren dasuke Yana daya daga cikin kebantaccen bangare da ba'a aje mutane da yawa yawanci ma sai couples sbd rashin hayaniya da tsaruwarsa Kai tsaye wayarsa ya fidda yayiwa Isma'eel text cewan gashinan hanyar dakinsu ya miqo Masa katin dakinsa.

Cikin sa'a katin na hannun Hanifa Dan Haka Kai tsaye ya karba ya fito suka hade a Hanya ya miqa Masa Yana Masa barka da isowa suka rabu ya wuce dakin duk da baya tareda gajiya sbd Babu wani nisa sosai daga can din zuwa Nan.

Kai tsaye bude dakin yayi da katin ya shige tareda karban luggage dinsa ya qarasa shigewa dashi ya rufe kofar Yana nufar Yana kunna wuta Mara haske ya aje wayarsa Yana Dan motsa fuskarsa sbd qamshin dayake gauraye da dakin na turarent possess dakuma humrah me sanyin qamshi.

Yamutsa fuska yayi Yana nufar fridge ya bude yaga har drinks dinsa ansaka a fridge din ya dauka daya ya bude ya shanye ya juya yabar gurin ya nufa toilet yashige tareda tubewa ya sakarwa kansa ruwan zafi yayi wanka da brush ya fito duk lokacin Bai lurada fararen panties din dake shanye a hanger na toilet din ba yafito daure da towel ya shirya cikin fararen _Fred Segal pyjamas_ ya kashe wayarsa gabaki daya ya nufi gadon ya Haye Yana yaye bargon zai shiga Yana ayyanawa aransa tabbas Hanifa tashigo dakinsa shiyasa yake ganin komai ba daidaiba da safe zasu sauya Masa kusan komai na dakin qamshin Nan na matane Yana Masa yawa.

Jin jikinsa yayi ya hadu Dana mutum da sauri ya tashi zaune Yana Dan yaye duvet din yakai hannu kan side lamp ya kunna Yana waiwayowa idanuwansa suka sauka Kan fararen cinyoyinta dasuke bayyane towel din jikinta ya zame saura kadan yabar jikinta 
Ya dauke idanuwansa Yana maidawa kan fuskarta dake fayau tana baccin wahala Wanda ya takeyi tana farkawa sbd tsananin azaba.

Saukowa yayi gadon Yana Dan rintse idanuwansa cikeda mamaki da takaici ya dauki wayarsa ya kunna Kai tsaye no Hanifa yayiwa text cewan waye a dakinsa.

Karanta massage din tayi yafi so biyar tana maimaitawa cikeda mamakin tambayar Wai waye a dakin nasa bayan yaga ko waye dinne.

Kai tsaye da takaicin tambayarsa ta rubuta masa "itadin daice wadda kagani ko kanada wata matarne bayan ita?"

Kashe wayar yayi ganin abindata rubuto Yana sake boyayyan tsaki ya shafa sumar kansa sbd baya iya kwanciya da wani a gado daya baimasan ta Yaya zai kwanta da ita a gadon.

Hawa yayi gadon ya kwanta gefe daya tareda rufeta sbd jikinta dake bayyane ga towel din ta saman kirjinma yakusa zamewa Yana rufeta ya kashe wutar dakin ya kwanta Yana rufe ido dandai shi bazai iya kwanciya a sofa ba yabar Mata gadon.

Cikin bacci yaji mutum cikin jikinsa gabansu daya tana fidda wani irin numfashi me zafi da 'duminsa yake sauka cikin wuyansa yanasashi Jin wani iri ya bude idanuwansa ahankali ya zubawa fuskarta dake cikin wuyansa tana Nishi ya daga hannunsa ahankali yakai jikinta zai janyeta hannuwan ya sauka Kan shafaffen cikinta dake Mata ciwon zuwa mararta take tasaki wani irin numfashi da ajiyar zuciya wadda tasashi janye hannun Yana rufe ido sbd dumin numfashinta Yana Masa wani iri.
##MAMUH#



*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*


*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107
[1/16, 2:58 PM] +234 808 457 6211: *_DM 19_*
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*

https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*

https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw


*********************
Juyowa yayi Yakuma kallonta da idanuwansa da bacci yagama sakinsu yafara karantar yanayinta ahankali sai ya lura da kaman tanada matsalane Dan kuwa ko ayanda yasanta sama sama yasan bazata shiga jikinsa a hayyacinta ba,
Qaramin numfashi da yasaki Yana waiwayawa ya duba agogo yaga Daren yaraba sosai Babu ta yanda zai iya Kiran Hanifa yanzu ya lumshe idanuwansa Yana Kuma kallonta kafin Kai tsaye ya saka hannuwansa biyu ya juyota daidai Yana kallon fuskarta dake Dan tsatsafo zufa duk da sanyin aircon daya Kama dakin.
Baisan ya zaiyiba tunda ba Saba irin wainnan abubuwan yayiba aikine kawai su Hanifa suka hadosa dashi kawo Masa ita dakinsa gabaki daya.

Shafa fuskarta yayi tareda bude bakinsa ahankali cikin nutsuwa akaro na farko daya Kira sunanta.
Bata motsaba sbd wani irin rawa da jikinta keyi zufa na keto Mata 
Ganin irin zufan yasa ya yaye musu bargon gabaki daya Yana dauke idanuwansa akan jikinta dake bayyane yakai hannu Yana janyota jikinsa Yana sake Kiran sunanta wannan karon da 'dan sauti saidai har lokacin Babu wani alamar tasan wayema yake tareda ita bare kiransa.
Dayaga baisan meyake faruwaba Kuma gadai zafi tanaji tunda tana zufa shikuma bazai iya kallonta ahaka ba Kaya jikintaba sai towel Wanda shida Babu duk daya sai kawai ya kwanta ya rufe jikinta da nasa ta hanyar sanyata cikin jikinsa ahankali yaji dumin jikinta na shigewa jikinsa.

Qamshintane yafi komai takura Masa sbd qamshine daya riga yagama kame jikinta tun Yana Dan rufe ido Yana budewa yanajin wani irin rashin sukuni ahakan Kuma baccin dole me daukeda ciwon Kai me qarfi ya daukesa Dan kuwa a rayuwarsa kaf baya iya tuna ranar dayayi baccin takura irin wannan Mai cikeda rashin sukuni na komaima. 

Qarfe bakwai da arbain ta bude idanuwanta dasukai Mata mugun nauyi da kanta ma dayake Sara Mata sosai ta lumshe idanuwanta dasuka Dan kumbura tasake budewa tareda juyawa gefen gadon Dan lalubo wayarta taga karfe nawa gabaki daya batada qarfin jikin daqyar ta daga hannun tana lalubowa ko Ina taji bataji wayarba saita sauke numfashi Mara karfi tana tashi zaune ahankali ta zauna dakyau tsakiyar gadon tana bude idanuwanta da kyau suka sauka kan mutum zaune akan sofa Yana aiki da laptop a gabansa jikinsa sanyeda kayan geaming daya dawo jikinsa dake daukan ido duk kusan a bayyane sbd rigar jikinsa batada hannu hakama wandon jikinsa three quarter ne sai slippers din Gucci masu taushi a qafarsa gabaki daya hankalinsa nakan abinda yakeyi duk da yaji tashin nata Amma Bai dagoba abindake gabansa kawai yakeyi.

Wani irin mummunan faduwar gaba da firgicine ya shigeta lokaci daya tasake kallonsa da idanuwanta dake neman sauyawa da shakkar Shidin ne kuwa kokuwa?
A firgice cikin tsananin tashin hankali ta kalli jikinta da Babu komai har towel dinma Babu Yana cikin gadon 
Mummunan faduwa gabanta yayi tashiga wani irin tashin hankali da baqin cikin dayake neman danne numfashinta jikinta ya dauki rawa ta janyo rigar baccinta dake kan kujeran mirror hannuwanta duka rawa sukeyi ta saka rigar tareda lalubo towel din ta daura ta sauko gadon ko cikakken qarfin jiki batada taqaraso gabansa murya a shaqe da tsananin baqin ciki da tashin hankali tace"

Menene yafaru anan?
Menene kakeyi anan?
Yaushe kashigo?ta Yaya kashigo Nan?
When?How? and why????"" Ta qarasa da fushi me tsanani acikin muryarta sbd dukkanin inda tsoro da tashin hankali yake tashiga so take taji menene yafaru,fatanta komai Bai faruba a tsakaninsu Dan kuwa Babu abindatake iya tunawa sbd drink din bayan qarfi da yayi Mata daya Bata reaction har fitarda ita hayyacinta yayi she just can't remember anything.

Dagowa yayi akaro na farko ya zuba Mata idanuwansa fuskarsa a matuqar hade ya qare Mata kallo saiyaga bazai iya tsayawa Mata mgna ba sbd yafara Mata kallon Bata hayyacinta ciwon Kai zata saka Masa kamar yanda ta sakawa kanta.

Ganin kallon rainin dayayi Mata ya dauke kansa baida niyyar tanka Mata hakan yasake Cinna Mata hauka Rai bace ta dauke laptop din dayake aikin ta dire gefe tana kallonsa da idanuwanta dasukai jajir Kai tsaye tace"

Banyi Kama da mahaukaciyaba inaga
Zan bude maka zance akan maganar aure dayake tsakaninmu Wanda haryanzu ban amince dashiba maganar Miji da Mata a tsakaninmu bakada wannan rights din akaina sbd bana maka kallon miji idan akwai abin dayake tsakaninmu shine Kai qanin Hanifa ne,
Bakada iko ko wani izini dazai baka Daman kusanci Dani can you leave this room now please tafada tana nuna Masa kofa idanuwanta na cikowa da hawaye sbd kukan datakeson fashewa dashi da tsoron ko wani abun yafaru.

Bai dago ya kalletaba ya miqe tsaye tareda damqar hannunta ya nufi kofa da ita tana fizgewa tana qwacewa ya tsaya jikin kofa da ita ya kalleta da fararen idanuwansa dake bayyanarda  bacin Rai qarara acikinsu ya saki hannunta ya bude Baki yace"

Babu abin daya faru anan Kuma Babu abin dazai faru din ko ba'a yanzuba sbd Babu abindake jikinki dazaisa wani abun yafaru idanma akwai ajikin naki to Ni yamun kadan so kidaina tunanin wani abun yafaru sbd bana sha'awan macenda bata iya banbance tsakanin namiji da muna maza Dan kuwa idan har wani abun zai faru bakinki bazai tambayaba da ajikinki Zaki tabbatar, mganar karban aure ko tashin karbansa wannan nine Zan sanar Dan a hannuna yake get that to your dumb Head and get out of my room now.

Ballewa hawayen idanuwanta sukai takasa daga ko qafarta sbd tsananin qunci da baqin cikin daya rufe zuciyarta kukan dakeson subuce matane yasata nufar toilet tashige tana rufo kofar da qarfi hawayenta suka qarasa ballewa suna gudu kan fuskarta.

Meya sametane?
Wace irin rayuwace wannan?
A rayuwarta kila Bata taba magana da fushiba irin yau din,
Ta Yaya za'a gane damuwarta da wannan auren,
Tayaya zasu gane Bata so da qaunar wannan auren har cikin zuciyarta.
Kuka sosai tayi idanuwanta dasuke a Dan kumbure suka qarasa kumburewar daqyar ta danne tayo wanka tareda alwala ta fito sanyeda kayan data shiga dasu tana fitowa ta dauki Kaya Takoma toilet din ta sanyo ta fito ta tayarda sallah har lokacin Yana zaune Yana aiki a laptop Babu alamar zai nuna dayasan da akwai wata halittar a dakin aikin kawai yakeyi Amma gabaki daya ransa har lokacin a bace yake Dan kuwa baitaba  saka bacin ran kowabama aransa Amma yau ta kunnasa ta yanda yakejin ko ganinta baya buqatan yi.

Tana idarwa ta miqe ta tattara kayanta ta maida cikin akwatinta duka ta janyo akawatin ta dauka wayarta da handbag ta nufi kofa ta bude ta fice.

Dakin Hannah ta nufa Kai tsaye tayi Knocking tana jiran abude har lokacin idanuwanta a Dan kumbure suke.
Jin shiru yasa ta fiddo wayarta takira Hannah din.

Hannah dake bacci taji ringing wayarta na tashi ahankali ta lalubo tareda bude ido tana dubawa taga sunan Naj tasaki wani tsokin takaicin Naj din kafin ta dauka cikin bacci tace"

Yes Naj menene?

Kintafi da room card dinkine ko Yana reception ko hannun Hanifa?

Tashi zaune Hannah tayi tana bude ido dakyau Dan kuwa idan har Naj na neman Mabudin dakinta kenan Marshal ya iso kaman yanda tasani they can't share a room.
Cikin farin cikinta da Bata boyeba tace"

The card is here with me Amma kiban  10min koma kiban 6min ganinan zuwa na bude Miki you are most welcome Naj.

Kashe wayar tayi tana dirowa gadon dakin gidansu Sofia dasuka kwana ta dauki Jakarta da kayanta a hannu tareda daukan key din motar Sofia ta fice da sauri sauri gudu gudu tana Isa inda motar take tafada tareda tadawa taja da qarfi ta fice.
##MAMUH#


*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107[1/16, 2:58 PM] +234 808 457 6211: *_DM 20_*

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw


**************
Batason Kiran Hanifa sbd batason damunta tunda tana tareda Isma'eel shiyasa ta takura kanta tayi tsayuwar jiran Hannah bakin kofar dakin tanajin gabaki dayama gida takeson komawa Amma sbd bazata iya barin hanifar ba ayanzu datake buqatarta akusa da ita shine kawai zaisa ta tsaya Amma da baby abun dazai hanata barin qasar a ranar gabaki daya toshewar numfashi takeji a garin gabaki daya.

Da kayan bacci riga da wando sai jacket data doro a sama jikin Hannah Babu kunya ta iso lodge din tayi parking tareda fitowa taqarasa reception ta wuce da sauri sauri
Tana qarasowa tahau bude dakin tana cewa"

Sorry nabarki kina jira,shiga 
Shigo ki aje kayanki Zaki iya zama daganan har mu bar Sweden zanyi farin cikin zama taredake.

Bata cewa Hannah din komaiba ta shiga ta aje kayanta tareda nufar toilet tashige sbd tasan zatai matuqar wahala zama da Hannah sbd banbancin halayensu da rashin Jin juna dasukeyi,
Sam Hannah batai mataba sbd yanayin rawar kanta da iyayi dama komaima ita gabaki dayama Hannah is suffocating her Amma yanxu Haka zata zauna da ita kamema takeji akanta.

Wanka tayo tafito ta saka doguwar riga Mara nauyi ta zauna kan sofa tana shan tea me zafi ahankali tanajin Hannah dake cikin farin ciki shigewa toilet wanka,tana gamawa ta Haye gado ta kwanta ta rufa tana rufe ido.

Qarfe biyu zasuje asibiti Dan Haka biyu saura ta tashi tayi alwala tayi sallah ta shirya cikin _Pal zileri drawstring_ straight skirt navy blue da milk long sleeves sai milk scarf data daura ta fito daga ita sai wayarta a hannunta daidai Hanifa na qarasowa dakin zatai knocking suka kalli juna tana mamakin ganinta dakin Hannah ta waiwaya ta kalli hanyar kofar dakin Marshal tasake dawo da kallonta kan Naj din Kai tsaye tace"

Me kikeyi Anan Naj?

Kallonta Naj tayi Kai tsaye kafin ta Dan dauke tana cewa"

Nan nadawo.

Kallon mamaki Hanifa tabita dashi kafin ta kalli Hannah dake shiryawa cikin Adonta na daukan hankali ta Kama hannun Naj din tajata suka fita gabaki daya zuwa gurin motocin da zasu fita dasu ta saketa suna fuskantar juna cikin fara gajiya da halin Naj din tace"

Naj banso shiga cikin zancenku ba sbd ku duka biyun Ina sonku Ina qaunarku banason dayanku yashiga takura ko damuwa shiyasa nake dakatar da kaina ga fada Miki gskia duba da yanda akai Miki ba daidaiba ta hanyar daura Miki aure da Wanda kike ganin kin girma Amma Naga kinason yiwa kanki illa Dan kuwa shekarunki sun tashi sunbi iska daga lokacinda aka shafa fatihar aurenki da Marshal Dan kuwa yanzu shine me ikonki,
Duk ba wannan ba meyesa Zaki ringa bawa Hannah damar dazata ringa qara samun kusanci da mijinki bayan kinsan zata iya Jan raayinsa tunda ita mace ce Kuma itama din kyakkyawace kina ganin Jin kan Nan naki bazai damekiba agaba idan Baki dakata wannan shirmenba koni da hajjo bazamu iya taimaka Miki ba agurin Wanda kike rainawar sbd namijine wani lokacin Kaine zaka sauke Kai kabisa Amma bazaki gane hakan yanzuba sbd Baki Gama sanin meye auren ba kokuma nace kinsani zuciya ta hanaki fahimta.

Da yanayi na rashin me zatace ta kalli Hanifan idanuwanta akanta da damuwar meyene abin tattaunawa anan ta bude Baki zatai magana idanuwanta suka sauka kanshi Yana tahowa sanye cikin _Escada jeans_ blue da farar _Saint Lauren_ long sleeves sai _Shiels Emerald_ sunglasses dake fuskarsa daya Gama fito da fuskarsa dake wani irin daukan hankali Hannah ce taredashi tana sanye da jeans da Lois chiffon shirt sai qamshi take fitarwa suna tafe tana Masa firar outing dinta da friends dinta gabaki daya ta cika Masa kunne Amma baiyi yunqurin dakatar da itaba.

'dauke idonta tayi akansu tana fasa maganar dazatai ta Dan dauke Kai,
Waiwayawa Hanifa tayi tagansu ta juyo ta kalli Naj din data dauke Kai cikin kawar da zancen dasuka fara tace"

Muje wainda ake Kira sun fito.

Isma'eel yafadawa su hadu a asibitin kawai ya nufa motar dayasa aka kawo Masa ya karba key yashiga Hannah tashige gaba ya tayar suka bar gurin batareda ko kallon inda suke yayiba har it's har Hanifan Bai nuna yasan dasu dinba ya wucewarsa.

A motar Isma'eel su suka wuce motar shiru Babu Wanda yake magana sbd kowa da abindayake ransa musamman ita datake qara Jin duk garin yafita kanta.

Hanifa duk yanda takejin damuwarsu tata damuwar tafi damunta sbd tana cikin hali na tsananin damuwane Dan kuwa wannan karon idan akai Mata dashen baiyiba shikenan tasan batada Rabon zamtowa uwa da samun 'dan kanta.

Koda suka Isa asibiti Dr sa'id na can already Dan Haka shine ya tarbesu suka wuce zuwa ganin Dr Kenneth din Wanda ke fifth floor.

A reception ta zauna jiransu sbd Hanifan ce kawai zata shiga sai Dr sa'id Isma'eel Yana kofar office din Yana jira.

Kusan awanni hudu suka shafe kafin suka fito suka sauko daidai isowar marshal dake waya cikin nutsuwa har lokacin Hannah na gefensa Kamar wasu sabbin aure.

Dauke kanta tayi daga kansu tana kallon Hanifa cikin kulawa ta riqo hannunta tana cewa"

Are you ok sweetie?

Kallonta Hanifa tayi da idanuwanta dasukai jajir sai kawai takasa magana ta rungumeta tana sauke ajiyar zuciya sbd batason yin kuka tana neman qwarin gwiwane.

Kamo hannunta Isma'eel yayi Yana shafa kanta cikeda kulawa da bayyanarda tsananin Sonta dayake cikin zuciyarsa yace"

Hanifa Inshallah komai zaitafi lafiya
Zaki dauka cikin lafiya ki haihu lafiya 
Duk gamunan muna taredake I am here,Marshal is here, Naj is here too and Dr sa'id ma Yana Nan inshallah Zaki samu lafiya da abin dakikeso.

Ahankali ta gyada Kai tana cewa"

Thank you Zawj.

Murmushi yayi Yana cewa"

Muje to kina buqatan hutawa.

Kallon Marshal yayi Yana cewa"

Gobe za'a fara processing aikin.

Lodge suka koma tun a hanya Naj din ke Dan sake kwantarwa da Hanifan hankali Koda suka Isa daki ta wuce ta fada kan gado tana sauke nannauyan numfashi kanta na Dan sarawa sai daga baya ta samu ta lallaba tayi sallar la'asar Bata wani jimaba akai magriba tayi sai alokacin tasa aka kawo Mata abinci taci ta koshi iya cikinta ta tashi tayi sallar ishai tayo wanka tayi Shirin bacci ta kwanta har lokacin Hannah Bata dawoba.
Washe garima kusan a asibiti suka wuni sai dare suka dawo Banda hanifar wadda akai admitting sbd aikin.

Kwana biyu suna yawon asibiti kafin akai aikin nasara suna fatar cikin ya tabbata Dan Haka Koda aka sallamota suka dawo sabuwar kulawa take samu daga kan dukkaninsu Banda Marshal Wanda kobai nuna ba tasan yafi kowa jinta cikin ransa takumasan sbd Naj ne yake nesanta kansa dasu baya buqatar abin dazai hadasa guri daya da Naj din.

Ta warware gabaki daya Dr sa'id harya koma shi tuni su kadai suka rage Marshal dinma yariga yayi booking ticket na tafiya washe gari Dan Haka ranar tareda Hanifan suka fita dagashi sai ita Basu dawoba sai dare bayan ishai lokacin Naj na tareda Isma'eel a bakin pool din gurin suna fira Yana sake tausarta akan maganar auren ta Dan kallesa tana maida kallonta kan ruwan dake gabansu a natse tace"

Isma'eel banajin aurena aurene Kamar kowane sure sbd bana hango ranarda zai zama aure kamar yanda akai fata har aka hadashi.

Rufe idanu tayi ta bude zuciyarta na Shiga qunci daya bayyana cikin sautin muryarta tace"

Andai yimin fata fa matsin aure Kuma nayi saidai banajin daga sunan auren zai wuce ko Ina har abada bazan daina yiwa Wanda ake Kira da mijin kallon mijin ba......

Daga bayansu Hanifa tace"

Zawj mundawo.

Juyowa sukai gabaki dayansu ita nata idon akansa suka fara sauka Yana sanye da kayan dasuka fitarda samartakarsa sosai sai cika ido dayakewa mutane da kwarjininsa da ingarman jikinsa ta dauke Kai tana juyawa ahankali ya tako ya Isa har inda take ya durqusa ya dauketa gabaki dayanta 
Ta zabura da qarfi tana qwacewa saidai riqon gaske yayi Mata a kirjinsa   me Fadi ya dago ya kalli Hanifa da Isma'eel yace"

Wannan qawar Taki inason nuna Mata wani Abu ko zata Dan dawo daga shock da tarin shirmen samarinta na dah suka Bata.

Zillewa take neman yi cikin qarfi da baqin ciki Tama kasa kallon inda Hanifa take sbd tsananin baqin ciki da kunya take idanuwanta sukai jajir
Isma'eel ya kallesa Yana cewa"

Saida safe Naj Zan fadawa Hannah karta jiraki ta rufe kofa.

Akaro na farko da Marshal din yayi murmushin dayafi Kama Dana mugunta ya juya ya wuce da ita tana dukan kirjinsa cikin tsana da takaici.

Rufe dakin yayi Bai direta koina sai tsakiyar lafiyayyan gadonsa Yana kallon kyakkyawar fuskarta data koma ja take sbd tashin hankali da baqin ciki hakan yasake kunnasa ya ranqwafo yayi Mata rumfa da kirjinsa daya rufeta gabaki daya qamshinsa na shiga hancinta direct ta rintse ido da qarfi tana turesa iya karfinta Amma Kamar garu take turawa sbd ko gezau baiyiba saima matso da kyakkyawar fuskarsa yayi ahankali ya cusa cikin wuyanta ya shaqi qamshinta daya fara Dan sabawa da hancinsa tsawon kwanakin sbd gabaki daya koina dakinsa qamshinta yakeyi har gadon da bargon da komaiba kusan ko ina yasa kansa a dakin qamshinta yakeyi daqyar yake iya shaqar numfashi batareda qamshintaba tun ranar dayazo Sweden din Dan Haka ya manna hancinsa kan fatar wuyanta dake bayyane Ya shaqa qamshin Yana rintse fararen idanuwansa duk da bayajin komai game da ita Amma hancinsa sun Dan Saba da qamshin 
Ya dago fuskarsa ahankali Yana kallon fuskarta dake cikeda tsanarsa yakai hannu ahankali ya fincike botiran gaban rigarta gabaki dayansu farar lace foam bra din dake jikinta ta bayyana kan fuskarsa ya kalli kirjin nata zuwa shafaffen cikinta dashima yake bayyane ya daga hannunsa Yana kallon fuskarta da hawayen baqin ciki suka fara gangarowa ya Dora hanun kan cikinta yayi wata irin shafawa data Sanya su biyun kusan dauke wuta sbd abune dabai taba faruwa da kowannensuba.
##MAMUH#


*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107
[1/16, 2:58 PM] +234 808 457 6211: *_DM 21_*

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw


**********
Bude idanuwanta dasukai ja tayi ta yunqura kanta tareda daga hannuwanta takai zata turasa ya Dora hannunsa kan hannunta daya sauka Kan qirjinsa yana zuba Mata idanuwansa Kan fuskarta yakai bakinsa Kan kunnenta Saida ya sakar Mata numfashi me dumi dayasa tsikar jikinta suka tashi gabaki yace"

Meyasa kike yawan nanata auren Nan ba aure bane?
Idan bakijisa bane ajikinki daga yau Zaki ringa jinsa tunda kina saurine da alama.

Bude idanuwanta tayi dake tsiyayar hawayen baqin ciki ta kallesa cikin ido shima ya zuba Mata nasa idon Yana dauke gira daya yakai hannunsa Kai tsaye Kan bra Dinta dakeda hook a gaba ya balle idanuwansa Kan fuskarta a razane tayi saurin ware idanuwanta cikin idonsa tana girgiza Kai da qarfi sbd yariga yayi Mata runfar dabazata iya tashiba ta rintse ido hawayenta na tsananta gudu ta bude Baki muryarta na rawa cikin fushi tace"

I hate you,I hate you for this...ka barni...this is wrong..

Kirjinta yaqarewa kallon tsaf kafin yakai hannu kan wuyanta Yana shafawa zuwa cikinta ya qarasa zare bra din ya jeho qasa Yana qarasa shigar da ita jikinsa gabaki daya ya kamo fuskarta yayiwa bakinta wani irin kallo kafin ya Dora nasa yana Bata wata irin tsotsa Yana cusa hannunsa daya cikin kirjinta 
Take tahau mutsu mutsu tana jujjuyar dakai saidai Babu ta inda take samun motsawar musamman daya dago fuskarsa ahankali Yana kallonta ya dagata yayiwa rigarsa kyakkyawar yagar data rabata biyu daidai ya zare yayi wurgi da ita Yana kallon wandon jeans dake jikinta tafashe da kuka me sauti tana girgiza Kai idanuwan akan fuskarsa datai ja kadan alamar sha'awarsa ta 'dan motsa tabbas idan tabari wani Abu yafaru tsakaninsu rayuwarta tagama lalacewa bazata iyaba ta rintse ido tana sake girgiza Kai zuwa lokacin ko qarfin jiki batada dazata iya turesa tunda Kota turan baya turuwar.

Mayarda kansa yayi tsakiyar kirjinta Yana shaqar qamshinta yasake dagota ya hade bakinsu yana kissing dinta yanda yaga dama hannuwansa na yawo cikin jikinta gabaki daya tsikan jikinta sun Gama tashi nako Ina Banda kukan baqin ciki tana dukan bayansa Babu abinda takeyi Haka yabi dukkanin jikinta ya hargitsa Mata shi kafin ya saketa tareda sauka gadon batareda ya waiwayo ba ya nufi toilet ya shige yabarta agurin kwance daga ita sai farin pant dinta dake jikinta da qyar ta daga hannunta takai tajawo duvet ta rufe jikinta idanuwanta jajir zuciyarta Kamar ta fashe Mata ta huta da abin datake ji cikinta.

Dunqunqunewa tayi tareda rungume jikinta datakejin Kamar har lokacin hannuwansa da bakinsa yawo sukeyi jikinta wasu sabbin hawayen suka gangaro Mata ta rintse ido tana dafe zuciyarta dake Mata tsananin zafi da ciwo.

Daure da milk towel a qugunsa yafito jikinsa na tsiyayar ruwa alamar wanka yayi ko inda take bai kalla ba ya nufi mirror Yana goge jikinsa yagama yashafa egg yolk cream kadan ya fesa spray na _Creed Aventus_ ya shirya cikin black riga da wando na bacci guntaye ya dauko drink yasha ya dauki wayarsa da aka tarawa misscalls kusan guda Tara hadda na Hannah data dawo bataga Naj ba tana kuma tunanin Babu inda Naj zata fita tunda ita ba mutum bace me karauniya da rawar qafa.
Zaunawa yayi Yana waya da wani Marshal din gurin aikinsa cikin turancinsa dayafi Kama bakinsa dakayau akan yarensa hankali kwance.
Baibi takan misscalls din Hannah ba ya kashe wayar ya nufi gadon Yana zare slippers din qafarsa ya Haye yayi kwanciyarsa.

Saidata tabbatarda yayi bacci ta laluba rigarta a qasa ta rufe jikinta ta nufi wadon jeans dinta dake yashe shima ta dauka ta saka ko bra Dinta Bata tsaya nemaba ta zura rigarta ta dauki scarf dinta tafice dakin tana kamma jikinta da har lokacin tsikar jikinta Yi take tana tashi.
 
Bugu daya tayiwa dakin Hannah data kasa kwanciya ta taso da sauri ta bude Mata tana Mata kallon qurulla tana cewa"

Ina Kika tafi?
Daga Ina Kika dawo?
I mean tuntuni kina Ina?dare fa yayi sosai yanzu.

Batada lokacin sauraro ko kula Hannan zafi da radadi jiki da zuciyarta ke Mata Kai tsaye toilet ta nufa tayo wanka ta fito rigar bacci kawai ta saka ta hau gado ta kwanta tareda rufe ido tana sauke numfashi.

Kasa kwanciya Hannah tayi ta zauna kan sofa tareda rafka uban taguma tanajin itama tata zuciyar na daukan radadin rashin sanin taqamaimai inda Naj take tun farkon Daren fatarta dai ya tabbata Naj din taba gurin Marshal,ita gabaki dayama taji haquri nta na jiransa yagama qarewa kuka zata fasawa Dad Alfa adubi Allah da girmansa a daura musu aure sbd Jin take Kamar Naj zata zama barazana agareta gabaki daya Bata qaunar kusanci a tsakaninsu ko yayane.

Washe gari qarfe goma jirginsa zai tashi Dan Haka qarfe tara da rabi yafito a shirye cikin _Roberto cavalli_ straight trouser and shirt brown fuskarsa sanye da _Prada_ sunglasses black hannunsa sanye cikin aljihun wandonsa Hanifa dake tsaye tareda Isma'eel sai Hannah dake zuba qamshi Dan tuni tayi wanka suna jiran fitowarsa ta kallesa cikin kulawa da kewarsa da zatayi tace"

Marshal kamun alqawarin zuwa kodan baby right?

Kallonta yayi ya sakar Mata murmushinsa dakewa Hannah wuyar gani Yana gyada Mata Kai ahankali kafin ya Dan waiwayo ya kalli Hannah datake Masa kallon tsananin so da burgewa harma da sha'awa ya kalli kofar dakinta ahankali yace"

Tana ciki?

Bata gama fahimtar me yafadaba ya nufi dakin yayi knocking Kai tsaye duk suna tsaye suna kallonsa.

Ahankali ta tashi daga zaunen datake kan kujera idanuwanta da fuskarta gabaki daya a kumbure ta nufi kofar ta bude sbd tunanin ko hannace tadawo Dan Bata fita da card din dakinba.

Cikin idanuwansa nata idanuwan suka sauka ta dauke Kai take fuskarta na sauya zuwa wani mummunan yanayi ta juya zatabar gurin ya riqo hannunta Kai tsaye tareda Ciro abindake aljihunsa ya saka Mata a tafin hannu ta kalla da sauri ganin bra Dinta ta dago a fusace wata fitinanniyar kunyar Hanifa dake kallonsu tana dabaibayeta ta qwace hannunta tareda juyawa ciki a fusace.

Juyawa yayi baice komaiba shima yabar gurin ya nufi gurin Isma'eel dake jiransa a mota Hanifa da mamaki da wani boyayyan murmushi yagama kamata tabi bayansa tana waiwayan dakin 
Hannah kuwa kusan mutuwar tsaye tayi ganin fitowar bra din mace daga aljihun Marshal dinta daqyar ta iya daga qafa tabi bayansu suka nufi airport kaisa.

Bayan dawowarsu Babu Wanda yaga wani sakin fuska daga Naj din sbd sosai ta fuske Dan Bata buqatar wani magana dazai danganci JALAL din Dan Haka Bata Bari Koda Wasa Hanifa Tai Mata wata maganar ba ahaka suka lallaba suka qarasa kwanakinsu bayan anyi gwaji an tabbatarda cikin ya tabbata.

Da farin cikin nasarar da aka samu suka dawo gida inda aketa murnar cikin Hanifan musamman umma da duk maraice da abinda zata aikowa Hanifa hakama Dadah,
Ta bangaren Dad Alfa ma Yana tsananin farin ciki da cikin uwa uba hajjo data qwallafawa 'yayan da Marsha Rai shida yake namiji sai gashi na Hanifan zasu fara samuwa ta dauki buri da qauna tasakawa cikin itama duk da hannuwansu a gabansu suke da cikin sbd yanayin lafiyar Hanifan suna fatar dai Allah yasa adace wannan karon.
##MAMUH#_*DM 22*_

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

*****************
Ba sosai take jimawaba yanzu a office sbd yanayin Hanifa da hankalinta yafi kwanciya idan taga batayin nesa sosai da ita Dan kwanakin tana Dan samun laulayi masu wahala dan yanzu cikin Yana wata na hudu harya fara Dan tasawa Ana hangensa.

Yau Bata samu damar zuwa office ba sbd yanayi na ciwon Mara data tashi dashi na period dayazo Mata dama Kuma tana ciwon Mara sosai idan zatayi period duk wata saidai wannan karon ciwon yafi tsananta Mata Wanda takejin Kamar ba yanda tasaba bane Dan Haka da yamma hajjo da kanta takira Dr sa'id yazo ya dubata sbd ganin duk Naj din tayi wani iri Babu qarfi sosai ajikinta.

Herbal tea hajjo tasa ruqayyat ta dafo Mata da Zuma kadan aka kawo Mata ta gyara zamanta daga takuren datake dunqule Kan kujerar kusada hajjon ta karba tana kallon cup din ahankali kafin takai bakinta tafara kurba tana Dan rufe ido sbd 'dandanon da baya Mata ko kadan a Baki ta kalla Hanifa dake Mata sannu tace"

Bani tissue akusa dake.

Hannu Hanifa takai ta zaro Mata tissues din dake gefenta na 'dan Tara  yawu datakeyi sbd cikinta ta miqawa Naj din cikin kulawa tana cewa"

Sorry sweetie.

Gyada Mata Kai Naj din tayi tana dan lumshe idanu sbd saukar herbal tea din da zafinsa cikin cikinta yasa taji tana Dan Jin Kamar ciwon na Dan fadawa ta goge bakinta da tissue tana cigaba da kurban tea din harta shanye ta ajiye cup din hajjo na Mata sannu cikin kulawa.

Ahankali ahankali ta danji ciwon Yana fadawa Yana ragewa hartaji taji Dan saukinsa ba laifi sai alokacin ta miqe ahankali ta nufi dakinta Wanda take ita kadai yanzu aciki bayan an sauya Mata komai na dakin zuwa sabin furnitures dasukafi wainda aka sauya komai na dakin fari kamar yanda Hanifa ta bada zabin kalar sbd jalal ma yawanci komai na part dinsa farine,
Raba daki sukai da Hanifa sbd yanayin laulayin cikin hahifan dayakeda tsanani da zabe zabe Dan kuwa gabaki daya batason qamshin turare Wanda Naj Kuma ko zama tayi kusa dakai saita bar maka qamshinta me sanyi da dadi Wanda kamarma yariga yakama jikinta,
Hakama hahifa yawu takeyi wnda itakuma Naj takurane gareta,
Sai qamshin toilet din dakin nasu shower gels dasu feminine wash da bataso Wanda Suma Naj ke amfani dasu shiyasa Hanifan ta tarkata takoma dayan dakin dake palon aka sauya Mata wasu abubuwan dakin wainda bataso da sabbi.

Wanka tasamu tayi da ruwa masu zafi sosai tasake Jin Dan Jin qarfin jikin ta shirya cikin riga da wando masu Fadi sosai marasa nauyi ta saka hula ta Dan kwanta Dan samun bacci Bata Farkaba Saida Dr sa'id yazo aka tadota tafito sanyeda mayafi me Dan kauri rufe da jikinta ta qaraso palon tana tafiya cikin nutsuwa ahankali ta nufi kujera tana kokarin zama anty Amina na shigowa Nan suka zauna tare itama tana gaisawa da Dr sa'id din cikin sanayya da mutuntawa kafin ta miqe ta nufi dakin hajjo dake mutuniyar hirarta Dan suna qasan Kaka sosai da hajjon.

Kallonta Dr sa'id yayi kadan tareda Dan taqaitawa daga kallon Kai tsaye yace"

Menene matsalar?
Yaya kike jin ciwon Marar?

Numfashi ta Dan sauke tana dubansa a natse tace"

Wannan ne Karo na farko danake Jin wannan kalar ciwon duk da dai Ina ciwon Mara dama Amma wannan inajinsa dabam.

Kallonta yasakeyi Yana jeho Mata tambayoyi dabam dabam tana basa amsa tsawon lokaci Yana saurarenta ya hada amsoshinta Yana nazarinsu kafin ya dago Yana kallonta dason fada Mata abinda yake tunanin yasaka ciwon fin koyaushe wannan karon yace"

Ciwon mararki ya sauya yanayin tsarin ciwonsane ta hanyar tsananta da wani launin ciwom kamakon sha'awarki ta mace da aka motsa Wanda ke nuni da Baki taba ji ko aikata wani Abu daya taba motsa sha'awarki Wanda dakin Jima ahakan batareda an motsa Miki itaba kokuma yanayi yasa ta motsa da kanta Kika dauki shekaru ahaka kofofin sha'awan naki zasu rage qarfi matuqa kokuma suyi rauni sosai ta yanda zuwan sha'awan zaiyi Miki wuya.

Wani irin nauyi kanta ya dauka akaro na farko a rayuwarta da wata irin mummunan kunyar da Bata tabajiba ta Gama rufeta tako Ina har bazata iya kallonsaba saidai ta dago ahankali ta waiwayo duba Babu Wanda yafito bare yaji wannan mugun al'amarin daya sameta sukai ido biyu da Anty Amina data fito daga dakin hajjo takumaji abinda Dr sa'id din yafada Amma sbd ragewa Naj din nauyi da kunyar data hango tareda ita saita dauke Kai tana fuskewa tace"

Zan wuce nabarowa umma aikin hada sakon turarukan daza'a Kai mota gobe zuwa wani gari,Dr sa'id sai anjima.

Wucewa tayi batareda ta jira amsar Naj din ba sbd tasan bazata samu amsawar daga garetaba sbd halin datake ciki na tsananin Jin nauyi.

Babu wata kunya ko nauyin maganar dayaji sbd shi likita ne Babu kunya a tsakaninsa da patient dinsa Dan Haka Kai tsaye yabata shawaran ringa Shan ruwan dumi akai akai tareda bada shawaran zama guri daya da mijinta.

Tagane ma'anarsa ta cewa ta zauna guri daya da mijinta Dan Haka ko kallonsa bataiba tace"

Ngd Dr sa'id" tana miqewa daga zaunen shima ya miqe sukai sai anjima ya fice ita Kuma ta nufi daki tana dafa mararta datai nauyi.

Kwana biyu tagama period dinta ciwon Mara ya wuce Dan Haka ko maganar Dr sa'id Bata sake tunawaba bare sakawa arai taci gaba da sha'anoninta hankalinta kwance Babu tunani ko damuwar komai.
 
Yau da yamma sosai tadawo aiki sbd wani meeting da sukai me mahimmanci Wanda yasa take cikin farin ciki sosai sbd project ne dasuka Jima Suna buqatansa sai yanzu Allah yasa suka karbe.
Tana sanyo kan motarta cikin layin ta hangi qarin sojoji a kofar gidan Wanda yasa gabanta mummunan faduwa akaro na farko data tuna zai iya yiyuwa shine yadawo.
Sake faduwa gabanta yayi taji kaman tana neman shiga damuwa Amma dai ta danne ta qaraso suka bude Mata gate tashige da motarta tana amsa gaisuwar dasuke Mata daga ciki ta hanyar jinjina musu Kai da daga hannu.

Parking tayi tareda kashewa ta fito riqe da handbag dinta tasamu kanta da qin ko kallon daya daga cikin  motocinsa dakeda alamar da ita akaje daukarsa airport ta dauke Kai ta nufi cikin gidan Kai tsaye tana nufar sashensu ma'ana na hajjo.

Da siririyar sallama ta shiga palon Kai tsaye tana kallon Hanifa dake zaune palon da tissue dinta ta yawu,
Gurinta ta qaraso tana sauke qaramin numfashi tace"

Maman baby Yaya??

Murmushin farin ciki Hanifa ta saki tana cewa"

Sannu da dawowa sirikar maman baby.

Naj din Bata tankata ba sbd yanzu tasaba da wannan neman fitinar da Hanifa keyi yanzu Dan Haka Kai tsaye daki ta nufa tana cewa"

Bari na tube nayi sallah yau na gaji sosai jikina na ciwo sosai.

Shigewa tayi daki tareda rufo kofar ta tana aje handbag dinta tareda Dan mayafin dake kanta ta tube tareda Kai kayan cikin laundry ta janyo towel ta daura tashige toilet.
Jin Ana Kiran sallar magriba yasa tafasa wankan tayo alwala tafito ta Sanya doguwar riga ta tafara yin sallolin Dake kanta saidata gamasu kafin ta miqe tana tubewa wayarta tahau ringing batabi ta kanta ba ta nufi toilet tashige.

Wanka tayo tafito ta shafa Mai kadan sai body mist da khumrah ta Sanya doguwar riga me qaramin hannu ta Sanya hular da Bata Gama rufe kanta gashin kanta dukaba tana kokarin fitowa taga lokacin sallar Isha yayi ta tsaya tayi abarta kafin ta dauko wayarta ta fito tana duba Kiran da aketa Mata tun dazu ga zallar mamakinta sai taga no din kamar ta santa ta sake dubawa taga 9misscalls Dan Haka sai mamakin Kiran ya Dan kamata ta nufi palon da hajjo da Hanifa ke zaune a dining ta nufa gurinsu Kai tsaye tana cewa"

Me maman baby keyi a dining hajjo itada baby bayason cin abinci a dining San......kasa qarasa maganarta tayi sakamakon Wanda idanuwanta suka Shiga cikin nasa Yana zaune kan kujerar da Bata hangosaba saidata iso gurin gabaki daya fararen idanuwansa masu rikitarwa a zubasu akanta jikinsa sanyeda jallabiya fara qal tana qyallin daya tabbatarda tsadarta,
Samun kanta tayi da kallon hajjo ahankali kafin ta maida kallonta kan Hanifa dake kallonta da murmushi a fuskarta sai kawai ta juya zatabar gurin Kai tsaye taji muryarsa a kame yace"

Dawo ki zauna.

Wani mamakin gaskene ya kamata dan ganin isar dayakeson nuna Wanda ita Bata basa wannan damar ba Dan Haka Bata dakataba ta wucewarta saidai ko taku uku bataiba taji an dauketa sama an qarasa cikin dakinta da ita tareda rufo kofar ya direta tareda manneta jikin bango Yana kallon fuskarta Yana Kuma controlling zuciyarsa dama kansa ya lumshe idanuwa ahankali yasake budesu akanta ya bude Baki cikin nutsuwa da kamewarsa yace"

Next time Kika Kuma Haka Zakiyi mamakin abinda Zan Miki agaban hajjo dama qawar Taki da kike Jin girma agabanta.

Qin kallonsa tayi tasa hakai hannu zata turesa daga jikinta dayake manne  taji bazata iya Kai hannunta ajikinsa Dan kada wani tunanin ya shigesa ta dago ahankali ta kallesa da fararen idanuwanta shima idon nasa na kanta ya daga gira daya Yana jiran abin dazata fada ta Dan hade fuska tana dauke idonta daga cikin nasa murya a kame tace"

Bana buqatan sharadi ko doka akan waye Zan kula waye Zan gaida so can you just excuse me please.

Wani kallon daya tayar da tsikar jikinta batareda tasaniba yayi Mata kafin ya juya ya fice yabarta da qamshin turarensa daya maqale a kayanta takasa bin bayansa da kallo zuciyarta a Dan bace.

Kasa fitowa tayi lokacin saidata tabbatarda yabar sashen ta fito fuskarta a kame Dan kada Hanifa tasamu damar yimata wata magana 
Tana fitowa cikinsu Babu Wanda yabi takanta taje dining din taciyo abinci kadan tagama ta taso tadawo gefen hajjo ta zauna tana Dan fuskewa dayin kallon wata Mexican drama the forbidden love A tashar telemundo suna fira.
Dai qarfe goma da arbain ta shige lokacin tuni hajjo ta shige daga ita sai Hanifa kusan tare suka shige dakunansu.
##MAMUH#

*DAN ALLAH ZAKU RINGAMUN UZURI KWANA BIYUN NAN ZUWA RANAR SATURDAY HIDAMAR BIKIN QANWATA MUKEYI ZANYI KOKARI NA RINGA BAKU INSHALLAH IDAN KUMA HIDIMA TA RIQENI ZAN RINGA SKIPPING HAR MUGAMA BIKIN RANAR SATURDAY INSHALLAH*
_NAGODE🙏_




*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_1aHALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107*_DM 23_*

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw


**************
Kwanciya tayi bayan tagama duk abubuwan dazatayi ta rufe idanuwanta Nayan ta rufe Rabin jikinta da bargo me taushi takai hannu ta rage hasken wutar dakin sosai.
Tsowon mintuna hudu ta juya kwanciyarta tana sake rintse ido saidai har lokacin qamshinsa dake maqale a kayan jikinta Bai daina Shiga hancintaba Yana damunta gabaki daya ta rasa sukuninta ta tashi zaune tana sake Dan qaramin tsaki tareda dan yamutsa fuska tana sauka daga kan gadon ta nufi closet tana zame rigar jikinta ta jefa cikin wardrobe ta Ciro wasu riga da wando na bacci guntaye masu santsi ta saka tareda komawa ta kwanta tana lumshe ido bayan tayi adduar bacci.


Karar vibrating wayane ya tada ita da safen bayan tayi sallar asuba Takoma bacci,
Hannu takai ahankali tafara lalubo wayar tana bude idonuwanta dake tareda sauran bacci ta dago wayar ta duba taga no din jiyane da akaita kiranta da ita ta tashi zaune tana Dan sake sakewa daga baccin ta dauka Kiran cikin muryarta me taushi tace"

Hello,aslm alkm!

Shiru taji ba'ai magana ba cikin nutsuwa tasake cewa"

Hello.
Jin shiru ba magana yasata kashe wayar tareda ajiyewa tana kallon agogo taga qarfe Tara da minti uku.

Saukowa tayi Kan gadon tareda zura bedroom slippers dinta na dolce and Gabbana ta nufi toilet da sauri tafada wanka sbd tayi kafin ta Isa office tasan zatai latti.

Tana fitowa wanka tafara shiri cikin nutsuwa tashafa Mai da body mist kawai sai khumrah ta shirya cikin Givenchy floral chiffon skirt navy blue da milk blouse dinsa sai veil datai rolling ta fito daukeda wayarta da _D&G_ handbag dinta tafito Palo cikin sa'a duk suna dining suna breakfast daga hajjo sai Hanifa bandashi Dan Haka ta jiye handbag din a kujera tana qarasawa dining din cikin nutsuwa da sakewa tace"

Barka da safiya hajjo,
Ina kwana?

Taja kujera ta zauna tana kallon Hanifa dake kallonta cikin yabawa da samunta da 'dan uwanta yayi amatsayin Mata tace"

Good morning maman baby, how's our baby?

Murmushi Hanifa tasaki tana cewa"

Morning Auntie din baby.

Sama sama taci slice biyu na toasted bread da tea Mara shugar ta miqe tana cewa"

Hajjo zantafi saina dawo.

Adawo lafiya Amma yau ki dawo da wuri sbd kece Zaki ringa Mana dinner daga yau.

Murmushi tasake tana wucewa tace daga yau kuwa Zaki ringa cin dinner me Dadi hajjo,
Maman baby saina dawo,take care.

Fitowa tayi Kai tsaye ta nufi hanyar sashen Dad Alfa tana duba wayarta ta qarasa shiga da Hannah tafaracin Karo ta fito daga kicin fuskarta shafe koina da face scrub data shafa tana jiran yayi mintunan dazaiyi kafin tashiga wanka ta wanke Dan Marshal na gari Bata Sanya da qarin gyare gyare.

Kallon juna sukayi Naj tana ganinta ta Dan basarda fuska tana wucewa palon Dad Alfa din bayan ta amsa "morning" dinda Hannan Tai Mata cikin qure ido akanta sbd har yau tana shinshinowa kanta barazana daga Naj shiyasa take buqatan ayi gaggawan aurenta da Marshal Dan kuwa kyawu da kyan jiki tareda daukan idon Naj na daban ne duk da Bata wani qyale qyalen kwalliya Dan zata iya cewa Naj Bata taba shafa su jambakiba musamman masu shwty kala shiyasa komai nata yake unique and natural.

Tsoki hannan taja tana dauke Kai daga bin inda Naj ta shige da kallo ta nufa dakinta tana Jin tsanar Naj har Dan kuwa tashiga gabanta Kuma ta hanyar wainda Babu abinda zata iyayi bayan ta danne duk abin datakeji tabisu da yaqen dole tunda sune dolen Marshal dinta Dan tasan suna tsanarta to har abada bazai auretaba sbd yanda yakejinsu a ransa.

Fitowa Naj tayi bayan sungama magana da Dad din Dan ba gaisuwa kawai ta kawotaba harda magana akan ALFA'S company Wanda suke buqatan meeting dasu na saka hannunsa Dana Marshal akan wasu takardu na wani babban project da zasu fitar.

Fitowa tayi bayan sunyi magana Akan zasuzo ALFA'S din gobe gurin meeting din.

Tana fitowa daga sashen wayarta tasake daukan vibrating ta bude handbag dinta tareda Ciro wayar tana nufar motarta ta dauka tareda cewa"

Hello Aslm alkm!

Shiru takuma ji ta daga wayar daga kunnenta ta duba taga tana aiki ta Mayar kunnenta tana sake cewa"

Hello.

Mrs DEEN MARSHAL zankiraki dashi kokuwa Antyn JALALUDDEEN MARSHAL?
To koma dai wanne duk dayane basuda wani amfani tunda bashine dalilin dayasa nakiraba,
Akwai meeting qarfe goma da rabi gashi Banga alamar kintuna da hakan ba Dan bama iya jira idan lokaci yayi sbd munada iyalan da mukai auren soyayya bana cushe ko sadakaba dasuke jiran dawowarmu gidan Kan lokaci.

Cire wayar tayi daga kunnenta tareda kashewa Kai tsaye batareda tasamu damar cewa maganarsa ko kalma dayaba ta maida wayar jaka tana Shirin Shiga mota ta hangosa tsaye a balcony dinsa da mug a hannunsa Yana kurba ruwa masu dumi kadan da Zuma kadan aciki Wanda yake dabiarsa kullum Shan ruwan zafi masu Zuma kadan aciki.
Sanye yake da three quarter black da armless shirt sai slippers brown a qafarsa yafitone sbd fresh air ya shigesa Dan exercise din dayayi gabaki dayansa yasashi zufa shiyasa ya fito Yana Shan fresh air din jikinsa sai daukan ido yakeyi acikin baqaqen kayan dake jikinsa.

Dauke Kai tayi tana ciro keys na motarta ta bude ta shige tareda tada motar tana Danna horn aka bude Mata gate ta figeta ta fice daga gidan
Cigaba da abinda yakeyi yayi batareda yabi inda motar tata taficeba da ido sbd tun fitowarta daga sashen Dad Alfa idonsa ya sauka akanta ya qarewa kayan jikinta idon Yana tsayar da idonsa Kan Dan qaramin qugunta da skirt din jikinta ya zauna akai daga  sama ya Dan rintse idonsa Yana daukesu daga kanta.
Ciki yakoma kawai sbd Jin iskar ta sauya zuwa wani yanayi mara Dadi.

Tana Isa office tayi parking ta fito ta nufi ciki Sarah na qasa tana jiran isowarta Dan Haka kai tsaye tan isowa gurin meeting din suka wuce San sama hanyar office din chairman wato Abbas.
Ko data Shiga shareholders din companyn duk sun iso ita zatai representing Alfas,Marshal da Dad Alfa.

Sai qarfe biyu da arbain suka fito meeting din Dan Haka Kai tsaye ta wuce office dinta Dan duba wasu takardu tanayi tana duba agogo sbd komawa gida da wuri tunda tasan aikin dake jiranta a gidan.

Sai qarfe uku da hamsin da uku tasamu kanta ta fito tana sanarda Sarah Dake biye da ita takardun dazata kaiwa Abbas ya duba kafin goben a zauna next meeting.

Wayartace tahau vibrating ta Ciro tana dubawa cikin Dan yamutsa fuska  ta kashe wayar tareda maidawa cikin jaka tana kallon Sarah tace"

Ki tabbatarda kin kaiwa chairman duka takardun da ake buqatan ya duba kafin goben sbd bana buqatan wani aiki dazaisa yaringa kirana.

Ok Inshallah.

Fitowa tayi tafada motarta tabar companyn gabaki daya tana sake duba agogon hannunta.

Tana Isa bataga motorsaba a harabar gidan hakama sojojinsa Dan Haka tasawa ranta sun koma kenan ta fito ta Kai tsaye ta nufi sashensu.

Bakowa a Palo hajjo na sallar la'asar a dakinta, Hanifa Kuma na daki tana baccin yamma.

Dakinta ta nufa Kai tsaye saidata Dan zauna ta huta kafin ta tashi tasauya cikin doguwar rigar roba Mara nauyi tayo alwala tayi sallah kafin ta fito ta nufi dakin hajjo.

Sai yamma sosai ta fito ta Isa dakin Hanifa har lokacin bacci takeyi ta Dan tayarda ita cikin kulawa sbd maraice yayi ta kamata ta tashi ta nufi toilet kafin it's ta nufi kicin Dan aikin abincin dare da itace yau zatayi.

Aiki suka hau yi itadasu ruqayyat masu kama Mata wasu ayyukan
Suka Dora tuwon semo da miyar waterleaf da nama kadan aciki sbd Jin  daga bakinsu ruqayyat cewan idan Marshal na gari ba'a saka nama de yawa a abinci bayason nama sosai duk da dai bawai dansun fada tayiba itama Naman Bai wani dameta bane sosai hakama Hajjo itakuma sbd tsufa da manyanci.

Fruit salad tayi sbd Hanifa me juna biyu sai normal peach drink da black lemon tea me zuma data dafa Dan gidan gabaki daya kusan kowa mayen tea da zumane duk hajjo ce ta koyar dasu hakan tun suna qananu.

Basu Gama aikinba ta fito kicin sai bayan sallar magriba Dan Haka tana fitowa Kai tsaye ta nufi dakinta tafara tubewa gabaki daya ta nufi toilet yin wanka.
Ta Jima ciki kafin tafito daureda towel me girma blue tazo tafara saka doguwar riga tayi sallar magriba Da Isha kafin ta zare rigar ta zauna gaban madubi tashafa Mai kadan da spray din _Chanel_ ta sako doguwar riga Mara hannu ta fito daukeda wayarta lokacin hajjo da Hanifa tuni suka Isa dining Dan Haka Kai tsaye itama can ta nufa tana ajiye wayarta Kan kujerar palon.

Bata ganshiba Amma hancinta ya shaqo Mata qamshi _Tom Ford_ turarensa Dan Haka ta rage takun tahowar tata tana Dan Kai idanuwanta kujerar dayake zama a dining din wadda ba'a hangota sai ankawo cikin dining area din tana Kai idonta gurin tagansa zaune da tea gabansa Yana tiriri cikin Dan qaramin cup,Bai dagoba bare ya nuna yasan da zuwanta saidai ta tabbatarda yaji zuwan mutum agurin ta 'dan dakata kadan zata koma saikuma ta fasa ta qaraso ahankali tana Dan fuskewa batareda itama ta kalla inda yakenba tace"

Sorry nabarku jirana.

Bata zaunaba ta zubawa hajjo abincin kafin tazubawa Hanifa fruit salad da tuwon Dan kadan sai ta zuba itama Dan kadan Takoma ta zauna sai alokacin ya kalleta baice komaiba ya qarasa Shan tea dinsa ya miqe ahankali hajjo ta kallesa tace"

Abincin fa?
Najma kiyi serving mijinki abinci yagama Shan tea din.

Wani irin kallo yayi Mata dayasata kusan sarqewa duk da Bata dagoba Amma tanajin kallon ajikinta ga rigar jikinta duk tasata Jin haushi da takaicin fitowa ahaka.

Da muryarsa me kamewa yace"

Takaimun abincin acan ba anan zanciba.

Yana Gama fadar Haka ya wuce yabar gurin batareda yasake kallon inda takeba yabarta da wani irin takaici,baqin ciki da takaicin rashin gane meyake nufi da "Takaimun"
Wa yake nufi da kalmar Dan Bata tunanin da ita yake Dan kuwa bataga ranarda hakan zata faruba takai kanta sashensa to tace tazo ubanme.

Ganin idon hajjo akanta dake nuni da zallar rashin Wasa na tayi abinda yace din yasata sarqewa tana sakin tari ahankali
Hanifa ta dauki ruwa ta miqa Mata ta a cewa"

Sorry sweetie,sannu bi ahankali kije kidawo tukuna saiki qarasa.

Da manyan idanuwanta ta dago ta kalli Hanifa wannan karon Kamar sun sauya da yin Dan ja da Kamar hawayen takaici dasuka Dan ciko aciki sbd halinda take Jin zuciyarta aciki na takaici saidai Kuma Bata hango ranarda zata iyayiwa hajjo gardamaba.

Hanifa dakanta ta miqe taje ta dauko Kaya ta hada Masa abincin da komai aciki tasaka a basket ta miqawa Naj din tana cewa"

Bari na dauko Miki wayarki da hijab.
##MAMUH#



*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*


*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107

*_DM 25_*
Miqewa take kokarin Yi ya ajiye cup din dake hannunsa ya kalleta da mamaki akan fuskarsa datake sata dauke idonta daga kallonsa ya mayarda ita zaune kan qafafun NASA tareda zura hannayensa ya rungumota ta baya Ya zuro kansa ta wuyanta daidai kunnenta ya bude Baki ahankali ya furta"

Me kike yiwa gaggawa na guduwa bayan kin shanyemun yoghurt¿
Kinsan me hakan ke nufi kuwa?""" Ya qarasa maganar Yana shafa fuskarta da tasa.

Yi tayi kamar bataji abin daya fadan ba taci gaba da kokarin kwacewa daga jikin nasa yasake shigewa da ita jikinsa Yana kallon wuyanta dayake shaqo qamshi daga gurin ya lumshe fararen idanuwansa ahankali kafin ya saketa ahankali Yana Dan dauke kallonsa daga kanta ta miqe tsaye fuskarta a daure sosai duk da tanajin takaici da kunyar kanta data Sha yoghurt din gashi Yana kawo Mata wani zancen kunya da takaici Dan kuwa tasan fassarar kalmar daya fada ta cewan" tasan me Shan yoghurt dinsa yake nufi"

Miqewa yayi shima ya Dan kalli fuskarta dake daure ba sassauci ko kadan,
Juyawa yayi ya nufi kujera ya zauna Yana kunna tv tareda daukan remote yakai _Aljazeera_ Yana maida hankali akai.
Yana kallonta tagajinda tsayuwa batace ko kalma daya ba sbd qin yadda ta saukar da Kai tace ya maidata gida fuskarta har lokacin a daure Takoma Kan kejeran dining din ta zauna tana jiran yagama yabar palon.

Baibi takanta ba sbd shima bawai rigimar ya iyaba dakuma daure daurenta shiyasa yashareta yaci gaba da kallon labaransa Yana duba agogo akai akai har Sha daya(11:00) tayi ya miqe tareda kashe switch na komai ya nufi hanyar bedroom dinsa batareda yabi takanta ba sbd yaga har lokacin tana zaune daram ga idanuwanta dasuke nuna tsantsan baccin dake cinsu Dan Haka Yana shigewa ta taso a galabaice ta kwanta kan kujera tana rufe ido Dan kuwa tasan baccin wahala ne zatayi gabaki daya batajin zata iya bacci a sofa sbd uban gajiya da takurar datakeji na rashin wankan dare na kafin kwanciya data Saba uwa uba kayan jikinta Suma batajin zasu barta ta iya bacci Amma Haka ta kwanta tana rufe ido.

Wanka yafito ya saka riga da wandon bacci masu Dan kauri na rugby ya zura slippers ya fito palon Yana duba agogon dake bangon tsakanin Master bedroom dinsa da bedroom dinda zai zama na Matar gidan yaga 11:37.

Bacci wuyane yayi gaba da ita me Dan nauyi Dan kuwa harda yunwa na tareda ita,
Idanuwansa ya zuba Mata ya kalleta da kyau yanajin tausayinta dakuma mamakin taurin zuciyarta tareda bakinta dayake zaro ko wace irin magana ya fada.

Sunkuyawa yayi ahankali ya dauketa gabaki dayanta ya nufi dakinsa da ita Yana sake kallon fuskarta datafi komai tsaya Masa.
Bude dakin yayi yashige tareda rufowa ya nufi sofa ya kwantar da ita ahankali ya zare Mata qaramin mayafinta da iyakacinsa wuya zuwa kafada kadan yayi wurgi dashi Yana sawa aransa bazata sake saka ire iren mayafanba sbd qarancinsu yayi yawa.

Maballan rigarta yabi Yana cirewa ahankali gaba daya kafin ya zare Mata rigar idanuwansa suka sauka Kan fara tas bra din dake jikinta wadda take showing sosai sbd lace dinta transparent ne ya dauke Kai Yana Dan hadiye abin data tsaya a maqoshinsa ya zare Mata pallazo trouser dinta take yaji kamar zaiji zufa ya miqe tsaye tareda daukanta ya kwantar tsakiyar gadonsa yaja bargo ya rufeta tareda qarasa jikin qaramar bedroom fridge din dake dakin ya dauki ruwa me Dan sanyi ya bude yasha ahankali kafin ya maida sauran ya dawo bakin gadon ya zauna tareda lumshe idanuwansa dasukaso sauyawa ya Haye gadon gabaki daya Yana kwantawa gefenta tareda rufe Rabin jikinsa ya zura hannu ya kashe musu wutar dakin.

Bacci me nauyi yayi daqyar ya samu yatashi sallar asuba da ake gaf da tayarwa ya Dan waiwaya ya kalli fuskarta dake daf da tasa suna shaqar numfashin juna ya yakai bakinsa ahankali yayi kissing bakinta dayafi komai kunnasa idan ya jeho magana kafin ya zare yafita bargon ahankali ya sauka gadon ya nufa toilet.

Da alwalarsa ya fito ya sauya Kaya zuwa jallabiya da hula ya fice zuwa massalincinsu dake tsakiyar kamar estate din.

Harya dawo bacci takeyi sosai Dan Haka Saida ya maida kayansa na bacci kafin ya hau gadon yashige bargon ya kamota jikinsa ahankali ya shigar da ita qirjinsa Yana kallon fuskarsa yakai hannu ahankali ya shafo wuyanta cikin yanayin daya sata motsawa sbd Jin baqon lamari.
Sake shafa wuyan nata yayi tareda hura Mata iskar bakinsa a hankali cikin kunne take ta bude idanuwanta dake cikeda bacci suka sauka Kan kyakkyawar fuskarsa ta kafesa da idanu tana kallon fuskar tasa batareda ta saniba.

Gira daya ya daga Yana Mata alamar tambaya da ido da wata irin muryar daukan hankali can qasa ya furta"

Karki damu da yawa sun riga sun fada da kallo daya suke fadawa soyayyana me qarfi Dan haka naki ba damuwa bane tunda ke kinriga kin samu fadawanki son mijinki ba illa bane Ina tayaki murna.

Wani qaton takaicin kanta da baqin cikin maganarsa tareda kunya suka suka taru suka danne maqoshinta ta dauke Kai tana tashi zaune fuskarta a bace.
Kallon jikinta tayi ganin daga ita sai bra da wando da sauri ta rufe jikin nata da bargon tana kasa dagowa ta kallesa akaro na uku kenen Yana samun damarta,
Wannan wace irin jalalace take gani abin kunya da takaici kullum qaruwa yake a rayuwarta.

Kwanciyarsa yayi tareda rufewa ya rufe ido Kamar bashine yagama magana ba yanzun.

Duddubawa tafara yi Amma takasa ganin kayanta a koina cikin dakin gashi bangarenda closet dinsa take daban bazata iya zagayawa tabi bangarenda fuskarsa ke kalloba ahakan,
Sabuwar damuwa da baqin cikine yakuma dabaibayeta lokacinda idanuwanta suka sauka Kan jallabiyar daya cire daya dawo sallar asuban,
Batada wani zabin dayafi Mata daukan rigarsa ta Sanya sbd bataga kayanta ba Kuma bazata taba iya tambayarsaba Haka zalika bazata taba iya zama ahakan ba daga ita sai undies din Dan Haka ta Dan taka ahankali ta dauki rigar dake zuba wani irin qamshinsa me sanyi da dadi ta yamutsa fuska tana dauke kallonta kan rigar sbd idan tana kallonta zafin zuciyarta qaruwa yakeyi ta zura rigar datakai qasa ta zube sbd mugun yawan datai Mata ta daga hannuwan rigar dasuka rufe gabaki daya hannuwanta ko yatsanta daya ba'a gani ta dauke Kai tana sakin boyayyan tsoki ta tattara gaban rigar ta 'dan riqe ta nufa kofar dakin ta fice Kai tsaye ta nufa toilet din palon Wanda Tai amfani dashi tashige.

Da alwalarta tafito ta rasa abun rufawa tayi sallah Dole Takoma dakinsa acan tasamu qatuwar hijab din sallah cikin shopping bags dinda yashigo dasu jiyan da daddare ta Sanya akan jallabiyar ta tada sallah.

Tana idarwa tayi Azhkar ta miqe ta fito tadawo palon ta zauna tana bincike Jakarta sbd wayarta data kasa gani.
Duddubawa tashiga Yi Amma takasa ganin wayar gashi wayar takeson Yi kamar me dan kuwa Sarah zata Kira tasamo mota tazo ta dauketa kota Yaya bazata iya sake ko wuni anan din ba bare wani kwanan gashi babbar damuwarta da baqin cikinta bazata iya Kiran hajjoba ko Hanifa bare Dad Alfa tace suyi Masa mgn ya dawo da ita gidan ba sbd bazata taba son ma Susan cewar har yasamu kebewa da itaba Dan kada adauka rayuwar aure suke bazata iya daukan wannan kunyarba bazata iyama Bari Susan tana taredashiba koma Nan gaba bazata Bari wani yasan sun taba kwana gurin dayaba shiyasa takeson Kiran Sarah ta lallabo ta dauketa subar Nan tun ba'a ganeba Amma takasa ganin wayar Kuma tanada tabbacin tazo gidan da wayar.

Rashin mafitar wayar da madafa gareta yasa Takoma palon ta zauna bayan ta hada tea da shortbread biscuits Tasha ta koshi ta dunqule guri daya tana rufe idonta Dan tana Jin sauran gajiya da bacci har lokacin
Ahaka kuwa wani sabon baccin me nauyi ya dauketa.

Bata Farkaba sai Sha daya saura na Rana Dan Haka a kasalance ta bude idanuwanta tana tashi zaune gabobinta na Dan Mata ciwo sbd yanayin kwanciyar datai a kujeran Babu wani sakewa.

Agogo ta kalla tareda miqewa ta nufa toilet tashiga tayo fitsari ta wanko fuskarta tafito tanajin Kamar ta Dora hannu akai tayita rusa ihu sbd baqin cikin wannan al'amari daya sameta na zama Kamar a kurkuku.

Jin shiru Babu motsinsa yasa ta nufa dakinsa Nan ba baya Nan ta fito Palo ta duba harabar gidan motarsa daya batanan ta tabbatarda fita yayi Dan Haka ta tube tashige toilet din dayan dakin Wanda yadauka sanyin AC da qamshin Rosalle roomfreshner da alama shine ya kunna AC din dakin tunda Babu kowa,
Komai na dakin golden ne ita batada wani lokaci ko sha'awan Bata lokacinda kallon dukkanin wasu abubuwan burgewa na gidan Dan Haka wanka tashiga toilet tayo da ruwan zafi ta gasa jikinta koina ta Dade tana wankan saidataji ta sake sosai kafin ta fito ta kalli gaban mirror din dakin taga turaruka kusan guda biyar Kuma dukkaninsu wainda take amfani dasu ne sai qarin Tom Ford Oud wood Wanda tasan tsananin girman kudinsa sbd girman tsadarsa.

Sama sama ta fesa turarukan kafin ta nufa jakar siyayyar data gani a dakin ta bude taga duk cikin siyayyar kayan dayayi jiyan ne ta fiddosu tana dagawa taga wata fitinanniyar rigar baccin data sanyata maidata da sauri cikin jekar tana yamutsa fuska da zallar mamaki da qin gasgata me tunanin hakan ke nufi?
Yagama wulaqanta rayuwarta tako Ina idan har ya siyo wainnan kayan baccin ne Dan Yana tunanin ita tasaka.
##MAMUH#


*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*


*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107

*_DM 26_*
Akwai riga da wando three quarter red Wanda Suma kadaine kayan sawar ta fitar ta Sanya daqyar sai alokacin ta lura hadda bra da panties acikin siyayyar ta dago bra din ahankali tana dubawa cikin tsoro da mamakin ganin dukkaninsu size dintane,
Cikeda takaici da qin yadda da ya akai ya San sizes din nata ta maida kayan ta fice daga dakin tana Jin koina na gidan siqe Mata numfashi yake sbd tsananin kosawa da tsanar komai na gidan datake ji.

Sallar azahar Tai Takoma takuma hada tea tana cikin sha aka Danna doorbell ta waiwayo tana kallon hanyar kofar tana ayyana bashi bane
Idan shine baya buqatan doorbell din Dan Haka ta tashi da tunanin ko waye zai taimaka Mata ta nufa kofar bayan ta Sanya hijab ta bude Kai tsaye.

Sojace mace sanyeda uniform ta kalleta cikin tsananin girmamawa tace"

Good afternoon mah.

Qaton basket din hannunta dayake daukeda food warmers kusan guda uku sai ledojin fresh fruits ta nunawa Naj din tana cewa"

Marshal yasa akawo Miki wannan Yana meeting tareda sauran Marshals dinnmu dasuka zo.

Ahankali ta bude Baki ta furta"

Thank you" tana miqa hannu ta karba ta shige dasu sojar tabar gurin tana cewa"

Idan kina buqatan wani Abu Ina daga Nan waje tareda dayan soldier dinmu mune muke gadin Nan.

Tana ganin kulolin tasan na gidane take taji hankalinta a na neman tashi da fatar basusan tana Nan dinba gurinsa, daqyar ta iya takura kanta taci abincin sbd batason taqici takasa samun qarfin Hana kanta bacci yau bare yasamu damar kaita dakinsa.
Tana gamawa ta Kai kayan kicin tadawo ta zauna a palon lissafinta na neman mafita na ninkuwa Dan kuwa zuwa yanzu din tana ganin zai iya Kai hakurinta da rashin maganarta maqura Kuma batasan kwanaki nawa zai jata anan dinba tunda tasan ko ajikinsa tunda kamar tozarcine yakeson yimata Dan Haka kawai ta yanke hukuncin idan yadawo zatai masa magana Dan idan ya manta matsayinta na qawar yayarsa to ya tuna ita batada abin Yi dashi.

Hankalinta ko daya baya Kan TV dake aiki zuciyarta a cunkushe take bayan komawarta gida Babu abinda take buqata.
Sake daga Kai ta duba agogo tayi tana Jan numfashi me zafi ganin karfe hudu harda mintuna ashirin ta miqe takoma dayar dakin tayi sallar la'asar tayi zamanta Bata fito tana karatun wani littafin yaren French data gani a palon har akai sallar magriba Bai dawoba Dan Haka ta sake fitowa palon ta nufa dining ta zuba abinci kadan taci Tasha lemon tea da Zuma tana kicin taji dawowarsa taqi fitowa sai daya shige tafito ta nufa dakin tashige ta rufe kofar tana tayarda sallar ishai.

Baya tareda wata doguwar gajiya Dan Haka kayansa yafara rabuwa dasu duka ya daura towel a qugunsa ya nufa toilet ya sakarwa kansa ruwan dumi Yana lumshe ido sbd Jin kansa dayake yau din free Dan meeting dinsa na yau din ya kammala aikin daya dawo dashi dan lokacin dayake dawowar baiyiba.

Fitowa yayi yana goge jikinsa ya tsaya gaban madubi Yana sake goge kansa ya dauki Neutrogena oil kadan ya shafa ajikinsa kafin ya shafa body spray na _Creed Aventus_ yabar gaban madubin ya qarasa closet ya Sanya kayan bacci farare masu tsantsi ya zura slippers yafito Yana waya da Hannah a natse cikin qowa da surutunta nason zuwa Nan gurinsa tagansa.

Direct dining ya nufa Yana zaunawa ahankali yaci abinci kadan ya taso riqeda _Red Bull energy drink_ yanasha yazo ya zauna palon Yana kallon labarai.

Ya Jima zaune a palon Yana kallon labarai tareda amsa waya akai akai.
Bude kofar dakin tayi ta fito sanyeda hijab din datai sallah ta nufosa fuskarta a Dan hade ta qaraso tsakiyar palon ta Dan tsaya daga gefensa ta Dan kallesa tana taqaita kallon nasa Kai tsaye da muryarta mara hayaniya tace"

Inada abubuwan dasuke jirana a gida da gurin ai....shiru tayi tareda waiwayowa ta kallesa har lokacin Bai juyo ya kalletaba idanuwansa na Kan TV da waya ahannunsa ta dauke Kai tana tamke fuska Kai tsaye taci gaba da cewa"

Inada abinyi Babu wani dalili ko amfanin zamana anan pass na shigowa anguwar kawai nake buqata inada inda zansa Azo daukana acikin Daren Nan Dan bana buqatan qarin ko kwana daya anan.

Juyowa yayi ahankali ya zuba Mata fararen idanuwansa Yana qarewa fuskarta kallo zuwa hijab din dayayi Mata kyau tsawon seconds kafin juyar da kansa Yana duba Kiran daya shigo wayarsa yaga sunan Hannah ya dauke Kai Yana sake maidawa kan tv ya bude Baki Yana waiwayowa kadan ya kalleta da wani irin kallo yace"

Kije ki kawomun ruwa marasa sanyi sosai zansha.

Da mamaki me girma ta kallesa ganin yanda yayi maganar Kai tsaye fuska a kame ba alamar tsokana ko wani Abu Mai Kama da hakan,ranta ya ninka baci ta juyo gaba daya gabansa ta kallesa cikin gajiya tareda kosawa da duka wannan abubuwan dake faruwa tsakaninsu kai tsaye tana bayyanarda bacin ranta tace"

Inaga ai kaji abin Dana fada farko right?
Menene wannan kakeson nunawa?
Mijin ko me bada umarni? kokuma me?
Banda lokacin duka wainnan ban buqatan fada maka Amma ai kasan matsayinka da matsayin auren so please just quit all this kaban pass Ina buqatan barin Nan.

 fararen idanuwansa ya dago ya zuba Mata dasuka fara saka maganarta gargadan fita ta dauke idonta akansa tana Jin idanuwansa akanta suna neman hanata fadar abubuwan datake fadar ta juya cikin takaici zata bar garin ya riqo hannunta ahankali tareda janyota tadawo baya ta Fado jikinsa zaune yayi Mata wani irin riqo Yana kallon fuskarta dake kaucewa kallonsa cikin muryar data sanyata waiwayowa ta kallesa batareda ta saniba yace"

Meyasa kikeson nanata kalmar girman ikona akanki?

Ahankali ya zare Mata hijabin ya aje Yana sake shigarda fuskarsa cikin wuyanta Yana shinshinawa cikin ya zura hannuwa ya shafo cikinta Yana cewa"

Abin dake nuna kansa basai nafadaba shine nine mijin,nine me ikon,nine me bada umarnin Kuma nine Zan zamo me damar Amma yanzu bazaki gane hakan ba sai Nanda watanni Inshallah result din damata zai bayyanarda kansa Amma dai shi bakin Nan daga yau zai daina magana akan iko da dama...

Bata ankaraba taji hannuwansa cikin wuyanta Yana juyo da fuskarta ya hade bakinsa da nata yana lumshe fararen idanuwansa cikin nutsuwa.

Qwacewa tafara kokarin Yi Amma takasa sbd irin shigar da itan da yayi ajikinsa gabaki daya ya rufeta bayan sarquqan numfashinsu saitaji bugun zuciyarta na tsanantuwa da fargaba ta bude idanuwanta akan nasa idanuwan dake rufe takai hannuwanta biyu Kan fadadden kirjinsa zata turesa daga jikinta ya cirata gabaki daya ya nufi dakinsa da ita Yana sake Bata kyakkyawar runguma cikin jikinsa.

Tun Bai qarasa gadonsa da itaba Yana rufe dakin ya kashe wutar dakin Yana qarasawa Kan gadon da ita ya kwantar ahankali tareda zare rigar jikinsa ya Kuma janyota jikinsa sbd tuni ta sauko gadon qafafunta na rawa zata fice dakin.

Rigar jikinta yake kallon cikin yanayin dayasa bugun zuciyarta qaruwa hannuwanta na daukan rawa ya hade Fuskokinsu Yana shaqar numfashinta da 'duminsa yake tado Masa da wata irin tsimammiyar yanayi da akanta kawai yake jinsa ya lumshe ido Yana zare rigarta cikin wani irin salon da Bata saniba yabarta da bra wadda ya zubawa ido Yana yimata fitannan kallo sake tabbatarda baiyi kuskuren riqe size dinta ba yakai hannu Yana shafa wuyanta cikin nutsuwa da salon dake sake Sanya jikinta rawa da fargaba tana neman kwacewa duk da jikinta Babu inda Bai dauki rurin abin dayake matanba,ta yunqura da qarfi tana neman turesa
Yunqurinta ya basa damar balle hooks na bra Dinta ya zare Yana jehowa qasan gadon jikinta da Babu riga ya mannu da kirjinsa da Babu rigar shima take ya kusan rabuwa da numfahsinsa sbd haduwar kirjinta da nasa take control dinsa ya balle yakasa riqe kansa Ya hade bakinsu yana zura hannuwansa zuw kirjin nata.

Wani irin kukan baqin ciki da tsoron abin dazai iya faruwa tasaki tana turesa da qarfi Amma takasa ko motsasa daga jikinta daya Gama rabata da komai Yana Mata wasu irin abubuwan dasukafi qarfin tunaninta da kwanyarta Dan kuwa abune dabai tana faruwa da itaba Arayuwarta musamman dataga wannan karon sosai yake yanda yakeso da jikin nata tun tana iya daga hannuwan tana hurasa harsaida yagama tarwatsa duk wani qarfinta ta hanyar bin jikinta da wasu irin romance masu kunyar fada bayan wani irin Nishi Bai sake tsoratata Babu abin Dake tashi a dakin saikuma sheshekan kukanta daya kasa dannuwa
Ahankali taji Yana adduar data sanyata tattaro Dan qarfinta tana neman kwacewa da wani irin kuka Amma Babu wata damar hakan Dan kuwa ahankali yafara rabata da budurcinta Wanda tayi shekaru tana kame kanta ga kowane namiji dakuma qazanta.
Azabar datake Jin tana dosarta me tsananin da Bata taba jiba yasata fashewa da kukan dabatasan tanada qarfin yinsaba tafara roqonsa ta Kiran sunansa saidai ba wannan maganar Dan kuwa tuni komai yafara kammaluwa har batasanma lokacinda taji Kamar numfashinta yabar jikintaba.


****
Qarfe bakwai saura na safe ta bude idanuwanta datake ganin dishi dashi sbd tsananin kumburinsu ahankali ta saukesu akansa Yana zaune bakin gadon yana waya ahankali cikin yanayi na basarwa wanda ke nuni da yin wayar na damunsa 
Ta maida idanuwanta ahankali ta rufe  a wahalce da sanyaye hawaye suka gangaro Mata tafara kokarin juya baya daga inda yake sai alokacin ya lurada  farkawarta ya kashe wayar tareda ajiyewa ya birkitota tareda dorata jikinsa Yana kallon fuskarta dake tsiyayar hawayen dasuka kasa tsayuwa ahankali yakai bakinsa yayi kissing idon ahankali da wata murya me kamewa da taushi yace"

Good morning Anty NAJMA JALALUDDEEN MARSHAL.

Wani sabon qululune ya taso Mata ta fashe da wani sabon kukan ahankali idanuwanta a rufe sbd bazata iya bude ido ta hada ido dashiba bayan wannan qaddararren daren.

Jin kukanta yake Yana masa wani iri ya kalleta Yana Kai hannu kan fuskar ya shafa ta turesa da qarfi tana kokarin saukowa daga kan gadon Amma takasa sbd gabobin jikinda da qafafunta Babu inda baya Mata wani irin azababben ciwo da tsamin jiki ta bude idonta dasukai jajir ta kalli kanta ko Kaya Babu ajikinta ta zuro qafafunta da qyar zata miqe Amma takasa 
Baice Mata komaiba ya zagayo ya dauketa gabaki dayanta yakaita toilet ya aje zai kunna Mata ruwa ta fizgo towel ta rufe jikinta tana nuna Masa kofa da hannunta dake rawa sbd wuya.

Ficewa yayi yabarta ta lallaba daqyar ta iya fara gyara jikinta tanajin gasawa da ruwan zafi sosai duk da har lokacin hannuwanta rawa sukeyi sosai ta rasa meyasa.
##MAMUH#



*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*


*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107
*_DM 27_*
Kamar zataji sauqi idan tagyara jikinta tayi wanka da ruwan zafi sosai Amma sai zazzabi me qarfin gaske ya sauko Mata Wanda dama tanajinsa tunda ta farka din Amma ta dauka idan tayi amfani da ruwan zafi sosai zai tafi.
Bayan fitowarta wankan da qyar ta iya Kai kanta bakin kujera ta zauna qafafunta na rawa sbd tsananin azabar ciki da wajen datakeji batabi takan qaramin towel data fito dashiba hakama kanta dake digar ruwan wanda yafi komai sake daukan hankalinsa ya taso ahankali cikin kulawa ya ranqwafa ya dauketa yakaita gaban madubi ya zaunar ya dauko wani towel din Yana goge Mata gashinta da duk ruwa suka digo daga cikinsa saitaji kamar ta kurma ihu.

Da hand dryer ya busar Mata da Kan sama sama ta lallaba tayi sallah tun kafin tagama jikinta ke rawar sanyi sosai Dan Haka kodata Gama Kan gadon ya maidata bayan ya Sanya Mata wata shirt dinsa datai Mata yawa da wandon baccin kayan baccin daya siyo Mata ya rufeta Yana fita.

Tea Mara shugar ya me kauri sosai ya hado Mata yakawo ya tadata zaune yabata kadan da dubara saidai yanayinta da yayi tsanani yasa yakasa nutsuwa damuwa ta shigesa sosai ya Ciro waya ya Nemo no din Dr sa'id ya saka kiransa ya sanar dashi yana buqatarsa anan.

Massage yatura na pass daga garesa yayiwa security check point dinsu na shigowa anguwar Da sunan Dr sa'id din Dan Haka Koda yazo suka duba sunansa da pass dinda Deen Marsha din yatura aka bude Masa ya wuce.
Dayake yasan gidan Marshal din Kai tsaye ya nufa gidansa yana zuwa aka bude Masa gate yashige yayi parking yafito daidai fitowar Deen din daga kofar babban palon Yana sanyeda three quarter kalar Navy sai shirt mara hannuwa me hula qafafuwansa sanyeda slippers na Brian Atwood marasa nauyi hannuwansa cikin aljihun wandonsa ya qaraso Yana cewa dr sa'id ya qaraso.

A Palo suka zauna ya kalli Dr sa'id suna sake gaisawa ya kallesa Kai tsaye yace"

NAJMA tana fama ne da zazzabi me qarfi plus gabobinta na ciwo sosai kaita asibiti zai sake wahalar da ita banason hakan I hope akwai taimakon da za'a iya Bata anan gida batareda an wahalar da ita zuwa asibitin ba?

Kallon tsanaki Dr sa'id yake Masa jikinsa na matuqar yin sanyi zuciyarsa ta saki sbd idan ya karanci yanayin Marshal din dakyau zai iya cankar cewan ciwon Naj din yanada alaqane da kila marshal din ya kusanceta Wanda dama hakan a gurin wasu matan is normal ciwon zazzabi Dana gabobi a ranar farko da aka fara kusantarsu.

Sauke boyayyan numfashi yayi Yana Dan taqaita kallonsa ga Marshal din Kai tsaye yace"

Pain relief Zan Bata kawai Inshallah zai sassauta zazzabin da ciwon gabobin zuwa gobe Inshallah duk zata warke
Idanma jikin baiyi saukiba zuwa goben idan tasamu karfin jikin zaku iya zuwa asibitin sai aduba jikinta acan din.

Mota yaje ya dauko maganin ya bawa Marshal din Yana cewa"

Hot milk zai taimaka Mata shima da abinci Mara nauyi shima dai me Dan zafin, Allah yabata lafiya.

Thank you" ya furtawa Dr sa'id din Yana juyawa shikuma ya fada mota ya fice jikinsa a mace Dan kuwa Deen Marshal ba namijin da mace zata iya rabuwa dashi bane duk da yasan Naj dinma Babu Wanda zai sameta yayi gangancin rabuwa da ita idanba Abbas da Allah yayi Mara rabo ba a duniya.

Da kansa yabata maganin Tasha ya maidata ta kwanta baccin wahala na sake daukanta ya miqe yakoma kan sofa Yana duba saqonni a laptop dinsa daya dawo da ita jiya daya dawo.

Yana buqatan komawa Hawaii zuwa jibi Dan aikin dayake gabansa dakuma tafiyar dazasuyi Cyprus akan wasu sabbin sojojinsu da za'a qaddamar....
Dagowa yayi ahankali ya kalli gadon datake kwancen tana bacci ya Dan zubawa fuskarta datake kumbure ido ya Dan lumshe idon Yana daukesu daga kanta Yana rufe laptop din ya miqe ya fice zuwa balcony dinsa na qatoton windown dakinsa Yana amsa wayar Hanifa dake tambayarsa Naj ya  bude Baki a natse Kai tsaye yace"

Tana bacci batada lafiya ne?

Ajiyar zuciya ta sauke tana cewa"

Please Marshal ka kuka da ita tanada rauni.

Yaya jikinki?
Fatan keda babyn lfy?

Murmushi tayi Jin ya basar da zancenta Wanda tasan lokacin amsarta ne baida hakan Kuma na nuni da itace kenan zata fada Masa abin daya kamata da matarsa.

Kashe wayarta tayi tana cewa"

Ku kula da kanku I love you both bye.

Sai bayan sallar azahar sosai Ana gaf da la'asar ta farka lokacin zazzabin ya rage tasake yin wanka da ruwan zafi sosai ta fito tayi sallar azahar tana kokarin miqewa yashigo ta dauke Kai daga kallonsa tana komawa bakin gadon Bata qarasa zamaba ya dauketa Yana cewa"

Zo kici abinci tunda kinyi sallah.

Abincin da Hanifa ta Aiko musu ya zuba Mata white rice da kidney sauce dataji kidney din sosai dasu carrot ta miqe tana cewa Bata ci
Ya janyota tana qwacewa cikin masifa da qyar yasa taci kadan Tasha tea me zafi sosai takuma Shan magani batareda ta kalli duk inda yakeba tabar gurin tana tafiya ahankali ta Isa daki ta dauka hijab din datagama sallah tasaka ta fito tana Shirin nufar kofa ya rungumota ta baya Yana sauke ajiyar zuciya a hankali yakai fuskarsa Kan wuyanta Yana cewa"

Karkiyi wahalan tafiya Zaki qarawa kanki ciwone basai kintafiba nasan irin fushi da masifan dake cinki zo ki zauna ki huta idan kin warke Zaki iya sauke duka fushinki ba damuwa bane.

Daukanta yayi yadawo da ita palon ya zauna Yana kwantar da ita a jikinsa yace"

Ki daina Bata ranki Babu Wanda zaisan me qanin qawarki yamiki bare a rainaki Kiji kunya nasan duk wannan ne damuwar ko???" Yafada Yana shinshina wuyanta da sauke Mata numshinsa me dumi da qamshi tanajin hannunsa na yawo Kan shafaffen cikinta Yana shafawa tafara kokarin miqewa ya riqeda Yana kwantar da kansa a bayanta.

Yamma nasake dosowa zazzabinta ya dawo me qarfi ya sake Bata magani tareda kwantar da ita cikin jikinsa ya rufe zafin jikinta na shiga jikinsa nasa  Dan daga ita sai qaramar shimin daya Sanya Mata kuka yadawo sabo dama Kuma tunda garin ya waye take tsiyayar hawaye Bata dainaba baqin cikin duniya ganin takeyi yau yaqare acikin zuciyarta da rayuwarta datake ganin ta rushe saidai har cikin ranta bazata iya wannan rayuwarba dashi sbd Babu Randa matsayinsa na qanin qawarta zai goge a ranta yanzu Kuma yakai kololuwar wuce hurumin haquri da juriyarta Dan Haka yakai maqura bazata Bari wannan abin daya faruba yabasa damar ji da daukan kansa cikakken miji me iko agareta,
Bazata Bari yasake samun wannan damarba dan Haka ya dauka hakan amatsayin kuskure zata sanarda iyayensu araba auren kawai Koda hakan zai kawo bacin Rai tasan zai wuce.

Koda gari ya waye ta bude idanuwanta akan fuskarsa suka sauka ta juyar da Kai tana cire jikinta daga nasa ta sauka Kan gadon tareda ficewa dakin ta koma dayan dakin tayi sallah tahirya cikin hijab ta fito palon da niyar ficewa saigashi tagansa a tsaye cikin jallabiya da waya da laptop dinsa a hannu sai key din mota ya kalleta da fararen idanuwansa kafin ya tako ahankali ya qaraso gabanta Yana kallon fuskarta ya ranqwafa ahankali yakai bakinsa saitin kunnenta ya furta"

Yanzune kike Kama da matan sure cikkaki Dan Haka be very careful idan bana nan,
Maganar aikinki Kuma Zaki iya komawa kafin wani dalilin na hanaki zuwa  ya bayyana.

Kallo ma Bata samu damar binsa dashiba ta nufi kofar ta fice Allah yasa driver zai jasu Dan Haka tana fitowa motar ta nufa ta shige Koda yafito fuskarsa a matuqar kame sai zuba qamshi da kwarjini yake kamar bashine yagama maganaba aciki yanzu ta hade fuska sosai tana kallon gefe harya shigo aka tada motar suka bar gidan Babu Wanda yasake magana acikinsu suna barin anguwar suka hau titi ta bude Baki tareda Dan kallon drivern ta dauke Kai tana cewa"

Kayi parking Zan sauka anan.

Ta madubi ya kalla uban gidansa yaga ko kallonsa baiyiba yasan ba wannan maganar Dan hakan Bai tsayaba yaci gaba da tafiya har Saida suka Kai gida ta kallesa cikin bacin Rai zatai magana Deen din ya waiwayo ya kalleta Kai tsaye yace"

Bakya gane shiru ne idan anmiki?
Koba yau ba duk ranarda na samu labarin anganki a hanya bazaki Kuma marmarin ko fita ba.

Anayin parking ta fito ta daidai fitowar Hannah zata fita a mota ta gansu zuciyarta na wata irin bugawa da ganinsu tare suda akace musu Naj tayi tafiyar aiki tareda Sarah ko hajjo ma Haka Hanifa ta fada Mata to daga Ina suka hadu suke tahowa gida tare da sassafen Nan bayan shi Daren yau jirginsa zai tashi na komawa.

Dannewa tayi tana qarasowa gurinsa cikin wani irin yanayi na Jan hankali tana cewa"

Good morning my Zawj.

Kota kansu batabiba tayi hanyar sashen hajjo tana tafiya ahankali Dan har lokacin Bata Gama warkewaba.
##MAMUH#


*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*


*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107

*_DM 28_*
Da wani irin kallo yabi bayanta da fitinannin idanunsa Yana karewa tafiyar datakeyi ahankali kallo wadda ke sake tabbatar Masa da ita din tasace tako ina,wannan hurumin nasane iya shi daya.
Saidata shige ya dan sake kamewa Yana kallon Hannah kadan wadda tagama shagwabe Masa tana cewa"

A hanya ka hadu da Naj ne ka rage Mata Hanya?
Sbd nasan dai cewan tayi tafiyane tareda secretary dinta yakamata ace tare suka dawo.

Wucewa yayi hanyar sashensa batareda ya Bata amsar tambayar dataiba cikin muryarsa datake bayyanarda kamewarsa Yana tafiya tana biye dashi yace"

Tambayan nada mahimmanci ne?

Zatai mgna ya bude kofar palonsa tareda waiwayowa kadan sai alokacin ya kalleta dakyau tana sanyeda Gucci pencil jeans da farar long sleeves me yankakken hannu sai scarf qarami dake kanta daure ya dauke Kai Yana nuna Mata kofar da ido da alamar kosawa da ita yace"

Kinada abin yi ne idan kinbini ciki?

Dakatawa tayi tana kallonsa cikin tsananin sonsa dayasa Sam batajin haushi ko zafin duk abinda zai Mata ta saki wani yalwataccen murmushi tana kashe Masa ido daya tace"

A yanzu dai banidashi Amma zuwa gaba nice nakeda abinyi aciki 
Zan fita,bye,take care I love you.

Juyawa tayi ta bar gurin tana murmushin farin cikin ganinsa Dan kwananta biyu rabonta da ganinsa saidai waya shima idan ta nace da kirane yake dagawa.

Rufe kofarsa yayi bayan ya shige ya aje wayarsa da key din mota ya nufa hanyar bedroom dinsa Yana zare jallabiyar jikinsa.

Maimakon ta nufi motarta datai niyar fita saita juya ta nufa hanyar sashen hajjo tana ayyanawa ranta son sanin meyake faruwa.

Naj ko data shiga palon Babu kowa saisu ruqayyat dake aikin gyara koina hajjo na daki,hanifa ma tana dakinta tana bacci Dan Haka Kai tsaye dakinta ta wuce tana amsa gaisuwar dasu ruqayyat ke Mata da Kai Dan bazata iya bude bakin ba Yar tafiyar datai tasa tanajin Kamar ciwon datakeji ya dawo sabo ta lallaba ta shige dakinta tareda rufowa.

Hijab dinta tafara cirewa kafin ta zare kayansa dake jikinta takai cikin water ta jefa ta shige toilet tareda hada ruwa masu shegen zafi ta shige tana sauke ajiyar zuciya tareda rufe ido ahankali sbd Dan sauki da rahamar dataji sai hawayen dasuka balle suna tsiyayo mata ta rasa Ina zata saka ranta taji saukin abinda takeji a zuciyarta Dan bazata iya wannan aurenba,suqeta al'amarin keyi gabaki daya.

Ta Jima sosai acikin toilet din kafin tafito bayan tayi hadda wanka Wanda yasa jikinta sakewa sosai saidai fuskarta da zuciyarta cike suke da zallar damuwa da baqin ciki
Ta shafa Mai kadan ta shirya cikin riga da skirt na atampa dark purple dataiwa farar fatarta kyau sosai musamman yau din da fuskarta tayi fresh duk da kumburin idanuwanta datasha kuka Yana nunawa ta fesa turare ta fito kanta ba dankwali sai qaramar hular da Bata rufe gashinta duka ba hakan Kuma ya qara Mata kyau ta nufa dakin hajjo tana kokarin nutsar da kanta Dan kada agano halinda take ciki.

Saida takai tsakiyar dakin ta tsaya cak ganinsa zaune gefen hajjo gabaki daya dakin yadauki qamshinsa yayi wanka yana sanyeda riga da wando na farin yadin filtex me laushi da tsada 
Yaji shigowarta da dakatawarta Bai juyoba hankalinsa na Kan hajjo dasuke mgn Amma ganin Naj din itama saita tsaya kallonta cikin mamaki tace"

Najma kindawo ne?
Yanzu kuka dawo kokuwa cikin dare?
Qaraso mana,
Sai tafiya Kuma takamaki daga office Baki dawoba,
Anya wannan aikin yakamaceki kuwa yanzu Najma?
Shi wannan na tambayesa tun ranar da kukai tafiyar yace da saninsa Kika tafi,ga wayarki akashe haniface kawai tace tana samunki Kuna mgn.

Daqyar ta iya qaqalo wani munafukin murmushi tana kallon hajjon a natse tace"

Da safen nan nadawo duk Kuna bacci Bari naje gurin Hanifa kafin ki Gama.

Juyawa tayi ta fice batareda tajira wani zancenba Dan 
Batareda ya waiwayoba yasaki wani irin murmushin dayasa hajjo kallonsa  da dukkanin nutsuwarta cikin mamaki dan ba abune daya fiya yiba ta maido hankalinta kansa yace"

Yaushe ka shirya tafiya da matarka?

Bai kalletaba hankalinsa nakan waya yace"

Saita shirya Bina da kanta.

Bana tunanin zatai hakan sbd haryanxu Bata amintaba da auren 
Kuma Sam banason a takurata Akan komai.

Wani shegen guntun murmushin yakuma saki Yana cewa"

Kar a takurata abarta harta Aminta dan kanta.

Tsoki hajjo tasaki cikin quluwa dashi tace"

Tashi ka ficemun sbd kedai haryau zance dakai bayada Dadi 
Mutum saiya zage yamaka mgn me tsayi ko mahimmanci ka jeho Masa kalma daya amsa,banason kayan takaici tashi kaje kafin na qarasa quluwa da wannan muguwar dabi'ar taka mara Dadi.

Bai tashiba saima kallonta da yayi yanaci gaba da duba wayarsa Yana cewa"

Ahaka fa kike damuna yaushe Zan dawo idan bana nan.

Murmushi tasaki tana cewa"

Ta Nan ka bullo Kuma.


Naj Kuma tana fitowa dakin ta nufa dakin Hanifa ta tura kofar Kai tsaye ta  Shiga saiga Hannah zaune a kejarar dakin tana Taya Hanifa yanka qatuwar guava data tashi tunda safen da marmarin ci 
Da mamaki Hanifan ke kallon Naj fuskarta na yalwatuwa da farin cikin ganinta ta ware Hannu tana cewa"

Hey sweetheart sannu da dawowa nayi kewarki sosai sirikata.

Tsuke fuska Naj din tayi tana Mata kallon daya sanyata rufe Baki tana cewa"

Sorry sorry.

Qarasowa tayi tana zama bakin gadon kusada Hanifan ta bude Baki cikin kulawa tace"

Ya ya?ya babyn?

Lafiya kalau muke,ya Hanya? Da gajiyan tafiya?

Alhmdlh" kawai ta furta tana basar da zancen ta hanyar Dan kallon Hannah datace"

Naj sannu da Hanya?
Inane kukaje aikin ne hala?

Yi tayi kamar bataji Hannan ba ta miqe tana nufar kofa tace"

Zanci abinci a dining.

Miqewa Hanifa tayi tana cewa"

Nima yunwar nakeji,
Hannah ko Zakiyi breakfast damu?muke ko.

No nariga naci abinci bana buqatansa qarawa Zan fitanema nace Bari nashigo na dubaki tun shekaran jiya banshigoba.

Dining suka nufa ita Kuma ta fice daga sashen batareda tasan Marshal na sashenba Dan da Babu inda zata.

Tea kawai ta iya Sha sai doya kadan da aka soya da egg sauce ta miqe tana kallon Hanifa dakecin doyar sosai tace"

Inajin Dan ciwon Kai da gajiya zanje na kwanta ko zansamu bacci kafin lokacin sallah.

Ok ki kula, Allah ya hutarda gajiya.

Daki Takoma ta Isa gadon ta kwanta tareda qarawa AC qarfi sbd zufi takeji na zazzabi dake hawa Yana sauka ajikinta ta rufe cikin bargo tareda rufe idanu ahankali bacci me qarfi ya dauketa.

Bacci Sosai tayi Bata Farkaba sai guraren la'asar ta tashi zaune ahankali tanajin tasamu sauki Sosai ko Ina nata ya sake ba laifi ta sauko gadon tareda cire kayan jikinta ta nufi toilet tadake wankan ruwan zafi sosai ta fito da walwalarta tafarayin sallar azahar da la'asar kafin ta Dan shafa Mai ta Sanya doguwar rigar atampa ta fito.

Daga hajjo har Hanifa na zaune palon Hanifa na kallo hajjo na karantunta data Saba da medical glass dinta a fuskarta,
Naj din na fitowa duk suka bita da ido hajjo Kai tsaye tana cewa"

Najma lafiyarki kalau kuwa?Naga duk kinyi wani iri kamar bakyajin Dadi?
Anya Baki debo sanyi a tafiyar Nan ba fuskarki duk ta kumbura,kodai bakyajin Dadi ne?

Hanifan ma zuba Mata idanuwa tayi tana jiran amsar da Naj din zata Bata Dan itama dai taga alamar Kamar batada lafiyar duk fuskarta a kumbure Dan ko yanzu data shiga wanka saidatasha kukan qaqa nikayi kafin tafito.

Dan murmushin Dole tasaki tana qarasawa dining tace"

Lafiyata kalau hajjo kawai dai garin akwai sanyi ne sosai shine yake damuna matuqa Amma zankira Dr sa'id saiya kawomin maganin sanyin Inshallah Kuma ma zuwa gobe Inshallah Zan warware tunda nadawo gida.

Zama tayi ta diba abinci tafara ci bayan Tasha ruwan zafi Dan tafijin dadinsu fiyeda abincin,
Saidata koshi ta taso tadawo gurinsu palon ta zauna Hanifa na janta da Hira sosai tana Dan qoqarin sakewa da amsawa 
Hajjo kuwa saiyi takeyi tana kallonta sbd hankalinta kamar Bai kwanta da lafiyar ba ganin take Najma din batada lafiya boyewa takeyi sbd kada ta daga musu hankali idan taga ankwana biyu Bata warware ba zata Kira Dr sa'id da kanta yazo ya duba musu ita.

Ba laifi ta Dan sake sunata hirarsu akan babyn Hanifa da duk suka qwallafa Masa Rai har akai magriba suka shige sallah 
A dakin Hanifa sukai sallar acan tayi zamanta har ishai Hanifa nata Koro Mata bayanin scanning dasukai shekaran jiya da Kuma dawowar da Isma'eel zaiyi qarshen wata.
Saida sukai sallar ishai suka Gama zantukansu da Naj daurewa kawai takeyi tana danne damuwar halinda take ciki kafin suka fito cin abincin dare.

Dukkaninsu suna zama Kan dining din ko fara cin abincin basuiba saiga qamshinsa ya fara tunkaro dining din tanajin hakan tasan waye ke zuwa Dan Haka ta Dan hade fuska tana daurewa Dan Hana kanta miqewa tabar gurin sbd hajjo dake gurin gashi tariga tana zaune ne da a tsaye take saitabar gurin..

Muryar Hannah taji cikin wani irin salon nemawa Kai gurbi tana cewa"

Hajjo anan zanci abinci Nima yau can masu aikin mum Malika abincin dasukai yayi Mai sosai zaisani zafin Zuciya.

Da Yar kulawa hajjo tace"

Eh gskia karki ci idan zai saki damuwa zoki zauna kici anan din.

Da sauri ta qaraso taja kujerar dake kusa data Marshal din ta zauna tana jifansa da wani irin kallo 
Shikuma hankalinsa gabaki daya baya kanta Yana Kan abincin da Naj ta zubawa kanta taqi ko dagowa ta kalla inda suke Dan Jin take cikinta yagama cika da wani irin takaici.
##MAMUH#


*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*


*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107

*_DM 29_*
Hannah da kanta ta miqe tariga kowa zuba Masa abincin duk da tana iya kokarinta na riqewa da kiyaye duk wani abin dayake so dakuma ya shafesa Dan Haka abincin iya daidai Wanda tasan yanaci ta zuba masa tareda lemon juice me zuma datasan bayan _RED BULL Blue edition Energy drink_ shikadai yakesha.

Zama tayi tana zuba nata abincin kadan sbd Babu wata yunwar datakeji taci abincinta tun dazu sbd Marshal din yasa tace zataci anan din duk da zuwa yanzu da Naj ke sake zamar Mata abin takaici da baqin ciki Sam said Dole take iya zama guri daya da Naj din Dan dai kawai tana mum Malika nasata dannewane tana boyewa.

Naj cin abincin takeyi a hankali duk da yariga ya gundureta cin kawai takeyi a natse batareda ta kalla kowaba sai hajjo data kalleta cikin kulawa ganin yanda takecin abincin cikin nutsuwa ahankali duk da tasan sanyi da komai a natse hali da dabi'ar Najman ne Amma ita dai tafiyar Nan duk tasake sakurkuce Najman,
Cikin kulawa tana kallonta tace"

Najma jikin ne haryanxu?
Nace ruqayyat ta dafa Miki Ginger tea da Zuma sbd da alamar wannan sanyi ya kamaki sosai a wannan tafiyar,
Gobe Dr sa'id zaizo ya dubaki.

Dagowa tayi ta kalla hajjon tana aje spoon din hannunta cikin nutsuwa tace"

Naji sauki fa Kuma bawani ciwo bane sanyi ne kawai basai Dr sa'id din yazo ba zansha Ginger tea din zuwa gobe Zan qarasa warwarewa.

Zanfi samun nutsuwa idan Dr sa'id yazo yadubaki" hajjo tafada Kai tsaye tana kallon Najman kafin taci gaba da cin abincinta.

Shiru Naj din tayi tana daukan spoon taci gaba da cin abincin tana ganin irin kallon da Hanifa ke binta dashi tayi Mata banza Bata bi ta kantaba.
Hannah ta karba zancen da cewa"

Naj inane kukaje da Sanya zai kamaki Haka?

Sai alokacin ya dago ya 'dan zubawa Naj din ido wadda tun dazu dasuke zancen Bai dagoba Yana jinsu tambayar hannah tasa ya dago yana kallon Naj din.

Ahankali taji idanuwansa akanta Dan Haka ta sake kame fuska tanacin abinci tana share tambayar hannah da shirun yasake habbaqa tsanar Naj din aranta ta dauke Kai daga kanta ta juyo gurin Marshal din zatai mgn ya aje tissue dinda ya goge Baki Yana miqewa tsaye ahankali alamar yagama ya zuba hannayensa ahankali ya tako zuwa inda take zaune ya sunkuya ya saukar Mata da wani irin lafiyayyan kiss a kumatunta na hannun dama ya Kai Bakinsa kan kunnenta ahankali qasan maqoshi da wata irin murya me tsananin taushi ya furta"

Ki tabbata kinsha ginger tea dinnan sbd wani sanyin dazai iya kamaki.

Dagowa yayi ya kalli su hajjo Kai tsaye cikin attitude yace"

Goodnight,Mu kwana lafiya." Ya juya ya wuce yabar gurin.

Mutuwar zaune tayi abincin dake cikin bakinta na neman dawo Mata da qarfi sbd mummunan yanayin mutuwar zaunen datai,wani irin tari ya taso Mata Hanifa tayi saurin daukan ruwa tana Bata daqyar ruwan suka wuce Mata ta dauki tissue tana goge bakin idanuwanta na yin ja sbd wahalar sarqewar datai dakuma ta halin data shiga na tsananin kunya da takaicinsa,
Ta dago ahankali ta saci kallon inda hajjo ke zaune taga abincinta take ci kawai tayi kamar batamasan menene ya faruba agurin sbd JALAL tasan zaiyi fin hakan agaban ko uban waye tunda rayuwar daya tashi acikine yake Kuma rayuwa aciki gabaki daya rayuwarsa irin ta 'yan can yake ta Dade da sanin kaai tsaye yake.

Ruwan juice Hannah ta zubarwa Naj ajiki ta hanyar ture cup din cikin tsananin bacin Rai da baqin ciki dukkaninsu suka kalleta Naj na miqewa sbd sanyin juice din na shigarta ta dago ya kalli Hannah data miqe itama tace"

Sorry ba da ganganbane hannuna ne yayi santsi cup din ya subuce, sorry.

Hanifa dake goge jikin Naj din tace"

Hannah tana fama da sanyi Zaki qara Mata wani juice din nada sanyi sosai fa ki ringa kulawa ko gaba please,
Naj kije ki cire kayan Kar sanyin ya shigeki.

Hajjo ma kallon Hannah tayi barin barin Naj gurin cikin yanayi na manyanci tace"

Hannatu wannan baida kyau kwata kwata kiyi gaggawan aje shashanci ki saka kula.

Barin gurin hajjo tayi Hannah tabi bayanta da wani irin mugun kallon tsana zuciyarta Kamar zata cinnu da wuta sbd baqin ciki da takaicinsu duk su dukan, Ahankali ta furta"

Munafukan Allah ta'ala.
Juyawa tayi ta bar sashen gabaki daya idanuwanta ko gani basayi Sosai sbd baqin ciki.

Naj na shiga dakinta Kai tsaye tube kayan jikinta tayi duka ta jefasu cikin kwandon kayan wanki ta daura towel ta nufa toilet ta bude Kai tsaye ta wanke jikinta tasake Dan watsa ruwan zafi tafito ta saka kayan bacci masu kauri riga da wando ta fito ta nufi kicin Dan Shan Ginger tea dinta da aka dafa Mata.

Tana fitowa palon taji qamshin Tom Ford turarensa taso dakatawa Amma sbd Bataga alamar kowaba a palon saita wucewarta kicin ta zubo tea din a cup me Dan girmata fito ta nufa dakin hajjo Dan batai Mata Saida safe a Kai tsaye tashiga dakin da cup dinta a hannu saidata rufe dakin ta juyo tagansu zaune a kujera daya shida hajjo Yana riqeda hannunta sai Hanifa dake Kan gadon hajjon kwance tana facing dinsu da alama duk su dukan magana suke.

Juyarda fuskarta tayi daga kallon dayake Mata zuwa gefen Hanifa a tausashe tace"

Zanje na kwanta saida safenku.
Juyawa tayi ta fice batama tsaya sauraron abinda hajjo ke fadaba na tambayarta jikin nata.

Dakinta ta koma ta zauna ahankali tafara shan ginger tea din Yana tiririn zafi harta shanye duka
Take zafi yataso Mata tako Ina taji Kamar tana cikin Rana ta miqe tsaye tana cire kayan baccinta masu shegen kauri ta sanya rigar bacci me Dan tsayi Mara nauyi ta qara qarfin AC sai alokacin taji tanajin daidai Kuma taji jikinta yasake sakewa sosai ta nufi gadonta ta Haye ta shige bargo tana kashe wuta Dan yau Kam baccin wuri zatai Dole tunda abokanan firarta nada abokin fira.
Bata Jima da kwanciya ba bacci ya dauketa.

Qarfe goma Sha daya saura yashigo dakin ya qaraso bakin gadonta ya tsaya kanta Yana qare Mata kallo cikin wani yanayi dashi kadai yasan sirrin abinsa.
Fuskarta zuwa bakinta dayake yanka wuyanta ya tsayar da idanuwansa kafin ya cire hannuwansa daga aljihun wandonsa ya zauna bakin gadon Yana gyara Mata rufarta data Dan bude rigar baccin red color na Dan daukan hankalinsa sbd kalar hot red ce ba transparent bace Amma ta lafe ajikinta ta kwanta,ya 'dan rufe ido ahankali Yana budewa ya shafa fuskarta da har lokacin Bata koma daidaiba da kuka da zazzabin datai.
Qarfe bakwai jirginsa zai tashi gobe shiyasa kawai yashigo gurinta saidai samunta da yayi tayi bacci yasa yafasa tafiya ya Haye gadon ya kwanta gefenta tareda shigar da ita jikinsa Yana sake gyara musu rufa.

Asubar fari alarm din gefen gadonta ya tada ita ta bude idanuwanta ahankali tana kokarin Kai hannu ta kashe taji mutum tareda ita
Gabanta ya buga da qarfi cikin sauri takai hannu gefen gadon ta kunna wutar dakin Mara haske daidai Yana bude idanuwansa ahankali ya kalleta da yanayin daya sake kayar Mata gaba da ganinsa ta yunqura da qarfi zata tashi ya girgiza Mata Kai ahankali Yana maidata jikinsa cikin kasala yace"

Banason farkawa da hayaniya Yana sani ciwon kai,ki riqe hakan.

A hasalce da bacin Rai da mamaki tana qin daga murya danma Kar tsautsayi yasa aji tace"

Meya kawoka Nan?
Menene hakan?
Banason wuce wuri fa,Abinka yayi yawa....

Bude idanuwansa yayi da kyau akanta har lokacin tana cikin jikinsa ya shafo bayanta da hannunsa dake cikin rigarta yace"

Ke bakinki baya mutuwa ne?
Just shut up ok¿Nafada Miki banason farkawa da hayaniya.

Turesa tahau Yi tako Ina sai hannuwanta daketa turesan suna Masa wani irin waiwayi dayasashi dagowa ya kalleta da mayun idanuwansa cikin kunnenta ya furta"

Kinsan me kikeyi kuwa?

Da sauri tasake turasa batareda ta kalli fuskarsa ba sbd Jin muryarsa data sauya.
##MAMUH#


*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107

*_DM 30_*
Riqe hannunta yayi ahankali yana sake kallonta da yanayinda yasake fadar Mata da gaba yace"

Ya Isa haka,kece Kika jawo wannan yanzu..

Shinshinan wuyanta yashiga Yi Yana sake shafa bayanta zuwa wuyanta da hannunsa dake cikin rigarta har lokacin,tsikar jikinta dasuka tashi gabaki daya sbd wani irin fitannan kiss daya sauke Mata a wuyanta da Babu komai,
Tasake daga hannuwan zata turasa can qasan maqoshinsa ya furta"
Kinayi Zaki Zaki ja na rasa jirgina Kuma wlh na rasa jirgina saimun bar gidan Nan ayau.

Bata tsaya sauraronsaba sbd idonta dasuka Gama rufewa taringa turasa Wanda hakan yake qarasa sauya yanayinsa ya juyar da ita gabaki daya Yana Mata rumfa tareda dago fuskarta yana hade bakinsa da nata hannuwansa Kuma na zare rigar baccinta ya jefar da ita Yana hada jikinsa da nata da Babu riga shima dama Bai Kwana da riga jikinsa dagashi sai dogon wandon baccinsa rigar sanyice yazo da ita Kuma yacire.
Saida kukanta ya daina fita gabaki daya kafin ya taqaita aikinsa daya mugun shagala ayi musammam yau daya samu hanyar da kyau
ya dauketa da kansa ya nufi toilet da ita,
Yana sauketa ahankali duk da batada qarfi da kuzari Haka tabi bango ta fito ko gani batayi sosai duk wani rauninta ya fama matashi zallar azaba takeji tana fitowa toilet din ta zube qasa da Jan jiki ta qarasa gadon ta kwanta bakin gadon hawaye na tsiyayo idanuwanta dasuke a matuqar kumbure.

Kamar zai biyota yasan Rigima kawai zatai Kuma batada qarfin yin rigimar Dan Haka ya barta kawai yayo wankansa duk biyu da yafito daureda qaramin towel dinta dayayi Masa kadan yahau goge jikinsa Yana duba agogon sallar asuba da aka tada tuni ya kalleta Yana qarasawa inda take bai tsaya komaiba yakuma daukanta duka ya nufi toilet da ita ya aje ahankali,
Zata qwace jikinta ya saketa a hankali Yana cewa"

Relax fita zanyi.

Juyawa yayi ya fice ya saka kayansa ya fice da sauri zuwa masallaci.

A palon kuwa Yana fitowa daga dakin ruqayyat na fitowa daga kicin data shigo ta kofar baya ta kicin din Dan fara aikace aikacensu dasuke farawa tun qarfe shida da rabi Amma yanayin ciki da Hanifa take dashi yanzu tun asuba take shigowa Dan hanifar tun asuba tana tashi saitaci abinci tayi sallah Takoma bacci kafin Kuma ayi breakfast da ita.

Tana ganinsa tayi saurin sauke Kai cikin tsananin girmamawa tana dakatawa daga inda take harsaida ya fice tukuna.

Ahankali ta gyara kanta tayi wanka da ruwan zafi sosai tasake shiga cikinsu sosai kafin tayi wankan Dole jikinta yayi Mata daidai tsamin jikin ya Dan tafi ta fito ahankali ta saka kayan data fara sawa jiyan ta cire riga da wando masu kauri tayi sallah ta koma gado ta kwanta sbd zazzafan zazzabin datake Jin Yana saukar Mata.

Qarfe shida da rabi ya fito shirye tsaf cikin Roberto cavalli jeans da white Armani rugbay shirt sai qatuwar tsaddadiyar rigar sanyi jacket daya Dora me tsayi sai qamshinsa ke tashi tuni aka fitarda motarda zata kaisa airport ya kalli hajjo cikin kulawa yayi Kama hannunta Kamar yanda yasaba cikin kulawa yace"

Allah ya sadamu da alkhairi,saina dawo Inshallah.

Dafa hannunsa tayi tace"

Allah yacigaba da yiwa rayuwarka albarka,
ALLAH ya tsare yakai lfy.

Kofar dakinta ya kalla kafin ya nufa kofar dakin ya tura yashiga yaganta kwance baccin wuya yayi gaba da ita ya qarasa ahankali ya sunkuya ya shafa fuskarta tareda Bata light kiss ya Ciro katinsa na banki daya tareda paper me daya rubuta password ya ajiye Mata gefen pillow ya fice.

Yana fitowa shida Hanifa suka fito zata rakosa mota a bakin motar suka tararda Hannah shirye cikin kayan sanyi itama sbd safiyace Sosai akwai sanyi zata rakasa airport Kamar yanda tasaba duk zuwansa
Suka Shige motar driver yaja suka fito motar mutanensa na waje suka Mara musu baya suka harba titi.

Bayan dawowar Hanifa ciki Kai tsaye dakin Naj ta nufa Dan ita Kam Hannah ke wasu abubuwan itakeji wa Naj din ba Dadi tunda Naj din Bata yiwa kanta fada da karatun ta nutsu ta amsa aurenta tun kafin ayi Mata sagegeduwa tun Bata ganewa komai a aurenba.

Bacci ta taddata tanayi ta qarasa bakin gadon tana tunanin kilama ko sallar asuba Bata tashi tayiba 
Tana Kai hannu jikin Naj din taji yadauka wani irin zafi sosai.

Da sauri ta kalleta tana sake taba jikin nata da har wani Dan guntun Nishi takeyi cikin sauri da damuwa tace"

Naj,Naj kina fama da zazzabi me zafine Haka?

Bude idanuwanta tayi ahankali cikin siriryar murya tace"

Nasha magani idan nayi bacci Koda Zan tashi Inshallah ya sauka.

Da kulawa Hanifa tace"

Wane magani Kika Sha?
Bari naje na sanarwa Dr sa'id a waya.

Girgiza Kai tayi ahankali tana cewa"

No please karki fada Masa ki Bari nayi bacci Dana tashi Inshallah shikenan.

Badan tasoba tace"

Shikenan Bari na kwanta anan din mugani zuwa anjima idan kin tashi daga baccin.

Duk da tana cikin zafin zazzabi saidata yunqura ta tashi zaune tana cewa"

Aa kije karki damu Inshallah nafada Miki ba wani ciwo bane.

Kallonta Hanifan take da mamakin ganin tashinta zaune Kai tsaye tace"

Naji Amma dai Zan kwanta anan ko natafi dakina bazan iya bacci ba idan nabarki ahaka.

Riqo hannunta Naj tayi da sauri tana Dan rufe ido ta bude sbd zafin zazzabin ta qaqalo murmushin daya sake sawa Hanifa zargin boyon wani abun Naj keyi tace"

Hanifa dan Allah kije dakinki 
Na Miki alqawarin Ina lafiya Inshallah.

Naj is there anything you're not telling me??

Like what Hanifa?" Naj din tafada cikin Dan mamaki.

Hanifa tace"

Like abin dayasa bakyason na kwanta anan din sbd na tabbatarda ba sbd karna damu bane wannan din.

Ajiyar zuciya Naj ta sauke tana rintse ido sbd rashin sanin yanda zata Hana Hanifan kwanciya a gadon Dan duk Wanda yasan Jalal farin sani to Yana hawa gadon saiyasan jalal din ya kwana a gadon Dan kuwa daga bargon har zanin gadon da pillows din qamshin turarensa sukeyi.
Tasan Hanifa na hawa saitace qamshin JALAL takeji,
Me zatace idan ta tambayeta hakan?
Wannan wace irin masifa ce ta sameta ta kame kame,
Wlh dai angama da rayuwarta.
##MAMUH#


*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107

*_DM 31_*
Ahankali ta sake hannun Hanifar tana  komawa ahankali ta kwanta sbd Jin hanifar tafara tunanin akwai dalilin dayasata batason ta zauna din tareda ita,
Har cikin zuciyarta tana Jin zafi da takaici tareda tsananin kunyar Hanifa ta Dan samu alama ta fahimta koma hasahsen wani Abu yafaru a dakin,bama dakin ba kawai a tsakaninta jalal din gabaki daya
Abune mafi kunya da tozarci gareta idan Hanifa tasan wani Abu gameda hakan,bazata taba Bari wani yasan wannan tsausayi da qaddarar data hau kantaba.

Ajiyar zuciya Hanifa ta sake cikin kulawa ta tako ta matso gaban gadon ahankali ta gyara Mata rufarta tana cewa"

Shikenan kiyi baccin zanje Nima na kwanta Dana tashi zandawo na dubaki.

Gyada Kai tayi ahankali tana rufe idanuwanta tareda gyara kwanciyar kanta a pillow.
Sai dataga fitar Hanifan ta saki Dan qaramin numfashi tana sake komawa baccinta dayake idanuwanta har lokacin.


Bacci tayi Sosai Bata fitoba Wanda yasa hajjo nacewa zancen tabbas Naj ba lafiya take ba Dan Haka Babu sanin  Naj din tasa Hanifa takira Dr sa'id Wanda baizo gidan ba sai yamma bayan yataso daga asibiti.

Dagashi sai ita ya Mata Yan tambayoyi tabasa amsa a Dan gaggajarce sbd son qin bada hanyar dazata saka koshi ya Dan gane wani abun 
Shima Bai wani zurfafaba sbd gane zazzabin tun ranarda Marshal yakirasa acan gidansane Bai Gama sakinta musamman idan sake kusantarta akai Wanda hakan ke nuni da Bata taba saduwa da kowane namijiba hakama Bata budeba ta hanyar tsallake tsallake da yawace yawace Wanda yake ragewa budurcin mace qarfi shiyasa take wannan wahalar Dan Haka Bai zurfafa tambayaba ya Bata maganin dazasu taimaka Mata nasu zazzabi da pain relief ya miqe Yana Dan kallonta yace"

Inshallah zaki warware zuwa gobe ko jibi idanma dai kinji bakyajin daidai har lokacin Zaki iya kirana kokuma ki sameni asibiti saimuyi waeu dube duben mugani Amma dai Inshallah ma Zaki warware din zuwa gobe.

Hajjo takira Masa ta fito tana kallonsa tana qarasowa tana cewa"

Dr sa'id zaka tafi?
Kagama dubatan?
Bansan menene wannan zazzabin sanyin dayaqi sakinta ba tun dawowarta na fahimci batada lafiya Amma tace sanyi ne,
Kuma anyi maganin sanyin kwana biyu yau Kuma abin yadawo.

Dan murmushi yayi Yana cewa"

Nabata magana Inshallah zata warware zuwa gobe
Ba wani ciwon daga hankali bane zazzabine kawai sai gabobi da zasuyi ciwo dama, ALLAH ya Bata lafiya Zan tafi hajjo idan kwana biyu zazzabin Bai tafiba nace ta sameni asibiti.

Ok Inshallah Dr sa'id, 
Agaida gidan dasu hajiya.

Zasu shi Inshallah.

Ficewa yayi daidai fitowar Hanifa data fito daga kicin tagama ciyo wainar fulawar dataji kwai wadda umma ta Aiko Mata,ta qaraso palon ta zauna gefen Hanifa tana kwadawa ruqayyat Kiran takawowa Naj Naman Hantar datasa ta dafa Mata dazu tareda ruwa Tash magani.

A gabanta ta ajiye Mata Kan table Takoma takawo Mata ruwa marasa sanyi sosai Dan kaidar Naj dinne Bata Shan ruwan sanyi sosai.

Ahankali takeci sbd ya 'dan yimata Dadi dan yajin da ya 'danyi sbd bakinta da baida apatite na zazzabin,
Taci sosai Saida cikinta yacika Tasha maganin da Dr sa'id yabata tasake dorawa da Ginger tea me zafi 
Ahankali taji jikinta ya Dan Yi Mata Dadi tasamu kuzari dakuma zazzabin daya sauka.

Ahankali ta kalli ruqayyat dake dauke kayan data Gama cin abincin tace"

Ruqayyat idan kinkai kije dakina ki dauke zanin gadon Dana cire Yana Nan Kan kujera kikai laundry.

Yes Ma." Ruqayyat din ta furta tana Kai kayan kicin tadawo ta nufa dakin Naj din ta kwaso zanin gadon ta fito.

Miqewa hajjo tayi ta nufa hanyar dakinta sbd kiran sallar magriba da aka fara daidai ruqayyat na kawowa da kayan zata wuce Hanifa tadawo daga dakinta dataje dauko Abu ruqayyat na giftawa gabanta ta kalleta cikin mamaki tace"

Ruqayyat wannan beddings din Marshal ne?me sukeyi a hannunki?
Ta Yaya sukazo hannunki?" Taqarasa fada tana sake shaqar qamshin Dake tashi ajikinsu kamar yanzu ya kwanta akai.

Hajjo ma dakatawa tayi tana kallon ruqayyat Jin abinda Hanifa ta fada Dan dai tasan Babu me shiga sashen nasa a taqaicema namijine me aikinsa dayake Masa gyaran sashensa da wankin kayan zanin gadonsa da komaiba.

Da sauri cikin tsananin tsoro da girmamawa ruqayyat ta kalli Hanifa tace"

Anty wannan da dakin Ma'am ne tace akai laundry ba na Sir Marshal bane.

Rintse ido Naj tayi zuciyarta na Shiga takaici wannan al'amari gashi ba damar tasa Baki tabada kanta dan Haka Tai shiru tana fatan ruqayyat din ta wuce ga hajjo ma datake saurarensu sbd Jin sunan Marshal Dan gskia ba'a Wasa da harkan Marshal ko bayanan ba'a yin abinda akasan bayaso.

Qamshin turensa ne yake tashi a kayan Nan sosai kin tabbata Wanda Naj tace ki dauko ne a dakinta,
Bafa sashensa tace kijeba a dakinta take nufi........

Da sauri ruqayyat tana sauke Kai tace"

A dakinta na dauko wlh
Acan ya kwana shine zanin yake qamshin,
Wlh banje sashensaba a dakin Ma'am na dauko.

Wata irin wuta Naj ta dauke zaune agurin wani zafi na huro Mata tako Ina ta dago ahankali zuciyarta na gaurayuwa da daci ta kalli inda hajjo take taga Bata gurin Dan tunda taji Ana neman tada sallah ta shigewarta Bata tsaya Jin zancenba tunda ga Hanifa.

Rufe ido tayi wani Dan sauki saukinda baida wani amfani na shigarta ganin hajjo bataji me ruqayyat din tafadaba 
Taqi waiwayowa ta kalli Hanifa datai Kamar bataji me ruqayyat din taceba duk da ta girgiza matuqa dajin zancen ruqayyat din ta fuske tana cewa"

Wuce kije aikin gabanki kardai ki kuskura Koda aike kije sashensaba batareda iziniba.

Ruqayyat na barin garin hanifar Bata waiwayoba tayi dakinta tana cewa"

Naj Bari nayi sallah kafin na zauna.

Rufe ido Naj tayi tana dafe Kai cikin tsananin hali,gabaki daya zuciyarta ta cike da damuwa da bacin Rai tana zamanta cikin kwanciyar hankali da rufin asiri kame kame da boye boyen bacin Rai yaganta,wane tashin hankali da damuwa ne wannan¿Bazata iya cigaba a hakaba kunya da baqin ciki zasu iya illatata kawai zata daukarwa abin mataki wlh kanta bazai iya daukan wannan ba.

Miqewa tayi ta nufa daki a sanyaye itama tayi alwala tayi sallah tana idarwa ta miqe ta nufi gaban madubi sbd abinda ta hango.
Sai alokacin idanuwanta suka gane Mata katin bankin Dake daukeda sunansa JALALUDDEEN ALFA da wayarta a gefe aje.
Wani sabon mamakinsane ya kamata ta kalli takardar dake daukeda pin na katin ta yamutsa fuska tana rintse ido tareda dafe goshinta sbd kanta dake sake daukan ciwon haukatata da komai nasa ke Naman yi,
Me hakan ke nufi daya bar Mata katinsa?
Ya dauki nauyintane da dawainiyarta  sbd ya karbi auren kokuma zai karba kuwa matsayinsa Miji yake son nunawa?to ita Bata karba ba Kuma batajin zata iya Dan Haka ta hada katin da paper din ta nufi wardrobe ta bude safebox dinta ta bude ta jefa ciki ta rufe tareda rufe wardrobe din gaba daya tadawo ta zauna da wayarta a hannu tana kunnawa saiga massages suna shigowa kusan duk na Sarah ne saina Abbas Wanda ko budesu bataiba ta gogesu tana Danna Kiran Sarah.
##MAMUH#


*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*


*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107

*_DM 32_*
Da daddaren ta daurewa tayi ta fito sbd nuna taji sauki Dan kada hajjon tacigaba da matsa cewan Bata warkeba Azo Ana tsananta bincikawa.

Suna cin abinci Hannah ta shigo ko dining room din Bata qaraso ba hangosu sunacin abinci tayi zamanta Palo tana jiran su qarasa wasu kayan zaqine takawowa Hanifa tsaraban shopping dataje.

Koda suka Gama a palon suka zauna fira sama sama Banda hajjo data shige qaramin palonta dake hanyar gefen dining room suna magana da Dad Alfa dayazo gaisheta kamar yanda yasaba matuqar Yana gari kullum saiyazo gaisheta.

Ganin wani irin dogon surutu da Hannah ke janyowa Wanda duk rabi na firar Marshal ce Dan nuna irin kusanci da soyayyar datake tsakaninta dashi,
Hanifa sai basar da zancen take sbd Hannah ta barshi Dan Naj dake zaune Amma sai sake jansa takeyi cikin salo da nuna isar matsayinta agurinsa.

Miqewa Naj tayi tabar gurin sbd surutun ya isheta musamman indai akansa ne Bata buqatan ji ta nufi hanyar dakinta tana musu Saida safe tashige.

Tana shigewa Hannah ta saki murmushi tana sauya zancen da cewa"

My in-law kinyi waya da Marshal ya Isa lafiya ko?sbd nakasa samunsa tun dazu,bazan iya kwanciyar hankali ba sainajisa,
Please idan kunyi waya ki sanar dashi inata neman wayarsa, please.

Ya Isa lafiya inshallah saidai Bai Isa qarasawa gidaba bare ya huta harya kunna wayar sai zuwa gobe Inshallah,idan ya Kira Zan sanar Masa Inshallah..Zanje na kwanta ko,Saida safe.
Miqewa tayi ta bar Hannah din a zaune ta nufi dakinta sbd tasan idan ba tashi tayiba Hannah Bata gajiya da magana.
Bin bayanta Hannah tayi da kallo tana Dan yamutsa fuska itama sbd tamafita Jin gundura dasu dukan dannewa kawai takeyi.
Miqewa tayi itama ta fice daga sashen.


Washe gari ba laifi ta tashi lafiya kalau sai Dan qananun abinda baza'a tasaba Dan hakama tana tashi wanka tayi ta shirya cikin riga da skirt na lace me tsada Mara nauyi ta fito sukai breakfast daga Nan sukai Shirin zuwa asibiti scanning din Hanifa da akeyi akai akai.
Koda suka Isa asibiti Dr sa'id na jiransu Dan Haka Basu wani Bata lokaci ba suka baro.
Driver ne yakaisu sbd Hanifa Isma'eel da Marshal sun hanata tuqi itama Naj din sbd Bata Gama warwarewaba hajjo tace itama Kar tayi tuqin.
Driver daga waje yayi parking daidai kofar shiga gidansu Naj din suka fito Kai tsaye suka shige gidansu Naj din kafin driver ya shige da motar can gida.

Tun a hanyar qarasawa cikin gidan suka hadu da Asmau zata fita ta qaraso tana cewa"

Anty Naj Ina wuni?gurinki fa zani yanzu,
Ta kalli Hanifa tana cewa"
Anty Hanifa Ina wuni?
Ya hajjo?

Lafiya kalau Asmau,ya karatu?Ina Umma habiba tana ciki?

Eh.

Wucewa Hanifa tayi Gama ta nufi sashen umma habiban suka gaisa kafin ta wuce sashen ummansu acan ta tadda Dadah zaune tsakar gida tana Shan radio da qatuwar sabuwar butarta a gefe sauraron Shirin hantsi.

Qarasowa tayi tana cewa"

Dadah hantsi akesha Bari nazo na tayaki Sha idan Zaki sanmun goronki.

Kallon Hanifan Dadah tayi tana washe Baki cikin farin cikin ganin cikinta daya fito tace"

Goro Kam Zan sanmiki kici Amma karki zauna Nan iska yayi yawa Zaki kwasa sanyi tafi gurin ummanku nasan dama can kikai gulmar na sanmiki goron ne yasa za'ai zaman Shan hantsi Dani.

Miqa Mata qaramin farin goro tayi tana cewa"

Allah ya nunamun NAJMA tazo tambayar goron Nan ranar nayi kwanan niyar azumin godiya ga Allah.

Najma dake qarasowa taji abinda Dadahn tace ta kame fuska matuqa rashin Jin dadin zancen da qyamarsa na bayyana fili a fuskarta tafasa zama gefen Dadahn ta gaidata kawai ta wuce dakin ummanta 
Dadah tabita da fadin"

Duk mugun halinki sai Naga 'yayanki da yardar Allah,
Mara godiyar Allah.

Daka tawa tayi ahankali ta waiwayo zatai magana gabaki daya ranta ba Dadi Anty Amina data fito daga dakinta ta riqo hannunta tana girgiza Mata alamar kada tafada koma menene tayi niyar fada.

Juyawa sukai suka nufa dakin ummansu dake zaune dakinta tana hada khumras masu shegen qamshi da kame jiki Kamar na _*YERWA INCENSE*_ tana jinsu takuma San da Amina Bata Hana Naj din mgn ba zata iya fadar abinda Dadah yau zata Hana uban kowa bacci a gidan sbd zaunarda Dattijo zatayi ta hada masu gurminda zai fatattaki kowa da bacin Rai.
Naj tareda Aminar ne suka shigo kafin Hanifa dake bayansu suka zauna Naj na cewa"

Umma barka da aiki,
Ina wuni?ya gidan?


Amsawa umman tayi batareda ta kalletaba sbd A qule take da ita akan wannan taurin Kan da muguwar zuciyar sbd Hanifa kawai ta kyaleta Dan batason tayi Mata fadan rashin son datake nunawa auren jalal a gaban Hanifa Dan kuwa tasan ko Dadah sbd Hanifan na gidan ta taqaita tata masifar.

Kusada umman Hanifa ta zauna tana daukar kwalban khumrah daya tana shinshinawa tace"

Umma wannan khumrahn wankane ko?
Eh Hanifa,Yaya jiki jikin?
Ankai Miki wainarki Kan lokaci kuwa?

Eh umma naci kafin mufita anjima alalan manja nakeso umma ko gobe da safe ruqayyat Basu iyaba idan sunyi qarfi yake.

Anjima Inshallah Zainab zata kawo Miki yanda kikesonta.

Yawwa Ngd ummana.

Ganin yanda umman fuskarta ba asakeba da alama ranta bace yake akan Naj hakama anty Amina ma Babu wani dogon magana ita kanta Naj din duk tayi wani iri ranta ba Dadi itama kowa sai kame kamen yaqen Dole yake Kuma duk tasan sbd itane ba'ason tada maganar Dan kada asa taji ba Dadi saidai ita Bata damu sosai da duk qin auren da Naj keyina sbd tasan Dole bazata iya karban aure irin wannan lokaci daya ba tunda har bata fitina ko fada akan auren ko ahakan ai ba laifi tasan wata Rana zata Aminta da auren.
Kallon umma da anty Amina tayi cikin nutsuwa da sanyin murya tace"

Umma kuyi hakuri ku sake bawa Naj lokaci Inshallah komai zai daidaita tunda na tabbatarda itama kasa amsar abin ne Kai tsaye yasa takejin bazata iyaba Amma ai komai lokaci yakeso.

Da kallon takaici umma tabi Naj din hakurinta na qarewa tace"

Kinji abin datake fada ko?
Fahimtarki takeso ayi abaki lokaci akan abinda kece aka rufawa asiri da kuwa da Bai aurekinba da yanzu kinanan kina zaman wulaqanci da matsuwa agidan wani,
Shine namiji shine yakeda damar cewa bayaso sbd shine me riqe auren Amma kece kike rainin wayon da kikaga dama sbd sun nuna suna sonki.

Dagowa Naj tayi da idanuwanta dasukai jajir suna neman cikowa da hawaye tace"

Umma.....

Katseta anty Amina tayi da cewa"

Naj bakida gskia ko kadan
Kuma wallahi kunya kike bani da wannan dabi'ar Taki sbd banyi tunanin ko Dan su hajjo ba ki nunawa wannan auren tsana haka,
Menene matsalarki?

Kukan baqin cikin datake dannewane tsawon lokaci ya kufce Mata tana cewa"

Wallahi bazan iyaba,
Nakasa,
Shin meyasa da aka tashi taimakon nawaba Amin taimakon da akasan Zan iya dauka,
Zuciyata zafi take,
Ciwo take,radadin hakan nakeji Dan Allah Araba wannan auren koba komai Ni bazan iya da Wanda yakeda wadda yakeso ba.....

Au bayan girman da kike ganin kinmasa yanzu Kuma hadda wadda yakeso tazama dalili kenan?

Sake fashewa tayi da wani kukan tana cewa"

Ni koma menene Dan Allah Araba auren Nan.....

Wani irin salatin Dadah sukaji data shigo tana kallon Najman bakinta na rawa gurin magana saikuma kawai ta fashe da kuka tana cewa"

Innalillahi-wainna ilaihirrajiun
Wace masifar ce zata kunno Kai rayuwarki Najma,
Wace tsanace kikewa wannan auren dako shekara daya baiyiba za'a kidawo zawarci,
Najma Dan Allah ki duba tsufana da mutuncin Dattijo ki hakura ki cirewa ranki masifa ki runguma aurenki....

Irin kukan da Najma da Dadah keyi yasa umman sake Shiga wata mummunar damuwa da baqin ciki ta tashi cikin tsananin fushi tayi Kan Naj din Hanifa da duk hankalinta itama ya tashi ta tashi da sauri ta janye Naj din tana kasa mgna sbd ganin cikin qanqanin lokaci Abu yazama tashin hankali.

Ba shiri Dadah tasa aka Kira Mata Dattijo tun kafin ya qaraso sashen yake jiyo fadan umma da ranta yayi mummunan baci qololuwa dakuma kukan dadah daya Gama daga hankalin kowa.

Anty Amina ce tayi Masa bayanin abin Dake faruwa tana dasa Aya ya kalli Naj cikin tsananin bacin Rai da baqin cikin daya rasa abin dazai Mata
Tana durqushe gefe har lokacin kuka takeyi me qarfi na rashin sanin mafitar abindayake cin ranta.

Kallon umma yayi cikin fushi da bacin Rai me tsanani yace"

Najma dai takai matakinda tafi qarfin umarnina Dan Haka ke dakika haifeta bakifi qarfin umarnin nawaba saiki shirya kayanki dan wallahi tallahi tana dawowa gidan Nan da sunan aurenta ya mutu bazata zaunaba tare zaku bar gidan nan.

Kallonsa umman tayi cikin baqin cikin koyaushe yayanta sukai laifi aurentane yake barazanar rawa,
Ta maida kallonta kan Najma tace"

Kinji ai saikije ki hado kayan naki mubi duniya tunda shine sakamakon dazaki bani.

Dadah cikin kula tace"

Najma Dan Allah ki dubi girman Allah kiyi hkr ki dangana wlh na zubarda makaman yaqina na yarda anmiki ba daidaiba ki dangana ki runguma aurenki wlh gaba Zakiyi farin ciki da yardar Allah.

Cikin fushi Dattijo yace"
Ki daina rarrashinta Dadah wlh ko ta tashi ta fice Kona nema mugun ice nai Mata dukan da bazata iya komawa da qafafuwantaba.
##MAMUH#


*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*


*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107

*_DM 33_*
Janyeta anty Amina da Hanifa sukayi ta suna sake bawa su dattijon da Umma hakuri Dadah kuwa kamata tayi tayi dakinta da ita ta zaunar tana kallonta tace"

Ki dauka dangana 'yar Nan kibi umarnin mahaifinki da mahaifiyarki tunda dai kinsan bazamu zabar Miki mugun abu ba,
Banda abinki Najma kinyi aurenki kina cikin kwanciyar hankali da nutsuwa meyafi hakan,
Dan shekarun da Kika basa waye yasani tunda idan aka kalleku ma sai adauka sa'an babban yayanki ne,
Shin menene illar auren qaninka tunda?
Shin kin manta Nana Khadija ko data aura Manzon Allah ya girmesa da shekarun dasukafi Wanda kikaiwa naki mijin ita datafi daraja ma ko farin ciki da wannan koyin bazakiyiba ki faranta Mana?
Mu idan bakya Yi danmu munada fada da takura to kiyi Dan hajjo da Alfa Mana,ga Hanifa Nan haryanxu Bata ganin laifinki tana bayanki sbd irin qaunar datake miki
Dan Allah kiyi hkr kiyi zamanki gidan aurenki tunda har daga mijin harsu hajjon sun amincew zamanki ba takura sai kinji kin samu nutsuwa da auren.

Haka Dadah ta ringa Bata rarrashi da maganganu sbd ganin fadan ba inda zai kaisu saiga tone tone har Azo abata goma biyar Bata gyaru Dan ita da wannan aure ya mutu gwara aje ahakan tana zaune gurin hajjo indai da auren yafi musu zasui jira har Allah yasa auren yazama Kamar kowanne auren.

A dakin Dadah tayi zamanta saidata nutsu kafin Dadahn da kanta ta rakasu har palon hajjo suka Kuma taruwa suka rarrasheta kafin Dadah ta tafi 
Har dare hajjo da hanifa na tarairayarta Dan tasake Haka suka Kwana 
Ko Dad Alfa da kansa Saida yakirata suka sake zama da hajjo suka ringa rarrashinta cikin kulawa hartazo tanajin kunyar abin qarshe Dole ta sake Dan ganin yanda duk suketa sake lallabata shiyasa ta sake sosai ta koma bakin aikinta,

Hannah da mum Malika Koda sukaji abindaya faru Dadi Kamar me musamman suka sake maida himma gurin ganin auren Hannah da MARSHAL din ya tabbata,
Duk yanda Hannah taso fadawa marshal din rigimar Bata samu damaba sbd baida lokacinta busy yake sosai gashi yanata tafiye tafiye acan din Dole ta hakura harta samu lokacinda zata fada Masa.

Umma da Dattijo Basu duk da zancen yayi kwanaki sosai Basu daina fushi da itaba sama sama suke amsa gaisuwarta idan tashigo gidan Dadah ce dai take lallabata dataga fushin ba yayi sai anty Amina daketa aikin dawainiya da duk abinda Hanifa keso sbd cikinta daya fito sosai yanzu.

Takoma aikinta gadan gadan sai yamma take dawowa musamman da ayyuka sukai Mata yawa na 'yar rigimar da ake wadda ta tarar Marshal ya fige Abbas daga ALFAs Amma sauran shareholders din Basu yardaba shikuma sbd yafi kowa hannun jari aciki yace hukuncinsa kenan.
Rigimar tasa ayyuka sun Mata yawa sbd dukkanin ayyukan office din president na companyn yadawo office dinta tunda Abbas an dakatar dashi say angama rikicin gashi Marshal din yatafiyarsa saiya dawo Kuma.

Da mamakin wannan qarfin halin nasa take aikin office din kullum sbd ayyukan sun Mata yawa ko yawon meetings yasa har wata Yar rama ta taso mata.
Saidatai wata daya da sati biyu tana fama da ayyuka kafin ayyukan suka Dan daidaita tafara samun kanta har tana dawowa gida da wuri.

Yau tunda tazo office din batai komaiba sbd jiri datake gani tun jiyan tafara jinsa yanayi Yana tafiya.

Dafe kanta tayi tana Dan rufe ido ta bude ahankali ta dago tana kallon Sarah data shigo office din ta bude Baki ahankali tace"

Sarah please bani ruwa me sanyi nasha.

Kallonta Sarah tayi da mamaki tace"

Me sanyi ko me Dan sanyi kadan?

Batareda ta dagoba tace"

Me sanyi sosai.

Da mamakin Sarah takuma kallonta sanin Bata Shan ruwan sanyi zatai mgn saikuma ta fasa ta nufa fridge ta bude ta dauko Mata ruwan roba masu sanyi sosai ta kawo Mata ta miqa Mata.

Karba tayi ta bude Kai tsaye takai bakinta tana Sha Sarah na kallonta da mamaki.

Ajiyar zuciya kadan ta sauke bayan tagama sha ta ajiye sauran ruwan tana cewa"

Sarah zanje gida yanzu kaina na ciwo Ina buqatan hutawa ko zai sake.

Tare suka fito da Sarah din itace take tuqin takaita gida suka nufa cikin gidan tare.

A Palo suka tararda Hanifa zaune tareda anty Amina data kawo Mata sabuwar Awarar da Umma ta Aiko Mata wadda akaiwa sauce din kayan miya dasu carrots da kwai.

Kallo daya Naj tayiwa Awarar taji tana son ci abinda Bata taba yiba shine ko dakinta Bata shigaba ta qaraso gefen Hanifan ta zauna ahankali tana cewa"

Yunwa nakeji sosai har kaina Yana ciwo.
Ta dauka plate tana miqawa Hanifan tana cewa"

Samun zanci.

Zuba Mata Hanifa tayi tana cewa"

Lallai yau 'yar gaban goshin hajjo yunwa takeji tunda ko daki bazaki iya qarasawaba.

Batace kalaba saidataci Awarar a bakinta taji kanta dake sarawa ya daina ta dago ta kalli Hanifan ahankali tace"

Thanks.

Sai alokacin ta kalla anty Amina tana cigaba daci suna gaisawa anty Amina na kallonta dakyau cikin nazari tace"

Naj bakida lafiyane Naga kamar kin fada.

Kallonta Hanifa tayi tana cewa"

Ramar aikice Amma duk da hakan Ni Banga ramarba haske dai Naga tayi sosai kodai bakida jini ne Naj?" Taqarasa fada tana Dan zare ido.

Batareda ta dagoba tace"

Lafiyata kalau stress ne kawai amma zanshiga hutu sbd komai yakoma yanda yake a office din Inshallah.

Saidata qoshi kafin ta qarasa dakinta tabarsu a palon ta tube ta shiga toilet wanka.
Sai datai wankan taji jikinta ya sake sosai ta fito daureda towel ta nufa jikin mirror kenan taji wayarta na ringing ta juyo ta nufa wayar dake Kan gado ta dauka sai kawai taga No din qasar waje destination id dinta ya nuna Mata United States of America.

Kai tsaye ta dauka batareda ta tsaye tantance kiranba Wanda yake Vidcall sai ganin mutum tayi ya bayyana kan screen din wayarta Yana zaune cikin lafiyayyan palonsa sanyeda uniform dinsa na sojojin America dasukai Masa wani irin kyau uwa uba hutu da nutsuwar daya samu ta bayyana ataredashi Ya zuba Mata fararen idanuwansa har zuwa kirjinta dake daureda towel Tsananin hasken data qara yasashi sake zuba Mata idanuwansa,
wannan ne Karo na farko data gansa cikin uniform ta dauke kainta ganin irin kallon dayake Mata sai alokacin ta tuna da towel ne jikinta ta kashe wayar tana jefarwa Kan gado ta tafi tahau shirinta.

Baccin maraice yayi sai magriba ta tashi ta fito bayan tayi sallar magriba sbd yunwa me tsanani datake ji.
Kicin ta nufa sbd sanin lokacin cin abincin Daren baiyiba tasan Hanifa na kicin sbd Bata jimawa bataci ba shiyasa take zuwa kicin taci ta koshi Kuma ahau dining aci da ita.

Tana Shiga kicin din ba kowa sai ruqayyat dake qarasa aikin abincin Daren ta nufa fridge ta bude ta dauko milk drink tasha sosai ta dauko cake guda hudu ta cinye ta qara da apple biyu kafin taji ta dan samu nutsuwa ta fito suna hadewa da Hanifa dazata Shiga kicin din neman abinda zataci itama tace"

Naj yunwa nakeji cake zanci da Madara tunda kin cunyemun awarar da Umma takawo min dazu.

Batace komaiba Takoma Palo ta zauna tana duba wayarta tana jiran agama abincin akawo dining.

Sallar ishai taje tayi tana fitowa hajjo na fitowa suka dunguma dining Hanifa tuni ta riga kowa Isa.

Naj din ita tazubawa hajjo abinci takawo Mata ruwa da komai ta kalli Hanifa da Bata harta zuba abincinta tafara kaiwa Baki.

Zama tayi itama tareda zubawa ta zauna suna binta da ido ta dago ta kallesu ganin irin kallon dasukewa abincinta yasata kallon abincin sai alokacin taga ta zuba da yawa ba kamar yanda ta Saba ba dama kwanakin gabaki daya cin abincinta ya sauya ta Dan fuske tana cewa"

Yunwa nakeji sosai duk yau banci wani abincin kirkiba.
##MAMUH#

*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107

*_DM 34_*
Hajjo kallon abincin takuma Yi kafin ta kalli Naj din cikin kulawa da nutsuwa tace"

Najma ki daina zama da yunwa Haka sbd zata iya Miki illa yanzu wannan abincin zai iya qulle Miki ciki,Kisha tea kafin ki ci abincin cikinki ya sake tukuna.
Kallon Hanifa tayi tana cewa"

Miqa Mata tea din ta zuba ta Sha.

Qaramin flask din dake cikeda black tea dinda yaji kayan qamshi da hadinsu lemon da Zuma wanda koyaushe dashi ake jere abincin safe Rana da dare Wanda qaidar hajjo ne wadda ta Saba da Shansa Kuma al'ada da dabi'ar Shan nasa ya Kama duk Wanda yake gidan ko baqi akai idan za'a kawo musu ruwa sai an tambayesa ko akawo Masa tea din.

Miqawa Naj Hanifa tayi tana cewa"

Kin riga kinfara cin abincin kinsha tea din daga baya" ta aje tana daukan spoon tafara cin nata abincin.

Kamar yanda tasaba cin abinci a natse ta cinye abincin tas tasha ruwa kadan ta zuba tea din Wanda kurba daya Tai Masa ta ajiye tana cewa Alhmdlh ahankali.

Kallonta hajjo tayi tana sake cewa"

Idan Zaki ringa zama da yunwa irin Haka Zaki sa ciwofa ya kamaki karki sake hakan daga yau.

Guntun murmushi tasaki ahankali tana kallon Hanifa da har lokacin abincin takeci tace"

Yaune kawai hakan bazai Kara faruwa Inshallah hajjo.

Barin gurin tayi ahankali tanajin nutsuwarta ta dawo ta dawo palo ta zauna sai alokacin ta dauka wayarta tana dubawa har Hanifa da hajjon suka Gama suka baro dining din hajjo tayi dakinta sbd qafafunta da ruqayyat zata gasa Mata da ruwan dumi.
Hanifa Kuma gefenta ta zauna tana daukan tata wayar itama tace"

Naj gobe umma zata faramun sabon gyara Isma'eel zai dawo next week fa.

Juyowa Naj din tayi ta kalleta tana sake maida hankali kan abinda take dubawa a wayar tace"

Shine kike Zillo Haka?
Cemasa zanyi yayi zamansa sai zaki haihu yadawo muga qarshen gyaran.

Dariya Hanifan tasake tana cewa"

Zillo ma ai kadan ne zille zille zanyi ma idan ya dawo tunda bansan kalar zille zillen da matan duniya ke can suna Masa ba tunda bana kusa Dana Haka idan yazo nawa lokacin ne nayi haukama idan Zan iya,
Hannah kina ganin duk ranarda tasamu auren Marshal wannan rawar kan datake ai uwar ubansa zamu gani akan wannan datakeyi Yan.......

Hade sauran maganar tayi tana rufe bakinta Jin Naj din tayi shiru sbd gabaki daya ta manta da Naj take maganar,ta Dan kalli fuskar Naj din data juyo itama ta kalleta tareda sake wani irin guntun murmushi tana basarwa da cewa"

Ashe kinada qarfin yiwa miji zille zillen Kike makure Mana fuska ki nade muna dawainiya da matarsa.

Haba sirikita idan bakiyi hidima daniba waye zaiyi....

Dan kame fuska Naj din tayi Hanifan tasaki dariya tana cewa"

Sorry my Naj.

Wayar Hanifan ce tayi ringing ta waiwayo tana kallon wayar ta maida kallonta kan Naj da kallo daya tayiwa wayar taga sunan me Kira ta dauke tana maida hankali akan tata wayar.

Dauka Hanifa tayi cikin murmushin ganin video call ne ta dauka Kai tsaye tana cewa"

Hey Deen Marshal,ya kake?

Kallonta yayi Yana Dan gyara crossing qafafunsa da yayi wayar na ajiye saiti dashi a gabansa Yana zaune acikin office dinsa sbd sun safiyace har hantsi ma yafara,
Ya bude Baki ahankali yace"

Lafiya kalau,ya baby?
Kinje scanning din kuwa?
Nayi mgna da Dr sa'id,ki turamun scanning din I want to see it.

Ok,ok,Baby is fine,and iam fine also" satar kallon Naj tayi tana cewa"

And Naj ma tana Lafiya.

Jingina yayi baya Yana folding hannuwansa fararen idanuwansa akan wayar cikin muryarsa data Gama Isa cikin kunnuwanta yace"

Bata wayan.

Kallonsa Hanifa tayi tana Dan kame fuska da murmushi akan fuskarta tace"

JALAL karka damu qawata da wannan kamewan naka,
Wani irin kallo yayi Maya Wanda yasata harararsa tana cewa"

Kome ka zama karka manta dai Ni yayarkace.

Dan rufe idanuwansa yayi ya bude da wata muryar yace"

Matan auren dake gefenki Zaki bawa wayar.

Naj dake zaune duk takasa ma qarasa abinda take a waya sbd zancen a bayyane yake fita ta miqe zata bar gurin lokacinda Hanifa ke kokarin miqa Mata wayar Kai tsaye taji muryarsa ba Wasa aciki yace"

Kika bar gurin Zakiyi mamakin hukuncin hakan.

Dakatawa tayi tareda waiwayowa ta kallesa ta cikin wayar zatai magana saita kasa ta fuske tana kokarin wucewa tabar Hanifa ta riqota tareda maidata zaune tana cewa"

Dawo ki zauna Bari Ni natashi kicin zanima.

Miqewa tayi tabar gurin bayan ta aje wayar saiti da Naj din.

Dauke Kai Naj din tayi tana cigaba da duba wayarta tanajin idanuwansa na yawo akanta duk sai hakan yasata kasa nutsuwa ta dago ahankali fuskarta a hade suka hada idanuwa ta dauke Kai kafin tayi wani motsi a natse yace"

You look sexy in that dress.

Da wani irin yanayi na kunya da takaicin kayan dake jikin nata ta motsa zata kashe wayar yasakar Mata wani kallon daya sata hadiye wani yawun dake neman sarqeta yace"

Ok goodnight jeki kwanta.

Kashe wayar yayi sai alokacin ta sake daure fuska tana dauke idanuwanta daga gefen wayar tana kallon kayan jikinta da gaban rigar take a Dan bude Ana hango tsakiyar kirjinta da condom bra Dinta ta rabasu ta miqe tabar gurin ta nufa dakinta.
Tana shiga tubewa tayi Bata sake wankaba sbd Dan sanyi datakeji ta saka kayan bacci tayi kwanciyarta take bacci ya dauketa.

Washe gari sallar asuba kawai ta Gama ta fito taje kitchen Tasha tea me zafi tana lumshe ido sbd rashin shansa a Daren jiyan yasa takejin yunwa Kamar hakan.

Da cake Tasha tea din ruqayyat data fara ayyukanta tana binta da satar kallo sbd sanin gabaki daya Naj din batada ciye ciyen abinci qaidarta taci lokacin cin abinci tagama takuma shikenan.
Har tagama tafito Hanifa Bata zoba Dan Haka Takoma daki ta kwanta wani sabon baccin me nauyi yakuma dauketa.


Sai qarfe goma da mintuna ta farka tana kallon agogo ta saki wani qaramin numfashi tana dafe Kai sbd ganin irin lattin datai Wanda Bata Saba lattin ba irin Haka.
Zuro qafafunta tayi ta sauko gadon tana nufar toilet Kai tsaye tayo wanka ta fito.

Babu Bata lokaci ta shirya cikin doguwar jallabiya Maroon da qaramin mayafin data nade kanta dashi Wanda kalar abayar ta fitarda tsananin hasken data qara ta fito qamshin khumrah kadan Yana Dan tashi a jikinta..

Kai tsaye gurin hajjo dake zaune palon ta qarasa ta zauna gefenta cikin kulawa tace"

Good morning hajjo, muntashi lafiya?

Kallonta hajjo tayi cikin kulawa tana cewa"

Lfy kalau,yau kinyi lattine?

Eh,zanci abinci na wuce.

Dining ta nufa ta zauna tareda Kiran ruqayyat takawo Mata ruwan sanyi tafara cin abincin kenan saiga Zainab din Anty Amina tashigo da sallama ruqayyat data bude Mata kofar palon tana biyeda ita zuwa dining din.

Anty Naj Ina kwana?

Lafiya kalau zainab yasu umma da anty Amina suka tashi da Dadah?

Lafiya kalau,ga wainar Anty Hanifa Nan Zan koma aikin su daughnuts mukeyi da ummana da aka kawo Mata na wani bikin idan Anty Hanifa ta fito Ina Mata Ina kwana.

Juyawa tayi ta qarasa gurin hajjo tana gaidata har hajjon na Bata sako gurin umma kafin ta wuce.

Qamshin wainar ya ringa Shiga hancinta Amma dayake Sam waina Bata dametaba saita dauke Kai tana daukan hakan amatsayin rashin damuwa da bataiba da waina
Amma qamshin sai sake Shiga hancinta yakeyi Yana sata Jin wani iri ba shiri ta miqe tabar gurin tana goge bakinta da yawunta keyi Kamar zasu tsinke Dan Haka Kai tsaye handbag dinta ta dauka tana cewa"

Hajjo na tafi office saina dawo.

Ok ki kula,saikin dawo.

Sai data Shiga motarta ta sauke wata irin Ajiyar zuciya tana sauke numfashi ahankali.

Sai data samu nutsuwa kafin ta tayarda motar ta fice daga gidan ta nufi office.

Isarta office taji abinda take no yakuma taso Mata da qyar ta daure ta iya kaiwa office dinta tana Shiga ta nufa toilet da sauri wani irin amai me qarfi da wahala na kufce Mata.

Da sauri Sarah tabiyo bayanta ganin irin yunqurin Aman datake me wuya da qarfi.

Daqyar Aman ya tsaya ta wanke fuskarta tareda dagowa ahankali tana miqewa dukkanin Rabin qarfinta ya tafi ta kalli Sarah tana cewa"

Bani ruwan sanyi zansha.

Cikin kulawa da damuwa Sarah tace"

Naj kinci wani Abu ne?
Ko Zan Kira Dr sa'id ne yazo ya dubaki idan bakyajin Dadi.

Girgiza Mata Kai Naj din tayi tana fitowa toilet ta zauna a kujera tana karban ruwan sanyin ta bude Tasha ahankali tana ajewa tace"

Basai kinkira Dr sa'id ba inaga naci abinci da yawane kawai zanji sauki yanzu tunda na same na rage kawai dai karki Bari a dameni banajin Dadi Kuma.
Lumshe idanuwa tayi tana dafe kanta dake Dan juyawa sbd Aman, Sarah ta fice tana sake Mata sannu.

Wunin kasa gane kanta tayi gabaki daya a office din Haka dai ta tattara Takoma gida wani Dan zazzabi na damunta.
Ko a gidan data Isa abinci kawai tasamu taci ta kwanta saikuma taji daughnuts din dazu da Zainab tafada Mata takeson ci Dan Haka ta daga wayarta takira anty Amina tace"

Anty Amina kibawa zainab daughnuts takawomin nakasa cin abinci cikina ya qulle.

Kash wlh wainda akaiwa harsun Aiko an karba duka saidai ko samosa akwai sauranta Bari akawo Miki.

No ki barshi banasonta zanci cake kawai.

Tana kashe wayar taji zazzabinta na neman qaruwa Haka dai ta lallaba har dare shima tanacin abincin dare ta kwanta gabaki daya Aman ya sakar Mata da mutuwar jiki da guntun zazzabi.

Ko washe gari wani sabon uban latti ta buga dayasa fita ko abinci bataciba 
Sai data Isa office Tasha milk drink aikuwa tana gamasha Amai ya biyo bayansa Wanda yafi na jiya take hankalin Sarah ya tashi ta zubawa Naj din data Gama galabaita tana cewa"

Naj please kibari nakira Dr sa'id.

No tattara min kayana gida zankoma jiri nake gani.

Tsayawa Sarah tayi tana kallonta cikin tsananin shakkun tunanin daya shigeta da mamaki me tsananin qarfi tareda kasa gasgata tambayar dazatayin tace"

Naj are you pregnant?

Wani kallon mamaki da takaici tayiwa Sarah din duk da tana Dan jin jiri ta yamutsa fuska a hade tace"

Are you stupid?
Ta Yaya zakimun wannan tambayar inada Wanda zaimun cikine?
Sarah please karki karamun ciwon Kai just leave,kije ki dauki key din motar muje ki kaini bazan iya tuqin ba.
##MAMUH#


*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*


*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107

*_DM 35_*


Albishirinku mata💃shin Ina ma'abota ado da kwalliya🗣️Ina team no makeup🗣️Mata gareku inamai tabbatar muku dacewa duk wnd takeneman kayan gyaranjiki walau matsalan fata kike fama dashi kamarsu pimples, tabo, sunburn,nankarwa, knuckle ko Mai Kika shafa yabatamiki jiki Dama sauransu walau Kuma kawai kinasan kigyara fatarki kizamto tauraruwa abarso abar marari agurin kowa😍Mata inamai tabbatar muku dacewa kujaraba kayan mg's skincare Koda gudane dg cikin kayansu kuga abun mamaki🧚🏻‍♀️ domin kayansu kankat ne Koda iya sabulunsu Kika Dana saikinfita zarra cikin Mata domin ynd fatarki zaikoma Shar kamar Madara kidinga kyalli kina haskakawa duk inda kikayi se ankalleki😘Kuma wani abun jindadin ma shine duka kayansu organic ne  Babu na bleaching kawai zaigyaramiki jikine yafiddomiki d ainihin natural beauty dinki inma NASA haske kikasiya natural ne kawai bn bleaching b💁‍♀️mekike jira hjy maza garzayo kinemi naki acikin farashi merahusa kigyara jiki kiyi fes abinki baruwanki da sekinyi kwalliya inzaki fita😃kifita aganki da zallar kyawunki hjy😍kanawa mutanenmu ina godiya Kuna nunama mg's one luv tnx for ur patronage dama Yan sauran state mg's na godiya may your pocket never lck azo asiya Kaya hilis karnakoma kauyenmu🥺Yar shawarmannan karta gagareni🤧😂
Henajiku lvs🤭
Meso should chat
08062991549
07046881166
Call 08064532391
Soap:3k, beauty kit:11k,bridal kit 18k
Instagram:glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare

Team glow✅

Masu buqatan makeup ma duk mgs skincare suna kulawa da wannan ko a makeup studio dinsu kokuma a gidanka.
08062991549



************
Sarah binta tayi da ido tana sake qure kallonta akanta Dan kuwa duk da ita ba likita bace Amma ta taba aure harma da bari na ciki harso biyu kafin suka rabu da mijin Dan Haka tana iya ganewa ko hasashen ciki ajikin mace Amma Kuma Kamar yanda Naj din tafara batada Wanda zai Mata ciki bayan mijinta Dan kuwa tare sukai karatu da Naj qawartace ita din cikakkiyar sheda daga Nan har koina zata iya bayarwa akan nutsuwa da kamun Kai irin na Naj din to Kuma Marshal Wanda yake matsayin mijinta kowa ya iya yanda ya tabbata Babu ko gaisuwa a tsakaninsu bare su Aminta da zamansu ma'aurata a taqaice dai Babu ma wani maganar ciki da zai yiyu ajikin Naj din itama din tayi banzan tunani data Yi tunanin hakan harta fada din.

Kallon Naj din tasake Yi cikin kokarin kawar da dukkanin alamun da idanuwanta da zuciyarta ke nuna Mata a natse cikin kulawa tace"

Sorry Naj,Nima bansan tunanin daya shigeniba nace hakan kawai dai ganin yanda kike yawan Amai a kwanakin Nan ne dakuma wannan jirin dashima yake yawan kamaki,duk da hakan please Naj ki daure kiga Dr sa'id sbd Kar wani ciwon ne yake damunki yazo yayi qarfi.

Ahankali ta girgizawa Sarah din Kai suna fitowa daga office din tace"

I will be fine Inshallah,nafi tunanin ko stress ne yamun yawa so daga yau zanshiga hutu na huta sosai idan Naga Bai daina bane Inshallah Zan sanarwa Dr sa'id kokuma zanje asibitin sbd karna kirasa yazo su hajjo hankalinta ya tashi ta dauka wani babban ciwon ne.

Mota suka Isa ahankali ta bude gaba ta zauna ita Kuma Sarah ta shiga gurin driver ta zauna tareda Dan sake kallon Naj din data jinginar da Kai a rufe idanuwanta sbd baccin datakeji Yana cika idanuwanta ta sauke numfashi tana sake Kore tunanin tsananin hasken da fatar Naj din taqara zuwa kirjinta da Kamar sun Dan qara cikowa,tayi saurin girgiza Kai tana Kore tunanin abinda itama tasan bazai yiyunba wato ciki ajikin Naj bayan kowa yasan ko Gama daidaituwa auren baiyiba bare har asamu kebewa babba irin wannan dazatasa ciki a yanda Naj Babu ko alamar auren acikin kanta Dan Haka gskia ba ciki bane kawai sauyin yanayi ne.Tayarda motar tayi ahankali ta ja suka bar ALFAs.

Suna cikin tafiyar ta bude idonuwanta dake cikeda bacci ta kalli Sarah din tace"

Mu biya Bakery zansiya daughnuts idan na Isa gida Zansha da tea cake Yana dannemun zuciya idan naci yanzu kamar kwanan Nan ruqayyat idan zasuyi cake din suna cika butter ne ko kwai¿Nadai gaji dashi Zan gwada Sha da daughn din.

Ok,kokuma kisa suyi Miki ko Anty Amina tai Miki sponge cake shi bazai Miki nauyiba.

No daughnuts din nakeso dai yanzu.

Biyawa sukai wani babban bakery Basu shigaba suka nada ordarsu daga cikin Motar aka kawo musu doughnuts din cikin qaramin farin kwali me dauke da sunan gurin suka wuce.

Suna Isa gida Sarah daga harabar gidan ta juya Ta fito ta hau taxi Takoma office Naj dince kawai tashigo cikin sa'a kuwa tana shiga Dad Alfa na fitowa daga sashen hajjon ta qaraso gabansa ta gaishesa cikin girmamawa yana amsawa tareda tambayarta wasu ayyukan yace idan tasamu lokaci zasuyi mgn akan Marshal daya tsaya akan zai Saida shares dinsa a companyn matuqar Abaas yadawo.

Tana sane da wannan rigimar Dake kwance a ALFAs Dan kuwa Marshal din na janyewa Babu wani sauran nauyi sosai a ALFAs din Dan kuwa kusan Rabin uwar dukiyar tasace aciki saita mahaifiyarsu wadda kasonsane shida Hanifa sai sauran ta Dad Alfa da wasu abokanan kasuwancinsa su uku.

Ok tom Inshallah" kawai tacewa Dad din,Yana wucewa itama qarasa ciki.

A palon ta tadda Hanifa harma da hajjo data kalleta ganin lokacinda ta dawo cikin kulawa ta dago daga karatun datake a wani littafi _The sacred path to islam_ cikin kulawa tace"

Harkin dawo ne?
Lafiyanki dai ko?
Naga idanuwanki Kamar bakyajin Dadi,qaraso zoki zauna Nan.

Kusa da ita ta nuna mata tana kallon yanayinta da duk ita ya sauya Mata a ido Nan tasake tabbatarda ba lallai lafiyar Naj din kalau ba.

Kallon Hanifa hajjo tayi tace"

Kira mun Dr sa'id.

Zama Naj tayi tana hanawa da cewan"

Hajjo lafiyata kalau wlh kawai dai rashin hutune yake damuna na wahalar aiki Amma Inshallah Zan huta kwana biyu saina ji duk wata gajiya ta sakeni Dan Haka ba buqatan Kiran Dr sa'id.

Aje qaramin kwalin hannunta tayi tana budewa tareda kallon Hanifa tana cewa"

Maman baby ga doughnut me chocolate nasan baby nason ci.

Kallon daughnuts din Hanifa tayi tana  murmushi tace"

Baby batacin me chocolate saidai next time kila yanzu nagama cin fatan wake da doya da Umma ta aikomun.

Kallonta Naj tayi tana miqewa taje kicin tafara wanke hannuwanta da kyau tadawo ta zauna tana faracin daughnuts din dasukai Mata Dadi sosai.
Guda biyar ta cinye tabar biyar dan guda goma be Tasha orange juice da ruqayyat takawo Mata me sanyi har hajjo na maganar yaushe tafara shan sanyi Haka tace"

Zan daina hajjo Nima bason sanyin nakeba Sarah ce tafara koyan Sha sanyin Nan inaga a office.

Miqewa tayi ta nufi daki tana cewa"

Bari naje nayi sallar azahar nayi bacci ko kaina zai sake.

Tana Shiga daki handbag dinta tafara ajewa kafin ta nufa toilet Kai tsaye tashige tayi alwala da komaima ta fito ta dauki hijab ta saka ta tayarda sallah.
Tana idarwa hijab din kawai ta zare ta Haye gado wani irin bacci me Dadi ya dauketa take.

Bacci Sosai tayi sai yamma ta farka bayan zirga zirgar da hanifa tayita yi a dakin na zuwa dubata ganin baccin yaqi qarewa Dole ta tadata lokacin har qarfe biyar ta Dan gota cikin mamaki Hanifa tace"

Naj da gskiar hajjo fa Anya lafiyarki kalau kuwa?
Wannan baccin me lafiya bazaiyisa ba saidai me ciwo gskia.

Saukowa gado tayi ta nufa toilet bayan ta duba agogo ta shige tana Dan dafe kanta dake sarawar baccin Bai Gama isartaba.
Alwala tayo tafito har lokacin Hanifa na dakin tana zaune kan sofa tana waya mijinta.
Qarasowa tayi ta dauko hijab ta inda zata tayarda sallar ta tayar har lokacin Hanifa na waya.

Ko data idar kicin tafara zuwa ta debo abinci a plate tareda ruwan sanyi na roba a hannunta tadawo dakin ta zauna lokacin Hanifa ta Gama wayar tafaracin abincin ahankali tana cewa"

Yau bakije gyaran bane gurin umma?

Naje dazu kina bacci Amma zankoma yanzuma da yamman Nan gamaci muje Dan Nima Ina buqatan kiyi gyaran Nan tunda kema Amarya ce duk da haryanxu dai Baki zama cikakkiya macen aure ba." Taqarasa maganar tana Yar dariya.

Qin kallonta Naj din tayi taci gaba da cin abincinta Dan sanin neman maganarta kawai Hanifan keyi Wanda ko tankawama bazataiba Dan ba zancen tankawar bane.

Tana gamawa wanka tayi ta Sanya jallabiya kawai suka nufi gidansu bayan sun sanarwa da hajjo dake dayar palon da baqi datai.

Tunda suka shigo gidan Dadah dake zaune tsakar gida ta zubawa Naj din ido tana cewa"

Masha Allah,
Wannan Ya Allah yaqara tsare Mana ita daga Baki da ido Tubarkalla Masha Allah,
Gatanan sai qara santalewa takeyi Kamar abiya kudi a taba wannan aure da ace lafiya lafiya ake da ita akan auren Kuma da ace ta tare agurin mijin ne da Babu abinda zai Hana tace cikine a jikinta Amma Ina wannan magana datake Kamar babban sa6o me zunubi agurin Najma zata fadu ko kwatantuwa Dan Haka sbd ma karsu Bata da maraicen ta tsuke bakinta ko fatarta Bata fitarba a fili ta hadiye abarta ta kallesu tana amsa gaisuwar Hanifa data wuce gaba zuwa gurin uwarta Naj kuwa gefen Dadahn ta zauna Tama cewa"

Dadahn wannan kallon badai wani laifin nawa za'a tadoba?

Wata qaramar dariyar tsofi Dadah tayi tana dauke idonta daga kan Naj din zuwa Kan Amina dake zaune tana hada odar snacks din wasu dasuka kawo dazu da Rana tace"

Yayarki nake kallo Ina kallon santaleliyar budurwarta zainab gatanan Allah yabata sai fatar ganin aurenta bada jimawaba zaku samu siriki Amma ke Banga alamar zanga naki 'yayanba.

Kallon dadar tayi fuskarta n sauyawa ta kame fuska tana dauke Kai tareda share zancen ta hanyar miqewa tana cewa"
Bari na qarasa gurin umma na gaisheta.

Bayanta Dadah tabi da muguwar harara tana cewa"

Wannan Yar baqin cikin Allah ya tausasa zuciyarta tasamu tabawa auren Nan dama itama tasamu nata 'yayan kanta,
Tausayinta nakeji Amma Sam ita ba tausayin kanta a zuciyarta Dan kuwa bansa ran zata sauko Nan kusa bare muji alkhairi.

Gurin umma ta qarasa ta gaidata tana zama gefen Anty Amina tana cewa"

Anty Amina yauma Zakiyi snacks din kenan?
Idan kinyi ki ciremin daughnuts please.

Kallonta Hanifa tayi kafin Anty Amina tabata amsa tace"

Duk me Zakiyi da daughnuts bayan ga Wanda Kika siyo can ma Baki cinyeba?
Wancan din baiyi Dadi bane Hala?
Dama kayan kasuwa Basu cika dadin Kamar na gidaba.

Wancan din su ruqayyat su cinye na anty Amina yafi Dadi Zan karba din.

Sai dare suka baro gidan bayan sunci ruwan semo da miyar zogale me Dadi sosai ba Anty Amina ba ko umma sai datai mamakin abincin da Naj taci kafin suka fito suka nufi gida.
Suna Shiga Kai tsaye daki ta wuce bayan ta Dan tsaya zance da hajjo a dakinta tayi wanka ta sauya Kaya sai alokacin taji sakat ta fada gado sai bacci.
##MAMUH#

*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107

*_DM 36_*


Albishirinku mata💃shin Ina ma'abota ado da kwalliya🗣️Ina team no makeup🗣️Mata gareku inamai tabbatar muku dacewa duk wnd takeneman kayan gyaranjiki walau matsalan fata kike fama dashi kamarsu pimples, tabo, sunburn,nankarwa, knuckle ko Mai Kika shafa yabatamiki jiki Dama sauransu walau Kuma kawai kinasan kigyara fatarki kizamto tauraruwa abarso abar marari agurin kowa😍Mata inamai tabbatar muku dacewa kujaraba kayan mg's skincare Koda gudane dg cikin kayansu kuga abun mamaki🧚🏻‍♀️ domin kayansu kankat ne Koda iya sabulunsu Kika Dana saikinfita zarra cikin Mata domin ynd fatarki zaikoma Shar kamar Madara kidinga kyalli kina haskakawa duk inda kikayi se ankalleki😘Kuma wani abun jindadin ma shine duka kayansu organic ne  Babu na bleaching kawai zaigyaramiki jikine yafiddomiki d ainihin natural beauty dinki inma NASA haske kikasiya natural ne kawai bn bleaching b💁‍♀️mekike jira hjy maza garzayo kinemi naki acikin farashi merahusa kigyara jiki kiyi fes abinki baruwanki da sekinyi kwalliya inzaki fita😃kifita aganki da zallar kyawunki hjy😍kanawa mutanenmu ina godiya Kuna nunama mg's one luv tnx for ur patronage dama Yan sauran state mg's na godiya may your pocket never lck azo asiya Kaya hilis karnakoma kauyenmu🥺Yar shawarmannan karta gagareni🤧😂
Henajiku lvs🤭
Meso should chat
08062991549
07046881166
Call 08064532391
Soap:3k, beauty kit:11k,bridal kit 18k
Instagram:glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare

Team glow✅




***************
Washe gari ki data farka da jiri ta tashi sai Bata damu sosaiba tasan warwarewar da Bata Gama Yi bane Dan Haka breakfast kawai tayi taredasu hajjo Takoma daki tayi kwanciyarta Hanifa kuma tayi gurin umma.

Sai Rana ta farko shima ko yau din hanifa ce ta tadata sbd lokacin sallah daya wuce sosai bayan ta idar Koda Hanifa ke sake tambayarta lafiyarta kalau itama zuwa yanzu tafara jin kamar ba lafiyaba Dan Kamar tanajin komai nata batajinsa daidai ta dago ta kalli Hanifan dake jiran amsarta tasaki wani qaramin numfashi tareda murmushi sbd kada tasa sufara Kiran sunan Dr sa'id hajjo tabi ta damu tace"

Lafiyata kalau dama bana fada Muku zanyi hutuneba kwana biyu shine naketa kokarin ganin nasamu hutun yanda ya kamata,Yaya harkin dawo daga gidan.¿

Ajiyar zuciya Hanifa ta sauke tana cewa"

Nadawo Amma please Naj idan dai kinji akwai abinda yake damunki ki fadamun sbd Kar abin yayi qarfi ok??

Gyada Mata Kai tayi tana kallonta cikin kulawa tace"
Yes madam.

Daughnuts din da anty Amina tabata tazo Mata dashi ta miqa Mata tana cewa"

Ganshinan Bari naje nayi sallar nima.

Karba tayi tana budewa qamshinsa na shigar Mata hanci ta lumshe fararen idanuwanta ahankali tana daukan daya tareda kaiwa bakinta tana fara Ci.

Sai dataci sosai kafin ta fito da sauran ta miqawa ruqayyat a kicin ta aje Kai tsaye ta nufa dakin Hanifa acan suka zauna Yar fira datakeson ta wartsake sbd Dan zazzabin yamma datake ji.

Da daddare suna zaune suna fira a dakin Naj din Dake kwance Kan gado daga ita sai riga da wandon bacci gajeru hankalinta na Kan wayar datakeyi da Sarah data Kira tana sake jin Yaya jikin nata wayar Hanifa tayi ringing tana dubawa taga sunan Marshal akan wayar Kamar yawanci yanda yasaba dai video call ne Dan Haka earphn dake kusa ta dauka tayi connecting sbd kada Naj taji muryarsa ta dauka kirana tana kallonsa Yana gidansa yau ba gurin aikiba cikin kulawa da farin cikin ganinsa tace"

Hi.

Wani irin qayataccen murmushi ya saki Yana kallonta shima sbd yanda ta maidasa baturen gaske ganin rayuwar dayafi sabawa kenan.

Cikin nutsuwa da sauti me dadi yace"

Assalm alaikm.

Qaramar dariya Mara sauti tayi tana kallonsa tace"

W slm,how are...kasa qarawa tayi ganin Naj Dan kallonta da fararen idanuwanta Jin tana wayar da turanci Wanda tasan shi kadaine baturen gidan Wanda kowa ke waya dashi da turancin fiyeda hausarsa.

Basarwa Hanifa tayi tana maida zancen cikin hausa tace"

Yaya aiki?

Ahankali ya bude Baki yace"

Alhmdlh,hw are you and The Baby?
And the other baby next to you?

Satar kallon Naj dake waya har lokacin tayi tana murmushi tace"

Duk lafiyanmu kalau kawai dai the other babyn is not that ok,I mean she's not..kasa qarasawa tayi sbd Naj dake kokarin Gama wayar karta gane maganarta takeyi Dan Haka ta basar da zancen da kallonsa tace"

Duk lafiyanmu kalau sai Dan zazzabin da ba'a rasabane kawai.

Sakamun ita Zan ganta" yafada Kai tsaye Yana aje cup din lemon tea me zafi dayake Sha.

Cire cameran daga front tayi tana maida Masa cameran wayar ta baya 
Naj dake kwance akan gado ta bayyana kan screen din iPad dinsa dayake vidcall da ita,kwance take tana waya fuskarta fresh da alama Bata Dade da yin wankan bacciba ya tsayar da idanuwansa Kan fararen cinyoyinta dogaye dake bayyane suna sheqin haske da lafiyan fata da Allah yabata.

Lumshe fararen idanuwansa yayi ahankali Yana jinginarda bayansa jikin kujera ahankali Hanifa tayi Masa sauti da wayar akan Naj ya aje wayar ta miqe ta fice tana cewa Naj din tana zuwa zata dawo.

Bayan fitarta gyara kwanciyar Naj tayi bayan tagama wayar da Sarah ta juyo da idanuwanta kan sauran boiled plantains da Hanifa tabari acikin plate take taji zuciyarta ta motsa ta dauke ido daga kan plate din sbd zuciyarta data fara tashi akan Amai datakeji
Yana kallonta yakumaga abinda ta daukewa kan,
Duk da ta juyarda Kai zuciyarta takasa daina tashin ta sake juyowa tareda tashi zaune ta zuro qafafunta qasa ta miqe ta tako da niyar dauke plate din ta fita dashi saidai tana qarasowa kafin ta dauka wani irin amai me qarfi yataso Mata da gudu ta nufa toilet tana rufe Baki tashige tafara zuba Amai me qarfi.

Rintse idanuwansa dasukai wani iri yayi tareda dauke Kai daga wayar bayan ya kashe ya Nemo no din Hanifan yasake Danna Mata wani Kiran wanda ba video ba Amma ba'a daukabaya saki wani guntun numfashi me Dan zafi tana jefar da wayar gefensa Kan kejera ya lumshe idanuwansa ahankali.

Amai tayi Sosai Wanda ya mugun galabaitar da ita ta sake watso ruwan zafi sosai ta fito ta saka Kaya masu kauri sbd zazzabin daya taso Mata ga mutuwar jiki ta Haye gado tareda shigewa bargo tana rufe idanuwanta.

Baccin rashin lafiya ne ya dauketa Koda Hanifa tashigo daukan wayarta Bata tashetaba ta dauka wayar ta fice sai alokacin taga misscall dinsa ta saka kiransa saidai Bai dagaba Dan Haka itama ta wuce daki Kai tsaye tafara Shirin kwanciya tana gamawa ta kwanta.

Washe gari sosai Naj din ta tashi da zazzabi, hankalin hajjo ya 'dan tashi sbd dama tasan Najma batada lafiya boyewa kawai takeyi sbd duka alamun Bata daidai ya bayyana.

Dr sa'id aka Kira yazo dubata Dan ko abinci daqyar aka samu ta iya ci sai Amai takeyi Wanda duk ya qarar Mata da qarfin jiki.

Koda Dr sa'id ya iso Anty Amina na gidan itama harta shigo duba Naj din Dan Haka itace ta kamota suka fito Palo bayan ta sanyo doguwar hijab akan kayan baccinta.
Zama sukai Dr sa'id ya Dan zubawa Naj din ido Yana yimata kallon tsaf.
Dauke idonsa yayi tareda Ciro paracetamol ya miqawa Hanifa yace"

Inaga Tasha paracetamol sbd wannan Dan zafin zazzabin ya sauka tukuna Dan gskia inaga saitaje asibiti saina dubata acan Dan inason Zan Mata wasu test musan asalin menene yake damunta.

Cikin kulawa hajjo dake kallonta tace"

Babu wani maganin wannan Aman datajeyine?duk qarfinta ya qare,kodai food poison ne yake wahalar da ita?

Eh zai iya yiyuwa hakan ne Amma dai saimun gwadata zamu sani.

Bayan tafiyar Dr sa'id aka kawo Mata abinci taci ko kadan Amma takasa cin komai,
Kallonta Anty Amina tayi tace"

To akwai abinda kikaji Zaki iyacin sai akawo kici ko kadan ne Kisha maganin.

Ahankali tace"

Aban orange drink ma kawai is ok.

Kawo Mata akai Tasha sosai Tasha maganin sai alokacin tasamu damar watsa ruwan zafi tayi salloli kafin ta iyacin white rice da miyar busasshen kifi.

Tana gamawa anty Amina dasu biyun ne kawai suka rage a dakin ta kalleta dakyau hat zuwa yatsin hannayenta dasukai wani irin fresh ta maida kallonta zuwa Kan fuskarta data Dan ciko kadan Kai tsaye cikin mamaki da shakku idanuwanta cikeda kasa boye mamakin tambayar tace"

Naj ciki ne dake?????

Dukan zuciyarta da qarfi maganar tayi harsaida kanta ya Sara ta dago ahankali ta kalli anty Aminan data tsareta da ido a waje tana jiran amsarta ta dauke Kai Yana sauke wani irin numfashi me wahala na gabanta daya dauki faduwa da tambayar sbd Karo na biyu kenan Ana Mata wannan tambayar,Sarah tayi yanzu Kuma Anty Amina.

Girgiza Kai tayi Kai tsaye tace"

Tayaya zakice ciki ajikina Anty Amina.
Cikin fa haihuwa kike mgn,Ina Zan samesa.

Da wani sabon mamakin anty Amina tace"

Kinada Miji kike tambayar Ina Zaki samu Miji duk da dai ansan auren baigama daidaitaba Amma yanayin naki ne da sauye sauyen danaga duk kin samu a Yan kwanakin Nan yasa nayi tunanin hakan sorry.
Duk da hakan kije asibitin gobe Dr yadubaki ciwo Haka batareda kasan menene yake damunka ba Dadi wuya zakiyita Sha.

Gyada Kai tayi ahankali zuciyarta na wani irin daukan nauyi da maganar Anty Aminan ta farko,
Ta Yaya za'a ringa tunanin ciki ajikinta?
Shin ciki zai iya shigartane a mu'amala biyu da akai bama da so ko yardartaba?
Rufe idonta dasuka sauya tayi tana girgiza Kai da cewan bazai yiyuba wannan masiface me girma,
Aa aa Bata fata, Allah ya tsareta daga wannan abun kunyar me girmanda bazata taba iya kallon ko kanta a madubi ba bare wani.

Bayan tafiyar Anty Amina daurewa tayi ta cije tafara nuna tasamu sauki Sosai sbd abar wani maganar zuwa asibitin Dan kuwa da kanta zata samu zuwa asibitin ita kadai saita fara Jin abinda yake damunta.

Haka ta tilastawa kanta dauriyar ciwon Wanda take matuqar jinsa Amma ta daure tana kannewa ta nuna taji sauki Sosai da wannan tasa aka bar zancen zuwanta asibiti har aka kwana biyu anty Amina ma data saka Mata ido Dan ta basar da ita akan zancen kullum tare suke zuwa gidan da Hanifa gurin gyara da ake Mata na zuwan Isma'eel itama wani lokacin takanyi wani lokacin Kuma batayi sbd qamshin su kurkum da bataso.
##MAMUH#

*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107

*_DM 37_*
A gidansu duk wani Abu dazai sake bawa Anty Amina damar sake saka ido akanta tana kokarin kauce Masa 
Sbd gabaki dayama ta rasa tunanin Yi abinda dai tasani shine cikin Marshal ajikinta bazai zama gskia ba.

Washe garin ranarda taji abun yafara Mata yawa ta yanke shawaran komawa aiki ranar Isma'eel ya dawo suna zaune Palo tareda hajjo Hanifa na daki tana sake shiryawa ya iso da sallama ya shigo palon bayan ruqayyat taje ta bude Masa kofa ya qaraso fuskarsa daukeda murmushi ya nema gurin ya zauna Yana gaida hajjo cikin tsananin girmamawa
Naj kuwa kallonsa tayi murmushi akan fuskarta tace"

Sannu da dawowa dadyn baby da maman babyn.

Dariya yayi Yana kallonta yace"

Sannu da zaman hutawa Amarya Kuma uwar gidan Marshal,
Hajjo ta daure Miki kina zuba ikonki akan Marshal.

Basarwa tayi tareda sauya zancen da cewa"

Yanzu dauke matarka zakayi ko kunyar hajjo bakwaji.

Satar kallon hajjo dake duba sako a waya yayi Yana maida da kallonsa kanta Yana hadiye dariyarsa Dan kuwa ta shammacesa agaban hajjon yace"

Zan Rama ne kinci bashi Naj.

Murmushi tayi tana maida kallonta kan Hanifa data fito cikin Ado sai daukan ido takeyi sbd fatarta datai kyau Tasha gyaran umma dakuma cikin daya qara Mata kyau sbd ya fito sosai.

Zaunawa tayi tana Masa sannu da isowa daganan suka koma dayar palon hajjo kafin aka gama jere abinci Sukaci abincin dare kafin suka wuce Naj din ta rakasu har mota bayan Isma'eel yaje gurin Dad Alfa ya dade Kuma acan din suna mgna.

Bayan tafiyarsu a hanyarta takomawa sashensu ta hadu da mum Malika da Hannah zasu nufa part din zuwa gurin hajjo
Mum Malika na ganin Naj din ta zuba Mata ido tana Dan bude idanuwanta akanta sosai tana qare Mata kallo a sirrance,
Dan shiga tunani tayi tana sake kallon Naj har Naj din ta iso gabansu cikin nutsuwa tace"

Barka da maraice mum Malika.

Washe Baki mum din tayi tana Dan dawowa daga tunanin data shiga ta kalli Naj din suna qarasawa tace"

Naj Yaya kike?yaya jikin naki kinji sauki kuwa?
Ki daure kije asibiti,idanma bakyason zuwa akwai wani babban likita Dan uwan baban Hannah dake Nan ko Zan kirasa yazo ya dubaki harma da kayan dibar samples na awon idan ya Kama kokuma Hannah ma zata iya kaiki ki gansa.

Da Dan wani yanayi na kame fuska Naj din ta kalli mum din kadan kafin ta dauke Kai batareda ko inda Hannah take ta kallaba tace"

No thank you mum Malika ba buqatan hakan,Dr sa'id ma ya Isa.

Wucewa take kokarin Yi Hannah da tuni Naj din tagama isarta data bar gurin ta daga wayarta tana dorawa a kunne tace"

Hey sweetheart harka qara missing Dina yanzu fa muka Gama waya.

Ko dakatawa Naj bataiba ta wuce sbd Kota kanta zancen baibi ba Dan Haka ko data Isa palon Bata tsayaba ta wuce dakinta Kai tsaye Dan tasan fira suka kawowa hajjo Kamar yanda sukeyi akai akai.

Washe gari Haka ta shirya Takoma aikinta sbd rashin Hanifa ma agidan duk kadaici takeji sbd hajjo ko yaushe karatun littafantane a gabanta.

A office ko dataje kasa samun sukuni da nutsuwa tayi ta ringa zuba Amai Wanda yasa hankalin Sarah tashi Haka dai suka lallaba harta tashi Takoma gida,
Tana Isa gida abinci taci sosai tayi wanka tayi kokari ta zauna Palo sbd Kar hajjo tasan batajin Dadi.

Hakama washe gari a office Bata ganewa komaiba Haka ta jera kwanaki tana zuwa office Amma Babu wani sauki qarshe dai haka taji kamar qamshin office din ne yake sata wannan yanayin Haka tasa Sarah aka kusan sauya Mata komai na office din tasamu Dan saukin abinda take ji Amma duk da hakan gabaki daya tana cikin wani irin yanayi me wahala sbd yawan cin abinci akai akai ga yawan zazzabi da jiri dasuka sakota gaba uwa uba Amai dayafi komai wahalar da ita,
Takasa Kai kanta asibiti sbd tsoro da shakkar Jin wani ciwone ke damunta zuciyarta na cika da wani irin mummunan yanayi idanma tunanin hakan ya shigeta wato na zuwa asibitin.

Sarah duk tabi ta damu akan rashin lafiyan Naj din gashi tana boyewa hajjo sbd Karta damu Dan Haka ta takurata akan Dole suje asibiti kokuma ta sanarda hajjo rashin lafiyan.

Itama al'amarin ya isheta tana buqatan ganin Dr Dan Haka ta yanke shawaran zuwa asibitin,
Daga office batareda sanin kowaba suka nufa asibitin itada Sarah wadda itama tata zuciyar ke harbawa da abinda zasu jiyo sbd zuwa yanzun tagama tabbatarwa kanta cikine da Naj din Wanda tasan akwai tashin hankali idan har hakan ta tabbata agurin Naj,qarin mamakinta Kuma yaushe har hakan yafaru duk da dai ba abin mamaki bane tunda tanada aure Amma auren da mijin Kuma.....

Isowarsu asibitin yasa ta dakatarda tunaninta suka fito Kai tsaye office din Dr sa'id Wanda takira a waya suka nufa.

Tana buga kofar yasan itace Dan Haka ya taso ya bude Yana kallonta yace"

Kafin mu zauna muje a dauka sample dinki ko?

Gyada Masa Kai kawai tayi ahankali suna juyawa zuwa Lab yana sake Mata tambayoyi akan yanayin datakeji tana basa amsa ahankali sbd jikinta dake amace.

Bayan an dibi jininta a lab din suna fitowa daqyar suka Isa office dinsa ta ringa Amai a toilet dinsa daqyar ya tsaya Mata ta dawo ta zauna Sarah na shafa bayanta tana Mata sannu cikin kulawa da tausayawa.

Ruwan roba Dr Sa'id ya dauko daga fridge ya kawo ya miqa Mata Yana Mata sannu cikin kulawa saiga result din ankawo.

Karba yayi Yana budewa ya nufi kujerarsa ya zauna Yana fara karantawa.

Ajiyar zuciya ya sauke ahankali bayan yagama dubawa ya dauki biro yayi signing ahankali ya miqa Mata Yana cewa"

Well kamar dai yanda nayi tunanin ciwon shine kina daukeda juna, You're pregnant Naj.
Yanxu zanmiki scanning sai muga ko wata nawa ne.

Daukewa numfashinta yayi cak sbd wutar jikinta tako Ina data dauke ta zubawa bakinsa dake bayanin ido tana daina fahimtar abinda yake fada.

Da sauri Sarah ta dafata tana shafa bayanta tareda bude Mata ruwan tana kaiwa bakinta cikin kulawa da tsoron yanayinda Naj din tashiga tafara Kiran sunanta tana cewa"

Naj, Naj, Naj are you okay?
Please ki saki numfashinki Mana,
Say something Naj.

Buga bayanta tayi da Dan qarfi sai alokacin numfashinta yadawo da qarfi ta dago ta kalli fuskar Dr sa'id din da idanuwanta dasukai jajir Nan take sbd firgici da tashin hankali Babu tunanin komai sbd kanta da tunaninta dasuka cushe Kai tsaye tace"

Banason sanin ko wata nawa ne ka ciremun cikin.

Wani kallon tsananin mamaki da Dan qaramin firgici Dr sa'id dama Sarah sukai Mata atare yasake kallonta Yana cewa"

Ciki fa nace Miki kinadashi Naj.

Rintse ido tayi wasu irin hawaye na balle Mata tace"

Ka ciremun kawai Dan Allah bana buqatan kowama yasan da cikin Nan.

Ajiyar zuciya ya sauke sbd abinda yakeson fada Mata ba lallai ta fahimtaba ya kalli Sarah da itama shi take kallo tana fatar karya amince din ya maida kallonsa kan Naj din cikin nutsuwa yace"

Kije gida yanzu kina buqatan hutawa tukuna zuwa gobe ko jibi zamu sake mgna sbd Dole saina Miki scanning dinnan kafin wani maganar Amma dai cire cikin shine abinda bazai faruba.

Miqewa tayi Sarah na riqeta ta zame ta fice ahankali result din awon na hannunta ta share hawayenta ta Isa mota ta bude ta shige sai alokacin tasaki wani irin kukan daya daga hankalin Sarah takasa tada motar Kuma batace kalaba sbd karata damu Naj din Dan kuwa ko ita Jin wannan Batu yasa taji hankalinta ya tashi da yanda cikin zai bayyana ga maganar cirewa da Naj din keyi Wanda bazata bartaba gskia saidai suyi fada kowama yaji abinda yake faruwa.

Tada motar tayi suka nufi hanyar gida Naj din ta dauka tissue ta goge fuskarta datai ja sbd kukan datai din 
Saikuma zuciyarta dake doka wani irin tsalle.
Suna shigowa layin gida Sarah ta hango sojojin dasuka saka gabanta faduwa itama Dan kuwa da yiyuwar Marshal ne yadawo.

Naj Bata lura dasuba Saida suka Shiga harabar gidan taga motarsa dake quryar rumfar motoci a fili sai sheqi takeyi ta dauke ido sbd gabaki halinda take ciki baya barinta bi takan tunanin komai ta fito ta nufi ciki bayan Sarah ta wuce batareda ta Shiga cikiba itama.

Kai tsaye ta shigo palon ahankali cikin yanayi na son boye halinda take ciki ta qaraso cikin palon ba kowa sai hajjo dake waya hankalinta Kuma duka Yana Kan wayat ta nufi hanyar dakinta takai hannu zata bude taji an rungumota ta bayanta ahankali hannuwansa na sauka Kan takardar dake hannunta har lokacin
Ya sako fuskarsa wuyanta ahankali tareda sakar Mata wani irin numfashin daya sakata juyowa da sauri bugun zuciyarta na tsananta 
Idanuwanta suka sauka cikin nasa Ya qaro wani irin haske da fresh na hutun gske da rayuwarsa take ciki ahankali yakai bakinsa kunnenta ganin irin kallon datake Masa zaiyi mgn hawayen idonta suka balle tana sake damqe result din a hannunta.
##MAMUH#



*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*


*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107


