Bismillahir Rahmaanir Raheem.              *DUKAN RUWA...* FARKO. Ta yi zugum kanta jingine jikin kujera tana kallon halittun manyan  duwatsun da suke ratsawa a wannan dajin, tafiya suke yi tamkar ba za su kai ba. Wani lokacin idan sun gifta bukkokin jama'ar wani yankin, takan yi murmushi cike da al'ajabin ta yadda mutum ƊAN ADAM ke iya rayuwa a wannan wuri. Tun tana kallon har dai ta zame ta gyara zama gami da lumshe idanu, bacci ke ƙoƙarin ɗaukarta tana yakicewa. Babu abin da ta tsana sama da bacci a hanya, hanyar ma da ko a mafarki ba ta taɓa ganin za ta bi ba,  zuwa Nijeriya daga Nijar. Ajiyar zuciya ta saki tamkar wacce ta ci gudu, lokaci guda nannauyen tunanin da take ƙoƙarin kaucewa na ƙara yi mata saukar aradu a kwakwalwa. Idanunta ta sauke akan matar dake kusa da ita, baccinta take haiƙan har carbin da ke riƙe a hannunta tana ja, ya faɗi. Sai dai duk da baccin da ta lula, hakan bai sa ta saki yaronta ba, yana rungume a kirjinta ɗam! Kai ka ce wani ne zai ƙwace mata shi. Juya kai tayi ta koma kallon hanya da murmushi ɗauke saman fuskarta. Soyayya da shaƙuwar dake tsakanin ɗa da uwa na daban ne, a kowane yanayi, a kowace rana burin kowace uwa ganin gudan jininta cikin walwala da annashuwa, ba ta fatan wani mugun abu ya same shi. Shakka babu duk wanda ya rayu da uwa ya more.   Sai kuma kewa ya lulluɓe ta dalilin Dada da ta tuno, watanni biyar kenan da rasuwarta amma jin sa take a rai tamkar jiya-jiya. Kullum mutuwar kakarta kamar sabo ne fil a wurinta, mace mai hakuri da dattako, ta yi namijin kokari wurin ba ta kulawa daidai gwargwado da kuma tarbiyyar islama. Ba ta shaƙu da kowa ba sama da ita sai ko Kawunta ɗan uwan Mamanta, Kawu Umaru. Shi ma ba ta jin za ta manta da irin namijin ƙoƙarin da ya yi a kanta, koda dai dama barewa ba ta yi gudu ba ɗanta ya yi rarrafe, wannan kyawawan ɗabi'un Dada ne suka kwaso. A wannan irin namijin ƙoƙarin ne a yau Kawunta ya tashi haiƙan suka bi wannan doguwar hanyar kawai don ya sada ta da mahaifinta, mutumin da tun da ta buɗi ido ba ta taɓa ganinsa ba. Hatta a waya ba su taɓa koda gaisawa ba.  Duka wannan bai sa ta riƙe mahaifinta a zuciya ba domin kuwa ya samu kyakkyawar shaida a gurin Dada da Kawu. Ko sau ɗaya ba su taɓa kawomata kushensa ba, asalima sun ce yana sonta sosai, kuma acewarsu ya sha zuwa ganinta tana ƙarama, su ɗin ne suka ƙi amincewa ya tafi da ita bisa dalilan da su kaɗai suka bar wa kansu sani. A yau kuma da aka wayi gari babu Dada, Kawunta ya ɗauki ɗamarar cika wasiyyar da Dada ta bari na cewar ya sada ta da Mahaifinta idan har rai ya yi halinsa.   Ɗan girgizar da motar ta yi sakamakon taka wani ɗan tudu ne ya sa ts ji saukar ruwa a saman leɓɓanta, sai lokacin ta gane kuka take. Kukan kewa da damuwa ne, Dada ta tafi, tafiya ta har abada, ta tafi wajen da ba za ta sake ganinta ba sai ko idan nata ajalin ya iso, ta je ta tarar da ita.   _"Kar ki taɓa bakin ciki da zuwa wurin Mahaifinki Shatu, mutum ne nagari mai sanyin hali, za ki yi farin ciki da ganinsa. Yana sonki sosai Shatu."_ Kalaman Dada suka faɗomata a rai, ta sauke ajiyar zuciya na samun nutsuwa, lokaci guda ta ciza leɓɓanta na ƙasa tana ƙara murmusawa karo na barkatai. Ya mahaifinta yake? Da wane ido za ta ɗaga ta kalle shi ya kalle ta? Dagaske tana kama da shi ko kuwa dai Kawu ya faɗi ne don ta ji dadi? To an ce yana da wasu yaran, su ma tana kama da su ko aa? Duka waɗannan tambayoyi ne da ta hargitsa lissafin kwakwalwarta da su alhalin babu mai ba ta amsa. Haka dai ta yi ta saƙe-saƙenta har suka fita gaba ɗaya daga Nijar suka nufi bodar Nijeriya. Nan ɗin ma bayan kammala cike-cike da duba kayyakinsu, suka gangara cikin Nijeriya, ta baza ido tana kallon yanda cikin iko da hukuncin Allah, shuke-shukensu ya sha bamban da na ƙasar da ta fito. *** "KATSINA" Ta karanta sunan a hankali, sannan ta dinga bin garin da kallo tana ƙarewa bambance-bambancen garin da nasu. Tunaninta ya katse sa'ilin da direba ya  tsaya a gefen hanya domin ba su damar gabatar da sallar la'asar. Mazan duk suka riga su sauka, su ma suka sauko. Kawu ya dube ta. "Ki bi su ku yi sallah kar ki je ko'ina kin ji ko?" Ta gyada kai ta amsa da toh, tana rungume da ƴar ƙaramar jakarta ta hannu haka ta dinga bin matan su uku har zuwa wani ɗan wuri da aka katange, suka samu gefe guda da ba mutane, masu jin fitsari suka yi sannan suka ɗaura alwala. Bayan sun idar suka dawo motar, nan kuma kowa ya hau zuge jaka ya na siyan abin motsa baki. Tana nan zaune cikin motar Kawu ya kawo mata ruwa da lemu sai nama a leda, kaɗan ta ci bayan ta yiwa ƴan motar bismillah, sauran ta naɗe ya ajiye a gefe, lemun dai ta sha sosai. Daga nan suka ƙara miƙa hanya har dai cikin hukuncin Allah suka ƙaraso cikin garin KANO. Ta nanata sunan a kan harshenta jin wata Mata ta ambata, ta maimaita har sau uku, lallai idan ba ta mance ba shi ne sunan da Dada ke yawan ambata idan ta tambaye ta sunan garin Mahaifinta.  Nan da nan zuciyarta ta yi fari ƙal, ta kasa rufe bakinta, wannan karon murmushi take tun daga ƙasan zuciyarta har saman leɓɓanta don har siririn wushiryarta na bayyana. Sai da suka ƙarasa tasha suka sauka, daga nan ne kuma Kawunta ya ɗauki akwatin kayanta suka fito bakin titi. Suna hawa taji ya ce unguwar Gadon Ƙaya, daga nan direban ya hau tafiya ita kuwa tana ta kallon hanya har suka sauka. Sun yi ƴar tafiya a ƙafa sannan ta ga ya tsaya daidai bakin wani ɗan shago ya yiwa mai shagon sallama. Koda suka gaisa ya ce. "Don Allah gidan Alhaji Isuhu Maiagogo nake tambaya." Mai shagon ya gyada kai ya ɗan fito sarari ya hau yi musu kwatance da hannu. Ya yi godiya suka nufi inda ya ce. Koda suka karasa wajen wani ƙaton gini ta ga ya tsaya cak a gaban ginin, ta bi ginin da kallo ta ji gabanta ya yanke ya faɗi lokaci guda, ba kuma don tasan dalili ba. Ta kasa kwakkwaran motsi har Kawunta ya taka zuwa ga kofar gidan yana tambayar wani dattijo ko nan ne gidan, amma ita kam ba ta dauke kai daga kallon ginin ba, gwuiwoyinta suka yi wani irin saki, ganin yanayin da ta shiga har zufa na tsastsafomata a goshi yasa ta dinga maimaita kalmar innalillahi. "Shatu ke!" Kiran da Kawu ya kwalamata ne ya maido ta hayyacinta, a hankali ta soma takawa har ta ƙarasa gefensa, ba ta kuma san dalili ba ya ji ta sa hannu ta riƙo nashi yatsun gam! Hakan da tayi ya sanya shi dubanta, itama shi din take kallo, ya yi dariya. "Tsoro gidan ya ba ki ne? To ki shirya yaƙar tsoron nan don nan ne gidan zamanki daga yau in sha Allahu." Dattijon ya taya shi darawa kaɗan duk da bai fahimci komai ba. Amma ta lura da yadda yake ta kallonta har ya kasa hakuri ya tanka. "Amma dai wannan ƴar uwar Alhaji ce ko?" Kawuna ya yi dariya ya amsa da eh kawai. Ita dai ba ta ce musu uffan ba sai sadda kai ƙasa da ta yi, ta na ji Dattijon nan na kara zuzuta kamanninta da Alhajin wanda shi ya sanya shi tankawa.  Suna nan dai  tsaye sai ga wani ɗan matashin yaro ya fito, ashe wai Dattijon ne ya aika shi gidan don a shaida wa Maigidan zuwansu. "Ya ce maza ku shigo ciki. Muje na raka ku." Daga haka  suka shiga ciki. Madadin faɗuwar gabanta ya ragu, sai ma ƙara hauhawa da ya yi, ta ci gaba da maimaita innalillahi har ƙarshe, sai ta ji gaba daya ta bar rawar ƙafar son haɗuwa da Babanta Isuhu.    Koda suka ƙarasa cikin ƙaton falo, wani irin sanyi da ƙamshi mai dadi ne ya daki hancinta. Ta gefen ido take bin wurin da kallo tana so tayi ido huɗu da Babanta, sai dai kuma duk irin girma da daular da ke shimfiɗe a falon wanda ya ƙara ƙawatashi, babu rai ko ɗaya mai numfashi face su ukun da suka shiga. Wuri ya nuna masu saman kujera suka zauna, ita kuwa ƙasa ta zauna gefen Kawu don ba'a ba ta tarbiyyar zama saman kujera alhalin manya na zaune ba. Matashin ya kara juyowa fuskarsa a sake.   "Ku jira Yallaɓai nasan ba zai jima ba zai fito." Kawu ya amsa daga nan ya fice ya bar su a nan. Sun samu mintoci goma da sakanni, don gaba daya hankalinta yana kan ƙaton agogon da ta zauna saitinsa, kafin ta ƙarasa ƙirgenta suka tsinkayi sallama. Lokaci guda suka kai duba ga gefen da muryar ta ɓullo, baki da ido ta saki tana kallon mutumin yayinda shi kuma idanunsa ke kan Kawu, kallon mamaki da tsantsar farin ciki yake binsa da shi. A gefenta kuwa halittar fuskarsa take ƙarewa kallo. Eh, tabbas suna kama, fuskarsa doguwa kuma siririya irin nata, yana da dogon hanci masha Allah, sai kuwa bakinsa daidai. Idanunsa manya kamar naya hatta da cikar halittar girarsa da gashin kai, duk kuwa da cewa shi nasa gashin ya yi fari fat na manyanta amma kamanninsu da shi sun fito fes har tsawon. Ba ta ƙara gani ba sai da ya saki dariyar farin ciki, anan kuma baki hangame ta ce. "Kai!" Ta furta a fili ba tare da ta shirya ba. Gaba daya suka juyo su na dubanta. Ta kama bakinta da sauri gami da ƙara sunkuyar da kai, mutumin ya matso ya durƙusa a gabanta, zuciyarsa ta yi wani irin nauyi, abubuwa da dama suka shuɗe a tsawon shekarun baya suka dawo mishi sabo fil. Ita kuwa kunya ce ta kama ta, bata ma gaida shi ba, ta gaishe shi a hankali don a zaton ta ma bai ji ba, amma ga mamakinta ya amsa. "Barka da zuwa Mamana. Ki saki jikinki nan gidanku ne, gidan Abbanki, ba ki da inda ya fi nan kinji ko?" Da ya fadi haka wai sai ta kalli Kawu, hakan da tayi ya ba su dariya. Kawu ya gyaɗamata kai. "Idan eh kike so nace ko aa, toh eh Shatu, gidan mahaifinki kenan. Abin tunƙahonki." Ta yi murmushi tana kara duban wanda ya kira kansa da Abbanta, sai nan da nan kwalla ta cikamata idanu. Wannan fargabar ta kau, so da kaunar suka dawo daga hutun da suka je, ta rungume hannunsa ta saki kuka sosai. Abubuwa da dama take tunawa, tabbas ta yi kewarsa a rayuwa. Koda ace ba ta rasa ci, sha da sutura ba daidai da kwana ɗaya a rayuwa, to ta rasa wannan kusancin na ɗa da mahaifi, shi din na dabanne. Ko ma dai tace ta rasa soyayyar iyaye gaba ɗaya. "Kiyi hakuri Mamana, ba zan ƙara yin nesa da ke ba, wancan ma ƙaddara ne, amma wannan karon in sha Allahu ni da kaina zan miƙa ki ɗakin mijinki. Allah ya ji ƙan Mahaifiyarki da Hajiya Dada." Suka amsa da amin. Nan kuma ya shiga jan ta da hira kadan har ta sake, waya ya zaro a aljihu ya danna kira, sunan wata ya ambata, Ummita, ya ce ta zo yanzu. Daga haka ya  juya ga Kawu suka yi ta hira yana ba shi labarin rashin lafiyar Dada har zuwa rasuwarta. Suna nan zaune ita kam ta kasa ɗquke ido akan Abban, suka tsinkayi sallamar wata ƴar budurwa da ba ta wuce sa'arta ba. Baƙa ce, irin baƙin da hutu ya ratsa, riga da wando ne a jikinta sai dai ba su ɗame ta ba, ta saka hijabi iyaka kafaɗarta. Ta gaida Kawu sannan ta maida hankali ga Abba. "Yauwa Ummita, kama hannun ƴar uwarki ku je a ba ta abinci ta ci ta yi wanka. Ki kuma faɗawa Maminki ina da baƙo a shirya masa abinci kafin mu yi sallah. A kawo ruwan sha." Ummita ta amsa da toh tana kallonta fuskarta a sake ta ce.      "Lah Abba wallahi kuna kama sosai." Duk sai ta ba su dariya, Abba ya dubi Aisha Humaira kafin ya maida duba gareta.   "Itama ƴata ce, ita ce mai sunan Umma." "Abba ita ce wacce ka ce tana Nijar ko?" Wannan karon da wani irin zumuɗi ta yi tambayar. Ya amsa mata da eh. Ta kuwa karaso da sauri ba tare da nuna kyankyamin komai ba ta rungumeta tana fadin. "Welcome Sister." Ba ta gane me ta ce ba amma itama ta rungumeta tana mai jin kaunarta har can ƙasan ruhinta.   Ummita kenan, tana daga cikin mutane masu girma da matsayi sosai a rayuwar Humaira, har abada Humaira ba za ta cire ta a tarihin rayuwarta ba, ta karɓe ta a yadda take, ƴar kauyen Maine. Ƙamshi take a yayinda ita kuwa ba ta ma sani ba, ƙarnin kifin da ta ci a mota take yi ko kuma naman da ta ci ne. Kai ko ma mene ne, ta sani Ummita ba ta irin wannan ƙarnin, ƙamshi ne a jikinta, amma ba ta duba komai ba ta rungumeta. Ta tabbata tana daga cikin masoyanta na haƙiƙa. Ta kama hannunta ɗayan hannun kuma ta ɗauki akwatin kayanta wanda duk ya ci gidansu, akwati ne irin na da da aka yi yayinsa, Dada ta ce nata akwatin tun na auren Mamanta ne.   Suka nufi wata ƴar siririyar hanya suka fito wurin wani ƙaramin hanya nan ma gefensa duk shuke shuke. Wurin ya burge Aisha Humaira sosai, a daidai ƙofar shiga wajen ma, shukoki ne sun kewaye jikin ƙofar da bango sun ba da zane mai kyau. Ummita ta ci gaba da tafiya har suka nufi wani ɓangaren, baranda ne sai kuwa wata ƙofa, suka shiga Ummita ta shiga kwala ihun kira. "Mami! Mami!! Fito ki gani!" Ihun da take tana kira ya sa sauran mutanen dakin suka fito. Maza da mata wadanda sun ɗan girme ta sai ko yara. "Wai Ummita me ke damunki haka? Tun ɗazu bakinki ya ƙi..." Aisha Humaira ta lura haɗa idanun da suka yi ne ya sa sauran kalaman bakin matar suka maƙale. Kallonta take kamar a razane, ita kuwa kallonta take tana so ta ga ta inda suka yi kama da Ummita don ko kaɗan ba su yi kama ba. Ummita baƙa ce, wannan kuwa ta tsaye a gabanta da alama ma buzuwa ce. Gashinta a tufke a baya, ta kai duba ga wasu a cikin yaran, su ma farare ne ƙal, kyawawa da su. "Wace ce wannan?" Ɗaya daga cikin ƴanmatan ta tambaya tana bin Aisha Humaira da kallon tara saura. Ummita ta yi dariya ta jawota ta rungumo kafaɗarta. "Mami, mai sunan Umma ce ta zo daga Nijar, Aisha Humaira. Abba ya ce shikenan ta dawo nan da zama cikinmu." Wacce aka kira da Mami, ta tamke fuska babu ko ɗigon annuri, suka kalli juna a kar na biyu. Kallon da ya da ya sa Aisha Humaira ta ji hantar cikinta ta kaɗa, dariyar matasan ne ya sa ta maida idanu kansu.    "Wai! Ni da yagwalgwal, amma wannan ma a Nijar ɗin a can ƙauyen kike ko?" Ɗaya a cikin matasan ya furta yana dubanta, idanunta nan da nan suka cicciko da kwalla. "Kai Yassar, bana son haka. Sannu da zuwa Humaira, maza Ummita kai ta ɗakinku ta yi wanka lokacin sallah ya gabato." Da sauri na kalli matarnan, na sha mamaki ganin kamar ba ita ba, ta saki fuska sosai tana murmushi har haƙorin makkanta ana gani. Har Ummita ta faɗi saƙon Abba, Humaira ba ta iya tankawa ba hakanan ba ta iya ɗauke idanu daga kanta ba, itama jefi-jefi tana magana da Ummita tana kallonta ta kuma rasa dalili. Har Humaira ta bi bayan Ummita zuwa ɗaki ba ta daina waigenta ba, kuma itama Mami ta ƙi matsawa balle ta dauke ido a kanta.    Ita kam Humaira jikinta ya ba ta kamar akwai wani abu. ®️Rufaida Umar.   02 A hankali ta bi kowace kusurwa a ɗakin da ido, gado ne kananu har hudu kowanne a nashi wurin, a gefen kowane gado akwai sif na kaya kamar dai ɗakunan makarantun kwana, babban daki ne mai yalwa wanda har akwai gurbin da ire-iren gadon uku za su samu matsuguni. Daga can gefe jikin taga kuwa, ƙaton madubi ne a saman dirowar gaban cike da kayayyakin kyalkyali na adon fuska da mayuka. Dakin tsaf-tsaf babu ƙazanta, ɗakin ƴanmata kenan. Ummita ta ɗaga akwatin tana shirin ajiyewa saman ɗaya daga cikin gadajen nan, baki bude tana kallon Humaira da niyyar magana, aka daka mata wani uban tsawa daga baya. Muka juyo, wannan dai budurwar ce ta ɗazu mai ƙibar ciki. Ta zo da sauri ta janye akwatin ta yi wurgi da shi gefe. Idanu cike da masifa ta soma magana.   "Wallahi kar ki kara  gangancin ajiyemin jakar wannan korar yunwar a gadona, don gulma da kinibibi idan abin naki dagaske ne meyasa ba za ki ajiye a naki gadon ba. Aikin banza kawai, uwar shishshigi. Haka za ki ƙare." Tana kai wa nan ta  fice daga ɗakin tana mita,  Ummita ta kalli Humaira gami da jifanta da murmushin yaƙe. "Ki yi haƙuri." Ta gyaɗa mata kai tana maida mata martanin murmushin sai dai can ƙasan ranta, tana maimaita kalmar da ta ambata "Korar Yunwa". Ta fahimci manufarta tsaf, ta kuma gane ko wace ce ba ta samu karɓuwa a wajenta ba. Koda dai, ba ma ita kaɗai ba, ta lura da irin kallon da Mami ta watsamata. Ko ya zamantakewarta a wannan sabuwar duniyar za ya kasance? "Hey, tunanin me kike? Amm..nidai bari kawai na kiraki da Humaira, kinga babu damar ce maki Aisha kai tsaye saboda sunan Umman Abbanmu kika ci ko? Hakan ya yi?" Humaira ta gyaɗa kai karo na biyu tana mai sakin fuska, ta lura Ummita akwai kirki.  Bandaki ta nuna mata, ita kuwa ta yi  godiya, har za ta shige ta dakatar da ita. "Yauwa Humaira ga wannan zanin ki yi amfani da shi ki goge jiki." Ta sa hannu ta karɓa, zani ne a wanke a goge. Ummita har ta kama hanyar fita sai kuma ta dawo ta shiga bandakin gami da ba ta umarnin ta bi bayanta. Su na shiga ta kunna mata famfo gami da faɗin amfanin kowannensu. Ta fiddo mata sabon sabulun wanka daga cikin wata ƴar kwaba dake a gefe jikin bangon, sai kuma ta tambayeta ko ta taho da soso, Humaira ta amsa da eh. Hatta da ƙofar banɗakin sai da Ummita ta nuna mata yadda za ta ƙulle kuma ta buɗe, daga haka suka fito, nan ma sai da ta ajiye mata dardumar sallah saitin gabas sannan ta fice ita kuma ta ciro  sosonta a akwti ta koma banɗakin ta rufe. Wanka ta yi gaba ɗaya ta ɗauro alwalar Magriba, koda ta fito wannan budurwar ta ɗazu tana zaune gefen gadonta tana waya, suna haɗa ido ta bita da harara ba shiri Humaira ta kauda kai. Idanunta ya kai ga akwatin kayanta, ƙarasawa ta yi ta buɗe sai dai gaba ɗaya ba'a nutse take ba sakamakon idanun wannan budurwar a kanta suke duk kuwa da wayar da take amsawa. Turanci zallah take zubawa har wani shagwaɓa take yi tana dukan gadon, kalmar I Lobiyun da ta ce yasa Humaira ta fahimci koma dai wane ne toh masoyinta ne. Ba ta ko ƙara kallonta ba gudun ganin abin da zai sosa zuciya, ta fiddo doguwar rigarta ta yadi ta warware ta zura. A gurguje ta ciro hijabinta, ta linke kayan da na cire na ajiye daga saman akwatin. Ba ta jima da tada salla ba sauran ƴanmatan nan biyu suka shigo suka cika ɗakin da hayaniya, rabin hirar tasu da harshen turanci suke yi. Koda ta idar ba ta iya nutsuwar jan addu'a mai tsawo ba, ta yi istigfari da hailala da salati ta shafa. Zama ta cigaba da yi anan ba tare da ta miƙe ba gudun ma kar ta yi wani abin ya jazamata baƙar magana. Hankalinta yana ga Abbanta wanda take da tambayoyi birjik da za ta yi mishi a kwakwalwarta. Eh yana sonta yana ƙaunarta, amma meyasa bai ƙara waiwayarta ba, meyasa ba ta taɓa ganinsa ba? Meyasa kuma koda a waya bai kira domin su gaisa ba? Dukkan wannan rashin kulawar nasa da ba ta samu ba, ace yana kaunarta ya kuma damu da itq? Ita kam tana son sanin amsar da zai fito daga bakinsa. "Ke Indo." Ta ɗaga kai ta dube su kawa, suka kwashe da dariya. "Kai Raihana ba ki da kirki wallahi, au ba ma za ki kirata Humairar ba sai Indo ko?" Wacce aka kira da Raihana ta yamutse fuska. "Aa, ina ce sunan Umma gareta, tunda kaka ce ai ko Indon ma da na ce ta gode min. Ku ni ba wannan ba, wallahi mu tashi mu yi magana fa tun kan a ƙaƙaba mana ita a ɗakinnan. Ni wallahi  tsoro ma take ban. Mu faɗawa Granny ta yiwa Abba magana don Mami ba za ta goyi bayanmu ba." Humaira ta kalle ta dakyau, doguwa ce kamar dai Abba, don ta fi Maminsu tsawo, Mamin ba ta da tsawo sai jiki kuma  gajeriya ce. Fara ce tas itama kalar buzayen, gashinta da ya sha kalba ya sauka har gadon bayanta, riga doguwa ce ƴar kanti ta sa mai kama jiki. "Kallon me kike yimin kamar wata mayya? Kar ki ji ance wai wani ke ƴar Abbanmu ce ki yi ƙoƙarin haɗa kanmu da ke, wallahi kar ki kuskura don bakin rijiya ba wajen wasan yaro ba ne, atoh. Gwara ma Abban ya zo a yi meeting ɗin a bambance tsakanin aya da tsakuwa." Duka wannan bayanin daga bakin Raihana su ke fitowa, Humaira ta sauke idanunta a hankali zuciyarta na zafi, dagasken dai ba ta samu karɓuwar kenan ba, zuciyarta na da ƙarfin jure abu idan har wanda ya fi ta a shekaru ne ya aikata gareta, amma ba ta jin za ta iya ɗaukar wannan rainin wayon. "Futuha mene ne haka wai? Meyasa kullum burinku ku tozarta mutum?" Maganar Ummita ya sanya Humaira ɗago kai, ashe wai akwatinta wacce aka kira Futuha ta nufa ta buɗe. Ita dai wacce ke faman  waya tun ɗazun. Ai kuwa kamar an mintsile ta haka ta miƙe tsaye a zafafe, ta ƙarasa daidai sadda Futuha ta ɗaga akwatin da niyyar doka shi da ƙas, da wani irin zafin nama ta ture ta, daga ita har akwatin suka faɗi, akwatin ya faɗa saman  gado, ita kuwa ta yi rashe-rashe a ƙasan gadon bayan ƙugunta ya bugi katakon. Ai kuwa  ta kurma ihu, Raihana da ɗaya budurwar da  Ummita ta ambata da Tasleem suka yo kai Humaira gadan-gadan, Ummita ta tare su. Ita kuwa Humaira  ko a jikinta ta nufi akwatin ta shiga harhaɗa kayan da suka zube tana maidawa lokaci ɗaya hawayen da ta fi zaton na ɓacin rai ne, su na kwaranya. Ya yi daidai da faɗowar Maminsu ɗakin wanda hakan  bai wuce sanadiyyar ihun Futuha da ya mamaye ilahirin ɗakin ba. Jin muryarta da ta yi sai da gabanta ya faɗi, ta rasa dalilin da yasa take jin haka a kanta. Ta shiga ambaton sunan Allah a ƙasan ranta.   "Lafiya? Me nake gani haka kamar waɗanda aka ƙwato daga bakin kura? Ke Ummita sake ta, kyale su na ga gudun ruwansu. Au, don ku nuna mata rashin tarbiyyarku ba komai ba ne ba ko? Har kun soma yada halin?" Tana maganar ne fuskarta a murtuke tana bin su da kallo ɗaya bayan ɗaya, ita dai Humaira sam ba ta tofa ba sai ci gaba da tsince kayanta da tayi tana harhaɗawa tana mayarwa ciki. Ba ta san ma'anar juya harshe zuwa wani can daban da ba ta sani ba, ta dai ji Mamin a cikin yare ta yi musu magana wanda ba ta fahimci koda harafi guda a ciki ba, sai gani kawai ta yi duka sun fice daga ɗakin idan ka cire Ummita da ta durkusa tana taya ta haɗi da ƙara ba ta haƙuri. Tana niyyar amsawa Ummita ta ji  an shafa kanta, ta runtse idanu ba tare da ta  ɗago kai ba don tasan Mami ce. "Ki yi hakuri kin ji Humaira, su Tasleem su na da irin wannan halayyar na son yiwa baƙo shaƙiyanci. Kinga yau ki ka zo kuma kafin su karɓe ki za'a ɗan kwana biyu, a hankali idan sun gane ke ɗin ɗaya ce a cikinsu komai zai wuce kin ji ko? Ki ɗauke ni madadin Uwa, don mahaifiyarki mun yi zaman mutunci da nutunta juna da ita. Kema kuma nasan muddin dai kyawawan ɗabi'unta kika kwaso, ba za mu samu kowace iriyar matsala ba. Ina fatan haka?" Jin bayanan Mamin sai ta tsinci zuciyarta da yin sanyi, ta ji lokaci guda kaso saba'in na fargabarta akan Mami ya ragu, wannan furuci nata na madadin Uwa, ba ta jin za ta iya kwatanta daɗin da ya sanya ta. Kai ta gyaɗa alamar toh,  Mamin ta maida dubanta ga Ummita. "Sai ku hanzarta ku fito ta ci abinci daga nan zuwa bayan sallar isha'i, Abbanku na neman mu duka." "Toh Mami." Faɗin Ummita cike da girmamawa. Daga haka ta fice ta bar mu. Ummita ta kalli Humaira da murmushi saman fuskarta. "Sai fa kin yi hakuri sosai Humaira, da gaskiyar Mami, dama ya lafiyar giwa balle an jefe ta da kashi. Su Tasleem ba su da kirki, har gwara su Yassar a kansu, don su ba su kunyar ido, za su yi maka abin da suka so. Ki yi hakuri don Allah. Nima haka nake fama da su, don ma dai babu yadda suka iya da ni ne, Mamin na taka musu burki sosai a kaina." Jin haka ta ji ta sosamata inda yake mata ƙaiƙaiyi. Aikuwa ta kasa shiru sai da ta furzar. "Yauwa nikam Ummita, amma ba Mami ce ta haifeki ba ko?" Ummita ta yi dariya. "Kin gan ni ƴar baƙa ko?" Sai kuma ta gyaɗa kai ta ɗan sauya fuska alamar damuwa. "Ba Mami ce ta haife ni ba kuma ba Abba ne mahaifina ba. Mahaifina ƙanin Abba ne, mahaifiyata kuwa ƴar asalin garin Bichi ce, gaba ɗaya sun rasu ne a sanadiyyar gobara. Ni kaɗai ce rai da aka fitar a gidanmu ko kwarzane tun ina da shekaru biyar a duniya, amma daga su har ƙannena jarirai ƴan biyu duka sun rasu. Tun daga wannan lokacin ne, na soma rayuwa a hannun Kakarmu sai daga baya ne Abba ya maido ni gidansa ya damƙa amanata ga Mami. Matar da ta riƙe ni har zuwa yau ba tare da ta nuna bambanci tsakanina da nata yaran ba, kusan ince a zamanin dai samun irin Mami abu ne mai wahala. Ga kirki da son mutane, ke ba don dai kar nayi hauka ba zan iya ce maki Mami ta fi nunamin ƙauna da so fiye da nata yaran domin hatta da ragamar kula da ɗakinta da na Anna ni ta damƙawa. Ke daidai da shawara wani lokacin da ni take yi. Sai ta ture shawarar nata yaran ta ɗauki nawa." Jinjina kai Humaira ta yi, eh lallai kam Mami ta yi abin a yaba mata, a zamanin nan kafin a samu mai fifita ɗan wani akan nashi abu ne mai matuƙar wahala. "Wace ce Anna?" Humaira ta watsa mata tambayar.  Ta miƙe ta shiga rufe akwatin a lokaci guda tana ba ta amsa.      "Anna kakar su Tasleem, wacce ta haifi Mami. Ai anan gidan take rayuwa, a baya ma har da ƙanwar Mami da ba ta yi aure ba muka zauna. Amma yanzu Allah ya taimaka tayi aure tana zaune a can Misra da mijinta, ke kam ai Allah ya taimake ki ba za ki rayu inuwa ɗaya da ita ba. Don ta fi su Tasleem zafi da tsangwama, ke ta dai tsani duk wanda ba jininsu ba. Hatta da dangin Abba ba ta kaunar gani a gidannan, sai kuma Allah ya sa su ɗin ma ba su fiye zuwa ba." Humaira ta buɗe baki za ta yi magana kenan sai ga wani ƙaramin yaro cikin yara ƙananu uku da ta gani ɗazun ya shigo a guje. Masha Allah yaron kyakkyawa duk kuwa da cewar bai ɗau hasken Mamin sosai ba, ya fi yin kalar Abba, amma kuma hakan ma sai ya ƙara mishi wani kyan na daban. "Adda Ummi ku zo inji Mami." Ya kai ƙarshe yana nuna su duka biyum da yatsa, alamun dai mu biyun ake nema. Sai ma ya ba Humaira dariya. Suka miƙe a tare zuwa falon. Ko ɗaya ba abokan faɗan nata a ciki, bada ɗayansu ba sa nan sai Mami da yaran, sai kuwa ɗaya a cikin matasan nan na ɗazu kwance saman doguwar kujera ya toshe kunnuwa da earpiece. Suka ƙarasa ga Mamin, ta zauna a gefe a ƙasa. Duk yadda Mamin ta so ta hau kujerar ta ƙi, haka dole ta rabu da ita. Ummita ta kawomata abincin amma gaba ɗaya ta kasa sakewa balle ta ci, ƙarshe dole dai ɗakin suka yi da abincin bisa umarnin Mami. Nan din ma dai kaɗan ta ci ta ce ta ƙoshi. Hankalinta kuma ya koma ga Kawu da Abba, ba ta gaji da ganin Abba ba, ba ta kuma gaji da jin muryarsa ba. So take ta samu damar da za su yi doguwar hira da shi, tasan dai ba yau ba domin dare ya yi. Suna nan da Ummita tana ƙara ba ta labari akan zuri'arsu har lokacin sallar isha'i ya yi, koda suka idar kai tsaye falon Abba suka nufa sakamakon kiran da ya yi musu. Nan suka tarar shima Kawu har ya ci abinci ya yi wanka, hirarsu kawai suke yi da Abba wanda shima ya sha doguwar jallabiya ruwan madara. Har Humaira ta zauna kallonta yake da murmushi saman fuskarsa kafin ya maida duba ga Kawu ya girgiza kai. "Allahu Mai Halitta." Kawun shima murmusawar ya yi, ita kam sai ta yi kasa da kai. Zamansu ba jimawa sai ga Mami ta shigo ta lulluɓe jikinta da ƙaton mayafi. Sai da ta zauna ne ta dubi Kawu. "Umar, kwana da  yawa. Idan babu Fatima  a gidan shikenan kuma sai zumunci ya yanke? Dama kun raba ni da ɗiyata, toh dama ƙarshen alewa ƙasa, ka ga yau dai ungulu ta komo gidanta na tsamiya." Kawu ya yi ƴar dariya. "Hajiya Maryam kenan, idan dai kin yarda kin amince da komai lokaci ne, ba za ki ga laifinmu ba. Sai dai kamar yadda kika ce, na yi kuskure kuma na ji kunya da ban tashi zuwa ba sai bayan babu Adda Fatima, Allah ya gafartamusu. Ina kuma neman afuwa." Gaba daya suka amsa da amin.  Abba ya yi gyaran murya ya dubi Mami. "Ina yaran nan suka shiga ne wai?" "Su na can wurin Anna, na rasa me suke yi alhalin na sanar da su. Bar..." Ba ta ƙarasa ba sai ga su sun faɗo ɗakin kamar daga sama, babu ɗaya cikinsu da ya yi tunanin yin sallama. Yaron ɗazu ne da ya je kiranmu ya shigo a guje ya rungume kafaɗun Abba, wani da ya fi shi tasawa yana biye da shi a gujen. Sai kuwa su Tasleem da samarin nan uku. "Kai Muhsin, me ya yi maka ne?" Wanda aka kira Muhsin ya turo baki ya nunawa Abba bindigar ruwa da aka raba gida biyu. "Ba shi ne ya karyamin bindiga ba. Allah kuwa sai ya biya ni." Abba ya ja hannun karamin mai suna Waleed ya maido shi gabansa. "Haba Autan Mami, ya haka? Ba shi hakuri toh." Da dariya irin na yarinta ya furta kalmar sorry. Abba ya maida idanunsa ga su Tasleem waɗanda suka yi ɗare-ɗare saman kujera ba su ko gaisar da Kawu ba. Fuska ya ɗan ɗaure. "Ba ku iya gaisuwa ba ne?" Jin furucin Abban ya sa suja gaida Kawu ciki-ciki, ba tare da jin komai ba  ya amsa har da nema musu albarkar Allah. Babu wanda ya amsa da amin a cikinsu. Mami ta kalle su ta yi musu alamar su sauko ƙasa su zauna, ba a son ransu ba dole suka zaune a ƙasan kafet kamar dai yadda Humaira da Ummita suka yi. Sai dai Abba ya buɗe taron nasu da addu'a sannan ya gabatar da Humaira a wajensa. Ya kuma gargaɗe su da kar su kuskura ya ji wani zance na daban koda nuna bambanci ne. A karshe ya sa kowannensu ya gabatarwa da Humaira sunansa. Su tara ne cif, Mubarak ne babban ɗan Abban, shi kuwa yana ƙasar Ghana yana karatu, sai Dawud, Yassar, Ƙasim, Futuha, Tasleem, Raihana, Muhsin da autansu Usman da ya ci sunan baban Mami suke kiransa Waleed. "Humaira toh, yanzu dai ba wanda ba ki sani a ƴan uwanki ba ko? Sai babban yayanku shi kam sai ranar da ya samu hutu idan ya dawo sai ku gaisa. Ko kuma ma ina iya haɗa ku a waya wataran." Jin abinda ya fadi ya sa ta murmushi, ta gyaɗa kai tare da furta toh. Daga haka Abba ya sallame su baki ɗaya suka tashi. A wannan daren dai ba ta samu damar hira da Abbanta ba, ta koma ɗakin da ba ta kauna dalilin yadda suka kaya da masu ɗakin. Mami ta sa aka yi mata shimfiɗar katifa a ƙasa kafin nata gadon da sif ya iso, acewarta. Hakanan ta kwanta, mutanen ba su ƙara tanka mata ba musamman ma Futuha da ta sha ƙasa har lokacin ƙugunta na ciwo. Sun dai sha jinin jikinsu, sun kuma fahimci Humairar ba kanwar lasa ce ba itama. *** Washegari tun da asuba ta ga ƴanmatan ba su koma bacci ba, ita daman baccin safe ba ya daga cikin ɗabi'unta, a can ƙauyensu daga sun tashi to sannan za'a hau ɗora ruwan wanka da kuma abin kari, wannan dalilin yasa ta kwanta kawai tana kalle-kalle da saƙe-saƙen zuci. Tana kallo suka yi wanka har Ummita, kowannensu ya hau shiri. Ummita da Raihana cikin shigar uniform na makaranta, ita kuwa Tasleem shigar fararen kaya ta yi na ma'aikatan asibiti riga da wando da ɗan ƙaramin hijab. Sun mata kyau kwarai, gogar kuwa, wato Futuha, kayan gida ne jikinta, riga doguwa ta atamfa da ya ɗame ta ɗam ya fiddo da surarta. "Wai ke Futuha ni ban gane ba, ina mamakin yadda kike rawar ƙafa da jiki duk sadda aka ce kuna da English, ko uban me yasa oho." Faɗin Tasleem kenan sa'ilin da take ɗora agogo a tsintsiyar hannunta. Kafin Futuha ta yi magana, Raihana dake fesa turare a jikin uniform dinta wanda iri ɗaya ne da na Ummita, kalar fari da ruwan makuna dinkin riga da wando sai ɗan hijab da ya rufe kirji kaɗan, dariya ta yi ta amsa wa Tasleem. "Wai ke ba ki da labarin IBB Gusau? Tab, ai kusan kaf matan department dinsu sonsa suke ban ciremaki matan aure ba, toh itama har da ita a ciki, ba ki ganin kwalliyar ta daban ce." Futuha ta jefowa Raihana murfin man shafawa, Raihana ta kauce tana dariya. "Af, akwai ƙarya cikin maganata ne? Ke fa naji kuna hirar da wannan ƙawartaki me wuya kamar mariƙin lema, ni me ma sunanta? Yauwa Khalisat, kina wani koɗa shi kina cewa nan duniya shi kike so." A fusace Futuha ta nufo ta, Raihana ta sunkuci jakar makarantarta da waya a gefen gado ta fice daga dakin da sauri tana dariya. Itama Tasleem dariyar ta yi. Ummita kam dama ta fice daga dakin tun da ta zura uniform, dakin su Muhsin ta wuce don yi musu shirin makaranta. Humaira lumshe idanunta ta yi tana ji suna faman hira tsakanin Tasleem da Futuha inda Futuha ke kara jaddada dagasken dai tana son Ibb Gusau. "Ke malamin fa ƙarshe ne wallahi, ya haɗu ba zan nuna masa komai ba. Nidai fatana Allah yasa ya karɓi tayina ya aure ni. Wallahi zan jure dukkan wulakanci muddin zai yarda ya so ni. Yau in sha Allahu sai na nemo lambar wayarsa." "Lallai, kina ruwa kusa da breaker." Cewar Tasleem. Fuska dauke da damuwa Futuha ta amsa. "Ai na yi nisa ma cikin ruwan Tasleem, ki dai yi fatan kar Allah ya jarabceki irin yadda ya jarabtan." Tasleem cike da mamaki ta ce. "To tsaya, don iskanci kwanakin nan da wa kike waya kike kashe murya kina furta kalaman so?" Yamutsa fuska Futuha ta yi. "Mujahid ne, wallahi akan dole nake kula shi, shi ke fa taya ni da attendance da ma test. Kinga kuwa dole ce ta haifar da shiga lamarinsa. Ɗan taya ni na ci jarrabawa ne." Suka sheƙe da dariya. Ba jimawa suka fice zuwa falo. Ita Tasleem nursing take karanta duk ta fi su kwakwalwa da basira, tana da kokari sosai shiyasa wasu lokutan take samun alfarma daga Abba koda zai yi hukunci ba ya tsaurara mata, yayinda ita kuwa Futuha ke karantar Mass Com, ba laifi tana da kokari sai dai matsalar tun zuwan wani matashin malaminsu makarantar ta susuce ta zama shiritacciya. Wannan yasa lokaci guda ta kwaso C.O a zango na biyu a aji na biyu a makaranta, hakan ba ƙaramin ɓata ran Abba ya yi ba. Shi mutum ne da ya tsani asarar kwandalarsa a abinda ba zai kawo mishi ribar komai ba sai asara, hakanan mutum ne mai son abin hannunsa sosai, dakyar Mami ta shawo kansa ya aminta da tura Mubarak karatu, ya kuma ce daga kansa ya rufe, sauran kowanennsu sai dai ya yi a jami'o'in Kasarnan. Dawud na ajin karshe a jami'a inda yake karantar Accounting, Yassar wanda tare suke tafiya da Dawud din adalilin maimaicin aji da Dawud ya yi a sakandire, shi kam Bussiness ya ke karanta, su biyun tare suke da Futuha a jami'ar Bayero. Sai Ƙasim dake karantar fannin Kasuwancin shima dai inda yake aji na uku a jami'ar Maitama Sule Kano. Wannan kenan. Humaira jin ɗakin ya yi shiru ta buɗe idanunta, ajiyar zuciya ta saki tana mai jinjina wannan rayuwa ta Futuha, shakka babu ta ɗorawa kanta wahala, koda dai faɗan da ba ruwanka, daɗin kallo gareshi. Mikewa ta yi ta nufi banɗakin bayan ta ɗauki zanin wankanta da brush. Sai da ta wanke jikinta tsaf kafin ta fito ta soma shiri cikin doguwar rigarta ƴar kanti ruwan madara, tana daga cikin suturun da Kawunta ke siyamata. A dai fannin sutura daidai gwargwado itama tana da su, sai dai ace ba wasu masu tsada ba ne, ba kuma masu kyawun gaske ba ne idan an haɗa da na su Tasleem da ta gansu a jikinsu a kwana ɗayan nan. Tana cikin kwashe shimfiɗarta sai ga Ummita ta shigo da sauri, ganinta ta saki fuska sosai. "Au Humaira ashe kin tashi, kinga mu ma makaranta za mu wuce. Mami tace idan kin kammala ga abin kari can an rufemaki a kicin, idan ma ba ki gani ba ki tambayi Ladidi mai aikin Mami tana falon tana gyara." Duka wannan zancen tana yi ne lokaci guda da sauri tana bincike dirowarta, littafi ta zaro ta dauki jakar makarantarta sai safarta a hannu da takalmi ta kama hanyar fita. "Toh, sai kun dawo." Faɗin Humaira, Ummita ta amsa ba tare da ta tsaya ba sakamakon hon din mota da ake faman dannawa. Ganin haka yasa Humaira ƙarasawa jikin windon wanda ake iya hango farfajiyar gidan, ganinsu tayi gaba ɗaya a motar sai Tasleem dake tsaye a waje rike da ƙugu, Ummita na karasawa ta hau ta da masifar wai tana ɓata musu lokaci. "Allah ya baku hakuri." Ta ji Ummitan ta fadi sannan ta shige motar da sauri, tsaki Tasleem ta ja ta bita da harara sannan itama ta faɗa ciki, direban ya ja suka fice. Ajiyar Zuciya Humaira ta saki ta bar jikin windon, mamaki fal a ranta na ɗabi'un ƴan matan. Ta lura ba su san wani abu wai shi kara da mutunci ba, haka dai ta ture zancensu ta hau gyaran ɗakin. Abin ban haushi a saman gadon Futuha daidai da ɗan kamfenta da ta cire anan ta bar shi a ajiye, aikuwa haka ta tsallake gadon, ba ta yi karambanin gyara musu gadajensu ba, da ace dai Ummita ba ta gyara nata ba to tabbas wannan kam za ta gyara mata, ita din mutum ce mai mutunta DAN ADAM. Fita waje ta yi, falon babu kowa hakan yasa ta nufi hanyar kicin da ta nakalceshi tun jiya da Ummita ta tattara kwanukan abinci ta nufi ciki. Anan ta iske wata mata da ba za ta girmi Mami ba tsaye tana goge gas nan ta fahimci ita ce Ladidi. Ta gaisheta a ladabce, matar ta amsa fuska a sake. "Baƙuwarmu Humaira ko? Sannunki da zuwa, ga abin karinki can." Ta fadi tana nuna mata wani tireda aka ɗora filet da kofi sai kayan shayi da flask a kai. Humaira ta murmusa. "Nagode, amma zan sharo dakin sannan na ci." "Ai da kin bar shi, idan na kammala da nan sai na share." Girgiza kai Humaira ta yi. "Babu komai kar ki damu zan yi ai ba wani girma ne da dakin ba." Ladidi ta amsa da toh gami da yi mata sannu. Tsintsiyar ta nunamata da makwashin shara, ta dauka ta nufi dakin. Sai da ta kammala tas kafin ta koma ta wanke hannu ta dauki abin karin ta koma daki don ba ta jin za ta iya ci a falon. Bayan ta kammala ne ta fito da niyyar maida kayan kicin suka yi karo da Ladidi. "Yauwa, ki je inji Alhaji wai za ku yi sallama da Kawunki zai wuce." Ladidi ta karɓi kayan hannunta ita kuwa jin haka jikinta ya yi sanyi, ta koma dakin ta dauki karamin mayafinta ta yafa a kai. Falon Abban ta nufa, Kawun ne kadai a ciki ya yi shiri tsaf na tafiya, sallamarta ya sanya shi dubanta. 03 Ta durƙusa ta gaida shi, ya amsa sannan ya ce. "Toh Shatu, ni zan koma. Ina fatan zaman nan zai maki dadi fiye da rayuwar da kika yi a Maine. Ina kuma roƙonki da ki zauna da kowa lafiya, kamar yadda suka karɓeki da hannu bibbiyu, kema ina son ki rike su haka. Gidan mahaifinki ne, nan ɗin dai shi ne gatanki, ba ki da sama da nan. Sannan don Allah ki zama mai hakuri, na sanki sarai muddin aka taɓo ki ba  kya kai zuciyarki nesa. Abu na gaba, kar ki sake ki bada kofar da za'a ga wallenmu, a ga kamar mun gaza a wurin ba ki kyakkyawan tarbiyya a iyaka zaman da kika yi hannunmu. Sannan addu'a, ki yawaita addu'a da ibada in sha Allah sun ishe ki." Humaira wacce tuni fuskarta ta yi jage-jage da ruwan hawaye ta sa hannu ta share su. Gani take yi tamkar shikenan fa za ta yi nesa da asalin garin da aka haifeta, shi kenan ganin Kawu da Tanti Hafsatu matarsa  zai yi wuya a gareta. "Nagode Kawu, in sha Allahu zan kiyaye abin da ka ce. Amma ai Abba zai dinga bari na naje maku wataran ko?" "Me zai hana na bar ki Mamana?" Jin maganarsa gaba daya suka dub shi, sam ba su san ya shigo falon ba balle kuma tsayuwar da ya yi a bakin  ƙofar da za ta sada shi da sashinsa na ainahi.  Ya karaso da murmushi saman fuskarsa ya zauna, ta gaishe shi, ya amsa. "Ban maki alƙawarin nan kusa ba, amma da yardar Allah duk sadda na tashi aurar da ke, zan kai ki har Maine ki kwana biyu. Nidai fatana yanzu shi ne  ki saki jikinki ki zauna da mu bisa kauna. Kin ji ko?" Ta gyaɗa kai tana murmushi mai dauke da kunya jin wai Abbanta ya ambaci aure. Ita duka nawa ma take yanzun a shekarunta goma sha huɗu? Koda dai, akwai sa'anninta su Murja, Fatsima da ma sauransu wadanda duka an aurar da su a can. Tashi tsaye da Kawun ya yi ne ya maido ta hayyacinta. Ta mike itama, Kawu suka yi sallama da Abba. Daidai nan Mami ta shigo da sallama, tana sanye da dogon hijabi har ƙasa, gaida Kawu ta yi sannan ta yi mishi sallama. Sai a sannan Humaira ta gaishe ta. Humaira ta takawa Kawu har wurin motar Abba inda direban Abban zai kai shi tasha. Tana hawaye haka ta tsaya har Kawun ya shiga motar, hannu ya ɗago mata itama haka har suka fice daga gidan. Ji ta yi zuciyarta ta yi wani irin tsinkewa, haka kurum ta ji wani irin tausayin kanta ya kama ta. Kanta Abba ya dafa da muryar rarrashi ya ce. "Haba Mamana, kukan fa? Ya isa haka, ba fa rabuwa ku ka yi kenan ba, in sha Allahu zumuncin ba zai yanke a nan ba matukar akwai rai da lafiya,  ki kwantar da hankalinki nan ma gidanku ne." Ta gyada kai, daga haka suka shige gidan. Mami dake tsaye a windon falon tana kallonsa, itama juyawa ta yi ta koma ɗakin Abban hawaye a saman fuskarta wanda ita kaɗai ta bar wa kanta sanin ma'anarsu. A falon Abban suka zauna yana fadin. "Bari dai nayi hira da ɗiyata kafin na fita aiki ko?" Ta yi murmushi har sannan yatsunta na saman fuska tana goge ruwan hawaye. "Ba ni labari toh, meyasa ba ki shiga makarantar boko a can ba? Kawunki dai ya cemin kina zuwa islamiyya har kin yi sauka, na kuma ji dadin hakan." Ta gyara zama ta amsa a nutse. "Dada ce ta ce ba zan je ba saboda koda na fara ba lallai na ƙarasa ba. Ta ce kuma faransanci ne." Abba ya yi shiru, ya gane sarai manufar Dada, wato dai ta san cewa ko ba jima ko ba dade ranar nan za ta zo da Humairar za ta dawo hannunsa, sai dai ya so ace ko na faransancin ne ta yi, da irin haka biyu babu. Ya tuna shawarar da Mami ta ba shi a daren jiya da suke maganar karatun Humairan. _"Zai fi dai ka sanya ta a inda za ta koyi sana'a koda kuwa na girke-girke ne, kasan can idan ma ta yi karatun faransanci ne, nan kuwa turanci ake. Zai iya ba ta wahala."_ Toh shi ɗin ma dai ya ga hakan ya fi mishi sauƙi, yanzun ma dubunnan da yake fitarwa na karatun yaran kaɗai sai godiyar Allah kawai, ina kuma da ace ya sanya Humaira wacce ya tabbatar kafin ta fara sai an yi mata lesson a gida sosai, ɗaukar karatun ne ma abin tunani, bai san ya kaifin kwakwalwarta yake ba. "Abba." Ya tsinci muryarta wanda  hakan ya katsemishi tunani. "Na'am Mamana." "Abba meyasa ba ka taɓa zuwa ka gan ni ba? Meyasa ko a waya ba ka damu da kira mu gaisa ba idan ma aiki ne ya tsare ka?" Ya tsare ta da ido, yanzun ya gama raina kaifin kwakwalwar yarinyar, sai dai ya sha mamakin tambayoyinta duk kuwa da ya sani lallai ne dama watarana ta yi mishi su. Sai dai bai tsammace su nan kusa ba. Dogon numfashi ya ja ya furzar. "Kiyi hakuri Humaira, eh na yi maki laifi amma hakan ba wai yana nufin ban damu dake ba ne. Sai dai nayi hakan bisa alƙawarin da na ɗaukarwa mahaifiyarki wanda hatta da bayan mutuwarta ban karya shi ba." Cikin sauri ta ce. "Wane alƙawari?" Ya yi shiru sai kuma ya ɗago da niyyar magana, muryar Mami ta katse hanzarinsa. "Wai nikam dai yau Abban yara ba ka da niyyar fita ko? Gashinan har goma ta gota." Suka dubeta, a ɓangaren Humaira ji ta yi gaba ɗaya zuwan Mamin bai burgeta ba, sai da aski ya zo gaban goshi tana shirin ta san ta ya ya aka haihu a ragaya lokaci guda kuma Mami ta yi mata katsalandan. Mami kuwa ganin hankalin Humaira ba ya kanta sai ta girgizawa Abban kai cike da damuwa. Abba shi din ma jinjina kan ya yi, ya fahimci manufarta. Don haka ya dubi Humaira da murmushin yaƙe. "Af, kinga na sha'afa har lokaci ya ja, kar ki damu Mamana, muna tare ai yanzu, a kowane lokaci idan na samu dama da kaina zan yi kiranki mu yi hirar nan kin ji ko? Yauwa Maminki ma ta ba da shawarar a sanyaki a makarantar koyon girke-girkenku na zamani, ina fatan za ki so hakan?" Duk da yanayin rashin jin dadin da take ciki sai da ta yi farin ciki da hakan. Dama tana da son girki, ko a can gida ita ke yiwa Dada dahuwa daga lokacin da ta soma zama budurwa. Ta kuwa saki fuskarta har wushiryarta na fitowa muraran. "Eh Abba ina so." Abba ya dubi Mami suka yi murmushi, Mamin ta karaso ta dubi Humaira. "Yauwa ƴar Abbanta, kin ga da girki adon mace ce. Kuma na tabbatar za ki iya sosai idan kika mayar da hankali. Ana samun alheri sosai da girki. Kar ki wani damu idan ba ki yi boko ba, da yawa babu bokon amma sun samu ci gaba ta fanni da dama a rayuwarsu." Humaira ta jinjina kai, tabbas haka ne don ta ga mijin Mammati wata ƴar uwarsu a Maine, shi ma babu bokon amma yanzu kaf ƙauyen nasu babu mai kuɗinsa. Idan ya zo hutu da yaransa kowa sai ya san ya zo saboda alherin da yake yi musu. "Ki je ciki nasan zaman da kaɗaici ke kadai, ki sa Ladidi ta kunna maki kallo a wayarta sai ki yi." Ta fadi hakan saboda babu wuta, ƙa'idar Abba tun sha biyun dare ake kashe masa inji, sai ko idan aka ci sa'a Kedco sun hasko wuta.  Humaira ta fice a falon bisa bin umarni.  Bayan fitarta Mami ta ƙarasa ga Abba fuska dauke da damuwa. "Ya haka? Kana son ka karyawa yarinya zuciya daga zuwanta? Ko kuwa so ka ke ta riƙi mahaifiyarta da mugun zato a ranta alhalin ba ta ji ba ba ta gani ba? Don Allah kar ka fara, kar ka yi wannan kuskuren. Tabo ne da yaro kan yiwa gurguwar fahimta." Abba ya numfasa. "Hakane, sai dai ki sani ba karamin taimakona ki ka yi ba don ba ki da masaniyar abin da zan ce a sannan. Na gama iyakar nazari ban san ƙaryar da zan shirga don rufe zancen ba. Na gode maki mace ta gari." Ya karashe yana jifanta da murmushi, ta rausaya  kyawawan idanunta tana maida mishi martani. "Nima na gode da wannan yabon, muje ka shirya lokaci na ƙurewa. Idan ka dawo ni kuma kafin nan na bincika wurin wacce ya dace a kai Humaira ta fara daukar darasi." "Hakane, amma zan fi so ta gama shiga ta san ƴan uwana. Kafin a durfafi wannan." Mami ta ɗan yi jim sai kuma ta amsa da toh. Bayan shigar su ɗakin yana cikin shiri ta sanyo zancen kaya. "Ka ga ya kamata a ɗan ɗinka mata suturu ko ba yawa, mutumin da ya zo daga ƙauye na tabbata ba wasu kayan kirki ne da ita ba." "Ke dai wato burinki kawai na karya bakin aljihu, toh wannan na jikinta ba sutura ba ce? Kin fi kowa sanin ba na son kashe-kashen kuɗi ko?" Ta yi ƴar dariya, an zo wajen. Ai idan har batu na fitar da kuɗi ne toh nan suke kai ruwa rana, a karshe dai hakanan ta ke cin nasara a kanshi, kafin ya botsare akan jima. "Haba Abban yara, Humaira fa uwa guda ce, idan ba ka yi mata ba wa za ka yiwa?" Ta ƙarashe murya a narke kamar wata matashiyar budurwa, hakan ya tuna mishi zamanin tashen soyayyarsu. Ya yi dariya gami da girgiza kai. "Maryam kenan, ke kam ba a kayar da ke a magana. Shikenan idan na dawo zamu ga yadda za'a yi. Na fita ai ko?" "Eh ka fita kam, Allah ya kara buɗi." Ta ba shi amsa tana dariyar itama. Ya amsa da amin. ***   Washegari kuwa Mami da kanta ta bada aka siyowa Humaira atamfa da leshin sai kuwa kananun kaya dogayen riguna duka dai ba masu yawa ba, hatta da takalmin shiga taro ƙafa biyu da mayafai kala uku sai da Mami ta siya mata, ba kuma ta tsaya anan ba sai da aka haɗo da kayan shafe-shafen mata da na kwalliya da kuma undies. Abba ya kalli kayan sannan ya kalli Mami. "Yanzu dukkan kayan nan a dubu talatin?" Mami ta ɗan bishi da hararar wasa. "Au, ka yi zaton kowa irinka ne? Wannan dai ya fi ƙarfin abin da ka bayar, Mami ta cika ta siyawa ɗiyarta. Wanda ka bayar ma mun gode." Ya yi ƴar dariya. "Maryam mai halin girma, ai shikenan, wannan tsakaninku kun fi kusa. Allah ya saka da alheri." Ta amsa da amin.  Sannan ta umarci Ummita dake zaune wadda ita ce ta dauko kayan zuwa sashin Abban akan ta ɗauka ta ba Humaira na shafe-shafen, suturun kuwa ta sa a leda Humairar ga shirya su kai wurin telansu. Ummita ta amsa da toh, sannan ta kwashi kayan ta fice. A falon Mami kuwa, Tasleem ce zaune a gefe daga ita sai vest sai kuwa wandon makarantarta da ba ta cire ba, zaune take tana cin ɗan wake tana ba su Raihana labarin wata ƴar ajinsu Suhaima da kusan kullum ta Allah babu ranar da ba sa taɗinta. Sosai ta tsayawa Tasleem ɗin a ƙoƙon rai, a cewarta yarinyar ta fiye rawar kai, ga nunawa sauran ɗalibai kamar ta fi uban kowa ƙoƙari. Tasleem ta cusa loma a bakinta sannan ta dube su. "Kun san yau wallahi ta ci arzikin Babandi da ya shiga tsakaninmu amma da sai na gwabje bakinta. Ƴar iskar yarinya ta dubi tsabar idona ta ce wai ina mata katsalandan a harkokinta saboda kawai tana yin tutorial din sanya kai na ce ita kanta ba ta gane ba shikenan fa ta tasomin, su kuwa ƴan korenta su Teema Small saboda na taɓa Hajiyarsu me zuwa da mota nan suka goyi bayanta." "Ke dai Tasleem ina raba ki da nuna bakin cikinki a fili ga Suhaima, kin kasa ɓoyewa har sun harbo jirginki, ke ba ki iya kwantar da kai ba? Ai irinsu da sannu za ki shige mata har ta yarda dake ki zama aminiyarta, kika san wane Don ɗin za ki samu ta hanyarta? Ko kin mance cewa ubanta fa ya fi naki arziki, koda dai namun akwai sai maƙo." Faɗin Futuha tana ƙarashewa da murya a ƙasa gudun kar ta yi shuka a idon makarwa. Suka kwashe da dariya, shiru Tasleem ta ɗan yi sai kuma ta ce. "Ke kuma fa haka ne wallahi, don ba ki ga wani arnen gaye da ya taba zuwa wajenta a makarantar ba, wallahi ƙarshen dai haɗuwa ya haɗu, ba wai kyawun fuska ba aa, motarsa ma kanta abin a kalla ce." "Ahaf, to kin gani. Ai kinga kakarki ta yanke saƙa muddin ki ka samu irinsa. Bare ma yanzu da Abba ya yi sanyi da batun auren, da ace ban da Mami ta shawo kansa ya bari ai da yanzun mun haihu. Taɓ ni nasan da yarana biyu." Suka yi dariya, hankalinsu ya koma ga niƙi-niƙin kayan da Ummita ta shigo da su daga bangaren Abba. "Ke." Cewar Futuha. Ummita yarinya mai sanyi da hakuri, ta juyo ta kalle ta. Da yatsa ta nuna ledojin kafin ta ce. "Wannan fa? Daga ina zuwa ina?" Duk da tambayar ta rainin hankali ne, amma ta amsa. "Aiken Mami ne, ta ce a kai wa Humaira." Daga haka ta ci gaba da tafiya, dukkan su ukun ba wacce ta tanka sai faman furzar da hucin ɓacin rai da baƙin ciki. Can sai Tasleem ta ja tsaki tana ture kwanon da ta ci ɗanwake da ƙafa. "Mami! Mami!! Wallahi ban taba ganin uwa irin tamu ba wacce ba ta damu da lamarin yaranta ba. Kunsan Allah, ba don kamanni da kuma Ann dake ƙara ba mu tabbacin cewa ita din mahaifiyarmu ce dagasken ba da zai yi wuya na yarda." Cikin taɓe baki Futuha ta amshe zancen. "Uhum, kema dai kya fada. Ai shiyasa nake so mu samu mazan kece raini da za'a kalla a ƙara kalla. Ko ba komai za mu huta da baƙin cikin Abba da Mami." Tsaki Tasleem ta ja ranta na zafi, sai dai ta kasa magana karshe kawai ta mike ba ta ko kara kallon kwanon ba kuma babu niyyar ɗaukewa. Bayan wucewarta kallon Futuha ya koma kan Raihana wacce ta maida hankalinta ga waya tana  murmushi. "Ke kuma ke da wa? Mu gani." Raihana kamar wacce aka tsikara ta mike tana ja baya da dariya. "Toh sa ido, ina ruwanki da wayata?" Futuha ta taɓe baki. "Kya ji da gulmarki dai, kullum latse-latsen waya, wayarki ta munafukai babu wanda kika taɓa bari ya ga meke ciki. Ni ban san irinki ba, ko hoto za ki nunawa mutum sai dai ya kalla haka tana dunkule hannunki kamar wacce za'a sacewa." Raihana na dariya ta yi hanyar waje gami da fadin. "Eh ɗin dai, wasu ma ba a san me suke shukawa ba. Gwara ni ko failed ban taɓa samu ba sai ku masu C.O." Futuha ta yi kwafa kawai tana huci, zafi biyu ya haɗe mata. *** Murna sosai Humaira ta yi da wannan kyautar ban girman. Ta ɗaga wata riga ja mai adon fulawa ruwan madara tana mannawa a jikinta. Haƙora a buɗe ta dubi Ummita. "Kinga kamar Mami ta auna, daidai da ni." Ummita ta yi dariya. "Eh mana, sai ki sa hijabi su na falon Abba kiyi musu godiya. Kinsan Allah, Mami tana ban mamaki. Wai fa har cikawa ta yi da kudinta ta ƙarasa yi maki siyayya, nidai ban taɓa ganin mace mai kirkinta ba." Humaira ta jinjina kai tana murmushi cike da gamsuwa da zantukan Ummita. Tabbas itama a farko ta yiwa Mamin gurguwar fahimta, amma yanzu kam ta ga saɓanin tunaninta. Sai kuma da sauri ta dubi Ummita. "Wai anya ban yi wauta ba? Kin ga ban je na gaida Anna ba tun da na zo." Ummita ta ɗan yi shiru alamar damuwa, har dai Humaira ta ce. "Lafiya kika yi shiru?" Girgiza kai ta yi. "Anna fa ba ta wani murna da zuwanki, ta cewa Mami koda wasa kar ta sake ta turo ki ɓangarenta. Ki share kawai, ni nasan Mami za ta shawo kanta, kuma tunda kuna tare a gidan dole watarana ku haɗu ai. Zance ne kawai irin na Anna. Kinga jeki ki yiwa su Abban godiya mu wuce, yamma na yi." Humaira ta gyada kai kawai ta numfasa, dama ba dole ne kowa ya ƙaunaceka ba. Ba tare da damuwa ba ta zura hijabin ta fice a ɗakin.04 Humaira ta ware idanu tana ƙarewa garin Kano kallo a hanyarsu ta komawa gida bayan sun kai wa telan Mami dinkunan an kuma auna ta, sosai akwai bambanci da inda ta fito koda dai dama ita din a ƙauye take. Sai dai kuma hatta da titunan garin burgeta suke yi. Ummita ta kalleta ganin yanda gaba ɗaya hankalinta ke a waje, murmushi ta yi. "Humaira kenan, idan dai garin nan ne har sai kin gaji da shi ina tabbatar maki." Jin haka sai ta yi dariya. "Anya kuwa? Nidai sosai ya burgeni wallahi. Ji nake tamkar kada mu koma gida." Dariya Ummita itama ta ɗan yi. "Shiyasa ai na ce a bi da mu ta wannan hanyar ba ta farko ba, kinga sai ki ƙara kalle garin sosai ko?" Jinjina kai Humaira ta yi tana murmushi sannan ta jefo mata tambaya. "Ni kuwa yar uwa su Abba su nawa ne a wajen Umma? Umman na raye?" "Umman su Abba tun ina firamare, yaranta uku kawai Allah ya ba ta daga nan ba ta ƙara haihuwa ba sai ko yaran ƴan uwa da ta riƙe ta aurar. Kinga Abba shi ne babba sannan Babana, sai autar ɗakinsu Baba Amina, ita a can gadon kaya take zaune da mijinta. Kuma Kakanmu wanda ya haifi Abba shi ya riga ma Umma rasuwa, ita kadai ce matarsa har ya bar duniya. Kar ki damu kedai, tun da kika zo garin nan babu gidan da ba zamu je ki ga ƴan uwanki ba in sha Allahu." Murmushi ya suɓucewa Humaira har ta ɗan lumshe idanu ta buɗe su, ranta ya yi fari sol, burinta ya cika. Yadda ta san kaf ƴan uwan Mamarta, yau Allah ya nufa za ta san na Abbanta. Haka suka karasa su na tafe Ummita na mata nuni da wuraren ƙayatarwa a garin. ***     Dattijuwar mace ce hakimce saman kujera ta haɗe girar sama da ta ƙasa. Banda tsufanta da ya fito muraran, kallo ɗaya idan ka yi mata za ka ga tsantsar kamannin da ta yi da Mami har ta so ta fi Mami hasken fata. Ta gyara zama gilashinta gami da amsa sallamar da Mami ta yi mata ciki-ciki. Anna sam ba ta iya ɓoye abin da ke ranta wannan ya sanya a kallo daya Mami ta gane fushi take da ita. Da harshen buzanci ta ce. "Anna yanzu zancen nan ba zai wuce ba? Ina ce na yi maki bayanin komai?" Anna da sai a sannan ta dubeta ta ba ta amsa cikin yare don ba kasafai take yin hausa ba, kaɗan-kaɗan take ji. "Ki ka ce bayani? Yanzu ke har kina tunanin zan gamsu da bayananki na wofi Maryam? Kina da masaniyar irin wahalar da aka ci a baya? Wato ke dadi miji ko?" Mami gaba ɗaya ta dube ta fuskarta duk a jagule. "Haba Anna, idan ban godewa bawan Allahn nan ba  bai kamata na watsa mishi ƙasa a ido ba. Mutumin da ya amince na zauna tare da ku, muke rayuwa. Duk da irin son abin hannunsa, hakan bai sanya shi watsi da lamarinki ba. Duk wata kulawar da mai shekarunki ya dace ta samu, babu ɗaya da ya taɓa nuna gajiyawarsa wajen yi. Toh mene ne aibu a ciki don ɗiyarsa guda ɗaya ta zauna a hannuna?" "Shashashar banza da wofi, dama nasan ba alheri ne zai fito a bakinki ba. Wato dai gori za ki yimin ko? Dama nasan akwai ranar ƙin dillanci ai, dadin abin da baza  ta kike rawa. Shikenan zan sa maki ido na ga inda wannan rashin hankalin naki zai kai ki. Kin fi kowa sanin wahalar da aka sha a baya ai." Mami dai ba ta ce komai ba, ta so a bar maganar a sanyo wata amma sam ba ta samu fuska wurin Anna ba dole haka ta miƙe ta kama hanyar barin ɗakin, daidai ƙofa ta ɗan dakata kafin ta juyo ta sakarwa Anna wani murmushi da ita kanta Anna ya ba ta ɗumbin mamaki da baƙin ciki, to wannan sabon raini ne ya gifta tsakaninta da Maryam din ko kuwa dai kishi ya taɓa kwakwalwarta tun a shekarun baya? Haka Anna ta cigaba da saƙe-saƙenta da babu mai warware mata. ***   A kwana a tashi babu wuya a wurin Allah, har a yau Humaira ke cika sati uku cif a garin Kano. Abubuwa da dama sun faru na alheri a rayuwarta da suka rinjayi sharrukan ciki. Ɗaya daga ciki har da ƙarin suturu da ta samu, sai kuwa gadonta da sif din kayanta da Abba ya sa aka yi mata. A gefe guda Abba ya mallaka mata wata ƙaramar waya ƙirar Vivo sai dai tana yin whatsapp, kuɗin wayar dai dakyar suka  fito daga aljihun Abban nan ma sai da Mami ta sha fama har ta nuna ɓacin rai ƙarara, a duniya kuwa babu abin da Abba ya tsana kamar ganin Mami ta sauya mishi, nan da nan take cin galaba a ka sa muddin buƙatarta bai shallake tunaninsa ba.   Ummita ta yi mata rakiya wurin dangin Abbansu na kusa, sun yi murna kwarai da ganinta. Sun kuma karɓe ta da hannu bibbiyu, babu abin da ya fi faranta ran Humaira irin shaidar kirki da suka yiwa mahaifiyarta. Ta kuma ji dadin hakan ba kaɗan ba. Rashin abin yi ne ya sa kusan koyaushe idan ba ta komai tana kan wayar tana danne-dannenta ganin ta riƙe abubuwan da Ummita ta koyamata tunda dai harshen turanci ne, ta kuma sani koda faransancin aka mayar ba za ta tsinci abin kirki ba. Abba ya sanya mata lambar Kawunta, sun gaisa sau ɗaya ta waya don ita kam ko whatsapp ma cewa Ummita tayi kada ta buɗe mata, ba ta ga wanda za ta yi hira da shi ba. Ta dai gwammace ta kunna rediyo ta yi ta saurare don hatta da waƙoƙi iri-iri na soyayya da Ummitan ta sanya mata ba ta damu da su ba.   A wannan yammacin kamar koyaushe tana zaune a ɗakinsu gefen gado ta buɗe labule iska mai daɗi na dukanta, garin wuni aka yi cikin zafi yanzu kuwa sai ya ɗan huce. Rabin hankalinta yana ga farfajiyar gidan inda take hango Yassar tsaye da abokinsa wanda ta ji ana kira da Affan su na hira, a gefe ɗaya Muhsin ne da ball yana wasansa tare da Waleed, daidai nan Futuha ta buɗe gidan ta shigo, dawowarta kenan daga makaranta, Humaira na lura Affan na mata magana ko kallonsa ba ta yi ba, daga yanayin tafiyarta za ka fahimci ba a nutse take ba, har ta gifta hankalin Humaira na kanta, ta san dai babu lafiya, tana kuma fatan ba gurguwar shawarar da ta ji jiyan wata aminiyarta Aina'u da ta zo tana ba ta ba shi ta gwada a yau ɗin, gabanta ya faɗi. Ba ta mance kalaman da suka fito daga bakin Aina'un bayan Futuha ta gama amayar mata da damuwarta akan mahaukacin soyayyar da take yiwa Ibb Gusau.    _"Ke ki na ban mamaki wallahi Futuha, ki na da kyawun da babu namijin da zai kalleki bai ƙara ba. Da ace ni ce ke, wallahi babu abin da zai hana na kai wa Ibb Gusau kaina. Kina da sura irin wadda da zarar kin tallata mishi kanki zai ji nan duniya babu wata sai ke. Ke idan ma wannan bai yi ba, ki zo na raka ki wurin Malam Aci Bulus, na rantse maki ko me kike so za ki samu. Ke wallahi sai kin mallaki malamin nan kin juya shi kamar waina a tanda."_ Gaban Humaira ya yi wata iriyar faduwa, ta ambaci Allah a ranta, ta yi nisa da saƙe-saƙen zuci ta ji an banko ƙofar ɗakin an shigo, ta juyo da sauri, Futuha ce. Ba ta ko lura da ita ba ta kife a saman gadon Tasleem tana kuka har da sheshsheƙa. Humaira ta yi shiru, kafin ta lalubo abin faɗi duk kuwa da cewar ba shiga sabgar juna suke yi ba, Tasleem ta shigo ɗakin da sauri a bayanta kuma Raihana. Za ta soma magana amma idanunta na sauka kan Humaira ta fasa, cikin haɗe rai ta ce.   "Malama ba mu waje za mu yi magana." Jin haka tsam, Humaira ta miƙe ta kama hanyar barin ɗakin, bayan fitarta Raihana ta karasa ta rufe ƙofar har da sanya muƙulli sannan ta dawo. Futuha suka ɗago su na magiyar ta sanar da su abin da ya faru. Dakyar ta iya tsaida hawayenta ta shiga ba su labari. "Ai na faɗamaku yadda muka yi da Aina ko?" Suka gyaɗa kai duk sun ƙagu su ji komai. "Shi ne..shi ne.." Sai kuma ta yi shiru ta rasa me ma za ta ce. Tasleem ta zaro ido. "Shi ne me Futuha? Kada dai ki cemin kin gwada aiwatarwa?" Futuha ta runtse idanu gami da shafa gefen fuskarta tana kuka sosai. Sai a sannan idanunsu ya kai ga gefen fuskar, ya yi ja ya yi ruɗu-ruɗu alamun dai mari ta sha. Koda alama ma ba guda ɗaya ba.  Ba ta bari sun nemi ba'asi ba ta cigaba da maganarta. "Na iske shi zaune a ofishinsa shi kaɗai yana aiki a system, koda na shiga bai ɗaga kai ya kalle ni ba, daga motsawar leɓɓansa na gane ya amsa sallamata. Duk da cewa gabana na faduwa hakan bai sa nayi ƙasa a gwuiwa ba na karasa ga teburinsa. Na sauke mayafina yanda rabin kirjina ya bayyana, na shagwabe murya ina mai batun ban gane abin da ya koyar a aji ba. Koda naga bai kalle ni ba, sai na yi gangancin kai hannu saman nasa, shi ne ya gaggauramin tagwayen maruka a kuncina. Ya kum rantse idan na ƙara shiga ofishinsa sai ya ɓalla ni kuma daga kaina masu tunani irin nawa za su dawo hayyacinsu." Tana kaiwa nan ta ci gaba da kukanta. Tasleem da Raihana kusan a tare suka sauke ajiyar zuciya. Raihana ta ja tsaki. 'Kema dai Futuha wataran kina abu kamar Waleed marar wayo wallahi. Ke kin manta tun farko itama Aina'un sonsa take yi wai? Ko don ta ɓata ki a wurinsa ku yi biyu babu kinga ai za ta ba ki gurguwar shawara. Ai mun faɗamaki amma ke idanunki ya rufe." Tasleem ta amshe. "Yanzu shikenan koda ace wannan mutumin na ganinki da mutunci kin ɓarar da shi, yadda za'a yi ki gyara ma nikam ban sani ba. Kada dai garin gyaran a ƙara jagula abubuwan shi nake tsoro. Ke!!! Wai don uwaki shi kaɗai ne namiji a duniya ma? Aikin banza kawai! Ga samari ƴan kasuwa da ƴan bokon su na matowa a kanki a instagram amma kin tsaya biyewa wani so, so, ke fa kike ban shawarar na shigewa Suhaima don na samu na yi mata koda snatching ne, amma ke nan kin tsaya ɓata lokaci akan wani kuturu gurgu." Jin haka ran Futuha ya ɓaci, ta harari Tasleem kafin ta ja tsaki. "Da ace kun san mene so da duk baku ɓata bakunanku ba. Sannan Ibb Gusau lafiyayyan mutum ne kar ki kara aibata shi. Tunda kuma ba ku da shawarar da za ku ban, ni nasan me zan yi." Tana kai wa nan ta miƙe ta yaye mayafin ta faɗa banɗaki ba tare da ta amsawa Raihana da ke jefomata tambaya akan abin da za ta aikata ba. ***   Mami ce tsaye a farfajiyar gidan ta haɗa cikin atamfa ruwan ƙasa mai adon fari, ta sha mayafi ruwan ƙasa hakanan takalminta. Ta dai yi kyau ƙarshe, idan ka kalle ta ba za ka ce ita ta haifi yaran ba saboda daidai gwargwado ta iya ɗaukar wanka. A gefenta Yassar ne su na magana yana ƙorafin shi dai mota yake so tasan yadda zata yi Abba ya siya mishi. Mami jinsa kawai ta ke yi tana yi kuma tana duban gate, da ta gaji ta ja guntun tsaki. "Wai ina Yakubu ya je ne? Daga jeka ka sha mai shikenan har yanzu bai dawo ba?" Yassar ya taɓe baki yana zura hannu a aljihun wandonsa. "Mami ina magana ba ki amsamin ba, koda dai nasan wannan halin na Abba zai wahala ma ya siyamin. Amma fisabilillah ina ɗan jami'a ina kallon abokaina har ma da matan da na raina su a makaranta su na da motocin kansu ni kuwa ko keke Abba ya kasa siyamin saboda mammaƙo." Ran Mami a ɓace ta dube shi. "Yassar ka shiga taitayinka, mahaifin naka kake yiwa waɗannan kalaman marasa daɗi? Toh ya yi maku mammaƙon, kai ai namiji ne, namiji kuma da nema aka san shi. Guminsa ne ya gina wannan gidan, ya kuma mallaka mishi motocinsa, kai ma ka yi zuciya ka mayar da hankali a karatunka watarana ba Abbanku ba, da kanka sai ka siyawa kanka motar, ba na son shirme. Ni kiramin Yakubu a waya ka ce ya yi sauri ya ƙaraso, ina Humairar take ne..." Ba ta ƙarasa zancen ba ta waiga, Humaira na tsaye a gefensu kasancewar su na magana ba su ko lura da ita ba. Itama ta yi shirinta tsaf cikin atamfarta koriya wacce tana ɗaya daga cikin ɗinkunan da aka yi mata. Ta yi kyau sosai, murmushi ta ɗan yiwa Mamin. "Mami na fito ai." Yassar ya ja tsaki ya bar wajen don takaicin Mamin da kuma na ganin Humairar da yake jin haushi da kishin tattalinta da iyayen nasu suke yi sai ka ce su ba ƴaƴa ba ne, Mami na kwala mishi kira amma bai ko waigo ba sai amsawar da ya yi da ƙarfi. "Zan je na ɗau wayar ne na kiramaki Yakubun." Daga haka ya ci gaba da tafiyarsa, Mami ta girgiza kai fuskarta ɗauke da matsanancin damuwa. Sai jikin Humaira ya yi sanyi, wannan kalar zamantakewar mutanen gidan na ba ta mamaki, ace ƴaƴa ba sa ganin iyayensu da gashi, kowace magana ta fito a bakinsu hakanan za su watsa musu ba tare da taunawa ba, toh wace riba ake samu a hakan? Ita tunda ta zo ma ban da Ummita da Raihana sai Muhsin masu ƙokarin zuwa islamiyya, ba ta ga wani cikin su Tasleem na zuwa ba. Bar su dai da yawon gidan ƙawaye a ɓoye Abban bai sani ba. Itama dai Raihanan ba zama take sosai ba amma takan tsaya har a biya karatu da ita,  wasu lokutan sai dai ta ji tana amsa wayar zasu haɗu da wani saurayin idan ta fita makaranta.     A yanzu kuwa daga maganganun Mamin ta fahimci watakila Yassar kuɗi ya nema ko wani abin da bai samu ba ya faɗi abu game da Abban shi ne take goranta mishi. "Muje Humaira, ya zo." Ta amsa da toh ta bi bayan Mamin cike da jin tausayinta, kowace uwa na son ta ga nata na bin ta sau da ƙafa, amma Mami ba ta samu wannan biyayyar ba na yara. Daga manyan har ƙananan, koda dai ta ji Ummita na cewa shi dai babban ɗan nasu ya bambanta da sauran, kuma su na masifar shakkarsa, akwai abubuwa da dama wanda idan yana nan ba sa aikatawa. Ta ce daidai da hantarar da suke yi mata idan har yana nan ba sa yi. Har dai suka soma tafiya a titi tunane-tunane take yi, hankalinta jiya bai kwanta ba sai da ta tsinkayi Tasleem na hira da Raihana su na tsokanar Futuha akan marin da ta sha har su na faɗin gobe ma ta ƙara. Daga baya dai ko don tana ɗakin ne sai suka juye harshe zuwa turanci, ta lura ba su fiye yin buzanci ba su kam, a yadda Ummita ta ce ma, ba komai suka iya faɗi a yaren ba, sun dai fi ganewa idan an musu magana ba su iya mayarwa yadda ya kamata ba. Wannan sai babban yayansu. Shi dai yana ji sosai. Daidai wani babban gida motar ta tsaya, suka fito suka nufi ciki. Kyau da tsaruwar gidan har ya so ya kere na su. Da murmushi Mami ta dubi Humaira lokacin da suka shiga farfajiyar gidan. "Gidan aminiyata kenan Hajiya Lubna, ita ce za ta kai ki wajen koyon girki. Ƙanwarta ke yi." Humaira ta gyaɗa kai ranta ya yi fari sol, ta san dai Mamin ta ce ta shirya zasu je unguwa amma ba ta kawo a rai fitar ta shafe ta ba. Daidai za su shiga babban falon suka yi karo da ɗan Hajiya Lubna shi kuma zai fito, matashin saurayi mai jini a jika, ya sha ƙananun kaya abinsa ya yi tsaf. A fuska ba za ka kira shi da kyakkyawa ba sai dai hutu da jin dadi ya sa fatarsa murmurewa. Gaisawa ya ke da Mamin amma hankalinsa kacokam na ga Humaira wacce daga kallo ɗaya da ta yi mishi ta kauda kanta don ita kam a duniya ta tsani kallo. Mami na lura da yanayin kallon da yake jifan Humairar da shi, ita kanta bai mata ba don haka don ta katse shirun ta ce.   "Hajiyar dai na ciki ko? Don na san ta yanzu sai ta iya ficewa ta bar ni zaman jira." Dariya ya ɗan yi yana shafo ƙeyarsa. "Tana ciki Hajjaju. Ku shiga kafin na shigo." Ta amsa mishi ta yi gaba Humaira ta bi bayanta da sauri har tana tuntuɓe saboda kallon da yake bin ta da shi. Mami ta kalleta kawai ta kauda kai ba ta ce uffan ba. A falon gidan suka iske ƴan mata da yara ana kallo ana hira, wuta tarr a gidan madadin gidansu wanda idan har ba wutar Nepa aka ci sa'a suka kawo da rana ba, zai yi wahala ka ga hasken fitila a gidan sai Magriba zuwa ƙarfe sha biyun dare. Gaba ɗayansu suka gaida Mami, ta amsa. Ta dubi Humaira. "Ki zauna ki jira ni bari na ƙarasa wajenta." Ta amsa da toh ta nemi wuri ta zauna. Ta lura gidan dai ƴan boko ne, ba su ko damu da ita ba sai mai aikin gidan da ta miƙe ta kawo mata ruwa da lemu ganin da ta yi tare suke da aminiyar uwar ɗakinta. Godiya ta yi mata amma ba ta sha ba, hankalinta kacokam na garesu, wani shiri suke kallo na india, sun maida hankalinsu kacokam. Itama sai nata hankalin ya tafi can. Ta shafe mintuna goma a nan tana jiran Mami, can sai ga wani ɗan yaro ya sauko daga benen da Mamin ta hau. "Ki je ana kiranki a sama." "Toh" Kawai ta ce ta miƙe ta nufi hanyar da yaron ya fito, kafin ta ƙarasa ta tsinkayi wata muryar babbar mace na faɗin. "Ke dai ki bi a hankali, kar ki yi garaje kamar yadda ki ka so yi a wancan lokacin." Sallamarta yasa suka kalli hanyar da sauri, ba ta lura da yanayinsu ba ta karasa ta durkusa gefe ta gaida matar wacce kamanninta sak da wannan matashin da suka gani ɗazun. Matar ta amsa mata fuska a sake. "Ah Maryam, ki ce ɗiyar tamu kyakkyawa ce masha Allah. Humaira ko?" Humaira ta gyaɗa kai tana sunkuyar da kai murmushi a saman leɓbanta. "Masha Allah, Allah ya yi albarka kin ji? Allah ya gafartawa Hajiya Fatima, idan kika biyo halinta kin more. Mace mai hakuri da kawaici. Allah ya gafarta mata." Ta ji wani sanyi a ranta, a duniya tana jin daɗin a yabi Mahaifiyarta. Ta amsa da amin ita da Mami. Mamin ta dube ta. "Toh Humaira, gobe idan Allah ya kaimu koda ba ni ba, sai ku zo da Ummita a kaiki gidan koyon girkin. Na faɗamaki ta gida ce, ƙanwar Hajiya Lubna ce. Sai ki mayar da hankali ga abin da ya kai ki. Nasan kina da fahimta da saurin ɗaukar abu, don Allah kar ki ba mu kunya kin ji ko?" Ta amsa da toh Mami. Kafin Mami ta ɗora daga inda ta tsaya wannan saurayin na ɗazu ya hayo. Suka maida duba gareshi. Wani irin ajiysr zuciya ya sauke yana duban Humaira sannan ya maida kallonsa ga Mami. "Ai na ɗauka har kun tafi." Mamin ta ɗan yi murmushi kaɗan ta girgiza kai. "Ina nan Kabeer, amma yanzun za mu tafi. Abban yara ya kusa komawa gida." Ya karasa ya zauna. Hajiya Lubna nan da nan fuskarta ta sauya ganin kallon da yake jifan Humaira da shi. Mami ta dubi Humaira ta bata umarnin ta koma ƙasa ta yi jiranta za ta sauko su tafi. Daga fitarta shi ma ya miƙe caraf ya bi bayanta. Hajiya Lubna za ta yi magana, Mami da sauri ta hana ta ta hanyar ɗan dafe kafaɗarta. Dole ta fasa. Amma ta kudurce a ranta lallai za ta yiwa abin tufka don ita kam ɗiyar ubangidan mijinta take so ya aura, ta kuma lura da yadda yake bin Humaira kamar jela to akwai wata a ƙasa. Ƙwafa kawai ta yi ta watsar suka ɗora hirarsu daga inda suka tsaya. A can kuwa Humaira duk ya takura mata, ita ba ta saba da wannan rayuwar ba. Kawai wani garjejan saurayi ya zauna yana jan ta da hira ba hadin uwa da uba, ita kam abin ya girmi kanta. Ta kula bai ko damu da jama'ar falon ba waɗanda su din ma kallonsu kawai suke jifa-jifa su na mayar da hankalinsu ga tv.  Tambayoyi yake mata iri-iri, amma ba ƴar Mami ce ke ba? Yaushe ki ka zo? Karatu  kike? Da dai sauransu ita dai eh ko aa kawai take ce mishi duk ta takura. Haka Mami da Hajiya Lubna suka sauko, ganinsu ya sa ya miƙe yana shafar ƙeya. "Wai Kabeer ina aiken da na maka ne? Idan ba za ka je ba, ka fadamin na aiki Bala direba." Hajiya Lubna ta faɗi rai bace tana watsa mishi harara, sarai ya gane manufarta, amma shi kam yana ji a ransa ko karatu Humaira take yi zai iya dakon jira ta kammala ya aure ta. Ya lura auren jari Hajiyartasa take so ya yi. "Sorry Hajjaju, bari na tafi. Mami ku gaida gida, sai na tako har falonki na ƙara gaida ki." Mamin ta yi dariya. "Ai babu laifi Kabeer, ko da wacce ka zo ka shiryawa amsar da za ka samu." Ganin ta ɗago shi ya fice yana ƴar dariya gami da faɗin. "Na shirya Maminmu, amma dai ba zan ja baya ba." Mamin ta ƙara darawa. Humaira ta miƙe suka kara yin sallama da Hajiya Lubna, har farfajiyar gidan ta rako su. Humaira dai har ta ɗan kwashe mintuna a mota ba su gama tsayuwarsu a bakin ƙofar falon su na tattaunawa ba, ba ta san me suke cewa ba dakyar dai Mamin ta taho ta shiga motar suka tafi. ***  05 Humaira ce zaune a falo da safe, yaran gidan duka sun fice makaranta kasancewar sun soma jarrabawar zango na uku (Raihana da Ummita kenan), a yadda Ummita ta ce mata, daga jarrabawar to aji na gaba za su je. Kallon tashar Arewa24 take inda ake hasko wani wasan kwaikwayo na marigayi Ibro. Ta shagala gaba daya tana tuntsira dariya ta ji ɗif, wuta ta ɗauke. Guntun tsaki ta ja, ita kam ba ta san matsalar wuta a nijar ba domin koyaushe akwai. Ba ruwanka da tayar da janareto. Ganin haka kawai sai ta miƙe da zummar komawa ɗaki. "Humaira." Muryar Ladidi ta katse ta, ta juyo ta amsa. Tire ne a hannun Ladidin ta karaso gareta. Fuskarta duk ta yi narai-narai alamun roƙo. "Ki taimakamin don Allah ki miƙa sashen Anna, kinga suyar agadar Mami nake kada ya ƙone. Kuma Annar za ta sha magungunanta ne lokaci na tafiya." Kirjinta ya ɗan buga dam, ta kasa magana. Toh akan me za ta cewa Ladidin ba ta taɓa shiga sashin Anna ba? A ganinta hakan su ta shafa. Ganin yadda Ladidin ke magiya yasa ta karɓa, godiya ta yi mata ta koma kicin. Ita kuwa ɗan hanyar da take ganin su Muhsin na yawan zirga-zirga zuwa wajen Annar ta zubawa ido sannan ta sauke ajiyar zuciya ta nufi wajen. Anna ɗin ai mutum ce ba aljana ba balle ta illata ta, za ta je ta ga me zai faru idan ta yi karo da ita. Koro ta za ta yi daga ɗakin ko kuwa dai duka za ta yi mata. Da haka ta tunkari hanyar. A hankali ta tura ƙofar ɗakin da sallama, jin shiru yasa ta maimaita. Wata murya ta amsa, ta tabbatar ba shakka muryar ta Anna ce. Shiga ta yi ta karasa ta ajiye saman ƙaramin tebur dake wurin. Anna dake zaune gefen gado ta soma magana tana laluben gilashinta. "Ladidi sai yanzu ake kawomin abin karin? Yau me ya tsaida ki haka? Ina gilashina na jefa?" Humaira ta hadiyi miyau, kenan dai Anna ba ta san ma wace tsugune a gabanta ba. Ta daure ta ce. "Ina kwana. Ya karfin jiki?" Jin  baƙuwar murya ya sa Anna saurin sanya medicated glass ɗinta wanda da shi ne ta ke gani sosai ba dishi-dishi ba. Yarinya budurwa ce durƙushe a gabanta, fara sol. Kanta duk da cewar akwai hula, sumarta ba ta ɓuya ba don hatta da goshi da bayan ƙeyarta sumar ce kwance. Ta ƙuramata idanu tana ƙokarin tuno inda ta san fuskar. Sai dai a ɗan lokacin ba ta ankare ba don ita shaf tuni ta mance da wata wai Humaira a gidan tunda ba su taɓa karo ba. Ba ta damu da shiga sashin ɗiyarta ba, ya fi rayuwa anan dai ɓangarenta. Daidai lokacin Mami ta shigo ɗakin kamar wacce aka jefo, ta samu labari daga Ladidi cewar Humaira ta tura kai wa Annar kari. Shigowarta ya sa Anna mayar da dubanta gareta. "Ina kika samu yarinya ha..." Sauran kalaman Anna suka maƙale a fatar bakinta, shakka babu ta tuno komai. Ta tuna ashe akwai wani ran bayan jikokinta a gidan da aka ce tsatson Fatima ce. Ta tuna Humaira kamar yadda ta ji sunanta a bakin su Yassar masu yawon kawo ƙorafi a kan fifikon da Mami ke yi mata sama da su. Nan da nan ta haɗe girar sama da ta ƙasa. Daidai lokacin Humaira ta ƙara gaidata wannan karon muryarta har ɗan rawa yake. Ta nuna Humairar da yatsa idanunta akan Mami. "Me wannan abar ta zo yi wurina? Me na faɗamaki? Ban ce maki ba na son ganin baragurbi  a wurina ba? Ke don uwaki wa ya ba ki iznin zuwa wurina, ko ni na haifi uwarki?!" Maganar sosai ta daki Humaira, nan da nan idanunta suka cicciko da kwalla, uwarta kuma? Uwar dake kwance a kushewarta? Mene dalilin sanyo ta ciki? Ba ta jira umarnin Mami ba ta miƙe a zuciye ta kama hanyar fita daga ɗakin, Mami ta riƙe hannunta wannan ya dakatar da ita sai dai ba ta ko juyo ba. Daidai nan kuma hawayen suka sauka saman kuncinta. Da harshen buzanci Mamin ta yiwa Anna magana, Annar kuwa cikin harshen da Humairar za ta ji ta amsa a fusace cikin ɗaga murya. "Au! Don na zage ta kike kirana marar adalci? Ni Maryama kike kallon idona ki ce ba na adalci? Toh anyi rashin adalcin. Idan maye ta manta ai uwar ɗa ba ta mance ba. Ke da kika ga za ki iya haɗiye duk baƙin cikin da kika risƙi kanki a baya, ki yi. Nikam ba da ni ba, kuma ke duk radda kika kuskure ki ka ƙara gangancin takowa ɗakin nan sai na sa jikokina sun nakastamin ke. Sauran yunwa kawai." Humaira tuni ta janye hannunta a na Mami ta bar ɗakin da sauri. Kai tsaye ɗakinsu ta nufa ta zube saman kafet ta shiga kuka kamar ranta zai fita. Ita fa duk abin da matar ta ce bai dame ta ba kamar sanya uwarta da ta yi a ciki. To me Mamarta ta yiwa Mamin da har Anna ke batun ba za ta mance ba? Wane irin zama suka yi a baya? Ita Mami da ma ƴan uwan Abba, sun yiwa Mahaifiyarta kyakkyawar shaida, amma me Anna ke nufi da kalamanta? Ko kuwa dai ita ke taya ɗiyarta kishin kamar yadda Ummita ta taɓa faɗi? Ba ta ji shigowar Mami ɗakin ba sai ji ta yi an kama hannunta an ɗaga ta. Ta miƙe tsaye, Mami ta yi mata murmushi. "Ki yi hakuri Humaira, kin san iyaye ne sai mun yi hakuri da su mu samu a rabu lafiya. Ki taya ni yi mata biyayya,  kar ki kara zuwa ɗakinta har sai don kanta ta nemi hakan wataran wanda in sha Allahu nake fatansa nan kusa. Kar ki sa komai a ranki, ki kuma shirya anjima da kaina zan kai ki gidan koyon girki. Ki cire komai a ranki ki mayar da hankali, ni kuma anan gida idan kin dawo zan dinga iyakar ƙokarina wurin ganin an samar maki dukkan kayan girkin da ki ka koyo a can ki yi a nan mu ci mu ɗanɗana, kin ga daga haka hannunki zai miƙa. Wataran sai a wayi gari kina odar biki da suna har ma da wuraren party ko? Kin zama Hajiya." Zancen Mamin ya sanya ta murmushin da har wushiryarta ta bayyana. Mamin ma murmushin ta ƙara yi. Daga haka ta fice a ɗakin. Humaira tuni ta share batun Anna ta tattara ta watsar. *** Sun je gidan Anti Laila ƙanwar Hajiya Lubna tare da Mami, ta ba da form bayan sun biya komai, Mami da kanta ta cikewa Humairar. Anan aka ajiye ranar litinin matsayin ranar da za ta fara zuwa koyon girkin. Daga nan suka yo gida ranta fari sol. Kai tsaye ɗaki ta nufa hannunta riƙe da na Waleed wanda zuwa yanzu daga shi har Muhsin sun sake da ita,  fuskarta a sake, zuciyarta wasai. Ummita ce kaɗai zaune tana karatun jarrabawa, ganin haka Humaira ta dubi Waleed. "Tafi wajen Muhsin ku yi wasa ka ga Adda Ummita karatu take yi. Anjima sai ka zo ka koyamin turanci ko?" "Okay! Bye." Itama ta amsa da bye din tana dariyarsa, ya dage a lallai zai koyamata turanci, haka za ta biye mishi tana ɗan tsintar wasu abubuwan da ya iya. Ummita ta kalle ta tana murmushi. "Yau dai fara'arki ta musamman ce. Kada dai ki cemin har kin soma shiga aji?" Dariya Humairar ta yi daidai sadda take zama a gefenta. "Aa fa, amma an gama komai an biya, litinin zan soma zuwa." "Kai naji dadi wallahi. Allah ya nuna mana." Ta amsa da amin, ta mike ta hau cire kaya da zummar shiga wanka. Ta dai kula kamar Ummitan ranta a jagule ya ke, ba ta ce mata komai ba har ta shiga wanka ta fito. Anan kuma ta ga ta amsa waya ta yi jifa da wayar saman gado tana ɗan goge fuska. Jiki a sanyaye ta ƙarasa gareta ta zauna. "Ummita, lafiya? Meyafaru?" Ummita tana kallon littafin amma ta kasa karatun sai kawai ta girgiza kai tana shirin cewa ba komai amma tuni hawayenta ya zuba saman littafin. Humaira ta janye littafin. "Don Allah meke faruwa? Anyi wani abu ne bayan fitar mu?" Nan ma girgiza kan ta yi. Ganin haka sai kawai Humaira ta mike ta nufi sif dinta, har ta sanya kaya jiki a sanyaye Ummitan ba ta da niyyar cewa wani abu. Ganin haka sai ta ƙarasa wajenta karo na biyu. "Na tambayeki mene ne kin kasa cewa komai, kuma kina kuka." Jin ta yi shiru ne yasa Humaira fadin. "Toh bari na kira Mami mai yiwuwa ita za ki faɗamata." Har ta miƙe da sauri Ummita ta riƙe hannunta. Suna haɗa idanu ta girgiza mata kai, itama Humaira tuni idanunta sun cicciko don a duniya ta tsani kukan mutum. Kuka ma irin na waɗanda  ta ke yiwa ƙauna domin Allah. Duk abin da ya shafi irin mutanen nan tana jin abin a ranta tamkar ita ya shafa. "Kar ki je, zauna na faɗamaki." Ta koma ta zauna tana mai zuba mata ido bayan ta share kwallarta. "Yayar Mamana ce ta kira ni daga Bichi, kwanakin nan duk sun takura akan lallai sai na fiddo miji na yi aure wai karatun ya isa hakanan. Su sam hankalinsu bai kwanta da zamana a gidannan ba. Ita Babbar yayar Mamana, Anti Maijidda cewa take yi wai har mafarke-mafarke take yi a kaina don haka za su yiwa Abba magana a dakatar da karatun nan, ida n ma aure ne dai a yimin. Ni kuwa na dage akan ba zan yi aure yanzu ba, na ce musu ko zance ba na yi, sun ce ai kuwa anan da Bichi ba zan rasa mijin aure cikin ƴan uwa ba, Anti Maijidda har cewa ta yi ga babban ɗanta Yusuf nan, wai ya kammala  gininsa za ta turo shi ya zo mu yi hira mu fahimci juna. Kin taɓa jin wannan irin abu don Allah Humaira? Duka-duka nawa nake da za su ce za su aurar da ni yanzu? Zangon karshe nake a Ss1 zan wuce Ss2, idan ma auren suke buri su ga na yi, ai sa bari dai shekaru biyun da suka ragemin a sakandire na kammala su. Haka kawai don wasu mafarke-mafarken da ba su da tabbas ku rushemin ginin rayuwata? Sun bi sun kafawa Mami karan tsana, ban san hawa ba ban san sauka ba, amma nima su na hantarata akan na mayar da ita tamkar uwar da ta haife ni, gani suke na fifita dangin Babana sama da su. Toh don Allah faɗamin, mutanen nan sai na je wurinsu duk shekara a can nake hutun dogon zango da ake ba mu na makaranta har ya ƙare, amma su ko sau ɗaya ba su taɓa zuwa garin nan da zummar ganina a gidan nan ba acewarsu su da Mami har abada don ba su yarda da zuciya ɗaya ta ke riƙe da ni ba. Akan Mami na sha duka a wajensu idan na je domin duk wanda ya aibata  ta zan buɗe baki nace sam ba haka take ba, to fa anan sai na ɗanɗana kudata. Yanzu wannan matsalar auren da ta taso ki faɗamin Humaira, ta ina zan kashe ta ba tare da na samu matsala da su ba, nikam wallahi gaba ɗaya kaina ya ƙulle." Humaira ta sauke ajiyar zuciya. "Wai Allah!" Shi ne abin da ta furta don ita komai ma ya tsaya mata cak, ta rasa me za ta cewa Ummita. Mamaki take yi na yadda suke yiwa Mami kallon baibai alhalin matarnan iyakar kokari tana yi a kansu, irin kokarin da ko mahaifansu na usuli sai haka. Can kuma ta dubi Ummita. "Toh kodai ki yiwa Abba bayanin komai? Na tabbata zai fahimceki kuma ba zai rasa matakin ɗauka ba yadda zumuncinku ba zai taɓu ba." Shiru ta ɗan yi, sai kuma ta ce. "Ko? Nima na yi wannan tunanin, wallahi maganganunsu ke hargitsa ni tun wancan satin su ke huran wuta, tun fa ina dannewa har suka soma sanya ni kuka. Amma hakan zan yi kawai, zan faɗawa Abba komai, ke nasan ma kai tsaye zai nemi Kakana wanda ya haifi Mama ya yi mishi magana. Shi kaɗai zai iya tsawatar musu, daman tsoro ne ya sa na kasa faɗa mishi, amma na tabbatar zai magancemin." Humaira ta jinjina kai. "Sai dai don Allah kar ki faɗawa Abba zargin da suke yiwa Mami." Ummita ta kama baki. "Rufamin asiri Humaira, dama me zai kai ni?" Murmushi Humaira ta yi. Suka ɗan taɓa hira sannan ta kyale ta don ta yi karatu.   Aikuwa a daren Ummita ta samu Abban ta zayyane mishi komai, ransa ya ɓaci. Ƙarshe dai ya ce ta tashi ta wuce zai san matakin da zai ɗauka. A ranar kashe wayarta ta yi ta kuma yi alƙawarin ba za ta kunna ba har sai komai ya wuce don ta tabbata zagi ne dai za ta sha a wurin su. *** BAYAN WATA BIYU... Gadan-gadan Humaira ta fara zuwa koyon girki, abin da ya burge su Abba da Mami bai wuce irin hazaƙarta ba na saurin ɗaukar abu. Ita kanta Anti Laila sosai take yabawa da Humairar. A farko-farko ne dai idan aka koyar da su ta zo gida ta yi sai ya kasance bai yi dadi ba ko gishiri ya yi yawa ko dai wani abin, har su Tasleem na ci don su yi mata dariya da kuma kushe. Har su na cewa Abba ya yi asarar kuɗinsa. Amma yanzu kam duk da su na kaucewa ba su son nunawa a fili yana musu dadi, to fa a ƙasan zuciyarsu su na son su ɗanɗana idan ta yi. Amma fa ana ci ana yamutse fuska ana nuna ba laifi ya ɗan yi dadi. Ita dai ba ta tanka musu tunda har Abba da Mami da Ummita su na yabon girkinta. A farko direba ke kai ta, daga baya kuwa Mami ta nemi ɗan sahun da zai dinga kai ta kuma ya ɗauko ta. Watarana kuwa da aka yiwa ɗan sahun rasuwa da kanta ta Mami ta sanya yaron gidan me musu wanki ya raka ta titi ya sanya ta a adaidaita, a dawowa da kanta ta dawo. Tun kuma daga nan ta soma zuwa da kanta ta dawo, a karshe kuma ya kasance koda ɗan sahun bai zo ba ita ke zuwa ta dawo. Ganin ta gane hanya ya sa Mami kawai ta sallami ɗan sahun ake ba ta kuɗin mota. Komai idan ta koya tana samun ɗan littafin da Ummita ta bata ta rubuce tsaf da hausar ajami. Rubutunta mai ɗan karen kyau da burgewa har ya kasance Ummita ta yi ta santin handwritting din. A bangaren Islamiyya kuwa, kusan tare suke tafiya da Ummita a aji duk kuwa da cewar a can karatunta ya zarta na su, akwai abubuwa da dama da ta sani na daga litattafan addini wanda na ajin ƴan gaba ne. Hakan ya sa idan ba sa komai ta ke zama malamar Ummita. Su yi ta karatunsu musamman yanzu da ake cikin hutun dogon zango na makarantun boko. Idan ka cire Tasleem da Futuha sai samarin, babu wanda ke zuwa makaranta. Gidan sai yake yiwa Humaira daɗi fiye da a baya. Ranar wata Asabar da yammaci su na zaune a ɗakinsu, Humaira ke taya Ummita gyaran sif ɗinta, gaba ɗaya sun sauke kayan Ummitan saman gado. Humaira sai tsokanarta take yi akan da tuni yanzu an sanya ranar aurenta da Yusuf, ita kuwa tana kai mata bugu da ninkakkiyar rigarta. Sai kuma ta ja guntun tsaki ta zauna gefe tana murmushi. "Ke nifa ina da mijin aure a hannu, kawai dai bai taɓa zuwa gidannan ba, ba na so kowa ya sani sai na kammala karatu." Humaira ta zaro ido da wani irin zumuɗi ta ce. "Don Allah dagaske? Waye wannan mai sa'ar?" Ummita ta ɗan harareta sai kuma ta miƙe ta ci gaba da ninkin da take yi. "Oho, idan ta yi wari kya ji." Duk irin magiyar Humaira dai ba ta samu Ummita ta furta komai ba, da ta ga hakan ba mai ɓulla bane sai ta sauya ta ce. "Toh abu ɗaya za ki faɗamin, Allah kuwan daga shi ba zan ƙara tambaya ba. Na san shi, na taɓa ganinsa? Eh ko aa?" Dariya Ummita ta yi. "Wai ni za ki yiwa wayo ko me?" Itama dariyar ta yi. "Allah ba wayo ba, kawai ina son sani." Ummita ta ɗan yi shiru, ta sani idan har ta ce mata ta san shi to za ta ƙara damuwa da son ji ita kuwa duk data yarda da Humaira ba ta shirya kowa ya ji yanzu ba. Sai ta girgiza kai. "A'a toh." Jin haka Humaira ta taɓe baki. "Toh shikenan, idan ta yi wari ma ji." Kafin Ummita ta tanka sai ga Muhsin ya shigo a guje. "Adda Humaira, ki zo inji Mami za ku gaisa da Yaya Kabeer." Humaira ta ji kanta ya yi wani dum, wani irin ɓacin rai da bakin ciki na taso mata da ba ta san silarsa ba. Nan da nan ta haɗe fuska tamau kamar ba ita ke dariya yanzu ba. "Ka ce gatanan zuwa." Ummita ta amsa jin ba ta da niyyar amsawar. Ta sani Humaira ta tsani Kabeer, tun ganin da ya yi mata a gidansu tare da Mami yake bibiyarta. Amma yadda fuskarta ta sauya ita kam ba ta taɓa ganinta cikin wannan yanayin ba. "Ke lafiya? Daga ance maki Kabeer ya zo?" Tsaki ta ja ta miƙe a fusace cike da wata iriyar tsiwar da ita kanta Ummita ba ta san ta da ita ba ta ce. "Aikin banza da wofi, na tsani naci da takura wallahi. Mutum sai shegen naci, itama Mami ta biyemishi har da wani aikowa a yi kirana." Ta kara jan tsaki. Maganarta na karshe kan kunnen Raihana da ta shigo ɗakin tana danna waya, baki buɗe take kallonta. "Ke, Mami za ki yiwa rashin kunya? Har da tsaki?" Ko kallonta ba ta yi ba ta juya ta ci gaba da ninkin kayan da alama ba ta da ko niyyar tashi balle ta je. Ummita ta kalli Raihana itama ta dube ta, a fusace Raihana ta karaso ta fisge rigar dake hannun Humaira ta yi jifa da shi. Humaira ta mike a zuciye ta ce. "Malama na fada! Nace na fada! Kabeer din banza da wofi! Ba zan je ba din akwai abin da za ki iya yi? Ko waye ya tilasta ni shiga lamarinsa sai na gasa mishi maganganun da zai yi dana sani!" Raihana gaba daya ta tsorata, kamar dai Humaira kamar ba ita ba. Kawai sai ta gifta ta fice daga ɗakin ba tare da ta tanka ba don dama Raihana akwai tsoro. Ummita ta mike ta kama hannun Humaira a sanyaye. "Humaira, lafiyarki kuwa? Me ya yi zafi?" Ba ta ce komai ba kawai ta zare hannunta a cikin na Ummita, zama ta yi ta yi shiru sai huci ga gumi na tsastsafo mata. A haka Mami ta shigo dakin, Raihana duk ta ba ta labarin abin da ya faru, kallon Humaira take yi a nutse, sai kuma ta karasa ta zauna gefenta. A hankali ta dafe hannunta. Humaira ta kalleta, kawai sai ga mamakinsu ta fashe da kuka. "Mami don Allah kiyi hakuri, wallahi na tsane shi, ki ganinsa bana son yi. Kiyi hakuri don Allah ki janye batun zuwa mu gaisa da shi." Wani irin kuka ne da sheshsheƙa tamkar wacce ake kokarin raba ta da numfashinta. Mami da Ummita wacce duk ta firgice suka dubi juna sai kuma ta rungumo Humaira. "Kar ki damu, ya tafi ya bar gidan ma. Kuma na yi maki alƙawari Kabeer ba zai ƙara takura maki ba. Kin ji ko?" Sai a sannan ta gyaɗa kai ta bar kukan, lokaci guda kuma ta fara dawowa hayyacinta. Ita dai Ummita ikon Allah ta zubawa ido tana kallo. Abin dai kamar a wasan kwaikwayo.06 Dare ne misalin karfe ɗaya da mintoci, ɗakin ya yi shiru ban da munsharin Tasleem ba abin da kan addabesu kullum ba abin da ke motsi. Humaira wacce abu biyu suka hana ta sukunin bacci, ta zubawa tagar ɗakin ido tana kallon farin wata da ya hasko har cikin ɗakin nasu. Garin babu zafi sai iska dake kaɗawa kaɗan kaɗan hakan yasa rashin wutar bai hana mutanen gidan sukuni ba. Ta ja guntun tsaki ta miƙe zaune gami da runtse idanunta. _'Humaira ba ki kyautata kalamai ga Mami ba. An sani maganar Kabeer kika tsana, sai dai yanayin da kika yiwa Mami magana kamar wata Humairar aka chanja ba ke ba. Idan kin yiwa Raihana wannan dama abokiyar yinki ce, amma ga Mami, kin yi kuskure.'_ Ta tuno kalaman Ummita, wannan na daga cikin abin da ya damu zuciyarta, Mami fa, matar da ta ke ba ta kulawa da zuciya ɗaya. Ta maye mata gurbin Dada da Mamarta wacce ba ta buɗi ido ta gani ba. Ta kuma zame mata abokiyar hira a lokuta da dama idan tana zaune ita kaɗai a gidan. Hakan za ta dinga ba ta labarin Nijar itama ta ba ta na ainahin garin iyayenta wato Agadez su yi ta nishaɗi. Abu na biyu da ya tsaya mata a rai bai wuce na mamaki da tunanin abin da ta yi ɗin ba. Eh ta san ba ta son Kabeer, ta tsani ma ganinsa, amma tsanar har ta yi yawan da za ta kasa ɓoyewa har haka? Ita kam abin ya sha mata kai. Tana nan zaune dai ganin ɓatawa kanta lokaci da tunani take yi da b zai magance mata komai ba sai kawai ta maida kai filo a hankali bacci ya sure ra. Duka wannan zaman da ta yi har zuwa kwanciyarta akan idanun Raihana wacce munsharin Tasleem ya hana ta sukunin bacci. Tsoron yarinyar ya ƙaru a zuciyarta, ta kasa kwakkwarar motsi ga fitsari cike fal a mararta amma ina, ga ni take ai tana miƙewa Humaira za ta tashi ta shaƙe ta don ta gama ba zuciyarta cewar iskokai ne da Humairar. A wannan daren dai bacci ɓarawo ne ya sace Raihana. *** Ta kammala shirinta tsaf kamar koyaushe za ta wuce wurin koyon girki, ta fito falon. Ummita na zaune tare da su Muhsin a falon, Raihana kuwa na gefe ɗaya ta hakimce tana abin da ta saba, latse-latsen waya. Ganin Humaira yasa ta kalle ta sau ɗaya ba ta ƙara ba don ita ba ta so ma su haɗa ido, har ga Allah tun can tana tsoron mai aljanu. Tana kuma shakkar yi musu rashin kunya tun wataran tana jss 2 da wata abokiyar karatunta ta shaƙe ta akan ta zauna a kujerarta ta kuma yi magana amma ta ƙi tashi. Da ta fusata ta shaƙo wuyanta sai da malaminsu ya kwace ta. Abba har makarantar ya je, iyayen yarinyar suka ba da hakuri aka kuma sauya musu aji. Tun daga nan ta ke tsoron duk abin da zai danganta ta da mai iskokai. Ko kusa da su ba ta raɓa. "Har kin fito kenan?" Ummita ta tambaya tana kallonta fuska a sake. Itama murmushin ta yi. "Na fito, ina Mami?" "Tana sashinta." Daga nan ta nufi sashin Mamin, a falo ta iske ta tana waya tana dariya, ganinta yasa ta yi sallama da ɗaya ɓangaren ta ajiye waya. Cike da walwala ta ce. "Ƴar Mami har an fito?" Kunya ta kamata, ita kunyar Mamin take ji wallahi, ta karasa ta durkusanta gaida ta. "To, wata sabuwar gaisuwa ce nan ban da wacce muka yi ɗazu?" Mamin ta faɗi cikin wasa da dariya, Humaira dake sunne kai ta ɗan murmusa, ita ta manta ma sun gaisa ɗin. Mamin ta ƙara magana. "Au, ashe gidan Laila za ki ko? Bari ma na ba ki saƙonta ki tafi da shi." Mamin daga haka ta miƙe ta nufi ɗaki, can ta fito ɗauke da leda wacce Humairar ba ta san ma ko mene ba ta karɓa. Ta ba ta kuɗin mota tana fadin. "Abbanki ya riga ya fita na mance ban karɓar maki na motar ba, ki je kawai idan ya dawo sai na karɓa." Ta gyaɗa kai ta sa hannu ta karɓa da godiya, ganin ta ƙi motsawa balle ta tashi ya sa Mamin tattaro nutsuwarta gareta. "Lafiya Humaira? Akwai magana a bakinki ko?" Gyaɗa kai ta ƙara yi a karo na biyu, cikin nutsuwa kuma ta soma magana. "Mami dama akan abin da ya faru jiya ne, ina neman gafara." Murmushi Mamin ta yi ta girgiza mata kai. "Kar ki damu, ni nasan ba laifinki ba ne. Hakan ya sa na yi maki uzuri. Ki cire komai a ranki kedai ki tattara nutsuwarki ki cigaba da maida hankali ga darussanki. Laila na ta yabon kwazonki don haka ki ƙara dagewa, na maki alƙawarin Kabeer ba zai ƙara shiga sabgarki ba, kin ji ko?" Sai a sannan ta sauke ajiyar zuciya ta samun nutsuwa, ta amsa da toh daga nan suka yi sallama ta mike ta fita, Mamin ta bita da kallo tana murmushi. *** Tuƙi ɗan sahun ke yi cike da nutsuwa, sosai tuƙin ke mata daɗi yayin da iskar dake kaɗawa a garin ke ƙara jefa ta cikin walwala. Damuwar da ta kwana da shi a ƙarƙashin ranta, tas ya wanke ya koma annashuwa. Don haka murmushi take yi ma ba tare da sanin tana yinsa ba. Ba zato ta ji ta yi wani irin hantsilawa sai ga ta a bayan ɗan sahun nan hannayenta rungume a kan wuyansa kai kace wacce aka goyo. Shi kuwa ɗan sahun kansa ya ƙumu da jikin gilashin da karfi har sai da gilashin ya tsage, saura kaɗan adaidaitar ta wuntsila amma Allah ya taƙaita faruwar hakan, sai ya koma baya da ƙarfi har tayoyin na bugun ƙasa da ƙarfi, wannan ya sa ta koma mazauninta, lokaci guda ta saki ƴar guntuwar ƙara sakamakon cikinta da ya bugu da ƙarfen jikin mazaunin direban yake mata zafi dalilin buguwar da ta ƙara yi dalilin komawa baya. Ta runtse idanu daidai sadda ta ji salatin jama'a a kansu. Gaba ɗaya ma ta kasa buɗe idanunta tana dafe da cikinta, ta yi shiru kawai don hayaniyar ma ba burge ta take ba. "Sannu ƴanmata, sauko." Ta tsinkayi ɗaya daga cikin jama'ar wurin na fadi, wasu kuwa na hayaniya su na fadin ai laifin mai motar ne. Can kuma ta ji an ce. "Alhaji kai ne da laifi, kai ka bugi motarsu garin cin burki a kurarren lokaci." Ta buɗe idanunta a hankali jin wani daddaɗan kamshi a gefe, a hankali ta sa hannu ta ɗauki jakarta da ta tarwatse a ƙasa, duk tarkacenta sun zubo. Wani matashi ya shiga tattara mata ita kuwa tana son ta fito a adaidaitar kamar yanda ɗan sahun ya fita ya zauna gefen kwalta, amma ina tururuwar mazan dake wurin ya sa ko motsin kirki ta kasa. Da murya irin ta manyan mutane ya amsa. "Baba, ba abin zafi ba ne. Na sani ni keda laifi, ina mai ba da hakuri garesu. Zan kuma yi kokarin gyara ɓarnar da nayi. Ku yi hakuri don Allah." Humaira ta juya ta kai duba ga mai maganar, daidai lokacin da shima ya ɗan rankwafo don ya yi mata sannu da kuma neman alfarma akan ta sauko su je asibiti. Kalma ɗaya ta kasa fita a bakinsa da ya yi nauyi. Ƙafafunsa suka soma ƙoƙarin kayar da shi. Zai iya rantsuwa ba kaffara son budurwar yarinyarnan yake da idan da ace Uwargidansa ta yi haihuwar wuri to fa ya ci ya yi haihuwar fari da ita. A ɓangaren Humaira kallon da ta bishi da shi bai wuce na son ganin marar hankalin da bai iya tuƙi akan ƙa'ida ba har yake shirin kai ta barzahu. Babban mutum wanda ba gigin kuruciya tattare da shi, ya sha manyan kayansa har da babbar riga da hula. Kana ganinsa dai ka ga wanda ya ba arba'in baya. Ganin yadda ya ƙuramata idanu sai nan da nan ranta ya yi masifar ɓaci, ta ja tsaki wanda ya ba Alhajin nan mamaki, ba ta jira komai ba ta sauko daga adaidaita sahun ta ɗaya ɓangaren mutane na mata sannu. Matashin da ya tattara mata kayan ta yiwa godiya ta karɓi jakarta, ba ta so dubawa ba amma da yake ya matsa sai kawai ta duba, komai nata yana nan cif ba abin da ya ɓata. Dakyar take tafiya dalilin gefen cikin da har sannan ke mata ɗan zugi. "Sannu baiwar Allah, kiyi hakuri ba da gayya hakan ta faru ba. Direbana ne ya ɗauki waya bisa umarnina ba kuma mu ankara ba hakan ta kasance. Akwai inda ke maki ciwo sai a karasa asibiti." Ya karashe yana kai idanunsa kan gefen cikinta da take ta faman dafewa. Ganin haka sai ta saki cikin don ba ta kaunar taimakonsa saboda irin kallon da yake jifanta da shi, kwatankwacin irin kallon Kabeer. Fuskarta a daure tamau ta amsa. "Na ce maku babu abin da ke damuna, lafiyata kalau. Nagode da taimakon." Daga haka ta karasa tana cije lebba ta yiwa ɗan sahun sannu kafin ta kai hannunta dake rawa don har lokacin ba ta dawo daidai daga razanin da ta shiga na hatsarin ba ta fiddo kudi za ta ba ɗan sahun na hakkinsa dake wurinta amma ta kara tsintar muryar Alhajin nan wannan karon muryarsa har ƴar rawa take yi, kirjinsa kuwa bugu yake da karfi tsabar son da ya shiga zuciyarsa farat ɗaya na yarinyar. "Ki bar shi zan biya. A wane unguwa kike sai mu sauke ki?" Jama'ar duk idanunsu a kansu, wadanda suka lura da yanayin mutumin ba su ga laifinsa ba don Humaira ta haɗu iyakar haɗuwa, sai dai a ganin wasunsu, girma ne zai fadi muddin ya bari ta gasa mishi magana. Aikuwa masu wannan tunanin ba su kai ga furtawa ba suka tsinkayi muryarya cike da tsiwa tana magana tana kara zaro manyan idanunta masha Allah. "Baba ina mutunta furfurarka hakan yasa nake gargadinka akan ka fita a hanyata wallahi tun ban gasamaka wacce za ta hanaka bacci ba. Haba! Wannan ai shiga sharo ba shanu ne, ka kusan kaimu lahira na maka uzuri yanzu kuma me ya shafeka da kudin da zan bayar? Da kai ke biyamin kudin motar? Ina ruwanka da ni?" Daga haka ta ja dogon tsaki ta miƙawa ɗan sahun dubun gaba daya na motarta zuwa da komawa ba tare da ta jira chanji ba, daga haka ta juya daidai sadda wannan matashin ya kara miƙo mata ledar da shaf ta mance da batunsa, saƙon Mami zuwa ga Anti Laila. Sai lokacin ta ga ashe ma leshi ne sai atamfa. Godiya ta yiwa matashin a fusace ta bar wurin tana huci, ga cikinta inda ta ɗan bugu bai bar raɗaɗi ba. Kunya da tarin bakin ciki suka lulluɓe Alhajin, bai taɓa zaton yarinyar ba ta da kunya ba da tuni ya ɓoye zalamarsa a kanta. "Sai hakuri Alhaji, yaran yanzu ba su da kunya." Ya basar da zancen yana maida duba ga Ɗan sahun nan da ba da umarnin ya tashi su karasa asibiti ko kuwa dai ya sallame shi yanzun a nan, ɗan sahun ya aminta da hakan, nan take ya ba shi kuɗaɗe masu ɗan kauri gami da ƙara ba shi hakuri. Daga haka ya juya zuwa motarsa har lokacin bai daina jin kunya da ɓacin rai ba su sake shi ba. Ya kuma ƙudurta a ransa idan har haka yaran zamani su ke, to ya yi Allah wadai da ire irenta, ba kuma ya jin zai kara kallonta da sunan wata da ya taɓa gani har ya ji kaunarta cikin ransa. *** A ɓangaren Humaira dakyar ta karasa gidan Anti Laila, ita sai da suka yi nisa ma ta tuno ba ta da chanjin da za ta sallami mai adaidaitan don haka ta ce ya jira ta kawo mishi. Wajen Anti Laila ta karɓa bayan ta mata bayanin hatsarin da suka yi, nan kowa ya hau ta da sannu. Anti Laila da kanta ta kira Mami ta shaida mata, hankali tashe ko mintuna talatin ba a yi ba sai ga Mamin da direban Abba. Daukarta ta yi suka nufi asibiti, koda likita ya duba ta ya tabbatar kawai buguwa ce. Magunguna ya ba ta sannan suka wuce gida. Maganin ta sha bayan ta ci abinci ta kwanta. Abba har ɗakinsu ya shigo ya duba ta, ganin da sauki bacci ma take ya sanya shi fita. Sai da ta yi kwanaki uku ba ta leƙa ko farfajiyar gidan ba a rana ta hudu ta koma zuwa koyon girke-girke abin ta. *** Rayuwar ta ci gaba da tafiya yau dadi gobe babu, rashin dadin a wajen Humaira bai wuce na yadda su Tasleem ke kara nuna mata kiyayya a fili ba. Har ta kai da an wayi gari watarana sun yi mata sharrin sata, domin an tashi Mami tana neman kudin har dubi ashirin da ta ajiye ƙasan filo, gaba daya ran Mami a ɓace yake, sannan ma ita Humaira ba ta nan kuma ita ce ta gyara ɗakin kafin ta fice gidan Laila. Ganin an duba ko'ina sai Futuha da su Yassar suka ba da shawarar a duba ɗakunansu. Mami a farko ta ƙi, sai da Ladidi ta ce ya kamata a duba ko'ina tunda dai nema ake kuma abin da yasa Ladidin faɗin haka ganin su na neman ɗorawa yarinyar kirki Humaira ita kuwa tana da yaƙinin idan har Humaira ce ba za a sami ko sisi na wani a kayanta ba. Tasleem da ta dage tunda Humaira ce ta yi gyaran ɗakin a soma duba kayanta ya sa Ummita cike da kwarin gwuiwar sanin wace ce Humaira ta shiga fiddo kayan Humairar daga sif dinta. Sai dai tun kan ta yi nisa Futuha ta zura hannu ta jawo wata doguwar riga. "Kambu! Dama yarinyar nan ita ta ɗaukarmin wannan rigar? Tasleem ku dubi rigar da nake tunanin ta ɓata a wajen wanki?" Mami ta kalle su, ta yi shiru da mamaki. Can kuma sai ga ɗan kunne da sarƙa sun faɗo. Raihana ta zaro ido tana ɗauka. "Innalillahi, ku ga sarƙata da nake nema kwanaki? Ashe ita ta ɗauka?" Kai kamar wasa jikin Ummita na sanyi da wannan sharrin, ba ta yi aune ba ta kai hannu kan takardun kuɗi, tsabar razanar da ta yi ya sa ta fiddowa da sauri. Ladidi ce ta karɓa tana salati ta ƙirga, aikuwa dubu ashirin cif ne wanda Mami ke cigiya, Ummita kawai sai ta fashe da kuka tana faɗin. "Wallahi Mami wannan sharri ne, Humaira ba ɓarauniya ba ce. Ko kwandalar mutum ta gani idan tana aiki ajiyesu take a wurin da ta gan su." Mami dai ba ta iya magana ba domin kanta ya ƙulle, a sanyaye ta sa hannu ta karɓi kuɗin ta fice a ɗakin tana ji su Yassar na yiwa Ummita masifa wai sai ta faɗi wa ke mata sharrin amma ba ta ko iya tankawa ba. Ita kanta ta sani sata ba ya daga halayyar Humaira don ta sha ajiye kuɗin da suka fi waɗannan kauri ba ta taɓa su ba, amma ta sani mutum ka iya sauyawa. Bare ma a irin gidan nan na Alhaji Isuhu da ba a facaka da kuɗi. Humaira ba ta dawo gidan ba sai yammaci bayan la'asar, da murnarta ta tura kyauren gate ta shigo bayan ta gaida Baba dattijo dake zaune a benci yana siyan rogo a wurin ƴar tallah. Farin cikin bai wuce na yadda suka yi snacks har biyu a yau ba, samosa da springroll kuma cikin ikon Allah ta yi ya yi kyau a ido ya kuma yi daɗi a baki har a foilpaper ta nannaɗe ta kawo don Mami ta ci ta ji. Muryar Ƙasim ta tsinta a kanta. "Ɓarauniya ta dawo." Kallonsa ta yi gabanta ya faɗi, a duk irin wulakanci da jefa-jefan mugayen sunaye da suke mata, babu wani cinikinsu a ya taɓa kiranta da ɓarauniya wannan ya sa ta ji wani irin sanyi har ta kasa mayar masa da martani yadda ta saba idan ya jefe ta da marar dadi. Ya ɗan ɗaga gira. "Oh, bakin ta kanwa ya yi la'asar kenan saboda kin sani kin sata shiyasa. Dama ustazancin ashe na ƙarya ne, toh yau asirinki ya tonu. Ɗan adam butulu." Ta dafa kirji idanunta da suka cicciko da kwalla tun soma maganarsa ta kafa mishi. "Yaya Ƙasim sata fa ka ce? Ni na yi satar?" Ya harareta ya wuce kawai ba tare da ya ce komai ba. Ta bishi da kallo har ya shige gidan, itama a hankali ta soma taka ƙafafuwanta da suka yi mata nauyi saboda mutuwar da jikinta ya yi ta yi cikin gidan kirjinta na harbawa. *** Ma sha Allah, Alhamdulillah. Sai kuma bayan sallah in sha Allah. Allah ya karbi ibadunmu, a sanya ni a addu'a ina bararta don Allah. 🤲🤲 Fatan alheri.07 Tasleem, Dawud, Yassar da Futuha ne zaune cikin falon sai dai ba ta sha mamakin ƙin amsa sallamarta da suka yi ba, dama ya lafiyar giwa ballantana kuma an jefe ta da kashi? Su na ganinta Tasleem ta miƙe ta yi kerere gabanta hannuwa a ƙugu ta ce. "Ɓarauniyar banza da wofi, kin dawo kina wani sum-sum kamar munafuka. Koda dai dama munafukar ce, Mamin da ta daukake ki tana maki kallon kamar wata waliyya ai gashinan kin watsa mata ƙasa a ido. Ke ni ba wannan ba ma, earpiece dina da na jima ina nema idan kinsan ke ce ɓarauniyarsa wallahi tun wuri ki fiddomin abina. Atoh, bari ma Abba ya shigo gidan, ko Mami ba ta faɗamasa ba sai mun faɗa." Humaira wacce ta kasa tsaida hawayenta, kallon Tasleem din kawai take har ta kai aya, lebbanta na rawa amma ko harafi guda ta kasa fitarwa tsabar baƙin ciki. Wannan wace irin baƙar rana ce a wajenta haka da za a wayi gari da yi mata ƙazafin sata? Ta kasa motsawa, haka Futuha ma ta taso da nata kalar rashin mutuncin, su Yassar na taya ta. Ba ta iya cewa uffan ba sai kukan da ta ke rusawa kamar ranta zai fice. Tsawar da ta ji an daka musu ya sa ta kallon hanya, ruwan hawaye ya sa ganinta komawa dishi-dishi, sai a hankali bayan ta ɗan runtse idanu sun ɗan zuba ne sannan ta lura ashe Mami ce. Ƙarasowa ta yi fuskarta a ɗaure, sai ta koma mata Mamin da ta fara cin karo da ita a ranar farko na zuwanta gidan. Kirjin Humaira ya hau dukan tara-tara, ta runtse idanu saboda ta gama hasaso abin da zai afku, wato mari za ta sha a wajen Mami, sai dai ga mamakinta ta ji akalar faɗan sam ba a kanta yake ba, su Tasleem ta shiga yiwa tamkar za ta ari baki. "Ashe rashin mutuncin naku ya kai har haka? Raini ne wannan ku ka yimin ko mene? Ban hana ɗayanku yiwa Humaira maganar abin da ya faru ba? Ina ce har ɗaki ke Futuha kin biyo ni akan sai an ɗauki mataki na ba ki saƙo ga ƴan uwanki cewar na kashe maganar kada wanda ya tayar? Oh saboda ku nunamin ni banza ce wurinku, hukuncina ma na banza ne shi ne dalilinku na yin watsi da zancena a kwandon shara ko?! Toh wallahi ku fita idona tun wuri, kuma daga rana irin ta yau ku ka ƙara tada wannan batu sai na saɓamaku kamanni." Tana kai wa nan ta ja hannun Humaira zuwa ɗakinta. Ta bar yarannata a tsaye tamkar su haɗiyi zuciya su mutu don haushi, Yassar ne ya soma jan wani dogon tsaki kafin ya sa kai ya bar falon, Dawud ya mara mishi baya. Tasleem kuwa ƙwafa ta yi. "Innalillahi, ke Futuha na soma tsoro, na yarda dagaske ne da ake cewa ƴan ƙasarsu na da asirai, anya wannan shu'umar yarinyar da Kawunta hakanan suka  bar mana uwa? Anya ba sai da suka shuka tsiyarsu sannan ta dawo wajenmu ba?" Futuha da ta kasa magana kawai sai ta ja tsakin itama ta ɗauki wayarta ta wuce sashen Anna idanunta cike da kwallar baƙin ciki. *** A gefen Mami kuwa, su na shiga ɗakinta ta rungume hannuwanta a kirji ta daure fuska tamau har sai da Humaira ta sha jinin jikinta. "Zauna." Ba musu ta zauna a saman kafet, ita kuwa ta hakimce a gefen gado. "Na tsawatarwa yarannan saboda na riga da nasan takun saƙar da ke tsakaninku, ba na son a samu fuskar da za su ƙara ɗora maki karan tsana a matsayinki na yar uwarsu ta jini. Wannan ɗin ma da suke gwada maki fatana su daina na kashe shi gaba ɗaya. Amma meyasa haka Humaira? Har yanzun ina kokwanto akan kin aikata wannan laifin na ɗaukar kudi a ɗakina, amma idan  na tuna ganin da na yiwa kuɗin a cikin kayanki sai zuciyata ta tsinke. Ki faɗamin iyakar gaskiyarki, kamar yanda idan na ci karo da ɗaya cikin su Tasleem sun aikatamin laifi zan hukunta su, kema matuƙar da zuciya ɗaya nake zaune da ke ya zama wajibi na dauki mataki idan kin yi ba daidai ba." Humaira ta ja majina tana kallon Mami. Girgiza kai ta soma cikin muryar kuka ta ke magana. "Wallahi Mami, Allah ɗaya, ba zan yi wasa da Ubangijina wurin yi maki ƙarya ba, ban taɓa ɗaukar ko abin sakacen haƙori a ɗakinki ba tare da izninki ba ballantana kuma kudin da ba nawa ba. Mene ne bakya kokarin yimin a gidannan da zan yi maki sakayya da hakan? Kina yimin kyautatawar da ko na rayu da mahaifiyata abin da za ta yimin kenan. Toh a wane dalili zan zama butulu har na ɗauka daga asusunki? Mami wallahi ban ɗauka ba, ba ni kuma da masaniyar yanda aka yi kudin suka je cikin kayana, nidai na san na maki gyaran ɗaki, na kuma adana su a inda na gansu, na fita zuwa gidan Anti Laila." Mami ta yi shiru tana nazarinta, duk kushen mai kushe ba zai taɓa zama da Humaira ya ji ta masa karya ko sau ɗaya ba. Toh wannan dabi'a ce ta mahaifiyarta, ta sani sarai mahaifiyar Humaira haka take da faɗar gaskiya. Ta san kuma ko a gaban Abban maganar ba za ta chanja zani ba. Sai ta yi nufin kasheta a yanzu ta hanyar numfasawa ta dafa kan Humairar cikin taushin murya ta ce. "Ya isa hakanan, bari kukan kar ya ja maki ciwon kai. Na yarda dake ai dama, sai dai kin san kudi ba zai kai kansa cikin kayanki ba ko? Koda ace ba ke kika kai ba akwai yadda aka haihu a ragaya, kin ga kuwa dole na bincika matsayina na matar gida ko?" Humaira ta gyaɗa kai har sannan tana sauke hardadden numfashi irin na wanda ya ci kuka ya ƙoshi. Mami ta dora da fadin. "Toh don haka kar ki fahimce ni baibai don na tuhumeki, ya zama dole na aikata hakan ne ko don sauke hakki, yanzu kuma da ya kasance ba ke ba ce, zan bincika a sannu gaskiya za ta yi halinta. Tashi ki je ki ci abinci ki huta." Humaira ta gyada kai kawai ta mike ta fita. Har sannan jikinta bai bar ɓari ba, sharri ya fi komai ɗaga mata hankali, ta tsani sharri, ta kuma ci alwashin ita kanta za ta dage da addu'a har sai gaskiya ta yi halinta don a yanzu kam ba ta da amsar ba su Tasleem sai lokacin da komai zai bayyana muraran. A can ɗaki ma Ummita ta tarar tana nata hawayen, sai ya zamana ita ce mamai rarrashin Ummitan da nuna mata ai Mami ta fahimce ta. Ummita ta labarta mata yadda komai ya faru. Ta kara da fadin. "Ba ni da tabbaci akan ko su Tasleem ne da aikata hakan, amma shakka babu ina zarginsu." Murmushi Humaira ta yi. "Kar ki damu yar uwa, idan ma su ne ina mai tabbatar maki wataran gaskiya za ta bayyana." Daga haka suka bar zancen, koda Abba ya zo, babu wanda ya tunkareshi da zancen don ba karamin gargadi da jan kunne Mami ta yi musu ba, koda Anna ta hau faɗa, sai Mami ta sanyayar mata da jiki da faɗin abin da ta fi tunanin akan sharrin da aka yiwa Humairar. Dole itama Anna ta lallaɓa su akan zanceya mutu. Daga ranar kuwa ba a kara tayarwa ba kuma basu fasa kiran Humaira da wannan sabon suna na ɓarauniya da suka laƙaba mata ba. Wanda hakan ya fi komai yi mata zafi, duk kuwa da Mami ta tsawatar amma a fakaice a bayan idon Mamin ba sa fasa faɗi. *** WATA BIYU BAYAN HAKA... Ranar ta kasance yammacin Asabar, gaba ɗaya ahalin gidan su na nan idan ka cire Abba wanda ya fita zuwa kasuwa tare da Dawud. Fuskar Mami a kallo daya za ka shaida tana cikin farin ciki. Su Tasleem dai murnarsu ba yabo ba fallasa. Humaira kuwa da Ummita aiki suke tare da Mami ba kama hannun yaro, Raihana na can ɓangaren yayannasu tana aikin gyara bisa dole don ba yadda za ta kaucewa umarnin Mami, sai dai rabin aikin tana yi ne amma hankalinta na ga chatting din da take yi da sabon saurayinta wanda ya kasance abokin yayan ƙawarta. Humaira ta zage damtse wurin yin kayan snacks yayinda Mami da Ladidi su ke aikin girka masa dambun shinkafa da kuma kunun aya, kamar dai yanda ya buƙata. Sun kammala da wuri suka jera komai a saman tebur, Humaira a gajiye ta nufi hanyar ɗakinsu da zummar watsawa jikinta ruwa adalilin zafin da ke tasomata, Mami ta dakatar da ita ta hanyar kiranta. Juyowa ta yi gami da amsawa. "Maza je dakin Yayanki ki dubamin waccan mashiriciyar ko ta kammala gyaran nan, idan ta kammala ki dawo ga charcoal ki kunna a sanya turaren wuta." Ta amsa da toh sannan ta juya cikin bin umarnin Mamin. Tana zuwa daidai kofar dakin Yaya Mubarak ta ji muryar namiji kamar ta waya ya na fadin. "Um um sweetheart, ban gaji da ganin su ba, ni da ace za ki ɗan buɗemin ko saman ne kaɗai na kalla zai taimakamin ya magancemin wani abin. Please taimakamin kin ji? Gaba ɗaya ta miƙe wallahi." Humaira ta zaro ido, sam ba ta fahimci komai ba, ta na shirin faɗawa ɗakin don ta ga meke gudana ta tsinkayi muryar Raihana na amsawa da wata murya tamkar ba nata ba tana wata iriyar shagwaɓa. "Um um Baby, ba zan iya buɗemaka ba ina jin kunya." "Toh naji, ki yimin hotonsu na miki alkawari ina kalla zan goge, nima zan aikomaki da hotona nikam ko ace ba ki goge ba ba zan damu ba saboda ina maki son da nake jin cewa komai na jikina mallakinki ne koda ba mu yi aure ba. Uhum?" Humaira ta dafe kirji, yanzu kam ta fahimta, ta gane komai. Nan da nan ta nemi gajiyar da ke ɗibanta tana tafiyar rangaji ta rasa, da wani irin azama ta daga labulen dakin ta fada ba ta ko tuna da sallama ba. Raihana da ke fuskantar madubin dakin rike da waya tana videocall da wanda ta kira Baby, ta hango Humaira ta cikin madubi, ba ta san lokacin da ta kashe kiran gaba daya ba gami da saurin ajiye wayar saman madubi. Cikin rawar baki da danne firgicin da ta shiga na irin kallon zargin da Humaira ke watsa mata ta ja guntun tsaki tana kama gefen bedsheet wanda tuni ta kammala gyaransa amma ta hau kara cusawa. "Ke kuma Malama kawai sai ki faɗomin haka babu sallama babu komai?" Humaira ta karasa, ita ban da haushin Raihana da ta ji, har da wani irin bakin ciki da tsanar saurayin da Raihanan ta yi waya da shi ta ji. Ta yarda ba su ga maciji da yan uwanta, amma fa tana kaunarsu kuma tana ji a jikinta sai inda karfinta ya kare matukar ta ga ɗayansu zai cutu. Don haka tana zuwa saitin Raihana ta fizgo hannunta suka kalli juna, Raihana har sai da ta yi taga-taga za ta fadi kafin ta warce hannunta a tsorace, da karfi ta ce. "Ke kuma Malama wai mene haka? Me na yi maki za ki nunamin hauka?" Ta fadi ne cike da karfin hali domin a tsorace take, tana gudun ace aljanun Humairar ce suka tashi. Humaira wacce idanunta har sun rine tsabar bacin rai ta kalleta sosai. "Raihana kina da hankali kuwa? Kin san me kike shirin aikatawa kanki? Ɓangare masu muhimmanci da girma a jikinki wani jakin banza ya ke so ki tura masa? Kina hauka ne? Wannan saurayi ne da za ki kula? Toh wallahi muddin kika yarda kika aikamasa kin gama cutar da kanki har abada, balle kuma akai ga ya nemi ku hadu da shi a waje. Ina iliminki ya tafi? So ba hauka ba ne ki bude idanuwanki ki fidda baragurbi cikin rayuwarki." Raihana da tun da ta fahimci dagasken Humaira ta ji dukkan hirarsu sai ta hau borin kunya ga zufa na yankowa saman goshinta har yana jiƙa sumar dake kwance a wurin. "Me kike nufi? Ni ba ni da hankali ne da zan tura masa? Ko kin dauka shashasha ce ni? Toh ni nasan yanda nake tafiyar da ire-irensu don haka ki rabu da ni. Wannan rayuwata ce. Zan gudanar da ita ne yanda na so. Bai shafeki ba." Humaira ta yi shiru, can ta nisa za ta kara magana wayar Raihanan ya hau kara, aikuwa da azama ta nufi wayar har tana ture Raihana. Ɗagawa ta yi ta sa a kunne, Raihana na son dakatar da ita amma tana tsoron kar ta sha duka a hannunta. "Sweetheart na ji shiru, muna waya..." "Ba ita ba ce, wannan yayarta ce. Zan kuma yi maka gargadi da babbar murya. Wallahi wallahi ka kara gangancin neman yar uwata da tura maka wani hoto na sassan jikinta sai na nunamaka ba kowace mace ake taɓawa ba a sha ba. Sai ka raina kanka. Banza dan akuya kawai! Tirr da matasa irinku wadanda ba su ajiye komai a cikinsu ba sai tsabar iskanci da baɗala. Mu zuba ni da kai mafashi ya fasa!" Ba ta saurari me zai ce ba ta datse kiran ta wurgawa Raihana wayar tana jifanta da muguwar harara, Raihana dai kasancewar ta yi amannar wannan jinnun Humairar ne ke magana ba ita ba, ta kasa kataɓus sai rawar jiki tana ji kamar ta saki fitsari a gefe guda tana jin bacin rai da tsanar shiga hanci da kudundunen da take mata amma ba dama ta yi magana, ta kuma sa a rai za ta yi duk yadda za ta iya ta ga ta ba shi hakuri kar ya kai zancen Humaira zuci. "Idan kin kammala wayar ashararancin sai ki yi sauri ki kammala aikin Mami na jira. Shashasha da ba ta san ciwon kanta ba." Daga haka Humaira ta ja tsaki ta fice cikin zafin rai. Wayar Raihana na ta ƙara amma ta kasa ɗagawa don gani take yi da zarar ta ɗaga aljanun Humaira za su isar mata da saƙo ta kuma dawowa, wannan karon kam ta sani lugudar ta za ta yi mata. Hawaye na zubomata tana ci gaba da gyaran dakin, hawayen na bakin cikin abin da Humaira ta yi mata ne, tun da take samari a duniya ba ta taɓa yin wanda har a zuciya ta ji tana mishi son aure ba irin Musaddam, yanzu ga shi nan ta ɓata mata shirinta. Tana mishi so da zuciya daya wanda take jin ko mene ne za ta iya yi a kansa. Don haka a gaggauce ta share dakin ta fice zuwa bangaren Anna domin ta samu damar ba shi hakuri sosai. Ai kuwa duk kalar hakuri da karyar taɓin hankalin da ta dorawa Humaira duk domin ya aminta da ita ya kasa, cewa ya yi shi din son da take mishi bai je ko'ina ba tunda har za ta bari wani ya ji sirrinsu. Raihana kamar ta mutu don bakin ciki, ta tsinewa Humaira ya fi a ƙirga. Ita kuwa Humaira umarnin Mami ta cika ta sanya turaren wuta a dakin ta fice nasu dakin. Koda Ummita ta nemi sanin abin da ya jefa ta cikin ƙunci, cewa ta yi babu komai. Har ta yi wanka ta shirya ba ta cikin walwala. Misalin karfe takwas da mintoci Mubarak ya iso gidan. Su Muhsin suka cika gidan da Oyoyo, Tasleem su ma duk yanda su ke ganin yayannasu da shige musu hanci da kudundune sun yi murna da ganinsa. Humaira na gefe tana murmushi ba ta karasa ba tana karemishi kallo. Shi kam kammaninsa da Abba har ta ɓaci, shima dai ba ya kama da Mami, sai ko baƙi da laushin gashi irin na yan uwansa da ya dauko. Kansa cike taf da suma ya tara. Bayan ya zauna ganin Ummita ta karasa ta gaida shi ya amsa cikin sakin fuska ne ya sa itama karasawa su gaisa. Ya nunata da yatsa ya yi shiru alamar dai so yake ya tuno wani abin. Can kuwa ya ce. "Humaira, right?" Ta dai fahimci so yake ya tabbatar ko haka sunan ya ke sai ta gyada kai. Su Tasleem suka kwashe da dariya, ya tambayi dalili suka amsa da ba komai. Mami ta fito fuskarta cike da fara'a, ganin mahaifiyarsa ya mike tsam ya karasa ya dan rungumo kafaɗarta, ta dan tureshi tana murmushi. "Ba ka girma ko?" Ya kuwa kara marairaicewa. "Girma fa kika ce Mami, yaushe rabonki da ni don Allah?" Har lokacin murmushin take yi ta amsa. "Amma ai ana waya da videocall ko?" Da wasa ya sake ta ya juya. "Shikenan bari na koma inda na fito tunda kin ƙoshi da ganina." Da sauri ta riƙo rigarsa har duka falon aka dara. Ya ja hannunta suka nufi bangaren Abba su na hira. Abba ya yi murna da ganin ɗan nasa, ya kasa rufe baki. Nan suka hau taɓa hira karshe kuma Abban ya ce ya je ya kimtsa ya ci abinci tukunna. Da wannan ya mike ya fita, daga uwa har uban suka zuba mishi ido cike da kauna kowannensu kuma da abin da yake ayyanawa a ƙasan rai. *** Zaune yake a babban falon dake cikin Airport din Abuja, ya kalli agogon dake ɗaure a tsintsiyar hannunsa mai cike da gargasa ya fi a ƙirga, ya maida duba saman wayarsa yana latsawa. Cikin sa'a kuwa ya ji muryar ma'aikaciyar ya karaɗe wurin inda take umartar fasinjojin da za su je Kano akan su nufi ciki. Ya mike kuwa don dama abin da ya zaunar da shi kenan. Hannunsa ɗaya riƙe da trolley ɗinsa yana ja, tafiya yake da sassarfa. Bayan komai ya kammalu jirginsu ya ɗaga. Isar su keda wuya, ya yiwa abokinnasa IBB GUSAU waya. Kafin ya kai ga magana ya ji saukar muryarsa daga gefe. "Barka da zuwa." Juyawa ya yi yana dubanshi da idanunsa dake ɓoye cikin wani arnen baƙin gilashi, sai kuma ya ja guntun tsaki yana ɗan murmushi, lokaci guda ya ba shi hannu suka yi musabaha kafin su rungume juna suna cike da farin ciki. Bayan sun saki juna da mamaki ya ga idanun Ibb sun kaɗa, nan da nan ya daure fuska. "Ok, hakan na nufin ba ka yi murnar ganina ba kenan na koma inda na fito ko?" Girgiza kai Ibb ya yi ya sa hannu yana karɓar trolley dinsa yana fadin. "Hakan ba zai taɓa faruwa ba, in sha Allahu ka dawo kenan. Tafiyar kuma daga ni har Alhaji ba za mu ƙara bari ka yi irinta ba. Shekarun da ka yi sun isa hakanan." Ya shafi sumar kansa bai ce komai ba ban da baki da ya ɗan taɓe ya yi gaba kai kace ya san inda mazaunin motar amininnasa ya ke. Ibb da murmushi ya mara mishi baya. Suka jera su na gifta filin wurin, Ibb ba gajere ba ne, amma fa duk tsawonsa bai kama ƙafar abokinnasa ba, kusan su biyun duka sai ka rantse ba su ne suka gama yiwa juna murmushi da runguma ba, tafe suke su na kallon hanya kai ka ce ba su san juna ba, duk inda suka gifta sai an bi su da kallo, ƴan matan dake wurin kuwa ji suke inama inama, inama za su yi nasarar samun sa'a a cikinsu ɗaya ya yaba, da sun tabbata masu sa'a. Shi yana sanye da ƙananun kaya yayin da Ibb ke sanye cikin manyan kaya dinkin babbar riga har da hula kai kace wani Ango. "Ina ka nufa?" Ya yi tambayar fuska a haɗe a sadda Ibb ya murza sitiyari ya nufi gate din Airport din, shi ma ba tare da ya kalle shi ba ya amsa. "Ka fi kowa sanin inda ya dace mu soma manufa. Tushiya masomin dawa." Girgiza kai ya yi. "No Ibb, i am not ready for it, muje ka kai ni hotel. Hakan na fi buƙata. Please." Ba musu Ibb Gusau ya amsa da Alright, ba ya so fadi tashin da ya jima su na yi da Alhaji ya tashi a tutar wofi, ai an yi mai wuyar da suka samu ya dawo garin. Don haka kai tsaye Bristol Hotel ya kai shi ya kama mishi masauki, da wani irin walwala da annuri dauke saman fuskarsa ya fito ya rabu da shi ya kama hanya don ya je ya ba Alhaji kyakkyawan albishir. Lallai ya san da zuwan ɗan nasa, amma bai taɓa kawo wa a rana irin ta yau ba da ake shagalin bikin ƙaninsa mafi soyuwa ba a rai.08 Kasancewar gidan cike yake da jama'a ƴan uwa, makwafta har ma da abokan arziki ne ya sanya Ibb zagayawa ta ɓangaren Alhajin ya shiga ainahin falonsa na karɓar baƙi. Kamar yanda ya yi tsammanin hakan ya tarar, wato dai Alhajin ba shi ɗaya ba ne a falon, yana tare da babban yayansa Baffa Gidado sai ɗan gidan Baffa Gidadon, Harɗo. Sai ko ƙannensa guda biyu dake zaune  su ma a gefe ana ɗan taɓa hira, kallo ɗaya za ka yiwa fuskokinsu ka fahimci su na cikin annashuwa. Sallamarsa ce ta katse hirar tasu wadda ke gudana da harshen fulatanci, suka dube shi gaba daya, ya karaso yana ƙara miƙa gaisuwa a karo na biyu domin dazun daga gidan ya fita. Alhaji ya amsa gaisuwar yana bin fuskar Ibb da kallo ganin yadda yake wata irin fara'a na musamman wadda rabonsa da ganin kwatankwacinta tun a baya kafin afkuwar wasu lamura marasa daɗi. Ganin bakin Ibb na ta motsi amma ya kasa magana ya sanya Alhaji miƙewa tsaye wannan karon kirjinsa bugu yake da sauri-sauri. "Muje." Shi ne kawai abin da Alhajin yace, aikuwa kamar jira yake har da tuntuɓe a kokarinsa na bin bayan shi. Wata ƙofa suka bi wacce kai tsaye main parlour din Alhajin na cikin gidan suka faɗa. Ko zama Alhaji ya kasa hakurin yi su na karasawa tsakiya ya juyo gaba ɗayansa. "Ibrahim, ya ake ciki? Meke faruwa?" Madadin ya amsa sai kawai ya rungume Alhajin kafin ya sake shi yana dariya. "Mafarkinka ya tabbata zahiri Alhaji." Alhaji hannunsa har rawa yake ya kama kafaɗun Ibb har idanunsa sun cicciko da kwalla. "Ya..ya..ya..da..wo?" Ya yi maganar da rawar murya, jinjina kai Ibb kafin ya amsa. "Eh, FADEEL ya dawo." Alhaji ya sauke nannauyan ajiyar zuciya. "Alhamdulillah, Alhamdulillah. Yana ina yanzu? Muje ka kai ni na gansa." Ibb zai musa amma babu dama domin dagasken dai ba abin da Alhaji zai saurara. Don haka sai kawai ya juya, Alhaji biye da shi suka fito. A farfajiyar gidan suka yi kiciɓus da Ango Fu'ad wanda shigowarsa gidan kenan daga Hotel din da abokan karatunsa suka sauka. Ya karasa ganin irin rawar jikin da Alhajinsu ke yi, ga Ibb na kokarin buɗe mota. "Alhaji, fita za ku yi ne?" Alhaji ya dafa kafaɗarsa fuska a sake ya ce. "Maza shiga mota." Ba musu ya zagaya ya shiga har sannan fuskarsa dauke da mamaki, ya kuma kasa tambaya. Ibb bai ko hana Alhaji wannan yunƙuri ba don ya sani Fadeel zai yi farin ciki kwarai da ganin ƙaninnasa. ***   Ya yi wanka ya shirya tsaf cikin riga body hug fara ƙal sai blue jeans. Yana zaune yana kurɓar ruwan shayin da aka kawo mishi, hankalinsa kaf yana wajen Mahaifinnasa, wata zuciyar na ce mishi ya je ya gan shi, wata kuma na kwaɓarsa. A hankali ya ajiye mug din dake hannunsa ya jingina kai jikin kujerar yana mai lumshe idanunsa. Dogayen gashin idanun suka kwanta luf saman fatar wurin. Ji ya yi ana buga ƙofar, ya buɗe su kafin ya miƙe. Yana da tabbacin Ibb ne. Hakan yasa koda ya bude bai tsaya kallonsa ba ya juya ya koma cikin ɗakin gami da faɗin. "Wato gadina ka koma kenan?" "Muhammadu." Ya tsaya cak a tsakar ɗakin, kaf duniya mahaifinsa kaɗai ke kiransa da ainahin sunansa, da hanzari ya juyo, tuni lumsassun idanunsa sun kaɗa. Alhajin ya taho da sauri ya rungumeshi, shi kuwa ya tsaya kamar wanda aka dasa a wajen ya kasa motsi. Fu'ad da bai san wainar da ake toyawa ba sai yanzun, kawai kuka ya sanya tsabar murnar ganin yayannasa da ya nisanta da su saboda wasu dalilai. Ya karaso da sauri ya haɗa daga Alhajin har Fadeel ya rungume yana kuka. Duk jarumta irin ta Fadeel sai kawai ya ji hawayensa sun zubo. Suka saki juna Alhaji da kansa ya sa hannu yana share masa hawayen. "Ashe da raina da lafiyata ban mutu ba zan ga wannan rana? Alhamdulillah." Abin da Alhajin ya furta kenan. Fadeel ya yi murmushi da gefen kumatu yana dafa kafaɗar Fu'ad. "Ango, har ka girma za ka yi aure." Suka yi dariya har Ibb, Fu'ad kuwa yan sunkuyar da kansa gami da shafar ƙeya. Nan fa Alhaji ya matsa akan lallai sai ya tattara sun tafi gida da shi. Anan ne kuma ya tamke fuska kwarai, ya koma Fadeel ɗinsa na ainahi. "Muddin tana gidan nan ba zan iya shiga ba. I am sorry Alhaji." Jin haka Fu'ad da Alhaji suka kalli juna suka yi murmushi. Shi sai a lokacin ma ya ji nauyin Fu'ad din, wai uwarsa yake ikrarin ba zai shiga gidan idan tana ciki ba. "Yaya Fadeel, Mama ba sa tare da Alhaji, tayi wani auren a garin Kogi. Sai dai ko Anti Amarya our new Mum." Sai Fadeel ya kasa cewa komai, ya maida dubansa ga Alhajin, ya gyaɗa masa kai don ya ƙara tabbatar da abin da Fu'ad ya faɗi. "Yanzun ka shirya bin mu?" Ya jinjina kai yana murmushi. Ibb tuni ya soma haɗa mishi shirginsa. Fu'ad ya karɓi akwatin suka fito baki ɗaya, suka yi mota yayinda shi kuma Ibb ya tsaya a reception. Isar su gidan kai tsaye suka nufi sittingroom wajen su Kawu Gidado, sai dai tuni sun fice masallaci gabatar da sallar La'asar. Koda dawowarsu ganin Fadeel gaba ɗaya dakin ya kaure da murna. Magana dai ta bazu a gidan Fadeel ya dawo, babban ɗa namiji a wurin maigidan. Nan fa mata gwaggonninsa ƴan uwan mahaifinsa kowa ya fito zuwa falon. Murna kam ba a magana. Yayyunsa mata waɗanda kaf dinsu su na da aure sai guda ɗaya bazawara da aurenta ya mutu take zaune a gidan da yaranta, su din ma kowaccensu ta halarci falon. Kallonsu kawai yake yi yadda kowacce ke haba-haba da shi, murmushi kawai ya ke yi don ba shi da tabbacin ko abin nasu ya kai zuci ko aa. Sanin da ya yi musu daban a baya, ba shi da masaniya akan yanzu. ***   Raihana ce zaune a can lungun gadon Tasleem ta maƙure a gefe tana zuba kuka ga waya saman kunnenta. Musaddam take ta ba hakuri adalilin ya ƙi ya huce tun sadda Humaira ta gasa mishi zafafan maganganu. Ya kuma ci alwashin ko don ya nuna wa Humaira ba ta isa ta tsaida shi daga abin da ya yi niyya ba, sai ya kusanci Raihana ko ta ƙarfi kuma ya yi hotuna don ya shayar da ita mamaki. Yana sane da gangan ya ƙi ya huce saboda kawai ya ƙara fahimtar irin matowar da Raihanan ta yi a kansa. Sati ɗaya kenan da dawowar Yayannasu amma ko kaɗan walwalwarta ba ta dawo daidai ba ga wani irin tsanar Humairar da take ji a ƙoƙon rai amma shakkar kada ta tona mata asiri da ma tsoron ita kanta Humairar ya hana ta labartawa koda Tasleem ce balle Futuha. Sai ƙawarta da ta ba labarin, ita kuwa ƙara hure mata kunne ta yi akan kar ta yarda wata can bare ta raba ta da abin sonta. Da wannan huɗubar da kuma mahaukacin son da take yiwa Musaddam idanunta suka rufe ruf. A wannan yanayin walwalarta ba ta dawo ba sai da ta tabbatar ya haƙura bisa alƙawarin za ta zo gidan su Munirat su gaisa. Humaira ta shigo ɗakin daidai sadda Raihanan ke fadin. "Shikenan zan zo goben idan har ganina zai samar maka da nutsuwa." Wannan kalmar ta daki zuciyarta, sai dai ta dake ba ta ko kalle ta ba ta ƙarasa ciki, dama mayafin abayarta za ta ɗauka zasu je Shoprite ita da Ummita, Mami ta aike su. Raihana kuwa ganin Humaira ya sa ta shan jinin jikinta. Ta kasa magana kwakkwara sai um da humm ina jinka. Guntun tsaki Humairar ta ja ta fice, ta sha alwashin ko ina ne a goben sai ta bi bayanta ta kuma kama ɗan iskan dumu-dumu ta ci uwashi.   A falon ta haɗu da Ummita, har suka soma tafiya ta ga dai hira suke amma ita ke kiɗa da rawarta hakan yasa ta dube ta. "Wai ke lafiyarki kin wani haɗe rai kamar wacce aka aikowa saƙon mutuwa? Koda dai ɓata bakina nake dama ai halinki ne. Amma naga ai yanzun ba kiciɓus kika yi da maƙiyinki naki ba ko?" Tana nufin saurayi, Humaira ta ja tsaki ta girgiza kai. "Ba komai fa." Taɓe baki Ummita ta yi ba ta ƙara magana ba sanin hali. Sai kuma can don kanta ta saki fuska suka hau hira. Kayan maƙulashe irin su Jam, Ketchup, Mayonnaise da sauransu, shi Mami ta bada su siyo na Yaya Mubarak. Sun kammala suna dab da ficewa suka tsinkayi sallama a gefensu. Lokaci guda suka juya ga mai shi, wani matashin saurayi ne gajere mai ƙiba. Irin ƙibar da ba ta da muni. Daga yanayin yadda ya saki fuska za ka fahimci mutum ne mai fara'a. Humaira wacce kallo ɗaya ta mishi ta dauke kai gami da ci gaba da tafiya, ganin haka itama Ummita ta mara mata baya, ya kuma bin bayansu da sauri ya sha gaban Humaira. "Ranki ya dade, kiyi hakuri na tsayar da ke. Nima kuma na san darajarki da ƙima ta zarce a tsayar da ke a hanya a..." "Kai Malam saurara don Allah! Ni nan da ka ke gani da mijina a hannu don haka kama kanka. Muje." Ta fisgi hannun Ummita ta bi gefe suka fice a nan. Hakan da ta yi ba karamin ɓatawa Ummita rai ya yi ba, ba yau farau ba, idan da sabo ya ci ace ta saba da ganin irin cin kashin da yar uwarta ke yiwa samari. Ita har mamaki take yadda gaba daya Humairar ke sauyawa kamar ba ta taɓa zama haɗa hanya  da wani abu wai shi mutunci ba. Ta fara gasƙata zancen Raihana da ta ce jinnu ne da ita. Kamar kuma ba ita ba, sai ga shi a hanya ta saki rai sun ci gaba da hirarsu lafiya lau. ***   Washegari tun safe take dakon Raihana tana jira ta ga sadda za ta fita ta mara mata baya. Aikuwa wuraren karfe biyu tana zaune a falon da littafi a hannunta na koyon rubutun hausa tana ɗan duba inda muhsin ya biyamata, Mami kuwa na gefe tana yankewa Muhsin farce sai ga Raihanar,  ta tambayi Mamin zuwa gidan ƙawarta Munirat. Farko Mamin ta hana sai can kuma da ta dage da naci ta samu Mamin ta aminta. Humaira ba ta ko ɗaga kai ba balle ta yi yunkurin miƙewa, har sai da Mami ta soma barin falon, tana nan zaune ba ta ko motsa ba har Raihana ta fito cikin shigar fita, ta ci wani arnen kwalliya ta sanya riga da siket da ya yi matuƙar kama ta sai ta dora afterdress a sama wanda da shi da babu duk ɗaya. Tana fita Humaira ta yi wuf ta miƙe ta zari hijabinta dake hannun kujera. Tuni ta yi shirinta dama ta sa kuɗi a bayan gidan wayarta. Bayan Raihana ta bi, sai da ta kai ƙarshen layin ta nemi can jikin wata  bishiya ta ɓoye fuskarta cikin facemask. Haka ta shiga ɗan sahu ta bi bayanta har gidan su Munirat. Kamar yanda ta zata kuwa hakan ne, wani saurayi matashi ne tsaye jikin wata mota suna hira da wata budurwa. Raihana na karasawa ta cafke da budurwar da bayan ta matso ta gane Munirat ce saboda ta taɓa zuwa can gidannasu ba sau ɗaya ba ba biyu ba.     Can kuma sai Munirat ta shige gida ita kuwa  saurayin ya buɗe mata gidan gaba ta shiga ya maida ƙofa ya rufe. Baƙar mercedez ce mai baƙin tinted wanda duk iyaka hangen mutum bai isa ya ga na ciki ba. Humaira ta ji ƙirjinta na dukan tara-tara da wani irin sauri ta soma takawa ta nufi wajen kai ka ce kafin ta karasa abin da take tsoron afkuwarsa ya afku. Da tsayuwarsu a wajen, da shigar budurwar motar, duka ya faru ne akan idanun Ibb da Fadeel wadanda ke tsaye a ƙofar gidan su Fadeel ɗin su na taɓa hira. Ya rako Ibb ne zai wuce gida suka tsaya. Ganin shigar budurwar ya sa Ibb jan tsaki. "Wallahi ina mamakin rayuwar ƴan matan yanzu da ba su da kunya kuma ba su san mutuncin kansu ba. Yau da ƙanwata ce daga ita har shi sai sun raina kansu." Ya faɗi ransa na wani irin ƙuna, Fadeel kuwa da zuciya ta kai mai wuya bai san sadda ya soma takawa ba da sassarfa hakan da ya yi ya sa Ibb bin bayansa da sauri ya dakatar da shi sanin hali. "Aa Fadeel, please don't, ba ka san waye ba a.." "Sai nasan waye? Idan ƙanwartaka ce za ka zuba ido kana kallo rayuwarta ta ɓaci!" Yana kai wa nan ya fisge hannunsa, sai dai kafin ya kai ga tafiya suka hangi Humaira wacce gadan gadan ta nufo motar a fusace. 09 Zuciyar Humaira har wani tafarfasa ta ke yi, tana isa ta sa hannu ta ja murfin motar cikin sa'a kuwa ƙofar ta buɗe. Raihana wacce yatsunta ke sarƙe da na Musaddam gaba ɗaya ta kasa sukuni amma ƙarfin soyayyarsa a ruhinta ya sa ta daurewa ranta, daidai sadda ya kai bakinsa ne da nufin sumbatar hannun aka wangale ƙofar hakan ya sa a firgice gaba ɗaya suka juya. Humaira ta fisgo Raihana, ba shiri ta fito har tana tuntsirawa. Ba ta yi wata wata ba ta ɗauke ta da mari hagu da dama ga wasu zafafan hawaye da suka zubo saman fuskarta lokaci guda. Musaddam tuni ya fito ya zagayo wurinta, hannu ya ɗaga shi ga marar kunya zai ramawa Raihana marin, amma tuni Humaira ta riƙe hannunsa ta ba shi nasa rabon. Hannunta har rawa yake ta sa hannu ta fisge facemask din da ke rufe a hanci da bakinta. Fadeel ya yi mata ƙuri da idanu babu ko kyaftawa yana jin tamkar gangar jikinsa ne kawai tsaye a wurin, hannu ya sarƙe a kirji yana so ya ga matakin da za ta ɗauka. Humaira da ba ta san wainar da ake toyawa ba, gaba ɗaya ba ta tattare da nutsuwa hankalinta kacokam a tashe yake, yana kan Musaddam da take jin kamar ta shaƙe shi. Ɗan firit da shi sai sirantaka, fari ne yayinda lebbansa suke baƙake wuluk shaidar yana shan sigari. Hannunsa dafe da ƙunci yake duban Humaira rai ɓace ya ce. "Ke! Ni kika mara?" Bai yi aune ba ta kara wanke shi da mari. "Yanzun ka daina tantama? Eh marinka nayi! Da kuma ace ni wata mai ikon ce, abin da ya fi mari shi zan maka. Ɗan iska marar tarbiyya! Ka yi amfani da son da ka ga yarinya na maka za ka cutar da ita saboda a gidanku ba a baka isassan tarbiyyar islama ba sai na bokon da bai amfaneka da komai ba. Idan har ba ka raba kanka da kanwata ba ina maka rantsuwa da Allah sai na yi maganinka ta yadda rayuwarka za ta ƙare a kurkuku. Ke kuma..." Ta juya gaba ɗaya ga Raihana wacce ke kuka ga dukkan ilahirin jikinta na rawa. Ba ta jin an taɓa tozarta ta irin yau, a gaban saurayin da take yiwa son duniya? Lallai Humaira ba ta da kirki ko kaɗan. Aljanun nata ma ƴan iska ne na ƙarshe da alama. "Kin ɗauka ba shi jikinki shi ne zai sa ya ga mutuncinki ya gane irin son da kike mishi har ta aureki? Toh kin yi kuskure, wallahi wallahi duk sadda kila bari wannan ɗan akuyan ya kusanceki kin cuci rayuwarki har abada Raihana, za kuma ki yi kukan nadamar da babu mai share maki hawaye. A haka kuke kirana da ƴar kauye, wannan ita ce wayewar? Toh wannan birnin naku na jahilai ku ke ciki, idan za ki farka tun wuri ki farka idan kuwa ba haka ba wallahi muddin irin haka ta ƙara faruwa a kunnen Abba. Wuce kuma mu tafi tun ban kakkaryaki ba." Raihana ta dubi Musaddam da ya haɗe girar sama da ta kasa yana kallonta, ta maida duba ga Humaira wacce ke cika da batsewa kiris take jira ta fashe ga hawaye kace-kace a fuskarta. Ta lura ma jikin Humairar har rawa yake. "Muddin kika bi umarninta ki sani daga yau babu ni babu ke Raihana, alaƙarmu ya zo karshe. Sannan ke kuma ba ki san waye ubana a ƙasar nan ba ko? Zan nunamaki daga kaina ba za ki ƙara gangancin marin wani namijin ba." "Musaddam ɗan gidan Alhaji Jafar Nababa, right?" Gaba daya har Humaira suka juya a inda suka tsinci muryar, Raihana ta yi mutuwar tsaye ganin Ibb Gusau mutumin da yar uwarta Futuha ke mahaukacin so tare da wani haɗaɗɗen guy wanda ko fuskarsa da take a haɗe ka kalla, sai ya burgeka. Kunyar da ta ji ne ya sa ta saurin amfani da gefen mayafinta ta rufe baki da hancinta gudun kar su gane ta. Humaira kuwa kallo ɗaya ta musu ta maida duba ga Musaddam ɗin fuskarta har lokacin a mugun ɗaure tana jiran ta ji amsar da zai ba da. Musaddam ya kai duba ga me maganar, nan da nan ya ji gumi ya karyo masa, Malaminsa ne a jami'a da ya taɓa yiwa gadara da matsayin Ubansa, shi kuwa ya nuna masa nashi Uban da matsayi sun kere na babansa. A sanadin wani rikicinsu sai da Musaddam din ya yi kwanaki uku a ofishin ƴan sanda kafin a fiddo shi. Ya kasa cewa komai sai shafar ƙeya, Ibb Gusau ya nuna shi da yatsa. "Kai ba za ka taɓa nutsuwa ba kenan a rayuwa ko? Ina mai gargadinka, wannan ya zama na ƙarshe, ke kuma zan ba ki lambata duk sadda kika ƙara ganinsa da ƙanwarki ki kirani kai tsaye nasan maganinsa. Ke kuma ki yiwa kanki faɗa ƴanmata, kar ki bari shaiɗan ya kaɗa maki ganga, irin su Musaddam ba su dace da ke ba. Daga ganin yanayin ƴar uwarki an san daga gidan mutunci ki ka fito saboda haka please be careful." Raihana da ta yi mutuwar tsaye da mamakin mutumin da Futuha ta ce ba ya magana mai tsawo yana zuba zance ta gyada kai. Ga kuma wani iri da ta ji cewa wai zai ba Humaira lambarsa. Aikuwa Humaira ta miƙa mishi wayarta ya sanya mata lambar ya danna kira ta fito kan wayarsa sannan ya miƙa mata. Musaddam dai na tsaye kamar an kafe shi a wurin ya kasa motsi sai wani ɗaci da ya ke ji a maƙoshi ganin an dake shi an kuma hana shi kuka. Ya yi biyu babu kenan. "Ko za su bi ka ka sauke su a gida?" Ya yi furucin da sassanyar murya. Sai a sannan ma hankalin Humairar ya kai gareshi karo na biyu don ta mance ma  da wanzuwarsa, ranta ya yi fari sol da taimakon da Ibb ya yi mata, ko ba komai ta ga tsoro fal a saman fuskar Musaddam wanda hakan ya fi komai faranta mata. Ganin irin kallon da Fadeel ke jifanta da shi ya sa ta kauda kai. "Aa mun gode, zamu hau ɗan sahu." Fadeel kamar ya tanka sai kuma kawai ya basar bai ce uffan ba. Humaira ta kalle su, kalmar godiya ce kadai ta fito a bakinta kafin ta juya ta dubi Raihana. "Muje." Ba musu kuwa Raihana ta bi umarninta, zuwa yanzu jikinta a mugun sanyaye yake. Ta dai tabbata Humaira ta fi ƙarfinta. Ba kuma ta son tada wani borin su Ibb su ƙara ganin rashin kunyarta ƙarara. Bayan tafiyarsu, Ibb ya shiga yiwa Musaddam faɗa mai haɗeda nasiha, a karshe  ya ba shi damar tafiya. Sai da ya bar wurin sannan ya dafa kafaɗar Fadeel yana murmushi. "Toh ya aka yi?" Fadeel ya zura hannuwansa cikin aljihu ya fiddo hannunsa na dama riƙe da waya ya miƙawa Ibb gami da ɗan ɗara  gira kaɗan. Dariya Ibb ya yi ya girgiza kai. "No, haba Malam, da wuri haka?" Ya narkar da wuya. "Please, ina rantsuwa da Allah ban taɓa jin abin da na ji a kan wata ba sai ita." Murmushi Ibb ya faɗaɗa. "Alhaji da sannu dai Allah zai cika masa burikansa." Guntun murmushi Fadeel ya yi. "Ko? Kai kuma kana neman ka dakile faruwar hakan." "Ah wane ni? Ba ni na sanya maka." Ya karɓi wayar Fadeel da tuni ya buɗe, lambar Humaira ya sa a ciki sai kuma anan ya dafe goshi. "Oh no, ka ga ko sunanta ba mu sani ba. Da me zan maka saving?" Jin haka ya lumshe idanunsa yana hasko kyakkyawar fuskar Humaira wacce kumatunta har wani sheƙi suke saboda fushi, ya kuma lura ko ya ya ta buɗe bakinta sai wushiyarta ta bayyana. A hankali ya ce. "Mrs Fadeel." "What?" Ibb da kunnuwansa kamar ba su ji ba ya tambaya. Buɗe idanunsa ya yi ya dube shi dakyau. "Yes, haka za ka yi saving lambar." "Aa, riƙe ka yi da hannunka. Ka gani koda wani abun ya je ya zo, ba za ka kalle ni da shi ba." "Babu abin da zai je ya zo face alheri. Da yardar Allah ba ta da miji sai Fadeel." Ya ba wa Ibb amsa sa'ilin da ya sa hannu ya karɓi wayar. Aikuwa da hakan ya yi saving sunan. Ibb dai mamaki ma yake, to kodai ɗan lokacin da ya kwashe ba ya tattare da su ya sauya ne daga yadda ya san shi? Mutum da zancen aure ma ba ya so a yi mishi, daidai da hira idan ta budurwa ce aka ɗauko cikin abokai yanzun gayyar za ta watse a wurinsa don tsam yake tashi ya bar musu wurin yana mitar ba shi da lokacin shirme. "Sai goben?" Maganar Fadeel ta katse mishi tunanin, ya sauke ajiyar zuciya. "Allah ya kaimu. Amma ina mai ba ka shawarar kada ka zurfafa, duk abin da aka zurfafa ana shan wuya a cikinsa. Balle kuma irin wannan faɗawar da ka yi lokaci guda." Madadin ya amsa sai ya yi murmushi ya soma tafiya kawai, sanin da Ibb ya yi shikenan sallamar tasu ya sa shima ya nufi motarsa cike da fatan shi din ma Allah ya kawo mishi mace ta gari ya huta da gorin ƙannensa sun yi aure sun bar shi da Mahaifiyarsa ke yawon mishi. ***   A can gida kuwa, Mami tun da ta ji wai Humaira ta fita ba da saninta ba gaba daya ta ji ta kasa sukuni. Har ta kasa ɓoye ɓacin ranta ta hau faɗa a falon. "Wannan wani sabon salo ne da har Humaira za ta sa ƙafa ta fice a gidannan ba tare da neman iznina ba? Me take so na faɗawa Abbanku idan ya tambaye ta?" Tasleem da Futuha suka kalli juna suka taɓe baki, yayinda Ummita da aka kira tuhumar ko ta san inda take, ta ke gefen kujera a zaune. "Toh wai Mami, ba Humairar na da waya ba? A kira mana." Faɗin Mubarak wanda ke shigowa falon daga masallaci, tun kafin fitarsa Mamin ke faɗan fitar har dai ya dawo ba ta chanja zani ba. Ganinsa ne ya sanya su Tasleem nutsuwa. Mamin kuwa dubansa ta yi kafin ta kauda kai ta ja guntun tsaki na takaici. "Kira na nawa kuma? Wayarta idan ba a kashe take ba to na fi tunanin babu network." Ya kai duba ga Ummita. "Ke ba ta faɗamaki komai ba?" Kafin Ummita ta amsa, Futuha ta yi caraf. "Nima dai ita nake zargi don babu ta yadda za ta fita ace ba ta sanar mata ba. Bakinsu daya wallahi Yaya." Kallon da ya watsa mata ya sa ba ta ƙara cewa uffan ba, Mami ta ja tsaki karo na ba adadi ta nufi ɗakinta. Ganin haka Ummita ta miƙe ta yi nasu dakin da zummar gabatar da sallar La'asar, ita kanta tunanin da take yi bai wuce na inda Humaira ta je ba tare da neman iznin Mamin ba kamar koyaushe. Tsoronta kar Abba ya dawo ya tambaye ta ace ta fita alhalin ba ta da makaranta yau. Aikuwa dai sai wuraren biyar da mintoci suka shigo gidan, ko ci kanki ba wanda ya cewa wani a cikinsu. Su Yassar dake zaune cikin abokansu a kofar gidan su ka bi su da kallo. "Ga uwar girman kan gidannan ta dawo." Faɗin wani abokin Yassar yana nuni da Humaira. Tun ranar da ya yi gangancin kulata da sunan so ta ci mishi mutunci yake jin tsanarta. Yassar tsaki ya ja. "Kai ka so ai dama ka ga kalar nata girman kan, amma ga mata a gari kamar ƙasa ka rasa ta kulawa sai wannan ƴar ƙauyen nijar din?" Sauran suka yi dariya. Shi kuwa Yassar miƙewa ya yi ya bi bayansu ganin kamar Raihana na sharce hawaye, jikinsa har mazari yake don muddin ya kasance Humaira ce sila to ya rantse sai ya rama mata koda kuwa gaban Abba ne ba Mubarak ba. *** A falon gidan suka iske su Futuha zaune, sallamar Humaira ta dakatar da Ummita daga shiga kicin, ta dawo cikin falon da sauri don ta ganewa idonta ko ita ɗin ce. Futuha da Yasmeen kuwa ido suka bi Raihama da shi ganin yadda fuskarta ta yi ja ga shatin yatsu kwance saman fuskarta. "Ke, Raihat, me nake gani haka? Uban waye ya mareki?!" Tasleem ta faɗi da buɗaɗɗiyar murya tana kallon Humaira. Humaira da ita dinma kiris take jira ta dube ta dakyau. "Ni ce nan, ko za ki rama mata ne?" Aikuwa jin haka gaba daya Tasleem da Futuha suka yo kanta, ta kuwa shiga tarewa, duk wacce ta bugeta sai ta sa hannu ta rama da iyakar ƙarfinta, duk da cewar su biyu ne a kanta, ta yi iyakar kokarinta amma itama ta ji jiki. Ummita ta hau kwala ihun kiran Mami, ga Yassar a gefe da ya ƙi ya tsawatar don dama ya jima da haushin Humaira a ƙoƙon ransa. Raihana na ihun su kyaleta akan ba ita ce ta mare ta ba amma inaa dama sun jima su na dakon rana mai kamar ta yau din hakan ya sa da gayya suka yi biris da ita. Yayinda a ɓangarenta shakkar tonuwar asirinta take musamman da ya kasance Yaya Mubarak na gari, ta sani koda ace Abba bai taɓa lafiyarta ba, shi kam ban da lafiya ma, hatta da wayar da take tunƙaho da ita sai ya raba ta da shi. Kusan a tare Abba da Mami suka shigo falon. Wata tsawa Abba ya daka da ta sa gaba daya suka saki juna, Humaira gefen kumatunta na fidda jini sakamakon yakushi da ta sha da dogayen faratan Futuha. Su kuwa daga mai riƙe baya, sai mai riƙe gefen fuska da naushin Humaira ya kumbura har ya tasa. Mami zuciyarta ta yi wani iri, ta kasa magana ta yi shiru tana kokarin hadiye abin da ke cinta. Abba ya karaso falon ya dube su gaba daya. Humaira tuni ta durkusa, ganin haka su ma suka durƙusa. "Mene ne hakan? Wane sabon shashanci ne haka? Ke Humaira wadannan ba su girmeki ba? Ku kuma manyan wofi ba kanwarku ce ba? Duk me ya kawo rigimar ne?" Humaira ba ta ce uffan ba, Yassar ya yi saurin sa baki. "Abba ba fa wani abu ba ne, Humaira ce ta mari Raihana har fuskarta ya yi shatin yatsu, shi ne don Tasleem ta yi magana kawai sai ta taso mata da faɗa wai ta mara ko akwai shegen da zai rama mata. Kalmar shege ya fusata su suka yi kanta da duka." Murmushi mai ciwo Humaira ta yi lokaci guda hawayen da take dannewa suka zubo samam fuskarta, zubar hawayen a inda Futuha ta mata rauni ya sa ta jin zafi amma ba ta ko damu da sharewa ba don wata azabar ta fi wata, ita daya ta san me take ji a zuciyarta. Ummita ma hawayen take na ganin yadda gaba daya Yassar ya juya magana. Ita kuwa Mami, karasowa ta yi ta ɗaga fuskar Raihana tana kallo. Tabbas mari ne, fuskar ta yi ja, ga yatsu kwance ta ko'ina a gefen fuskar. "Mari?! Mamana dagaske ne kin mari ƴar uwarki? Me ta yi maki da zafi har haka da kika ɗau hukunci da kanki?" Raihana nan fa ta shiga zare-zaren ido, Humaira ta kalleta na ɗan dakiku, har abada ba za ta tona mata asiri gaban iyayensu ba. Mami ta kai matsayin da ko laifin ɗiyarta ta gani za ta iya rufa mata asiri don haka dakyar ta haɗo abin fadi. "Ka yi hakuri Abba. In sha Allah ba zan kara ba." Nan kuma Abba ya kara fusata. "Oh, dagasken kenan kin mare ta ko?! Wannan ai hauka ne! Kamar babu manya a gidan? Ke waye ya mare ki?" Nan ya shiga bude mata wuta, sai da ya gama sannan ya maida hankali ga su Futuha wadanda duniyarsu ta yi dadi, ko babu komai wacce suke yiwa kallon ta fi su a wurin Abban yau ya rufe ido ya wanketa tas kamar zai kai duka. Hakan yasa ba su ji zafin nasu faɗan sosai ba. Sai da Mami ta sa baki sannan ya bar wurin. Humaira na ta kallon fuskar Mamin don ta hasaso yanayinta amma ba ta fahimci komai ba sai dai jikinta ya yi sanyi ganin ko kallonta Mamin ba ta yi ba. Hakan na nufin ba ta ji dadin hukuncin da ta yiwa Raihanan ba? *** "Ban da abinki Humaira, duk son da Mami za ta nuna mana ai ba zai kai son ƴaƴan da ta haifa da kanta ba. Ni ba abin sa ya fi ban haushi irin yadda ba a damu da tambayar inda ku ka je ba. A jikina nake ji ba hakanan kawai za ki mari Raihana ba, akwai abin da kike ɓoyewa. Amma wace rana zai maki? Zai siya maki daraja ne a gun Raihana da yan uwanta kike zato? Babu ɗaya fa, halinsu ne ba na jin za su taɓa sauyawa." Ummita ke zubo mata zance sa'ilin da suke kicin su na gudanar da girkin dare, awanni kusan biyu bayan afkuwar komai, Humaira wacce tuni ta yi wanka ta sauya shiga cikin riga da siket ƴan kanti ta yi murmushi daidai sadda ta motsa tukunyar miya ta rufe gami da rage wuta. Juyowa ta yi tana kallon Ummita da ta mayar da hankali tana juye farar shinkafar da ta dafa a cikin ƙaton warmer. "Ban damu da abin da kowannensu zai ce ba, ban kuma damu ko Raihana ta sauya ba ko aa, abin da na sani shi ne, ko a gaban waye, kuma a ko'ina ne, su din ko naƙi ko na so, ƴan uwana ne na jini, ba zan taɓa ganin abin da zai cutar da su na yi shiru na zuba ido ba, sai inda karfina ya kare. Kar mu ja zancen Ummita, ni yanzu damuwata Mami, ta ina zan soma wanke kaina a wajenta? Na mari diyarta har shatin yatsuna sun bayyana ƙarara a saman fuskarta, anya kuwa za ta karɓi dukkan hanzarina? Ni dai na san soyayyar uwa akan nata, dagaske ne Mami na yi mana so na hakika, amma wace uwa ce za ta kara kallonka da ƙima alhalin ka sa hannu ka daki nata?" "Sai ni nan, Maryam." Gaba daya suka kalli bakin ƙofar shigowa kicin din, Mami ce wacce ta tsinkayi zantukan Humaira na karshe. Humaira ta zuba mata idanu tana so ta ga ko za ta fahimci yanayinta, ba ta gane komai ba sai murmushin da ta gani kwance saman fuskarta. Kicin din ta karasa shigowa sosai ta ce. "Sai ni nan Maryam, haba Humaira, kina zaton ba ni da hankali ne? Na sani duk yadda aka yi akwai wani abu da Raihana ta yi kika yi mata wannan hukuncin. Kar ki manta tazarr fitarku ba nisa, da nayi nazari sai na ga kodai wani wurin za ta je da bai kyautu ba kika bi bayanta? Kar ki sa komai a ranki, koda ba ki faɗi komai ba ni na fahimceki kinji ko?" Humaira ta sauke nannauyan ajiyar zuciya na samun nutsuwa. Wai mami wace iri ce acikin matan uba? Komai nata daban ne, kirkinta da kawaicinta akwai mugun yawa. Sai kunya ta lulluɓe ta, ta sunkuyar da kai. "Kiyi hakuri Mami. Ban yi..." "Bana buƙatar ji ko sanin komai kinji ko? Komai ya wuce. Ku hanzarta shirya kayan abinci, Abbanku na jin yunwa." Suka amsa da toh a gaggauce suka ci gaba da aiki, Mami ta fice daga kicin din fuskarta ba yabo ba fallasa. *** Kwance take saman gadonta tana buga game a waya, hankalinta kacokam ya tafi a game din sai ga kira ya shigo. Ta yi tsam tana duban wayar, lamba ce da ba ta da masaniya a kanta. Ganin haka sai ta katse kiran ta ci gaba da game dinta, aka kara kira, ta katse, a na uku ta ɗaga a fusace amma sai ta danne ta yi sallama. Jin muryar namiji ya amsa sallamar ya sa ta jin wani abu tun daga tsakiyar kanta har zuwa yatsun ƙafa, ba ta san ma'anr hakan ba. "Ina mai ba da hakurin yi maki katsalandan a rayuwa. Hope ba za ki damu ba idan na ce jiya na karɓi numbernki wurin Ibb Gusau." Shiru ya biyo baya, ita ba ta fahimci komai ba don har ga Allah ta mance da su. Jin shiru ya sa Fadeel ƙara magana a tausashe. "Ok, ba ki gane ba ko? Jiya ni da abokina da ya ba ki numbernsa akan wannan saurayin ƙanwartaki, Musaddam nake tunanin sunansa ko?" Nan da nan ta tuna komai, wannan me kama da aljanun ne mai shegen kallo. Ta ja guntun tsaki kaɗan. "Uhm, na gane. Ina fatan lafiya?" Ya yi shiru yana jin amsarta a wata kala na daban, madadin ta ba shi haushi sai kuma ya ji bai ji haushin nata ba. "Lafiyar ce ta sa na kiraki. Suna na Fadeel, magana nake son mu yi amma ta fi ƙarfin waya, idan kin ba ni dama ko zan iya sanin kwatancen gidanku?" Ranta ya soma ɓaci, ta ji wani abu na taso mata. "Idan maganar ba za ka iya yinta a waya ba don Allah kada ka ƙara gangancin kirana. Hakan zai fi maka alheri, sannan ina bukatar ka goge lamba ta a wayarka, tunda ba wani muhimmin abu ne ya sa ka kira ba." Tana kai wa nan ta katse kiran, ta yi wurgi da wayar saman gado, game din ma ya fice a kanta. Ita kaɗai ce a ɗakin, sai ga Raihana ta shigo. Ko kallonta ba ta yi ba ta mike ta faɗa banɗaki, koda ta fito ganin Raihanan zaune saman gadonnata yasa ta mamaki. Fuska a ɗaure ta ƙarasa. "Malama lafiya?" Jiki a sanyaye Raihana ta soma magana. "Kiyi hakuri Humaira, na ja an maki faɗa an kuma zalunceki. Don Allah ki yi hakuri. Ina neman gafararki bisa dukkan abin da na taɓa yi maki a gidannan. Ban kara gasƙata kaunarki gareni ba sai a jiya da kika shanye faɗan Abba ba ki faɗi ainahin abin da ya faru ba. Wallahi na ji kunyarki sosai, kiyi hakuri ki yafemin." Taɓe baki Humaira ta yi tana fadin. "Ya wuce. Kar ki damu." "Dagaske kike?" Ta tambaya da sauri kamar za ta yi kuka don muryarta ta karye, Humaira ta zauna a gefe. "Ni ban taɓa binku da kallon maƙiyana ba, kallon da nake maku na ƴan uwana ya bambanta da irin wanda ku ke yimin. Sai dai dukkan wannan ba zai sa na ga abin da zai cutar da ku na kasa magana ba. Idan na yi hakan na ci amanar kaunar da Mami ke nunamin. Raihana mutunci da darajar mace ya fi gaban ta tsaya ta siyarwa wani ƙaton banza a waje. Musaddam da kike gani wallahi ba zai taɓa aurenki ba matuƙar kika yarda kika ba shi kanki a waje, ke koda ba ki bayar ba, yaron ba aure ne a ransa ba face iskanci. Idan kuma dagasken auren yake sonki da shi, meyasa bai taɓa zuwa nan ƙofar gidanku da sunan zance ba, kema kin san karya ne kawai. Tun wuri ki yiwa kanki faɗa ki rabu da shi zai fiye maki alheri." Raihana da tuni ta soma hawaye ta kamo hannun Humaira. "Toh naji Humaira, amma wallahi ina sonsa, wani irin so ne da ban san yanda zan fara yakice shi ba a rai. So ne da ya rufemin ido naji ko me Musaddam zai nema a wurina zan iya yi mishi." Sai kuma tausayinta ya lulluɓe ta, tana kuma godewa Allah da bai ɗora mata son kowane ɗa namiji ba balle har ya wahalar da ita. "Wannan son za ki yaƙa, domin halaka ne a wajenki. Musaddam ba sonki yake yi ba muna nan da ke watarana za ki ban labari. Ki kai kukanki wurin Allah sannan ki shagaltar da kanki wajen duk abin da kika san zai dauke maki hankali daga tunaninsa. Nima kuma zan tayaki addu'a har sai Allah ya amsa, ya rabaki da wannan makahon son. Ke ina kika hango dacewarki da shi wai? Wallahi ta ko'ina ke din ba ajinsa ba ce, ban da ma dai shi son da kike ikrari bai san inda zai je ba, ai sawun giwa ya shafe na raƙumi." Murmushi Raihana ta yi cikin jin salama, sai kuma hira ta buɗe tsakaninsu, tana ba ta labarin ainahin yanda aka yi ta hadu da Musaddam din. Humaira ta gefen ido na kallon wayarta da ke silent tana ta haske alamar shigowar waya amma ta yi biris da ita. Su na a haka Futuha ta dawo daga makaranta ta iske su, mamaki ya dabaibayeta, ta cire facemask din da ta sa don ɓoye kumburin gefen bakinta da Humaira ta daka, ba ta cewa Raihanan komai ba sai zama da ta yi gefen nata gadon tana ci gaba da kallon ikon Allah. Ita kuwa Humaira ko ta nuna ta san da wanzuwar wata a dakin bayan su. Can kuma Raihana na juyawa tana yiwa Futuha magana ta ga hasken wayar Humaira ta jawo. "Lah, kinga fa kiranki ake ta yi. Lamba ce. Kodai Ibb ne?" Jin sunan da ya fito bakin Raihana ya sa Futuha zaro ido waje a razane. Ita kuwa Humaira fuska ta yamutse. "Waya sani, tun dazu ya kira wai wani kwatancen gidanmu." "Wane Ibb din kika nufi Raihana?" Suka dube ta, sam Raihana ta mance, yanzu me za ta ce idan Futuha ta dage akan son sanin komai? Kada dai allura ta tono garma. Ita kuwa Humaira sai a sannan ta tuno ashe fa a hirarsu tana jin Futuha na yawan maganar son da take yiwa Ibb Gusau da haduwarsa. Kodai shi ne Ibb din da take magana? "Ibb Gusau wanda kika sani." Humaira ta furta da murmushi saman fuskarta, ta karbi wayarta a hannun Raihana ta katse kiran amma sai ta sa a kunnenta kamar gaske ta hau fadin. "Assalamu Alaikum, ina neman afuwa ka kira bana kusa. Fatan ka karasa gida lafiya?" Tana kaiwa nan ta sa kai ta fice daga dakin, sai da ta isa falo sannan ta kwashe da dariyar ganin yanda Futuha ta cika tayi tam har gefen bakinta da ya kumbura sumtum yana kyalli. Ta dai san ta harba mata bomb a zuciya.10 Dariya take yi har ta shiga kicin ɗin, Ummita dake amsa waya tana lumshe idanu ta yi azamar katsewa tana dubanta. Humaira kuwa ganin haka ta karasa fuska dauke da walwala tana bin ta da kallon tsokana. "Waya kike amsawa ko? Shi ne ina shigowa kika yi saurin katsewa. Nidai ya kamata zuwa yanzu na san waye wannan majnun ɗin naki." Ummita dai ba ta tanka mata ba sai maida hankalin da ta yi wajen ɓarar tafarnuwa tana murmushi, sai kuma ta share zancen da hanyar fadin. "Wai dariyar me kike yi ne?" Sai a sannan ta tuna abin da ta yiwa Futuha, dariyar ta kuma taso mata. Ta fayyacewa Ummita labarin, baki buɗe take kallonta. "Ke kuma ina kika samu lambar shi?" Ita shaf ta mance Ummita ba ta da labarin komai, ta yi ajiyar zuciya. Labarin da ba ta so bayarwa ba amma ya zama dole ta sanarwa Ummita don ba ta da yar uwa kuma aminiya sama da ita. Ta labarta mata duk abin da ya faru da sanadiyyar marin Raihana ta kara da jan tsaki da fadin. "Shi ne wannan mayen ya takuramin da kira fa, toh ita Raihana ta yi zaton ma Ibb din ne. Ni kuma don na shaƙawa ƴar banza shi ne na sa wayar a kunne ina wayar gangan na soyayya." Ummita da iyakar burgewa yar  uwar ta burgeta sai ta shiga murmushi kawai da mamakin kaifin hankali da tunaninta, ta sani ko ita ba lallai ta iya shiru a irin wannan gaɓar ba. Amma ta gwammace kowa ya yi mata kallon rashin kyautatawa akan dai ta bayyana gaskiyar abin da Raihana ta aikata. Sai kuma karar wayar Ummitan ya katse tunaninta. Da sauri har su na rige-rigen ɗauka ita da Humairar, sai dai a karshe wayar ta faɗa hannun Humaira tana dariya, ga nata wayar ta na ta haske shaidar faɗowar saƙo amma ko a jikinta. "Ki yiwa girman Allah kada ki ɗaga." Gwalo ta yi mata suka hau zagaye a kicin din. "Sai kin rantse cewar za ki fadamin ko wane ne mai kiran." Da sauri ta amsa. "Eh wallahi zan fadamaki, yanzu dai ban wayar." Ba musu ta ba ta tana dariya, ta ja kujera ƴar tsugunno ta zauna tana duba nata wayar da saƙon ya faɗo tun ɗazun. _*Kar ki yi tunanin akwai abin da zai sa Fadeel ja baya ko tsoro. Ki tambayi wadanda suka san waye shi, yana da naci akan abun da zuciya da gangar jikinsa suka yi na'am da shi. Ba shi da saurin karaya, ba kuma ya jin zai soma daga kan ɗiya mace. Ina kuma farin ciki shaida maki ke ce halittar farko a mata da na ji zuciyata ta yi na'am da kasancewarta rabin jiki kuma abokiyar rayuwata. Nasara tana tare da wanda ya miƙa lamarinsa ga Allah. Have a nice day.*_ Ta karanta har da karkata kai kusan sau uku, sai ta ji ma abin kamar irin a fina-finan da ake haskowa a tashar Hausa da su Tasleem ke kunnawa. Ranta na wani irin huci da zafi, a gefe guda kuma duk da wannan radadin wai sai ta ji tana so ta san ma'anar kalmomin karshen da ya rubuta mai kama da farasanci da turanci. "Lafiya ki ka ba waya hankalinki?" Muryar Ummita ya katse mata tunani, ta isa wajenta ta miƙa mata waya. Har a sannan hausarta ba ta dawo daidai irin ta Kanawa ba. "Ɗan fassaramin ƙarashen saƙon nan, me yake nufi?" Ummita ta karanta tun daga farko, tun kuma somawarta take zabga murmushi don ba ƙaramin burgeta ya yi ba. "Fatan alheri ya yi maki a wannan rana. Kai Humaira wannan mutumin akwai iya tsara kalami, ina ji a jikina kin samu mijin aure." Guntun tsaki Humaira ta ja gami da warce wayarta tana ƴar harararta. "Ai ke ce mijin, ni raba ni da wannan shirmen soyayyar kin ji ko. Ba ni da lokacinsu." "Anya Humaira kalau kike kuwa? Ko dai sai an haɗa da addu'a?" Yamutse fuska ta yi kawai ta kwashi tafarnuwar ta dauraye ta watsa a turmi ta hau daka. Ganin haka itama Ummita ta share batun. A gefen Futuha kuwa, gaba daya ta yo kan Raihana. "Ke! Wane Ibb din ki ke nufi ne?" Raihana ta yi jim, ba ta son ta ce Ibb Malaminta allura ta tono garma don haka sai ta kife ta da fadin. "Ba fa wanda kike zato ba ne, wannan wani Ibb ne Ibrahim sunansa suka hadu da ita a hanyar islamiyya." Nannauyan ajiyar zuciya Futuha ta yi kafin ta juya ta koma gadonta tana jan tsaki. "Toh barkanta, amma da ace Ibb da nake mutuwar so da kauna ne wallahi sai na koyamata hankali. Ke kuma wani sabon salon gulma da munafunci tun da ta wanke maki fuska da mari kike wani shakkarta har da taya ta hira. Ke kika sani." Raihana dai ba ta tanka ba ta mime ta bar mata ɗakin. Amma ta sa a ranta babu wani abu da zai sa ta kara biye musu wurin nunawa baiwar Allah da ba ta ji ba kuma ba ta gani ba ƙiyayya kawai saboda don zuciya irin nasu. *** Gidansu cike taf da jama'a sakamakon daurin auren Fu'ad da aka yi a ranar, haka ya dinga kutsawa ransa duk a ɓace har ya shige bangarensu, kai tsaye dakinsa ya nufa, tun daga falo ya cire hularsa ya yi jifa da ita, hakanan babbar rigarsa blue itama ya ajiye saman kujera kafin ya zauna ya shiga kokarin cire covershoe din da ke a ƙafarsa da kuma safa. A duniya Fadeel ya tsani hayaniyar jama'a, wannan ta sa kansa har wani sarawa yake yi. Ya ja guntun tsaki gami da kwantar da kai jikin kujerar ya lumshe idanu. Zafi biyu ya haɗe mishi, ga na rashin samun haɗin kan yarinyar da yake jin ta a ƙoƙon rai, ga kuma wata irin yunwa da yake ji domin ko karin kumallo bai yi ba suka fice masallaci wurin daurin aure. Kowa kuma a dangin sai ya yo kansa da tsokana a wajen, su na fadin saura kai babban yaya. Wadanda ba su da labarin dawowarsa kuwa, sai a ranar suka gan shi. A hankali ya bude lumsassun idanunsa ya murza yatsunsa suka yi ƙara, har wani zogi suke yi mishi saboda gaisuwar da ya dinga yi da jama'a. Lokaci guda kuma ya miƙe ya nufi bandaki, hannun ya wanke tas da hand sanitizer sannan ya fito rike da karamin tawul yana gogewa. Ya yi daidai da shigowar Ibb tare da wani dan uwansu Imran. Sallamarsu ya amsa ya koma mazauninsa har da kwanciya wannan karon. Kafin Ibb ya yi magana ya riga shi. "Wai so ku ke na mutu? Yunwa fa nake ji." Harararsa ya yi. "Kai dai an yi ɗan iska, muna can Alhaji ya sa mu nemoka ku gaisa da abokansa ashe kai nan ka yo? To sai ka tashi ka shirya muje idan ya so kafin mu dawo na yiwa Anti Amarya magana a kawo mana abinci." Fadeel ya lumshe idanu. "Kasan Allah ba zan iya fita ko'ina ba, ni fa ji nake idan ma na kara sa ƙafa na fita cikin wannan ranar hanjin cikina za su fito waje." Imran ya kwashe da dariya, shi kuwa Ibb kamar ya shaƙo amininnasa haka yake ji. Yana niyyar magana kuma sai ga kiran Alhaji karo na uku. Ya ɗaga ya mishi bayani, dama bai tsammaci faɗan Alhajin ba, cewa ya yi babu komai maza ya yi waya a kawomusu abinci. Da wannan suka yi sallama shi kuma a nan take ya yi kiran Anti Amarya ya sanar da ita. A bangaren Anti Amarya wacce ta ci ado cikin arnen leshi ruwan toka da ya sha adon stones, ga ƙunshi ta yi sai baza ƙamshi take, jin wayar Ibb ya sa  da rawar jiki ta amsa ta ba ɗaya daga cikin hadiman gidan Larai umarnin haɗawa Fadeel da abokansa abinci za ta turo a kai musu. Ta shiga falonta inda yan uwanta hudu ke zaune su na shan hira. Uku a cikinsu matan aure ne, ɗaya yayarta sai sauran gaba daya ƙannenta. Ƙanwarta Murja dake kwance tana danna waya ta kai wa duka a ƙafa.  Ba shiri ta mike zaune. "Ke tashi maza ga dama ta samu, jeki wurin Larai na sa ta haɗa abincin su Fadeel ki kai musu, kika sani ko Allah zai sa a dace ko cikin abokansa wani ma ya ce yana so?" Jin haka babbar yayarta Saddika ta amshe. "Ke wallahi hakane kam, tashi Murja, Allah ya ɗora ki akan su." Murja ta haɗe girar sama da ƙasa. "Nikam wallahi Fadeel nake so. Shi dai za ku taya ni addu'a ya ce yana sona." "Kin ji wawiya, ke kanki kinsan kaf abokansa ma babu na yar wa musamman Ibb. Ai dai kinga irin jama'arsa da suka kawo masa ziyara muna nan dake a gidannan tun zuwansa ko?" Murja wacce ta zo hutun makaranta gidan ƴar uwarta ta, ta mike tana gyara zaman ɗaurin dankwalinta. "Nidai kam shi nake so, ai duk kyawunsu ba su kai shi ba. Malam ga aji na musamman. Kiga fa ko sadda su Sholy suka zo gidannan ko kallo basu ishe shi balle su ga haƙoransa. Nima din ba.." "Ki yi zaman hira har sai ya gaji ya turo wani ya karɓar musu abincin. Shashasha marar wayo kawai. Ana kai ki kina ƙin zuwa. Ke kika sani. Zauna har ki yi biyu babu." Jin haka da sauri ta fice daga falon tana dariyar maganar Zuwaira, mai bi wa Anti Amarya. A kwando ta ga Larai ta haɗa komai har da cokula da farantai, ta kinkima ta yi gaba inda ta tsallake yan uwan Alhaji da suka zo daga ƙauye ko kallo ba su ishe ta ba ballantana ta yi tunanin gaishe su. Su kam suna hau gulmarta da harshen fulatanci. A ƙasan ranta ta ja Allah ya isa. Tana zuwa ƙofar ta kwankwasa, Ibb ya ba da umarnin a shigo. Lokacin dukkansu har Imran sun cire babbar riga ana shan iskar fanka ana hira, sun zama su biyar a ɗakin sakamakon shigowar abokan Ibb biyu, Saifullahi da Idris. Da sallama a bakinta ta shiga, kasancewar Fadeel ne a saitin ƙofa ya bi ta da kallo ɗaya ya kauda kai ya maida saman kwandon dake hannunta. Dama abin da yake jira kenan, ita kuwa kusan zaucewa ta kusa yi sakamakon kwayar idanun Fadeel da suka haɗu da nata, gaba daya ta ji ta ƙara narkewa a tekun sonsa. A ranta tana ayyana ba gudu ba ja baya shi din dai ranta ke so. Babu wani abokinsa da ta ga ya burge ta, gwara ma Ibb don a baya tana mishi kallon hadadden saurayi duk sadda suka hadu ya zo gaida Alhaji, ita kuma ta zo gidan, yanzu kuwa ta fahimci Fadeel ya kere shi. "Ba sai kin zuba ba, bar shi za mu yi serving da juna." Fadin Ibb fuska a sake ganin ta sauke kwandon ta hau fito da kayayyakin tana shirin buɗe warmer. Ta kalle shi kadan tana dan murmushi. "Lah ba komai, bari na zubamaku, wannan ai aikinmu ne mata." Bai kara magana ba sai mayar da hankali ya yi ga Imran dake nuna mishi wani hoto a waya. Shi kansa Ibb ba mai yawan zance ba ne sai ta kama, don haka bai hanata ba. Shi kuwa gogan kallonta bai kara ba, sai Idris da ya zuba mata ido kamar ya haɗiye ta. Shi dai kam lokaci guda ya ji ta kwanta masa a ƙoƙon rai. Don haka bai yi ƙasa a gwuiwa ba ya dubi Fadeel. "Wannan ƙanwarmu ce?" Tsaf Fadeel ya karance shi, don haka ya gyada kai kawai fuska ɗaure. Ita kuwa da rawar jiki ta miƙa kwanon abinci ga Fadeel. Madadin ya karɓa sai ya dube ta. Ta ji kallon tun daga tsakar kanta har tafukan sawayenta. "No, ki fara ba su tukunna." "Kai Malam, idan za ka karɓa ka soma ci ka karɓa. Tun ɗazu ka ke mana raki da kukan yunwa kamar wanda ya shekara bai ci ba. Wannan ta ya ya kake azumtar watan Ramadan?" Jin haka ya ja filo ya jefawa Imran a fuska, gaba daya aka sa dariya shi kuwa ya shafi sumar kansa yana mai lumshe idanu lokaci daya ya bude su akan Murja, wannan karon sai da ta ji miyan bakinta ya sarƙe ta sai ga shi ta soma tari ba ƙakƙautawa. Idris da sauri ya miƙa mata ruwan roba dake gefensa saman kafet. Ta karba ta sha tana satar kallon Fadeel da bai ƙara dubanta ba sai waya da ya ke faman dannawa. A haka da rawar jiki ta zuba kowa ta miƙa mishi. Friedrice ne da hadin coslow sai chicken pepper. Ta bude firij ta ciro musu lemuka ta ajiye. Daga haka ta sa kai ta fita. Tana fita Idris ya gyara zama ya shiga rantse musu akan ya ga matar aure shi dai yana sonta idan za'a ba shi. Fadeel ba ya fahimtar komai ban da ta cikinsa da ya ke yi, ganin duk da fankar da ke busawa yana gumi kawai sai ya mike ya cire rigarsa daga shi sai dogon wandon shadda da vest ya koma ya zauna. Sai da ya tashi da abincin tas kafin ya ɗauki ruwa ya kora ya dubesu. Kowannensu bai kai ga kammala ci ba, suka kwashe masa da dariya, shi kansa murmushi da tsaki ya yi lokaci guda kuma yana sa hankicif ya goge fuska. "Ku na da matsala wallahi, ba za ku gane illar da yunwa ke min ba. Yanzu sai ta tayarmin da ulcer." "Ai mun gane komai ranka ya daɗe. Ko za ka ƙara?" Saifullah ya faɗi da zolaya. Fadeel ya ɗan harareshi. "Saboda na zama rumbu ko?" Haka suka yi ta zolayarsa shi kuwa tuni ya maida kai kan wayarsa yana kiran abu na biyu da ya tsaya mishi a ƙoƙon rai amma har ta kammala ringing ba a ɗaga ba. Haka ya kira har sau uku, sai a na huɗun, aka ɗaga. Kafin ya kai ga cewa komai ta soma faɗa. "Wai Malam kai din maye ne?! Na ce ka bar kirana ka ƙi! Dole ne zuwanka gidan namu? Haba, wannan jaraba da naci har ina wai? Mtsw." Daga haka kit, aka kashe kiran, nan da nan kansa ya yi wata irin sarawa, dama ga ciwon kan da tun ɗazun yake ji. Gumi ya karyo masa saboda tsananin ɓacin rai, idanunsa tuni suka kaɗa. Sauyawar yanayinsa ya sa Ibb ƙuramasa idanu. Sai dai bai ce komai ba ganin ba su kaɗai ne a falon ba. Sai bayan da gaba daya suka fice don gaisawa da Alhaji sannan Ibb ya dube shi, lokacin ya mayar da kai jikin kujera ya lumshe idanu don har su Imran suka fita sun yi zaton bacci ne ya kwashe shi su na mishi tsiya. Shi kuwa duk yana jin su ba shi dai da karfin biyewa shirmensu. "Fadeel, wai meke faruwa haka?" Jin muryar Ibb yasa shi bude idanun, ya mike zaune sosai. "Yarinyarnan nema take ta kashe ni, daga ranar da na gan ta har zuwa yau ban huta ba." Cikin rashin fahimta Ibb ya dan wurga hannu. "Wace yarinya ce haka? A rayuwarka har ta hanaka sakat? Wace ce?" Tsakaninsa da Allah ya yi furucin don shi gaba ɗaya ma ya manta da wata Humaira. "Wacce muka haɗu da su tare da wannan ɗan iskan yaron." Shiru Ibb ya yi cikin nazari sannan ya dube shi a hanzarce. "Are you serious? Kana nufin ka kira ta?" Cikin ido Fadeel ya dube shi. "Yes, mun yi waya, amma duka ba masu dadi ba ne." Ya kora mishi bayanin duk abin da ya faru, Ibb ransa ya ɓaci. "Unbelievable! Yanzu akan mace ne ka shiga wannan yanayin? Fadeel kai ne dagaske dai wanda na sani? Mutumin da gaisuwar kirki abu ne mai wuya a ganka kana yi da wacce ba muharramarka ba, kai ne yau da bakinka ka ke faɗin cin kashin da wata shashasha can take maka? Kuma har ka ke tolerating in the name of love? Is this love or madness?" A fusace Fadeel ya soma magana, tun da Ibb ya jefi Humaira da kalmar shashasha ya ji ransa ya yi masifar zafi. "Oho! Idan ma haukan ne naji ni na jefa kaina ai ba da sa hannunka ba ko? Ban damu da duk wani tunani da za ka yi ba. Ina sonta, ka zo gabana kana kiranta da shashasha ba zan iya jura ba Ibb! Ina haɗa ka da Allah, idan har ba goyamin baya za ka yi ba toh kada ka kara kuskuren zaginta a gabana. Kawai dai ina ji a jikina wataran za ta gane ni din masoyinta ne na gaskiya." Yana kaiwa nan ya mike ya nufi hanyar ɗaki, Ibb kuwa baki a wangale yake binsa da kallo har ya ɓace masa. Meke damun Fadeel? Ya jefawa zuciyarsa tambaya, a take kuwa amsar ta zo masa, Soyayya ce. A fili ya ce. "Idan kuwa har wannan ita ake kira da soyayya, ina nemawa kaina tsari da ita. Kai kuma Fadeel ina roƙon Allah ya yayemaka wannan haukan son." Daga haka ya mike ya fita a dakin domin shi har ga Allah ba ya fatan wannan rashin hankalin da mace za ta zage shi ya kasa daukar mataki a kanta. Ko ƴar uban wace ce ba zai ƙara yi mata kallon wata abar so ba, ballantana har ta ci galabar yi mishi son ranta. *** Humaira na  kwance a yammacin ranar juma'a ta ji ihun ƴan matan gidan ya karaɗe falo, ta mike zaune tana mutsistsiƙa idanu. Hayaniyar ta mene ne? Kafin bacci ya gama wartsake mata sai ga Ummita ta shiga fuska ba yabo ba fallasa. "Wai hayaniyar me ake yi?" Fadin Humaira. Tsaki Ummita ta ja haɗi da taɓe baki. "Aunty Jannat ce ta zo, kanwar Mami." Humaira ta zaro ido, ba ta taba zama da ita ba amma ta sha jin labarinta a bakin Ummita na irin uƙubar da ta sha a wajenta sadda tana rayuwa a gidan. "Dagaske? Ki ce mun shiga uku." Ganin ruɗewae Humairar har ya so ya fi nata ne yasa ta dariyar dole wanda ba ta shirya masa ba. "Ke da ba ki taɓa zama wuri guda da ita ba? Ba lallai ki fuskanci matsalar da na fuskanta ba ai." Ita dai Humaira ta ji ne kawai ba don ya zauna a kwakwalwarta ba.[7/24, 9:39 PM] Maman Imaan Nvl Lvrs: *LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* Suna nan zaune Humaira na cewa  ita kam za ta so ganin ya wannan Jannat din take mai shegen son mulki sai ga Muhsin da Waleed sun faɗo ɗakin a  guje. Kira ne daga Mami akan su fito a gaisa da Jannat. Ummita ta dafe kirji, yayinda Humaira mikewa ta dube ta. "Wai ya haka, kinsan fa yarannan akwai daukar zance yanzun sai su fasalta musu yanayinki." Ummita sai ta maze ta mike. Suka kama hanyar falon, tun kafin ma su kai ga ƙarasa shiga ta hange ta. Kamanninta sak da Mahaifiyarsu wato Anna. Kusan har ta so ta fi Mamin hasken fata, siririya ce ba ta da tsawo duk kuwa da cewar tana daga zaune ne. Yaranta ƴan biyu tamkar an tsaga kara an karya, ba su wuce sa'o'in Muhsin ba. Wato shekaru goma a duniya. Riga da wando ne a jikinta sai abaya dake ajiye a hannun kujera wanda ga dukkan alamu cire ta ta yi. Gashinta ya sha kananun kalba an tufke a tsakiyar kan ya yi kamar ta sa ribos din acuci. Gaba daya iyalan Mami na falon ciki kuwa har da Anna wacce ba kasafai ta fiye fitowa ba. Humaira ita kanta sai da ta sha jinin jikinta ganin Anna a falon, sai da itama ta ji kamar ta ja hannun Ummitan su juya. Aikuwa su na ganinsu Anna ta tamke fuska gami da juya harshe zuwa buzanci. Ko me ta fadi oho, gaba daya suka kalli su Humaira, matasan suka gimtse dariyarsu sakamakon Mubarak dake zaune, sun tabbata muddin suka ce fiddo shi waje to fa kashinsu ya bushe wurinsa.  Hatta da Raihana ba ta ji dadin zancen Anna ba domin har ga Allah yanzu ba ta da matsala da su, ta riƙe su ƴan uwan na gaske kuwa. Ita kuwa Jannat kallon Humaira ta ke yi kamar wacce ta ga kashi. A yatsine ta amsa gaisuwarta, Ummita kuwa gaisuwar ma ba ta samu ba sai harara da ta watsa mata ta ja tsaki. "Wai Anti Jannat har yanzu wato kina nan yadda na sanki." Mubarak ya fadi ransa duk ba dadi, tun daga kalmar agolar da Anna ta kira Humaira da shi har zuwa yanda Jannat ta karɓi gaisuwarsu.  Rai a ɓace ta amsa. "Toh ko za ka sa hannu ka buge ni ne? Dama ai kai na faɗa can dai dangin uba ka biyo ba mu ba." Zai yi magana da sauri Mami ta ɗaga mishi hannu, aikuwa abin da take gudu shi ya afku domin Anna faɗa ta hau yi kamar ta ari baki wai laifin na uwarsa ce da ta fifita bare a kan nata. Ganin dai abu ya ƙi ƙarewa Humaira ta miƙe tana mai jan hannun Ummita, itama ba shiri ta miƙe sun kama hanya tana ji Jannat ta kwalawa Ummita kira tana ba ta umarnin ta ja Hassan da Hussein ɗakin su Muhsin ta musu wanka. Ita dai Humaira a fusace ma ta karasa ɗakin don ta matsu ta daina jin muryar tsohuwarnan da ma Jannat din wacce ta ji tsanarta lokaci guda ya rufe ta. Me ake da wanda bai san daraja ta DAN ADAM ba? Ita kadai a dakin ta yi ta mita tana tsaki. Ji take kamar ta je ta shaƙe wuyansu baki ɗaya. Sai kuma ta yi kwafa tana cije lebbanta, ita kadai ta san damuwar da take dannewa a ranta, amma a kwanakin nan abin yana neman fin karfin zuciyarta. Damuwar bai wuce Abba ba, mutumin da ya kasance bango majinginarta a gidan, wanda shi take yiwa kallon uwa kuma da uba. Wannan kauna da soyayyar da ya nuna mata a farkon zuwanta gidan yanzu ta rasa laifin da ta yi mishi ya sauya. Hira ma ya ƙi ba da fuskar ta ja shi da shi, idan har ita ɗaya ce a falonsa, nan da nan zai hau wasu ƴan aikace-aikacensa kamar gyara takardu ko kuma kiran abokan cinikayya, shaida dai ta cewar ba ya son ta ja wani dogon zancen. Ba dai za ta ce ba ya mata fara'a ba ne, sam a'a, sai dai babu ja a jiki balle har su shaƙu tamkar yanda ya nuna a farkon zuwanta. Toh wanda ma ka ke taƙama da shi bai wani damu da sha'aninka sosai ba ina kuma ga wasu can da har gobe sun ƙi karɓarta matsayin ƴar uwa ta jini? Kewa, kewar Dada da Kawunta duka suka mamaye ta, ba ta san cewar ta soma zubar da hawaye ba sai bayan ta sa hannu saman fuskar ta ji danshin lema. A hankali ta share su, ya kuma yi daidai da shigowar Raihana ɗakin. Ganin hawaye a fuskarta gaba daya sai ta ji ba dadi, ko ita ce ake yaren da ba ta ji tsarguwa yake sanya ta ballantana kuma wannan da dama din sun san ba da kowa ake ba sai su. "Humaira kuka? Don Allah ki yi hakuri." Ta fadi a sanyaye gami da zama a gefenta. Jin haka ta yi murmushin da ya fi kuka ciwo lokaci guda tana gwale idanun da hannu tana share su. "Ke ba fa komai, ba kuka nake ba. To me aka yi da zan yi kukan?" Raihana itama murmusawar ta yi ba don ta yarda ba, ta sani Humaira akwai juriya da nuna jarumta, sai dai kuma itama ai ƴar adam ce, tana da zuciya ta kuma san meke ma ta zafi. Kafaɗarta ta dafa. "Na sani su Anna ba su ..." "Raihana mu bar zancen, ya wuce wallahi. Ai komai mai ƙarewa ne. Lokaci ne." Cewar Humaira da sauri tana katse Raihana don a duniya yanzun idan da abin da ta tsana bai wuce a ambaci sunan Anna ba. Ta tsani mutum da ba ya ganin kowa da gashi. Tsohuwar sam ba ta riƙe girmanta. "Kinga kuwa mutuminki koda wasa bai ƙara gangancin kirana ba?" Maganar Raihana ya katse tunaninta. Cikin rashin fahimta ta ce. "Wa fa?" Ta yi tambayar don har ga Allah ta mance, sai kuma bayan ta yi ta tuno da Musaddam din. Ta ɗan ɗaga gira. "Au, ɗan iska za ki cemin." Suka ɗan yi dariya. A haka su Tasleem suka shigo ɗakin suka iske su.  Zuwa yanzu Raihana ba ƙaramin haushi take ba su ba don haka daga kallo daya ba su kara bi ta kansu ba. Tasleem ta nufi sif din kayanta ta buɗe  ta sa hannu a ƙugu tana kallo. "Oh God! Ni wane kaya ma zan saka? Wallahi gaba daya na diririce." Futuha da ta faɗa saman gadonta ta yi dariya. "Atoh, sai ki ƙure a daka ko ba komai dai wannan ne first meeting ɗinku." Raihana na jin haka ta mike da sauri ta karasa ga Futuha. "Wai Hamza D ne zai zo?" Harararta suka yi a tare, Tasleem ta ja tsaki. "Ina ruwanki? Ai ke yanzu munafuka kika zama. Ba a sirri da ke." Humaira ta yi tsam ta mike ta fice a dakin ba ta ko kalle su ba. Cin fuska ne ta san za a yi mata. *** Rayuwar ta ci gaba da gudana, Humaira tun tana ganin ire-iren bautar da Jannat ke sanya su na ƙare ne abin dai ya ci tura. Daidai da wankin pant da rigar mama su take ba, Mami ke tsawatarwa a wasu lokutan shiyasa kawai su ke hakuri. Idan kuwa ta kai Humaira abin ya ishe ta rantsuwa take yi da ƙari cewar ita ba za ta wanke ba, sai Ummita ke tausarta ta karɓa ta wanke gudun samun matsala. A wannan gaɓar kuma ba irin takurawar da Fadeel ba ya yiwa Humaira, iyakar ƙularwa ya yi mata, ta yi bakaken maganganun amma ko gezau, kusan kullum sai ya aiko mata da saƙonninsa da ke yiwa Raihana dadi. Ita ke karɓa ta yi ta karantawa har a wasu lokutan ta yi yunkurin ba shi amsa, Humaira ta nuna ba ta so. Jannat ba ta bar gidan ba sai da ta yi wata ɗaya cif. A sannan tuni Mubarak ya tattara ya koma, shima daf yake da kammala Masters. Yayinda  Yassar da Dawud suka soma jarrabawar ƙarshe na kammala degree dinsu a jami'a. Su Ummita ma tuni an koma karatu, Humaira kam ta yi nisa a fannin girke-girke don yanzu girki ɗaiɗaiku ne ba ta iya ba, kama daga cimar fulawa har dai sarrafa shinkafa da sauran kayayyakin abinci. Girkin gidan zuwa lokacin ya koma kan ta rankatakaf don kowa burinsa ta girka ya ci. Ita kam ko a jikinta, za ta yi girkin ba son jiki amma fa ba ta yarda da wulakancin su Yassar da Tasleem masu cewa su na son cin wani abu daban.  Yassar su na dab da kammala jarrabawarsu ne suka tada hankalin Mami lallai sai ta tambayar musu Abba kuɗin da za su haɗa party da abokan karatunsu sai dai duk inda  suka ɓullo Mamin ta ƙi asalima cewa ta yi su tuntuɓi Abban da kansu. Yassar ya mike tsaye yana huci. "Shikenan, idan Abban ya zo zamu yi mishi maganar. Mu dai gaskiya wannan karon ya sakar mana mu fita kunyar abokai. Wannan rayuwa har ina." "Ni ban san irin Abba ba wallahi, Mami ke ma ba kya mishi magana, tun farko ai Anna ta fadi, ke kika ba da damar ba ya hidimta mana sosai. Nifa Allah kuwa har kunyar nace Babana mai kudi ne nake, saboda ba a gani a jikina." Dawud ya fadi yana daga tsaye dafe da kujera. Mami ta yi mishi daƙuwa. "Karɓi nan Dawud, shi uban naku sa'anku ne da ku ka tsaya ku na wannan ɓarin zancen a kansa? Kuna maganar kamar yau idan kun je gabanshi za ku iya maimaitawa? Kunsan Allah ku kiyaye ni, gaba daya zan tattaraku na kai kararku wajensa tun da dai shi kuna shakkarsa." Suka ƙara tunzura, Humaira na gefe tana gogewa Mami mayafi bayan ta kammala goge nata kayan dalilin wutar nepa da aka kawo, biki ne Mamin za su je har da ita na ɗiyar mijin Anti Laila malamar girkinta. Katin gayyatar har ita aka ba da ta kuma tabbata saboda mutuncin da suke yi da Shema'un ne, sannan Anti Lailar ma ba ta da matsala ko kaɗan.  Gaba ɗaya hirarsu babu wanda ba ya shiga kunnuwanta, tana mamakin irin wannan rashin tarbiyya na su Yassar da ba sa tauna zance kafin su furzar kan kowa ma. Haka suka yi ta mita a karshe dai kiran sallar la'asar ya sanya su tattarawa su bar falon. "Allah ya shiryamin ku." Humaira jin furucin da Mami tayi kafin ta wuce dakinta yasa ta amsa da amin, zuciyarta sai ta cika da tausayin Mamin. Matar dai na iyakar kokarinta a kansu. Ba zato ta ji an watso mata kaya saman kafafunta da ke miƙe a harɗe. Ta ɗaga kai ta dubi mai wannan aiki. Futuha ce tsaye daga ita sai vest da leggings. Gashinta a barbaje a gadon bayanta take duban Humairar fuska a yamutse. "Ɗan dannemin kayan nan kafin su dauke wuta." Kallonta ba ta kara yi ba ta hadiye zafin da ta ji na wannan kalar rashin mutuncin na Futuha. Itama daga haka ta juya zuwa daki, ƙwafa ta yi ta kuma rantse ba za ta yi ba. Hakan yasa tana kammala na Mamin, ta hada da nata kayan da ta goge ta miƙe bayan ta ɗauke dutsen gugar a wajen gudun kar su Waleed su taɓa.    Dakin Mamin ta soma shiga, sallah ta iske ta tana yi don haka ta ajiye mata a saman gadon kusa da wani haɗaɗɗen leshinta peach colour da ya sha adon duwatsu, ya hau sosai da mayafin. Humaira har sai da ta murmusa don tuni ta hango Mamin a ciki, karshen kyau ko ba a faɗa ba ta sani kalar da kuma kayan za su karɓe ta. Abar ka da farar mace. Koda ta shiga ɗakinsu Tasleem na tsaye tana fente fuskarta da hoda. Ita kuwa Raihana tuni ta shirya tsaf cikin wata maroon atamfa mai haske an yi adon yellow colour jikinta sai dai bai yi dau ba. Tana tsaye ta karkace sai hotuna ta ke yi a gaban window. Futuha da alama tana bandaki. Suka dubi juna da Raihana, da wani irin zumudi ta karkace hadi da ɗan ɗaga gira. "Ya? Na yi kyau?" Humaira ta yi mata murmushinnan nata mai fiddo da zahirin kyawunta. "Kin fito tsab. Masha Allah." Raihana ta yi dariya, ita kuwa Tasleem dogon tsaki ta ja. Ba wanda ya ce mata ci kanki a cikinsu. Kasancewar ta yi wanka kafin zaman guga kuma ba ta da sallah hakan yasa ta kawai ta shiga sauya kaya. Itama atamfar ce amma nata dark brown ce mai haɗe da milk colour. Tana cikin shafa hoda Futuha ta fito daga wanka tana baza ƙamshin sabon showergel da suka ci arzikinsa a zuwan Antinsu Jannat gidan. Kallon Humaira ta yi kafin ta kalli gadonta ta gani wai ko ta ajiye mata kayan amma wayam. Don haka a fusace ta dube ta. "Ina kayan da na ba ki guga?" Humaira ta kalle ta da irin kallon wulakancin da suka saba yi mata itama. "Ai gugan Mami kika iske ina yi ko?" "Shekara kika yi kina gogewa Mamin mayafi? Don tsabar is..." Ba ta kai ga ƙarashewa ba ɗif aka ɗauke wutar, aikuwa Raihana ta tuntsire da dariya itama Humaira sai da murmusa a ranta tana fadin Allah ya ƙara. Nan fa Futuha ta hau zuba fada wai Humaira na sane iskanci ne ta fara sabo, tunda har ba a isa a sanya ta aiki ta yi ba. Ta tattara ta ba banza ajiyarta duk da cewa ranta wani irin tafarfasa ya ke yi na irin zagin da Futuha ke yi mata. Korar yunwa dai ya ƙi fita a bakinsu, ta kasa jurewa ta juyo, kamar ta maida martani da cewa su dinma asalin uwar Maminsu Nijar din ne, daga can suka fito can kauyen Agadas sai dai ta haɗiye tuna albarkacin Mami. Ummita ta shigo dakin, ita tuni dama ta shirya cikin atamfarta mai kyau ruwan sararin samaniya. Fitar da ta yi aiken Mamin ne zuwa siyan kati. "Mami ta ce ku yi sauri." Wannan ne ya katse zancen, kayan da Futuha ba ta sanya ba kenan sai kuwa wani ta sauya. Ba wata kwalliyar hayaniya Humairar ta yi ba amma iyakar kyau ta fito tsaf. Ba su suka yi haramar tafiya ba sai biyar da kusan rabi. Koda suka fito baki daya, Ladidi kawai aka bari tana musu a dawo lafiya sai kuwa su Muhsin dake can ɓangaren Anna, Ummita ta dube ta da murmushi. "Kin yi kyau sosai." Ta riƙe haɓa. "Idan babu wadannan buzayen a kusa ko?" Suka yi dariya. Anan farfajiyar gidan suka sha hotuna a wayar Raihana dake faman jan su, su Tasleem na gefe su na kallonsu ita da Futuha, ko me suke tattaunawa? Mami na fitowa suka shiga mota, kai tsaye ƙawataccen hall ɗin Marhaba suka nufa inda anan ne taron bikin. "Ba ku mance katinanku ba dai ko? Ba na so a je wurin taro mutum ya yi tsaye kamar wanda ya zo gayyar soɗi." Tasleem ta haɗiye dariyar muguntar da ya so kwace mata har sai da Futuha ta ɗan zungureta akan ta nutsu. Katin Humaira tun fitarta kiran Mami, ta ɗauke shi ta raba gida biyu ta wurga shi bayan gadonta. Ummita da Raihana suka amsawa Mamin bayan sun duba sun ga katinansu, ita kuwa Humaira ko jakar ba ta buɗe ba tunda dai ta riga ta sani duk wani abun buƙatarta ta jefa a ciki. "Humaira, Tasleem da Futuha fa?" Suka amsa da eh su ma yana nan. Su na isa bakin ƙofar kowaccensu ta fito, motoci ne na alfarma fake a wurin. Yanmata har ma da manyan mata ƴan gayu kawai kake gani a wurin, kasancewar Angon Shema'u ɗa ne ga kwamishinan ƴan sanda hakan yasa motar ƴan sandan har biyu a wurin su na lura da shige da fice. Mami ce ta soma gaba suna gaisawa da wata ƴar uwar aminiyarta ta miƙa kati ta shige. Hakan ba karamin dadi ya yiwa Tasleem da Futuha ba sanin muguntar da suka shiryawa Humaira. Suka shige abinsu zuciyarsu fari kal bayan sun miƙa katinansu, Raihana ma tuni ta yi gaba. Ummita kuwa ganin yanda Humaira ta rikice da bincike jaka ya sa ta tsayawa gami da ja baya ta ba wasu hanya. "Lafiya? Ya kika tsaya?" Humaira ta ja guntun tsaki. "Wallahi ban ga katina ba. Kinga ba ya cikin jakar." Ta dafe kirji. "Ba dai a gida kika bar shi ba?" Ta girgiza kai cike da takaici, ta kasa cewa uffan ma. Ganin su na tsaye kawai ya sanya ta duban Ummita. "Shiga ciki kawai, ni sai na koma gida." Girgiza kai Ummita ta yi. "Aa wallahi, sai dai ni na /24, 9:39 PM] Maman Imaan Nvl Lvrs: Dukan Ruwa 11*LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* 09034973645 Fitowarsu kenan daga Bristol Palace dake kam titin farmcenter, Ibb ke jan motar yayinda shi kuwa ya kwantar da kai jikin kujera idanunsa lumshe. Babu abin da ya kai su face gaishe da abokin baban Ibb da ya zo daga Kaduna zai tashi zuwa Egypt sakamakon rashin lafiya. "Hall dinnan ba ya rabo da biki." Jin haka ya sa a hankali Fadeel ya buɗe idanunsa. Cikin iko da hukuncin Ubangiji, dubannasa ya sauka kan Humaira dake tsaye ta harɗe hannuwa a kirji fuskar nan a ɗaure kamar koyaushe. "Wait please." Yanda ya yi maganar da sauri ya sa Ibb shima soma tafiya a hankali gami da neman wurin parking. Sai da ya daidaita motar a gefe kafin ya dube shi da alamar tambaya. "Lafiya?" Fadeel ya soma kokarin cire seat belt. "Ita ce. Ba na so na ƙara rasa damar da za ta kubcemin." Ganin yana kokarin bude ƙofar yasa Ibb saurin dafe hannunsa. Fadeel ya dube shi. "What? Kana nufin kar na je?" Girgiza kai Ibb ya yi. "No, ba haka nake nufi ba. Sai dai ina so ka ba ni damar muje tare, idan kuma da hali kar ka ce komai. Ma'ana kada ka yi mata zancen soyayya da ma sauransu. Ni zan san ta yadda zan ɓullo mata, ok?" Fadeel ya sauke ajiyar zuciya yana hangenta ta jikin side mirrow. Ba tare da ya dauke idanunsa ba ya amsa. "Ok." Daga haka Ibb ya kashe motar, suka fito kusan lokaci guda. Gaba ɗayansu ƙananun kaya ne jikinsu. Fadeel baƙar tshirt ne a jikinsa mai ƙaramin hannu sai blue jeans.  A tsintsiyar hannunsa kuwa, agogo ne ɗaure na fata baƙi, sumar kansa baƙa wuluk sai sheƙi take yi. Ya fiddo gilashinsa baƙi a aljihu ya rufe ƙwayoyin idanunsa, a yanda ya karanci Humaira a farkon haɗuwarsu hatta da kallo ta tsana. Ba ya jin kuma abu ne da zai iya jure bari ne, wato kallonta, musamman ma da ya kasance sun fi watanni biyu ba su sake haɗuwa ba. A ɓangaren Ibb kuwa, blue tshirt ya sa da baƙin wandon jeans. Kallo ɗaya idan ka yi musu sai ka kara. Fadeel fari ne tas kuma dogo, har ya so ya fi Ibb tsawo. Shi kuwa yana da ɗan duhun fuska balle idan ya jera da Fadeel, kai tsaye za a kirashi baƙi. Tana nan tsaye ba ta motsa ba har suka ƙarasa wajenta. Wani irin bugu kirjin Fadeel ke yi, kallonta yake tun daga sama har ƙasa, ba ya jin ta haura shekaru sha takwas, idan ma ta cika hakan kenan, amma ƙirarta ko a yanzun abin a kalla ne ina kuma ga nan gaba? Ya ja numfashi daidai sadda suka ci burki a gabanta. Sallama Ibb ya yi gareta, ta bar duban wayar da take yi a kokarinta na kiran Mami ta ce mata ita kam gida za ta koma. Zaratan samarin suka sanya wani irin kwarjini ya mamayeta da har ta kasa tantance su ɗin ko su wane ne, ta mance ma a inda ta san su. Daƙyar ta amsa sakamakon nauyi da harshenta ya yi, daga haka kuma ta  dauke kai ta raba jikinta da motar da nufin barin wajen.     "Kamar ba ki gane ni ba ko?" Cike da ƙosawar ta tafi ta dube shi. Kallo na ƙurilla don ta fahimci ko dagaske yake ta san shi ɗin, duk da cewa ba wannan ne karon farko da samari suke mata irin rainin hankalin nan ba idan sun ga ba ta kula su ba, amma hakanan a ranta ta ji wannan dai ya yi kama da kamilallan mutum, ba ta jin zai yi mata ƙarya. Bayan gama kallonsa ta maida kwayar idanunta kan Fadeel, ba ta ci nasarar ganin halittar kwayoyin idanunsa ba, shi kuwa wani yarr ya ji tun daga tafin ƙafarsa har tsakar kansa. Dakyar ya iya jarumtar juya fuskarsa gefe kafin ita ɗin ta kai ga ɗauke nata kwayar idanun a kansa. Ta tsuke baki ta ce. "Ban gane ku ba." Ibb ya yi mata bayani a taƙaice, nan da nan kuma ta ɗan sakar mishi fuska. Ko babu komai ta ji dadin mutunta da ya yi a wancan ranar wanda tun daga shi, Musaddam bai ƙara gigin shiga hurumin Raihana ba. Ba ta da masaniyar ko Fadeel mai yawan kiranta shi ne tsaye a nan ko kuwa dai wani abokin na Ibb ne daban kusa da ita hakan yasa ta gaishe su a jam'u. Suka amsa, Fadeel kam lebbansa ne suka motsa amma tuni ya yi nisa a kallonta, bai san lokacin da ya ƙara mayar da hankalinsa kacokam kan kyakkyawar fuskarta ba. 'Wallahi ina sonta.' Ya yi furucin a can ƙasan ransa kafin ya sa haƙori ya cije lebbansa ya sauke numfashi nannauya. A cikin ɗakin taron kuwa, Tasleem da Futuha suka hana Ummita zuwa ga Mami, karshe suka ce ta zauna su za su je su shigo da Humairar wurin taron. Suka fito suka kara amsar katinsu suna dariyar mugunta, kawai burinsu su ga fuskar Humaira a karshe su ce Mami ta ce ta wuce gida ba za ta sanya ta roƙon kati a nan ba. Haka suka fito su na ta rarraba idanu, Futuha idanunta ya kai kan Ibb dake tsaye yana zuba wannan murmushin nasa mai tsada, a gefensa kuwa wani haɗaɗɗen matashi ne da ya zarce shi a haɗuwar. Ta dan murza idanu tana kara dubawa, tabbas Ibb ne. "Ke, zo ki raka ni. Wayyo zuciyata, me Ibb ke yi a wajen bikin nan? Ko abokin Ango ne?" Tasleem ta juyo, tuni Futuha ta soma tafiya ganin haka kawai ta mara mata biya. Shi kuwa Ibb babu abin da ya sanya shi murmushi illa gani da ya yi Humaira ta ɗan saki jiki da shi tana sanar mishi cewa ai kam daga ranar Musaddam bai ƙara shiga rayuwar ƴar uwarta ba. "Alhamdulillah. Hakan na da kyau. Sai ki ci gaba da yi mata nasiha. Allah ya ƙara nesanta ta da ire-irensu." Murmushi Humaira ta yi lokacin da ta ke amsawa da amin. Kallon Fadeel ba ta ƙara ba balle ta fahimci hankalinsa kacokam a kanta yake. Har za ta tafi sai kuma ta kara duban Ibb. "Yauwa, nikam ranar da abin ya faru, akwai wanda ka ba lambata?" Fadeel ya yi saurin dubansa, girgiza masa kai ya yi don haka ya dube ta kamar bai fahimce ta ba. "No, meyasa zan ba wa wani lambarki alhalin ko ni ban taɓa kira ba?" Ta ɗan yi shiru, haka kawai ta ji abin kamar rainin hankali amma ta rasa tsakaninsa da wancan Fadeel din me kiranta a waya wane ya raina mata? Don haka ta ce. "Ba ka da aboki mai suna Fadeel?" Fadeel dake tsaye ya ji tamkar ta ci gaba da ambaton sunansa sanadiyyar hakan ba ƙaramin daɗi ya yi mishi ba. Ibb ya ɗan yi gyaran murya domin ankarar da Fadeel ganin yanda ya harɗe hannuwa a ƙirji yana faman zabga murmushi. Sai kuma ya ce. "Yau na fara jin sunan gaskiya, wani abun ya faru ne?" Ta girgiza kai. "Aa ba komai." "Humaira." Gaba daya suka juya ga inda kiran ya fito, Tasleem ce. Futuha kuwa idanunta sun cicciko da kwalla, ji take kirjinta na wani zafi. Mutumin da take kwana da tashi da tunani, shi dai wanda ya gagari kowace budurwa da ma zawarawa a jami'arsu, shi ne tsaye a gaban Humaira kucakar da ba ta kamo sawunta a kyau da hasken fata ba yana mata murmushinsa mai tsada da take ji a ranta za ta iya kashe ko nawa ne ganin ita ta sami wannan damar. Amma a banza gashinan ya na jifan Humaira da shi. Tasleem kuwa ta yi mutuwar tsaye wajen kallon Fadeel, sai yanzu take jin ba son Hamza D take yi ba, son ƙarya ne. Wannan abin da take ji game da Fadeel a yanzun shi ne so, soyayya kuwa ta haƙiƙa. Fadeel ya nanata sunan da ya ji Futuha ta ambata. Humaira, shakka babu ta dace da masu sunan. Ibb kuwa ganin Futuha ya sanya shi tamke fuska kamar ba shi ke yiwa Humaira murmushin ba. Sai gaba daya matasan suka yi musu kwarjini, ita Futuha da ta yi niyyar wulaƙanta Humairar a gabansu sai ta yi laushi, yayinda Tasleem dama tuni miyan bakinta ya kafe, tunani take irin wadannan tsadaddun ai sai irin su masu zubin larabawa. Dakyar Futuha ta yi magana. "Mami ta ce ki wuce ki tafi gida tun da dai kin manta katinki." Jin haka sai ta ji babu dadi kadan, ta kwallafa ranta a bikinnan ba don komai ba sai na son ta ga yanda tsarin biki yake a nan. Hatta da fuskarta ta nuna rashin jin dadinta. Tasleem kuwa da sauri ta gaida Ibb da Fadeel har da ɗan ladabin ƙarya. Suka amsa. "Sorry to ask, ba ta samu shiga wurin event din ba ne?" Fadeel ya tambaya a sanyaye, tun zuwansu wurin sai a sannan ya yi magana. Humaira ta dube shi, kamar muryar mutuminta na waya, ya kauda kai ya kara shan mur kar ta samu fuskar tambaya. Tasleem da ta kusa shiɗewa jin ya yi mata magana duk kuwa da cewa akan Humaira ne ya sa ta saurin tankawa da wata murya cike da yanga. "Eh ta bar katin nata a gida ne, so shi ne Maminmu kawai ta ce ta koma tunda ba za ta samu shiga ba." Humaira ta tsaya kallon ikon Allah kawai, mamaki da haushin irin wannan karairayar murya na Tasleem ya cika ta. Har sai da ta ja guntun tsakin da sautinsa bai fito sosai ba. "Muje." Yana  fadin haka ya yi gaba, Ibb ya kalli Humaira. "Ku je za ki shiga yanzu in sha Allah." Ta amsa da toh, ta bi bayansa ita da Tasleem, ita kuwa Futuha ta ja burki gefen Ibb. Ya kauda kai tamkar bai san da ruwanta ba. "Amm, Malam ba ka gane ni ba ko? Ni ɗalibarka ce a.." "Ban sanki ba." Ya tari hanzarinta da sauri, daga nan ya taka ya nufi wurin motarsa ya tsaya. Futuha ido ya raina fata, ta dubi wasu maza a gefe tsaye da wasu ƴanmata da ma matan auren da ba su kai ga shiga ciki ba suna mata dariya, tana kallonsu suka ɗauke kai. Gwuiwa a sake ta kama hanya ta bi bayan su Tasleem, ranta ya yi tsananin ɓaci.  Ita kam ta soma gajiya da wulakancin Ibb, amma za ta yi hakuri tunda Anti Jannat ta haɗa ta da wata ƙawarta dake garin za ta yi mata rakiya gurin wani Malami a yi musu aiki a kansa. Amma zuciyarta na kokwanton aikin don ta ji wadanda sun buga sun kasa a kanshi. Humaira kuwa na tsaye gefe Tasleem na tambayarta inda ta san su Ibb ta yi banza da ita kamar ba ta ji ba. Hankalinta na ga Fadeel dake magana da ɗaya cikin masu tsaron wurin. Ba ta san ya aka yi ba sai juyowa ya yi wannan karon gilashin da ya rufe ƙwayar idanunsa ya cire, lumsassun kyawawan idanun suka bayyana, suka kusan susuta Tasleem har ba ta san ta ce "Masha Allah." a fili ba sai da Humaira ta ɗan dube ta. Shi kuwa cikin ido ya kalli Humaira ya mata alama da ta zo. Sai da ta karasa dab da  shi kafin ya samu damar magana. "A sha biki lafiya. A gaida Mami." Ta ji dadi sosai ganin da ta yi an ba ta damar shiga. Ta kuwa buɗe masa haƙoranta har wushiryarta na bayyana a fili. "Nagode sosai." Ga Fadeel shima murmushin ya bita da shi, ji yake kamar ya jawo ta jikinsa ya rungume. Da ace shari'a ta halarta masa ita ma, sai ya sumbaci kuncinta wadanda har gani ya yi kamar su na sheƙi idan ta murmusa. Bai taɓa ganin murmushinta ba sai a yau, sai ya ji inama za su dauwama ta na jifansa da shi. "Always welcome." Ita dai ta yi gaba don bai san ba ta jin turanci bane, ta dai tsinci welcome din. Zuwan Mubarak ta ji yanda su Tasleem ke faman welcome welcome har ta nemi fassararsa a wajen Ummita. Babu wani iyaka kuwa aka bari ta shige, tana ɓacewa ganinsa ya maida gilashinsa. Ganin Tasleem tsaye tana kallonsa ya dauke kai, har zai wuce sai kuma dabara ta faɗo masa. Ya dubeta. "Gidanku ɗaya?" Ta yi wani farr da idanunta. "Eh, babanmu ɗaya da ita." Ya ɗan jinjina kai. "Idan ba damuwa, ko zan iya samun full address na gidan naku?" Ba musu jiki na rawa ta hau yi mishi kwatance, ta kara da fadin. "Ko na ba ka phone number dina kaga ko da ace ba ka gane ba sai na yi maka bayani ta waya idan ka tashi zuwa." Kamar ya ce aa, sai ya tuna ba lallai ya samu cikakken bayani daga Humaira ba dalilin haka kawai ya amince. Wayarsa ya ciro ya miƙa mata. Tasleem ji ta yi kamar ta daka tsalle ta yi rawa da juyi, hannunta har rawa yake yi. Ya dubi yanda take danna wayar cikin rawar jiki ya ɗan taɓe baki. Ya fahimci inda ta dosa kwarai amma ya basar. Babu gurbin wata ɗiya mace a rayuwarsa, madallah da Humaira da ta ciri tuta har ta yi nasarar sace zuciyarsa. Ya karɓi wayar kafin ma ya tambayi sunan da zai yi saving da shi ta riga shi. "Sunana Tasleem. Kar ka manta ka yi flashing ɗina kaga koda ka kira zan gane kai ne saboda ban fiye ɗaga unknown number ba." Bai sake kallonta ba kuma bai tanka ba ya fice yana zura wayarsa cikin aljihu. Ta bishi da kallo kamar ta haɗiye shi. Futuha ita kuwa tuni ta shige ciki saboda kunyar yanda Ibb ya yi watsi da ita. Ta kuma rantse koda ace son Humaira yake, sai ta yi yanda ta yi ta raba su har abada. Tana ji a jikinta ba lallai ta sami Ibb ba, toh kuwa Humaira ta yi kaɗan ta samu abinda ita din ta rasa shi. A ɓangaren Tasleem kuwa gani take yi kawai ta tsinci dami a akala, ta samu mijin aurenta. A farko har ta amincewa Hamza D da zuwa gaishe da Abba, amma yanzu kam za ta dakatar da shi tunda ga Fadeel nan. Wannan kenan. *** Tun daga wannan ranar Futuha ke tsananin sanya idanu akan Humaira. Daidai da wayarta idan ta yi ƙara sai ta yi saurin kallonta ta ga wane ne. Rannan ta titse Raihana sai da ta titse wai wato Ibb ke kiran Humaira amma ta nuna mata sam ba shi ba ne, tsabar ta koyi munafunci. Raihana rai a ɓace ta amsa. "Wai ke meyasa kin fiye son kanki ne? Toh koda ace soyayyar ce tsakaninsu ai ke kin fi sauran masu haukar sonsa cin riba tunda ko ba komai ƙanwarki yake aure." Wannan magana ta fusata zuciyarta nan kuwa ta hau kilar Raihana kamar an aiko ta. Lokacin Humaira na can gidan koyon girkinta. Ita kuwa Tasleem ba ta dawo daga asibiti ba don yanzu su na asibiti an tura su daga makaranta. A falon daga su Muhsin sai Ummita. Hankali tashe Ummita ta ruga kicin ta kira Mami. Ganin abin da ke faruwa yasa Mami dakawa Futuha tsawa. Sai a sannan ta miƙe daga ruwan cikin Raihana, gaba daya fuskarta ta yi tabo. Kuka kawai take da ihun fadin Allah ya isa, raini kam ta daɗe da raina su. "Wane irin hauka ne wannan? Kashe ta kike son yi?!" Cewar Mami tana duban Futuha dake faman huci. Sai kawai ta fashe da kuka. "Wallahi Mami ba don kamannin yarinyar nan da mu ba sai ince ba ƙanwata ba ce! Wai saurayina ne Humaira ke so har da karɓar lambar wayarsa suna waya. Raihana ta san komai tsakaninmu, kema Mami kin san shi, wai shi  ne take fatan da ace ya auri Humaira. A gaban idanuna." Mami ta saki baki galala tana duban irin kukan da Futuha take yi, lallai abin da zai sa ta kuka har haka ba ƙaramin abu ba ne. Tana da taurin zuciya a wasu lokutan, ita kanta zancen ya shige ta don ba ta mance yanda ta sha ba ta labarin wani Ibrahim ko kunyarta ba ta ji. Daidai da Anna ta san da zaman soyayyar da Futuha ke yiwa Ibb, sun kuma ji daga bakin Tasleem da ma su Yassar cewa mutumin bai damu da ita ba. Ta sauke ajiyar zuciya. "Allah ya kyauta, shi ne akan wanda bai damu da ke ba za ki kashe yar uwarki? Kar ku kuskura na ƙara ganin wannan rashin hankalin." Haka kawai ta fadi ta juya, madadin kicin ta wuce dakinta. Futuha ranta ya yi baƙi, wato ma abin da Mamin za ta ce kenan? Ita dai ta tsani halin rashin kulawar da Mamin ke nuna musu. A fusace ta yi sashin Anna har tana bangazar Raihanar. Ita dai Ummita ba ta ce uffan ba, toh ban da abin Futuhar ma, koda ace son Humaira yake, ta tabbatar ba zai samu fuska ba. Ita ta lura kowa ma Humairar ta tsana muddin zai furta mata kalmar yana sonta. *** Anti Amarya ta ƙurawa Murja dake zaune tana faman jijjiga ƙafafu ido waya ta ke amsawa amma gaba daya fuska a jagule sai bayan ta kammala ta ajiye wayar, sannan Anti Amarya ta soma magana. "Yanzu ke wannan Idris din kinsan matsayin babansa kuwa? Meyasa Murja ba ki da wayo da tunani? Kin maƙale akan yaron da idan ya shigo gidan nan kallo ba ki ishe shi ba? Komai kika yi ba ki iya ba, amma Idris tun haɗuwarku a bikin Fu'ad ya manne maki kuma dagaske aurenki ya ke son yi. Kinga ina raba ki, wannan fa shi ne saki reshe kama ganye. Kin gani sarai da idanunki yanda Ubansa ke ji da shi kamar ba shi da wasu yaran bayan sa, ko a haka ya dace ki fahimci babu wanda zai yi mishi auren dole. Ko da ace kuwa ba namiji ba ne, tun da ya sa ƙafa ya dawo ƙasar nan, Alhaji ke gudun abin da zai ƙara sanya wa ya yi nesa da shi. Toh kuwa ki kama kanki tun wuri ina shawartarki, soyayyar Fadeel ba za ta kai ki ko'ina ba. Ina kara faɗamaki wallahi ba ya sonki ba ya kaunarki." Ta sani gaskiya ne tsagwaronta yayarta ke faɗi, amma ina, ta riga ta yi nisa da son Fadeel. Ta gama tsara yanda za su yi rayuwar aurensu wannan ya sa maganganun ke shigarta su na fita ta kunnen hagu. Ta furzar da huci. "Shikenan, na yanke shawarar abin da zan yi." A zaton Anti Amarya, ta dauki shawararta don haka ta murmusa. "Ko kefa." Ita kuwa murmushi ta ɗan yi, ta kuma ƙudurta a ranta za ta tari Fadeel kawai ta ce mishi tana sonsa. A yanda ta ga yana ganin mutuncin Antinnasa, ba zai watsa mata ƙasa a idanu ba. *** BAYAN SATI ƊAYA... A wani yammacin ranar Juma'a ne, Humaira na tsaye tana ninkin kayanta tana jerawa a sif. Futuha kuwa ta ƙure volume ɗin waƙar Kalmar So na breaker tana bi tana daukar bidiyo na kanta a tiktok. Riga gown ne a jikinta lemon green fuskar ta sha make up. Gashinta a waje ko ɗankwali babu, sai raye-raye take. Raihana da Ummita na zaune su na aikin lissafi na makaranta da aka ba su, su na ɗan taɓa hira jifa-jifa da Humaira. Su na yi suna kallon ikon Allah wajen Futuha da ta saita Camera ta waya sai raye-raye ta ke yi. Wannan karon ta sauya waƙar zuwa Warr na Ado Gwanja. Kusan yanzun aikinta kenan, ta yi rawa ta ɗora a Tiktok da Instagram, babu laifi kuma ta samu mabiya sosai, wannan ya kara fasa mata kai, a farko hotunanta kawai take ɗorawa iri-iri a instagram, amma ba ta jima da soma Tiktok ba ta ga ta samu karɓuwa wannan ba karamin ɗauke hankalinta ya ke ba a yanzu. Su na a haka sai ga Tasleem ta faɗo ɗakin da gudu. Jiki na rawa ta karasa sif din kayanta ta bude. Futuha wacce ta kammala tana editing kafin ta dora ta dakata tana dubanta. "Ke kuma lafiya?" Ta juyo da wani irin zumudi. "Kalau, babban baƙo zan yi fa. Kin tuna guy dinnan da na hadu da shi ranar bikin Shema'u? Abokin Ibb?" Futuha ta gyada kai. Tasleem ta daka tsallen murna. "Shi ne ya yimin waya ya kara neman kwatance, yau zai zo." Ita kanta Futuha ta jiye mata dadi, amma haka nan ta ji ɗan kishin yar uwar a ranta. Me Tasleem ta fi ta da har za ta yi kamu me zafi haka lokaci ɗaya amma ita kuma ta kasa samun Ibb? Tun su na yara an sha cewa ta fi Tasleem kyau, balle kuma yanzun da suka girma. Kowa ita ya fi kira kyakkyawa a kan dai Tasleem. Wannan ma na daya daga cikin abin da ya fasawa Tasleem kai a yanzun, itama tana jin takaicin kusheta da yan uwan Mami har ma da na Abba ke yi a lokuta da dama su ce wai Futuha ta fi ta kyau. Sai Futuha ta kasa ce mata komai bayan "Inyee, na maki murna." Daga nan ta ci gaba da latse-latsen wayarta tana murmushin da bai kai zuci ba. Tasleem ta maida hankali ga duban sif dinta, ta san Futuha mace ce mai kishi, ta fi kaunar komai ta fi kowa, kuma sai gashinan nasarar a kanta take. Tashi guda ta yi kamun babban kifin da ya fi wanda Futuhar ke hari. Raihana kuwa duban Ummita ta yi. Cikin sanyin muryar da ba lallai su Tasleem su ji ba ta ce. "Kada dai ace Fadeel me son Humaira ne zai zo?" Ita ma Ummita hakan ta ke zargi, Humaira na jin su ta yi kamar ba ta ji ba. Ta sani tabbas shi ne, sai bayan sun rabu ta kara tabbatarwa shi ne mai kiranta adalilin saƙon da ya turo mata bayan shigarta wurin bikin Shema'un, inda ya ce mata ta yi kyau kuma ya yaba da murmushin da ta yi mishi a lokacin. Sannan bayan sallar juma'a a yau din, ya bar mata saƙo inda yake shaida mata batun zuwansa gidansu a yau. Ya kuma roƙe ta kar ta ƙi fitowa. Ita kuwa a take ci kanka ba ta aika mishi ba balle ta kira ta dakatar da shi daga zuwan, ta fi kaunar ya zo ta jaddada masa ido cikin ido cewa ita ba ta soyayya, kuma ba ta sonsa ya rabu da ita. Tunano hakan sai ta ji dariya ya kama ta, dakyar ta danne ta hanyar murmusawa. Wato dai yau din akwai kallo kenan. Ta kara duban Tasleem da ta sauya kaya zuwa wani leshinta ja mai ɗigon baƙi a jikinsa mai ɗan karen kyau, murmushin ta kara saki wannan karon har da sautin dariyar da ya sa su Raihana dubanta, suka kuma dubi junansu, sun tabbatar Fadeel ɗin Humaira ne a hanyar zuwa. Akwai dai matsala kenan. ©️Rufaida Umar.*LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* 09034973645 Wayar Tasleem da ta ɗau ƙara ne ya sa ta saurin jifa da kwalbar turaren dake hannunta a saman gado, ta zari mayafinta da ya hau da leshin ɗan firit wanda ko kirjinta bai gama rufewa ba, ficewa a dakin ta yi bayan ta kara wayar a kunne tana fadin ga ta nan fitowa waje. Futuha ta mike ta bi bayanta wai za ta gani ko dagaske Tasleem din ta ke. Suna fita Humaira ta tuntsire da dariya har da faɗawa saman gado. Raihana da Ummita su ma dariyar suka shiga yi. "Ni dama ya ce yana son nata dagaske ai da naji dadi, ko ba komai na huta da alaƙaƙai. Haba, ina dalili mutum ana korarsa yana mannewa sai ka ce mayen ƙarfe." Ta ja guntun tsaki ta mike ta ci gaba da ninkin. "Kai Humaira anya a duniya za ki yi aure kuwa? Wannan abu har ina wai? Duk kyau da kwalisa na saurayi ba kya sonsa? Meke damunki?" Ummita ta ce tana duban ta, ji take kamar ta kai hannu ta buge ta tsabar haushi. Itama Raihana ta cafe "Rabu da ita Ummita, ai kanta akwai alamar kuncewar notina. Da ace ma ni ce ke, ko don na nunawa Tasleem ita ɗin ba komai ba ce a wurin Fadeel ai wallahi da hannu bibbiyu zan tarbe shi, shima dai Fadeel din da ba shi da zuciya ya kyaleki ya ƙi, ya bari kina ta wulaƙanta shi son rai. Da ni ce shi ko?" Ta yi ƙwafa amma ba ta ce komai ba, Humaira wacce tun soma maganarsu take kwaɗa musu harara, ta ja tsaki. "Matsalarsa, ni dai ai ban yaudareshi ba, tun farko kuma na faɗamasa ya rabu da ni, ya ficemin a rayuwa amma ya ƙi. Aikuwa babu abin da zan ce mishi, ya je can ya ƙarata da Tasleem." Ba su ce uffan ba sai kallon mamaki da suke mata, dagaske dai take ko a jikinta don ba su ga wani ɗigon kishi a saman fuskarta ba. A ɓangaren Tasleem kuwa, tana ƙarasawa falon ta ci karo da Mami a zaune tana amsa waya. Ganin ta da shirin fita ya sanya ta yi sallama da abokiyar wayar ta dube ta dakyau. "Ke kuma sai ina haka?" "Mami baƙo fa nayi, bari na shigo da shi falon saukar baƙi sai na zo." Ba ta ma kara jin abin da zai fito a bakin Mamin ba ta yi wuf ta fice, Mami ta yi kasake tana duban hanya, fitowar Futuha ya sanya ta maida akalar tambayar a kanta. "Wannan wane baƙon ta ƙara yi a yanzu ne? Duka-duka yaushe shi Hamzan ya zo da har zai ƙara zuwa?" Taɓe baki Futuha ta yi cike da jin kishin ƴar uwarta ta amsa. "Uhum, wai fa abokin Ibb ne yake sonta shi ne take wannan rawar jikin." Wani ɗan murmushi Mami ta yi. "Wato dai ruwan ido ne abin nata kenan? Ya za ta yi da shi wanda ta yiwa iznin zuwa su gaisa da Abbanta?" "Mami, wannan fa ya fi Hamza kudi da haɗuwa, na tabbata abin da ya ruɗe ta kenan." Mamin ba ta ce komai ba face Allah ya kyauta. *** Yana zaune a cikin motar hankalinsa rankatakaf akan ƙaton ƙyauren gidan da Tasleem ta yi mishi kwatance, ji yake tamkar ya yi tsuntsuwa ya shiga ya yi ido huɗu da abar ƙaunarsa, ganin ya kwashi mintuna babu alamar Tasleem sai ya ji gaba ɗaya ya karaya. Kodai ba gidan ba ne? Waya ya fiddo da niyyar ƙara kiranta sai ya hange ta ta fito daga gidan. Da farko sam bai gane ta ganin tamkar wannan ɗin shirin fita unguwa ta yi, ga dukkan alamu ma ba gidan ba ne. Amma a hankali tana matsowa ya gane ita ce don haka ya sauke tinted glass din motar wanda ya katange ta daga ganinsa sai waige ta ke. Tasleem kuwa yana saukewa ta ji numfashinta na barazanae ɗaukewa ba don tsoro ba sai domin tsananin burgeta da ya yi, ga kuma wani irin kyau da ya yi mata. Shadda ce a jikinsa coffee colour, ya ɗora hula a kansa, wannan karon babu gilashi a idanunsa don haka kyawun fuskar ya ƙara bayyana muraran. Ta kasa furta koda harafi har sai da don kansa ya fito daga motar ya rufe. Murmushi mai tsada ya sakar mata. "Ashe kin iya kwatance." Ta yi farr da idanu haɗi da sakarmasa nata kalar murmushin itama. Cike da yanga da kwarkwasa ta ce. "Kai kuma kana da basira tunda har ka iya ganewa. Barka da zuwa, bismillah mu shiga daga ciki." Ba musu ya karɓi tayinta, bayan sun gaisa da maigadi dake zaune a benci, tana gaba yana biye da ita yana ƙarewa gidan kallo. Hatta da gidan sai da ya ji kaunarsa a zuciya, ya kuma rantse albarkacin masoyiyar tasa ce.  Falon suka shiga ya zauna bayan ta mishi bismillah, sai ƙamshi kuwa ke tashi a ciki don dama tunda ya yi mata kiran farko ta ba mai wankin Abba dari biyu akan ya taimaka ya kara share mata a sa turaren wuta. "Ina zuwa." Ganin ta furta haka tana niyyar ficewa sai bai ce mata uffan ba, ba ya son ya yi garaje da tambayarta Humairar, tunda har ta ce tana zuwa to ya sani ba zai wuce ita za ta rako ba. Ya lumshe idanunsa kafin ya buɗe ya sauke saman hoton Abban dake maƙale jikin bangon. Ko wani bai faɗamasa ba, wannan mahaifin Humaira ne, kamannin ya ɓaci kwarai. Sai ya ji kaunar Abban ya lulluɓeshi, ƙauna dai kwatankwacin irin kaunarsa da Alhajinsa. Sallamar Tasleem din karo na biyu ya katse dukkan tunaninsa. Ganinta ɗauke da tray na kayan sanyi nan da nan ya ɗan ɗaure fuska, shi fa duk ba wannan ne a gabansa ba. Tana ajiyewa ya ga tana kokarin zama ya karya bille ya ce.   "Where is she?" Ta dube shi cikin rashin fahimta, ta yi ƙarfin hali ta ce. "Who?" Ya dauke kai daga kallonta, ya soma hasaso wani abun, ya gane ita ɗin manufarta daban, tunaninta ya tafi wani wajen. Mafarkinta daban. "Wacce na zo domin ta, Humaira." Kirjin Tasleem ya hau bugu, har ji ta yi ganinta ya ɗan dusashe. Miyan bakinta haka ta neme shi ta rasa, dakyar ta tattaro jarumta ta ce. "Humaira kuma? Dama wajenta ka zo." Sai a sannan ya dube ta tsakar ido. "Yes, wurinta na zo. Ko sadda muka haɗu dama haka nace wujenki zan zo?" Tasleem da har ta soma hawaye ta kasa magana, eh bai furta cewa wajenta zai zo ba, amma wane rainin hankali ne ya sa bai nemi kwatance daga Humaira ba sai a wurinta? Ta kuwa daure fuska tamau, ta rantse daga ita har Humairar sai dai su yi biyu babu. Kowa ya rasa don hana ta ce. "Toh Humaira ban santa ba, asalima a wurin biki muka haɗu. Na yi zaton gidanmu kake nufin na kwatanta mana. Don haka babu Humaira a gidannan." "Ko?" Ya furta idanunsa a saman hoton Abba, itama ta kalli hoton. Ranta ya ɓaci ainun, ta san kamannin Humaira muraran da ya gani a fuskar Abba ya sanya shi furta hakan. Ta mike tsaye ta  koma gefen Fadeel  ta zauna. Zuwa yanzu ransa ya kai maƙura wajen ɓaci amma yana tausar zuciyarsa da tunanin bai dace ba, ta ci alfarmar abin sonsa. Ko babu komai tace masa  mahaifinsu guda. Ita kuwa da muryar kuka ta soma magana. "Wallahi ina sonka. Tun ganin farko da nayi maka zuciyata ta kamu da begenka. Me za ka yi da Humaira? Da me ta fi ni? Na rantse babu abin da za ta nunamin." Ya runtse idanu, ransa ɓaci yake ya na kokarin danneshi, amma jin ana kushe abar sonsa ya bude idanunsa da suka yi jawur tarr a cikin nata. Sai da ta ji rishin kukan ya tsaya na ɗan lokaci tsabar fargabar kar ya shaƙo ta. "Ki san kalaman da za ki faɗi a kanta. Idan kuma kina son kanki da mutunci, ki yakice ni a ranki. Ki sani kuma ki kara, Humaira ta fiyemin ire-irenki dubu. Kyau da sura ba su ne a gabana ba. Da ace su ne, na bar da yawansu a inda na fito, ba na sonki, ba kuma na son kowa sai ita ɗin. Idan za ki iya ki shiga ki yimin sallama da ita, idan ba ki iyawa ni zan sa a kira ta." Da gudu Tasleem ta mike ta yi hanyar fita tana kuka sosai. Fadeel ya mike tsam ya fito farfajiyar gidan inda ya ci karo da Muhsin na wasa da keke. Ƙarasawa ya yi wurinsa ya ɗan durkusa daidai tsawon yaron yana murmushi kamar ba yanzun aka ɓata ransa ba. "Boy, ya sunanka?" "Muhsin." Ya jinjina kai, da alama duka sunayen yan gidan su Humaira masu dadi ne, shi kam dadi yake mishi, ya ji ance Futuha, Tasleem yanzu kuma ga Muhsin. Ganin yaron na shirin janye keken ya sanya shi saurin riƙe keken. "Ɗan shiga ciki ka ce Humaira ta zo, Fadeel ya iso." Jin haka Muhsin ya amsa da toh, ya juya kan kekensa bayan Fadeel ya saki ya wuce ciki. *** A can kuwa, Mami da Futuha na zaune sai gani suka yi  Tasleem ta fado falon a guje, tana  zuwa ta zube cinyar Mamin tana kuka. "Ke lafiya? Meyafaru?" Cewar Mami cikin ɗaga murya gaba daya ta ruɗe. Wannan ya yi sanadin fitowar su Humaira daga ɗaki sai a sannan Tasleem ta ɗago ta dubi Mami. "Wai ba ki yake so ba, wajen Humaira ya zo." Jin haka Futuha ta ji zuciyarta dan yi sanyi, ko ba komai Tasleem ba za ta ƙara hura mata hancin ta yi wanda ya fi Ibb ba kuma ta gane ba Ibb ne masoyin Humairar ba. Amma a gefe kuma kishi da tsanar Humaira ne ya kara mamaye ta, mene ne da ita wanda har namiji irin Fadeel zai gani ya maƙale mata, su da suke buzaye ma ta kasa shawo kan Ibb ya kaunace ta sai wata can bafulatanar ruga? Mami kuwa gaba daya fuskarta ta sauya, kafin ta yi magana dai ga Muhsin a guje da kekensa ya shigo falon, yana cin karo da Humaira ya ce. "Adda Humaira, ki je inji wani a waje." "Ka je ka ce ba za ta fito ba! Kada ya kara gigin zuwa gidannan!" Gaba daya suka dubi fuskar  kowannensu dauke da mamaki idan ka cire Humaira da kalaman ya yi mata dadi ainun, haba ta gaji da naci irin na Fadeel, shi bai san ba ta son komai da ya danganci saurayi ba. Meyasa ya ƙi fahimta? Ai gwara Mamin ta kora mata shi. A bangaren Raihana da Ummita kuwa tunaninsu daban da nata. Akan me Mami za ta ce Fadeel ya tafi? Wato don ba ya sin Tasleem shikenan kowa ma ya rasa? Tasleem da Futuha kuwa dadi ne ya mamaye su, wato dai uwa uwa ce, ta damu da yaranta. A farko sun yi zaton kwata-kwata Mamin ba ta kaunarsu ta fi kaunar ƴan riƙonta musamman ma Humaira. Amma a hukuncin da ta yi abin ya musu dadi, Tasleem ta ji gwara ma kowa ya rasa. Muhsin kuwa tuni ya fice don cika umarnin Maminsa. Humaira dai ta juya zuwa daki don ci gaba da abin da ya rage na ninkin da take yi, ganin haka Ummita ta bi bayanta, Raihana kuwa da sauri ta bi bayan Muhsin. Futuha na kwala mata kira ta yi mata banza. *** A can farfajiyar gidan kuwa, Muhsin ne ya karaso har kusa da Fadeel, yana shirin faɗin saƙon Mami da sauri Raihana ta kwala mishi kira. "Kai Muhsin." Suka juya har Fadeel suka dube ta, ta karaso da sauri ta ce. "Jeka zan faɗamasa." Ya kuwa tura kekensa ya ci gaba da zagaye a gidan yana waƙe-waƙensa da ake musu a boko. Ta gaida shi ya amsa, zuwa yanzu ya karaya da ganin Humaira. "Suna na Raihana ƙanwa ce ga Humaira, don Allah ka yi hakuri ba za ka samu ganinta ba a yau sai dai ko watarana idan an ɗan kwana biyu." Murmushin da bai kai zuci ba ya yi, ta tabbata shi kadai ke kiɗa da rawar sa, wacce ya ke yaƙin don ita ba ta san yana yi ba, ko kuma ya ce ta sani amma ra'ayinsu ya sha bamban. "Kar ki damu, ba komai. Idan kin shiga ki ce ina gaishe ta, na kuma cika alƙawarin da na daukarwa kaina na zuwa gidansu. Amma hakan ba ya nufin ko a mafarki zan iya fita a rayuwarta. Ina sonta." Daga nan ya juya ya fice. Raihana ta zuba masa idanu har ya fita daga gate din gidan, tausayi sosai ya ba ta, Humaira dai tana neman cutar da kanta. Samun masoyin gaske irin Fadeel abu ne mai matuƙar wahala. Ta ji haushin Humaira a zuciyarta kamar ta je ta rufe ta da duka. Gwuiwa a sake haka ta juya ta koma ciki. *** Tun faruwar wannan lamarin Fadeel ya shiga damuwa ainun, yana da tabbacin shi yake so ba a sonsa, ya kuma shirya rungumar wannan jarrabawar ya yaƙe shi. A gefe ga mahaifansu da suka soma matsawa akan su fito da matan aure shi da Ibb. Satinsa guda bai kira ta ba balle ya aika mata saƙo, jarrabawa ya yi domin ya ga ko zai iya yakice ta a rai bisa shawarar Ibb amma sai ya ji kamar yanzun ne ma ya soma kaunarta. Ba kuma ya jin zai iya haƙura da ita. Ya miƙe daga saman gadon da yake kwance wanda tashinsa kenan daga bacci mai cike da mafarkan Humaira, kamar daga sama ya ji ana kwankwasa ƙofar falon, agogon dake maƙale a bangon ɗakin ya kalla, ƙarfe goma har ta gota. Ya ɗan ja ƙaramin tsaki, ya tuna yau suka yi da Alhaji zai soma zuwa kamfaninsa ya kama aiki, jin ƙarar kwankwasar yake har cikin kansa dake radadin ciwo, iya sati ɗaya zuciyarsa ta jigatu da rashin ji ko ganin Humaira, ta ina zai soma fidda ta daga rayuwarsa? Wannan abu ne da ba zai yiwu ba sam. A hankali ya miƙe daga shi sai vest da dogon wando ya fito falon. "Waye?" "Ni ce Yaya Fadeel, abin kari na kawomaka." Guntun tsaki ya ja jin muryar Murja. Ƙofar kawai ya bude ya juya ba tare da ya ko kalle ta ba ya ce. "Ki ajiye ki fice. Na gode." Ta ji ciwon hakan amma da ta tuno da batun Malam na cewa idan har ya ci abinda ta girka da laƙanin da ya ba ta to fa ba makawa hankalinsa zai karkato gare ta. Ya yi mata gargadi akan lallai ta tabbata ya ci, idan kuwa bai ci ba to fa haka za ta kara narka uban kudade a yi mata wani sabon aikin. Don haka sai ta zauna a falon ta ƙi bin umarninsa, shi kuwa wanka ya shiga bayan sun yi waya da Alhaji ya buɗe mishi wuta akan rashin zuwansa ofis da wuri, hakuri ya dinga  a shi ya ce yana tafe. Suka yi sallama. Koda ya fito wankan a gaggauce ya shirya cikin kananun kaya, dark green din tshirt sai wandon jeans. Ya ɗaura agogo a tsintsiyar hannunsa, ya gyara sumar kansa. Fitowarsa falon ya ga mutum zaune, nan da nan ya tamke fuska, ita kuwa Murja da rawar jiki ta ce. "Barka da safiya, bari na haɗa maka shayin." Ba tare da ya kalle ta ba ya ce. "No ki bar shi nayi latti, Alhaji na jirana. Ki je da su kawai." Murja cikinta ya bada sautin kululu, ita dai ta shiga uku, wannan rashin sa'a har ina? Yanzu shikenan ta yi asarar dubu tamanin? Ita kuwa wa za ta je ya ba ta wasu kudaden a ƙara maimaicin aiki? "Ba kya ji ne?" Wannan karon ya yi maganar yana ji kamar ya ɗauke ta da mari hagu da dama, abu ɗaya da ya sa yake raga mata bai wuce na tunanin shi ɗin ma fa haka yake fama da soyayyar wata ba ta sonsa. Ganin yanayinsa sai ta maida kayan kwandon ta dauka ta fice har da kwallarta. Fadeel yana so ya kashe ta, yanzun ma ji take kamar ta faɗa wannan faɗaɗɗan kirjin nasa ya yi mata rumfa da hannuwansa, sai dai kash! Wutsiyar raƙumi ta yi nesa da ƙasa. Amma kuma komai nisan jifa ƙasa zai faɗo kuma sannu sannu ba ta hana zuwa, ta na ji a jikinta watarana haƙanta zai cimma ruwa. *** Abba ne zaune fuskarsa cike da walwala, babu jimawa iyayen Hamza suka tafi bayan sun nemawa ɗansu auren Tasleem kuma ba musu ya amince ya ba su. Tasleem da kanta ta kira Hamza ta ce ya turo saboda bakin cikin abinda Fadeel ya yi mata, ga faɗan da suka yi da Futuha me  yi mata dariyar ta rasa shi, ita kuma don ta nunawa Futuha tana da mai sonta dagaske ba irin ita me bin Ibb ba ya sonta ba yasa ta kiran Hamza ta ce matukar dagaske yake toh ya turo a nema mishi aurenta a kwana uku, idan kuwa ya wuce haka to kaunar da yake mata a baki ne. Dama kuma shi abin da yake jira kenan, don haka sai kawai ya ba da kai bori ya hau. Mami ta shigo itama fuskarta dauke da walwala ta zauna gefen Abba. Kafin ma ta ce wani abu ya riga ta. "Maryama yau ina cike da farin ciki, ba ni da burin da ya wuce naga na aurar da yarannan mata lafiya kowaccensu ta tare a ɗakinta. Ina tsoron sharrin wannan zamani. Ita ma Futuha zan mata magana, ta fito da miji na haɗa aurensu baki ɗaya zai fi min. Karatun can su je su ƙarasa a ɗakin mazajensu, naji da kannensu masu tasowa." Mami ta jinjina kai, "Hakane Abban yara, in sha Allahu itama zamu yi magana da ita naji ko tana da tsayayye. Na san dai wani yaro da ta kwallafa rai a kansa amma shi bai san tana yi ba." Abba ya ɗan yamutse fuska. "Ai kinji irin shirmen yaran yanzu masu biyewa soyayya, ban da shiririta ke ba manema kika rasa ba, mutane nawa ne suka tare ni akan suna sonki amma ki nacewa wanda ba ya so? Allah ya kyauta, lallai ki ce mata nace ta nutsu ta fiddo miji a haɗa aurensu da ƴar uwarta. Kina ji dai iyayen shi Hamza sun ce nan da wata shida suke so a yi komai a ƙare." "Shikenan, zan mata magana." Mami ta amsa a sanyaye, fatanta Allah yasa Futuha ta cire ran da ta kwallafa akan Ibb ta kama wani. ***   Futuha na zaune tana danne-dannenta a waya kamar koyaushe, bidiyo mai zafi ta ɗora tana bin waƙa, ta ci ado a bidiyon har ta gaji, ta yi ɗaurin ture ka ga tsiya da dankwalinta na leshi, karanta comments kawai take tana jin dadi tana zabga murmushi, wasu kuwa zagi ne da addu'ar nema ma ta shiriya. Irin wannan sai dai ta ja tsaki ta wuce. Ta ci gaba da kallon bidiyoyin jama'a nan ta ci karo da wani bidiyo da ya ɗaga hankalinta wacce wata Sa'a Ƴar snow ta yi a kanta, zagi ne na cin mutunci da sharri, wai Baby Futuha ta tiktok karuwa ce kuma tana da hotunanta da shaidu akan hakan. Tashin hankalin har da hotonta daga ƙasa gefen bidiyon. Ba ta san sadda ta kwalla ƙara ba a ɗakin bar ya farkar da Humaira me baccin sha biyu. Su biyu ne dama kaɗai a ɗakin, ita Humaira ma ba ta san Futuhar ta shigo ba domin gaba daya sun fita makaranta, kenan ta dawo ita. Kuka sosai Futuha ke yi hannunta har yana kakkarwa. Humaira ta ji hankalinta ya tashi, duk kuwa da cewar ba sa shiri ta miƙe ta ƙarasa gareta.   "Anti Futuha lafiya?" Ba ta ko kalleta ba ta wuce da sauri ta yi hanyar fita. Humaira dai na kallon ikon Allah. Toh me ya yi zafi haka? Ta watsar da batunta gami da buga hamma.    *LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* 09034973645 "Shi Fadeel din ya sani?" Ta girgiza kai tana kara sunne wa kamar mai jin kunya. Alhaji ya yi shiru sai kuma ya ce. "Shikenan, ni dai b na yiwa yarana dole balle kuma namiji. Zamu yi maganar da Fadeel duk amsar da ya bayar za ki ji daga Antinki." Ji ta yi kamar Alhajin ya harba mata mashi a ƙahon zuciya, da irin wannan amsar ai gwara kawai ya ce mata aa kansa tsaye. Abu ne da ya sani kamar yanda ta sani, zai wahala Fadeel ya amince da shi, ta yi zaton yanda Alhajin ke yabawa da nutsuwarta zai ce ya amince ya zaɓawa Fadeel din ita matsayin matarsa. Haka ta mike ta fice gwuiwa a sake. Bayan fitarta Alhaji ya yi shiru, ta ina zai soma ɓata ran ɗannasa wanda a baya ya sha baƙar wuya a dalilinsa da mahaifiyar Fu'ad? Ya musguna mishi, bai duba maraicinsa ba na rashin uwa ya yi watsi da shi. Karshe don kansa da ya gaji bayan ya yi hankali ya fice ya koma dangin mahaifiyarsa a can ƙasar Kamaru. Sai kuma bayan da ya kwashe dogon shekaru har kusan biyar ya dawo yanzun kuma ya hargitsa shi komai ya ƙara hargitse mai? Yaransa biyar kacal a duniya, Fadeel ne babba sai Fu'ad sai kuwa ƙanwar Fadeel uwa ɗaya uba ɗaya Hannatu dake aure a can Adamawa, sai yaran Anti Amarya biyu, Khadija da Abdulmaleek. Shi hakanan Allah ya yi shi ba mai yawan haihuwa ba, matansa babu me yin tsarin iyali.   A ƙarshe dai ya yanke zai mishi maganar auren don shi kansa yana damuwa kwarai akan zaman yaran haka(wato Ibb da Fadeel) ba tare da iyali ba. Har ga ƙaninsu Fu'ad ya yi auren ya bar su. ***   Fadeel ya nutsu a gaban mahaifinsa, bai katse shi ba har ya kai aya. Sai a lokacin ya yi magana.   "Na ji bayananka Alhaji, ina neman addu'arka musamman a wannan wata mai alfarma da za mu shiga akan neman zaɓin Allah. Sai dai kuma ba na kaunar Murja, ba na sonta matsayin matar aure. Don Allah abar zancenta." Jinjina kai Alhaji ya yi, ya ɗan murmusa kaɗan. "Shikenan, Allah ya sa hakan ya fi alheri. In sha Allahu zan tayaku kai da ɗan uwanka. Ya kamata ku maida hankali." Fadeel ya amsa a ladabce. Daga nan suka rufe wannan babin suka cigaba da tattaunawa akan abubuwan alheri na sadaka da neman lada da Alhaji ke yi duk shekara idan watan azumi ya kama. Kamar yin kunu da abincin sadaka, kyautar butoci, ruwa, dabino da ma sauransu a masallatai., daukar nauyin tafsir, sai kuwa idan sallah ta matso ya yiwa ƴan uwansa marasa ƙarfi da marayu da dama sutura. Da wannan suka rufe babin Murja da ma batun aure. Anti Amarya dake laɓe a bayan labulen ɗakin Alhaji, ta ji ciwon cewa da Fadeel ya yi ba ya son ƙanwarta. Ta yi ƙwafa, ai idan ya san wata bai san wata ba. *** A daren ranar Lahadi gaba ɗaya garin aka dau murnar ganin watan Ramadan. Lokacin Sahur gaba ɗaya gidan suka tashi aka yi idan ka cire Tasleem wacce ba ta da sallah.   Lokacin shan ruwa na kawo kai, Humaira da Ummita har Raihana ana kicin ana faman kai da kawowa, Tasleem ba ta shiga ba don langaɓewa ta yi wai mararta na ciwo. Ita kuwa Futuha tana tsaye kawai tana yatsine-yatsine da gwatsale wani abun idan Humaira ta yi wai ba haka ake yi ba. Ita dai ba ta tanka mata ba albarkacin watan da suke ciki na ibada. Sai da suka kammala komai sannan suka jera a tsakar falon bayan shimfiɗa ƙatuwar ledar cin abinci. Na Abba kuwa can ɓangarensa suka kai aka shirya komai. Itama Anna, Raihana ta kai mata komai ta bar ta tare da su Muhsin don a duniya Anna ba ta fiye son zuwa falon Mamin ba sai da kwakkwarar dalili.   Sai a sannan Tasleem ta shiga kicin din ta ɗibi abinci ta dawo falon tana ci ta a yatsine fuska wai gishiri ya yi yawa. Ba ta ko jin nauyin yan uwanta maza dake zaune a falon su na taɓa hira. Haka aka sha ruwa aka yi zaman cin abinci bayan kowa ya yi sallah. Mazan suka dinga santin girkin amma da zarar sun yi ido da Humaira su watsa mata harara idan ka cire Ƙasim wanda tun wata rana da ya shiga ɗakin Mami zai ɗau kuɗi ta gan shi kuma ta rufamasa asiri ba ta faɗawa kowa ba, tun a ranar ya soma ganin ta da ƙima a idanunsa. Ya ke kuma jin kunyarta. Yassar kuwa faɗi yake ai ba basirarta ba ce, koyamata aka yi. Futuha  ta ja tsaki.   "Wai kai kana wani zance, ina abin yake? Ni ba abin da ya kara ɓatan rai wai sai da Abba ya ce wani mu shiga kicin mu koyi girki wajenta. Don Allah ku ji wani abu." Dariya suka yi idan ka cire Ƙasim dake faman cin sandwich da ya ji kaza da su cheese yana santi. "So ya ke ki je ki yiwa Alhaji Yakubu kar a ji kunya mana." Jin an ambaci Alhaji Yakubu nan da nan ta ɗaure fuska. A duniya yanzu babu wanda ta tsana irinsa, mutum dai kamar maye. Abu daya da ta sani shi ne, daga maganar zuwa kamawar watan da suke ciki na azumi ya yi mata ɓarin kuɗi sama da dubu ɗari, wannan kaɗai shi ne ya burgeta musamman ganin cewa Tasleem ba  ta samu hakan ba. Rabu dai da Hamza akwai kulawa a baki amma babu ko asi da ya taɓa kawomata. Wannan abu na yiwa Tasleem ciwo kuma yana fasawa Futuha kai, tana son ta ga ba ta son mutum yana bibiyarta kamar jela. "Kar ka sa na tashi, har wani tsami na ji abincin ya soma yimin a baki." Yassar da Dawud suka kwashe da dariya. Tasleem ta yamutse fuska ta ce. "Gulma, a bakya so kike kwace ƴan chanjinsa. Fuska biyu." Futuha ta dire fork din hannunta da ta ke cin haɗin salad da shi, tun ba ta kai ga haɗiyar wanda ta ke tauna ba ta soma balbaleta da masifa. "An kwata ɗin, ina ce albarkacin kaza dai ƙadangare ke shan ruwan kasko? Ko kin manta abin da Mami ta ce akan amfanin kudin?" Tasleem ta hadiye zancenta, ta tuna Mamin cewa ta yi Futuhar ta saki jiki da Alhajin ta dinga nuna masa kulawar koda iyaka baki ne, muddin dai zai bayar da kuɗin ba za a ji kunya a auren ba tunda ba su da tabbacin samun yanda ake so daga wajen Abba. Wato na siyayyar kayan ɗaki da sauransu. Maganar Futuha ta katse ta. "Kuma ko banza gwara Yakubu tun daga nan an san zai iya riƙe mata biyu, wani kuwa da ko ɗayar ma ya kasa nunawa zai iya sai afkin waya da ƙalƙalar  turanci kamar tsatson sarauniyar Ingila." Suka kwashe da dariya. Ran Tasleem ta kai kololuwa a ɓaci, su Humaira na zaune su dai su na shan ruwa abin su daga gefe suna kallon ikon Allah. Raihana ce ta tofa. "Kai Adda Futuha, ramuwar gayya fa akwai zafi kar ki kai Adda Tasleem bango." Aikuwa tana cewa haka kamar ta kara zuga Tasleem sai kuwa ta yi caraf ta ba ta amsa. "Kyale ta Raihana, ai mugun abu ya ƙare a gindinta tunda ko ba komai nidai auren soyayya zan yi, Hamza gani ya yi yana so a mutunce. Wata kuwa sai bayan an jefe ta da kalmar karuwanci, ƴar rawar Tiktok sannan ta yi na'am da Alhaji mai zubin moɗa." Lallai, baki idan ya san me zai faɗi bai san me za a mayar masa ba. Aikuwa Futuha ta yi kukan kura har ta na cilli da bowl din salad dake saman cinyarta zuwa ƙasa, ta yi kan Tasleem da kokawa. Itama Tasleem kasancewar a wuya ta ke kawai sai ta biye mata suka hau jibgar juna. Dakyar Yassar ya shiga tsakaninsu gudun kar Abba ya ji. Tasleem na  huci ta ce. "Ni kuɗi bai dameni ba tunda zan auri wanda yake sona nake sonsa. Arzikin dai ai na Allah ne, kuma ko makaho ya shafa ya san Hamza ba talaka ba ne. Alhamdulillah ba a taɓa yimin wannan mugun ƙazafin na karuwanci  ba." "Shegiya! Ni kike kira karuwa, ai gwara ni sharri ne, ke kuwa sau nawa kina yiwa Mami sata? Ko ranar da aka yi na Humaira, ina ce ke ce kika kawo shawarar a yi mata wannan sharrin don ki wanke kanki. Ke ce kika ɗauki kuɗaɗen, ganin Yassar ya kama ki sai aka shiryawa Humaira tuggu don kar Mami ta zarge mu." Humaira da ke shirin kai kofin kunu bakinta ta yi saurin ajiyewa, ashe ma ɓarayin biyu ne? Ba ma wannan kadai ba sai ganin yau dai Allah ya karɓi addu'arta gaskiya ta yi halinta. Tasleem gaba ɗaya ta yi wuri-wuri da idanu, ko kaɗan ba ta zaci Futuhar za ta yi mata wannan tonon sililin ba. Yassar ya dakamusu tsawa amma kasancewar girma ya faɗi ko a jikinsu, sai dai tsawar farko daga Abba ya sanya gaba daya suka yi tsit. Ashe yana tsaye a bakin ƙofar falon tun sadda suka soma kokawa, Mami na biye da shi a baya. Gaba ɗaya hankalinta a tashe, wato dai ya allura ta tono garma? Ba wannan ba ma, babu uwar da za ta so ganin yaranta kansu a rabe. Gaba daya falon ya yi tsit su Tasleem sai rarraba idanu ake. Ya shigo tsakiyar falon ya wanke su ganin ba su duba girman watan da ake ciki ba na ibada su na yi mishi faɗa a falo. Daga nan ya nemi sanin abin da ya faru da Humaira a baya, nan fa Raihana kamar wacce ake tsikara ta ba shi labari. Humaira kanta a ƙasa tana hawayen farin ciki, wato da Allah ya tashi wanke ta sai ya sa Abba da kansa ya ji zancen ba iyaka Mami ba. A ranar su Yassar da Futuha sun ga tashin hankalin Abba, ya kuma ci alwashin saɓawa duk wanda ya ƙara jarraba musgunawa Humaira. Hatta da Mami mai kokari akan Humaira a ranar har da ita ya haɗa ya ce ai laifinta ne da ba ta tsawatar musu shiyasa suka samu sake. Haka Abba ya yi faɗan da ba su zata ba har Humairar daga nan ya fice daga falon. Mami ta bi yaran da kallo sai kawai ta juya ta bi bayan mijinta. Humaira ta mike ta kalle su fuskarta dauke da murmushi ta juya zuwa ɗaki.  Ranar jin ta take ranta babu ko ɗigon bakin ciki sai dai ba ta ji dadin dorawa Mami laifin su Yassar da Abba ya yi ba. Amma ta yi mamakin Abban, a baya tana tunanin ko sonta ne ya daina, ko ya manta ma da ita a lissafin ƴan gidan sai kuma abin da ya yi yau ɗin ta fahimci tana nan daram a zuciyarsa kawai dai ba shi da lokacin kansa balle na hira saboda yanayin kasuwa.  Banɗaki ta shige ta ɗora alwala ta dawo ta zura hijabinta ta shiga lazimi. Ta na nan zaune ta yi shiru, wani lokaci can take tunowa ita da Dada musamman a wata irin na azumi yanda suke zama bayan shan ruwa a yi hira kafin lokacin sallar isha'i.   Ƙarar wayarta ya katse mata tunani, ta sa hannu ta ɗauka. Fadeel, shi ne  sunan da ya bayyana saman screen din, haka Raihana ta adana mata lambar ba da son rai ba. Albarkacin watan da suke ciki ya ci ta ɗaga da sallama. Ya amsa daga can ransa fari sol.    "Ina fatan kin sha ruwa lafiya?" "Lafiya kalau." Ta amsa a taƙaice. Shiru ya ɗan biyo baya, ya rasa me zai ce yana gudun ya yi furucin da zai sa ta katse wayar gaba ɗaya. Ya kasa hakuri balle ya danne don haka ya ce. "Sai yaushe Humaira? Sai yaushe za ki samarwa wannan ɗan marayan gurbi a zuciyarki? Ba zan gaji da roƙo ba, ki ba ni dama Humaira. Wai kin san so kuwa?" Nan da nan ta ji ya har ta soma harzuƙa a sanadin kalmar so da ya ambata, cike da gatse ta ce. "Sai nan da shekara." "Kin yi alƙawari nan da shekarar za ki amince ki yarjemin da batun aure?" Ta dauki maganar a zancen banza, ta sani babu wahalallen da zai yi dakon shekara ya auri budurwar da ba ta ko son zancen auren balle auren. Don haka babu dogon tunani ta amsa. "Eh, na yi muddin za ka rabu da kirana ka bar takuramin." Shiru na wasu lokutan sai kuma ya sauke nannauyan ajiyar zuciya. "Za ki same ni da bin umarninki, amma kiyi hakuri koda saƙo na dinga aikomaki ta waya. Ke kuma ki daure ko da sallama ki amsamin domin na san kina sane da ni." "Naji." Ta amsa gabanta na faɗuwa ba tare da ta san dalili ba, ta ji zufa ta keto mata. Tsanarsa ta ke ji yayinda a wani gefe can a ƙasan ranta ta ke jin wani abu da ba ta tantance ba. "Na bar ki lafiya, ki yi hakuri na adana dukkan wayoyinmu, abin nufi nayi recording tun daga farkon wayarmu har na yau. Hakan kan ɗebemin kewa wasu lokutan idan son jin muryarki ya ci ƙarfin kwakwalwata. Ki dage da addu'a a wannan wata mai alfarma. Ina roƙon Allah ya yi maki zaɓin abokin rayuwa nagari, koda ba Fadeel ba." Yana kaiwa nan bai jira cewarta ba ya katse kiran. Ta yi ƙuri tana duban wayar, hakan na nufin wayar ƙarshe ce tsakaninsu sai nan da shekara? Ta taɓe baki, ta sani cewa ta ba shi aiki mai wahala. Kuma ba zai ma iya shekara yana wahala a kanta ba. Watakila ma kafin sannan ya yi aurensa. Ta watsar da tunani ta yi jifa da wayar ta mike jin an soma kiraye-kirayen sallar isha'i. *** Anna ce ke yiwa Mami faɗa kamar ta ari baki. "Kin bari miji ya rainaki ya raina uwarki, dama tun akan batun auren Futuha na san cewa Isuhu ya sauya daga yanda na san shi. Wato yanzun ya ci moriyar ganga ya yar da koren, ke yanzu ban da ke sakara ce wawiya, kina tunanin har wani karfin iko kike da shi a wajensa? Mutumin da ya dubi tsabar idon mahaifiyarki ya ce ba zai janye kudurinsa na aurar da Futuha ba? Toh wallahi Maryama ki shiga taitayinki tun kafin dare ya yi maki, mazan nan dai babu amana bar ganin wai girma ya soma kama shi, don ya dankaro maki kishiya ƴar zamani ba komai ba ne. Tun wuri ki ƙwatarwa yaranki ƴanci a wajen mahaifinsu, ki murje idanunki dakyau ki daina bari yana wulaƙanta min jikokina akan wasu bare can. Ban da ma mutum mai shegen mantuwa, Isuhu ko kare ne ya fito daga gidan su Fatima zai kalla da daraja? Matar da ta nunawa duniya cewa ta tsane shi har kwanciya ciwo take akan sai ya sauwaƙe mata ta koma garinsu? Mts, Allah ya wadaran naka ya lalace." Har Anna ta kai aya ita dai Mami ba ta ce komai ba banda huci da take furzarwa, daga ita sai zuciyarta ta bar wa sanin abin da take tunani. Dakyar ta taushi zuciyar ta soma magana bayan sakin ajiyar zuciya mai nauyi. "Anna ki yi hakuri, babu amfanin mayar da hannun agogo baya tunda mai afkuwa ya riga da ya afku. Na ba ki wuƙa da nama akan ƙwatarwa jikokinki ƴanci, ki yi abin da kika ga ya dace. Sai dai ki sani, ni Maryam ba da yawuna ba saboda daidai gwargwado yarannan su na kyautatamin, ba ni na haife su ba amma su na bi na sau da ƙafa fiye da ma yaran da na haifa a cikina. Kiyi hakuri idan maganata ta maki zafi." Anna ta wurga mata harara. "Au haka kika ce ko? Toh shikenan, ni zan san abin yi a kai kamar yanda kika ce. Koda kuwa zan rasa kwabo a asusuna, zan kwatarwa jikokina ƴancinsu, sai ya zama Isuhu ba ya ganin kowame ɗa a gabansa idan ba su ba. Mu zuba ni da ku." Mami ganin yanda ta ɗauki zafi kawai sai ta miƙe itama ranta a jagule ta bar mata ɗakin. Da ace Anna ta san damuwar da ke cin ranta da ba ta soma ƙara mata fetur a kan wutar da ta riga ta soma babbaka a zuciya da kwakwalwarta ba. Ta ja tsaki ya fi a ƙirga a hanya har ta ƙarasa ɗakinta. *** Azumi yana ta tafiya har a yau sun kai goma sha shida, lamarin su Tasleem da Abba ya ƙara tsauri musamman da ya fahimci ba su bi zancensa ba na shiga kicin. Futuhar da ta soma shiga, tun bayan faɗan da Abban ya yi ya goyi bayan Humaira sai ba ta ƙara leƙawa ba. Cikin ikon Allah wataran kwatsam sai ga shi a kicin din abin da Humaira za ta ce tun zuwanta gidan banda ranar da ya ji fitar gas ya cika gidan ya shigo, ba ta taɓa ganinsa a ciki ba. Ganin daga ita sai Ladidi da Ummita a kicin din ya shiga bambamin faɗa, a sannan Raihana na fama da Malaria mai zafi har allurai ta sha. Aikuwa har ɗakin ya shiga ya titsa ƙeyar Tasleem da Futuha zuwa kicin din yana gargadin Humaira akan lallai duk sadda ba su shiga ba ta sanar mishi. Tun daga wannan ranar ba su ƙara fashin shiga ba. Sai dai shigar da rashinsa ba amfani don kusan zama suke yi kawai ba sa komai. Abba ya yi siyayyar kayan sallah, kamar kowace shekara wannan ma da kansa ya yiwa kowa zaɓi idan ka cire samarin da ya ba kowannensu kudi su siya shadda. Yanmatan kuwa atamfa ce iri ɗaya sai dai bambancin kala, sai dubu uku da ya ba kowace budurwa a siya takalmin sallah. Shikenan bai ƙara daga haka ba, su Futuha aka dinga kauɗi ganin Alhajinta ya kawo mata shadda da atamfa har da leshi masu tsada sai kuwa dubu ashirin na mayafi da jaka da kuma ɗan kunne. Tasleem kuwa dayake ta soma shaƙa sai ta budewa Hamza wuta akan ko kyautar biyar bai taɓa ratsawa tsakaninsu ba. Ranar shi kansa ya yi mamaki da ta iya karya bille ta tambaye shi kuɗi, aikuwa ya ce ta turo acc no, take ya yi mata transfer dubu goma sha biyar. Tsabar rainin da ta yiwa kyautar ko faɗawa su Mami ba ta yi ba sai dai sun mata amfani ta siya abin da take so. Su Humaira kuwa Mami da kanta ta kara musu dinki, leshi mai kyau na ɗankwarai ta siya musu su uku kala ɗaya. Ana saura kwana biyar sallah sai ga Anti Jannat a gidan. Zuwanta ya yiwa su Futuha daɗi ko ba komai mace ce mai sakin bakin aljihu ga fankama. Burinta ta buɗa ko don ta nunawa Mami ita fa mijinta mai bayarwa ne, yana da kyauta sosai. Daidai da Anna ta fi ji da ita, abinda ya hana ta zama wajen Jannat din bai wuce na ganin surukanta sun nuna ba su kaunar hakan ba. A farko ta gwada amma aka so samun matsala, dole ta tattara ta dawo gidan da ta raina, gidan Abba. Suna zaune a ɗaki bayan sun kammala gwada dinkunansu na sallah, ya yi musu cif da cif, washegari kuma sai tafiya kitso da ƙunshi. Sai faman tsokanar Ummita suke yi ganin saurayinta ya kira tana kashe murya a waya, koda ta ajiye Raihana ta dube ta. "Wai ni yaushe za ki ba Ya Sayyadi damar zuwa gidannan?" Kasancewar zuwa lokacin sun sani ba kowa Ummitan ke soyayya da shi ba face Ya Sayyadinsu na makaranta hakan yasa suka samu abin tsokanarta. Ashe wai dama yawan tashinta da yake yi ta biya musu karatu mai dalili ne. Ummita ta ɗan harareta. "Ke me ya hana ki ba Jafar daman zuwa gida? Ni ai mun kashe magana da shi, na ce ya bari sai nan da shekaru biyu ko ma ince ɗaya da rabi idan mun yi candy, tunda yanzu muna SS2." "Kai Ummita, shekara ɗaya da rabi fa? Gaskiya sun yi yawa ina laifin ma shekara ɗaya?" Faɗin Humaira dake tsaye tana maida kayanta sif. Raihana ta tari numfashinta da sauri ta ce. "Wai ke ce mai yiwa wata faɗan shekaru sun yi yawa? Allah ya ba Fadeel hakuri. Wallahi idan na tuna abinda kika yi masa sai na ji kamar na yi maki dukan tsiya." Ummita ma kwafa ta yi cikin kunar rai ta ce. "Bar ta kawai Raihana, nima ba ki ji raina ba. Kuma babu kunya ba tsoron Allah har faɗamana take yi ya hakura sai nan da shekara. Shi marar zuciyar ina ne da zai biyemaki ya yi zaman jiranki? Ai tana sane, kora da hali ne kawai ta yi mishi. Ba fata nake maki ba, amma wallahi kafin ki samu kamar Fadeel a maza sai dai tsananin rabo." Humaira ta taɓe baki gami da jan guntun tsaki. "Kanku ake ji, ni na faɗamaku ina so nayi auren ne? Auren ku yake burgewa ba ni ba. Sai me? Idan ba auren zan fasa rayuwata yanda ya kamata ne? Ya yi ma gangancin zaman jirana ya gani idan haƙansa zai cimma ruwa. Ya ƙare rayuwarsa a tuzuru." "Allah ya kiyaye wallahi, bakinki ya sari ɗanyen kashi. Fadeel ya wuce nan, kuma ina masa fatan alheri, ya samu haɗaɗɗiyar da ta fi ki komai ƴar kwalisa in sha Allahu." Cewar Raihana. Haka kawai sai ta ji zafi a ranta, ta ji tana son yin kukan da ta rasa dalili, kawai sai ta fashe da kukan ba tare da ta yi shawara da zuciyarta ba. Raihana ta dubi Ummita kafin su dube ta jiki a sanyaye. Tun tana kukan su na ganin kamar wasa su na rarrashinta, har dai suka ga kamar kukan ba na lafiya ba ne suka fita da sauri suka yiwa Mami magana. Kai abin tsoro Humaira duk iyakar rarrashin Mami ba ta yi shiru ba, hakanan harafi ɗaya ya kasa fita a bakinta. Mami ta juya garesu. "Meyafaru ta soma kukan?" Nan suka ba ta labarin komai, ta ja hannun Humaira kawai suka fice a ɗakin. Su Raihana za su biyo bayansu ta dakatar da su, can falo suka tsaya yayinda Mamin ta shige ɗaki da ita. Sun yi jugum kuma sai ga Mamin ta fito ta dube su ranta a ɓace. "Don me za ku dinga yi mata batun saurayin da ba ta so?! Ina gargadinku daga rana irin ta yau koda wasa kada wanda ya kara kuskuren ko ambaton sunansa balle ya yi mata zancensa. Fadeel ko? Daga yau sunan nan ya fice a bakinku." Suka ce toh, su ma abin ya tsorata su, sun kuma kara gaskata zancensu, Humaira na da aljanu musamman da suka ji Mami ta mike tana fadin wai ta samu bacci idan ta tashi komai zai wuce a ranta. Tabbas zarginsu ya tabbata gaskiya, aikuwa ga mamaki Humaira sumul ta tashi tamkar babu abin da ya faru. Yanda ba ta yi zancen ba hakanan su ma ba su kara tada shi ba. Ba ma kamar Raihana mai shegen tsoron aljanu, Ummita sai dariya take mata ciki-ciki ganin ko zama kusa da Humairar ta ɗan rage yi a ranar. A gefe guda kuma ta yi alƙawarin muddin ta je Bichi za ta yiwa mijin yar uwar mahaifiyarta magana akan lamarin Humaira, yana ba da hayaki da maganin jinnu, in sha Allahu za ta karɓo mata. *** *LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* 09034973645 Ibb ya mike tsaye yana safa da marwa kafin ya naushi bango a zuciye ya juya ya nuna Fadeel da yatsa. "Wai kai wace irin soyayya ce wannan da ba ta da mafaɗi? Wace irin soyayya ce mai neman kai ka ga halaka?" Murja wacce ke shirin kwankwasa ƙofar ɗakin don ta miƙa musu fruitsalad da ta haɗa ta tsaya cak jin abin da ke fitowa daga bakin Ibb, kirjinta har wani lugude ya ke yi. Fadeel kuwa jin an danganta soyayyarsa da sunan halaka ya ɗan ɗago idanu dakyar ya dubi Ibb sanadiyyar ciwon kai da ya wuni da shi ga azumi a baki. Ibb ya kara jaddada masa furucinsa. "Yes halaka mana, mutumin da ya amince da zaman jiran gawon shanu alhalin yana da damarmaki da yawa da ma ƴanmata masu ilimi da aji da ke rububin ya amince ya aure su ai kuwa ya jefa kansa a halaka tunda wacce ya ke zaman jiran kora da hali ta yi mishi. Fadeel wake up, ka runtse idanunka da kyau ka fahimci yarinyar nan kora da hali ta ke maka, ba soyayya ba ce. Ba ta sonka, a wautarta lokacin da ta ɗibarmaka zai sa ka ƙosa har ka gaji ka sauya sheƙa amma ba ta san yanda ka mace a kanta ba, ka shirya aikata komai! Toh ni abin ya ishe ni, zan je na sanar da Alhaji komai a je a nema maka aurenta." Fadeel dai ya yi shiru kawai yana cigaba da kurɓar ruwan shayi don  ba su jima da shan ruwa ba. Jin maganar tunkarar Alhaji ya sanya shi ɗago kai ya daure fuska. "Ban saka ba Malam, kar ka sake ka aikata wannan gangancin. Ba za ka taɓa fahimtar ya nake jin Humaira ba, ni dai na yarda ita ɗin mahaɗi ce ga rayuwata. Kai duk fa son da za ku yimin ba zai kai yanda ni nake son kaina ba, tun farkon ganina da ita nake addu'ar neman zaɓin Allah amma daidai da sakan guda ban ji ta sauya a raina ba. Ni dai na sani, ina mata so ba iyaka wanda nake da tabbacin ko ba ta sona, nawa son ya yi ƙarfi da isar da zai wadace mu gudanar da kyakkyawar rayuwar aure, na koyar da ita yanda za ta fara sona. Ballantana kuma ina ji a jikina tana kaunata." Tsaki Ibb ya ja ya koma ya zauna, tabbas ya ji daɗin dawowar ɗan uwansa wajensu, amma ya yi danasanin haɗuwar da suka yi da Humaira. A can ƙasan ransa tausayinsa ne lulluɓe, son maso wani akwai wahala. Don haka sai kawai ya ja bakinsa bai kara cewa uffan ba ya tsiyayi ruwa mai sanyi a kofi ya soma kurɓa. Daga can bakin ƙofa kuwa, Murja tuni tsayuwar ta gagareta, don haka ta ja ƙafafunta da suka yi mata nauyi ta bar wajen cikin sauri ba tare da ta miƙa musu abin da ta kawo ba. Dama na gulma ne ta kirkiri aikinsa don kanta kawai domin ta burge Fadeel, daga abin da ta ji yanzu ta fahimci babu abin da za ta yi ta burge shi tunda ya makance har haka a san wata banza wacce take da yaƙinin ba lallai ta fi ta kyawun zubin jiki ba. Kafin ta karasa falon Anti Amarya idanunta sun yi jage-jage da ruwan hawaye, ta gifta yaran ta shige ɗakin da kusan yanzun ya zama mallakinta bayan ta ajiye kwanon fruitsalad a falo gami da ba su umarnin shanyewa idan su na so. Kuka sosai ta fashe da shi, babu kalamin da yake mata baƙi kamar na jin da ta yi Fadeel na ambaton wata ɗiya mace da sunan so har yana ikrarin wai yana mata son da ya ishe su rayuwar aure koda ita ba ta sonsa. Ta nanata sunan a ƙasan zuciya, wato Humaira. Sai ta yi ƙwafa gami da tsaida kukanta, a fili ta ce. "Fadeel muddin ina numfashi sai na mallake ka a rayuwa koda ace hakan na nufin na ɓatar da Humaira a doron ƙasa." Wannan shi ne alƙawarin da ta ɗaukarwa kanta. *** A daren da aka yi shelar ganin wata kowa ya tashi da farin ciki da walwala. Humaira tuni sun sha kitso da ƙunshi abinsu, a wannan daren wuni ta yi a kicin tare da Ummita su na aiki ita kuwa Raihana tana can falo tana taimakawa Tasleem jera stones a atamfarta da tela bai samu damar yi ba. Shirin waina, sinasir da miyar taushe ake yi, tun safe suke aiki inda Humaira ta yi snacks har kala hudu, samosa, springrolls sai meatpie da cincin. Ko kusa ba ta huta ba, wata iriyar gajiya ce tattare da ita dukkan gaɓɓanta ciwo suke, kusan ita kadai da Ladidi ne karfin aikin don Ummita ba ta zauna ba, tana kula da yaran Anti Jannat, ko mintuna biyar ba ta yi a kicin din take kiranta ta sanya ta aiki. Dahuwar indomie, haɗa cornflakes, wankin kashi da sauransu. Ita kuwa Futuha ta tare can sashin Anna wajen Anti Jannat suna hira kamar ba gobe. Mami sai dai ta leƙo ta bita da sannu ta kuma ga yanayin tafiyar aikin sannan ta koma. A wannan daren ba ita ta bar kicin ba sai wuraren karfe ɗaya da mintoci. Da asuba dakyar ta tashi ta yi sallah ta faɗa kicin aikin suyan waina. Kasancewar Ladidi a gidan ta kwana bisa umarnin Mami ya sa ta kama mata. Sai dai duk da gajiyar dake tattare da ita, ranta fari sol, kowa ya san irin murna da farin ciki da bayi ke tsintar kansu ciki idan aka ce yau sallah. Wannan murnar ne ya ɗan ƙara mata kuzari, kafin dai zuwa karfe takwas sun yi sun kammala. A gaggauce ta sanya zuba komai kamar yanda Mami ta umarce ta, ta dauki na Abba za ta kai sai ga Ummita wacce ta tsaya shirya yaran Anti Jannat ta shigo tana mata sannu. Ta karɓa ta ƙarasa da shi. Ya yi daidai da fitowar Mami wacce ta ci adonta cikin doguwar rigar atamfa dinkin three-quarter da zani, peach colour ya sha adon stones. Ta yi kyau sosai abinka da farar fata. Humaira ta gaishe ta, fuska a sake Mamin ta amsa tana mata sannu da aiki. "Kin yi kyau sosai Mami." Ta yi ƴar dariya. "Nagode. Muje na ga aikin naki sai ki je ki shirya." Ta amsa da toh, suka koma kicin ta bubbuɗa tana jinjina kai. Cike da farin ciki ta dube ta. "Girki ya yi kyau Humaira, na kuma sani a baki ma zai fi haka. Sannu da aiki. Ladidi kun sha aiki, Allah ya bada lada." Ladidi dake tsaye tana ɗan tattara kwanuka ta amsa fuska a sake. Daga haka Mami ta juya itama ta bi bayanta. Dakinsu ta nufa, tun kafin ta karasa ta ji ƙamshi iri-iri na turare yana busowa. Hakan sam bai burgeta ba don ta sani Futuha ce da wannan aikin, yarinyar babu ruwanta da haramcin fesa turare mai ƙarfi ita kusan ma turaren maza ya fi burgeta akan masu sanyin ƙamshi marasa ƙarfi. Futuha ce kuwa tana tsaye an ci ado cikin atamfarta super mai kyau sky blue da ratsin fari da ruwan toka mara turuwa cikin wanda Alhaji ya kawomata, ta yafa blue mayafi mai kauri da girma kasancewar sallah za ta je yi sai takalminta mai shegen tsini shi kuma baƙi. Ko mahassadi ya sani ta yi kyau sosai, sai hotuna take ɗauka tana cuno baki. Ita kuwa Tasleem bata kai ga zuwa kayan ba tana tsaye gaban madubi tana gyara fuskarta, Allah ya taimaka an kwana da wutar nepa kuma an wayi gari da shi. A gajiye take likis, ta zauna gefen gado zaman jiran fitowar Raihana daga wanka, babu wanda ya ce mata ci kanki kamar yanda ita ɗin ma ba ta kula su ba. Tun tsawatarwar Abba ta samu suka sakarmata mara kaɗan, duk da a wasu lokutan ana bin ta da baƙar magana ko kuma kallon banza amma ko kallo ba su ishe ta ba. Su din ma ba kasafai yanzun suke shiga harkarta ba, sun fi maida hankali a hirar bikinsu. Kusan kullum sai an shiga instagram an ga tsarin bikin ƴan ƙarya ana cewa irinsa za a yi, ko kuma kayan amaryar sun yi kyau shi za su yi.      Har ta soma buga hamma bacci na son kwasarta sai ga Raihana ta fito, ta mike Raihana na mata sannu da aiki ta amsa ta ɗau zanin wankanta ta shige. Tana fitowa ta hau shiri, itama Ummita tuni ta yi wanka kafin ta ta je shirya yaran Anti Jannat don haka tana shigowa shirin ta hau yi. Atamfarsu na wurin Abba suka sanya. Sun yi kyau abinsu tsaf kowacce da jilbab wanda ya hau da kayanta. Humaira kalar maroon ne nata, ya fito da farar fatarta sosai ta yi kyau sai rama da fuskarta ta yi ba ma ita kadai ba, dukkansu babu wanda bai rame ba a watan azumi. Itama Ummita ta yi kyau tsaf cikin jan hijabinta mai haske, sai kuwa Raihana da nata brown. Sun yi kyau gaba ɗayansu. Fararen ƴaƴan Mami kamar wasu larabawa. Haka suka jera har su Muhsin da Waleed da suka sha adon babban riga farare tas zuwa farfajiyar gidan. Nan ma su Yassar ne ke faman ɗaukar hoto hannun kowannensu saƙale da darduma. Yaran Jannat ma har da su, mota uku suka yi har da motar Jannat wanda mijinta ya siyamata tun kafin kamawar watan azumi kafin su iso gari saboda zirga-zirga da yaransa. Kasancewar ta iya tuƙi ita ta shiga su Futuha abokan hirarta suka shige motarta sai kuwa yaranta. Ummita da Humaira su na tare da Mami sai motar Abba da matasan yaransa ke ciki. Haka suka jera zuwa masallacin idi kasancewar akwai tazara da gidansu. A mota Jannat suka yiwa Raihana caa akan yanda take shigewa harkar Humaira da Ummita, ita dai ta hademusu rai kawai ta ƙi cewa uffan. Bayan sun yi parking suka karasa da ƙafa.    Koda suka isa gida nan kuma aka tsaya yin hotuna a farfajiyar gidan, anan ne Raihana ta dinga yiwa Humaira hotuna kala-kala, ita kaɗai ta san me take niyyar yi. Ta kuma ranta sai ta aiwatar. Suna kammala cin abinci ana santin girkin Humaira, Abban da bai fiye kyauta ba shi ne har da ba Humaira dubu uku barka da sallah sakamakon girkin da ya yi mishi dadi sosai. Mami ta zuba na makwafta aka miƙa. Humaira ta ji dadi kwarai na yanda kowa ya ci sai ya yaba, hakanan abokanan su Yassar har da neman ƙari. Ita dai tana kammala ci ta yi daki ta sauya kaya zuwa doguwar riga marar nauyi ta shimfiɗe a gado ta hau ramuwar bacci. A sannan ne Raihana ta shigo ta dauki wayarta dake a gefenta ta fice zuwa falon. Ummita da ta kammala tattara falon ta dube ta. "Ke kuma me kike shirin yi da wayarta?" Ta yi murmushi ba tare da ta kalleta ba ta amsa. "Lambar masoyinta zan ɗauka na turamasa hotunanta. Ko ba komai zai rage zafin takunkumin da ta sanya mishi." "Um um Raihana, kada fa ta ji babu dadi." Raihana ta ɗan harareta. "To ke za ki faɗamata?" Taɓe baki Ummita ta yi gami da neman wuri ta zauna. "Me ya yimin zafi? Ke ce dai abin ji tunda bakinki ba ya shiru." Raihana dai ba ta ƙara tankawa ba, sai da ta tabbatar ta kwafi lambar Fadeel ta yi mishi sallama ta whatsapp gami da gabatar da kanta sannan ta mike ta maida wayar inda ta ɗaukota, baiwar Allah ba ta san ma meke faruwa a duniyar ba tsabar gajiya da baccin da ke kanta. *** Mintuna kusan sha biyar da shigowarsu gidan daga masallaci, Fadeel wanda ya sha gayu da babbar riga fara ƙal mai kwalliyar baƙi, ya shige sashinsa ya bar Alhaji anan falon saukar baƙi tare da makwafta an kai musu abinci iri-iri. A duniya idan akwai abin da ke damunsa to fa babbar riga, ya matsu ya cireta. Hakan yasa tun kan ya ƙarasa ɗakin ya cire hularsa ya riƙe a hannu, yana shiga kuwa ya fidda ya ɗora saman kujera. Zama ya yi sannan ya fiddo waya ya hau kan whatsapp. Anan ya tadda missedcalls din ƙanwarsa Hannatu, ya danna mata videocall kamar jira take ta ɗaga. Sun jima su na hira har ya gaisa da mijinta da kuma ɗanta ƙarami kafin daga bisani su yi sallama. Sauka ya ƙara yi ya kira wayar kakansa wanda ya haifi Mamansa, nan ma ya gaisa sosai da ƴan Kamaru har da wasu cikin ƴan uwansa. Bai ajiye wayar ba sai da ya kira Mahaifin Ibb da suke kira Daddy ya yi mishi barka da sallah ya ci sa'a su na tare da Maama, itama sun gaisa ya kuma jaddada musu zai shigo zuwa anjima ganin Maama na faɗin ba ta karɓar miƙe ya zo har gida.   Koda ya ajiye wayar sai ya ji wata irin nutsuwa ta ziyarce shi, wato dai babu abin da ya kai zumunci daɗi. Wayar ya ƙara janyowa, a hankali yake sarrafata har ya kai kan lambar da babu ranar da ba ya buɗowa. Kewar muryarta ya ke sosai, kullum cikin sauraron phone record dinsu yake amma ba su ƙosar da shi ba. So yake ya ji muryarta a zahiri, da kuma yana da dama ace ya ganta. "Why all this?" Ya furta a sanyaye yana kallon lambarta kamar wanda yake jiran jin amsa daga garesu. A hankali ya sauke ajiyar zuciya, damuwar da yake kwana da tashi cikinsa ita ce ta ke kokarin mamayeshi, idanunsa suka kaɗa. Kalmar kora da halin da Ibb yake faɗi ba ya so ya kasance gaskiya. Sai dai kuma ya sani, gaskiyar kenan, mai ɗaci. Amma ya zai yi? Ya kasa raba zuciyarsa da Humaira. Ya kuma kasa yi mata gangancin tura magabatansa kai tsaye wajen nata, ba ya son ta kalleshi a mugu mai son kai. Yana da yaƙini irin su Humaira idan suka faɗa tarkon so su ne masu riƙon alƙawari, zai wahala su ɓata ran masoyi da gangan. Idanunsa ya sauka saman alamar faɗowar saƙonnin whatsapp da ke nuni ta saman screen din. "Raihana ce ƙanwar Humaira." Wannan saƙon shi ya ɗauki hankalinsa daga baƙuwar lamba. Cikin sauri ya buɗo whatsapp din ya shiga. Aikuwa idanunsa suka yi kyakkyawan gani saman hotunan abar kaunarsa. Ya rasa me zai yi don farin ciki da kuma dadi, ya ja filo ya yi jifa da shi ya mike tsaye ya shafi sumar kansa yana bin hotunan da kallo yana murmushi. Wannan zinariyar kuma lu'u-lu'u a cikin mata ita Ibb ke cewa ya rabu da ita? Inaa! Ba mai yiwuwa ba ne, sai ko idan ƙaddararsa ce ta zo a haka. Ya kasa hakuri kawai ya dannawa Raihana kira. *** A lokacin tana tare da su Futuha a ɗakin Anna, ita kuwa Mami tana falo amsar gaisuwar ƴan barka da sallah yaran makwafta sai wasu a cikin ƴan uwan Abba da suka zo. Mikewa Raihana ta yi da sauri ganin sunan FH a saman screen ɗinta, ta san Fadeel ne. Ƴar barandar dake a wajen ta nufa ta tsaya gami da yin sallama. Ya amsa mata suka kara gaisawa kafin ya ɗora da fadin. "Kin bani kyakkyawan goron sallah ƙanwata, na kuma ji daɗi sosai. Ki turon acc no dinki nima na ba ki naki goron." Ta yi ƴar dariya. "Aa Yaya Fadeel, ni wallahi don Allah na maka. Ba abinda ni da Ummita ba mu sani ba game da sharuɗɗan da Humaira ta gindaya maka. Ni kuma sai na ga wannan hanyar ce kawai zan yi na ragemaka damuwa." Ya ji dadi kwarai, ya kuma tabbatar da cewa iyalan gidan abar sonsa su na da kirki kamar ita. Bai yi zaɓen tumun dare ba. "Nagode sosai Ƙanwata, ki gaidamin Ummita. And please ki turo idan kin bani matsayi ɗaya da Humaira." Ta amsa da toh sannan ta yi godiya. Koda ta tura ta yi mamakin ganin dubu ashirin matsayin barka da sallah, ya aiko da text ya ce su sha sweet. Ta kuwa hau washe baki da murna har su Futuha da Anti Jannat na neman ba'asi, sai kawai ta mike ta bar su tana dariyar jin su na cewa wai alert ta ji daga saurayinta. A dakinsu ta iske Ummita, karasawa ta yi a hankali ta ja hannunta gudun kar su tashi Humaira, Mami ta ce a rabu da ita ta huta. Sai da suka fito Ummita ta tambayeta. "Ke wai mene ne?" Ta nuna mata kuɗin da Fadeel ya turomata, Ummita ido waje don ba ta ma fahimci sunan ba ta dube ta. "Wa ya aikomaki wadannan kudaden?" Ta yi mata alama da yatsu cewa ta yi a hankali. Nan ta nunamata hotunan da ta aikawa Fadeel da kuma yanda suka yi a waya. Ummita duk sai ya ba ta tausayi. "Allah Sarki Fadeel, nikam yana burgeni wallahi. Humaira ta tsinci dami a akala take wasa da shi." Raihana ta yi ƙwafa. "Rabu da ita, in sha Allahu ba ta da miji sai shi. Itama ai tana sonsa gulma ce kawai." Girgiza kai Ummita ta yi. "Bari faɗin haka, kar ki manta jinnu babu abinda ba su sanyawa, Ya Sayyadi ya ce har raba mata da miji su na yi saboda sanyawa ɗaya ƙiyayya da kuma hana zaman lafiya." "Allah ya karemu da sharrinsu. Itama Allah ya yi mata magani." Ummita ta amsa da amin. *** Hajiya Kubra wacce suke kira da Maama, mahaifiya ga Ibrahim (Ibb) ta dubi Fadeel tana mai faɗaɗa murmushinta har ana ganin haƙorin makkanta mai sheƙi. "Ɗan Alhajinsa, ganinka sai an yanki tikiti." Fadeel ya shafi ƙeyarsa yana murmushin jin nauyi, yau gaba ɗayansa cikin nishaɗi ya ke ji, babu hoton dake yawo a kansa sai hoton Humaira da ya gani tana murmushin da wushiyarta ta bayyana zahiri. "Ina nan Maama, ai ko ba ku yanka ba ni fa ɗanku ne." Ta yi dariya aka ƙara gaisawa. Suka ɗam taɓa hira bayan an kawo mishi ruwa da lemu sai snacks ya ci. Ibb ba ya nan sun ɗan fita da Daddy. Maama ta gyara zama sosai babu alamun wasa a fuskarta ta ce. "Ɗana kamar yanda ka ce ni uwa ce gareka, ina son ba ka wata shawara kar kuma ka ce na maku katsalandan kai da abokinka." Duk da cewa tuni ya ɗago zancen, tunda ai tatsuniyar gizo ba ta wuce ta ƙoƙi sai ya tattaro dukkan hankali gareta ya ajiye kofin dake hannunsa. "Maama kin isa da mu ɗin ne, uwa kuma da ta isa, ai ɗa ba ya taɓa wuce faɗa daga gareta ba ballantana kuma nasiha ko shawara." Maama ta yi murmushi, hakika kalamansa sun burgeta. Ta jinjina kai. "Wannan hakayake Fadeel, maganar ba wata mai tsawo ba ce sai ta buri da mafarkan iyayenku. Mun yi hakuri mun zuba idanu, daga kai har ɗan uwanka kamar babu niyyar faranta mana. Kun fi kowa sanin bamu da burin sai na ganin kun fidda matar aure amma shiru kamar maye ya ci shirwa. Ba mata a garin ne?" Ta ƙarashe da ƴar dariya, shi ma murmushin ya yi mai dauke da damuwa. "Akwai Maama, ku yi hakuri, in sha Allah zamu yi. A taya mu neman zaɓin Allah. Mun fi kaunar farin cikinku sama da komai." "Shikenan, Allah ya yi maku zaɓi mafi alheri da albarka." Ya amsa da amin. Yana shirin tafiya sai ga Ibb ya shigo tare da Daddy. Shi ma fararen kayan ya sanya irin na amininsa. Nan kuma hira ta dawo sabuwa, Daddy ya hada su ya kara yi musu zancen aure. Ya jima a gidan kafin ya fito tafiya. Sai da suka karasa har bakin motarsa sannan Ibb ya dube shi. "Wai lafiya? Yau kamar wanda aka yi ma albishir da aljanna sai fara'a kake yi. Akwai labari ne?" Fadeel ya ƙara fadada murmushinsa. Hotunan Humaira ya nunamasa, da mamaki Ibb ya dube shi murna fal ciki. "Dagaske ne abin da nake gani? Ita da kanta ta turomaka? Ah lallai dole ka yi fara'a, ka ce tsayuwar darenka a azumi Allah ya karɓa." Fadeel ya ɗan basar ta hanyar sosa kara hanci. "No ba ita ce ta aikon ba, Raihana ce ƙanwarta." Nan fa Ibb murna ta koma ciki, ya ja guntun tsaki. "Allah ya yayemaka wannan makahon son Fadeel. Ka ture batun wannan yarinyar ka nemi matar aure ta gaske please. Ni dai dab nake da kawowa su Daddy matar aure." Fadeel ya bude mota yana murmushi yana kallom hanya har wasu ƴanmatan da suka zo giftawa suka maida mishi martani don a zatonsu da su yake. Ya kauda kai. "Shikenan, ka ga na huta sai ka yi auren ka samar mana yara da wuri, su Alhaji idan su na ganin jikokinsu hankalinsu zai kwanta ni kuma na cigaba da jiran abar ƙaunata." Ibb ya harareshi. "Ɗan iska, sai aka ce maka daga auren sai haihuwa ko?" Fadeel dai dariya ya yi. "Toh me ya yi saura idan har ba juya ba ne kai?" Shima Ibb dariyar ya yi. Anan yake faɗawa Fadeel wata ce Salma, likita ce kwararriya ta mata. Sun jima su na abotar da ta juye ta rikiɗe zuwa soyayya a yanzun. Ya yi shiru ne don ya gani ko abin zai ɗaure. "Masha Allah, Allah ya tabbatar mana da alheri." Cewar Fadeel. "Ameen, kai ma Allah ya kawomaka mace tagari da za ta mantar da kai Humaira." Ya yi murmushi ba tare da ya amsa ba ya shige mota abinsa. Ibb ya matsa shi kuma ya ja ya tafi. A ransa ya na auna addu'ar Ibb din, ba kuma ya jin mai tabbatuwa ce. *** Murja ce zaune gaban Malam wanda tun a waya ta zayyane mishi komai, batun Fadeel da kuma Humaira wacce ta ke buƙatar a shiga tsakaninsu a raba su gaba daya, ya kasance son da yake yiwa Humaira kacokam ya dawo kanta. Malamin bayan ya kammala aikin da duk abin da ya kamata ya mata umarnin ta zo. Tun da ta zauna take cike da fargaba na tunanin me zai fito a bakinsa, malamin yayarsu ce tana yawan zuwa karɓomata saƙo wurinsa, ba ta taɓa zuwa don aikin kanta ba sai a yanzun da soyayyar Fadeel ke neman haukata ta. "Akwai hatsari a kanki babba idan kika ce za ki raba waɗannan mutanen." Ji ta yi cikinta ya kaɗa, ranta idan ya yi dubu ya ɓaci har wani duhu take gani ya mamaye idanunta. "Akwai hatsari fa ka ce? Toh wallahi na shirya tunkararsa nidai, zan aikata ko mene ne duk tsananinsa don Fadeel ya zama mallakina." Malam ya yi shiru yana dubanta gami da auna irin rashin hankalinta. ®️Rufaida Umar.*LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* 09034973645 Assalamu alaikum, ina mika saqon taaziyyar rashin member makaranciyar Dukan Ruwa kuma masoyiyata ta don Allah, Aysha Salisu. Allah ya gafarta zunubanta. Ya sa aljanna makoma, ameen. **** Malamin ya jinjina kai. "Aa Murjanatu, kar ki zo gaba kiyi kuka da ni, jimawar da muka yi da da yar uwarki da irin alherin da nake samu a wajenta, ba zan yi abin da zai cutar da ke ba. Ki je nan da kwanaki uku ki kara nazari, idan kin shirya fuskantar kowane ƙalubale da zai biyo bayan aikin, sai ki dawo." Murja ta yi jim, a yanda ta ke jin Fadeel gani take babu wani abu da ba za ta iya jurewa ba. Can ta nisa ta ce. "Malam, idan har dai ba hauka ba ne ko wata nakasa naji na gani zan jure." Ya yi wani murmushi. "Kina da gaggawa Murjanatu, eh ba nakasa ba ne, amma rushe maganar wannan yarinya a zuciyar Fadeel ba zai amfaneki da komai ba sai halaka. Abin nufi, har abada kema ba lallai ki aureshi ba, idan kuwa aurenku ya tabbata toh fa har ki mutu ba zai kusanceki ba. Ke za ki kasance kare ma ya fiki daraja a rayuwarsa. Ki yi hakuri, ita gaskiya ɗaci gareta kuma kin fi kowa sanin ni Malam Tanimu ba na ɓoyewa mutum koda kuwa idan ya aikata abun zai haɗu da mummunan bala'i sai na sanarmaka idan ka ji ka gani a tafi a haka, sai a tafi. Kin yarda kin amince?" Ta ji zufa na karyomata, ita da take burin rayuwa mai kyau da inganci da shi? Take burin ta mallake shi su ji dadin tarayyar aure? Kai sam ba ta yi imani da faɗar Malamin nan ba duk kuwa da sanin da ta yi mishi ba na yau ba don haka kawai sai ta ce ya ba ta lokacin shawara, daga haka ta miƙe ta bar wajensa da nufin sauya sheƙa. Wannan Malamin ba abokin tafiya ba ne, ba zai mata yanda take so ba. *** Sun yi yawo sosai gidan ƴan uwan Abba, wannan kam ita da Ummita ne sai ko Raihana da ta jera da su. Si Futuha kuwa daga gidajen ƙawaye sai ko ƴan makarantarsu na sakandire da suka haɗa reunion aka ci aka sha. Sun je hawan sallah Humaira ta sha kallo, abin ya yi matukar burgeta. Ta dauki hotuna sosai a wayanta, ita kuwa Raihana babu kwalliyar Humairar da ba ta ɗaukarwa Fadeel ba, daidai da bidiyonta a wurin kallon hawa sadda take murmushi da haska bidiyon sarki ta ɗauka ta tura wa Fadeel. Sosai sallar ta yi mata dadi, ta kuma yaba da kalar wasannin da aka yi. *** Zaune take a falo tana ta kallon yanda a hankali ta soma samun mabiya a shafin Instagram, hakanan hatta a facebook da Raihana ta budemata ta sanya ta a shafukan tallace-tallace na sana'o'i nan ma ta samu abokantaka da mutane da dama, sai dai babu wanda suka taɓa hira a akwatin sirri (inbox). Ita kaɗai tana ta murmushi ganin yanda hotunan girke-girken da ta yi yake samun likes da kuma comment. Jannat ta shigo falon da rawar jikinta, dawowarta kenan daga gyaran gashi. Su Futuha sun fice shoprite sun kai yara, Ummita ta je albarkacin yaran Jannat da suka sa rigimar su sai an tafi da ita don ba karamin shaƙuwa suka yi ba. Humaira ta ɗago tana dubanta don har ta tsorata ta, sam ba ta tunanin ta yi sallama. Su na cikin sati na uku ga sallah, a yanda ta ji daga Ummita, bai fi kwanaki uku ya rage Jannat ta bar gidan ba wannan yasa take ta shirye-shirye. Kallo ɗaya Jannat din ta yi mata ba ta ko amsa sannu da zuwan da take mata ba ta yi gaba, har ta ɗan yi nisa ta dawo baya tana yatsine fuska. "Ke, ki dafamin abu marar nauyi yanzu." Humaira ta amsa da toh, daga haka ta watsa mata harara ta shige. Taɓe baki Humaira ta yi, ko kaɗan ta daina jin ciwon ƙiyayyar da suke mata, ta lura ba ƙasa suka kwasa ba. Jinin Anna ne dole su kwatanta halinta. Ban da ma rashin ta ido, ina uwar mace da zuwa gidan surukai ta tare ko tuna asalinta ba ta yi? Mami ce dai ta sha bamban da su. Tana wannan saƙe-saƙen zucin wayarta ta ɗauki ƙara. Ganin baƙuwar lamba ya sanya ta yin jim tana tunani, tana da tabbacin ba shi ba ne. Mutumin da gaba ɗaya ya sauya bai ko ƙara kiranta ba, ganin wayar na shirin katsewa ya sa ta ɗauka. Muryar mace ce, ta amsa sallamarta suka gaisa. "Ina magana da Humaira? Humaira Yusuf mai yin snacks?" Ai sai ta miƙe tsaye ta hau washe haƙora. Ta amsa cikin zaƙuwa. "Eh, ita ce." "Masha Allahu, ina bibiyarki a shafinki na instagram, na ga tallace-tallacenki. Ina son snacks ne, za'a iya samu nan da kwanaki hudu haka zuwa biyar?" Humaira ta ɗan yi tsallen murna sai ta ɗan toshe baki gudun kar dariyar farin ciki ya suɓuce mata, wannan kusan shi ne order din farko tun da suka soma talla. Nan ta tambayeta kalolin snacks din da take so, ta yi mata bayani, a karshe suka yi sallama da zummar Humaira ta lissafa adadin kuɗinta sannan ta turo acc number. Ai don murna tuni ta mance da batun wata Jannat, gudu-gudu ta nufi falon Mami tana kwala mata kira. Amma ina! Ba ta nan tana bangaren Anna, tsabar rufewar idanu kawai sai ta sa kai har cikin dakin Anna tana kwala kiran Mami. Su na zaune su na hira sai ganinta suka yi. Mamin ta nemi ba'asi nan ta hau sanar da ita yanda suka yi da mai order. Itama sai murna da hamdala. "Kai Alhamdulillah. Dole kiyi murna, maza muje ayi lissafin sai a turamata." Da murmushinta mai bayyana kyawunta da tsantsar kamanninta da Abba ta amsa da toh. Har ta juya za ta fice ta ji tsawar Anna. "Ke!" A firgice ta juyo kuwa, har ga Allah sai a sannan idanunta suka buɗe. Ta tuna inda ta faɗo da kuma kuskuren da ta yi na rashin sallama ballantana gaisuwa. Kawai sai ta durkushe ta gaida Annar, Jannat ta karasa ta ja kunnenta har sai da ta saki ƙara. "Don ubanki dayake kin raina mutane uwarmu sa'arki ce da har ki faɗo ɗakinta kamar na uwarki?! Ba aiki na sanyaki a kicin ba? Kema kuma Mami laifinki ne." Daga nan ta juya harshe zuwa buzanci ta cigaba da sababin faɗa, Anna itama tana taya ta. Daga yanda Mami ta yi shiru ta haɗe girar sama da ta ƙasa Humaira ta fahimci magana suke gasamata. Nan da nan jikinta ya yi sanyi, a gefe guda ga na gorin ɗakin uwa da aka yi mata, ba don darajar Mami dake a idanunta ba sai ta faɗamusu mai zafin da ba zasu ƙara mararin daɗa kwana ko ɗaya a gidan ba idan har su na da sauran kunya. "Humaira, tashi ki je, ki yi aikin da ta sanyaki kafin na zo." Muryar Mamin ta katse ta. Ta mike tana mai amsawa da toh gami da share kwallar da ta cika idanunta. Bayan fitarta Anna ta ce. "Maryama ban san irinki ba, ban san wa kike son ki burge ba. Wato har wani girki za ta fara na harkar kuɗi? Wannan naki salon uƙubar ce ko kuwa dai son yarinyar ne fiye da naki yaran ya rufemaki idanu kike son ta kere su a komai ta yi musu zarra? Idan bacci kike ki farka, kin nemawa yarinya har ya zama mai arziki, a kuma yanda naji zaƙin miyarta ina mai tabbatar maki watarana sai ta fi ki kuɗi. Tukunna ma, kuɗaɗen kina nufin ita za ki dinga damƙawa?" Mami ta yi shiru na ƴan sakanni har Anna ta ƙara tankawa yayinda Jannat kuwa ta ja tsaki don tana jin haushin yayarta sosai, tana abu tamkar a duniya su Humaira ta haifa ba su Futuha ba. Can dai Mamin ta yi magana. "Ta asusuna kuɗin za su shigo." Murmushi Anna ta yi mai tarin ma'ana kafin ta ce. "Na sanki Maryama, ni na haifeki. Kar ki zo mini da rainin hankali da wayo kinji ko? Wato ni ga sakara shi ne za ki rufe ni ruf, to ai koda ta asusunki kuɗaɗen suka shigo a yanda kike nunawa yarinyarnan kamar ki lashe ta, ke me iya yin hidimar ta ce ba naki ko yaranki ba. Kaiconki Maryama, lallai idan ba bi a hankali ba yarinyar nan watarana sai ta watsa maki borkono a idanu. Kina wasa da wuta." Janant ta kalli Mami, sai kuma ta girgiza kai. "Anna, zai fi kyau ki bar wahalar da bakinki a kan wannan saboda ɗiyarki ta yi nisan da ba ta jin kira. Ita mai miji, burinta ta nunawa duniya ta fi kaunar ɗa wani sama da nata yaran. Idan kin ji yanda yarannan ke ƙorafin nuna halin ko in kula da take yi musu sai ki rantse ba ita ce ta yi naƙudar su ba a bola ta tsinto su. Babu ma kamar su Yassar wadanda su ubansu bai sakarmusu sun ji dadin rayuwa irin na matasa sa'anninsu ba, su ba su sami wata kyakkyawar kulawa a wurin uwar ba. Ni na rasa irin wannan gidan da rayuwar cikinsa. Ba haka nake rayuwa a gidan nawa mijin ba, shi koyaushe burinsa ya wadata mu da abinda za mu huta ni da yaransa, amma tun da na rayu a gidannan har na yi aure, mijinta bana jin ya kashemin sama da dubu ɗari biyar a rayuwa." Mami ta miƙe tsaye tana duban Jannat, zuwa yanzu ranta idan ya yi dubu to ya ɓaci. "Ya isheki hakanan! Ke tsabar rashin kunya har kya kalli kwayar idanuna ki faɗan magana? A gidan dai da kika raina nan kika rayu sannan ko Yusuf bai kashe maki sama da kuɗaɗen ƙaryar da kika buga lissafinsu ba, ai kin ci kin sha daga jikinsa. Ke yanzu idan da kina can wannan dajin kina rayuwa, har kin isa ki ga shi mijin da kike tutiya da shi ki aura? Ni na isheki! Nan da kike ganina kar nake, na fi ku sanin inda ke mini ciwo. Ba damuwarki ba ce kuma balle ki sani, idan har ba za ki dauke idanu daga lamuran gidana ba, ki tattara ki..." "Maryama!" Tsawar da Annan ta bugamata ne yasa ta yin shiru tana fesar da huci mai zafi, ta kalli Anna sai kuma ta juya ta fice daga ɗakin. Jannat nan ta haukacewa Anna wai Mami ta yi musu gorin zama a gidan don haka su tattara su bar mata gidanta. Anna dai ta dinga lallaɓa Jannat, ta sani muddin ta bi cewarta ta bar gidan to fa komawa can wani ƙauyensu dake garin Agadez ya kamata, yanda ta fito ta ɗanɗani rayuwar daula koda ace bai kai yanda ta ke so ba, ta gwammace ta cigaba da rayuwa a nan. Ta sani babu ta yanda za'a yi shegiyar surukar zamani irin ta Jannat ta amince da zamanta a gidan ɗanta. Dakyar dai ta samu Jannat ta janye ƙudurinta, tsana da haushin Humaira ya ƙara ninkuwa a ƙasan ranta. *** Humaira kuwa sai ta nemi murnar da take yi na Oda ta rasa, jiki a saluɓe ta yi mata dahuwar dafadukan macaroni mai busasshen kifi. Ƙamshinsa ya karaɗe kicin ɗin da falo. Koda ta kammala ta haɗa komai a ƙaton faranti ta kai mata babu godiya ba kallon arziki, itama ba ta sa a ka ba kawai ta jya da zummar tafiya. "Ke zo nan!" Muryar Anna ta ji, ta runtse idanu kirjinta na dukan tara-tara cike da tunanin da wanne kuma Annar ta zo yanzu ta juya ta koma ta durkusa ba tare da ta kalleta ba. Ta soma magana a kausashe. "Ɗago ki kalleni nan, ni da kike gani dai na fi ƙarfinki. Mun ci dubu sai ceto, zuri'ar Mamman Ɗan Jika daidai nake da kowane bafillace mai taƙama da asiri. Har mu za a gayawa asiri? Tun wuri ina gargaɗinki ki fice a rayuwar ɗiyata, idan ma wani mugun ƙullin aka kawoki da shi don ki shiga tsakaninta da yaranta toh ahir ɗinku, ni dai na fi ƙarfinku balle kuma tsatsona. Ki kama kanki tun kafin na ɗau mummunan mataki a kanki. Ɗan girkin da kike taƙama kin iya ni mai iya juya lamarinki da shi ne, idan kuma kina da ja ki cigaba kar ki fasa. Asir dai ba za ki nunamana ba, mun saka Allah a gaba ne kawai shiyasa muka watsar. Amma muddin kika ce za ki cigaba da juya ɗiyata kamar waina da shiga tsakaninta da yaranta da ta haifa da cikinta ni nan zan nunamaki iyakarki." Tana kaiwanan ta juyar da kai tana girgiza ƙafa na bala'i. Humaira ta dubi Anna dakyau, an zo gaɓar da ba za ta jure ba sai ta ba ta amsa ko yaya ne. Ƙazafin sihiri ba za ta jure shi ba don haka ta soma magana da wani irin ƙunar rai. "Kiyi hakuri Anna, amma kalamanki laifi ne ko a wurin Ubangiji, kin yimin mummunan zato kin kuma yimin ƙazafi. Lallai Ubangiji zai yi mana hisabi a gobe ƙiyama. Na samu kyakkyawan tarbiyya a wurin Dada da Kawuna irin wanda nake da yaƙinin ko uwar da ta haife ni sai haka. Ban san boka ba balle mugun malamin da zan je ya yi min wani mugun aiki ba, asalima ban da a fina-finai da kuma labari ban taɓa karo da su ba. Wanda ya riƙi Allah, ai ba zai aikata abin da kuke yi ba. Kullum cikin zagi da aibata musulmi ɗan uwanku, ni Humaira babu wani mahaluƙi a duniyarnan da zan kai ya yimin aiki a kan wasu, kenan idan nayi hakan ma ban riƙi gaskiya ɗaya ba, ban yi imanin Allah zai iya amsamin addu'ata ba komai muninta komai kyawunta ba kenan. Ai Ubangiji ya wuce duk zatonku. Balle ma ban taɓa roƙo mai muni kan kowane ɗan uwana musulmi ba, kuma ba zan fara akan Mami ko yaranta ba. Tsakanina da Mami sai addu'a, ta yimin riƙon da ya sa nake jure dukkan wani abu da za ki yimin ke da jikokinki. Har abada kuma bisa darajar Mami ba zan taɓa daina ganin mutuncinki ba. Kiyi hakuri idan da abin da na faɗi mai zafi." Tana kaiwa nan tuni ruwan hawaye sun wamke fuskarta, a bisa tilas ta kalli idanun babbar da ba ta riƙe girma da tsufanta ba ta gasamata maganganu. Ita ta fi Anna jin ciwon haka, sai dai haka take, ba ta iya hakuri idan aka kai ta bango musamman idan abin ya kasance ya haɗu da baƙin ƙazafi. Juyawarta ya yi daidai da saukar igiyar chaja a gadon bayanta, Jannat ce wacce a farko ta yi ɗif don gani tayi tamkar a mafarki wai wata ƙaramar yarinya na gasawa uwarta maganganu, sai da ta motsa da zummar barin ɗakin sannan ta zabura ta janyo igiyar chazarta. Nan fa ta hau jibgar Humaira amma kamar ba mutum ake duka ba, ta ƙi tafiya ta kuma ƙi ƙwatar kanta. Zuciyarta tafarfasa take yi. Kallon Jannat take kawai tsakar idanu yayinda idanunta suka kaɗa sosai sai ruwan hawaye. Ganin da ta yi Humairar babu ko gezau sai kawai ta hau wanke ta da mari tana zaginta. Ta yi biyu, za ta ƙara ta riƙe hannunta gam, ba ta san ya aka yi ba, ba ta kuma jin za ta iya tunanin mai kyau da marar kyau a lokacin, kawai ta ji yatsun hannunta sun sauka saman fuskar Jannat da mugun ƙarfi ji kake tas!!! Ya yi daidai da faɗowar su Futuha ɗakin waɗanda dawowarsu kenan daga shoprite cike da nishadi. Ganin abinda ya faru ne ya sa Tasleem sakin ihu mai ƙara da ya ja hankalin Abba da Mami dake a sashin Abban, suka nufo da sauri Abba ya ɗan tsaya daga ƙofa yayinda Mami ta kutsa kai ɗakin. Alokacin rufewar idanun Humaira har ya kainta shaƙi wuyan Jannat ta dangana ta da bango, babu sautin kuka sai ruwan hawaye, Jannat ta raina kanta, ta ji ashe ba ta da ƙarfi don ji tayi kamar ba iyaka Humairar ba ce ta shaƙe ta ba. "Wayyo Allahna! Ku taimaka za ta kashemin yarinya!" Jin wannan furucin na Anna ya sa Abba danno kai cikin ɗakin. Tsawa ya dakawa Humaira ba ta ko kalleshi ba. Ya kuwa ƙarasa ya ɗauketa da wani marin sannan ya fincike hannunta. Mami kuwa mutuwar tsaye ta yi, ita kadai ta san me take ji a zuciyarta, wannan shi ne lokacin da take gudu, ta juya da sauri ta bar ɗakin. Su Futuha kuwa suka yi kan Antinsu suka rirriƙe suna kuka yayinda Anna ma kukan take har da biyu saboda ganin Abban. Shi kuwa rufe Humaira ya yi da duka sai da ya ga har ba ta motsi kafin ya karasa ga Jannat yana ba ta hakuri, Jannat kamar jira take kawai sai ta fashe da kuka sosai da fadin. "Wannan wane irin cin mutunci da zarafi ne? Da aurena da darajata da shekaru sa'ar ƙanwar ƙanwata ta shaƙi wuyana? Wannan rayuwar da me ya yi kama? Kiyi hakuri Humaira, watakila laifina ne da na zo gidannan. Na saba ganin girmamawa daga mahaifinki, hatta da marigayiya Anti Fati ba ta taɓa yimin koda kallon banza ba, amma yau ga ɗiyarta nan ta shaƙeni tana ƙoƙarin kai ni lahira. Aikuwa a yau zan bar maki gidanku." Ta ƙara fashewa da kuka, Abba ya ji kamar ya ƙara rufe Humaira da duka, wannan banzan halin a ina ta ɗaukoshi? Tabbas ba halin mahaifiyarta ba ce. "Nima yau zan bar gidanka Isuhu, tun zuwan yarinyarnan naga rashin kunya iri-iri da ban taɓa gani a wajen yan uwanta ba. Na yi kokarin janta a jiki da nunamata kauna, sai dai ban sani ba ko tana ji a ranta ni ban kai ta girmamani ba saboda ina zaune ina cin arzikin gidan mahaifinta ba, tunda abin ya kai ga haka in sha Allahu zan tattara na koma can Agadez, kiyi hakuri Humaira, wallahi ni ba muguwa ba ce. Tsakanina da duk abin da ya fito daga jikin Isuhu babu komai sai girmamawa." Dakyar Abba yake magana saboda ɓacin rai ga nauyin Anna da ya dinga ji, wai yau diyar cikinsa ce ke ci wa tsohuwar mutunci ta hanyar dukan ɗiyarta a gabanta. "Ki yi hakuri don Allah Anna, wannan gidana ne ba na Humaira ba. Mallakina ne, kamar yanda uwata mahaifiya da ace tana raye take da iko kai karfi a kaina da gidannan, haka nake ganinki don haka ina roƙonki kiyi hakuri ki janye ƙudurinki. In sha Allahu daga yau irin haka ko da wasa ba zai ƙara afkuwa ba. Ni zan ɗau mataki kwakkwara a kanta." Ya ƙarashe yana duban Humaira da sai lokacin take sheshsheƙar kuka, itama shi take kallo, ta sunkuyar da kai. "Don ubanki ba za ki buɗi baki ki ba su hakuri ba?!" Ya faɗi a tsawace, hakan ya yiwa ran su Tasleem dadi, yau dai ga wacce suke ganin ta fi su a wurin Abba tana ɗanɗanar kudarta. Abin ya zo musu a daidai. Ita kuwa mikewa ta yi dakyar ta durkusa sosai, hakuri ta shiga ba su har Jannat din. Dakyar suka ce ya wuce saboda ganin idanun Abba. "Muje." Ba musu ta mike jikinta duk ya yi tsami ta bi bayan Abban zuwa falonsa yanda ya buƙata. *** Fadeel da murmushi ya ɗagawa yayartasu hannu alamar jinjina. Yayar Ibb, Anti Ruƙayya wacce ke aure a Kano, sun saba sosai da Fadeel din tun kafin ma ta yi aure. Ibb ya dube shi. "Wai ni ban gane ba, toh idan odar ta sauka wa zai karɓa?" Fadeel ya yi murmushi karo na biyu. "Nan gidan Antinmu za'a kawo mana, ni kuma sai na zo na karɓi rabona." Hajiya Ruƙayya ta yi dariya. "Amma dai wannan ina zaton ita ce zaɓin ƙanin nawa ko?" Ya kasa magana sai shafar sumar kai, Ibb ya taɓe baki. "Ita ce dai yake yiwa son mutuwa ba ta san da zamansa ba." Fadeel ya harareshi shi kam dauke kai ya yi ya cigaba da ba Ruƙayya labarin komai. Sosai ta ji ya ba ta tausayi. "Allah Sarki, yanzu kai zaman jiranta za ka yi kuma?" "Um." Shi ne kawai abin da yace yana hararar Ibb da ya kasa rufamasa asiri. Ibb shima ya rama sannan ya ce. "Ai wai haka yake nufi, nidai ban san irin wannan abu ba, ace mutum ya kasa hakura da son wanda ba ka gabansa? Kinsan Allah, mutumin nan akwai mata da yawa da suke kawo mishi hari, na ce ya runtse ido ya zaɓa ya darje amma ina. Wai ya hakura da auren har sai Humaira ta yi koda ba shi ta aura ba sannan zai yi nashi." Rukayya ta yi salati. "Fadeel kana cikin hayyacinka kuwa? Wannan wane irin so ne?" Nan da nan fuskarsa ta sauya. "Nawa son da haka ya zo. A sanya ni a addu'a kawai Anti." Ta ɗan yi jim tana kallonsa. Sai kuma ta numfasa. "Shikenan, Allah ya zaɓa abinda ya fi alheri. Zan so naga wannan yarinyar da ta sace zuciyarka har haka." Ba musu ya fiddo waya ya buɗe hotunan Humaira wanda hatta a saman screen dinsa ita ce ya miƙa mata. Ta kalla sosai ta ce. "Babu ƙarya Humaira kam ta haɗu. Daga kuma yanayin fuskarta ka san za ta yi haƙuri." Yabon da ta yi sai ya karawa Fadeel farin ciki, a duniya ya tsani wanda zai kushe abar sonsa. Ganin har Ruƙayya ta yaba sai hankalinsa ya kwanta. Sun jima suna hirar lamarin Humaira kafin a karshe su yi sallama bayan Fadeel ya ce mata zai dawo idan an kawo odar snacks ya karɓa. *** Jannat ce tsaye tana kallon hanyar waje, har lokacin zafafan hawaye take fitarwa na baƙin cikin abinda Humaira ta aikata gareta. Fuskarta ya yi jazur, ta juyo ta kalli Anna wacce ta yi shiru tana kallonta, a duniya Anna ba ta son damuwar yaranta. "Anna, na yi alƙawari sai na ga bayan Humaira da duk abin da take taƙama da shi. Ta yimin cin fuskar da ban taɓa tsammata ba, ni zan nunamata iyakarta koda kuwa zan yi yawo tsirara." A firgice Anna ke duban ɗiyarta, ta san halin kayanta, muddin ta furta abu, komai nisan lokacin da za a ɗauka sai ta aiwatar. Wani lokacin ma, sai ta tabbatar da shafewar abin a kwakwalwarka kwatsam sai dai ka ga sakamako a aikace. Don haka ta sani ko mene Jannat za ta aikata ba ƙarami ba ne duba da yanda ta saki fuska lokaci guda har da dariya. A karshe ma hatta da abincin da Humairar ta kawo sai da ta ɗiba ta yi zaman ci tana santi. Ita dai Annar ba ta ce mata komai ba, ta fi kowa sanin baƙar zuciya irin na ɗiyarta.*LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* 09034973645 Kanta na ƙasa, fiye da mintuna uku shi bai ce mata uffan ba kamar yanda ita ɗin ma ba ta buɗi baki ta ce komai ba face kukan da take yi ƙasa-ƙasa. Can dai Abba ya sauke ajiyar zuciya ya soma magana a kausashe. "Kin bani kunya da mamaki Mamana, ban yi zaton hali na rashin kunya da ɗa'a daga gareki ba. Me ya hau kanki har haka? Meke yawo a kwakwalwarki kika aikata abin da yau ace mahaifiyarki na raye za ta yi bakin ciki?" Humaira ta ji ƙarfin kukanta ya ƙaru, kewar mahaifiyarta mai yawa ta ji, ta sani ta aikata ba daidai ba amma ba ta jin Mahaifiyarta za ta kasa fahimtarta koda kuwa ace ta nunamata kuskurenta. Ta danne abin da ke taso mata dakyar ta iya magana. "Nayi laifi Abba, ka yi hakuri ka yafemin." Ya kuramata idanu duk sai ta ba shi tausayi kuma, sai dai hakan ba zai sa ya fasa nunamata kuskurenta ba. "Shikenan, amma ki tabbatar kin samu uwarki kin ba ta hakuri. Matar da take ƙimanta ki, ai yau ko wani mugun bautar mahaifiyarta da ƴar uwarta ke nunamaki ai sa ci albarkacinta ballantana ma babu ɗaya. Amma ki rasa da me za ki sakamata sai da cin mutuncin yan uwanta? Wannan ba daidai ba ne Humaira, Maryama ta wuce nan a wajenki idan kina da tunani. Burinta duk a kanki ya ƙare, kar ki so ki ji yadda koyaushe ba ta da magana sai naki, kullum cikin yabonki take da burin ki zama hamshaƙiyar ƴar kasuwa mai siyar da abinci irin wanda ko Otel sai haka. Ba ina faɗamaki ba ne don wani abu  a face sai na son ki fahimci irin girman da ta ba ki. Daidai da batun bikin yarannan idan aka ɗauko, sai ta ce ita dai burinta ta ga auren ƴan ukunta (Ummita, Raihana da Humaira), su ne ƴaƴanta. Toh kiyi takatsantsan, ki kuma kara martaba wannan girma da soyayyar da take nunamaki. Na san ke ɗin mai jin magana ce kuma ba na shakku akan tarbiyyar Dada, sai dai ina roƙonki kar ki sake na ƙara jin makamancin wannan daga gareki. Kin ji ko?" A sannan kukanta ya tsaya, sai Mami dake yawo a kanta wadda Abban ya kara sa ta ji kaunarta ta cika zuciyarta ga wani irin nauyi da kunya da ta ji. Shakka babu ta kai maƙurar da har ta kasa danne a zuciyarta ta aikata abinda zai sosa ran Mamin da ma Raihana da Ƙasim wanda a yanzun suke ɗan gaisawa sama-sama. "Na ji Abba, ina neman gafararka, zan samu Mami na ba ta hakuri. Na kuna yi alkawarin ba zan kara ba" Murmushi Abban ya yi. "Masha Allahu, ko ke fa. Maza tashi ki je wajen Mamin taki." Itama ɗan murmushin ta yi kafin ta miƙe ta bar falon. Kai tsaye ɗakin Mami ta nufa, sallama ta yi aka amsa sannan ta faɗa. Mami dake zaune gefen gado ta yi shiru ta ɗago ta dube ta sai kuma ta sunkuyar da kai. Gaban Humaira ya faɗi, tabbas Mami kuka ta yi, idanunta sun tasa sun kumbura. Sai ta ji nata hawaye sun dawo sabbi, ta durkusa gami da ɗan dafa gefen gadon. Dakyar ta iya tattaro jarumta ta ce. "Ma..Mami nayi kuskure, nayi babban laifi. Ki yafemin, ki yi hakuri. Maganganun ne suka yimin nauyi, zuciya ta kwasheni na aikata haka." Sai ta kasa kara wani abin a kai, ta yi shiru. Mami ta kalleta ta ɗan yi wani murmushi mai kama da yaƙe. "Tabbas kin aikata babban laifi Humaira, kar ki damu, abinda ya faru ya riga da ya afku. Ni na sani, matsalar ni za ta shafa yanzu. Uwa ce ya zama wajibi ga duk mai neman dacewa da rahmar Allah ya bi ta sau da ƙafa, ba zan iya sauya tsanarki a zuciyarta ba kamar yanda ba zan iya jure ƙiyayyar da ake nunawa jinin Fatima ba don a duniya da ace za'a samu abokiyar zama ta gari irin mahaifiyarki, shakka babu da an zauna lafiya. Ƴar uwata kuwa, ni da ita mu biyu kaɗai Allah ya mallakawa Anna, zan iya cewa ƙauna da soyayyar da Anna ke yiwa Jannat ya ninka nawa son a wurinta. Da ace tana da damar zama tare da ita, da tuni yanzu ba ta tare da ni sai ita. Hakuri nake yi ina takatsantsan da abin da zai haɗani faɗa da Jannat sabida na sani ɓacin ran Anna kawai zan fuskanta. A wasu lokutan har nakan yi tunanin Anna ba ta sona kwata-kwata, sai dai son da naga tana yiwa jikokinta ya shafe zargina. A hankali kuma na ke gudun zuciyarta, amma faruwar wannan lamarin, Anna ta yimin maganganu masu zafi wanda ba sani bakinta halaka ce gareni. Har cewa ta yi ba zan gama da duniya lafiya ba. Wannan shi ne dalilin kukana. Na san kema mutum ce mai zuciya a kirji, yau da gobe ana maka abu wataran dama dole a kai ka maƙura. Ina da yaƙinin hakan ce ta kasance yau, amma ina mai baki hakuri a madadinsu." Humaira wacce ta gama narkewa sosai a tausayin Mami, ta yi saurin girgiza kai ta riƙo hannuwanta, cikin muryar kuka ta ce. "Mami ki daina faɗin haka. In sha Allahu bakin Anna ba zai kama ki ba saboda mu ma shaida ne akan iyakar biyayyar da kike mata, ni nayi laifi Mami, ni ce mai bada hakuri ba ke ba. Na kuma yi maki alkawarin jure dukkan wani abu daga Anna da Anti Jannat albarkacinki. In sha Allahu hakan ba za ta sake afkuwa ba. Ki yafemin, ina jin kunyarki." Murmushi Mamin ta yi. "Kar ki damu, ya wuce. Share hawayenki, kukan ya isa. Allah ya sa mu dace." Humaira ta share fuska bisa umarnin Mamin tana mai amsawa da amin. Itama Mamin ta sauya darasin da yin batun odar da aka ba Humairar. Ita sai a sannan ma ta tuna da wata oda, nan fa ta kara yiwa Mami bayanin matar da ta kirata. "Toh kinga kuwa zama bai ganki ba, anjima ki zo muyi lissafin komai, idan ya so sai mu ga nawa ya kama sai a sanar da ita ko?" Zuciyar Humaira tas ta gyaɗa kai tana murmushi. Daga nan ta miƙe ta fita, Mami ta bita da kallo har ta fice.   Raihana ta fahimci Humaira sai dai ta ɗan nuna rashin jin dadin marin Anti Jannat a fili, ta dai ɗan basar da Humaira na lokaci sai kuma aka shirya suka ɗinke. Su Futuha kuwa ta rasa  me ya hana su yi mata maganar sai dai kallon banza kawai da suke watsa mata a duk sadda aka yi katari suka haɗa ido. Ummita dama ba ta da matsala, wata iriyar yarinya ce mai sanyi da hakuri, ta nunawa Humaira kawai bata kyauta ba da har ta bari zuciya ta kwashe ta suka kasa cin albarkacin Mami. Koda ta fadi haka da toh kawai ta bita, ita kanta ta sani Ummita ta juri abubuwa da yawa wanda ko rabinsa ba za ta jure ba. Ta taso tun bata san mene ne ma'anar hankali ba, ta rayu cikin duka da zagin Jannat, ga Anna a gefe wacce a baya Ummitan ke bala'in tsoro kamar mutuwa. A wurin Mamin kaɗai take samun sa'ida, su Yassar ba su wani damu da zamanta ba tunda tun kafin ta gama mallakar hankalin kanta take basu girma. Komai suka ce ta yi ba ta ƙi, koda kuwa ya fi ƙarfinta haka za ka jagula. Ummita ta ci wahala ta kuma yi hakuri ta jajirce, wannan ne ya sa har gobe ƴan uwan Mamanta na Bichi ba su taɓa kaunar zamanta a gidan ba. ***   Mami da Humaira sun lissafa komai yadda ya kamata, hatta da ribar sai da suka fitar sannan ta tura acc number din Mamin ga Hajiya Rukayya tunda ita ɗin ba ta da account kamar yanda Mamin ta ce. Aikuwa ko mintuna biyar ba'a yi ba sai ga shi ta aiko kudin. Wannan abu ya yi musu dadi, washegari kuwa da wuri ta fice siyayya ita ɗaya, sauran sun tafi makaranta.   Koda ta dawo da kaya niƙi-niƙi ga uban rana a garin haka ɗan sahu ya dinga tayata sauke ledoji. Ta kinkima zuwa ciki. A falo ta yi karo da Jannat za ta fita tare da yaranta, dama ta ga an wanke motarta tas yana sheƙi, tun faruwar lamarin sai a ranar suka haɗu, ta gaida ta amma ko kallon arziki ba ta samu ba sai giftawa da ta yi ta fice yaranta na biye da ita. Humaira ta yi mamaki don ta yi tsammanin da duka za ta rufe ta ma duk ranar da suka yi karo. Ba ta wani tsawaita tunanin ba ta maida hankali ga kayanta. Mami ta fito ta dinga yabon siyayyar. Bayan ta watsa ruwa ta sauya kaya zuwa tshirt da zani sannan ta fito zaman aiki. Sai wani nishaɗi take yi, ita da Ladidi ne suka soma, bayan dawowar su Ummita, ita ma ta shiga su ke yi tare.   Aikin da aka ba Humaira kwanaki biyar sau gashinan a kwanaki uku an kammala komai an haɗa. Hajiya Rukayya ta sha mamaki da ta tsinci wayar Humaira cewa an gama don babu laifi da ɗan yawa snacks din. Ta yi godiya ta kuma nemi kwatancen gidan acewarta za ta turo direbanta a karɓa, nan Ummita ta karɓi waya ta kwatanta mata. Awanni bai fi uku ba sai ga direban ya karɓa ya tafi. Humaira ta dawo ciki bakinta ya ƙi rufuwa tsabar murna. Futuha ganin yanda take washe haƙora yasa ta jan tsaki.   "Sana'a ba ilimi shirme kenan, mu dai mun yi gaba mun bar mutum, hakanan zamu kammala karatu mu zama manyan ma'aikata muna daga sama  kujera muna juya kowa. Ai Tasleem nan gaba wasu na da kallo." Tasleem ta tuntsire da dariya. Humaira kuwa hijabinta take ninkewa da ta sanya ta fita waje ba tare da ta ce musu uffan ba, a yanda take jin zuciyarta cike da walwala ba ta jin cewa za ta biye musu su ɓata mata rai a banza. Raihana ce ta yi caraf ta sanya musu baki kuwa. "Tab, ai  wallahi yanzu a zamanin nan dai babu abin alfahari kamar sana'a, ita fa mace mai sana'a ta huce takaici. Ba ruwanta da jiran sai an bata ko kuma an yi mata, kawai gani za'a yi a jikinta tana fitowa ɗas abinta. Muna nan daku in sha Allahu Humaira sai ta zama abin kwatance, wacce ko mai Masters ba zai nunamata arziki ba. A wannan lokacin kuɗi kawai, ilimi ba a taɓa yin latti da nemansa, ballantana ma me zai damu mutumin da yake neman ilimin Muhammadiyya. Ai shi ne maƙurar ilimi, sauran duka bogi ne." Jin haka ai sai Futuha ta harzuƙo ta kai wa Raihana bugu, Raihana  ta kauce. "Shegiya kai! Na sa da ke? Ko kin ji na ambaci sunan wata? Da ke nake magana ko Tasleem, iskanci kawai. Ina magana kina sanyamin baki duka zan maki a gidannan. Kin wani raina mu sai kace sa'o'inki. Kema watarana idan ba mu yi dagaske ba shaƙe mu za ki yi tunda ai zama da maɗaukin kanwa shi ke kawo farin kai." Ta karashe tana  watsawa Humaira wani banzan kallo ita kuwa ta kauda kai tana murmushi. Aikin banza, idan rashin kunya ne na nawa kuma suna gwada yiwa har Mamin balle a junansu, babu kamar Futuha da yanzun kanta ke bala'in rawa ana lallaɓa ta, hatta da Mami kamar ma tsoron sanya Futuhar aiki take yi a yanda ta lura, ba ta sani ba ko don Alhajinta mai hidima ne ko kuwa dai kawai saboda ta kusa aure ne. Tasleem dama ba koyaushe take wuni a gidan ba, saboda zuwa asibiti. Ba ta kara bi ta kace-nace da suke yi da Raihana ba ta ɗauki takarda da bironta ta koma wurin Ummita wacce itama a yanzu ke kokarin koyamata wasu kalaman na boko irin na yau da kullum da take ji ana ɗan faɗi. Sosai kanta yana ɗauka. *** Ya lumshe idanu yana taunar samosa,  har ya kammala bai iya ya buɗe ba, sai can ya buɗe gami da kai hannu zai ƙara, caraf Ibb ya riƙe tsintsiyar hannun yana dariya. "Wai kai na tambayeka, ni da na zo wurinka, ni ka kawowa na ci ko kuwa dai kanka? Tun dazu ka kawomin abu amma ka zage sai ci kake, oh don ban ce a bani nawa kason ba tunda dai a gabana aka ƙulla kasuwancin?" Fadeel ya harareshi. "Ban da wanda Anti ta cemin ka ci a can? Wannan kuma ni da kai na kawo wa, idan za ka ci ka ci, ka biyemin kaf zan tashi da shi." Ibb ya saki hannunsa yana murmushin wannan irin kauna. Shi kuwa bai ko kalleshi ba ya cigaba da kai girkin Humaira bakinsa. Can a gajiye ya dubi Ibb. "Yarinyarnan tana son kashe ni da raina." Ya kalle shi da kyau kawai ya ji ya ba shi tausayi. A sanyaye yace. "Meyasa za ka yarda da hukuncinta? Fadeel ka wartsake daga baccin da kake, sorry to say, amma yarinyarnan ba ta sonka. Idan kuma ba za ka hakura ka cire ta a zuciya ba, toh ka yarda mu samu su Alhaji a je nema maka aurenta." Fadeel ya girgiza kai yana jin ciwo a kirjinsa idan ya tuna wai Humaira ba ta sonsa. "No, ba zan taɓa yi mata dole ba, amma zan ɗaukar maka alƙawari ɗaya." "Mene ne shi?" Ibb ya faɗi cike da zaƙuwa. "Muddin lokacin da ta ban sun cika, zan sanar da Alhaji a neman aurenta. Idan kuma ba ta amince da ni ba, zan haƙura da ita saboda ta samu nutsuwar zuci." Ibb ya sauke ajiyar zuciya, shi fa sam ba haka ya so ji ba. So ya yi aminin ya furta kalmar rabuwa wanda ya sani sai dai ya yaudari kansa, ba mai yiwuwa ba ne. Yana kuma ji a ransa, muddin Fadeel ya yi dakon shekara, toh shakka babu ba abinda zai sa ya iya hakuri da rashin Humaira. Amma sai ya bar komai a ransa. "Shikenan, Allah ya yi maka zaɓi nagari." "Ameen." Ya amsa shi ma. "Ba za ka ci ba ne?" Cewar Fadeel wanda zuwa lokacin cikinsa ya ƙoshi amma bakinsa na son ɗanɗanon don haka ya haƙura ya ɗau gorar ruwa. Harararsa Ibb ya yi. "Oh, bayan ka cinye kenan ko?" Murmushi Fadeel ya yi ya cigaba da kora ruwa a cikinsa ba tare da ya tanka ba. *** BAYAN WATANNI BIYAR...*LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA. KAR KI MANTA BAYAN NAN AKWAI CAN, ALLAH YA SA MU DACE AMEEN.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* 09034973645 Gidan Alhaji Yusuf wanda aka fi sani da Maiagogo sun wayi gari ranar alhamis da shirye-shiryen bikin yaransa biyu, Futuhatul-Khair Yusuf da kuma Tasleem Yusuf wanda kwanaki uku kawai ya rage a fara. An samu sauye-sauye da dama, na farin cikin ya fi kowanne yawa ga Humaira da duk ma wanda ke tare da ita. A wannan watannin ta samu alheri mai yawa daga sana'arta. Babbar customer dinta ita ce Hajiya Rukayya wacce ta hanyarta kaɗai ma ta samu oda na biki da party har ya zamana tana gwada na abinci bayan snacks sai dai gaba ɗaya sau biyu ta gwada abincin taro ba laifi kuma masu shi sun yaba hakanan Hajiya Rukayya ta ji dadi da ba ta ba su kunya ba. Duk abin nan ba su taɓa ganin juna da ita ba sai dai waya. Mami ta sa an buga leda da stickers mai tambarin DEELSHA'S DELICACIES. Suna na musamman da Raihana da Ummita suka ba Humaira a sadda Mamin ta ce ta yi tunanin sunan da za'a sanya a ledar. Sunan ya yiwa Humaira daɗi ko kadan kuma ba ta tambayesu ma'anarsa ba. Mamin ma ta ji dadin sunan, ganin kalmar turancin ya sa ta tambayar wacce ta sa, nan Humaira ta sanar da ita su Ummita ne. Daga haka ba ta kara cewa komai a kai ba.   A yau da ya rage kwanaki uku bikin yan matan Mamin, gidan nasu ya soma karɓar baƙi ƴan uwan Mami daga Agadez sai ko ƙawayen Futuha waɗanda suka zo daga nesa kasancewarta mai jama'a fiye da Tasleem. Yan uwan Abba kuwa ba wanda ya zo gidan da zummar kwana. Mubarak shima ya zo gari, sai kuwa Anti Jannat. Ya kasance a wannan lokacin gidan ba ya rabo da jama'a, Mami ta sa Ladidi kawo mataimaka a aiki har su uku saboda yanayin cikar gidan da zummar bayan biki za ta sallame su.   Anko har kala biyar aka fitar, na ƙawaye daban wanda zasu sanya ranar kamu da na daurin aure da yini sai ko na ranar dinnerparty. Na manya su ma kala biyu, na fita kamu sai na ranar daurin aure. Humaira, Raihana da Ummita daban aka fitar musu da na sisters wanda zasu saka na yini sai kuma na dinnerparty da Mami ta yiwa su Futuha jan ido ta karɓar musu katinsu ta riƙe a wajenta don a farko sun nuna su ko kusa ba su kaunar su halarci dinner din.    Amare sun sha gyara ba na wasa ba daga mai gyaran jiki na musamman da Mami ta samar musu suke sintirin zuwa. Hajiya Lubna ita da kanta ta ɗauki nauyin gyara su, gyara irin na mata. Ta kashe kuɗaɗe masu kauri kuwa wanda hakan ya burge aminiyarta kwarai ta yaba.  Ba ma ita ɗaya ba, ƙawayen Mami da dama manyan mata masu kudi sun ba da gudunmuwa mai yawa na kudi, kanta ya fasu sosai ta kuna ga fa'idar mu'amala da masu hannu da shuni. Su Raihana sun karɓi dinkunansu a hannu, sun yo ƙunshi da kitso abinsu sun fito fes.    A na washegari kamu ne su na zaune suna hira a daki tare da wasu yan uwan su Raihana sa'anninsu da suka zo daga Nijar, Tasleem ta shigo. Fatarta har wani ɗaukar ido yake, ba ta da ƙiba irin na Futuha ita nata jikin daidai misali ne, duban Humaira ta yi fuska ba fara'a. "Ke Humaira, ke da Ummita ku zo na aike ku." Humaira ta ji ciwon ke din da tayi kiranta da shi, ita kuwa Ummita ko a jikinta ta miƙe tana murmushi. Hakanan halittarta yake, tana da yawan murmushi, abinda zai sanya hawayenta zuba kuwa, toh fa ba ƙaramin abu ba ne kamar dai akan Humaira ko kuwa wani abun daban. Kamar ba za ta miƙe ba sai kuma ta yi tunanin ba komai ta yi tunda dai aure ma za su yi su bar gidan sai ziyara don haka ta taushi zuciyarta ta miƙe itama. Saƙo ta ba su a leda na ankon Dinner su je su kai can asibitin Malam wajen ƙawayenta kuma abokan karatunta da suka samu dakyar don har ta ƙare. Ta miƙawa Ummita dubu su yi kuɗin mota sai kuma lambar wayar ɗaya daga ciki, Sadiya, sun gane ta, takan rako Tasleem din gida wasu lokutan don ta dauki wani abun ko kuma ta zo takanas ziyara.    Bayan sun fito waje Humaira ta dubi sararin samaniya yanda garin ya haɗu da hadari ana cida, lokacin uku da mintoci, ta ja guntun tsakin takaici.   "Kinsan Allah, sa'ar da ta ci kawai na ganin wannan shi ne aike kusan na karshe da za ta yi mana kafin ta bar gidannan shiyasa kawai zan je, amma ban da haka wannan ke ɗin da ta ce wallahi da babu inda zan je matukar ba Mami ce ta sa baki ba." Ummita dake kokarin cusa ƙaramar lema a jaka ta ɗago tana murmushi. "Humaira ko rigima, rabu da ita lokaci ne ai wataran sai labari fa. Yanzu kalli, ina Anti Jannat? Ba ta yi aure ba sai dai ta zo kawai ziyara ta tafi? Toh su din ma hakan ce za ta kasance, mu ma watarana sai ki ga mun yi namu auren mun tafi mun bar gidan. Sai a dade ma kafin a ganmu." Tsaki Humaira ta ƙara ja. "Ke dai Ummita kina son aure na lura, magana kaɗan za a yi da ke sai kin yi zancensa." Da mamaki Ummitan ta kalleta kafin ta amsa. "Aure ai abin so ne saboda sunnar ma'aiki (s.a.w) ne. Ke din ma ba sunnar kika tsana ba, mazan ne. Ban kuma san laifi kwakkwara da suka yi gareki ba." Taɓe baki Humaira ta yi daidai lokacin da suka fito babban titi. "Mu bar wannan magana, nikam ba kya ganin lamarin Anti Jannat da ɗaure kai?" Ummita ta yi shiru cikin nazari, tabbas da daure kai, tun bayan sadda ta zo hutun sallah lamarin nan ya afkuwa tsakaninta da ita, ba ta kara dawowa gidan ba sai yanzu. Wannan dawowar kuwa, daidai da kallon Humaira ba ta yi balle har ta jefe ta da kallon banza. Ta lura ko tana wuri Humaira ta shiga, mikewa take ta bar wurin. Haka dai tana ta kaucewa abinda zai haɗa su a inuwa guda.Har Humaira ta tarar musu abin hawa suka shiga ba ta amsa mata tambayarta ba sai da ta ƙara nanatawa kafin ta sauke ajiyar zuciya ta ɗan yi murmushi.       "Na lura sosai, amma ni abin da tunanina ya ban ko dai ta sauya ne tana gudun wani abu ya ƙara haɗaku ki maimaita abin da kika yi. Kin san fa ba zai yiwu ace ta mance ba." Dariya  ta yi. "Ikon Allah, toh ni ai na mance. Kawai dai sauyin ne ya ɗan bani mamaki. Babu kyara babu hantara, babu kirana da bare da ta saba yi ba komai. Sai na ke ganin kamar da walakin goro a miya." "Ki yi mata kyakkyawan zato, Allah yasa sanadin abin da ya kasance ta yiwa kanta faɗa. Ni kaina idan kin lura ai ta rage ɗoramin aiki tunda wannan zuwan ta sa an nemo mata yarinya mai kula da yara. Kawai dai mun saba da yaranta ba yanda za a yi ta iya raba wannan kaunar." Humaira ta kalle ta, zuciyar Ummita mai kyau ne, da Allah ya tashi, sai ya yi haɗa ta da mutumin kirki irinta wato Malam Sahabi. Mutum mai hakuri da kunya kamar wani mace. Amma abin mamaki duk kunyarsa idan suka ga saƙonnin soyayyar da yake turowa Ummita sai mamaki ya kusan kashe su ita da Raihana. Har rantsuwa suke kusan yi su ce ba shi ba ne waninsa ne. Ummita ta harareta. "Kallon fa?" Murmushi Humaira ta yi mai kyau da ya fiddo wushiryarta. "Kawai kina bani mamaki da kike kokarin kare wadannan mutanen da ba su taɓa kaunarmu ba koyaushe." "Uzurin kenan Humaira. Aure fa zasu yi su bar mu yanzu. Mu ma kuma..." "Toh naji ya ishe ni hakanan Malama matar Sahabi." Ummita ta sa dariyar jin abinda ya fito bakinta, ita din ma taya ta ta yi. Har suka isa ƙofar asibitin su na hira abinsu ana iska kaɗan kaɗan mai daɗi.       Ibb ne tsaye tare da masoyiyarsa Dr Salma, yayinda Fadeel ke zaune cikin mota yana jira su yi sallama. Mahaifiyarta ce kwamce a asibitin inda anan take aiki, suka zo dubiya ta yo musu rakiya har gaban mota. Bayan sallama da Fadeel ya koma mota yayinda suke hirarsu da Ibb tamkar kada su rabu, shi kuwa Fadeel kansa ya kwantar jikin kujera yana ɗan kallonsu yana murmushi. Shakka babu sun dace dari bisa dari. Dogaye ne su duka biyun don zasu kusan yin kai ɗaya, Dakta Salma baƙa ce, kwayoyin idanunta da haƙora ne kawai idan ta bude masu haske a fuskarta. Tana da kyau, ba ta da jiki sosai amma ba za ka kirata da siririya ba. Tana da diri masha Allah, sanya take da doguwar riga sai coat na likitoci da ta sanya saman kayan, sai kuwa mayafi ƙarami da ta yi rolling kanta da shi. Hannunta cikin aljihun rigar, gaba daya hankalinsu ba ya kan Fadeel da ya lula duniyar tunani da jin inama ace shi da Humaira ke wannan hirar ta nishaɗi. Allah kaɗai yasan yanda zai ji a lokacin. Ya soma gajiya, hakurinsa ya soma kai wa karshe amma yana dannewa gudun ɓacin ranta. Ya horu da rashin ganinta ido da ido ba hoto ba, ya sha zuwa ya tsaya a nesa kaɗan da gidansu ko zai ga wulkawarta sai dai ko mai kama da ita Allah bai taɓa ba shi ikon gani ba. Tabbas Raihana na kokari gurin aikamasa hotunanta wasu lokutan ma ba ta san ana ɗaukarta ba. Hatta da karamin video sadda take aikin snacks sai da ta ɗauka ta aikamasa. Yakan ji inama yana da iko da ita, inama matarsa ce yana kusa ya riƙo ƙugunta ya sanya ta a jikinsa ya bayyana mata irin yanda soyayyarta ke cin zuciyarsa sai dai kuma babu hali. Azabar da bidiyon ke sanya shi ciki ne ya sanya shi dakatar da Raihana daga turo bidiyo face hotuna.   Ya ja dogon numfashi ya furzar gami da kallon gefe guda yana mai kauda kai daga kan lovebirds. Hango wata ya yi kamar Humaira, ya ɗan yi tsai da idanu don so ya tantance abinda yake gani, sai kuma ya kauda kai. Ya fi tunanin gizo Humaira ta soma yi mishi, sai kuma ya kara kallo. Wannan karon ita ce tabbas, tana sanye da doguwar riga na material mai mayafi Jajaye. Yanayin kalar da garin ya yi, sai ya ba wa hasken fuskarta damar sheƙi musamman da ya kasance tana cikin annashuwa da kwanciyar hankali da alama babu wani abu dake damunta. Sai hira suke da abokiyar tafiyarta wadda ya gane ta, Ummita ce. Ya ganta a hoto don ba hoton Humaira kaɗai ba, hatta da ƴan gidan sai da Raihana ta turamishi hotunansu da kuma bayanin alaƙarsu. Har ya kama murfin mota zai fito ya tuna alƙawarin shekara da ya ɗaukar mata kawai ya fasa ya cigaba da kallonta. Dab da motar suka tsaya suna kalle-kalle kasancewar gilasanta tinted ya sa basu ganshi ba, shi kuwa Ibb shalelan Juliet, bai ma gansu ba ya lula wata duniyar sai buɗe haƙora yake yi kamar gonar auduga. Humaira ta ɗan yamutse fuska tana gyara gyalenta da iska ke kaɗawa. "Nikam asibitin nan juyar da kai gareshi, don Allah ƙara kiranta ki ce bamu gane wajen da ta ce ba kinga garin yana kara haɗewa." Itama Ummita duk ta damu ganin hadari ta fiddo waya ta dannawa Sadiya. Nan ta ce su tsaya inda suke ta gansu. Suka ja kuwa suka tsaya, Humaira ta zubawa mutanen dake ta shawagi a wurin idanu tana godiya ga Allah a ranta idan ta ga an wuce da marasa lafiya dayake suna daidai Emergency. Ba su wani jima ba sai ga Sadiyar ta iso, bayan sun gaisa ta karɓa ta yi musu godiya suka juya suka kama hanyar fita. Fadeel kamar wanda aka tsikarawa allura haka ya zabura ya fito daga motar ya dubi Ibb. "Malam ka zo mu tafi ba ka ganin yanda garin ke haɗewa wai?" Suka dubeshi, Dakta Salma ta yi murmushi. "We are sorry Amininmu. Bari na kyale shi haka. Nagode sosai ku gaida gida." Bai ko kalleta ba ya amsa da toh don shi gaba daya hankalinsa na ga su Humaira yana fatan Allah ya sa su amince su sauke su a gida. Ibb ganin an soma yayyafi ya yi mata sallama ya shiga motar ya tayar. "Please and please ka yi sauri kada su hau abin hawa, so nake ko yaya ka yimin kokari ta amince mu kai su gida." Ya tayar da motar ya soma tafiya sannan ya dubi Fadeel cikin rashin fahimta ya ce. "Wa kenan kake magana a kai?" Fadeel da idanunsa ke kan su Humaira wadanda suka kara ɗaga ƙafa ganin ruwa ya soma sauka bai ce komai ba face nuni da ya yi mishi da hannu. Sam bai ga fuskokinsu ba sai baya, kafin ya yi magana Fadeel ya sake tarar numfashinsa. "Humaira ce." "Ohh." Abin da kawai Ibb ya ce kenan. Yana zuwa daidai saitin inda suke ya tsaya har yana tare musu hanya, Humaira dake saitin wurin ta kalli motar ranta a ɓace don a ganinta ko waye yana sane ya sha gabansu. Ta bude baki da zummar magana Ibb ya sauke gilashi suka kalli juna. A gaggauce ta gaishe shi, itama Ummita haka, ta gane shi saboda tana ganin hotunansa a wayar Raihana, shi ne dai wanda y taimaki Raihanar. "Gida ku ka nufa ne? Ku shiga na sauke ku don yanzu idan ku ka shiga napep jiƙewa zaku yi." Ruwan sosai ya ƙara ƙarfi, Humaira ta buɗe baki za ta ja musu Ummita ta dafe hannun da sauri ta amsa. "Toh mungode." Ta kalli Humaira, a hankali kuma a gaggauce ta ce. "Muje Humaira, yanzu ba lokacin jan musu ba ne, wallahi nidai ina mura kin sani, ruwannan ya dake ni kuma lafkewa zan yi da bikin nan." Jin haka Humaira ta amince suka shiga, ita ta soma shigewa sai Ummita. Motar sanyi sakamakon Ac dake aiki. Sai a lokacin ta lura da wanda ke zaune a gefen Ibb din, ji ta yi kirjinta ya buga dam, ta rasa dalilin bugawar kamar yanda ta kasa dauke idanu a kansa. Shi ɗinma ita yake kallo babu ƙakƙautawa har bai iya ya amsa gaisuwar Ummita ba. A bangaren Humaira ji ta yi idan ta cigaba da kallonsa ranta zai iya fita saboda wani irin zafi da take ji a kirjinta ga kanta dake faman sarawa don haka da sauri ta kauda kai ta matsa ta maƙure a kujerar bayansa tana jingina da kofar motar. A hankali Ibb ya dan bubbuga kafaɗar Fadeel, firgigit ya dawo hayyacinsa ya gyara zama, gilashinsa ya zaro a aljihu ya rufe kwayoyin idanun da so da tsananin kauna ga kewa suka haɗu suka galabaitar. Dakyar Humaira ta iya gaida Ibb sannan ta gaida Fadeel din ba tare da ambaton suna ba. Shi ma amsawa ya yi can ƙasa. Ibb ke tambayar Ummita abin da ya kawo su asibiti. "Kuna da marar lafiya ne?" "Aa, aiko mu dai Anti Tasleem ta yi. Ita ɗin ɗaliba ce a nan. Nursing take karantawa ne." Dan jinjina kai Ibb ya yi. "Ok, na fahimta." Jin motar ta ɗauki shiru sai rediyo dake aiki sai ko ruwa da ke jiƙa gilasan motar yana sauka a guje saboda karfin da ya yi. Ummita ta dubi Humaira. "Wai, da tuni yanzu fa mun jiƙe." "Uhm." Shi ne amsar da ta ba ta. Fadeel kuwa lumshe idanun ya yi ya ji sautin Uhm din har tsakar kansa, gaba ɗaya sai da ya ji tsikar jikinsa ya tashi. Kamar kuma haɗin baki sai ga gidan rediyon sun saki waƙar Breaker mai taken Kalmar So. Humaira sam hankalinta ba ya jikinta, ji take kamar ta buɗe motar ta dira a cikinta. Gaba daya koina a jikin rawa yake, Ac ke kaɗawa a motar amma ita zufa take. Ta tuna da ambaton Allah ba shiri ta shiga ambata a ƙasan ranta a hankali ta soma dawowa cikin nutsuwarta. A bangaren Ummita da Ibb, hira suke ɗam taɓawa kaɗan, shi kuwa Gogan da Humaira ba ka jin komai daga bakinsu, babu kamar Fadeel da yake jin waƙar ta zo daidai da yanayin da yake ciki. So yake ya tambayi ya take? Ya lamuran rayuwa? Ba ta hakura ba har yanzu? Ba ta amince ya turo iyayensa ba? Sai yaushe? Amma ina! Babu ko kalma ɗaya da yake jin zai iya furtawa, ba ya fatan rabin shekarar da ya kusan cinyewa ya tashi a banza balle ya ga shekarar ida  da rai da lafiya, wannan ya sa yake takatsantsan ya kuma jure bai ƙara kallonta ba tunda ko ya kalli side mirror ba ya ganin komai face danshin ruwan dake kwarara sai ko hasken fitilun motocin dake saman titi. Har suka iso gidan ba ka jin uffan daga Fadeel, shi kansa Ibb sanin halin mutumin ya sanya bai takale shi da hira ba ko sau ɗaya. Ya dai san yau Humaira ta fama mishi inda yake mai ƙaiƙaiyi. "Ko mu karasa da ku har cikin farfajiyar?" Wannan kalmar ya sa Fadeel cire gilashin idonsa, ya dubi gidan su Humaira, wato har an iso kenan. "Aa, mungode sosai. Bari mu karasa ciki." Cewar Ummita. Humaira kuwa har ta kama ƙofar ta bude, amma ina, iska mai karfi da ruwan da ya fesomata ya sa dole ta koma ta rufe. Fadeel ganin haka ya juya bayan, sai a sannan ya kara kallonta ido cikin ido, da sauri ya dauke idanunsa ya dan kai hannu baya ya dauko lemar dake ajiye a wurin. Fitowa ya yi ya buɗe lemar, babba ce don ta fi ta Ummita girma, Ummita kam tuni ta fita itama ta bude nata lemar da ba zai ishe su ba su biyu koda a dazun ne. Kofar Humaira ya bude gami da miƙamata lemar. A sanyaye take dubansa. "Karɓa mana Humaira." Ibb ya furta, ta kalleshi. "Mungode sosai, Allah ya kiyaye hanya." Daga nan ta fita, sai ya kasance su biyun a ƙasan lemar. Kan Fadeel a ƙasa ba ya son kallonta gudun ɓarowa kansa aiki, ta sa hannu ta karɓa sannan ta dan ja baya kaɗan. "Idan na shiga zan aiko a kawo." Murmushi ya yi mai kyau har a sannan bai kalleta ba ya amsa da toh. Daga haka ya fice ya koma cikin motar ya rufe. Ita ma ta nufi kofar da gudu-gudu. "Muje." Ba musu Ibb ya yi reverse ya juya kan motar suka bar layin. Ƴar dariya ya yi. "Fadeel kana son Humaira." Fadeel bai iya kallonsa ba ballantana ya samu amsa. Ya kara cewa. "And you know what? Kun dace sosai." Nan ma bai kalleshi ba sai dai ya yi murmushi. Ganin ba ya son magana ne ya sa Ibb rabuwa da shi. *** A can kuwa Humaira na shiga ta bada lemar a miƙa musu, ɗan aike ya dawo ya ce babu kowa a wajen, ta karɓa a sanyaye ta shige ɗakinsu da shi. Madadin ta karasa ciki sai ta ajiyeshi a ɗan gefen don ya sha iska. Suka sauya kayan jikinsu saboda jiƙewar da suka ɗan yi. Ummita ta ɗauro alwala sannan itama ta ɗauro, koda ta idar da sallah kwanciya ta yi saman dardumar don kanta har lokacin sarawa yake yi kamar jijiyoyin kan nata za su tsinke. Tuna Fadeel kaɗai yana haifar mata da rawar jiki da ciwon kai, daga haka kuma sai ta ji kamar ana mata ihu a kunne. Kafin ka ce wannan sai ga Humaira ta soma kuka sosai. Ummita da ke kwashe jiƙaƙƙun kayansu ta juya da sauri ta juyo. Allah ya taimaka su kaɗai ne a ɗakin ta roƙi yanmatan akan su fita ta gyara don sun yi kaca-kaca da shi. Tuni ta fahimci matsalar jinnunta ne, ta sha mamaki ma da bai tashi a mota ta yiwa su Fadeel rashin mutunci ba. Da sauri ta fice zuwa kicin, can baya ta zagaya inda ake dora babban tukunya a icce saboda yawan da aka yi. Garwashi ta zuba cikin kasko ta dauka da sauri gudu-gudu ta nufi dakinsu. Mami dake kokarin shiga kicin don ganin kwandunan kayan miyan da Abba ya ce an kawo na girki ta tsaya cak hankalinta ya yi kan Ummita wacce ke tafiya kamar wani abu ya faru. Da sauri ta bi bayanta. Ita kuwa Ummita, tun cikin babbar sallah da ta je Bichi ta karɓowa Humaira hayaƙi a wurin ɗan uwan mahaifiyarta hakan yasa Humaira na fara kuka ta yi niyyar turara mata. Abin mamaki har ta isa yanayin kukan Humairar bai sauya ba. Ta ciro maganin ta barbaɗa cikin kaskon ta ajiyeshi kusa da Humaira. Nan da nan kanta ya soma juyawa. Daidai lokacin Mami ta faɗo ɗakin. Abin da ta gani ne ya sanya ta kallon Ummita, "Lafiya? Meke faruwa da Humairar? Wannan wane irin hayaki ne kuma?" Ummita ta sha jinin jikinta don gaba daya ba ta sanar da Mami ta karɓowa Humaira hayaƙi ba. "Ba komai Mami, kukan nan ta soma wanda take yi idan aljanunta suka tashi shi ne.." Mami ta daka mata tsawa. "Shi ne me?! Shi ne kike yi mata hayaƙi ba tare da kin sanar da ni ba? Haba Ummita, yanzu idan Abbanta ya ji wa zai yiwa faɗa? Maza ɗauke hayaƙin nan." Ummita ta dauka ta fitar zuwa bandaki ta kashe, ta sani ta yi kuskure amma kuma cikin ikon Allah Humaira ta yi shiru sai gumi take haɗawa da alama kuma bacci ya ɗauketa. Ummita ta kai duba ga Mami, zuwa lokacin tana zaune gefen gado. "Ki yi hakuri Mami." Girgiza kai Mami ta yi. "Ba laifi kika aikata ba Ummita, na sani kulawa ce da yar uwarki, amma ko mene ne ya dace na sani saboda nima ina nawa kokarin a kanta don har na yiwa Abbanku maganar wani mai bada magani zan kai ta wurinsa bayan biki ya ga mece ce matsalarta." Gyaɗa kai Ummita ta yi tana murmushin farin ciki. Ba ta da fatan da ya wuce ta ga Humaira ta samu lafiya ta amince da auren mai kaunarta irin Fadeel. "Toh Mami. Allah ya sa a dace." Mamin da murmushi ta amsa da amin. Har ta mike ta kai ƙofa ta juyo. "Ɗaukomin maganin da kike turara mata, idan ya so sai na yi mishi bayani." Ba musu Ummita ta ɗauko ta ba ta, murmushi ta yi ta juya ta fita a dakin. *** BIKI BUDURI.... ®️Rufaida Umar.*LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* 09034973645 Yau ranar ta kama ranar Kamun ƴanmatan Mami, Futuha da Tasleem. Tun safe Humaira  ba ta zauna ba, tana tsaye akan aikin suyar snacks da aka haɗa tun ana saura kwanaki biyu aka sanya a firij, sai da aka ci rabin aikin kafin ta bar wurin bisa umarnin Mami acewarta yanda ta kwashi gajiyarnan gwara ta je ta huta kafin lokacin da za a tafi event center da aka tanada don Kamun. Haka ta karasa ɗakinnasu a mugun gajiye tana jan ƙafafunta da suka yi tsami. Hayaniyar ƴanmatan  dake ɗakin ko kaɗan bai mata ba, ji ta yi da ace tana da hali da kaf sai ta sa an fice an bar ta ta huta. Hakanan dai ta karasa tana amsa sannun da wasu ciki ke mata tana murmushin yaƙe. Ummita tun safe ta raka Anti Jannat ƙunshi har lokacin ba su dawo ba. Ita dai daga wannan kwanciyar tana jira ta a fito daga bandaki ta shiga wanka, ba ta san ya aka yi bacci ya yi awon gaba da ita ba.   Ba ita ta farka ba sai da aka kira sallar la'asar, nan ɗin ma Raihana ce ta tashe ta. "Kai, har kin ban tsoro. Kin fa jima kina baccin nan tun ɗazu nake safa da marwa ba ki tashi ba." Humaira dake dubanta da manyan idanunta da suka kaɗa suka yi ja ta ce. "Har an tafi ne?" Harararta ta yi. "Jimin ke ɗinnan, an tafi ne za ki gan ni anan? An dai soma kwalliya da shirin tafiya. Ki tashi kiyi sallah ki wanka mu tafi lar mu makara." "Ina kuma za mu je?" Humaira ta tambaya da mamaki. Sai kuma don kanta daga yanayin kallon da Raihanar ta jefamata ta tuna. Ta gyaɗa kai tana hamma da miƙa lokaci guda. "Oh na tuna, kin ce wajen kwalliya za mu je ashe. Toh ita Ummitar ta dawo?" Raihana da tuni ta miƙe ta hau fiddo karamin akwati da zummar daukar sarƙa ta amsa da eh. Ji tayi kamar ta rufe Humairar da duka, dama dakyar ta amince za ta yi kwalliyar. Ba  ta kara bi ta kan Humaira ba, itama ganin haka sai kawai ta ja zani ta faɗa banɗakin. Ranta ya ɓaci ganin yanda aka yi kaca-kaca da shi, ba ta iya wanka ba sai da ta wankeshi tas har Raihana na kwankwasa kofar tana mitar ta san wankin bandaki take tayi biris da ita. A gaggauce ta sanya doguwar riga da mayafinsa ta tayar da sallah, Ummita na zuwa suka ɗunguma suka fice bayan kowacce ta dauki dukkan abin bukata. Babu nisa sosai da unguwarsu, Yahaya Gusau sula je gidan wata yayar ƙawar Raihana ta makaranta, ana kammalawa suka shirya a gaggauce matar ta yi musu ɗauri. Tsayawa kwatanta irin kyawun da suka yi ma ɓata baki ne. Idan ka kalli Raihana ka yaba, idanunka na sauka kan Ummita za ka ce ta fi su kyau duk kuwa da cewar ta fi su duhun fata, amma idan kallonka ya sauka ga Humaira sai ka yi saranda. Sun fito fes cikin ankonsu na atamfa na kamu. Raihana ce ta biya kudin kwalliyar ta account dinta, ta dai ce musu Mami ce ta ba su don haka ba su matsa da tambayar ba. Ta ɓoyemusu daga aljihun Fadeel ya fito, shi ne kuma ya matsa mata akan sai ta karɓa yana son Humaira ta yi kyau. Hotuna sosai Raihana ta dauke su, ta tura mishi na Humaira kaɗai. A  gidan suka bar kayansu suka fice. Kai tsaye Manal Event Center suka nufa. Wurin ya tsaru iyaka, kowa ka gani da irin nasa haɗuwar. Babu laifi kamu ya yi kyau sosai, Humaira tun da ta nemi guri ta ƙame ba ta ko motsa ba ballantana ta yi rawa. Ummita dai ta ɗan fita amsa wayar Sahabinta, ta kuma dawo Anti Jannat ta haɗa ta da ƴan biyu akan ta zauna da su kar su fita, hakanan ta zauna tare da Humaira da wasu cikin yan uwan Abba, su din ma ba duka suka zo ba.   A gajiye suka koma gida, kowa ya nemi wuri ya kwanta bayan idar da sallah. Su Futuha gaba daya sun bar kwana a dakin, daki daban suka koma tare da kawayensu wanda babu komai ciki, daga shimfiɗaɗɗen kafet sai katifu sai kuwa fanka dake wulwulawa.   ***   Tafe yake zuwa sashin Anti Amarya. Kusan kwanaki sama da biyar kenan rabonsu da juna, ba don komai ya dauke kafa daga shiga cikin gidan ba sai Murja da take neman matsawa rayuwarsa da kallo da kuma hirar dole. Tuni ya taka mata burki da zuwa sashinsa tun bayan da Alhaji ya sanar da shi saƙonta.   Yau ɗin ma, Alhaji ne ya ritsa shi akan Anti Amaryar tana tambayarshi wai ko ba ya gari. Nan fa Alhajin ya yi mishi faɗa sosai ya ba shi hakuri. Don ya wanke kansa ne kuma zai je a yau din. Da sallamarsa a baki ya tsaya har aka amsa sannan ya shiga. Wacce ba ya kaunar ganin ya ci karo da ita kuwa a kwance tana chatting, daga ita sai vest da dogon wando. Ya kauda kai ya juya zai koma, sai ya tsinci muryar Anti Amarya. "Ah, Fadeel ya za ka juya? Shigo mana. Ke kuma je ki suturta jikinki." Ta karashe maganar ƙasa-ƙasa tana duban Murja. Ta kuwa mike da saurinta ta yi ɗaki, yau ji take kamar an mata albishir da gidan aljanna, ba ta san haka ta yi kewar Fadeel din ba sai da ta gan shi a gabanta yanzu babu zato. Don haka da sauri-sauri ta zumbulo hijabi ta dawo falon. Lokacin ya maida hankali suna gaisawa da Anti Amarya. "Ai ni Fadeel na rasa laifin da na aikata gareka. Na ma yi zaton ko ka yi tafiya ne ashe kana gidan amma ka ɓuya." Ya yi murmushi yana ɗan shafar ƙeya. "Ko ɗaya Anti, babu abin da kika yi. Abubuwa ne suke ɗan riƙe ni, nakan fita da wuri sannan lokacin da zan shigo dare ya yi shiyasa. Amma tuba nake, ganinan yau na shigo." Ta yi ƴar dariya. "Toh shikenan ya wuce. Dama Alhaji ne na ga kana kawowa Meatpie da Samosa mai shegen dadi, har nake tambayarsa inda kake odarsa. Gaskiya ya yimin sosai, ina so ne a yimin na birthday ɗin autanku (Abdulmaleek) nan da two weeks, ko zan iya samun lambar waya?" Fadeel ya yi murmushi, ya na so a duniya ya ji an yaba da girkin Humairarsa. Kafin ya ce komai sai ga Murja ta tsoma baki. "Eh wallahi Anti, nima naji dadi. Babu tauri kuma komai ya ji a ciki sosai. Please ki yi order a wurin." Ya yi shiru kaɗan, ya sani ba shi da matsala koda ace ya ba su lambar Humaira tunda dai oda ne zasu yi. Ba ya tunanin kuma Murja ta san wacece, ba ma ita ba, shi kansa Alhajin bai san daga inda Fadeel ya yi odar ba don haka hankali kwance ya ce. "Toh Anti, zan turomaki ta message sai dai zuwa yanzun suna cikin biki ne ba za a samu ba. Kafin dai zuwa kwanakin da za a yi taron sun kammala." Anti Amarya ta jinjina kai. Murja dai ɗif ta yi da ta fahimci ko ma wace ce dai mace ce yar uwarta. Abin damuwar tana da aure? Sunanta Humaira? Shi ne ba ta da masaniya. Ita a duniya yanzu mai suna Humaira take son gani wacce Fadeel ya mato a kanta. Dama kawai take jira ta buɗe wayarsa ta bincika wanda hakan da kamar wuya. ***  A can gidan Alhaji Isuhu kuwa, yau aka wayi gari da daurin auren yarannasa wanda ya tara dubban jama'a daga wurare daban daban. Babu ma kamar jama'ar Alhaji Yakubu kasancewarsa mutum na mutane. Cikin gidan ko tun bayan da suka samu labarin an ɗaura auren, nan ya rincaɓe da guɗa da murna. Su Futuha amaren zamani idanun nan ko ɗigon hawaye babu sai ma murmushi da suke dokawa. Sun sha kwalliya da farin leshi sun yi kyau har sun gaji. Su Ummita kuwa shadda ce ruwan madara da aka yiwa kwalliyar stones suka sanya wanda Mami ta yi musu. Duk inda suka wulƙa sai an kalle su an kuma. Ƴan uwan Mami gulmar masu gulmarta suna yi, a cewarsu ta riƙi bare kamar ƴan cikinta, wataran za a wayi gari sun mata butulci. Yayinda a gefe dangin Abba ke yabon Mami da irin yanda ta ɗauka ki Humaira da Ummita, sun sani ba ta da laifi ko kaɗan a rashin zuwansu gidan sai ko na Mahaifiyarta Anna. Shi ma Abban da bai ba su fuskar su shigo jikinsa ba ya sanya suke ja baya. Sam Abba ba mai sakin aljihu ba ne, hakan ya sa yake ganin kamar duk wani da zai raɓe shi a yan uwan toh fa buƙata ce ya zo da ita koda ba hakan ba. An sha hotuna sosai, da yamma Amare suka kara shiri cikin atamfarsu mai ɗan karen tsada. Aka sha yini, sannan bayan Magriba aka hau shirin Dinnerparty. Nan ma ya yi kyau sosai, Angwaye da Amare sun sha ado, Amaren sun yi shigar golden lace su kuwa angwayen golden shadda. Ƙawayensu ƴan ƙarya kowacce ji take da kanta. Su ma Humaira leshi Mami ta yi musu coffee colour mai ratsin golden. Sun yi kyau kwarai. Washegari aka tattara da yammaci aka miƙa Amaren ɗakunansu. Gidan Futuha a rijiyar zaki yake. Danƙareran gida ne na Alhaji Yakubu mai ɓangare uku, nashi sai uwargidansa sannan na Futuha a gefe. Yan uwanta sun yaba sosai da gidan, ga kaya na alfarma da Abba ya yi musu bisa jajircewar Mamin akan ya daure ya fita kunya. Koda suka nufi sashin Uwargida suka iske shi a garƙame, sun bubbuga ya fi a kirga amma shiru, dole haka suka juya da ita zuwa nata ɓangaren suna mita. Wasu na fadin tana nan sun ga sadda aka buɗe labule ana leƙen zuwansu daga wani window a sama. Daga nan suka wuce Kuntau inda anan ne gidan Tasleem yake, babu laifi shi ma ya haɗu. Flat house ne amma an kashe mishi kudi daidai misali. Ita kadai ce a gidanta sai dai gidan iyayen Hamza na kallon gidan, sai da aka shigar da ita wajensu suka karɓe ta da hannu bibbiyu aka yi ƴar nasiha da addu'a kafin a kai ta gidanta. *** A sati guda kacal, gidan gaba daya an watse sai mutan gidan. Mubarak ma wanda bai fi watanni biyu suka rage ya kammala karatu ba ya tattara ya koma a yayinda a gefe daya Yassar da Dawud ke shirin tafiya bautar ƙasa. Gidan ya zama gwanin dadi ga Humaira, babu wani da ke matsa mata yanzu balle kallon banza. Raihana da Ummita sun je gidajen amare ita kuwa ko leƙe ta ƙi yi. Ta dai yi musu cincin bisa umarnin Mami, an kai wa kowaccensu gidanta saboda tarbar baƙi. Raihana da Ummita suka maida hankali a karatu don sun soma shirin jarrabawar fita aji SS2 zuwa SS3. Ita kuwa Humaira a sannan ta kammala darussanta na makarantar Anti Laila, hakan yasa koyaushe tana gida idan har ba wani aikin ta samu ba. Sai ya kasance ita ke girkin gidan, a cewar Mami, hakan zai ɗebe mata kewa. Ta kuma yarda da hakan dari bisa dari, ita kanta ba ta son zaman shirun don yana jefa ta tunani kala-kala. Ranar ta kama laraba tana tsaye tana shanyar undies dinta a gefe kuma tana sauraron waƙar Ala mai suna Shahara. Jin waƙar ya tsaya ne yasa ta fahimci kira ne ya shigo. Ta ɗan goge hannunta da sauri ta dauka ganin baƙuwar lamba a ranta tana fatan ya kasance oda ne ta samu don dazu suke magana da Mami take nuna rashin jin dadin yanda kwanaki biyu shiru ba'a samu ba. Da sallamarta ta ɗaga. Aka amsa daga can, muryar mace ce. Suka gaisa a mutunce. Nan take shaida mata ta samu lamba ne daga ɗaya daga cikin kwastamominta, tana son a yi mata snacks na birthday din yaronta da za ta yi. Nan fa Humaira ta ji dadi sosai, ba ta kawo kowa a kwanyarta ba sai Hajiya Rukayya, ita ce mai kokarin haɗa ta da mutane. Suka yi magana ta lissafa mata kalolin snacks din da take yi, ita kuma ta zaɓi kala uku. Nan ta fadi adadi. Suka yi sallama da zummar za ta turo rabin kuɗin, rabi kuma idan an kai za ta cika. Ta bukaci Humaira ta turamata acc no ta text. Da wannan farin cikin ta karashe shanyar da ta fara, ta dauki bokitin ta shige gidan ta kofar kicin ta baya. A falo ta hadu da Mami. Ta sanar da ita batun odar da suka samu, Mami ta ji dadi kwarai. *** Ita kuwa Anti Amarya tana ajiye wayar ta dubi Fadeel da murmushi saman fuskarta ta ce. "Yauwa mun yi magana. Zan tura mata kudin yanzu idan ta aiko." Ya ɗan murmusa. "Ok Anti. Bari na wuce ofis, sai na dawo." "Toh Allah ya ba da sa'a." Har ya soma tafiya ta kira sunansa, ya juyo. "Amma meyasa ka ce kar na ambaci sunanka?" Ya yi murmushi cikin son nemo abin faɗi can ya ce. "Saboda ba za ta gane ni ba, ba ni ke yin odar ba. Sister Rukayya ce ke yi mana. Idan kika ce Haj Rukayya za ta san ta." Cikin gamsuwa Anti Amarya ta amsa. Daga nan shi kuma ya fice. Murja dake jin su tana daga dinning table a zaune, ta bishi da kallo. Yana fita ta yi saurin karbar wayar Anti Amarya, tana tambayarta me za ta yi, babu amsa. Sai da ta kwafe lambar Humaira fes sannan ta adana a wayarta. "Me za ki yi da lambar?" Ta dan sha mur. "Ina tunanin ita ce budurwan nan tasa da yake mutuwar so." Dariya Anti Amarya ta yi. "Kin samu matsala Murja, me zai yi da ita toh? Nikam jikina bai ba ni hakan ba. Daga jin muryar wannan ɗin ma kin girme ta. Ba na ji a gaskiya zai kula yarinya, yaron ba ya son raini tun farko idan kin lura." Murja ta dan ji hankalinta ya kwanta, amma hakan ba zai hana ta bincikawa ba tunda dai ta kasa ɗaukar wayar Fadeel, idan ma ta ɗauka to ya sanya password ba ka iya shiga. Tsayuwar mota suka ji a farfajiyar gidan. Murja ta leƙa, ganin Fu'ad tare da Matarsa Kausar wacce a yanzun take dauke da karamin ciki, ta ja guntun tsaki. "Waye ne ya zo?" Yamutsa fuska ta yi. "Wannan dogon ne mana mai hankali a gwuiwa tare da matarsa. Ni na rasa wannan jaraba, mace da ciki sai shegen yawo." Ta kara jan tsaki. Anti Amarya ta bude baki ganin wannan karfin hali na Murja, mutum da gidan ubansa sai a hana shi kawo matarsa? Za ta yi magana ta fasa ganin Kausar din ta shigo. Ta tarbe ta da fara'a suka gaisa ta karaso. Shi ma Fu'ad ya biyo bayanta hannunsa rike da jakarta na kaya. Bayan sun gaisa ne yake cewa Antin tafiya zai yi na kwanaki uku zuwa Abuja zasu yi meeting da shugaban kamfanin da ya ke aiki shi ne ya kawo ta gidan ta zauna dayake ƴan gidan su Kausar din sun yi tafiya Saudia. Anti Amarya ta karbe ta hannu bibbiyu, ta sa Murja kai mata jaka daki. Murja na kumburi haka ta ja akwatin kayan zuwa ɗakin da babu kowa ciki wanda a baya ya kasance na Hannatu ƙanwar Fadeel. Kausar wayayyiya ce sosai kuma gogaggiyar ƴar boko da ba ta daukar raini koda na sakan, tun farkon zuwanta gidan ta ga take-taken rashin kunyar Murja wannan ne dalilin da yasa ba sa ga maciji. Ba ta shiga harkarta ko kadan. Murja kuwa ta tsani a duniya ta ga wanda ya fi ta iya kwalliya da komai ma a wuri, balle kuma kuɗi da uban Kausar ya ninka baban su Murja. Gaba da baya dai yarinyar ƴar gata ce kuma gatan da ta samu bai yi sanadin taɓarɓarewar tarbiyyarta ba. Tana da girmama mutane amma ba ta daukar raini. Hatta da wayarta sabuwar version ne na Iphone, hakan ya sa Murja ko kallonta ba ta yi idan tana dannawa tsabar bakin ciki. Wannan ne kuma ya kara mata son ganin ta mallaki miji irin Fadeel, ta san komai take so za ta same shi cikin sauki. Koda Fu'ad ya bar gidan, Anti Amarya da Kausar sun taɓa hira kadan kafin ta mike ta nufi ɗakin da aka tanadar mata don sosai bacci ne a idanunts. Ciki ya sanya ta zama kamar wata kaasa. Murja ta bi bayanta da harara. Anti Amarya kuwa ta kalleta dakyau ta ce. "Ke banza ce, ba ki da wayo ko na sakan, yanzu a gaban Fu'ad kike share matarsa? Ke da kike neman gurbi a zuciyar yayansa, to ta ina zai tayaki yaƙin? Ki cigaba da nunawa duniya ba ki da kunya, wallahi ina maki kashedi, ba a samun kan mutane sai an haɗa da kissa. Ai koda ace kina mata ƙin mutuwa bai kyautu ki nuna ba. Daɗina da ke sam babu wayo sai aukin ɓata rawarki da tsalle." Murja gaba daya sai jikinta ya yi sanyi. "Kuma fa hakane Anti. Ni wallahi abin ne ya soma yimin yawa. Wanda nake so bai san da zamana ba, na rasa ta ina zan soma Anti." Wani murmushi Antin ta yi. "Au, kin dawo hanya kenan? Da ba malamai kika ɗaura ɗamarar bi ba? Ke da ace na bi hanyar malaman za ki ganni a gidannan har i yanzu? Toh uwar Fu'ad abinda ya kashe ta kenan, ta nuna ƙiyayya da makircinta a fili karshenta kuma yanzu ga gidannan ya gagareta zama. Malama duk wata ɗabi'a mummuna watsi da shi za ki yi. Ki sauya salon shigarki zuwa na matan arziki. Wani matsewa ki fiddo sura ba shi ke burge Fadeel ba, idan kin lura yana son ya ga mace mai tarbiyya. Sai kin sauya sosai, ki kuma daina rawar ƙafa a kansa, a hankali nan gaba ko malamin ne sai a bi a shawo kansa. Amma kafin wannan matakin ke za ki sauya takunki." Murja ta dinga gyada kai tamkar ƙadangaruwa, sosai darasin na Anti Amarya ya shige ta, sai dai ta ina za ta fara? Sun jima Anti Amaryar na ƙara wayar mata da kai tana ɗauka, a karshe dai ta saki ranta sosai ta kuma gane Antin nata ba ta wasa ba ce. ****LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* 09034973645 Da taimakon Allah ta kammala aikin odar da aka bata. Kamar yanda ta saba, wannan karon ma waya ta yi akan a zo a karɓa. Aka ba ta lokacin zuwa karfe sha biyun rana. Bayan sun yi sallama ta sauke ajiyar zuciya tana mai jin wani irin nishaɗi. Hamdala ta yi kamar koyaushe kafin ta fiddo manyan ledojin mai tambarin Deelsha's Delicacies ta sanya. ***   Murja ta kammala shiri tsaf sai rawar jiki take yi ta je ta ga Humaira me snacks. Kausar na zaune a falo tana taya Khadija da Hanifa (Ɗiyar Saddika yaya ga Anti Amarya) hura  balan-balan su na tarawa. Murjar ta fito. Kallo ba ta ishe ta ba, ta gefen ido Murja ta watsamata harara. Daidai lokacin da Anti Amarya ta shigo bayan ta dawo daga farfajiyar gidan inda mai decoration ke ƙawatawa don anan za a gudanar da birthday din Abdulmaleek na cika shekaru uku a duniya.   "Ni na shirya zan wuce." "Toh tsaya na baki cikon kuɗinta. Don Allah ki yi sauri kina karɓa ki wuce ki karɓo Cake din." Ta amsa da toh. Anti Amarya na shiga ciki sai ga Fadeel ya shigo falon riƙe da Abdul yana mishi wasa. Nan da nan Murja ta ji ranta ya yi wani irin sanyi. Ta kuramasa idanu tamkar ta lashe shi musamman ganin yanda shigar jan t-shirt da baƙin jeans ya haskaka shi abinka da fari. Ta sauke ajiyar zuciya tana ji inama kawai ta tsinci kanta a faffaɗan ƙirjinsa. Sai da ta ji suna gaisawa da Kausar sannan ta dawo hayyacinta. Ajiyar zuciya ta sauke, ta ƙarasa ta zauna ita mai shirin fita. Murya cike da yanga ta ce. "Yaya Fadeel barka da rana." Kallo ɗaya ya yi mata ya kauda kai, shi a yanzu sam ba ta burgeshi tun sadda Alhaji ya faɗamasa saƙonta. "Yauwa." Daga haka ya maida hankalinsa ga Kausar suna hirar aikin Fu'ad da babu hutu. Ita kuwa Kausar hakan ba karamin dadi ya yi mata ba, ta gama lura da irin matowar da Murja ta yi a kan Fadeel, ta kuma sani zai wahala ta same shi tunda sam ba ta gabansa. Murja ta shaƙa, saukowar Anti Amarya daga saman bene ya sa ta mikewa. Fadeel ya gaisa da ita. Ta miƙawa Murja kudin tana fadin. "Ina daɗa roƙonki, na san halinki kar ki je ki zauna don Allah Murja. Kina karɓar snacks din ki biya ki dauko cake." Ta amsa da toh, ji take inama direban gidan ba ya nan sai ta ce Fadeel ya kai ta. Amma tun dazun yana waje ita yake jira. Fadeel kuwa yana jinsu amma bai sa baki ba. Ba ya son ya zaƙe akan lamarin Humairar har su shinshino wani abu babu ma kamar Murjar da bai gama yarda da ita ba. *** Ta tsaya daga ƙofar gate din gidan tana ƙarewa gidan kallo, yamutse fuska ta yi. Eh ba laifi su na da rufin asiri amma ko daga waje bai kama ƙafar gidan su Fadeel ba. Ta karasa ta yiwa Maigadi sallama ta kuma faɗi abin da ya kawo ta, iznin shiga ya yi mata kai tsaye don dama yana da masaniyar sana'ar Humairar. A sadda ta karasa ciki Humaira na zaune tare da su Raihana a falo bayan gama yi mata kwatance a waya, ta sani ba za a ɗau lokaci ba za ta karaso tunda a sanda suka yi wayar tana kusa da su. Sallamarta ya sa gaba daya suka dube ta. Ba laifi tana da nata tsarin daidai gwargwadod. Abaya doguwa ce a jikinta sai mayafinsa, sai ko wani ƙaton gilashi da ta rufe kwayoyin idanunta da shi. Tunda ta shigo falon ya karaɗe da ƙamshin turarenta mai ƙarfi irin wanda ya zama haramun mace ta fesa ta fita da shi. Suka tarbe ta da hannu bibbiyu aka gaisa. Humaira har da kawomata ruwa da ragowar snacks din ta ci. Kasancewarta wayayyiya ta sake da su aka ɗan taɓa hira har Mami ta fito suka gaisa da ita. Murja ta yaba kwarai da tarbar da aka yi mata, ta kuma ji a jikinta Fadeel ba zai so Humaira ba, ba ita ce wacce yake so ɗin ba don dai wannan din ba wata babba ba ce ba za ta wuce shekaru goma sha biyar ba. "Kina da page a instagram ne?" Humaira ta gyaɗa kai da murmushinta har wushiryarta na bayyana. "Eh akwai." "Mene sunan?" Nan fa daya, ta sani furtawar ne aiki ba ta iya ba sosai. Raihana ta karɓe zancen ta fadi. Murja har sai da ta ɗan kalli Humaira sannan ta kalli Raihanar da murmushi. "Ok zan yi following dinki. Na ji dadin ganinki na kuma ji dadin ɗandanon snacks dinki duk da daman na san ɗandanon. Akwai ɗan uwana Yaya Fadeel yana kawomana sosai. Ta wajensa muka sanki." Murjar ta fadi tana mai ƙurawa Humairar idanu don ta ga yanayinta, so take dai ta samu tabbacin babu komai tsakaninsu. Raihana kuwa ɗan jim ta yi a ranta tana tunanin wane Fadeel din? Kodai Fadeel wanda ta sani ne, tabbas ya faɗamata yana odar snacks din Humaira ta hannun wata Antinsa. Ko shi din wannan ke nufi? Idan kuma hakane ita wace ce a wajensa? Ta maida dubanta ga Humaira don ta ga yanayinta, sai ta lura ko kadan ba ta sauya daga murmushin da take yi ba, sai dai jin sunan kamar jikinta ya dan yi sanyi. "Allah Sarki, na kuwa gode sosai." Abin da ta ce kenan, wannan ya sa Murja kuma sakin jikinta sosai. Lallai wannan ba ita ce Humairar da Fadeel ke mutuwar so ba, wannan da alama ba ta ma san da zamansa ba. Dama ya ce ba shi ke yin odar da kansa ba. Yanzu kam ta yarda. Murja ba ita ta bar gidan ba tsabar shagala da ta yi suna ta kwasar hira da su musamman Raihana wacce ta fi su sanin mutane, kusan ma akwai ƙawayen Raihana na makaranta wadanda duk Murjar ta san su hakan yasa hira ta musu dadi sai da Anti Amarya ta kira wayarta tana faɗan jimawarta ba shiri ta mike, su Humaira kuwa har mota suka raka ta da ledojin. Murja ta karɓi lambar Raihana da zummar a dinga gaisawa duk da ta girme musu don za ta yi sa'ar Tasleem. *** Sadda ta isa gidan har yara sun fara zuwa ƴan party. Ta karasa Anti Amarya na mata faɗan dalilin jimawarta. Hakuri ta ba ta, ganin Fadeel a wurin wanda ke cin abinci a nutse saman dinning ta ce. "Wallahi hira muka sha da su Humaira, mutanen gidan akwai kirki kar ki so kiga kamar kada a rabu." Fadeel ya ji maganar har ransa, ya kuma ji dadi sosai. Bai dai ko ɗago ya kalle ta ba. Yana ji dai tana ta ba Anti Amarya labari ita dai ledojin ta hau buɗewa tana kallon snacks din. Koda ta dandana sun mata dadi kwarai. Nan aka shiga sanya wa a takeaway ana rufewa, Kausar na nan ana aikin da ita. An gudanar da party cikin armashi, yaran Daddy da Mommy ne suka cika gidan don Anti Amarya sam ba ta barin mara shi ya raɓe ta. Yawanci duk abokan makarantar Abdul din ne sai ko makwaftansu. Hatta a yaran yan uwanta ba kowa ta gayyata ba. *** Ɓangaren Amare kuwa, Amarya Futuha an ci amarcin sati daya cif ko ƙofar gida ba ta leƙa ba. Hotunansu ita da mijinta kala-kala babu wanda ba ta ɗorawa a Instagram, shi kansa Angon hakan na mishi dadi kwarai bai taɓa hanata ba. Tunda ta zo ba ta taɓa sanya Uwargida a idanunta ba, karshe ma sai Ango Yakubu ke sanar da ita ta yi tafiya Saudia ita da yaranta. Futuha tun da ta ji haka duk sai ta matsa mishi akan ita ma ya dace su tafi hutun honeymoon Dubai. Hakan ya yi mishi dari bisa dari, a lokacin ji yake ko nawa ne zai iya kashewa Futuha saboda dadin angoncin da yake kwasa. Ba ɓata lokaci aka soma shirin yi mata passport da sauran abubuwan da ya kamata ma tafiya. Sai bayan kammaluwar komai sannan washegari ta yi nufin zuwa gidansu ziyara da kuma sallama. A ɓangaren Tasleem ma, babu laifi Hamza na iyakar kokarin faranta mata, sun ci soyayyarsu yanda ya kamata, ba ta dora koda ruwan zafi daga gidan iyayensa ake kawomusu abincin safe zuwa dare. Sai da ta yi sati cif sannan suka kara shiga ta gaida Mahaifiyarsa da abokan zamanta su uku. Gidan dai babban gida ne mai tarin yara da jikoki. A ranar har gidajen facalolinta sai da ta shiga, wasu sun kata tarbar kirki yayinda wasu kallon tara saura suka dinga yi mata. Haka tattara ta dawo gida. A ranar da suka yi waya da Futuha take ba ta labarin tafiyarsu Dubai hankalinta ya yi mugun tashi, ji tayi inama ita ce ta samu wannan damar. Ciki-ciki ta yi mata murna, dama tana jin haushin hotunan da take karo da su a media na Futuhar da mijinta yanda kowa ke santin kyawun da suka yi. Futuha ta ce ta shirya za su zo har gida su yi mata sallama. Ba ta ma iya amsawa da toh ba ta katse kiran gami da jan tsaki. Ya yi daidai da shigowar Hamza falon, hannunsa rike da ledoji ya yi mata siyayyar kayan sanyi da kaza. Har ya karaso kusa da ita ba ta san ya yi ba tsabar ta lula duniyar tunani. Sai da ya ajiye ne ya dan zunguri kafaɗarta kadan. Ta dubeshi, murmushi tattausa ya sakar mata, itama ta bishi da na yaƙe. Rungumo kafaɗarta ya yi. "Tunanin me kike yi ne haka? Har na shigo da favourites dinki amma ba ki lura ba?" Ta kai duba ga ledojin dake ajiye, har gumin sanyi ɗaya yake, sai ta ji ta kasa farin ciki da abin da ya ajiye din duk da cewa a baya har so take ya kawo su ta dinga tsalle kenan tana rungumeshi. A yanzun kuwa ko ɗigon annashuwa ba ta yi ba. Sai jikinsa ya yi sanyi, ya kamo yatsun hannunta. "Wai me ya sauyamin ke haka? Ko bayan fita na kin yi baƙi ne?" Dama kiris take jira ai sai ta tunzura ta yakice hannunta. "Me kake nufi?! Na yi baƙi sun zugani ko sun ɓatan rai? Yan gidanmu kake nufin sun zo ko ƙawayena?! Au zargina kake yi akan wani zai iya zuga ni akanka? Ai ba sai an zuga ni b, ni mai zuga kaina ce!" Gaba daya ya razana, ya yi jim yana kallonta, a iya saninsa babu inda maganarsa ta kai nan. Me ya kawo batun zuga kuma ana zaune kalau? A ina ya ce hakan? "My Noor, me ya kawo zancen zuga? Ban gane inda kalamanki suka dosa ba?" Sai a sannan ta ɗan dawo hayyacinta. Ta ja guntun tsaki ta zauna. Nan da nan kuma Hamza ya ɗan sauya fuska. "No please, zan dauki komai amma ban da raini, ina maki warning na farko da karshe, bana son tsaki. Kar ki kuma." Ba ta ce komai ba face turo bakin da ta yi, sai ya ji ma gaba daya ta ɓata masa rai kawai ya mike ya yi daki. Ta bishi da harara, ita ta sani ko wannan motar tasa zai siyar ba zai ishe su su je Dubai har su kashe kudade irin wanda Futuha zasu kashe ba. Ta san muddn Futuha ta yi wannan tafiyar to fa kanta zai fasu, za ta ƙara jin wani girman kai har ma ta dinga yi mata fi'ili iri-iri. Don haka hankalinta ya tashi, ga babu yadda ta iya, nata mijin ba ta tunanin ma ya taɓa taka farfajiyar Airport balle ya shiga jirgi. Ta ja tsaki karo na biyu. Madadin ta kwashe ledojin da ya kawo ta adana komai koda ba lokacin za ta sha ba, kawai sai itama ta bar su anan ta shige nata dakin ba ta ko bi ta kansa ba don har sannan zuciyarta zafi take yi, hassada mugun ciwo ne. *** Tun karfe goma Humaira ta je kasuwa yin cefane bisa umarnin Mami wacce ke ta shirin tarbar Futuha da za ta zo. Tana dawowa kicin kawai ta shiga ta soma shirin girki, tuwon semovita miyar kuɓewa danya wanda ya ji nama da busassan kifi, shi Futuhar ta ce tana muradi sai ko lemun kwakwa. Wuraren karfe ɗaya ta kammala komainta jera a saman tire ta kai falon ta ajiye. Daga nan ta koma dakinsu. Ita ko kusa ba ta wani zumuɗin ganin Futuhar kamar yanda su Ummita ke yi. Tun dawowarsu daga makaranta jin ance tana hanyar zuwa suke faman rawar ƙafa. Ai kuwa ko awa ɗaya cikakka ba su yi da dawowa ba sai ga mota direba ya kawo ta har farfajiyar gidan. Da gudu Raihana ta fice tarbar yar uwarta, itama Ummita ta mara mata baya a nutse take tafiya. Humaira sai ta ja guntun tsaki ta cigaba da danna wayarta tana ganin sabbin likes da comment da sabon hotunan da ta dora na girke-girke suke samu. Ta shagala sosai sai ji ta yi an warce wayar, ta juya da sauri. Raihana ce. Dariya ta yi mata. "Ki taso inji Mami ku gaisa da Futuha. Ashe Dubai za su wuce da mijinta sati na sama." Ta ɗan yi murmushi, ba ta fiye son kushe su a gaban Raihana ba don haka ta taya murna a fili. "Kai amma na mata murna, Allah ya kai su lafiya. Muje toh. Bani wayata kuma." Raihana ta mika mata suka yi dariya. A falon ta iske Futuha zaune, masha Allah ta ƙara ƙiba da kyau, kumatunnan har wani kyalli suke yi. Wani arnen leshi ne a jikinta fari da ruwan toka ya sha aikin stones sai faman baza ƙamshi take yi, hira sosai take yi da Mami. Ƙassim ma na zaune banda Yassar da Dawud wadanda sula tafi Camp a can garin Jigawa. Humaira ta karaso ta gaida ta, ta amsa mata tana yamutse fuska kaɗan daga nan ta maida hankali ga uwarta su na cigaba da hira. Humaira wacce dama ta san a rina kawai sai ta mike ta saci jiki ta koma daki, Ummita ta mara mata baya. "Ke kuwa daga gaisuwar sai ki taho?" Harara ta dan watsa mata. "Idan na zauna me zan mata? Goyata zan yi? Ai dai kinga yanayin amsar gaisuwar da ta yimin ko? Toh ni kuwa marar zuciyar ina ce da zan tsaya?" Ajiyar zuciya Ummita ta yi. "Allah ya kyauta, kinsan Allah na yi zaton aure zai sauya su, amma naga har yanzu da sauransu." Taɓe baki Humaira ta yi ta ce. "Toh yaushe ma aka yi daren? Ke ta dai samu duniya ne kawai shiyasa abinta ya ƙara gaba. Nifa kinsan ba abin da ke ban mamaki face irin yadda matarnan ba ta yiwa kanta faɗan ta nutsu ba take faman ɗora hotunanta a media. Shi ma mijinnata soloɓiyo da ya biyemata." Ummita ta kama baki har da ɗan waigawa ta ga ko babu wani a kusa da ya ji kalamin Humaira. "Kinga ki rufamana asiri. Mutum ba shi ya ga zai iya ba? Kar ki manta har da shi din Ogan nata ake wannan taɓargazar kinga kuwa abu nasu maganin a kwaɓe su. Wayewar yanzu ce ta shirme ta zo da haka." Dariya Humaira ta yi. "Kenan kema haka za ki yi da Sahabinki ko?" Duka ta kai mata a cinya. "Allah ya sauwaƙe, mu aurenmu ko party ba zamu yi ba, walima kawai a cikin gida ta isa. Albarkar auren muke nema. Hum, nifa yanzu duk ya dameni akan zai turo a sanya rana kafin nan da shekara idan mun kammala nayi Candy a yi auren. Wallahi kwanakin nan duk akan hakan muke ta rikici. Na rasa yanda zan ɓullo masa." Humaira ta mike zaune sosai. A duniya ta tsani ta ga Ummita cikin damuwa ko na sakan, don haka ta ce. "To me kike jira? Me zai hana ki ba shi wannan damar? Kina sonsa yana sonki fa. Kuma sa rana ba shi ne auren ba, don Allah ki yi shawara da Mami tunda kinga ta san da zamansa, na tabbata za ta goyi da bayan ya turo." Ummita ta zubamata idanu ta yi shiru cike da damuwa, ga mamakin Humaira kuma sai kawai ta ga hawaye sun soma zuba daga kwayar idanunta. "Lafiya? A maganata akwai wacce ta maki zafi? Kiyi hakuri don Allah kinji?" Girgiza kai Ummita ta yi, "Ko ɗaya Humaira, ke ce dalilin da yasa na kasa ba Sahabi damar turo iyayensa. Wallahi bana jin dadin mafarkaina a kanki kwanakin nan. Humaira na damu da rashin bada ƙofa ga kowane saurayi ya nemi aurenki da kike yi. Ba na so na yi aure na bar ki a wannan halin. Gaba daya na damu." Shiru Humaira ta yi, toh ita da kamar abin yana damunta kamar kuma ba ta damu ba. Ta ma kasa fahimtar komai sai kawai ta dubi Ummita a sanyaye. "Kin manta ke ce me nusar da ni idan na ɓata? Ke ce me ƙarfafamin gwuiwa akan imani da Allah a irin wadannan lokutan? Toh ki sani, har ga Allah ba na jin son kowane namijin ba balle na ji son auren a raina. Hakan ba yana nufin wata matsalar ba, ki kaddara lokaci ne, duk sadda na ji son wani a raina, watakila..." Sai kuma ta ma rasa me za ta ce, kawai sai ta sunkuyar da kai ta riƙe hannun Ummita cikin nata. Karon farko da ta ji tana hawaye, hawaye mai dalili ba wanda ta saba yi a irin gaɓar nan babu dalilin ba. Ummita sai ta ji tausayinta ya lulluɓe ta, Humaira ai itama da zuciya a kirjinta. Dole akwai abin da ke damunta amma ba ta faɗa, ba ta magana sai dai ta yi shiru idan sun taso da zance ta maida su wasu cali cali. "Ki tayani addu'a Ummita, ina da damuwa amma ban gama gane kan damuwar ba. Ina da abin faɗi, amma zuciyata na kwaɓa ta a koyaushe akan bai kai abin magana ba nayi shiru kawai. Na rasa meke damuna, idan na ce zan zurfafa tunani sai jikina ya hau rawa, kaina ya hau sarawa. Watakila iyakar abin da zan iya faɗa kenan. Nidai ki dinga sanya ni a addu'a." Ummita ta ɗan rungumeta suna kuka. Kowannensu da kalar tunaninsa, dakyar suka rarrashi junansu suka share hawayen. Sai kuma Humaira ta cigaba da karfafa mata gwuiwa akan ta bari Sahabi ya fito a yi magana. Ta kara da fadin. "Kinga itama Raihana zan ce ta amince ta bar Imran ya turo. Shikenan sai ku bar min gida na huta." Ummita ta harareta, ita kuma ta yi dariya tana kokarin danne radadin ciwon kan da take ji gudun kar ta kefa Ummita a wata sabuwar damuwar. Koda Ummita ta fita don amsa kiran Mami wacce ta turo Muhsin, sai ta zame ta kwanta ta runtse idanu tana tauna maganganun da suka yi da Ummitar, hannuwanta riƙe da kan da ke faman sara mata. Tana nan kwance har bacci ya sure ta, Raihana ta zo ta tashe ta akan ta je Mami na kira. Ta ci sa'a zuwa lokacin ya rage ciwon, don haka dankwalinta da ya zame ta maida ya rufe kan ta fita. Anan fa Mamin ta mata umarnin ta shirya za ta bi Futuha don ta taimaka mata da girki abokan mijinta za su je gidan nan zuwa jibi. Kamar ta cewa Mamin a bari mana sai jibin ta je ta dawo, amma ba ta son jan musu da ita kawai sai ta ce toh. Ranta na zafi haka ta shirya ta bi Futuha suka tafi. Tana ji Futuhar na yiwa Tasleem waya wai gatanan a hanyar gidanta, ita dai ba ta ce mata uffan ba sai kallon window da take yi zuciyarta na zafi, wani sashi na zuciyar na kokarin ce mata Mami ba ta kyauta mata ba yayinda wani gefen ke kwaɓarta yana nusar da ita irin kirki da mutuncin Mamin. Bai kyautu ta munana mata zato ba. Da haka suka karasa gidan Tasleem. *** A yau Murja ta yi niyyar zuwa sashin Fadeel don ta rantse ko ta yaya sai ya saurareta ya ba ta damar amayar da abin da ke ranta ido da ido. Kwanakinnan ko bacci kwakkwara ba ta iya yi tsabar so da tunaninsa da ke neman zautar da ita, wannan ya sa ta zuri takalmanta kawai ganin an yi Magrib tana kuma da tabbacin yana nan ta nufi sashinsa. Yana zaune ya kafe manyan frames guda biyu da aka yi mishi na hoton Humaira da idanu yana kallo. Ta yi kyau matuka, daya tana tsaye ne a farfajiyar Manal Event Centre ranar bikin su Futuha, dayan kuwa wanda ta dauka da sallah ne ba ta san ma an yi hoton ba ta rike kafaɗar Ummita tana dariya mai bayyana wushiryarta. Ta yi kyau ainun, masifar son da yake yiwa hotunan ne ya sanya aka wanko da zummar zai adana duk radda suka yi aure ya kafe su a ɗakin baccinsa. Uzurin bandaki ya kama shi, ya mike ya shige ƙuryar dakin don kama ruwa. Daidai lokacin Murja ta hau kwankwasa ƙofar dakin, tana ji kamar ta tura kanta ciki ko ba izninsa. A yau ta kai maƙura a so da kauna da begen ganinsa.Ganin Fadeel ba shi da niyyar buɗewa sai kawai ta murɗa ta tura kanta falon. Babu kowa, ta ɗaga ƙafa da niyyar bin bayansa zuwa ɗakin, sai wata zuciyar ta kwaɓe ta. Ba ta son ɓata rawarta da tsalle, har ta juya za ta bar falon idanunta ya sauka saman hotunan dake ajiye. Jikinta har rawa yake yi ta karasa ta ɗauka. Ji ta yi kirjinta ya yi wani irin bugu da karfi, numfashinta kuwa dakyar ta iya jawo shi ta furzar. Ita ce! Humaira mai Deelsha's Delicacies, ita ce dai masoyiyar da Fadeel ke so. Kafin ka ce me idanuwan Murja sun soma zubar da hawaye. Maƙoƙon baƙin ciki da tsantsar kishi suka tokare kirji da maƙoshinta. Ta tuna ko ɗazun sai da suka gaisa ta waya da ita, ashe ba ta sani ba da rival dinta take mu'amala? Ji ta yi kwakwalwarta na rayamata kawai ta tarwatsa hoton a ƙasa idan ya so komai ta fanjama fanjam! Aikuwa ta ɗaga a zuciye da wannan niyyar amma ba zato ta ji tsawar Fadeel a kanta. Ya ƙaraso ya fisge hoton a hannunta, murya a ɗage ya ce. "Me ya kawoki ɗakina?! Uban waye ya baki iznin kutsowa ba tare da sanina ba?" Kamar ta ce mishi Ubanka ne amma ta danne, kishi dai bala'i ne. Ta kasa samun nutsuwa, ta kai hannu ta dafe kai har lokacin kuka take, ko kaɗan tsawar Fadeel bai razanar da ita ba. Wannan kaɗan ne akan yadda take jin raɗaɗin azabar kishin Humaira a zuciyarta. Dakyar ta iya tattaro kuzarin da ya yi mata saura ta soma magana. "Dama akan wannan yarinyar ka ke wulaƙanta soyayyata? Yaya Fadeel ina sonka ka sani amma ka ke nuna kamar ba ka san da zamana ba. Meyasa? Da me ta fi ni? Me za ta nunamin? Wallahi Yaya Fadeel muddin ka aureni zan maka fiye da abin da kake tunanin samu daga wannan yarinyar." Ransa ya ɓaci ainun. "Ke a naki tunanin koda ace auren zan yi don kyau ko suea  kin kai na aureki?! Toh ke ba komai ba don ba ki da suffar da zan gani har naji kwaɗayin aurenki. Daga yau ina maki gargaɗi ki fita harkata, na rantse maki duk sadda na ƙara ganin ƙafafunki a nan sai na ɓaɓɓallaki. Get out!!" Ta razana sosai, ga baƙaƙen maganganun da ya fesamata ga kuma tsawa, ta kalleshi tana jin ranta na suya sannan ta kara kai duba ga hoton Humaira kafin ta juya a guje ta fice daga ɗakin. Fadeel ya yi tsaki ya zaune yana jin zuciyarsa na zugi. Da ace yana da ikon fitar da yarinyar daga gidannan da tuni ya aiwatar. ***   Tasleem ta buɗe ƙofar kyauren, suka shigo. Humaira  ta bi ta da kallo, ba laifi itama ta yi kyau ta kara haske. Ta rungume Futuha suna murnar ganin juna, ba ta ko kalli Humaira ba suka shiga ciki zuwa ɗaki suka bar Humaira a falo zaman jira.   "Shegiya, haka gidanki ya yi kyau?" Cewar Futuha, Tasleem ta ji zancen kamar zagi hakan ya sa ta ja tsaki. "Ba dai baƙa kike faɗamin ba ko? Bayan naki gidan an ce ya kere nawa nesa ba kusa ba." Ta yi dariya. "Abar wannan zancen, ya ne? Kin ji labarin tafiyarmu ko? Kai Tasleem burina zai cika zan shiga jirgi nayi selfie, na kuma ga wurare da dama irin yadda su Ƴar Snow suke gani su na hoto suna mana yanga." Baki buɗe Tasleem ke kallonta cike da ɗumbin mamaki. "Futuha, anya kina cikin hayyacinki kuwa? Ƴar Snow dai da ta yi maki baƙin ƙazafi ita kike farin cikin za ki zarta? Wallahi ina rabaki da shiga harkar ƴan Tiktok, lallai idan kika sa kanki cikinsu sai kin yi kukan da na sani fiye da na baya." Futuha tun da Tasleem ta soma magana take faman doka murmushi, ta ba wa ranta cewa kawai baƙin ciki ne ke cin Tasleem saboda a duniya ta fi ta burin hawa jirgi da fita ƙasar waje sai kuma ya kasance ita ce ta samu wannan damar, ta ba kanta lallai Tasleem dai da biyu take wannan sabuwar nasihar. "Ƴar uwa kenan, ki bar wanda ya samu duniya ya ci abinsa da tsinke, ai komai da kike gani lokaci ne. Wasu ma damar da suka jima su na burinta kenan amma ba su samu ba. Mu kuwa tun da Allah ya kashe ya ba mu kinga kenan sai mu dama kununmu yadda muka ga dama." Tasleem ta yi dariyar yaƙe. "Ai shikenan, Allah dai ya kaiku lafiya. Nidai please and please ki yo min tsarabar dogayen riguna." Futuha ta yi farr da idanu tana dariyar itama. "Kar ki samu damuwa ƴar uwa, ai ke tawa ce." A falon kuwa, Humaira na nan zaune tana karewa gidan kallo aka yi sallama aka shigo. Ta ɗaga kai, wata budurwa ce da ba ta wuce sa'arta ba ta shigo kai tsaye ta nemi wuri ta zauna suka gaisa fuska a sake. "Anti Tasleem na nan?" Humaira ta amsa da eh. "Ok, bari na jira fitowarta a nan. Kema ƙanwarta ce ko?   Na tuna fuskarku da biki, ku uku cikin shiga iri ɗaya aka ce sisters dinta ne." Humaira ta ɗan yi murmushi. "Eh, ƙanwarta ce." "Ok, amma ba Uwa ɗaya ba? Naga su kamar buzaye ne." Humaira dai ta ɗan yi jim, ta rasa wannan maganganun da ake mata na babu gaira babu dalili. Sai a nan kuma ba ta amsa ba. Budurwar ganin haka ta sauya darasin. "Allah ba ƙaramin so Yaya ke yiwa Anti Tasleem ba. Akwai wata cousin sister din mu da ke masifar sonsa amma ko kaɗan ya ce shi ba ya yinta, kuma fa ..." Sauran zancen ya maƙale a fatar bakinta sakamakon fitowar Yayannata daga ɗaki. Humaira ta gaida shi, ya gane fuskarta sarai don takan fito kawo masa abin motsa baki lokacin da yake zuwa zance wajen Tasleem. Ya amsa gaisuwar fuska a sake, daidai lokacin kuma su Tasleem suka shigo falon. Nan aka hau sabuwar gaisuwa da Futuha anan take sanar da shi batun tafiyarsu Dubai da mijinta. Ya yi mata murna kwarai. Daga bisani suka yi sallama har bakin mota suka raka su, sai bayan sun tafi ne suka koma ciki. Har lokacin Hamza bai sakarwa Tasleem ba sakamakon haushinta da yake ji na irin kalaman da ta yaɓa masa. Ita kuwa budurwar ƙanwar tasa mai suna Fauziyya ba wani jimawa ta yi ba, daman shigowar don ta ganewa ƴar uwarta Ramlat irin zaman da ke gudana a gidan Hamza wanda har gobe yana nan daram a ranta. Akwai kuma da yawa cikin yan uwansa masu taya ta kishin Tasleem. Ciki kuwa har da Fauziyya. *** Daki guda na saukar baƙi Futuha ta ba Humaira, nan ta zauna. Madaidaicin gado ne a ɗakin sai kafet a shimfide da bandaki a ciki. Ya yi ƴar ƙura kaɗan ba ta damu a haka ta kakkaɓe bayan ta idar da sallah ta yi kwanciyarta tana danna waya. Tana nan kusan awanni biyu wuraren ƙarfe tara na dare ta ji shigowar mota. Ba jimawa kuma wayarta ta ɗau ƙara, Futuha ce. Ta ɗaga da sallama, ba ta ko amsa ba ta ba ta umarnin ta zo falo ta gaida Maigidan. Kashe kiran ta yi ta mike tana jan guntun tsaki. Mace ko sanin darajar sallama ba ta yi ba, an yi amma madadin ta amsa sai ta yi share. Hijabi ta sanya ta fito, su na nan falon dake saman, yana zaune ita kuwa tana saman cinyarsa tana zuba ruwan shagwaɓa. Sallamar da ta yi har aka amsa bai sa sun sauya a yanayin da suke ba, Humaira sai ta sunkuyar da kanta domin ba ƙaramin kunya suka ba ta ba. Wannan wace iriyar fitsara ce? Koda dai dama ta riga da ta san wace ce Futuha, matar dake tsayuwa gaban waya ta tiƙi rawa ta ɗora a midiya, ai kuwa ba za ta ji kunyar idanun kowa ba idan tana tare da mijinta. Haka Humaira ta ayyana a ranta. "Kika wani tsaya daga ƙofa, Malama ki ƙaraso ki gaida shi." Muryar kamar ba ta Futuha ba don gaba ɗaya ta wani ƙanƙantar da ita irin yadda ta saba idan tana waya da samari a baya. Humaira ta karasa shigowa ba tare da ta kallesu ba ta gaida Alhaji Yakubu, ya amsa murya a sake. Daga haka ta miƙe za ta yi ciki, Futuha ta dakatar da ita ta hanyar nuna mata wata leda akan ta ɗauka ta ci. Ta dauka ba musu ta fice daki. Ita dai mamaki kawai take yi na irin wannan wayewar zamanin. Tana shiga ta buɗe, shawarma ce a naɗe a paper sai ko gashin kaza rabi, ta cinye tas don dama yunwar take ji ta wanke hannu da baki ta dawo ta nemi makwanci. *** Kwanakinta a gidan Futuha babu abin da take yi sai ɗirkar aiki, akwai ƴar dattijuwar dake zuwan yini tana tafiya. Takan kama ayyukan gyaran ƙasa, ita kuwa Humaira ta gyara saman tas, duk wata dauɗa da Futuha ta bari tun zuwanta babu gyara kaca-kaca sai da ta dawo yana kyalli. Ga girkuna masu dadi da ta ke yi musu safe da yamma, Futuhar da ba ta ɗan sakarwa Humaira fuska, tsabar jin daɗin yadda ta ke mata bauta sai ga shi ta soma saki, babban ƙudurinta kuma bai wuce idan sun dawo daga tafiyar da zasu yi ba ta yi dabarar da Humairar za ta dawo ƙarƙashinta gaba ɗaya. Ana gobe su Futuha za su tafi ne, Humaira ta fito ta zagaye can bayan ɗakunan inda anan ne aka yi wasu shuke-shuke masu ban sha'awa, a lokacin babu koda a ɓangaren Futuhar, Baba Furera ta wuce gida, Futuha kuwa an tafi gyaran gashi da jan ƙunshi. Hakan yasa kaɗaici ya yi mata yawa, ga dai wuta nan daga safe har dare amma ta gaji da kallon balle kuma danna wayar. Wannan ne dalilin zagayawarta baya tana kallon shukokin masu burgewa da ɗaukar ido. Tana nan tsaye tana murmushi tana shafar su gami da shinshinar ƙamshin da ke jikinsu, ta kai duba ga sararin samaniya yadda hadari ya yiwa garin ƙawanya, a hankali ta lumshe idanu saboda jin daɗin yanayin. Sai dai kuma lokaci guda kamar wacce aka mintsila ta bude idanuwanta tarr jin kukan jariri da ke tashi sosai. Ta kai duba ga inda sautin ke fita har ƙirjinta na bugu da sauri-sauri. Sashin dai da aka ce na uwargida ne, daga nan ta dinga jin kukan na tashi. Cikin sauri da gudu-gudu ta bar bayan ta dawo bangaren Futuha, daidai nan suka yi kiciɓus da mai ba shuka ruwa. Ta dube shi, ganin yadda take faman haki ya sanya shi tambayar ko lafiya. Da yatsa ta yi mishi nuni da hanyar ɓangaren Uwargidan da ake kira Hajiya Saratu. "Me aka yi a wurin?" Ta haɗiyi miyau. "Da mutane a ciki ne?" Sai tambayar ta ba shi mamaki. "Hala ke baƙuwa ce? Ai ɓangaren Hajiya ne, tana nan. Ko wata biyu ba ta yi da haihuwa ba." Sai hankalin Humaira ya ɗan kwanta amma kuma sai ta hau wani sabon mamaki da al'ajabin. Don haka ta kuma dubansa ta ce. "Dama ta dawo daga tafiyar da ta yi ne?" Ya yi ƴar dariya. "Ko kusa, babu inda ta je tana nan. Ai da yake ba ta fiye fita ta wannan ƙofar ba, akwai ƙofa ta baya, ta fi fita ta can idan ta tashi zuwa unguwa. Kuma gaskiya dai ni zan iya cewa tun ma da ta haihu ba na tunanin na ji ance ta fita. Koda dai ba ganewa ake yi ba tunda Hajiya motar haya take shiga." Ya ƙarashe da wani irin jimami, har ya buɗe baki zai ƙara magana sai kuma ya girgiza kai kawai ya fice. Humaira ta bishi da idanu tana mai cike da al'ajabi. Idan maganganunsa gaskiya ne? Toh me Alhaji Yakubu yake nufi da ɓoyewa? Ita dai ta ji Futuha ta ce Uwargidansa ba ta nan su na Dubai da yaranta. Toh idan hakane su ne a gidan, meyasa ko da wasa ba a ganin gilmawar yaranta tunda dai ai yaro ba zai yarda da rayuwar ƙulle ba? Amsoshi ne da ba ta da amsar su kawai sai ta ja ƙafafunta da suka yi wani irin sanyi ya bar wurin. ***Humaira ta kama bakinta koda wasa ba ta sanar da Futuha komai ba, ba ta ga dalilin sanar da ita abin da bai kamata ta ji daga bakinta ba wannan ya sa ta bar abin a cikinta. Washegari da misalin ƙarfe biyun rana sai ga su Raihana a gidan sun zo rakiya Airport, daga nan direba zai mayar da su gida gaba ɗaya.   Jirgin dare ne wannan ya sa sai bayan magriba suka hau shirin tafiya, Humaira ta tattara kaf kayanta, dama ta gaji da gidan babban burinta shi ne kawai ta koma cikin ƴan uwanta. Sakewar da Futuha ta yi da ita bai sa ta iya sakin jikinta ba don ba ta saba da shi ba, ta fi ganewa rayuwarsu ta baya yadda suke hantararta a abu ƙalilan amma sam zuciyarta ba ta amince da wannan sauyin ba. Ƙarfe goma jirginsu ya tashi, su kuma aka kai su gida. Humaira ranar kamar an tsoma ta a aljanna, farin ciki biyu ya haɗe mata, na farko bai wuce dawowarta gida ba daga zaman uƙuba da bautar da ta ke yi a gidan Futuha, na biyu kuwa jin daddaɗan labari daga bakin Raihana cewar iyayen Sahabi nan da kwanaki biyu za su zo tambayar auren Ummita. Ranar dai bacci ɓarawo ne ya sace su don raba dare suka yi ana hira. ***   Anna ta dubi Mami ranta a tsananin ɓace ta ce. "Ke kam da a asibiti na haihu zan iya rantsuwa sauyamin ke a ka yi wannan ba jinina ba ce. Ni dai kaf zuri'armu babu macen da za ta aikata wanan abi da kike aikatawa na rashin sanin ciwon kai da kuma rashin zuciya. Wannan rawar ƙafa da murna da kike yi ko kuɗin auren Raihana aka kawo sai haka." Tana kai wa nan ta ja tsaki, Mami ta yi ɗan murmushi. Kawo kuɗin gaisuwar iyaye da sanya rana da aka yi na Ummita a yau ne ya sosa zuciyar Anna take wannan zantukan. Ita idan irin hakan ma abu na farin ciki ya afku ga Humaira ko Ummita har ba ta kaunar ya zo kunnen Anna saboda irin waɗannan bakaken kalaman da ba ta haƙura ta bar wa cikinta sainta furzar. Kamar ko yaushe a kwanakin nan, wannan karon ma Mamin shiru ta yi ba ta ce uffan ba. Itama Annar don kanta ta gaji ta bar zancen. Ta sanyo wani batun bayan ta kora ruwa a cikinta. "Af, yar uwarki tana nan tafe ƙarshen watan nan." Cike da mamaki Mamin ta dubi Anna ta ce. "Jannat kuma? Me zai kawo ta nan kusa alhalin yara ba hutu suka yi ba?" "Toh kina baƙin ciki da zuwan nata ne?" Jin haka da sauri Mami ta ce. "Ko ɗaya, Allah ya huci zuciyarki. Allah ya kawo ta lafiya." Anna ta amsa da amin, ganin tana neman ɗora maganar ɗazu sai kawai Mami ta miƙe tana mai ba ta uzurin zuwa wurin mijinta. Yamutse fuska kawai Anna ta yi ba tare da ta ce komai ba. *** Alhaji ne zaune saman darduma a barandarsa yana latsa waya, isowar Fadeel ne ya sanya shi ajiye wayar ya mayar da hankali garesa. Bayan amsa gaisuwarsa ya gangara kan batun da yake son yi. "Babban dalilin kiranka bai wuce kan maganar aure ba. Lokaci ya yi da za ka tsaida hankalinka wuri guda ka nemawa kanka abokiyar rayuwa. Kana gani dai ga ɗan uwanka nan har an soma batun zuwa gaisuwa da roƙon iri. Toh an kai lokacin da zubamaka idanun da aka yi ya kamata ace ya zo ƙarshe, ga baffanninka nan a ganinsu har da laifina a ƙin matsa maka da zancen. Har cewa suka yi idan babu dama ka je can gida ka zaɓa cikin ƙannenka wacce ku ka daidaita sai a yi magana. Rashin ba su goyon baya akan haka ba yana nufin na amince da zaman naka hakanan ba Fadeel. Shekaruna gaba suke ƙara yi ba wai baya ba, lokacin ƙure mana yake ƙara yi. Alhamdulillah ka fara gini, koda ace bai yi nisa ba, ina da tabbacin nan da shekara dai ka haɗa komai. Kai yanzu ɗan uwanka ba abin koyi ne gareka ba? Ka gwammace kana ji kana gani ya yi aure ya bar ka nan zaune? Har zuwa yanzu babu wacce ka tsayar?" Fadeel ya ƙara sunkuyar da kansa, ya sani dama tun da har zancen auren Ibb ya tashi, toh fa Daddy da Alhaji ba za su ɗaga masa ƙafa ba. Yana kuma da tabbacin yadda Alhai ya yi mishi magana, to fa shi ma Daddy zai ɗora da nasa bayan kwanaki. "Ba ka ji ne?" Ya ɗago ya ɗan ja numfashi, babu amfanin ɓoye-ɓoye, babu kuma alfanun faɗin gaskiyar da za ta jaza masa rabuwar da bai shirya ba da Humaira. Yana tsoron ya kasance idan ya zayyana komai yadda yake tafiya a yanzu, ran Alhajinsa ya ɓaci ya nemi ya fita a hanyar Humaira, wannan ne dalilin da ya sanya shi yiwa zancen kwaskwarima. "Ka yi hakuri Alhaji, ba wai babu wacce na tsayar ba ne. Akwai, sai dai yarinyar nan da watanni bakwai zuwa takwas za ta kammala makarantar da take zuwa, ta kuma roƙe ni na ba ta dama har su kammala. Wannan shi ne dalilin da ya hana ni gabatar da ita a wajenku. Ina neman ƙarin lokaci zuwa sannan, idan Allah ya yarda ba zan ba ku kunya ba." Alhaji ya ɗan yi jim, ba haka ya so ji ba, ya so ace kawai Fadeel din ya ba da damar a nemi auren a haɗa da na ɗan uwansa (Ibb) amma hakan ma ya ji daɗi tunda dai akwai wacce yake so. Don haka sai ya ɗan saki fuska. "Shikenan, su iyayenta sun sani cewa kana neman auren ɗiyarsu?" Ya ji gabansa ya faɗi, anan kam ba ya jin zai iya ɓoyewa don haka ya girgiza kai ya furta kalmar a'a. Murmushin manya Alhaji ya yi. "Fadeel kenan, to kai ban da ma abinka, yanzu idan aka tashi mahaifin yarinyar ya aurar da ita ga wani sai ka ce ya yi maka rashin adalci ko?Idan ba kai ba, ina aka taɓa wannan wautar? Kana son yarinya amma ka kasa gabatar da kanka wajen iyayenta? A zatonka sun san da zamanka ne kawai saboda kana zuwa hira wurin ɗiyarsu? Me zai hana mu ka bamu damar tura wa gidannasu a san da zancenka?" Ya ɗan sosa ƙeya kaɗan, inama hakan abu ne mai sauki, inama kuma idan an aikata ba zai ga bore daga Humaira ba wadda yana da tabbacin a yanda take gudunsa za ta iya cewa ta fasa auren ma baki ɗaya, ai ba don haka ba da gudu zai yi na'am da shawarar Alhaji. Sai dai kuma ya sani, ba abu ne mai sauƙi ba. "Ayi hakuri zuwa lokacin da na faɗa. Ni kuma zan yi kokarin samun mahaifinta mu gaisa." Alhaji ya ji abin wani iri, kamar ya yi magana sai dai ya fasa. Can kuma sai ya ɓige da nasiha akan kar ya biyewa soyayyar shirme da ake yi yanzu tsakanin matasa na wannan zamani. Abin har ya so ba Fadeel dariya don shi kam ya lura kamar ma Alhajin tunaninsa wani wuri daban ya tafi. Da wannan suka rufe babin zancen suka hau tattaunawa akan Hannatu dake shirin zuwa Kano don ganin mahaifinnasu da ta kwashi lokaci ba su sanya juna a ido ba. *** Anti Amarya ta shiga har ɗakin Murja dake kwance tana juyi, tsayawa ta yi gaban gadon tana ƙaremata kallo rai a kuntace sai kuma ta ja mugun tsaki ta soma magana tana ji tamkar ta shaƙo ta. "Aikin wofi kike yi fa Murja, na faɗamaki ke za ki wahala a banza muddin ki ka ce ba za ki kokarta ki ɓoye kishinki a kan Humaira ba a gaban Fadeel. Ke ba ma kishin ba, hatta da son da ace za ki yi hakurin dannewa babu abin da ba za ki iya cimmawa ba. Ke an faɗamaki koda ace asirin za ki yi masa zai ci shi idan ba ki kasance gwanar kissa ba? Ai komai ɗan dabara ne. Yanzu kiga, daga ganin hoto gaba ɗaya kin susuce har abinci sai kin yi dagaske kike iya ci? Yanzu idan kuma ace zancen auren kika ji ya za ki yi da ranki?" Murja ta miƙe zaune, gaba ɗaya idanunta sun kumbura. Ta dafe kirjinta. "Wallahi Anti ji nake yi kamar kirjina zai fashe, Anti ban san haka kishi yake da tsananin zafi ba sai akan Fadeel. Na rantse a yadda nake jin zuciyata zan iya sa wuƙa na tsire Humaira da ranta muddin aka wayi gari ta kasance matar Fadeel balle kuma har abada hakan ba za ta afku ba idan har ina numfashi a doron ƙasa." Kausar dake bakin ƙofa wacce ta yi niyyar shigowa don duba lafiyar Murjar da ta ji Anti Amarya na cewa ba ta da lafiya, kawai sai ta ja baya ta juya jin maganganun da suke fitowa daga bakin Murja, iyakar abinda ta ji kenan, koda ace ma Anti Amarya ta yi magana kafin nan toh ita kam Allah bai nufe ta da ji ba. Ita gaba ɗaya gidan ma ya ishe ta, Fu'ad wanda ya je Abuja da niyyar kwanaki uku, sai gashinan har ya cinye satin ya ƙara shiga wani satin. Burinta kawai ta bar gidan ta koma nasu, ita sam ba ta gane rayuwar da ake gudanarwa a gidan ba, Anti Amarya dai lamarinta kamar gaske kuma wasu lokutan takan ji kamar kawai wasan kwaikwayo ne. Ga Murja a gefe wacce kallo dubu idan za su yi wa juna a rana babu abin da take samu a wajenta sai harara. Su Khadija ne abokan hirarta sai kuwa wayarta, sannan Fadeel wanda ba kasafai yake shigowa falon ba. Hakan yasa duk ta ke jin ta a takure. A daki kuwa, motsin mutum ne ya sa Anti Amarya saurin fitowa, bayan Kausar ta hango lokacin da take barin wurin, ta dawo ciki ta rufe ƙofar. A fusace ta kalli Murja. "Kin gani ko? Zai wahala idan Kausar ba ta ji abin da muke tattaunawa a kai ba. Daɗina da ke ba kya iya ɓoye abin da ke ranki ko na sakanni. Kin san ba mu kaɗai ke zaune a gidan ba amma ki yi ta faman suɓul da baka. Mtsw, don Allah ji yadda kika maida kanki, babu wanka balle kwalliya, akan ɗa namiji kamar wacce ba ta yi karatu ba kina son ki zautar da kanki. Ke idan da ace ni ce ke, ai wannan ne lokacin da zan soma shigewa Humaira da hujja. Ki raɓe su, ki zama tamkar yar uwarsu, ki yawaita kai musu ziyara daga haka sai ki dinga gano sirrinta. Ke daga haka ma idan ma wani aikin ne sai kiga mun ci nasarar yi mata a sauƙaƙe mun farraƙa tsakaninsu. Ɓangaren Fadeel ki kwantar da kai ki ba shi haƙuri ki nuna masa cewa ke fa kin haƙura da shi tunda ba ya kaunarki. Ki yi iyakar ƙoƙarinki wajen ganin kin danne abin da ke zuciyarki a kansa, ki rage shige masa. Ladabi, rage kulashi da ma ba shi girma matsayin yayanki shi zai sa ki shawo kansa ya sakar maki fuska kamar yadda ku ke rayuwa a baya. Ki nuna masa kin fi shi so da kaunar Humaira, ki koɗa ta a gabansa da ma duk sauran kissa da kisisina na mata, wannan kaɗai idan ki ka aikata babu mai zarginki koda nan gaba wani mugun abin da za a yi ya kawo ƙarshen soyayyar Fadeel din da Humairar. Komai fa ɗan siyasa ne." Murja wacce a farko taje jingine da gado tana dafe da ciki tsabar horon yunwar da take yi wa kanta, ba ta san ya aka yi ba ta miƙe zaune sosai tana ƙara baza kunne ga Antin dake magana ƙasa-ƙasa kamar me raɗa duk domin tsaro da kuma gudun kar wani ya ji su. Anti Amarya na kawo wa ƙarshe ta rungume ta su na dariya, har ta ɗan ji ƙwari a jikinta, sai kuma ta ɗan yi sanyi. "Amma Anti anya zan iya danne son Fadeel?" Harararta Antin ta yi. "Da ya kike rayuwa babu soyayyar tasa? Hakanan za ki danne muddin kina son ki cimma manufarki. Ku yaran yanzu babu kissa ba dabara, sai soyayyar kawai. Toh abinci ma ki dafa shi zallarsa babu wasu sinadaran da zai ƙamsasa shi ya ƙara mishi ɗanɗano ai lami za a ci. Balle kuma soyayya, ai idan kana da kyau ka ƙara da wanka. Ba kashe Humaira ba, ko tsire ta za ki yi da wuƙa a gabansa, wataran ba zai ko kalla ba balle ya ji abin a ransa. Ki soma wannan ni kuma na san inda zan je a yi maki aikin da zuciyar Fadeel din zai huce ya soma sanyi a lamarinki. A hankali za ki mallake shi." Dariya Murja ta yi cike da jin dadi da annashuwa. Ta lumshe idanu tana jin wani sanyi a ruhinta, amma fa alƙawari ta ɗaukarwa kanta sai ta ɗanɗanawa Humaira azabar da sai ta gwammace kiɗi da karatu. Ba don tsoron kar ta kashe ta da hannunta itama a kashe ta ba, ai da tun a ranar da ta san Fadeel ita yake so sai ta je har gidansu ta shaƙe wuyanta har lahira. Da wannan ƙarfafa gwuiwa na makirci na Anti Amarya ta samu nutsuwa har ta miƙe ta shige wanka ita kuwa Anti Amarya ta fice a ɗakin. Koda suka haɗu da Kausar a falon, babu abin da Kausar ɗin ta nuna koda wasa kuwa wannan ya cirewa Anti Amarya zargin ta ji tattaunawarsu. *** MUƘADDARI... Ummita da Humaira tsaf cikin shiri, gidan Tasleem suka yi shirin zuwa ba ta jin dadi. Bisa umarnin Mami, Humaira ta yi mata romon ɗanyen kifi mai ɗan yaji saboda ta ji daɗin bakinta, ta shirya shi a kwando, suka ɗibarwa Raihana kayanta kala biyu kamar yadda ta buƙata, tun soma ciwon Tasleem ta je gidan ta ɗan kwana biyu. A hanya su na tafe Ummita na amsa wayar Sahabi tana faman doka murmushi, abin da ba ta saba ba kenan, wato waya a hanya. Asalima ta tsani su fito hanya Raihana ta ɗau waya tana dannawa ko kuma amsawa, hakan ya ba Humaira mamaki. Ummita na ajiye wayar ta dube ta. "Yau ke ce da kanki kike waya a titi? Lallai an gaida Sahabi, daga ranar da ya aiko aka sa ranar aure, shikenan sai soyayyarsa ta ƙara girma a zuciyarki har ta sanya kina karya sharuɗɗan da kika ɗorawa kanki." Ummita ta yi murmushi karo na barkatai. "Ke ni kaina yau jin soyayyarsa nake yi har cikin ƙoƙon raina. Kin san Allah, a yadda nake jin Sahabi a yau Humaira, da ace a karshen watannan ma a yi bikinmu da.." Sauran maganar ta maƙale a fatar bakinta sakamakon wata mota da ta gifta su a guje, idanu waje ta bi motar da idanu. Humaira dake kallon hanya jin Ummitar ta yi shiru ya sanya ta dubanta don ta gani ko lafiya. Ganin hankalinta na wani wurin ya sa ta ce. "Lafiya?" Cikin alamar ruɗewa kadan ta ce. "Wallahi wata na gani kamar Anti Jannat a cikin mota ta wuce." "Anti Jannat kuma? Ina ce sai jibi Mami ta ce za su taso?" Ummita dai da har lokacin matar na mata gizo ta amsa. "Eh, hakane, amma nidai sai naga kamar ita na gani a motar." Cikin rashin ba zancen muhimmanci Humaira ta taɓe baki gami da ɗaga kafaɗa kaɗan. "Wataƙila kama ce kawai ba wani abu ba." "Hakane." Ummita ta amsa, daga nan suka bar zancen. Kafin su kai ga tarar abin hawa sai suka ji wani ɗan sahu na magana. "Siii, ina ku ka yi?" Suka dube shi, ya sha jallabiyarsa ga wani a gefensa matashi cikin ƙananun kaya. Ummita ta zubamusu idanu ba tare da ta ce komai ba, sai Humaira ce ta amsa da cewa Kuntau. "Ku taho mu tafi." Har Humaira ta soma tafiya, Ummita ba ta tako ba don haka ta juyo ta dubeta. "Ki taho muje mana." Jiki a sanyaye kamar ta cewa Humaira su sauya wani ɗan sahun sai ta ji harshen nata ya mata nauyi ga kuma Humaira wacce har ta sanya kai a ciki wannan ya sa itama ta shiga. Sun soma tafiya hankalin Humaira a kwance idan ka cire Ummita da ta yi wani irin la'asar, sun yi gaba kaɗan wani namijin ya tsayar da su ya shiga yana rangaɗa sallama. Sallamar da ya yi ne ya sa Ummita ɗan samun nutsuwa, ko ba komai ai ba za ka yi tunanin cuta daga wanda ya nemar maku amincin Allah ba ku ka amsa. Gudu sosai ɗan sahun yake, Humaira na ta ɗan yiwa Ummita hira jifa-jifa, ita kuwa ta kasa nutsuwa sam, hankalinta rabi na ga kallon hanya da kuma gilashin ɗan sahun wanda ke kallonsu jifa-jifa suna hada idanu da shi. Ba ta san ya aka yi ba, ita dai ta kamar na kusa da ita ya fiddo wani hankicif, kafin ta yi aune ya hura mata a fuska, Humaira ma ta juyowa kafin ta kai ga wani yunƙurin ya shaƙa mata, ji kake yaraff, sun lafke bacci mai tsawo ya ɗauke su. ****LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* 09034973645 Ummita ce ta soma farkawa, a hankali ta shiga murza idanunta da suke yi mata dishi-dishi kafin ta buɗe su tarr cikin ɗan tsurkukin ɗakin da babu komai ciki. Daga wata ruɓaɓɓiyar fanka wacce kallo ɗaya za ka tabbatar da ba ta aiki, sai ko shimfiɗaɗɗiyar katifa wadda da ita da babu duk ɗaya tsabar yamutsewar da ta yi ta rabe biyu. Duk dai a ƙokarinta na son tunano abin daya faru ta ci gaba da bin bangon ɗakin da kallo wanda duk ya yi jirwayen ruwa ga yaana da gizo-gizo da suka cika lungu da kusurwarsa. Sai ko wata ƙofa wacce daga ƙasanta gaba ɗaya ta rarake har kama iya hango ruwan jirwayen banɗakin da ya kwanta har ya rine. Ban da tashin zarni da wari babu abin da ke fitowa daga cikinsa. Ta kuma miƙe tsaye a razane, ta tuna komai, su na hanyar zuwa gidan Tasleem ne su kai wa Raihana kayanta sai ko saƙon Tasleem din na girkin da aka yi mata. Toh nan ina ne? Ya aka yi suka ƙare anan? Fuskokin matasan nan uku ciki har ɗan sahun suka zo mata tarr tarr, da sauri ta nufi windon dake ɗakin, a buɗe yake sai dai an zagayeshinda wasu irin ƙarafana masu nauyi, ciyayi ne cike a wurin har ba ka iya hango bangon dake waje.  Ta juya ga Humaira da har lokacin hodar ba ta sake ta ba ta shiga jijjiga ta tana kukan tashin hankali, ga jikinta da ke rawa ta ko'ina. A ɓangaren Humaira kuwa, ji ta yi kamar a can wani nisan wuri Ummita ke kiranta, a hankali ta buɗe idanunta tana kallonta dishi-dishi. Sannu-sannu kuma har ta dawo hayyacinta ta fahimci dagaske ne dai Ummitar ke kwala mata kira. Ta miƙe zaune tana ambaton innalillahi. Irin yanayin da Ummita ta shiga, shi ta tsinci kanta a ciki. Da rawar murya ta ce.   "Na...nn..nan ina ne?" Ummita dake hawayen itama girgiza mata kai ta yi hankali a tashe. "Ban sani ba Humaira, ban san ina muke ba. Mun faɗa hannun mugaye azzalumai, jikina tunda muka fito yake ba ni cewa babu alheri a tafiyarnan amma ƙaddara ta riga fata. Na so na ce maki kar mu shiga dan sahun nan ban yarda da su ba amma.." Sauran kalaman Ummita suka maƙale a fatar bakinta sakamakon bankaɗo ƙofar da aka yi da ƙarfi aka sanyo kai cikin ɗakin. Mutum biyu ne cikin samarin, da matuƙin napep ɗin da kuma wanda ya zauna kusa da Ummita a hanyarsu. Hannun ɗaya riƙe da leda. Yayinda mai napep din ke shan taba hankalinsa kwance yana fesar da hayaƙi suna murmushi, matuƙin ɗan sahun ya ce.     "Kun sha bacci, sannunku da tashi." "Ku dubi Allah da annabinsa s.a.w ku yi hakuri ku kyalemu mu tafi. Iyayenmu ba su da kudin da za su bayar domin fansarmu. Ku yi hakuri mun tuba, wallahi komai da ke cikin jakkunanmu ku ɗauka halak malak mun bar maku." Ummita ke wannan zancen cikin rawar baki da murya. Ga kukanta da ta kasa tsaidawa, itama Humaira kukan take yi ta ma kasa cewa komai. Matashin da ya soma magana tun farko, ya kai duba ga na tsayen wanda ya fi shi sirantaka da tsawo, tun murmushin farko da ya yi bai ƙara koda buɗe haƙora ba, shi kuwa na durƙushen ya bi Ummita da kallo sannan ya yi ƴar dariya. Madadin ya yi magana sai ya zuƙi sigari ya busamata a fuskar, ta kauda kai tana tari, Humaira ma ta toshe hancinta. Hannu ya miƙawa na tsayen, ledar ya miƙo mishi ya karɓa ya buɗe ta. Shinkafa da wake ne sai manja da yaji, ya tura musu ledar ya ƙara fesar da hayaƙin sigari kana ya ce.       "Ga food ku eat. Kin gane bana son musu, if you follow za rules here, you will ji dadi sosai. If you break oza, za ku yi dana sanin haihuwar da uwarku ta yi." Anan ne Humaira ta samu ƙarfin gwuiwar taso mishi cikin ɗaga murya ta ce. "Sai dai taka uwar ta yi nadamar haihuwarka idan tana raye! Ba dai namu iyayen ba!" Tana fadin haka a zafafe ya ɗaga hannu ya sauke yatsunsa saman fuskarta ji kake tas! Ya fizgota ya take ƙafarta kafin ya ɗosana mata karan sigari inda hayaƙi ke fita a saman fatar wuyanta, ta saki ƙara iyakar ƙarfinta na azaba, Ummita ta shiga ƙokarin kwace ta tana haɗa shi da Allah da Annabi kan ya yi haƙuri. Don kansa ya sake ta, wurin kuwa nan da nan ya yi jazur ya ja ruwa. "Ke har kin isa na zageki ki rama don ubanki?! Banza ƴar iska kawai! Kika ƙara  yimin irin wannan kuskuren da shishshigin sai kin raina wayonki." Ya ƙara ƙudundumo ashar ya watsa mata, har ya sa kai zai fice ya dawo da baya ya sanya ƙafa ya murje abincin ledarnan har ya baje a ƙazantaccen tayils din wurin. Ya dubi wanda suke tare ya soma magana da muryar ƴan daba.   "Kai Bad boy, koda wasa kar a ba su abinci da ruwa har sai don kaina na baku iznin haka. Ƴan wahala kawai." Daga haka ya sa kai ya fice, wanda aka kira da Bad boy ya watsamusu mugun kallo sannan ya bi bayansa gami da maida ƙofar ya rufe gam da muƙulli. Su na tafiya Ummita cikin kuka ta ɗago Humaira tana duba wajen da aka sanya mata wutar sigari. Humaira hawaye kawai ta ke yi idanunta a runtse ga raɗadin da ya addabe ta. "Kiyi hakuri Humaira, don Allah ki kai zuciyarki nesa har mu samu kuɓuta daga hannun waɗannan azzaluman." "Toh." Shi ne amsar da Humaira ta iya bayarwa kawai, daga haka ba ta ƙara ko harafi ba saboda azaba. Ummita ta yi mata tofi a wurin sannan suka yi zaman shiru sai ambaton Allah da suke faman yi. ***   Mami suna tare a kicin ita da Ladidi, abinci suke ta hadar-hadar shiryawa na dare tana ta mitar zaman da su Humaira suka je suka yi a gidan Tasleem alhalin ta ce musu kar su jima. "Gashinan yanzu har an fara kiraye-kirayen sallar Magriba, itama gwanar duk da na gargadeta kar ta bari su yi zaman hira da mutuniyar tasu (Raihana) amma ta yi kunnen uwar shegu." Ladidi ta yi ƴar dariya tana goge kwanukan da ta wanke don yin kwasar tuwo. "Ai fa kam, ƴanmatannan naki uku idan suka haɗu a wuri sai haƙuri. Ji suke yi kamar ba su taɓa zaman hira ba a duniya sai a lokacin." Mami ta buɗe baki za ta yi magana sai ga Walid ya shigo da gudu riƙe da wayarta, a bayansa kuwa Muhsin ne. "Mami Mami! Anti Tasleem tana kira." Wayar a lokacin har ta katse, Muhsin yana kawo ƙarar Walid wai game yake ta yi har ana kira yana katsewa. Mami ta ɗan yi musu tsawa akan suf fice a kicin ɗin su ba ta wuri. Ta na kokarin dannawa Tasleem din kira sai ga kiran Raihana ya shigo, ta ɗaga ta kara a kunne. "Raihana, yanzu nake shirin kiranku, maza maza ki cewa yarannan su dawo. Ku idan ku ka samu hira ba ku san dare ba ya yi ku haƙura ko?" "Mami su wa kike magana? Ai kiran ma da Sis ta yi maki kenan ta ce kodai ta cire rai ne ta sanya Yaya Hamza ya yi mata odar wani abun? Nidai tun ɗazun ma na kikkira wayoyin su Ummita a kashe." Mami ta fiddo idanu gami da dafe kirjinta, cikin rawar murya ta ce. "Me kike shirin cewa? Kina nufin wai su Humaira ba su zo gidan ba? Kinsan tun ƙarfe nawa suka bar nan?" Raihana itama muryarta cikin tsananin ruɗewa da tashin hankali ta amsa. "Wallahi Mami ba su zo ba." "Innalillahi wa inna ilaihir raajiun! Na shiga uku ni Maryam." Hakan da ta faɗi ya sa Ladidi maido hankalinta gareta, itama gaba ɗaya jikinta ya ɗauki rawa. Mami ta kasa cewa Raihana komai sai kawai ta katse kiran cikin tsananin tashin hankali ta fito falon inda Ƙasim ke kwance saman kujera yana latsa waya.   "Ƙasim! Tashi ka bi sahun su Humaira! Na shiga uku, tun da rana suka fita a gidannan har yanzu ba su dawo ba." Gaba ɗaya a ruɗe take maganar, ta kasa nutsuwa balle ta yi mishi bayani yadda zai fahimta. Ba ta jira cewarsa ba ta yi gaba ta nufi ɓangaren Abba amma ina, ta iske ya fice zuwa masallaci. Ta dawo falon inda ta tarar Ƙasim tsaye Ladidi na mishi bayanin abin da ya faru. Shi ma nan take ya ji hankalinsa ya tashi.   "Amma Mami kodai sun biya gidan ƙawayensu ne?" Mami wadda gaba ɗaya cikinta ya ɗuri ruwa ga tsananin tashin hankalin da ya bayyana saman fuskarta ta amsa mishi. "Kayya Ƙasim, ba dai su ba. Ba su da wannan rawar kan, da ace dai Raihana ka ce shi ne zan yarda. Ni dai jikina yana ba ni akwai matsala." Ƙasim ya yi shiru, sai ya shiga kiran layukansu amma gaba ɗaya a kashe. "In sha Allahu lafiya kalau suke. Ku kyautata zato." Fadin Ladidi jiki a sanyaye. Itama ta rasa nutsuwar zuciya, a wannan lokaci da satar mutum sukutum ba shi da wuya, lallai dole ko rabin awa suka yi hankali ya tashi, balle kuma kusan awanni uku zuwa huɗu? Abin dai akwai ɗaga hankali. "Bari nayi sallah." Mami ta furta gami da miƙewa ta yi ɗaki. Ladidi ma ficewa ta yi kicin don kwashe tuwon da har ya soma kamu yayinda Ƙasim shi ma ya fice a sanyaye zuwa masallaci. *** Tasleem kuwa, Raihanana ajiye waya suka dube ta ita da Fauziyya da ta maida gidan na Tasleem gidan zuwanta hira da kuma kallo.     "Meyafaru da su Humairar ne?" Cikin halin tsananin firgici ta faɗamata abin da Mamin ta ce. Tasleem ta yamutse fuska kaɗan tana ci gaba da taunar tsamiyar da ke bakinta.   "Ke yanzu kin yarda ɓatan suka yi kenan? Kika sani ko Ummitan ta yiwa rakiya ɗakin Sahabi?" Maganar ta dake Raihana, wannan wane irin baƙin ƙazafi ne marar daɗin ji? Ba ta taɓa tsammanin jin makamancinsa daga bakin Tasleem ba musamman ma a gaban ƙanwar mijinta. Fauziyya kuwa ta ce.   "Kai Anti Tasleem, wannan Humairar da na gani dai kamar ba za ta aikata irin haka ba. Ummitar ma ba ta yi kama da ƴan iska ba." Sai a sannan ita ta tuna ashe ba su kaɗai ba ne. Don haka ta yi saurin gyara zancenta gami da nuna tarin alhini a saman fuska. "Hakane, amma kinsan zamanin nan, samarin yanzu ƴan iska don su hurewa mutum kunne ba komai ba ne. Allah dai ya tsare, ya sa su koma gidan." Raihana wacce ta lula tunanin inda ya kamata ta kira don jin ko su Humairar sun je ta dawo hayyacinta, firgigit ta miƙe tana fadin. "Nidai wallahi ba zan iya zama ba ana neman ƴan uwana, gida zan koma." A fusace Tasleem ta ce. "An fadamaki nima ban damu ba ne? Ai daren bai yi ba, kika sani ko napep din da suka shiga ne ya samu matsala? Toh wallahi babu inda za ki je ki jira har sai mun ji ya ake ciki." Raihana kamar ta yi magana sai kuma ta fasa, a fusace ta shige ciki tana jin kuka na taso mata, ta ina za ta iya nutsuwa alhalin ba a ga ƴan uwanta ba? Fauziyya ganin haka ta miƙe ta bi bayanta, ita kuwa Tasleem da sauri ta bi hanyar da suka yi da idanu sannan a gaggauce ta fiddo wayarta ta rubuta text ta tura kamar haka.     *_Aikin har ya kammala ne da wuri haka?_* Tana aikawa aka maido mata amsa. *_Tukunna dai, wani abun ya faru?"_* Ta yi shiru ta kasa maida amsar wannan tambaya, jikinta ya ɗan yi sanyi. Ita kanta ba ta da tabbacin abin da ke shirin faruwa. ***   Mami tana jin shigowar Abban falo ta miƙe da sauri har ya dube ta da ɗan mamaki. "Lafiya Maryama, ya na ganki a rikice?" Kawai sai ta fashe da kuka. Ya shiga tashin hankalin ganin haka, wannan ya sa shi saurin riƙo hannuwanta. "Ki samu nutsuwa ki faɗamin, meke faruwa?" Muryarta dakyar take fita ta amsa. "Kasan na aiki yarannan gidan Tasleem amma babu su babu dalilinsu. Ba su je gidan Tasleem din ba, kuma wayoyinsu gaba ɗaya a rufe. Hankalina ya tashi." Tabbas ya san da maganar amma kasancewar ya shiga tsananin ruɗani ya ce. "Su wa kenan? Ni ban fahimci komai ba. Wa kika aika?" "Humaira da Ummita da na ce maka za su je gidan Tasleem kai mata saƙo." Abba jin haka nan da nan ya soma haɗa zufa. "Innalillahi wa inna ilaihir raajiun! Kun tabbata ba sa  gidan ita yarinyar?" Mami ta amsa ta hanyar gyaɗa kai da motsa lebba don sautin muryar ma ta kasa fita. Jin haka Abba ya zari mukullin mota daga shi sai jallabiya sai ko wayoyinsa ya fita yana fadin. "Ina zuwa." Har ya kai ƙofa sai kuma ya juyo ya dubi Mami. "Maryama, ki kira dukkan inda kike tunanin za su iya zuwa ki ji ko can suka tafi, ni bari na je ofishin ƴan sanda na sanar." Ta kasa magana sai gyaɗa kan da ta yi.  Daga haka Abban ya fice. Kai tsaye babban station ɗin mandawari ya je ya yi report ya ba da hotunan su Ummita, ba shi da su sai da ya sanya Raihana ta turo masa. Anan ne itama hankalinta ya kara mugun tashi ta tabbatar dagasken dai an sace su. *** Raihana ta birkicewa su Tasleem ita lallai a daren take son komawa gida, kuka take yi ba ta jin koda rarrashi, wannan ya sanya ba shiri suka miƙe har Tasleem din suka nufi can gidan a motar Hamza.   Su na isa Raihana ta faɗa cinyar Mami ta ƙara ƙarfin kukanta. Wannan ya ƙara karyar da zuciyar Mamin, ta dafa Raihanar tana ɗan hawaye. Tasleem ta ƙaraso ta zauna fuskarta ɗauke da damuwar kukan da Mami ke yi ta ce. "Kiyi hakuri Mami, in sha Allahu za a gansu. Bana tunanin an sace su, idan da hali ku kira Sahabi ku ji ko..." "Malama ya isheki hakanan! Haba! Da wanne kike so a ji? Da ɓatan su ko kuwa da baƙin ƙazafin da kika ƙokarin yi musu na zuwa wajen saurayi? Ɗazu dama na maki shiru ne darajar Fauziyya, yanzu kuwa daidai nake da ba ki amsa. Ki faɗi muji, tarbiyyar wa kike shakku a cikin su biyun? Ke da kanki a bayan idanunsu kin sha yabon nutsuwarsu, ki dai ji da abin da ke jikinki ba ki zauna zaman ɗaukar haƙƙin mutanen da ba su ɗaukeki yadda ke kika ɗauke su ba!" Tasleem wacce ta cika ta gama batsewa da wannan kalar maganganun da ta ke musu kallon rashin kunyar Raihana gareta tuni ta harzuƙo za ta soma caccakawa Raihanar zagi sai Mami ta dakamata tsawa. "Ya ishe ni! Ya isa! Ku marasa tunanin ina ne? Da wanne zan ji ne? Ashe ba kwa hangomin abin da nake hangarwa kaina?! Ba ku hangen ire-iren maganganun da zan sha wajen jama'a sanadiyyar ɓatan  yaran amana da nake riƙo? Da ace cikinku ne wa zai ce sakacina ne?!" Mami na kaiwa nan ta ji kukanta ya ƙaru har da sheshsheƙa, ƙarshe kawai sai ma ta miƙe ta fice zuwa sashin Anna don tana da tabbacin ba ta sani ba. *** Duhun da ɗakin ya yi ne ya sanya suka matsu a gefe guda suka cure jikinsu ga uban sauro da ke yawo a kunnuwa yana kuma cizon fatar jikinsu. "Humaira, ya zamu yi? Babu ruwan alwala a banɗakin nan da na duba, bamu yi sallolinmu ba. Maƙogwarona ya bushe ƙishin ruwa nake ji." Ummita ta yi furucin cikin shaƙaƙƙiyar muryarta da ya dashe sanadin kukan da suka sha, itama Humairar wacce ƙishin ruwa da kuma yunwa suka galabaitar gefe guda ga wani fitsari da ya cikamata mara ta ce. "Ban sani ba Ummita, ban sani ba. Fitsari nake ji amma tunanin wannan banɗakin da muhallin ya sa na kasa yi. Sun bar mu a duhu kamar waɗanda ke cikin maƙabarta, ko a maƙabartar muna saka rai da rahmar Ubangijinmu. Mu cigaba da addu'a, ba zamu rasa mafita daga gareShi ba." "Toh." Shi ne kawai abin da Ummitan ta iya furtawa, ta koma ta nannaɗe a jikin bango ta runtse idanunta tsabar tsoron wurin, cikinta ya ɗuri ruwa sosai, ta cigaba da jan dukkan wasu addu'o'in da suka zo bakinta. Suna a haka suka soma jin muryoyin garada daga waje suna dariya har da kyakyatawa abin babu dadin sauraro. Kafin su tantance komai suka ji alamar buɗe ƙofar, gaba daya suka ƙara ruƙunƙume juna don fargaba. Aka haske musu fuskokinsu da torchlight mai shegen haske, wannan ta sa suka yi amfani da hannuwansu wurin kare hasken sakamakon ƙarfin da suka ji ya yiwa idanunsu da suka jima cikin duhu. Wannan karon matasan ne su ukunsu gaba ɗaya suka shigo. "Don uwarku ku saki juna, ƴan iskan banza kawai." Sun ji ciwon zagin sai dai tsoro ya sa da azama suka matsa gefe, kowaccensu babu inda jikinta ba ya rawa. Shi ne dai baƙin azzalumin na ɗazun. "Wizzy, a ina aka kwana ne?" Anan suka ji ashe sunansa Wizzy, ya watsawa mai maganar mugun kallo. "Kai Babba, don't kawo yaawa mana. Ka yi everything a muhallinsa mana ok? Here is not good to ce wani abu. Sai mun go out." Wanda aka kira da Babba ya amsa da. "Na fahimta Oga." Daga haka Wizzy ya yo gaba ya dan sa ƙafa ya shuri Humaira. "Ke gwanar na iya, koda wasa wallahi ki ka kara try din zagina sai na kasheki na yi killing banza! Kuma a nan za ku zauna har sai mun gama sanin makomarku! Badboy, a ba su abincin da ruwa, ka ajiye musu fitilar ba don halinsu ba shegu." Yana kaiwa nan ya sa kai ya fice yana ba wa Babba umarnin ya biyo shi su yi magana. Shi kuwa Badboy ya ajiye musu leda da ruwan sha na purewater sinƙi guda, sai kuwa fitilar daga nan ya fice ya garƙame ƙofar. Da sauri Ummita ta jawo ruwan hakanan itama Humaira, suka sha suka yi kat, daga nan haka suka daure suka kama ruwa a banɗakin ba don suna so ba, suka yi alwala, ɗankwalayensu suka mayar darduma, suka yi sallah. Humaira ta yi shiru ta zuba uban tagumi tana ɓarin hawaye, Ummita ta jawo ledar, shinkafa da miya ne garau garau. "Ke kika ce kina jin yunwa ɗazu, ki daure ki ci." Ta ɗan dubi abincin sannan ta dubi Ummita ta girgiza kai. "Ba zan iya ci ba Ummita, innalillahi wa inna ilaihir raaji'un, haka za mu yi ta zama tare da waɗannan azzaluman? Yanzu nan wurin zamu kwana? Su Abba na can hankalinsu a tashe Ummita. Wayyo Mami." Kawai sai ta sa kuka hakan ya sa Ummita itama da take danne nata sai kawai ta sake shi. Wannan karon ma babu mai rarrashinsu, su suka gaji suka yi shiru sai faman sheshsheƙa. *** KAMAR WASA... ®️Rufaida Umar      *LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* 09034973645 Kamar wasa, ƙaramar magana ta zama babba. Babu su Humaira ba labarinsu har aka yi kwanaki biyu, wannan ya ƙara tayarda hankalin iyalan gidan sosai. A ranar ne kuma Jannat ta diro gidan, labarin ɓatan yana risƙarta ta hau buga salati, cikin sanyin jiki ta ce. "Koda ace ba na kaunarsu, bana murnar ɓatan su. Allah ya sa a gansu." Mami ta amsa da amin, Raihana kuwa ba ta um bare um um a kwanakin nan sai kallon kowa da idanu. Tasleem itama dai tana gidan ba ta koma gidanta ba, Abba ne ma ke faɗan zamanta acewarsa zaman ko rashinsa ba shi zai sa a gansu ba. Wannan yasa a ranar ya ba ta umarnin tattarawa ta tafi. Jannat ce ta ce za ta kai ta tunda Hamza ya tafi ofis. Anna kuwa nunawa tayi ko a jikinta, cewa ta yi ba ta yarda ma da batun ɓatan ba, ta fi tunanin dai wani yawon nasu suka je za su dawo. Babu wanda ya ce mata komai a wannan bahagon tunanin nata. Zancen dai zuwa lokacin ya yaɗu har gidajen rediyo da social media inda Raihana ta ɗora hotunansu a dukkan shafuka tana mai tagging shafin Humaira saboda abokan kasuwancinta su taya ta yaɗawa. *** *_Tafkeken fili ne babu gida gaba da baya, tafiya kawai yake yi yana jefa ƙafafunsa yana faman kwala kiran sunan Humaira ga wani irin baƙin hadari da ya cakuɗe a sararin samaniya sai walƙiya dake haskawa akai-akai har bai ankara ba ya cimma ƙarshen hanyar yana shirin afkawa ƙaton ramin dake a gabansa ya ji an riƙo hannunsa da ƙarfi. Juyawa ya yi yana mai duban mai shi, wata mace ce dattijuwa fara tas, tana sanye da farin hijabi har da na hannu, komai na tufafinta fari ne ƙal. Hawaye ne kwance saman fuskarta ta ce. "Ka taimaka ka ceci rayuwar Humaira, tana cikin hatsari. Ka kularmin da ita. Duk runtsi kar ka rabu da ita. Alheri ce a gareka." Zuciyarsa ya ji ta tsinke, ya dawo da baya murya a sama ya ce "Ina Humaira ta ke?" Kawai sai ta nuna masa ramin dake gabansa, Humaira ya hango saman wani ƙaton dutse a kwance gaba ɗaya gaɓɓanta an sanya wasu sarƙoƙi an ɗaure ta tamau. Sannan ya maida duba ga Matar shima lokacin hawaye yake. "Ba ta sona, ba za ta amince na taimake ta ba." Matar karo na farko ta yi mishi murmushi "Kaf duniya babu matar da za ta so ka sama da Humaira. Tana sonka, ka bata lokaci ka zama mai hakuri." Tana kaiwa nan ta saki hannunsa ta soma tafiya da baya tana cewa "Ka ceci rayuwarta daga hannun azzalumai. Ina roƙonka a matsayina na mahaifiyarta._* Yana kai wa nan ya soma jin kiraye-kirayen sallar asuba a kunnensa, firgigit ya farka ya miƙe zaune yana ambaton Allah. Na'urar sanyaya jikin dake aiki bai hana zufa wanke mishi fuska da jiki ba hakan ya sanya shi saurin yaye bargon yana ajiyar zuciya kamar wanda ya yi tseran gudu. Kansa ya ji yana sarawa, wannan wane irin mafarki ne kuma? Wace ce? Meke faruwa da Humairar? Kwana biyu kenan rabonsa da duk abinda ya shafi social media balle ya samu damar magana da Raihana ko tambayar lafiyar Humairar, hakan kuma ya faru ne sanadiyyar ayyukan ofis da suka yi mishi yawa saboda shirye-shiryen tarbar baƙin ƙasar waje da suke yi a kamfaninnasu. Addu'a ya yi sannan ya miƙe jiki a saluɓe gabansa har lokacin na bugu da ƙarfi yana jin kamar ya kira wayar Humairar a sannan ya ji ko za ta amsa. Hakura ya yi ya shiga ya ɗora alwala ya zura jallabiya ya fice zuwa masallaci. Koda ya dawo wayarsa kawai ya ɗauka, ba ya jin zai iya haƙuri da kiran Humaira koda ace hakan na nufin rusa tsawon jiran da ya yi, ya gaji zai tunkareta kawai da batun aure. Zantukan matarnan da ya gani cikin mafarki da kuma yanayin da ya ga Humairar sun fi komai ɗaga mishi hankali duk da yana kyautata zaton alheri ne mafarkin. Ya kira ya fi sau uku amma amsar ɗaya ce, a kashe. Don haka ya yanke shawarar kiran Raihana, shi dai babban burinsa jin muryar Humairar. Ko ringing uku wayar ba ta yi ba ya ji Raihana ta ɗaga a gaggauce. Sallama ya yi mata ta amsa. "Ina son jin muryar Humaira, ki haɗa ni da ita please." Kawai sai ya ji ta fashe masa da kuka wanda ba ƙaramin rikita shi ya yi ba. "Me ya faru?! An yi wani abun ne? Ki faɗamin." Gaba ɗaya ya ruɗe, nan take sanar da shi ai kwanaki uku kenan babu Humaira da Ummita balle labarinsu ta kuma ƙara da cewa. "Abin damuwar shi ne ba a san su waye ba, idan kidnappers ne, ai za su kira su ce a ba su kuɗin fansa, waɗannan kuwa babu kira ba.." Maganarta ma ta kasa fita sakamakon kukan da ya ci ƙarfinta. "What nonsense! Takardu da za a ce kawai sun ɓata? Kar ki rainamin hankali mana!" Daga yanayin yanda yake zancen ma ka san a ruɗe ya ke. Cikin nutsuwa ta labarta mishi duk yadda komai ya faru har da batun cigiyar da aka sanya a jiya a gidajen rediyo da ma hotunan Humairar duk da ta ɗora a media. Ta ƙara da faɗin. "Ka taimake ni Yaya Fadeel a nemo su, wallahi ba zan iya rayuwa ba idan babu su. Jinin jikina ne." Idanunsa suka kaɗa, ya ji wani maƙoƙon abu ya tokare masa a ƙirji, ga kansa da ya yi mugun sarawa, bai iya cewa komai ba ya datse kiran. Zama ya yi dabas a ƙasa har lokacin yana riƙe da kansa da yake ciwo tamkar zai fashe. Ashe dagaske mafarkinsa ne zai tabbata? Humaira na cikin tashin hankali? "Innalillahi wa inna ilaihir raajiun!" Ya furta a fili. Kafin wayewar gari tarr jikinsa ya ɗauki tsananin zafi, amma hakanan ya daure ya ɗaga wayar Ibb wanda shima ya ci karo da hoton Humaira dake yawo a media. Hankalin Ibb tashe ya ce. "Fadeel ka ji labarin abin da ya faru da Humaira?" Shiru ya kasa ba shi amsa sai wasu irin zafafan hawaye da suka kwaranyo saman fuskarsa. Ya runtse idanu, fatansa bai wuce ace mafarki yake yi ba, inama duk abin da yake ji yanzun a mafarkin ne. "Fadeel, are you ok?" Ibb ya ƙara tambayar jin ya yi shiru. A sannan ne ya soma magana dakyar haƙoransa har su na bugun juna saboda wani mugun sanyin da yake ji. "No Ibrahim, i am not, Humaira rayuwata ce. Ibrahim ka taimakamin, ina tunanin mutuwa zan yi." Yana kai wa nan ya ajiye wayar shi bai kashe ba, shi kuma bai ƙara sauraron abin da Ibb din zai faɗi ba , yana ta faman Hello hello amma shiru kake ji. Yana nan kwance ya dai ji shigowar Alhaji dakin amma daga nan bai ƙara sanin inda kansa yake ba. Alhaji wanda ya samu waya daga Ibb a gigice ya tallafo shi ya hau kiran sunansa, Anti Amarya itama faɗowa ciki ta yi sanye da hijabinta har ƙasa. "Ya kamata a tafi asibiti." Jin abin da ya fito daga bakin Anti Amarya ya ankarar da shi abin da ya kamata ace shi ya ya yi wannan hankalin. Ya ba ta umarnin ta sa a fiddo mota yayinda shi kuwa ya taimaka da kama Fadeel suka fita. Murja da ta ji hayaniyarsu daga farfajiyar gidan ta fito daga ɗakinta tana murza idanu daga ita sai riga da wando na bacci ko sallah ba ta yi ba. Suka yi karo da Anti Amarya da ta shigo sauya sutura don ta bi bayan su Alhajin a wata motar. "Anti meke faruwa?" "Fadeel ne ba lafiya." Nan da nan ta ji tashin hankali, sai kuma ko me ta tuna kawai ta danne damuwarta. Wani abu ya tokare kirjinta kawai sai ta ce Allah ya ba shi lafiya, daga haka ta juya ta koma ɗakinta fuskarnan kamar an aikomata da saƙon mutuwa. Sai da ta dubi ƙofar shigowa ɗakin ta tabbatar babu mai tahowa kafin ta ɗauki waya ta danna kira sau uku ba a ɗaga ba, ƙarshe kawai sai ta aika da saƙo kamar haka. *_Lokacin aiwatar da aikin ya yi. An tafi da shi asibiti yana cikin halin rashin lafiya kuma bana raba ɗayan biyu a sanadinta ne._* Iyakar abin da ta rubuta kenan a saƙon ta tura zuwa lambar da ta yi saving da suna BLANK. Ta koma ta zauna gefen gado tana murmushin da ita kaɗai ta san ma'anarsa kafin ta ƙara fiddo wayarta ta lalubo saƙon da aminiyarta Saddy ta aikomata na labarin ɓatan Humaira da kuma hotuna. Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta ɗaga yatsunta biyu a kan hoton Humaira gami da girgiza kai ta ce "Good bye Humaira, daga yanzu kin fita daga rayuwar Fadeel, fita na har abada." *** Ruwan sanyi ƙarara aka sheƙa musu a fuska wannan ne ya yi sanadiyyar da firgigit suka farka daga baccin wahalar da ya kwashe su. Idan ka kalle su, ba za ka ce su ne wadannan ƴanmatan Abban ba masu iya ado da kwalliya uwa uba kuma tsafta. Sun rame sun yi baƙi a kwanaki huɗu kaɗai da suka yi a wajen, ga fatar jikinsu da ya yi ruɗu-ruɗu saboda cizon sauro da ma cinnaku. Ummita fama take yi da mugun zazzaɓi, ita kuwa Humaira a kwanakin amai kawai take kwararawa ga gudawa, gaba ɗaya sun zama wasu ƙazamai na ƙarfi da yaji. Suka kai duba ga wanda ya yi musu wannan aika-aikar, wannan dai azzalumin ne mai suna BadBoy. Ya ƙaraso ya ja Ummita kasancewar babu kuzari a jikinta kawai ta tafi luu, ya dakatar da ita ta hanyar tura ta da hannu ta faɗi tim a saman busassan aman da Humaira ta yi. Ya fisgo hannunta ta koma ta zauna kafin ya sa baƙin kyalle ya tamke mata idanu. Humaira da ta kasa koda ɗaga yatsa sakamakon galabaitar da ta yi na amai da gudawa ya koma kanta, ya toshe hanci jin ƙarni da warin dake tashi a jikinta, mari ya kifa mata. "Don ubanki ke wace iriyar ƙazama ce da ba za ki shiga banɗaki ba. An faɗamaki nan gidan gyatuminki ne da za ki yi mana kashi a wuri? Za ku wa ki raina kanki." Ya fisgota itama ya ƙullemata idanun. Daidai nan Wizzy ya ɗan leƙo da kai yana mai zuƙar sigari. "Wai ya ne? Ka tattaro su mu bar nan." Daga haka ya titsa ƙeyarsu Wizzy na kundumawa Humaira ashar ganin yadda ta yi kace-kace sai tashin hamami take yi. Ya rantse ba za su shiga motarsu a haka da ita ba. Wannan ya sa anan suka ɗauki ledar kayan Raihana dake hannunsu a falon gidan suka damƙamusu a hannu. "Ku sauya kayan kar ku kuskura ku gwada wani motsi idan ba haka ba sai na ciremaku kai da wuƙarnan." Daga gargadin da ya fito a bakin Wizzy, sai Badboy ya tura Humaira banɗakin da ke falon wanda ya fi na ɗakin da suke ciki kyau shi har da ruwa a ƙaton bokiti. Idanunta ya kunce mata sannan ya fice ya tura ƙofar. Humaira dakyar ta ɗaga rigar da suka bata, doguwar rigar Raihana ce na atamfa sai ɗankwali. Kuka ya kufcemata da wani irin kewarta. Ba ita ta iya saiya kayan ba sai da Badboy ya bugamata ƙofa da ƙarfi ya na zaginta akan ta yi sauri, wannan dalilin ya sa cikin rawar jiki ta shiga rage kayan dake jikinta, ta ɗan watsawa kanta ruwa a gaggauce har da ɗora alwala sannan ta sa kayan ta fito. Itama Ummita hakan ta yi duk kuwa da cewa ga zazzaɓi a jikinta, amma tana buƙatar tsaftar jikinta ko yaya ko don sallah. Itama dai kayan Raihanar ce riga da siket ƴan kanti. Wizzy ya kallesu su biyun yana mai haɗiyar yawu maƙwat. Shakka babu sun kai a kira su ƴanmatan da za a nuna, ban da ma baƙar wahalar da suka ci ai ya sani sun haɗu ne ƙarshe musamman Humaira da ya kasa ɗauke idanu a kanta. Saƙe-saƙen dake ransa, hakan ne a na Badboy wannan ta sanya shi duban Wizzy. "Ga nama amma babu damar ci." Wizzy ya busar da hayaƙi gami da yin wani shu'umin murmushi. "Akwai ranar ƙin dillanci. Yanzu dai mu yi haƙuri mu ci miliyoyin kuɗaɗen nan idan ya so ko mene ne sai a yi." Badboy ya jinjina kai, ya ƙulle idanun su Humaira wadanda duk iyakar kalle-kallensu sun kasa gane inda suke. Wizzy ne ya soma fita ya ɗan duba wuri sannan ya ba Babba dake gaban mota umarnin tayarwa daga haka ya sa Badboy fitowa da su Humaira suka tura su cikin motar mai baƙaƙen gilasai suka bar wurin da gudun gaske. *** Fadeel wanda likitoci suka duƙufa a kansa dakyar cikin taimakon Allah suka samu ya dawo hayyacinsa. Sai dai har lokacin zazzaɓinsa bai sauka ba wannan ta sa suka yi mishi allurai suka ɗora masa ruwan drip ganin gaba ɗaya jikinsa babu kwari saboda aman da ya yi mai yawa bayan farkawarsa. Ganin ya kasa nutsuwa sai kokarin miƙewa yake yi yana cewa zai je neman Humaira hankulan Alhaji da Ibb wanda tuni ya iso suka tashi, Likita dole ya yi mishi allurar da zai sanya shi bacci. Bayan fitarsa Alhaji ya dubi Ibb. "Wai meke faruwa ne? Me ya samu Humairar?" Ibb ya sanar da Alhajin labarin ɓatan su Humaira. Shi kansa ya jinjina lamarin. Shi tun daga sadda Fadeel ya ce mishi zai yi jiran Humairar ya fahimci irin zurfin da ya yi a kaunarta. "Toh ban da abin Fadeel, ai ba sanyawa zuciyarsa damuwa ya haifar mishi da ciwo ne mafita ba, mafitar ita ce a yi addu'a sannan a ƙara magana da hukuma don ganin an ƙarfafa bincike." Ibb ya jinjina kai. "Hakane." Suna nan zaune Daddy ya iso tare da Maman Ibb. Anan suke jin silar ciwon, shi ma dai irin hangen Alhajin ya yi. Daga nan ya ce Ibb ya yi mishi rakiya zuwa gidan su Humairar. Shi ma Alhajin ya bi su yayinda Mama da Anti Amarya wacce ta iso lokaci guda da Fu'ad suka zauna anan asibitin. *** Abba bai yi mamakin ji daga Ƙasim cewa ya yi baƙi ba domin tun faruwar lamarin yake ta samun baƙi daga kan ƴan uwa har abokan hulɗa. Ɗazun ba jimawa ƴan uwan Maman Ummita na Bichi suka iso su ma. Falonnasa na saukar baƙi ya shiga. Daddy da Alhaji suka miƙe aka yi musabaha da Abba sannan duk aka zauna shima Ibb ya gaida shi. Daga nan kuma Daddy ya gabatar da kansu matsayin iyayen Fadeel yaron wajensu dake neman auren Humaira. Abba ya ji zancen banbarakwai, Alhaji kuma sanin da ya yi cewa Fadeel bai bi maganarsa ba na gabatar da kai ga Abban yasa shi fahimtar komai. Nan ya yiwa Abban bayani cewa ai yaron nasu bai kai ga zuwa wurinsa ba. Abba ya ɗan saki fuska, watakila dai shiyasa Humairar aka ce ba ta kula kowa, kenan tana da wanda ta ke so. Nan kuma aka shiga jajanta batun ɓatan su Humairar, Abba ya ƙara ba su labari daidai sadda Raihana ta zo kawo ruwa kamar yadda Ƙasim ya shaida mata saƙon Abban. Ta shigo da zumɓulelan hijabi idanunta duk a kumbure, gaishe su ta yi. Abba ya bita da kallon tausayawa, sai a kwanakin nan ne ta soma magana amma tun bayan faruwar lamarin ta zama ƴar kallo. Suka amsa gaisuwarta, jin Ibb ya kira sunanta gami da jajanta mata ne ya sanya Abba kuma yarda dagaske dai akwai sanayya tsakanin Humaira da wanda suka kira da Fadeel. "Ina Yaya Fadeel?" Ta furta tana duban Ibb don tun wayarsu take ta neman layinsa yana ƙara ba a ɗagawa. Ya sanar mata da yana asibiti, tausayinsa ya kamata, ta yi fatan Allah ya ba shi lafiya suka amsa da amin daga haka ta mike ta koma ciki. Daddy a take ya yi kiran Commisioner na ƴan sanda wanda ya kasance abokinsa ya shaida mishi batun ɓatan su Humaira, nan ya ce ya san da maganar. Ya ƙara roƙonsa akan a tsaurara bincike ko Allah zai sa a dace. Daga haka suka yi sallama, suka yiwa Abba bankwana da zummar za su dawo, shima Abban ya tabbatar musu zuwa anjima zai shiga duba Fadeel. *** Raihana ta ci karo da Mami a falo, Mami ta ce. "Su waye baƙin?" Ɗan murmushin dole Raihana ta yi. "Iyayen Yaya Fadeel ne wanda ke son auren Humaira suka zo jajantawa Abba. Shima yana asibiti ba lafiya." Daga haka ta yi gaba ta bar Mamin a tsaye shiru. Sai kuma can ta ankara ta kai duba ga mutanen dake falon, ƴan uwan mahaifiyar Ummita ne da suka iso daga Bichi sai kuwa yan uwan Abba zaune ana ta jajantawa waɗanda wasunsu a cikin magana suke watsawa Mami habaici da baƙar magana. A ganinsu wannan ba tsautsayi bane, akwai lauje cikin naɗi. Juyawa ta yi ta shige ɗakinta da sauri ta rufe da muƙulli. *** A wannan daren sai ga waya daga kidnappers din Humaira kai tsaye Abba suka kira. Ya ɗaga ba tare da sanin ko su waye ba, lokacin su na tare da makwaftansa da wasu cikin yan uwansa maza ana zaune. "Da Alhaji Yusuf muke magana?" Abba ya amsa da sauri. "Eh, ni ne." "Sharaɗi na farko, idan a cikin mutane ka ke ka tashi ka bar wajen. Ko da alama kar ka nuna wani abu da zai sa a fahimci wani abu a saman fuskarka. Ka tashi maza ka koma ɗaki muddin kana son yaranka su tsira da rai da lafiyarsu." Jin haka Abba ya miƙe gabansa na dukan tara-tara, wannan kiran yake addu'ar ji don ya shirya salwantar da duk abin da ya mallaka matuƙar su Humaira za su dawo gida cikin aminci. Hanyar ɗaki ya nufa ba tare da ya da kowa komai ba suka bishi da idanu kawai. Muryarsa har tana rawa ya ce. "N..a.na..matsa. Ni kadai ne a ɗaki." Wata shu'umar dariya aka saki da ƙarfi sannan aka ce. "Dakyau! Ka buɗe kunnenka ka saurare mu dakyau! Kana da nan da awanni arba'in da takwas ka kawo kuɗin fansar yaranka miliyan biyar muddin kana son su ƙara shaƙar numfashi a duniya. Idan kuwa ka yi gangancin furtawa ƴan sanda wannan zancen toh shakka babu sunan msu matattu. Kar ka manta muna sane da komai dake gudana a nan. Idan kunne ya ji toh jiki ya tsira." Abba da tuni hawaye sun wanke mishi fuska yana shirin magana ya ji sun daka tsawa. "Don ubanku nace ku yi magana da Babanku! Ku tabbatar masa kuna hannunmu!" Sai kuma ji ya yi muryar Ummita ta zabga uban ihu, sai Humaira mai kiran sunan Abba da iyakar muryarta. Da alama dai wani baƙar muguntar aka yi musu. Abba ya miƙe tsaye yana fadin. "Ummita! Humaira! Ku yi hakuri don Allah kar ku cutarmin da ƴaƴa, in sha Allah zan ƙoƙarta cika umarninku." Jin haka sai aka sheƙe da wata iriyar dariya daga ɗaya ɓangaren sannan aka ce. "Idan ka yi hakan ka taimaki kanka da kuma su. Ka kiyaye sharuɗɗanmu ko kuma ka yi dana sanin abin da zai biyo baya!" Abba kuka yake sosai ya amsa da toh, aka datse layin kiran. Har lokacin bai bar rawar jiki da kuka ba, muryoyin yaransa na mishi amsa kuwwa a cikin kunne, ya rasa me zai yi, mene ne mafita? Ga shi nan dai an hana shi yin furucin ga ƴan sanda dole haka za su yi shiru da iyalinsa su tattauna a haɗa kudaden a biya kudin fansa. ***  *LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* 09034973645 A can kuwa, Wizzy yana kammala magana da Abba ya fidda layin a wayarsa ya kakkarya ya zubar, lokaci guda kuma ya mayar da layinsa. Suka dubi juna suka kwashe da muguwar dariya. Humaira da Ummita aka titsa ƙeyarsu zuwa cikin ɗakin. Babu laifi wajen da suka sauya ya fi wancan kyau, komai tsaf sai ƙura kuma ga dukkan alamu sabon gida ne da ba a kammala aikinsa ba. Banɗakin akwai ruwa har da butar alwala. Wajen dai ya fiye musu ɗayan amma kuma hankulansu ba a kwance suke ba. Ai babu wani gata da za a yi musu alhalin su na hannun azzalumai abin ya yi musu daɗi su samu kwanciyar hankali. Daga Ummita har Humaira tun sadda aka garƙame su a ɗakin ba sa aikin komai sai kuka hakan na da nasaba da jin muryar Abba da suka yi wanda gaba ɗaya sun fitar da ran ƙara ji ko ganin wani cikin fuskokin da suka sani. Wizzy kuwa bayan dawowar Badboy daga rufe ƙofar ya dube su ya ce. "Aski fa idan ya zo gaban goshi ya fi zafi, wannan lokaci ne da zamu ƙara zage damtse kuma mu yi takatsantsan don cik umarninta, a ƙarshe mu ma mu kwashi rabonmu, ta sallame mu." Babba wanda ke faman hura hanci yana fitar da huci ya soma magana a kausashe. "Wai ni fa bana son rainin hankalin da take yi mana! Matar nan tun da ta bamu aiki ba ta yarda ayi waya da uta sai rubutun saƙo. Ita ba ta san hatsarin da ke tattare da hakan ba? Idan fa ta yi sakaci har wani ya yi ya gani to fa akwai matsala. Sannan ta ƙi ta bayyana kanta sai ɗan aiken da ta ke turowa, ita kenan ko kama mu za a yi ta tsira kenan? Ba mu san wace ce ba, kuma ba mu san komai a kai ba, namu kawai aiwatarwa idan an cafke mu ta ci bulus kenan?!" Wizzy ya ɗaure fuska bai ce komai ba, ganin haka Badboy ya cafe. "Kai Babba ka iya kalamanka, ka sani koda wasa idan har ba mu ne muka so ba, toh fa ba za mu taɓa kamuwa ba. Mun fi ta iya shege ai kai ka sani. Ni fa duk ba wannan ne damuwata ba, yarannan su na hargitsa lissafina amma kai Oga ka ƙi bani damar gwangwajewa. Kenan haka muna ji muna kallo za mu bar su shikenan sun sha?" Sai a sannan Wizzy ya kalle shi. "Ba wannan aka umarcemu  da yi ba, asalima don horo ne ya sanya muka kai su tsohon gidan gonar can don kawai su shiha taitayinsu amma tun farko ba ya daga cikin bajat dinmu. Kai ne ka fiye garaje, ai na ce maka akwai lokacin da hakan za ta kasance, mu bari mana har mu samu tabbacin kuɗaɗen nan za su faɗo hannunmu tukunna mana, sai mu yi duk abin da muka ga zamu iya. Mu dai tabbatar ba mu kashe su ba don ba shi aka sanya mu ba." Suka yi shiru babu wanda ya tanka masa musamman Badboy da ke jin haƙurinsa na dab da ƙarewa akan ƴanmatan musamman Humaira da surarta ke fisgarta. ***   Hankalin Anti Maijidda (babbar yayar mahaifiyar Ummita ta Bichi) a tashe ta shigo babban falon na Mami da jama'a ke zaune ana jajanta wannan lamari na su Humaira. Ba ta ƙasar gaba daya ta je Umarah sai a jiya ta diro Kanon, ko gida ba ta je ba kai tsaye ta ce a sauke ta a gidan. Tana shiga ta zube jikin ƙanwar Abba, Baba Amina  da suka saba tun a baya tana kuka sosai ana ba ta haƙuri. A lokacin ne kuma Mami ta shigo daga ɓangaren Abba cikin dogon hijabinta, ta gama jin yadda aka yi da Abba da kidnappers din akan kuɗin fansa. Jin muryarta su na gaisawa da makwaftan da ba su jima da leƙowa gidan ba ya sa Anti Maijidda miƙewa kamar wacce aka tsiƙara ta hau tafi raf raf har sau uku, wannan ya ja hankulan kowa kanta yayinda wasu suka shiga tunanin kodai ɓatan Ummita ya girgiza kwakwalwarta har haka? Mami kuwa cak ta tsaya kawai tana mai zubamata idanu. Maijidda kenan, macen da ba su taɓa raɓar juna da alheri ba, babu wata jituwa da ta ƙara haɗa su tun bayan rasuwar Fatima mahaifiyar Humaira. Maijidda ta soma magana murya a ɗage kuma a kausashe. "Ki zuba ruwa a ƙasa ki sha Maryam! Ki tara jama'arki ku yi kiɗa ku yi rawa har da juyi! Yau burinki ya cika! Abin da kika jima kina ƙullawa akan yarannan yau kin cika shi!" Jin haka Baba Amina ta miƙe a firgice cikin kaɗuwa ta fisgo hannun Maijidda. "Maijidda ki shiga hankalinki mana! Ki yarda da ƙaddara ki yi imani da ita. Wannan wane irin zantukan banza ki ke yi akan baiwar Allahn da ta riƙi amanar ɗiyar ƴar uwarki da amana da kulawa tsawon shekarunnan koda wasa Ummita ba ta taɓa kokawa da ita ba? Wane irin baƙin ƙazafi kike shirin yiwa baiwar Allahn nan?!" Anti Maijidda ta fashe da kuka sosai tana nuna Mami da yatsa. "Har abada ni Maijidda ba zan taɓa kaunarta ba, kuma ba na jin zan yarda da ita koda ace gaba ɗaya mutanen duniyar nan za su taru su yi mata kyakkyawar shaida! Baƙar azzaluma ce! Amina ni nasan wacece Maryam, ni zan ba da labarinta! Don haka idan har bincike ake son yi na gaske daga cikin gida, a soma daga kanta da kuma azzalumar uwarta!" Wannan ƙazamin furucin ya sa Mami ta fusata sosai.  Hannunta na rawa kamar yadda dukkan gaɓɓan jikinta suke yi ta nuna ta da yatsa, daƙyar maganarta ke fita saboda zuciyar da ta taso mata da kuma ruwan hawayen da suka wanke mata fuska lokaci guda. "Na shanye dukkan baƙaƙen maganganunki na tsawon shekarunnan ba don komai ba sai domin albarkacin ƴar uwarki marigayiya Maimuna da muka yi zaman mutunci da ita! Na kuma cigaba da jure duk wani cin kashinki a dalilin Ummita jinin Maimuna ce da Naziru. Ban da haka ba ki da wata ƙima ko daraja a idanuna!" Baba Amina da mutanen ɗakin dakyar suka tsawatar aka kashe zancen inda Mami ta fice daga falon cikin ƙunar rai zuwa ɗakinta inda Anna ke zaune kuma tsaf ta ji dukkan abin da ya faru. Allah ya taƙaita lamarin Jannat ba ta gidan, ta fita dubiyar wata ƙawarta da aka yiwa aiki a asibiti, da abin zai fi haka ɓaci. Anna ta dube ta sai kuma ta yi dariya. "Maryama kenan, wannan shi ne sakamakon bautar da ki ka yi na riƙon Ummita ko? Wannan ranar nake jira dama, ban kuma zaci zan gani nan kusa ba. Shashashar yarinya! Ga shi nan tun ba a je ko'ina ba kin kwashi kashinki a hannu. Da ace tun a farko kin ji maganata hakan da bai faru ba. Yanzu sai kiyi kuka da kanki akan duk abin da ya faru." Mami ba ta ce da Anna komai ba, sai ta fidda hijabin da ta zumɓula ta ɗauki wayarta kawai ta zauna ta yi shiru tana aikin dannawa, Anna ta cigaba da zabga ruwan bala'i, da Mami ta ga abin ba na ƙare ba ne, kawai sai ta fice zuwa ɗakin su Raihana ta bar mata ɗakin. *** Fadeel ya farka gami da ƙurawa silin idanu, shiru ya yi yana ƙoƙarin tunano dalilin kwanciyarsa ciwo, a hankali kuma ya juya kansa ya dubi ɗakin. Ibb ne kaɗai a zaune yana danna waya bai ma lura da farkawarsa ba. Ya lumshe idanunsa lokaci guda komai ya dawo kwanyar kansa, a firgice ya miƙe zaune. "Ya Salam!" Ya faɗi da ƙarfi yana mai fisge drip din da aka sa mishi. Furucinsa ya sa Ibb mikewa da sauri ya nufo shi gami da riƙe kafaɗunsa. "Fadeel yi a hankali mana." Jin haka ya dube shi da rashin kwarin jiki. "No Ibb, kwana nawa nayi a nan? Humaira na hannun kidnappers, za su kashemin ita. Ka bar ni na je nemanta." Daidai nan Alhaji da Daddy suka shigo. Fadeel ya miƙe jiri na kwasarsa yayinda Ibb ke ɗan riƙe shi, Daddy da sauri ya tarbe shi ganin kamar zai faɗi ya ce. "Fadeel kwantar da hankalinka, in sha Allahu za'a ga Humaira." Kawai sai ya ji hawaye sun zubomasa, wato za ma a gan ta ba wai an ganta ba? Ya girgiza kai yana kallon Daddy amma sai ya kasa magana. Suka taimaka suka mayar da shi mazauninsa. Daddy a nutse ya karanta masa duk yadda suka yi da Abba ya kuma ƙara da faɗin. "Yanzu haka ba mu jima da waya da shi ba, ya tabbatar mana da cewar sun samu kira daga mutanen, sun kuma buƙaci kuɗi. Wannan damuwar ba zai magance maka kowacce matsalar ba, addu'a da kuma sadaka ita zamu duƙufa yi. Yanzu idan ka ce za ka fita nemanta, ta ina za ka fara? Ka san a inda suke ne? Daji, cikin gari, kasuwa, ƙauye, kai ko ma ba a garin suke ba gaba ɗaya wannan sanin Allah ne kaɗai don haka ka samarwa kanka ƙarfin zuciya ka dage da kai wa Allah kukanka. Babu abin da ba ya magancewa." Daddy ya cigaba da kwantar masa da hankali har da cewa koda ace kudaden da Abban za su haɗa ba za su kai ba, shi ya ji ya gani zai san yadda za'a yi a cika a bayar don su kuɓuta, balle kuma shi Fadeel din wanda yake jin zai iya sadaukar da dukkan abin da ya mallaka a doron ƙasa don kuɓutar rabin jikinsa daga hannun azzaluman nan. Sosai ya ji dadin zantukan Daddy, da wannan ya lallaɓa ya yi wanka, brush, da alwala, Ibb ya ba shi kaya ya sauya. Daga nan ya hau ramuwar sallolin dake kansa. Bai kai ga idarwa ba sai ga Anti Amarya tare da Murja sai ko Fu'ad da ya kawo su, hannun Murja riƙe da kwandon abinci. Ta gaida su Abban sannan ta karasa ta ajiye gefen gadon. Gefe ta koma tana satar kallon Fadeel ɗin da a kwana ɗaya kawai ya zabge. Zuciyarta na wata iriyar tafarfasa.   'Ka yi ka gama Fadeel, na rantse maka koda ace Humaira ta fito ni Murja sai na kashe ta da hannuna. Ballantana ma ba za ka ƙara ganinta ba.' Ta yi maganar a zuci, su Alhaji suka tafi saboda yamma ta kawo kai yayinda Ibb suka fita don yi musu rakiya. Fadeel na idarwa ya dubi Anti Amarya ya gaishe ta, ta amsa tana mishi sannu. Ido ta ɗan yiwa Murja hakan ya sa ta saurin gaida Fadeel, ya amsa ba tare da ya kalleta ba.   Nan suka zauna har sai da Fadeel ya ɗan sha ruwan shayi dakyar amma sam ya ƙi yarda da cin abinci, tunaninsa ko a wane yanayin Humaira take? Watakila ma ko abincin ita ba a ba su sun ci ba. Wannan ya daƙilar da shi daga ci. ***   Sahabi saurayin Ummita kullum sai ya zo gidan ya gaida Abba da Mami, gaba daya ya komaɗe ya rame tsabar tunanin Ummita. Iyaye da ƴan uwansa babu wanda bai shigo jajantawa ba. Hakanan ƴan makarantar islamiyyar su sun zo sun kuma yi saukar Alkur'ani akan Allah ya bayyana su. Hatta da yan makarantar su Ummita na boko sun zo har da malaman makarantar an jajanta. Aka yi addu'a suka tafi.   Labarin dai yana ta yaɗuwa don har waɗanda su Abban ba su ma sani ba sun zo sun taya su jaje, da yawansu a social media suka ci karo da shi. Mubarak dake Ghana yana jarrabawar ƙarshe hankalinsa gaba daya yana Kanon, ba don Abba ya ce kar ya zo ba ya zauna har ya kammala da tuni ya dawo. Hakanan su Yassar ba su zo ba. Amma sosai abin ya taɓa su duk da ƙiyayyar da suke yi musu.         Ɓangaren Futuha kuwa ƴar Dubai, kasancewarta mai mu'amala sosai da yanar gizo sai ga abin nema kuma ya samu. Bidiyo sosai ta yi tana kuka ga hotunan Ummita da Humaira daga ƙasa ta ɗora a shafinta tana addu'ar Allah ya bayyana su a ƙarshe ma har da sanya muryar shahararren Malamin nan wato Sudais yana addu'a. Koda ta ɗora hankalinta kwance ta shiga duba yadda ba a ɗauki dogon lokaci ba bidiyon ya yaɗu, nan fa jama'arta suka fara jajanta mata su na tambayar dama Humaira mai shafin Deelsha's Delicacies yar uwarta ce? Da yawa ma wadanda ba su san Humairar ba ko shafinta sai lokacin suka dinga followinh dinta, lokaci guda shafinta ya yi jama'a fiye da dubu talatin. Hakanan shafin Ummita ma ya yi jama'a. Raihana tana kallon duk abin da ke wakana amma ba ta magana, karshe ma sai ta kashe wayarta gaba daya ta ajiye.  Tun da Abba ya shaida musu da kuɗaɗen da aka ce a bayar na fansar Humaira da Ummita ta ke jin ƴar nutsuwa, ko ba komai kenan su na lafiya kuma Abban ma ya tabbatar musu ya ji muryoyinsu amma bai ce musu ga a yanayin da ya ji ba gudun tayar musu da hankula. ***   Fadeel da Ibb suka shirya tsaf a washegari zuwa gidan su Humaira kamar yanda Fadeel din ya nema. Hankalinsa ya kasa kwanciya da zamansa a asibiti alhalin ba a ga Humaira ba, kuma bai je ga iyayenta ba. Wannan ne ya sanya su Alhaji goyamishi baya don haka ana ba shi takardar sallama ya kama hanyar gidan. Sun samu tarba na mutunci daga Abba, Tasleem tun ganin da ta yiwa Fadeel matsayin saurayin Humaira ya zo jajantawa ta ji hankalinta ya yi mummunan tashi. Kishin nan daɗaɗɗe na Humaira ya taso ya soma  cin zuciyarta. Har gobe akwai son Fadeel a ƙirjinta, ta kuma tabbata da ace shi ta aura da yanzu wani labarin ake ba wannan ba. Kusan lokaci guda suka shigo gidan da Fadeel anan ta gan shi, shi kuwa bangaren Abba suka nufa inda Ƙasim da ya yi musu iso ya raka su ciki. Fauziyya ce ta yi mata rakiya gidan, tana kuma lura da sauyin da ya zo mata lokaci guda sadda Ƙasim ya dawo yana shaida mata ai manemin auren Humaira ne. Ta yi shiru ba ta ce mata komai ba tana ƙara nazarinta.   A falon ta bar Fauziyya ta faɗa ɓangaren Anna tana huci. Nan ta tarar da ita zaune da Jannat wacce ke zaune tana taunar gasasshiyar kazar da ta siyo suna hira da Anna kai ka ce babu wani tashin hankalin da ake yi a gidan. Ganin yanayinta ya sanya su dubanta.   "Toh mai ciki, yau kuma wa ya taɓo ki?" Ta zauna idanunta suka cicciko da kwalla yayinda zuciyarta ke faman tafarfasa. Kwafa ta yi kana ta amsa. "Wai Fadeel na gani ya zo jajantawa Abba fa? Har yanzu dama yana tare da Humaira? Shi ne don munafunci Humaira ta ci amanar Mami ta ɓoye zancen?" Murmushi Jannat ta yi. "Ke ban da abinki ina Humairar take a yanzu? Kina tunanin shirin na wasa ne za ta dawo, ai daga can inda take sai wata duniyar kuma ba wannan da muke ciki ba. Duk fa wanda ya samu dama ya dama.  Kuma da kike wannan maganar ba yanzu gashinan kin auri Hamza ba? Ba kya sonsa kika bari ciki ya shige ki?" Tasleem ranta ya ɗan yi sanyi jin yadda Anti Jannat ke fadin kaddarar Humaira kai ka ce ita ta rubuta hakan. Batun cikinta ya ƙara jefata damuwa, dama ba da son ranta ta samu ba kuma Hamza ya rantse sai ya yi mugun saɓa mata idan ta zubar. "Wallahi Anti idan har zan samu na auri Fadeel zan iya kashe ko nawa ne a yimin aiki a kan Hamza ya sake ni. Anti wai kin taɓa ganin Fadeel kuwa da irin yadda ya haɗu? Wallahi ba zan iya zuba idanu wata ta kwacemin shi ba." Anna tsohuwar banza ta kwashe da dariya madadin ta yi kwaɓa akan wannan haramcin da ake aikatawa sai ma ta ce. "Kina da Jannat Firdausi ai babu ke babu fargaba. Yadda aka yi wancan haka wannan ma zai kasance labari." Suka yi dariya. Can kuma Jannat ta ɗan jinjina kai. "Ko wane ne wanda ya aikata wannan kidnapping din ya yi matuƙar burgeni, da ace ina da damar ganinsa sai na mishi babbar kyauta. Sai hakan ya zo mana da nasara kuma akan gaɓa, Boka ya tabbatarmin da cewa Humaira a can za ta haɗu da ajalinta. Itama Ummita babu tunanin za ta rayu balle har su samu damar kuɓuta su dawo. Kawai dai zan so dawowar ita Ummita, yarinyar ta iya bauta." Tasleem ta yi murmushi. "Nima dai Ummita ba ta yimin komai ba, ba ni da wani ƙulli da ita kamar Humaira. Wallahi Anti na tsane ta na kuma tsani duk wani mai sonta." "Har da ni kenan!" Suka juya don ganin mai furucin a razane. ®️Rufaida UmarMurja ta jima tsaye jikin tagar falo tana hangen fitar Fadeel a gigice. Ranta idan ya yi dubu toh ya ɓaci. Hankalinta kuwa idan akwai abin da ya fi gaban tashi toh ta ya yi wannan dalilin ne ya sanya ta komawa cikin daki da sauri-sauri ta ɗauko gyalenta sai ko waya da jaka ta fice daga gidan a birkice har Anti Amarya wacce ta fito daga nata ɗakin tana tambayar ko lafiya kuma ina za ta je amma babu amsa. *** Kasancewar tare suka isa asibitin da ƴan sanda wannan ya sa a gaggauce aka karɓi Humaira da Ummita zuwa emergency. Abba ya kasa zaune balle tsaye, ban da hawaye babu abin da ke fita daga idanunsa, ga jiri na kwasarsa yana ta ambaton sunan Allah kamar zai ciri baki. Daidai lokacin Fadeel ya shigo a birkice ya ƙarasa ga Abba. "Abba sun fito? Su na ina? Me ya same su?" Dukkan waɗannan tambayoyin ba a hayyaci yake yin su ba. Abban ma da ba a wani nutse yake ba sai ya kasa tanka mishi kawai sai ajiyar zuciya da kallo ga lebban na motsi amman ko harafi guda ya kasa fitarwa sai D.P.O ne ya karɓi zancen ya yiwa Fadeel bayani. "Ka kwantar da hankalinka, in sha Allahu babu abin da zai faru garesu. Likitan ya tabbatar mana ga dukkan alamu kwayoyi aka ɗura musu amman in sha Allah za su yi iyakar ƙoƙari a kansu." Fadeel ya dafe kansa ya yi juyin, ya yi safar ya dawo ya kai marwar amma wannan kalmar ta ya kwantar da hankalinsa ya kasa samun matsaguni a zuciyarsa. Kwayoyi? Ya ma rasa inda zai jefa zancen a kwakwalwarsa ballanta ya samu ya yi aiki da shawarar D.P.O Salahuddeen.  *** A can gida kuwa, Tasleem tun sadda ta kai labarin tafiyar Abba fanso su Humaira, Jannat ta dauki waya hankali tashe ta kira Bokanta. Kaca-kaca suka yi sosai tana zaginsa akan ita fa ba su yi haka ba. Wannan ya sa  Boka tun a wayar ya ci alwashin sai ta girbi wannan tozarcin da ta yi masa. Kasancewar idanunta sun rufe ruf sai kawai ta ja mugun tsaki ta katse kiran. Awa bai fi ɗaya tsakani ba, sai ga wayar Abba zuwa ga Mami, a gaggauce ya sanar da ita kuɓutar su Ummita ya kara shaida mata cewar su na asibiti. Hankali a mugun tashe suka fice tare da Ƙasim da Raihana wacce lokaci guda wani mugun zazzaɓi ya rufe ta musamman jin cewar su na asibiti. Suka yi kiciɓus da Kawun Humaira da matarsa Hajjo wadanda isowarsu kenan garin. Ba su tsaya yi musu dogon bayani ba, Kawu ya bi su yayinda ya ce Hajjo ta tsaya ta jira dawowarsu a gida. ***   BAYAN AWANNI... Mummunan labarin da ya iske su Abba na keta alfarmar da aka yi ga Ummita ya sanya shi sumewa bai ko iya jin ƙarshen ba balle ya san ko har Humairar ma an taɓa. Nan aka kwashe shi shima don ba shi taimakon gaggawa. Raihana kuka kamar ranta zai fita yayinda Mami ke taya ta. Kawu da Fadeel kuwa tashin hankalin da suke ciki ba zai misaltu ba. A gabansu aka fiddo su bayan an yiwa Ummita ɗinki na mugun raunin da aka ji mata aka sauya musu ɗakunan zuwa na hutu, daki mai gado biyu. Fadeel ya ƙurawa Humaira idanu kamar kirjinsa zai fashe haka yake ji, nan take idanunsa suka kaɗa jawur. Gaba ɗaya ta lalace ta yi rama tamkar wata halittar ce ba ita ba sai ko hancinta da ya ƙara fitowa. Har aka shige da su bai iya kauda kansa ba. Shi ya yi ƙarfin halin biyan dukkan abin da aka kashe har da na kama ɗaki.   Cikin ƙanƙanin lokaci labarin kuftowar su Humaira ya cika gari, mutane da waɗanda suke dangi da ma yan uwa na gari suka dinga tururuwar zuwa yi wa su Abba barka, babu wanda aka bari shiga wajensu, hakanan labarin abin da ya afku gare su bai fita ba. Yan jarida kuwa suka dinga yaɗa rahoto, hakanan social media ta dauka.  Futuha mutanen Dubai ta ƙara yin bidiyo mai nuni da damuwa da kuma farin ciki tana shaida wa jama'a cewa an ga ƙannenta. Nan aka hau taya ta murna sosai. Mutanen Bichi da labari ya iske su su ma baa bar su a baya ba. Anti Maijidda ta yi kuka kamar ranta zai fita jin labarin keta haddin da aka yi ga Ummita, matsayinta na babbar yaya ga uwarta ya sa Abba sanar da ita a sirrance.   Sahabi kuwa baki har kunne, sun zo shi da abokansa yayinda mahaifinsa takanas ya zo ya taya Abba murna da addu'ar Allah ya kiyaye gaba.   Kwanakin su Humaira biyu suka dawo hayyacinsu. Ummita ce ta soma farfaɗowa, ranar Allah ya taƙaita Anti Maijidda na zaune tare da Baba Amina sun yi jugum su na dan hira jefi-jefi hannuwansu riƙe da casbaha. Wani gigitaccen ƙara Ummita ta saki da ya yi masifar tayar da hankulansu. "Wayyo Allahna! Kar ka kashe ni! Ka rabu da ni! Na haɗa ka da Allah ka rabu da ni!! Wayyo Allahna!!!" Cikin kuka da tashin hankali suka yi kanta su na riƙewa, aka bankaɗo ƙofar aka shigo, su Abba ne da  ihun Ummita ya iske su. Raihana a guje ta nufi wurin Nurses dake tahowa, kafin ta kai ga magana suka ce sun ji. An tafi kiran likitan. Su na shiga sai ga Likita, aka fitar da kowa a ɗakin. Gaba ɗaya matan kuka sosai babu kamar Raihana da take jin kamar ta shiɗe. A yadda take jin zuciyarta za ta iya fille kan wanda ya aikata wa yan uwarta wannan tozarcin. Koda likitan ya ƙarasa gareta flask din ruwan zafin dake ajiye a gefenta kawai ta ɗauka ta jefa masa. Ba don Allah ya sa shi kaucewa ba da babu abin da zai hana a same shi. Tana cikin wannan gigitar Humaira ta farka a matukar firgice, ta kira sunan Ummita da karfi sannan a guje ta diro ta zo ta rungumeta tana kallon jama'ar ɗakin kamar wasu sabbin halittun da ba ta taɓa gani ba. "Su waye ku? Me za ku yi mana?! Ku fice ku bar nan! Wallahi ku ka yi ƙoƙarin zuwa kusa da mu zan ji maku ciwo." Sai kuma ta juya a mugun firgice tana tattaɓa jikin Ummita dake kuka kamar ranta zai fita. "Ummita! Yi shiru, Abba zai zo. Naji suna cewa yana hanya. Yi shiru, sai mun kashe su." "Kin.." Likitan ya ƙaraso zai soma magana Humaira ta juya da azama tana nunashi da yatsa. A sannan su Abba gaba daya sun shigo sun kasa daurewa. "Kar ka taɓamin ƴar uwa! Zan kashe ka!!" "Humaira, Ummita." Humaira na ganin Abba ba ta ko damu da sauran jama'ar Abba ta karasa a guje ta rungume Abba tana kuka mai tsuma zuciya. "Abba za su kashe mu! Abba ka cece mu! Ka ɗauke mu mu bar nan!" Irin riƙon da ta yiwa Abban ba na wasa ba ne har maɓallan wuyar rigarsa sai da suka fita. Cikin hawaye ya ce. "Mamana babu abinda za su yi maku, likitoci ne. Kun kuɓuta daga hannun azzalumai. Ki kalla dakyau, ga Maminki ga yar uwarki Raihana. Kin gane Kawunki?" Ta tsaya cak kamar wata sokuwa tana kallonsu ɗaya bayan ɗaya, Ummita kuwa da nos ta lallaɓa ta yi mata allura tuni bacci ya kwasheta. Kawai sai ta soma ruwan wasu sabbin hawayen ta ma kasa cewa uffan. Zuciyarta ta gasƙata eh sun kuɓuta daga hannun azzaluman, amma kuma ta ji tana tantama tana gani ko mafarki ne. Wannan ya sa Raihana tahowa da sauri ta rungumeta ta kara sautin kukanta. A hankali ta ɗaga hannunta ta ɗaga fuskar Raihana ta na kallo kamar wata baƙuwar halitta ce gabanta, sai kuma da rawar murya ta ce. "Raihana ce?" Raihana saboda ƙarfin kukan ma ta kasa magana sai kawai ta ɗagamata kai. Humaira ta rungumeta sosai suna kukan tare. "Amm, don Allah a ragu a ɗakinnan. Alhaji ina son magana da kai." Fadin Likita, ganin haka duk aka fice banda Raihana wacce Humaira ta riƙe hannunta gam tamkar ita kaɗai ta gani. *** Likita ya dubi Abba cikin nutsuwa ya soma magana. "Lamarin ita Ummita na buƙatar rarrashi da ja a jiki. Kaso casa'in na ire-irenta da hakan ke afkuwa a kansu sukan samu matsala ta rudani, firgici da kuma rashin yarda ga kowa. Wasu kuma yakan taɓa musu kwakwalwa. Zamu yi mata gwajin kwakwalwa don a tabbatar da komai na ta lafiya kalau yake." Abba ya share fuskarsa. "Toh Likita, nidai babban burina lafiyarsu. Allah ya sa komai lafiya." "Ameen." Ya amsa cikin tausayawa yana mai lallaɓar Abba. *** Cikin iko na Ubangiji an yiwa Ummita gwajin kwakwalwa kuma an tabbatar da komai lafiya. Wannan ya kwantar da hankulansu. Humaira dai ba ta dogon magana tun farkawarta, kowa ta gani sai dai ta ambaci sunansa, idan an rungumeta an sa kuka itama ta soma. Da daddare ba bacci sai razana, ga Ummita haka. Wannan yasa aka raba musu ɗaki. Fadeel na zuwa, kuma abin mamaki Humaira na ganinsa ta kira sunansa, abin sosai ya ji dadinsa ya kuma tsaya a ransa. Sai da suka kwashe sati biyu a asibiti kafin su tattara su dawo gida. Babu laifi sosai zuwa lokacin sun samu nutsuwa ba kamar farko ba. Sai dai daga Ummitan har Humaira duk sadda tunanin cin zarafin da aka yi musu da kuma keta haddin da aka yiwa Ummitan sai su yi ta kuka. Har zuwa lokacin babu wanda ya san da mummunan labarin sai ko Anti Maijidda da Mami wadanda Abban ya faɗawa. Anti Maijidda nan fa ta dage akan lallai sai a ba ta Ummita su tafi Bichi, Abba ya ƙi amincewa. A dole ta haƙura ta tafi tana ƙunar rai da jin tsanar Mami har cikin ƙoƙon ranta. Jannat ko a fuska sai ka rantse nan jimamin duniya take yi akan lamarin don ba ta nuna komai wanda zai sa wanda bai sani ba ya fahimci takun saƙarta da su. Hakanan Anna wacce ta daurewa zuciyarta ta taka har ɗakinsu ta duba lafiyarsu bayan ta je asibitin a baya har sau uku. Wannan ya wanke ta daga zargin mutane da rashin nuna kauna ga su Humaira a baya. ****LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* 09034973645 Sai da su Humaira suka samu sati hudu cif kafin su ɗan maido da jikinsu, da kuma walwala kaɗan. Sukan zauna cikin jama'a, a taɓa hira da su idan ka cire Ummita da har lokacin ta tuno aika-aikar da aka yi mata sai kawai ta fashe da kuka wanda hakan ke tayarwa Humaira hankali itama ta sa nata kukan sai su haɗu su yi ta yi. Kawun Humaira ya so su koma can Nijar da ita amma nan ma Abba ya nuna sam bai amince ba dole haka ya tattara matarsa suka koma gida.   Su na zaune a ɗaki, Ummita riƙe da Alƙur'ani tana karantawa zuciyarta na yin sanyi yayinda Humaira ke kwance saman katifa ta yi shiru gami da zubamata idanu kusan ma hankalinta ba a kanta yake ba, ta lula wata duniya ta daban na tunani. Raihana ta shigo ta iske su haka, dawowarta kenan daga makarantar boko wanda har lokacin Ummita ta ƙi amincewa ta koma ganin haka babu wanda ya takura mata shi ma mai makarantarsu da ya zo har gida ya jajanta ya ce a kyale ta zuwa wani lokacin. "Wash! Wallahi na gaji! Ke kuma kina da baƙo a falon Abba." Ta faɗi da murmushi tana duban Humaira duk a ƙokarinta na son ta ga komai ya dawo daidai a mu'amalarsu. Humaira ta ɗan dube ta gami da ɗan haɗe gira kaɗan. "Wa kenan?" "Fadeel." Ta yi shiru, ita ba ta ce uffan ba balle ta yi wani yunƙurin kawai sai ta maida kai ta kwanta ta yi shiru. A karan kanta ba za ta ce ga abin da take ji game da Fadeel din ba, lamarin dai ba yabo balle kuma fallasa. Ummita na ji ba ta iya cewa komai ba, Raihanar ma ba ta sake magana ba sai ta miƙe ta rage kayan jikinta ta shiga wanka, ba ta son duk abin da zai takurawa rayuwar ƴan uwannata da ta ƙara sanin girman ƙauna da shaƙuwar da ke tsakaninta da su bayan sun yi mata nisan da ta zaci har abada ba za ta ƙara sanya su cikin kwayar idanunta ba.   Ummita tana kai wa ƙarshen surar da take karantawa ta juya ta dubi Humaira.    "Ki je ku gaisa mana." Humaira ta yi mamakin jin wannan furucin naga bakin Ummita, tun bayan dawowarsu ba ta wani magana kwakkwara, ko hirar Raihana ke jansu da shi, sai dai ta basar ta yi shiru. Wannan murmushin da ba ya barin fuskar Ummita, babu shi babu labarinsa tun dawowarsu. Ita ɗinma ƙarfin hali take yi don faranta ran Mami da su Raihana ga kuma Ƙasim waɗanda gaba ɗaya suke nuna musu kulawa da ƙoƙarin ganin sun saki jikinsu. "Kin ji?" Maganar Ummitan ya ƙara katse mata  tunani. Tana so ta ja musu amma a yanzun duk duniya babu abin da ta ke so irin ta ga ƴar uwarta ta dawo tamkar yadda ta ke rayuwa a baya. Abu na  biyu kuma ta sani ba ta jin za ta iya ɗaukar waya ta kira shi da zummar godiya bisa hidimar da ya yi akan fitowarsu, don ko cikon da suka bayar na kuɓutar da su a hannun ƴan fansa ƙin karɓa suka yi da Abban ya maida musu, ta sani wannan ita ce damar ta amma hakanan ba ta son Fadeel din ya cigaba da shigemata shiyasa. Abban har gidansu ya je ya ƙara godiya sosai shi da Mami wacce a sannan ne ta ga gidan da ya kere na Aminiyarta Hajiya Lubna. Ganin Ummitan ta zubamata idanu ya sanya ta miƙewa. "Toh, na ji Ummita." Ta faɗi kamar ta fashe da kuka sai ta miƙe ta ɗora hijabi akan doguwar rigar atamfar da ke jikinta. Suka ci karo da Mami a falon wannan ya sanya ta tsayawa. Gidan yanzu duk an watse sai su kadai, Jannat ta tattara ta koma bayan dogon kiran da mijin ya dinga danno mata har abin ya kusan zame musu rikici sannan ta tafi ba don ta so ba. Tasleem kuwa tun fitowarsu da kwana biyu Hamza ya zo suka koma gida.     Cikin sakin fuska Mami ta dubi Humaira. "Ina zuwa haka?" Ta sunkuyar da kai sannan ta ce. "Wai Fadeel ne ya zo za mu gaisa." Nan da nan fara'ar dake saman fuskar Mamin ya ragu. "Zuwan me yake ta yi haka ne alhalin jinyar ta ƙare? Ina ce na muku iyaka da shi tun a baya?" Humaira ta jinjina kai. "Hakane Mami, kiyi hakuri. Ai gaisawa kawai zamu yi. Ya yi abin da ko maƙiyina ne ya cancanci na ƙara yi mishi godiya." Mami ba ƙaramin mamakin furucin Humairar ta yi ba wanda daidai da fuskarta ta nuna. Sai kuma ta jinjina kai. "Shikenan, ki je amma kar ki ɗau lokaci." Murmushi kaɗan Humaira ta yi sannan ta amsa da toh ta cigaba da tafiya. Ban da abin Mami, ita ba ta tunanin ma za ta yi auren, wane namijin ne zai aure ta bayan ta gama wulaƙanta duk masu kaunarta domin Allahn? Ta rasa dalilin da a ƴan kwanakin nan take jin sauyi a jiki da kuma kwakwalwarta. Wannan ne ya sa Fadeel samun rangwame daga wurinta. Ɓangaren Mami kuwa ji ta yi kirjinta ya yi wani irin bugu. Meke shirin faruwa haka? A duniya ba ta kaunar Fadeel ya raɓi Humaira kamar yanda bai raɓi Tasleem ba. Kai ba ma shi ba... Sai kuma tunaninta ya katse, ta haɗiyi miyau da ta ji yana mata zafi. Sai kawai ta nufi ɗakinta a gaggauce. Tabbas ta yi sake a kwanakin da suka shuɗe ba ta bayar an ɗoramata sabon aiki ba.  Wayarta ta fiddo ta shiga zarya a tsakar ɗakin tana jira a ɗauka daga ɗaya ɓangaren. Doguwar magana suka yi sai kuma ta hau murmushi hankali a kwance ta katse kiran ta shiga danna wayar karo na biyu inda ta tura kuɗi ga wani akawun lamba. Daga nan kuma ta ji wata irin nutsuwa ya saukar mata. ***   Ya kwashi mintoci  masu yawa a zaune anan, shigowar su Waleed ne ma ya ɗauki hankalinsa suke hirar makaranta yana biyemusu. Ya gama fidda rai daga ganinta, gefe guda ga tsoron kada a koma ƴar gidan jiya, tunanin da ya sanya gumi tsastsafo masa a goshi duk kuwa da iskar dake kaɗawa a falon har tana kaɗa labule. Sai dai kuma ba zato ya tsinci sallamarta, cikin sauri ya kalli hanyar yana mai amsawa da rawar murya.    'Please Fadeel, Control.' Zuciyarsa ta ba shi shawara, ya sauke nannauyan ajiyar zuciya. Ya zubamata idanu, ta  fara dawowa ainahin Humairarsa, fuskar ta ɗan ciko ba kamar farkon dawowarsu ba. Hakanan ta yi haske fayau dama can a bayan har da rashin samun wanka ga uban cizon sauron da tabonsa ya yi ja a jiki da fuskarta.   Ita kuwa kanta a ƙasa ta ƙarasa ta zauna ɗan nesa da shi, tana ji ya kaɗa su Waleed ciki akan su je su cire uniform dinsu. "Barka da rana." Ya yi furucin yana dubanta tamkar ya haɗiye ta. Sai a sannn ta ɗan ɗaga kai ta dube shi. Ganin yanda ya zubamata idanunsa ya sanya ta maida kanta ƙasa ta na jin wani yaam a jikin da ba ta saba ba a baya. "Ina wuni, ya wajen su Baba?" Fadeel da ke jin kamar an tsoma shi a aljanna ya faɗaɗa murmushin fuskarsa yana hamdala a ƙasan ransa. Dama komai ɗan hakuri ne, idan ka yi to fa zai wuce. Ya shanye wulakancin da zagin, yanzu ga shi nan ya soma cin galaba. "Kowa lafiya kalau Alhamdulillah, Sisterna ma ta zo daga Adamawa. In sha Allah zuwa gobe za ta zo ku gaisa." Sai ba ta watsa masa ƙasa a ido ba ta amsa da toh. Shiru ya biyo baya, a ɓangaren Fadeel ba ya so ya faɗi abin da bai yi daidai da ra'ayinta ba ta sauya fuska ta miƙe ta bar shi anan, ita kuwa godiya take son yi mishi don su yi sallama ta koma ciki amma ta rasa ma ta inda za ta fara sai can da ta ga ba shi da niyyar ce mata uffan sai aikin kallon da ba za ta ce yana ba ta haushi ko kuma faranta mata ba a lokacin, ta daure ta soma magana. "Mun gode bisa dukkan ɗawainiyar da ku ka yi mana, Allah ya ƙara arziki." "Ban yi abin da za ki godemin ba. Ke kika yi wanda zan godemaki. Nagode sosai and I..." Sai kuma ya yi saurin haɗiye zancensa, ya san komai na tarihin Humaira a sannan daga bakin Raihana, ya san ba ta jin turanci amma kuma dai kalmar I Love You ko yaro ƙarami da bai je makaranta ba ya sani. Shirun da ya yi ganin zai yi taɓargaza ne, gaba ɗaya ji yake da ace Humaira za ta ba shi dama, zancen aurensu kawai za a yi. Ya sani hatta da Abbanta ya buƙaci a ba shi lokaci kaɗan yaransa su dawo cikin nutsuwa sai a haɗa auren Ummita da na su, shi ne a karon kansa ya roƙi alfarma a kyale Humaira ta amince da batun aurensa da kanta. Yana kuma ji a jikinsa hakan ce za ta kasance daga yanayin sauyin da ya gani tattare da ita. "Shikenan?" Ta katse mishi tunani, ya ɗan lumshe idanu sannan ya buɗe su a cikin nata, ta kauda fuska ta yi shiru. "Toh, zan koma bakin aiki, dama zuwa nayi na duba lafiyarku. Ki gaishemin da Ummita da mutan gidan. Allah ya ƙara lafiya." Ta amsa da amin, cikin sanyin muryar ta ce. "Zan fadamusu. Nima ka gaidamin ƴar uwarmu, sai ta zo goben in sha Allahu." Ambaton ƙanwarsa Hannatu da ƴar uwarmu da ta yi ya sanya shi jin tamkar yana tafiya a iska tsabar mamaki da farin ciki. Ya ji dadin wannan lamarin sosai. "Nagode." Hakan ya furta kawai sannan suka miƙe kusan lokaci guda, sai da ya ga shigewarta sannan shima ya juya yana murmushin da har haƙoransa suka bayyana, ga duk wanda ya ga fuskarsa ya san yana cikin farin ciki da annashuwa. *** Washegari Mami ta tashi da aikin girki na tarbar Futuha wacce ta yi waya ta sanarmata dawowarsu a ranar. Daga Dubai sai da suka je Saudia suka yi Umarah kafin su juyo. Humaira ba ta yi ƙasa a gwuiwa ba wajen shiga kicin ɗin din taimaka mata da aiki, zaman kaɗaicin babu abin da yake jefa ta ciki sai kogin tunani. Ummita ma ta fito falo kasancewar akwai wuta ta kunna tashar Saudia tana kallo. Gaba ɗaya samarin gidan sun dawo, Mubarak da ya kammala shima yana gida hakanan Yassar da Dawud wadanda sun fi sati da dawowa daga Camp suna nan tare da su. Anan Kano aka yi posting ɗinsu inda zasu yi service. Daga Humairar har Ummita ba su ƙara samun matsala da su Yassar ba, musamman Humaira wacce a baya suke ƙi sosai, ita hakan ma har mamaki yake ba ta. Tsakaninsu gaisuwar mutunci, wasu lokutan har su ɗan tsoma ta a ciki idan suna ƴar hira. Har a lokacin ba ta saki jikinta da su ba don ba ta saba da hakan ba. Suna girkin Ladidi na taya ta murnar yanda ta soma sakin jikinta tamkar a baya. Raihana ta shigo kicin din kamar an jefo ta har Mami na mata faɗa. "Ku yi hakuri. Humaira, Yaya Fadeel ya kira Sister dinsa Hannatu tana hanyar zuwa." Gaba ɗaya ta manta da wani batun zuwansu, Mami kuwa haɗe rai ta yi ba ta ce uffan ba har sai da Raihana ta ƙara magana. "Ki je ki ɗan sauya kaya don Allah. Kar ta ganki da Tshirt." Ladidi ta yi dariya Humaira kuwa ta maka mata harara ta rasa dalilin kuma da aka yi ta ɗan dawo da jin haushi-haushin Fadeel, sai lokacin kuma Mami ta yi magana. "Toh uwarta, ke kuma Humaira meyasa ba ki faɗamin kina da baƙuwa yau ba?" Cikin sanyin murya da kuma rashin jin dadin ɓatawa Mamin rai da ta yi ta ce. "Kiyi hakuri Mami, gaba daya na manta ma ya faɗamin." Mami ta sauke ajiyar zuciya, ta sauya yanayinta na farko sannan a sanyaye ta ce. "Ai shikenan, ba don girkin da ake na Futuha ba da sai dai ta zo ba a yi nata tanadin komai ba kenan. Ladidi ƙaro shinkafar nan kafin ki wanke." Ladidi dake shirin wanke ɗanyar shinkafa ta zuba a ruwa ta amsa da toh, sai da ta ƙara ruwan tukunyar sannan ta ƙara awon shinkafar da ajiye. Raihana dai ta tsaya jiran Humaira ta dage lallai sai ta sauya shigar jikinta. Mami ba ta sa musu baki ko kadan ba, Humaira har haushin Raihanar ta dinga ji saboda irin wannan nacin ba ta ko fuskantar yanayin fuskar Mamin. "Ki rabu da ni don Allah." Faɗin Humaira cikin haɗe gira. Sai lokacin Mami ta sa baki ta hanyar bin Humaira da murmushi. "Aa Humaira, da gaskiyarta. Maza je ki sauya suturar jikinki. Bai kyautu baƙuwarki ta ganki a hakan ba. Jeki." Ganin yanayin Mamin har a sannan ba ta gamsu ba, amma ta bi umarninta suka fice da Raihana zuwa nasu ɗakin. Ta iske Raihanar ta fiddo mata wata atamfarta purple mai ratsin fara da baƙi, ta kalle ta. Raihana ta murmusa. "Ya aka yi? Da magana ne? Ko na sauyamaki kayan?" Guntun tsaki Humaira ta ja. "Ke dai yadda kika damu da wannan Fadeel din da ma ke kika aure shi." Raihana ta ji ba dadi jikinta kuma ya yi sanyi, tana tunanin Humaira ta fara sauyawa daga lamarin nata da na Fadeel sai ta ga abin ba haka ba. "Allah ya huci zuciyarki tawan." Ta fadi tana riƙo hannun Humaira, sai itama ta ji ba dadi. "Shikenan. Bari na watsa ruwa na sauya ko don ke." Sosai Raihana ta ji dadin kalamanta. Ta yi dariya. "Toh." Daga haka ta fice ta bar Humairar da shiga bandaki. *** Murja tana zaune gaban motar ta hakimce yayinda Hannatu da yarinyarta mai shekaru uku da ta ci suna Husna suke a baya zaune. Tun da Murjar ta ji inda Hannatun ta nufa ta kafe akan sai ta bi ta, a farko Hannatu ba ta so ba don tana da labarin irin son da Murjar ke yiwa Fadeel daga bakin Kausar. Shi Fadeel dayake bai ɗauki maganar da muhimmanci ba ya sa bai ce mata komai a kai ba. A karshe dai ganin yadda Anti Amarya ta nuna ta yi na'am Murja ta raka su ya sa itama ɓoye nata rashin yardar suka tafi tare ba da sanin Fadeel ba. Karfe biyar na yamma suka shiga gidan. Raihana ta tare su da fara'arta zuwa ciki. Murja sai raba idanu ta ke ta ga inda Humaira za ta ɓullo kuma ta ga yanda ta sauya. Ummita itama ta fito suka gaisa da su, nan suka jajanta musu da addu'ar Allah ya kiyaye gaba. Ba ta amsa ba sai ta mike sakamakon idanunta da suka cicciko da kwalla ta nufi daki. A duniyarta yanzu babu abin da ta tsani ta tuna kamar abin da ta faru gareta a hannun Kidnappers. Gani take duk ranar da aka ɗaura mata aure da Sahabi babu abin da zai hana shi gano komai, Abba ya yi niyyar sanar da shi amma Mami ta nuna kar ya yi hakan. Ita kuma a karan kanta ta rasa ta ina za ta fara gayamishi. Ga wata sabuwar kauna da yake nunamata tun bayan fitowarsu duk domin ya kwantar mata da hankali. Ganin da ta yi Humaira na ɗakin, ta yi saurin share fuskarta ta dubeta fuskar a ɗan sake duk da ba kamar can baya da take Ummitarta ba. "Sun ƙaraso su na falo. Ki je ku gaisa, mace mai kirki da ita." Taɓe baki Humaira ta yi. "Toh." Shi ne abin da ta iya cewa, daga haka ta sa kai ta fice. Bayan fitarta Ummita ta tura kai a filo ta yi kuka mai isarta tana mai tausayawa kanta. Wannan baƙin ciki na keta alfarmarta da aka yi ta kasa gogeshi daga kirjinta, ta dai san an gogamata baƙin fentin da har abada ba za ta iya gogewa ba. Amsar da ta kasa ba wa kanta har yau shi ne, wane ne wanda ya sa a yi kidnapping dinsu. *_Ba don kar asirinmu da na Boss ɗinmu ya tonu ba, da sai na nemi aurenki na killaceki saboda kin haɗu ƙarshe._* Ta tuna wannan ƙazamin zancen da ya fito daga bakin Wizzy a sadda yake kam ganiyar raba ta da mutuncinta. Kenan dai akwai wanda ya sanya su wannan aika-aikar. Waye shi? Kuma a ina yake? Allah ne kaɗai masani. A karshe dai ta yakice wannan tunanin ta mike ta shiga bandaki. *** Hannatu ta dubi Humaira har ta ƙaraso ta zauna tana mata ɗan murmushi. Murja kuwa kallon Humaira kawai take yi cikin tafarfasar zuciya tana mai kuma cin alwashin ganin bayanta. Babu wani abu da ya sauya daga kyawunta wannan ne ya ƙara wa Murja baƙinciki a ƙasan rai. Ta kauda fuska tana amsa gaisuwar da Humaira ke yi mata a yatsine. Ita kuwa Humaira mamaki take na dama Murjar ta san Fadeel amma sai ta bar wa cikinta ba ta tambaya ba. Hannatu ta saki jikinta ta yi ta jan Humaira da hira, kasancewar da Raihana a falon ta samu ƴar tayi, tun dai Humaira ba ta saki jiki ba har sai gatanan ta soma murmusawa haƙoranta na bayyana. Raihana ta kawomusu abin motsa baki da kuma abinci. Husna ta maƙalewa Humaira tana mata hira iri iri na yara. Itama ta dinga biyemata. Can dai Murja ta kasa jurewa ko Mami ba ta tsaya sun gaisa ba ta amsa wayar ƙarya sannan ta dubi Hannatu. "Ni zan wuce sai kun taho. Ƙawata ce ta zo." Suka dube ta har Raihana da ta fahimci sauyin fuskar Murjar da irin harare-hararen da take wurgawa Humaira jifa-jifa. "Shikenan, sai mun taho." Ranta ya ƙara ɓaci, wato dama so take ta tafi ɗin don haka ta dauki jakarta ko sallama ba ta tsaya yi da su ba ta fice a fusace. Ba jimawa kuwa da fitarta Mami ta fito cikin shirin fita. Daga ganin yanayinta sauri take kuma fuskarta ya nuna rashin nutsuwa. Hannatu ta gaida ta, ta amsa da ɗan sauri. Ganin haka Raihana da Humaira suka tarbi Mamin da neman ba'asi. Guntun tsaki ta ja fuskarta dauke da tsantsar damuwa. "Wajen Tasleem zan je, sun yi dambe da wannan Fauziyar shi ne fa jini ya ɓalle mata amma sun wuce asibiti." Hankalinsu su din ma ya tashi. Suka nuna za su bi ta amma fir ta ce aa su zauna da baƙuwarsu sannan ga Futuha dake hanyar zuwa kada a bar gidan babu ƴan tarbarta. Dole suka jajanta suka dawo ga Hannatu aka cigaba da hira. Ba ita ta bar gidan ba sai bayan Magriba. Ta kuwa ajiyewa Humaira leda babba ta kayan kwalam sai ko turarukan da ta yo mata tsarabarsu. Firr Humaira ta ƙi karɓa sai daƙyar sannan ta yi godiya. Lokacin itama Ummita ta fito falon, tare suka yi mata rakiya har gaban motar da suka zo cikinta. *** Karfe takwas da mintoci sai ga Futuha a gidan, tun yamma ta sauka a garin tana gidanta, Ƙasim ne ya kai musu girke-girken da aka yi musu. Ta shigo gidan gaba ɗaya jikinta a mugun sanyaye. Matasan samarin duka suna falo aka tarbe ta da murna, su Humaira su din ma duka ana zaune ana kallon film din Krissh da ake haskawa a mbcbollywood. Ganin yanayin yadda take amsa musu hirar ya sanya Yassar dibanta dakyau. "Are you okay?" Ta yi murmushin yaƙe kai ka ce ba Futuhar nan ba ce mai ɗora hotuna iri-iri da murnar zuwa Dubai a tiktok. "Yes. Mamin ba ta dawo ba?" "Ta dawo tana ɗaki." Faɗin Raihana. Ta kuwa nufi ɗakin, ban da gaisuwar su Humaira babu wani jimamin da ta yi musu na abin da ya faru. Ƙamshin turarenta da ya cika falon ne ya sanya Ummita jin kanta na juyawa, ta ji tamkar hanjin cikinta ke kaɗawa. Da sauri ta mike ta yi dakinsu, kafin ta ƙarasa shigewa banɗakin wani amai ya tahomata wanda sai da ta amayar da duk abincin da ta ci a ranar. Humaira da Raihana wadanda suka biyo bayanta ganin irin miƙewar da ta yi ta bar falon suka tsaya cak cike da fargaba mai tsanani su ke bin ta da kallo.   *LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* 09034973645 Raihana ta karasa cikin sauri bayan fitowar Ummita daga banɗakin ta riƙe ta.    "Lafiya? Meke damunki?" Ummita ta yamutsa fuska kaɗan. "Ban sani ba, kawai dai na ji zuciyata tana tashi." "Allah ya sauwaƙe, ki ɗan kwanta ko za ki ji dadin jikin." Fadin Humaira cikin dauriya da ƙaryata zuciyarta har da jan istigfari bisa saƙe-saƙen da ta jefa mata. Ummita kuwa ɗan murmushi ta yi. "Kar ku damu, kalau nake. Naga duk kun yi wani sukuku da ku." Cikin kokarin basarwa Raihana ta zauna gami da jan guntun tsaki. "Ai dole, ga Tasleem can kwance asibiti dakyar aka tsaida jinin. Wai kawai saboda ta kama Fauziyya na waya da tsohuwar budurwar Yaya Hamza kuma ƴar uwarta tana ba ta labarin rayuwar ita Tasleem din da Yaya Hamza shikenan fa daga cacar baki sai cibi ya zama ƙari. Nima Mami naji tana ba Anna labari. Yanzu dai Maman Hamza ta ƙi zuwa ko duba Tasleem ta ce wai kashe mata ɗiya ta so yi." Humaira ba ta ce uffan ba, domin tun dawowarsu ta ƙara jin Tasleem ta fice a ranta, ta kuma ƙudurta ban da dai gaisuwa ta musulunci to fa babu abin da zai sa ta cigaba da tura kai ba kwarjini wurin waɗanda ba za su taɓa kaunarsu ba. Ko kaɗan Tasleem ba ta wani nuna farin cikin dawowarsu ba, ita kuwa me zai sa ta cigaba da shiga sabgar wacce ba ta yin ta? "Allah Sarki, Allah ya kawomata da sauki." Cewar Ummita sannan itama ta ja bakinta ta yi shiru. *** Yanayin da Futuha ta shigar wa Mami ne ya sanya ta ɗago kai daga wayar da take amsawa har da hawayenta. Cikin wani sauri ta sallame wayar ta miƙe, Futuha ba ta kawo komai ba ta ƙarasa da sauri ta rungumeta ta fashe da wani irin kuka mai tsuma zuciya. Mami wacce ta ji kirjinta ya yi wani irin bugu da ƙarfi ta ɗago kai da azama ta kalle ta har hannuwanta a rawa. "Ke mene ne ya faru ne? Ina Yakubun?" Gaba ɗaya ta ruɗar da cikin Mami wanda ta ji har wata ƴar ƙara ma yake yi. "Mami ƙarya yake yimin, ashe matarsa tana gidansa cikin wata irin ƙasƙantacciyar rayuwa?" "Toh ina ruwanki da ita! Ke ba kanki kika sani ba?!" Yadda Mamin ta yi furucin a zafafe ya sa Futuha shiru tana kallonta da ɗan mamaki saman fuskarta, kamar dai ba Mamin da ta saba karo da ita ba. Sai kuma ta tuno labarin ƴanmatancin Mamin da Anna ta ba su, mace ce da a tarihin soyayyarta ba ta taɓa kallon mai mata balle ta ji zuciyarta za ta iya ɗaukar zaman kishi da ita ba, har tana jinjina mamakin zaman da ta amince suka yi da Fatima ta kuma ƙaunace ta. A baya dai Mami ba ta san kowa da komai ba sai kanta da kuma nata. Wannan tunanin da Futuha ta yi ne na tsohon tarihin Mamin ya sanya ta sauke ajiyar zuciya lokaci guda kuma mamakinta na farko ya gogu tas daga kwanyarta. "Nifa ba wannan ƙaryar ce ta tada hankalina ba, tun kafin mu dawo likita ya bayyanamin ina da ciki bayan ƴar rashin lafiya. Na bar abin na ɓoye ban sanar mishi ba akan zan ba shi labari mai dadi, sai yau da muka dawo ne nake sanar da shi toh kawai sai ya sauya fuska. Ya kuma rantsemin shi bai aure ni don na haifarmasa, daga uwargidansa kawai yake da kwaɗayin samun yara. To fa shi ne da faɗa ya kaure tsakaninmu, ya ce na zubar ni kuma na ce ba zan zubar ba tunda ba shege ba ne, kawai Mami sai ya ja hannuna ya kai ni ɓangaren Uwargidansa. Nayi mamakin ganin ashe yaransa takwas har da budurwar da za ta yi sa'ar Raihana. Komai nata ya ci uwarsa a falon. Goyon ɗa take yi ma, a gabanta da na yaran ya nunamin yaranta sun ishe shi ba ya kaunar haihuwa daga kowace mace. Ya kuma aure ni don ya ci duniyarsa ganin da ya yi ni ƴar rawa ce wai a Tiktok na kuma san ta kan rayuwa sai ya ɗauka zan san dabarun family planning kafin aure." Kawai sai ta fashe da kuka. Mami zuciyarta har wani tafarfasa yake yi. Ta ji kukan Futuhar tamkar yana ƙara tafarfasa ƙwaƙwalwarta don haka ta dakamata tsawa. "Ya isa! Nace maki ya ishe ni haka! Haba! Da wanne ku ke son na ji? Da mummunan albishir din da Babandi ya faɗamin ko kuwa da hargitsinku?! Ke ba za ki iya cin uban shege ba?! Ba za ki iya yadda za ki yi ki ga kin fitar da yar iska daga gidanki ba?! Shashasha kai marar wayo!" Tana kaiwa nan ta nemi bakin gado ta zauna kirjinta na dukan tara-tara tana maida numfashin gajiya. Futuha kuwa ai sai ta ƙara yin mutuwar tsaye don mamaki. Toh Mamin nan dai ta tabbata ita ce ainahin Mamin can baya lokutan yanmatancinta, ita ce Mamin da Anna ta yi mugun kewarta. Faɗa, zagi kuma duk akan kishi? Yau Mami dai da bakinta ta mata iznin daukar kowane mugun mataki ne akan kishiyarta da mijinta. Futuha ta juya cikin sassarfa tana kukan har lokacin ta fice zuwa ɗakin Anna. Mamin kuwa sai bayan da kwanyarta ta ɗan samu nutsuwa, tashin hankalin dake ƙasan ranta ya ɗan lafa sai ta soma tunano irin maganganun da ta faɗawa Futuha. Ta lumshe idanu ta ja guntun tsaki. Ta san yarinyar dole mamaki ya kashe ta, amma ita ta san azabtuwar da take yi ko kuma ta yi a shekarun baya da suka gushe. Ta tsani kishiya tsana mafi munin gaske. 'Ciki har da Fatima?' Wani ɓangare na zuciyarta ta watso mata wannan tuni. A fili ta ɗaure fuska tamau, idanunta nan da nan suka kaɗa tsabar masifa da kuma abin da ta tuna na daga rayuwar Fatima da Yusuf a baya. "Har da Fatima." Ta furta a zahiri, can kuma ta miƙe ta shiga banɗaki ta wanke fuskarta. Sai bayan ta dawo daidai ne sannan ta fito zuwa ɓangaren Abba. Ta iske shi zaune yana kallon labarai, itama wuri ta nema ta zauna da wani irin sanyin jiki. Abba ya maido hankali gareta. "Maryama, na ganki wani iri, Futuhar ba su dawo ba ne?" Mami ta girgiza kai. "Sun dawo, tana wajen Anna ma suna gaisawa." "To ko jikin Tasleem din ne? Ni me ma ya faru ne da ita ta yi rauni?" Ko kusa ba ta sanar da Abban gaskiyar abin da ya yi sanadin kwanciyar Tasleem din a asibiti ba. Ta sani muddin ya ji to faɗa zai yi wannan ya sa ta gyara batun. "Zamewa ta yi ta faɗi a banɗaki. Amma ai da sauki tunda jinin ya tsaya." Jinjina kai Abban ya yi. "Allah ya raba su lafiya. Sai ta ƙara kula." Ta yi shiru tana kallon gefe guda ta kasa amsa mishi, ya riƙo hannunta cike da kulawa murya a tausashe ya ce. "Faɗamin, meke damunki?" Ƙasa ta yi da idanunta sai hawaye, suka zubo saman hannun Abba da ya ɗora bisa nata. Nan da nan ya ƙara shiga tashin hankali. "Kinsan bana son kuka ko? Taimaka ki faɗamin damuwarki Maryam. Zuciyata ba za ta ɗauki wani sabon tashin hankalin ba bayan wanda na fuskanta kwanakin nan." Ta jinjina kai ta dube shi. "Abban yara tunanin yarannan ya kasa barin zuciyata ta huta. Tun dawowarsu zan iya ce maka Ummita har yau ta ƙi dawowa cikin nutsuwarta. Yarinya mai fara'a da son jama'a marar hayaniya, ta koma wata iriya. Babu doguwar magana balle hira, koyaushe zaman tunani da shiru. Wannan abu yana damuna matuƙa." Shima Abban hakan da ta faɗi sai ya ƙara taso mishi da nasa damuwar. "Hakane Maryama. Toh a shawarce me kike tunanin za'a yi? Mece ce mafita?" Mami ta numfasa. "Mafita a samar mata abin da zai dawo da walwalarta. Abin nufi, madadin lokacin da aka sa na aurenta da Sahabi, me zai hana a yi mishi magana idan sun shirya kawai ya kawo lefe a sanya bikin nan da kamar sati biyu?" Ɗan jim Abba ya yi cikin hali na tunani. Sai kuma ya ce. "Kina tunanin idan an yi hakan ba a tauye ta ba kuma. Bana jin yarinyar nan ta samu nutsuwar da za ta karɓi aure a yanzu. Kada ki manta fa, keta haddinta aka yi ta ƙarfi. Aa Maryama, mu dai yi hakuri tun da abinda ya rage cikin shekarar bai wuce watanni biyar ba, ki jira mu ga abin da Allah zai yi a gaba." Ba haka ta so ba sam, ba kuma ta taɓa tunanin Abban zai watsamata ƙasa a ido ba. Kai ta mance rabon ma da ta bada shawara irin haka dangane da abin da ya shafi yaran ya musanta. Ganin sauyin dake saman fuskarta ne ya sa Abban ƙara riƙo hannunta ya ɗan matsa. "Kiyi hakuri Maryama, ba fa watsa maki ƙasa a idanu nayi akan al'amarin yaranki ba. Aa, ki dai daure na sani da zafi ka dinga ganin ɗanka cikin yanayi mai firgitarwa. Amma a shawarce, me zai hana ta je Bichi ko sati biyu ta yi kinga za ta samu nutsuwa da kwanciyar hankali." Daure fuska Mami ta yi. "Shikenan, ɗauke ta a yau ka kai ta sai Maijidda ta zuba ruwa a ƙasa ta sha tunda ta ga gazawata a kula da Ummita. Nagode." Tana kaiwa nan ta zame hannunta cikin na Abban ta soma kokarin miƙewa tsaye. Ya yi saurin dakatar da ita. "Haba Maryama, to kiyi hakuri naji na yi laifi a kalamaina. Ba zan kai Ummita ba face da izninki. Kiyi hakuri, shikenan? Yanzu me kike tunanin za'a yi don sama mata nutsuwa?" Ta sauke ajiyar zuciya. "Tunda har shawarar da na bayar bai yi ba, toh na fi tunanin ka bayar da kudi muje da su ukun nayi musu ƴar siyayya sai kuma ita Humaira da ka riga ka san matsalarta akan maza. Ganin wannan abu da ya afku ga Ummitan ya ƙara sanyawa ta tsani al'amarinsu. Daidai da Fadeel din da muke murnar ta soma sakin jiki da shi suna ƴar hira yanzun ko muryarsa ba ta wani son ji. Tun wuri gwara a yi mata maganinsa. Na kuma fadamaka labarin wani mai magani, idan har ka amince sai na kai ta a karɓo a gani ko za'a dace." Abba ya kurawa Mami idanu, a duniya bai taɓa ganin matar da ba ta damu da nata ba sai na wasu. Ba ruwanta da damuwar yaranta sai abin ya ci tura. Matar da ɗiyarta ke kwance a gadon asibiti amma ba ta ko zancenta, burinta ta samar da farin ciki ga yaran wasu. Kaunarta ya ƙara mamaye zuciyarsa, ya riƙo hannuwanta ya sumbata sannan ya sakarmata murmushinsa da ya san yana daga cikin abin da yake ƙara dulmiyar da ita cikin kogin sonsa. Ita kuwa sai ta ɗan kauda kai tana murmushi. "Ina kaunarki Maryam, Allah ya yi maki albarka ya bar mu tare. Kin cikemin gurbin mace hudu a duniya. Babu abin da zan ce maki sai fatan alheri. Yanda kika ce haka za'a yi, gobe ki shirya zan baku kudi, ku fara da siyayyar, koda zuwa jibi ne kuma sai ki kai ɗiyartaki wurin mai maganin. Ina fatan hakan ya yi maki?" Har lokacin tana murmushi ta gyaɗa mishi kai. "Ya yi ranka ya daɗe. Fatanmu Allah ya maidowa yaranmu farin cikinsu." Cikin jin dadi Abba ya amsa da amin amin. *** Washegari kuwa hakan aka yi, tamkar ba Mamin da Tasleem ɗiyarta ke kwance gadon asibiti ba, tamkar kuma ba wacce ɗiyarta mace ta farko ba (Futuha) ta kawo mata ƙorafin tashin hankalin da take ciki. Daga fuskarta za ka fahimci kamar a duniya ba ta da wata aba wai ita matsala ko kuma damuwa. Ta saki ranta suka zagaye shoprite da su Humaira da Raihana. Ummita sosai kuwa ta sake ɗin kamar yanda Mamin take buƙata, su kansu sun ji dadin yadda yanayinta ya sauya. A ɓangaren Ummitan kuwa, ta tabbatar domin ta saki jiki ne aka yi duk wannan shiri hakan ya sa ba ta watsawa Mamin ƙasa a ido ba, ta daure ta yakice damuwarta ta saki jiki. A ɓangare guda shima Sahabi na nashi iyakar kokarin ganin ya faranta ran abar kaunartasa. Wannan ma ya yi tasiri kwarai a zuciyarta amma har lokacin wannan baƙar ranar ta ƙi ɓacewa a tunaninta da mafarkanta. Su ne har gidan Hajiya Lubna, sun ɗan jima tare da yaranta a ƙasa inda Mami ta haye saman kafin daga bisani ta sauko su wuce. "Mami ba zamu leƙa Anti Tasleem ba?" Cewar Raihana. Mamin ta yi shiru. Ganin haka sai Ummita ta sa baki. "Mami don Allah muje a duba ta." Humaira kuwa uffan ba ta ce ba, asalima kallon shuke-shuken dake farfajiyar gidan Hajiya Lubna kawai take. "Shikenan, muje. Yarinyar ce ta ban takaici, kina da ciki don sakarci ki tsaya wani faɗa akan kishin banza da wofi." Su dai babu abin da suka ce. Humaira ta buɗe bayan mota ƙarama ƙirar KIA da Abba ya tsiya ta shiga. Mami ta ɗan bita da kallo sai kuma ta murmusa ba ta ce uffan ba. Ta dubi Hajiya Lubna. "Shikenan Hajjaju, sai mun yi waya." Ƴar dariya Hajiya Lubna ta yi. "Toh Hajiya Mamin yara. A gaida Tasleem din ki ce mata ta sha kuruminta zan zo." "Ai shikenan. Za ta ji." Daga haka suka yi sallama. *** Malamin ya yi shiru yana duban ƙasa, can kuma ya ɗago ya kalli Murja ya girgiza kai. "Abin da kike so ba zai taɓa kasancewa ba." Wani malolon baƙin ciki ya turnuƙe zuciyarta. Daƙyar ta haɗiyi miyau mai ɗaci ta ce. "A yanzu kake nufi ko har a gaba? Kenan Humaira ba za ta kasu ba?" Malamin ya yi ƴar dariya. "Wane mutum! Inji mutuwar. Ai Hajiya Murja babu wanda ba zai mutu ba. Kuma ni da na isa na duba mutuwar wani ai da nawa zan fara dubawa. Abin nufi kina son ta mutu kada ta auri Fadeel din ko? Toh hakan ba zai taɓa yiwuwa ba." Ji tayi wani abu mai nauyi ya tsaya a ƙahon zuciyarta. Malamin ya zubamata idanu, ya lura ba ta saduda ba don haka ya sauya zancen. "Amma fa idan kina so za'a iya nakasata rayuwarta. Zamu iya nakasta ta gaba ɗayanta. Amma da sharaɗi, matukar aikin bai ci ba, zai dawo kanki. Kin amince?" Ba tare da dogon tunani ba ta amsa. "Eh na amince." "Murja, ko za ki yi shawara?" Ranta ya ɓaci sosai. "Wancan karon haka ka ce min, wannan karon ma kana nema ka tauye ni da faɗin haka ko? Toh yanzu ba shawarar da zan yi, ga kudi nan ka yi duk abin da ya kamata." Ta bude jaka ta ciro bandir na dubu ta dire mishi. Ya yi murmushi. "Shikenan, ni nawa aiki. Sauran ke za ki yi da kanki. Dole kina bukatar zuwa inda ita yarinyar take. Ki je ki dawo nan da kwanaki uku." Murja ta ji kwanakin tamkar watanni a wurinta. Tana jin zuciyarta za ta iya bugawa na yanda Fadeel ke rawar ƙafa akan Humaira, kullum ya zauna da Hannatu a falon Anti to fa hirarta ne kawai. "Babu wani aiki da za ka yimin akan Fadeel?" "Aiki kai, ga wannan layar ki tabbatar kin saka a ƙarƙashin katifarsa, muddin ya kwana ya tashi ki ɗauke ki binne. Wannan kwallin kuma ki zizira ki tabbatar kun yi ido hudu." Ta yi murmushi, duk da cewa ta yi abubuwa da dama ba ta yi nasara a kan Fadeel ba amma hakan ba zai sa ta karaya ba. Ta karɓa ta sa a jaka ta mishi sallama ta tafi zuciyarta sol. *LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* 09034973645 Misalin bakwai da mintoci ne, Fadeel ne zaune a falon Alhaji tare da Hannatu da Alhajin. Wannan damar Murja ta yi amfani da shi wajen kokarin ganin ta ƙaddamar da shirinta, sai da ta fakaici idanun su Khadija da Abdulmaleek wadanda suke kallo ta nufi ɓangaren Fadeel. Sai dai ta yi mugun mamakin jinsa a garƙame da muƙulli. Ta ciji leɓɓa don takaici kamar ta haɗiyi zuciya ta mutu haka ta ke ji, sai kuma ta tuno duk abinsa da safe yana barin mukullin ɗakin ya fice don a yi mishi gyara. Wannan ya sa ta yi murmushin mugunta ta juya tana mai kara cin alwashi. *** Futuha na zaune tana faman cika da batsewa kamar ta fashe, Alhaji Yakubu ya shigo fuskarnan a murtuke ya zauna yana dubanta gami da jefamata ledar dake hannunsa. "Idan har kina son mu cigaba da rayuwar farin ciki da ke, to ki gaggauta shan magungunan nan, an tabbatarmin zasu yi sanadin zubewar cikin dake jikinki. Idan kuwa har ki ka ƙi, kika dage sai kin haihu da ni, toh shakka babu baƙar rayuwar da za ki fuskanta sai kin sha mamakinsa. Sannan rashin bin umarnina zai yi sanadin da zan yi aure." "Wallahi ba zan sha ba! Idan kuma aure ne ka yi idan ka isa! Kuma wallahi ka ji na rantse maka matukar ka ce za ka wulakantani ba zan zauna ba sai dai ka sakeni!" Ya yi wata muguwar kyakyacewa da dariya. Ya nunata da yatsa. "Ke Futuha, ba ki da hankali ashe? An fadamaki ni Yakubu zan saki mace? Ai babu wannan ranar a duniyata. Zaman aure da ni ya zamar maki dole. Koda bakya so kuwa sai kin zauna da ni. Na dai fadamaki, muddin rayuwarnan mai dadi da na ɗanɗana maki kina so ya ɗore, to sai kin bi umarnina. Idan kuwa kin ƙi zan auro..." Sai kuma ya yi shiru yana jinjina kai duk a kokarinsa na shanye sirrin dake ransa. Tun su na Dubai ya yi wani irin sabo da ɗinkewa da Sa'a Ƴar Snow, kullum yana shafinta yana jifanta da likes da kuma chatting da suke yi a ɓoye. Tsantsar kalaman iskanci da ma hotunan tsiraicin da take turomasa ya yi mugun hargitsa shi, ba ya fatan ya kusanci zina amma ya sha alwashin aurenta. Ta kuma amince sannan ta ba shi lokaci ya gama cin angoncinsa kamar yanda ta buƙata. Ya fi kowa sanin ƴar tsamar dake tsakaninta da Futuha, ya tabbatar idan zancen ya fasu to fa ba za su kwashe da dadi ba hakan ya sanya shi zaɓar yin shiru. "Ka auro wa?! Ka faɗamata ko ma wacece don ubanta ta yi kaɗan ta shigo gidannan!" Ya mike ya watsamata harara. "Saboda ke kika haife ni kenan? Titse ni za ki yi na faɗamaki ko? Toh sai ki yi da wani." Yana kaiwa nan ya kama hanyar fita, aikuwa ta yi tsalle ta dire gabansa idanunta har sun kaɗa tsabar kishi da ɓacin rai, cakumar wuyan rigarsa ta yi tun ma ba ta kai ga furta ƙala ba ya cire hannu sai ji kake tas a saman fuskarta. "Ke! Ashe iskancin naki ya kai haka? Ni kike cakumarwa wuya?! Wannan ya zama na ƙarshe idan kika ƙara mugun gangancin nan sai na nunamaki ba ki da wayo! Banza marar tarbiyya ƴar rawar Tiktok kawai! Mtsw." Yana kai wa nan ya fice yana gyara zaman babbar rigarsa, dama dawowarsa kenan daga wurin Ƴar Snow, don dai kalamai da rungume rungume wadannan ya sha su kamar ba gobe, ita ta yi mishi rakiyar siyan magani kafin ya maida ta gida da siyayya mai yawa sannan ya dawo gidan. Futuha ta yi kuka mai isarta tamkar ranta zai fita sai dai ta ƙudurta a zuciyarta Alhaji Yakubu bai isa ya wulakanta ta ba. Sai ta ɗauki mummunan mataki a kansa kamar yanda Mami ta ba ta shawarar ta kwaci kanta da gidanta, to kuwa za ta ƙwata ta ƙarfin tsiya. Gama tunaninta kawai ta ciri waya ta kira wata tsohuwar aminiyarta Aneesa Jafar. Matar aure ce amma tantiriyar ƴar duniya ce domin ko a rayuwarsu ta makaranta tana cikin masu neman soyayyar Sir Ibb duk kuwa da auren dake kanta. Ita din shaida ce a yanda take juya mijinta a gida hakan yasa ta yanke shawarar tuntuɓarta. Tun sadda ta yi aure ba ta ƙara nemanta ba saboda a ganinta ajinta ya fi nata, sai a yanzun da buƙatarta ta taso. Kasancewae Aneesa ta iya barikanci, ko kusa ba ta nunamata komai ba suka gaisa hannu bibbiyu. Sai kuma Futuha ta warware mata damuwarta. Dariya Aneesa ta yi kafin ta amsa. "Ai wannan ba matsala ba ce yar uwa, amma ki yi yanda yace. Ke banda abinki mene ciki don kin zubar da cikin wanda ya nuna ba ya son haɗa zuri'ar da ke? Kuma wallahi kika yarda kika haihu da shi to ina mai tabbatar maki nan da nan za ki lalace ki zama wata daban. Ki daurewa ranki ki zubar da cikin idan ya so ki kawo kudi mu san hanyar da zamu bi ki mallake shi, yanda ko tsinke bai isa ya tsallake ba matukar ba ki yi mishi izini ba." Cikin sanyin jiki da kuma ɗan nutsuwar da Futuha ta samu ta ce. "Toh Aneesa. Ni dama tsoron mutuwa nake, kada na sha na mutu naji ance masu zubar da ciki mutuwa suke yi." "Mutuwa ai sai lokaci ya yi, nidai ina ba ki shawarar ki zubar kuma ki je ki yi planning abinki hankali kwance. Matukar dai kina so mu cimma burinmu." Ta sauke ajiyar zuciya ta jawo ledar magungunan sannan ta ba Aneesa amsa. "Shikenan, yanzun nan zan sha. Nagode Aneesa, zuwa gobe duk yanda ake ciki zan kiraki mu ji abinda ya dace a yi." "Shikenan, sai na ji ki." Daga nan suka yi sallama. Ta ƙurawa magungunan idanu, a wata farar takarda suke, ta yi shiru can kuma kamar wacce aka tsikara ta mike ta dauko gorar ruwa ta bude, ta zazzaga magungunan a hannunta ta shanye su tas sai jiran sakamako. *** Tana kwance tana juyi yayinda yan uwanta duka ke bacci abinsu. Ta mike zaune ta yi shiru, tashin zuciya take ji sai dai ta rasa yanda za ta yi ba ta kaunar ta yi amai motsin yunƙurin ya tashe su. Zuwa lokacin ta soma shan jinin jikinta, tsoro da firgici ya soma shigarta. Bai fi kwanaki uku watan da suke ciki ya mutu ba amma har yau babu labarin ganin al'adarta. Tsoro iyaka Ummita na cikinsa. Ta kasa jurewa tashin zuciyar da take ji sai ta bude dakin ta fita da sauri zuwa falon bandaki, nan fa ta shiga kelaye amai kamar hanjin cikinta za su zubo. Duk wani kayan kwalam da ta ci a ranar sai da ta dawo da shi. Ta kammala ta wanke fuska ta gyara wurin, ta kuma ɗauro alwala ta dawo falon ta zauna. Sai kawai ta fashe da kuka mai tsuma zuciya ga wani irin mugun sanyi da ya lulluɓe ta lokaci ɗaya. Ba ta son koda tuna kalmar da take tunanin shi ya zama damuwarta balle har ta furta. 'Idan ya tabbata haka din ne ya za ki yi da Sahabi?' Zuciyarta ta watso mata tambayar, ta rike kai sai kawai ta fashe da kuka sosai. Ba ma Sahabin kawai ba, ta ina za ta soma karɓar wannan ƙaddara na rainon cikin da ta same shi ta hanyar fyaɗe? Fyaɗen ma daga ɗan ta'adda? Tana wannan kukan mai tsuma zuciya ba tare da sanin irin ƙarfin buɗe muryar da ta ke yi ba har sai da ta ga hasken fitila a falon an kunna saboda akwai wuta. Mami ce, kafin Mamin ta ce wani abu sai ga Humaira a gigice ta fito itama. Kusan lokaci guda suka ƙaraso gareta. "Mene ne ya faru Ummita?" Humaira ta tambaya jikinta har yana rawa nan da nan itama ta soma hawaye ba tare da sanin ainahin dalilin kukan yar uwarta ba. Ummita ta rungumeta tana kuka sosai. "Ciki Humaira, Humaira zan haifi shege." Da karfi kuma cikin daga murya Humaira ke girgizata kamar zararriya tana fadin. "Wa ya fadamaki kina da ciki? Karya ne! Karya ne ba ki da ciki!!" Mami ta dago Ummita. "Wa ya fadamaki wannan mummunan labarin? Kin ga wasu alamomi ne?" Mamin ta fadi nata hankalin itama a mugun tashe, nan da nan cikinta ya duri ruwa. Cikin sheshsheka Ummita ta ce. "Ma..ma.mi, amai nake ta yi." Ajiyar zuciya Mamin ta sauke. "Haba Ummita, amai kuma sai aka ce maki yana nuni da cewa kina da ciki kenan? Amai ai alamun cutuka ne da dama, ba lallai sai ciki ba. Lokacin al'adarki ya yi ne?" "Eh Mami, har ya wuce." Gaban Mami ya buga da ƙarfi, Humaira sunan Allah ta shiga ambato sakamakon ji da ta yi tamkar an zare mata wani laka na jiki. A durkushe take amma kuma jiri ne ke kwasarta. Tana ji tamkar a mafarki ake wannan diramar ba a farke ba. "Maryama, meke faruwa ne?" Suka juya gaba daya, Abba ne sanye fa jallabiya a tsaye a ɗan rikice, ya tako ya ƙaraso ganin Ummita na kuka ya sanya shi ƙara jin rashin nutsuwa sosai. "Ummita, meyafaru kike kuka?" Mami ta yi saurin share hawayen da suka zubomata, ta miƙe tsaye. "Babu komai, ba ta jin dadi ne. Humaira ku shiga ciki. Ki kwantar da hankalinki gobe idan Allah ya kaimu zamu yi test a gani." Bayan wucewarsu Abba wanda ya daskare a tsaye cikin wani mugun faduwar gaba ya ce. "Maryama, meye hakan kuma? Na kasa gano bakin zaren wannan tattaunawar da tsakar dare?! Me kike son ki ce?" Gaba daya ma Abban ya diririce ko kadan ba ya cikin nutsuwarsa. Mami ta dafe hannunsa. "Babu komai Abban yara, muje zan maka bayani." Zai ƙara magana ta hana shi ta hanyar roƙonsa akan su tafi dare ne kar a ji sai kuma ya hadiye maganar ba musu ya yi gaba zuwa ɗaki ta bishi a baya bayan ta kashe fitilun falon. Ya ji zancen tamkar saukar aradu, nan da nan ya dafe kansa. "Innalillahi wa inna ilaihir raaji'un! Maryama wannan mummunan labarin da me ya yi kama? Tashi tashi muje asibiti yanzu a dubamin ita." Mami cikin hawaye ta yi saurin dakatar da shi ta hanyar dafe kafarsa gami da girgiza kai. "Aa Abban yara, kar muyi haka. Yin hakan tamkar tonuwar asirinmu ne. Duniya sai ta san halin da muke ciki. Ka kwantar da hankali tunda ana siyar da Pt-strip na awon ciki, gobe da safe mu bayar a siyo a auna fitsarinta don mu ga halin da take ciki. Mu yi fatan alheri da fatan kar zatonmu ya tabbata. Ajiyar zuciya mai karfi Abba ya saki. "Innalillahi...Ya Ilahi! Wannan ranar dame zan kirata ni Isuhu? Inama tun farkon fari ban hana Hajiya Maijidda riƙon Ummita ba tun tana ƙarama, da watakila ba zan ga wannan ranar ba." Wani irin zuciya ya tasowa Mami, ta ji tamkar ta haɗiyi zuciya ta mutu. Ranta ya yi mugun ɓaci, wato duk hakuri da dauriyar shanye damuwa da bakin cikin RIƘON BARE da ta yi, da wannan sakayyar Abban zai bi ta? Ta so ta furzar da abinda ke ranta sai kuma ta daure kamar koyaushe ta shanye rabi da kwatan ɓacin ranta ta ce. "Wane irin rashin tawakkali ne haka Abban yara? Ka isa ka hana Allah ikonsa ne akan al'amarin Ummita? Ummita ko bangon duniya ta je idan hakan ya ƙadartu a kanta sai ya afku. Ban da haka ma, kenan kana kaicon rayuwar da ta yi a hannuna? Kana kaico da irin abin da ya fada mata? Ko a tunaninka a sanadina ne aka sace su har kaddarar fyaɗe ya faɗa kan Ummita?" Ta karasa zancen da wani irin kausasshen murya, ganin ya kalleta da sauri da alama zancen bai mishi dadi ba kuma bai san fassarar da za ta ba shi kenan ba ya sanya ta fashewa da kuka mai tsuma zuciya. "Dama na sani Yusuf, watarana sai ka ga gazawata akan yarannan duk kuwa da..." "Haba Maryama, don Allah don Annabi s.a.w ki yi hakuri. Wallahi zafin bacin rai da damuwa da tashin hankali ne ya sanya ni wannan maganganun marasa kyawun ji. Ko daidai da kiftawar ido ban taɓa kawowa za ki cutar da wani a cikin yaran da kika haifa a cikinki ba ma balle a kai ga Ummita. Yarinyar da kika daukaka ta kika kuma riƙe ta hannu bibbiyu tamkar ke kika haife ta a cikinki. Wane irin butulu ne ni da zan yi maki haka? Ki yafemin domin Allah. Na tuba kiyi min uzurin halin rudani da tashin hankalin da na tsinci kaina ciki." Mami ta mike ta ja guntun tsaki ya yi saurin tarar gabanta. "Haba Maryama, da wanne kike so na ji ne? Da tashin hankalin nan na Ummita ko kuwa da ɓacin ranki? Faɗamin, me kike so nayi ki huce?" Jin haka sai kuma ta yi shiru tana goge fuska. "Kar ka ƙara irin wadannan kalaman naka na rashin tawakkali." Ya yi murmushin karfin hali ya rungumeta. "Idan har wannan ne ba zan kara ba. Na ma yi istigfari tun sadda kika ankarar da ni kurena. Mu ji da damuwa daya yanzu." Ta gyada kai, bandaki ta shiga ta ɗora alwala ta sanya hijabi ta hau saman darduma. Sosai yake jin so da kaunarta a zuciyarsa. Shima sai ya fasa neman wuri ya kwanta kamar yanda ya so duk kuwa da irin sakensa a ibada lokuta da dama. Kusan wannan shi ne kadan daga inda ya kuskuro, rashin tsayawa kai da fata wurin ibada sosai sai idan ya fada matsala babba. *** Washegari tashin hankalin da suka riski kansu ciki sai ya mantar da su wani batun zuwa kai Humaira asibiti. Gidan ya zama tamkar gidan makoki. Suna zaune jigum suna jira Mami da Ummita su fita daga bandaki don sanin matsayar Ummita, akwai cikin ko babu. Abba ya kasa fita kasuwa si safa da marwa yake a falon balle kuma Raihana wacce tun jin abinda ke faruwa ta kasa motsawa ballantana ta wuce makaranta. Sai Humaira da ta dau carbi tana jin tamkar an yi mata mutuwa. Mubarak kuwa wanda shi ya fita ya siyo abin awon cikin, sai ya jingina jikin bangon falon ya yi shiru cikin bugun zuciya. A wannan yanayin Mami ta fito a gigice kuma a guje, gaba daya suka yi kanta har suna rige-rige. "Meke faruwa?" Faɗin Abba yana jin kamar ya kife tsabar jiri. Mami ta fashe da kuka. "Mun shiga uku! Shikenan Abban yara asirinmu zai tonu. Ciki ne da Ummita." Abba ya ja baya da sauri ya zauna saman kujera mafi kusa da inda yake, yayinda Humaira ta yi mutuwar tsaye. Ita kuwa Raihana kwasa ta yi a guje zuwa bandakin don ganin halin da Ummitan ke ciki. Aikuwa ta iske ta a kife tamkar babu numfashi. Ta kuwa ƙwalla ihun kiran sunan Abba. Kusan da rige-rige suka shiga banɗakin. Mubarak ne ya yi ta maza ya cicciɓe ta bayan ya tabbatar da bugun zuciyarta ya fiddo ta falon ya shimfiɗe saman kujera sai dai duk wani kokari na watsa ruwa da ma sauransu anyi amma babu alamun Ummita ta san ana yi. Ana shirin fita asibiti Mami ta dakatar ta ce gwara a kira makwafciyarsu wata likita gudun fashewar zancen a duniya. Abba ya yi na'am, Mubarak ne ya fita da rawar jiki har gidan Dakta Inteesar an ci saa kuwa ta fito cikin shirin tafiya asibiti. Ganin Mubarak aboki ga babban ɗan ta Najeeb ya sanya ta dakatawa. Roƙon da ya hau yi mata ya sa ba ta iya yi mishi musu ba sai ta shiga motarta suka kama hanyar gidan don akwai ƴar tazara kaɗan ita daga bayansu take. Cikin ikon Allah ta ba Ummita taimakon gaggawa ta farfado sai kuma ta dube su. "Ya dace a yi mata gwaji sosai din tabbatar da abin da ke damunta." Ta furta hakan ta yi shiru don jin me za su ce, a matsayinta na likita ta gama tabbatarwa Ummita na da juna biyu. Shiru ta yi musu don ta fi son ji daga bakinsu sun amince da gwajin. Tana sane da labarin abinda ya afku ga Ummita. Su kansu mutanen gida ba su da masaniyar cewa duk yadda suka so da ɓoye labarin fyaɗen Ummitan sai da ya fita ba. A duniyar yanzun ai mutum ake kiwo ba dabba ba, kana abu kana ganin tamkar duniya ba ta sani ba amma zirr ake kallonka. Abba ya yi yaƙe. "Babu damuwa Dakta, zamu kai ta asibiti." Ta lura ba su son zancen ya fasu, ita kanta ta tausaya musu babu kamar Ummita wacce tunda ta farfado uffan ba ta ce ba, kukan ma ta ƙi yinsa sai sauke ajiyar zuciya akai-akai. Haka Dakta Inteesar ta yi musu sallama bayan ta rubuta magungunan da ya dace wanda take da tabbacin zai taimaki Ummita bisa yanayinta na mai juna biyu. Mubarak wanda ke tsaye ya ƙurawa Ummita idanu yana jin abu mai nauyi na taso mishi wanda ya fi kama da tsabar tausayinta da kuma kauna ta ƴan uwantaka.  Kamar dai yanda yake tunani. Shi ne ya karɓi takardar magungunan ya fice. *** Kwance yake idanunsa a lumshe, babu komai a ransa sai Humaira. Yana ji a jikinsa an soma zuwa gaɓar da yake da tsananin buƙatar kasancewarsu tare a inuwar aure. Shi din fa ba dutse ba ne, namiji ne kuma lafiyye da yake buƙatar aure. Soyayya mai ƙarfin da yake yiwa Humaira shi ne silar da ya danne wannan buƙatuwar ya ɗora shi kacokam a kanta yana jiran lokacin da mafarkinsa zai tabbata. Sai dai kuma yaushe ne? Wannan damuwar ce ta hana shi fita ko'ina, hatta da mai gyara mishi dakuna bai san yana nan ba, shi dai Nura yana falo yana aiki kafin ya shiga ɗakin. Hatta shi bai dan cewa Fadeel na gidan ba sakamakon motarsa da ba ta nan tun daren jiya. Ɓaci ta yi a hanya ya bar ta can  makanikinsa ya je ya ɗauka. Daidai lokacin Murja ta faɗo ɗakin da ƙunshin kayan gugan Fadeel din a hannunta wanda ta karɓa a hannun Sadi mai gugansu, dama  ta jima a yar barandar da zau sada ta da ɗakin Fadeel tana tunanin dabarar da za ta yi wa Lawal ta shiga. Sai ko ga Sadi ya zo wucewa nan da nan ta karɓa ta ce za ta karasa da shi. Suka gaisa da Lawal a falo, ta nuna zai karɓa ya shigar da su ta ce masa ya bar shi za ta karasa ladanta. Bai ce komai ba, dama a farko gargadin da Fadeel din ya yi mishi ne ya sanya shi dakatar da ita, ya hana kowa ya shigo masa sashinsa idan ba ya nan matukar dai ba Fu'ad ko Alhaji da Ibb bane. Amma ganin kayan wankin ne kawai za ta ajiye ta fito ya sanya shi ba ta wuri shi kuma ya ci gaba da kakkaɓe kakkaben kujeru da kayan kallo. A lokacin da ta shiga dakin, Fadeel ya zagaya bandaki, yana dab da fitowa ya ji motsin mutum a dakinnasa, bai kawo kowa ba sai Lawal. Ya san ba shi da masaniyar yana gida bai fita ba. Don haka ya fito daga shi sai singilet da dogon wandon sport. Daidai lokacin da ta ajiye kayan a gefe ta yi wurgi da filo ta ɗaga katifar gaba ɗaya da zummar sanya layar. Kasancewar idanunta ya rufe ko kadan ba ta ga wayoyin Fadeel din dake gefe ba a ajiye. Tana zuci-zucin ta yi ta ƙare kafin shigowar Lawal ya isketa. Fadeel ya bude kofar ya fito, hakan ba  karamin razanata ya yi ba ta saki layun dake a hannunta suka zube a ƙasan darduma. Mamaki mai tsanani ya kama shi har ya bude baki ya kasa magana. Ya karasa sosai ya kara kallo, tabbas layu ne. Nan da nan ya tamke fuska tamkar bai taɓa wani abu wai shi dariya ba. "Zamanki a gidannan ya ƙare. Wallahi kin ji na rantse maki ko yau Anti Amarya ce ta haifeki dole ki bar gidannan. Ni Fadeel na fi ƙarfinki, na kuma fi karfin duk wani da zai sanyaki aikata mugun abu don ki ci galaba a kaina." Jin haka sai kawai ta hau tsuma da borin kunya. "Ni..nifa ba.." "Shut up!" Tsawar da ya yi ya sanya Lawal faɗowa ɗakin. Nan da nan hankalinsa ya tashi, shima idanunsa suka sauka kan layar dake ajiye a tsakar dakin. Fadeel ya hau shi da faɗan don me ya bari ta shigo masa daki alhalin ya gargaɗeshi. "Ka yi hakuri Yallaɓai, wallahi na yi nayi da ita ta bani kayan gugar na kawo ta nunan ita za ta kai. Shi ne.." "Shi ne me?!" Fadeel a zafafe ya tari numfashinsa jikinsa har ɓari yake yi ga tsikar jikinsa da ya tashi gaba daya. Abin da ya faru shekarun baya kawai ya fadomasa a rai, sadda ya kama  Mamar Fu'ad tsamo tsamo a ɗakin Mahaifiyarsa tana barbaɗa magani. Daga ranar ya tsane ta, rashin wayo da wauta kuma ya sanya bai yi tunanin sharewa ba. Tun daga kuma sadda mahaifiyarsa ta taka wannan magani ba ta ƙara zaman lafiya ba da Alhajinsu, har dai a karshe Alhaji ya yi mata sakin wulakanci. Shi kuma ya sha baƙar wahala a hannun Mamar Fu'ad. Ya ji ya ƙara tsanar Murja ninkin ba ninkin. Kuma yanda ya rantse ba zai yi kaffara ba sai Murja ta bar masa gida ubansa idan ko Alhaji ya ƙi to fa shi zai bar gidan gaba ɗaya. Murja cike da kunyar kamen da aka yi mata ga uwa uba Lawal dake tsaye ya ƙi fita yana kallon ikon Allah, ta durkusa ta kwashi layun ta fice tana dakawa Lawal wata uwar harara kamar idanunta zasu zazzago. Fadeel ya dafe kai yana mai runtse idanu zuciyarsa na tafarfasa tamkar an kunna ruwan heater.  "Ka yi hakuri in sha Allahu zan kara kiyayewa." Gyada masa kai kawai ya yi gami da yi mishi alama da hannu akan ya fita, Lawal ya juya ya fice mamakin wannan hali na Murja da bai taɓa zato ba. Lallai mutum ba abin yarda bane. Shi kuwa Fadeel sai da ya samu nutsuwa sannan ya fada wanka, ba shi da niyyar fita daga gidan amman daga faruwar al'amarin ya ji gaba daya gidan ya fita a kansa. Kai tsaye wurin Ibb ya tafi, dama tun jiyan yake faman kiransa akan zancen bikinsa da ya taso yana ƙin zuwa yana ba shi uzurirrika saboda damuwar Humaira da batun auren Ibb ke taso masa da shi. Murja kuwa tana zuwa ta shiga haɗa kayanta, ta gwammace ta bar gidan da ace Fadeel ya fasa zancen nan har Alhaji ya tsane ta ya kuma ƙi jinin haɗa zuri'ar ɗansa da ita. Anti Amarya kadai ta fadawa, nan da nan hankalinta ya yi mugun tashi, ta hau ta da faɗa tamkar ta ari baki. Babban baƙin cikinta ma ba ta yi shawara da ita ba ta yi raɗin kanta. "Ba ki da wayo ko kaɗan Murja! Wa ya fadamaki samun Fadeel a hannu abu ne mai sauki? Ke kinsan irin karfin ibadar wannan yaron? Toh wallahi ko wani Malamin ba zai nuna masa tashin dare da nafilfilu ba ko an fadamaki baƙin tabon sallar dake goshinsa da goge dutse a goshin ta same shi? Kai Murja! Toh kuwa  ya zama dole ki bar gidannan! Ni zan samu shi Fadeel din nasan siyasar da zan mishi don kar magana ta je kunnen Babansa." Murja ta kara jin wani malolon abu ya tsaya a ƙahon zuciyarta. Dama ta sani Anti Amarya ba za ta taɓa goyamata baya ba. Ta kuma soma  yarda da yayarsu Rabi da ta ce Anti Amaryar kanta kawai ta sani, ba wani so take yi ta tallafe ta ba shiyasa ta ce  ta sauya dabi'u ta nuna ita wata salihar ce. Ban da haka ai ta san wannan ba abu ne mai sauki ba da kuma zai yiwu kawai a yi duka ɗaya lokaci daya a wuce wajen. Ta shareta ta cigaba da hada akwatin kayanta. Kafin wani lokaci ta kammala ta fice abinta, Anti Amarya ba ta kara cewa uffan ba, ba karamin ɓata ranta ta yi ba, ita yanzu babban tashin hankalinta yanda za ta rufe maganar kar ta je kunnuwan Alhaji. Ta tsinewa Murja ya fi a ƙirga. Wannan ya sa ko kallonta ba ta yi ba da ta fice. Allah ya taƙaita Hannatu ba ta gidan ta je wurin dangin Alhajinsu. *** Gidan su Humaira tamkar gidan makoki, babu walwala a fuskar kowanne, Abba kasuwar ma kasa fita ya yi. Mami kuwa ta ƙulle a ɗaka ba wanda ya san me take yi. Ummita kuwa tana kwance shiru kawai har baccin dole ya dauketa sanadin magunguna da ta sha kuma a daren jiya ko kadan fargaba da damuwa sun hana ta runtsa. Karatun alkur'ani Humaira ta kunna a waya ya karaɗe ɗakin don su samu nutsuwar zuciya. Tana sauraro tana bi a hankali ta hanyar motsa lebɓanta duk cikinsu sun kasa yiwa Ummita kwakkwarar magana don ba su san ta inda za su fara ba. Raihana kuwa kanta ta cusa karkashin pillow tana kuka a hankali tana kuma bin karatun. Ji take yi inama komai dake faruwa a mafarki ne. Amma ina, wannan zahiri ne, shi ne kuma gaskiya mai mugun ɗacin da ke addabarsu. Hatta da Mubarak ya shiga wani irin hali, komai yake yi Ummita ce a ransa, bisa umarnin Abban ya bi su Yassar shago amma yana zaune cikin mugun ɓacin rai. Ya rasa dalilin da ya sa ta tsaya mishi a ƙahon zuci watakila kuma tsananin tausayi ne da duba da irin kirkin Ummitan yarinya mai kirki da sanin ya kamata. Bai taɓa ganinta ba face da murmushi saman fuskarta, tana da hakuri sosai da sanyi. Dabi'unta abin so ne ga kowane namiji. *** Mami a hargitse take ta faman danna kiran layin wayar amma abu ɗaya kwamfutar ke nanata mata, a kashe wayar take. Koda ta gaji ta yi wurgi da ita tana mai jan tsaki. Goshi ta dafe cikin tsananin ruɗu. Can kuma ta ji wayarta ta ɗauki ƙara. Ta yi azamar karasawa saman gadon ta ɗauka. Lambar dai da take ta kiciniyar kira ita ce aka kirata da ita. Ta ɗaga cikin sauri. "Kai Bala! Ina ka shiga ne?" "Kiyi hakuri Hajiya, chaji na bayar sadda kika kira ba'a ɗaga ba sai mai chajin kawai ya kasheta gudun a yi ta kira. Ina fatan lafiya?" Ta girgiza kai idanu a runtse tamkar yana ganinta. "Ba lafiya ba Bala, aiki ya ɓaci! Duk inda mutanen nan suke ina buƙatar ganinsu. Wannan karon ni da su zamu tattauna. Sun min ba daidai ba, na fadamusu dama idan har sakamako bai yi kyau ba to sai sun maidomin hatta rabin kudin da na ba su. Ba za su ci komai daga dukiyata ba tunda har kwalliya ba ta biya kudin sabulu ba." "Hajiya ban fahimci me kike son cewa ba? Ke ce fa kika ba su umarnin barin wajen koda kuwa kudaden ba su shiga hannunsu ba? Ta ya ya kuma za ki ɗora musu laifi kacokam?" "Bala sun yiwa yarinya fyaɗe, yarinyar da ban so hakan ta kasance da ita ba. Da ace waccan mayyar aka yiwa ba zai dameni ba. Yanzu dai mugun abun da suka yi ya bayar da mummunan sakamako, ciki ya shiga." Bala ya doka salati mai karfi. Can kuma cikin rage murya ya ce. "Ciki kuma Hajiya? Toh me ake jira da ba za'a zubar ba?" Mami ta sauke huci. "Zubarwa ai wajibi ne. Dole na zubarmata da shi ko don gudun tonuwar asirina. Amma yanzu ni ka nemo min su mutanen ko kuma ka aikon lambar shi Babban nasu sai muyi magana." "An gama Hajiya, zan kira na sanar da shi sai na hadaku a waya don dama ina shirin ce maki ba ya garin ya dan yi bulaguro zuwa Kaduna." "Shikenan, sai ka turo." Tana kaiwa nan ta katse wayar tana ji kamar ta zabga ihu, babu abin da idan ta tuna take takaici kamar rashin cin nasarar mallakar dukiyar Abba da ta kwallafa a rai. Ga kuma shirin tonuwar asirinta da ke son afkuwa, matukar cikin Ummita bai fita ba lallai babu shakka watarana abin ɓoye zai fito fili. *** Mami ta tabbatarwa Abba lalali sai dai a zubar da cikin Ummita gudun zubewar mutuncinsu a idanun duniya. Tun Abba ya na nuna bai amince ba har dai ta ci nasara a kansa ya yarda. Ranar da zasu je a daren Mami ta shiga wurin Anna don amsa kiranta. Anna ta dube ta a yamutse. "Sai wani rawar ƙafa kike yi a cire cikin yarinyar nan, idan an cire wa kike tunanin zai aure ta? Shi Sahabin ko kuwa dai shi mijin naki ya ba babban ɗansa aurenta? Ba kya wannan hangen?" Mami ta ji kirjinta ya buga da ƙarfi. Wannan zance na Anna ko kusa bai mata dadi ba amma sai ta zaɓi ta ɓoye saboda dalilin da ita kadai ta bar wa kanta sani. "Idan har asirinmu zai rufu mene ne ciki Anna?" Daƙuwa Anna ta wurga mata. "Ungo nan nace! Ni dai da ace a asibiti nayi naƙudarki zan iya rantsewa sauyamin ke aka yi ba ke ce jinina ba. Yanzu ke koda wasa idan mijinki ya ce zai hada auren wannan gantalalliyar da ɗansa abin yarda ne a wurinki? Babban ɗanki wanda bai taɓa kusantar zina ba a duniya shi ne za ki yarda a hada shi da ita?" Kafin Mami ta kai ga cewa komai Anna ta ji an bata amsa. "Anna, kar ki kara danganta yan uwana da zina, kowa shaida ne ba zina suka aikata ba, kaddara ce da za ta iya faɗawa kan kowa. Sannan idan auren ne ma sai me? Ni ina sonta kuma na rantsemaki a yau Sahabi ya janye da batun aurensa da Ummita to fa ki rubuta ki ajiye ba ta da miji sai ni nan Mubarak!" Ba Anna kadai ba, hatta da Mami wanda ganin inuwar mutum a farko yasa ta ɓoye abinda ke ranta sai da maganar ta yi mata wani irin duka a kirji. Ta dago tana kallon Mubarak din, sanin da ta yi mishi ba ya taɓa sauya magana. Mutum ne mai magana daya wannan ya yi matukar ɗaga mata hankali har ta kasa siyasar data saba na danne abin a zuciyarta. Fuskarta ta nuna tsantsar ɓacin rai na gaske, idanunta har wani kaɗawa suka yi tsabar bala'i. "Mubarak! Kar ka kuskura na kara jin makamancin wannan maganar daga bakinka. Wacce kake faɗawa ka dinga tunawa ita ta haifar maku ni. Ka kiyayi harshenka!" Mubarak ya yi shiru kawai yana jin zafin maganganun Anna har lokacin suna tarfafasa zuciyarsa. Anna kuwa ta hau zagin Mami tana fadin ta yi mata shiru ai da sa hannunta a rainin da yaran suka yi mata. Shi dai ya dubi Mamin ya isar da sakon Abba akan ta fito su wuce asibiti sannan ya kaɗa kai ya bar musu dakin. Mami ta mike ba ta ko biyewa maganganun Anna ba ta bar dakin. Wannan kalma ta so da Mubarak ya furta yana yiwa Ummita ya tsayamata a ƙahon zuci, abu ne da har abada ba za ta bari ya afku ba muddin rai. *** A kokarin zubar da cikin Ummita aka kusa jaza mata matsala, zubar jini sosai ta shiga yi dakyar aka samu ya tsaya. Sai dai cikin hukuncin Allah mai kaddarawa cikin yana nan daram bai fita ba. Haka aka shafe watanni hr biyu ana fama da abu daya amma cikin bai ko girgiza ba wannan dalili ya sanya Abba cewa a hakura kawai amma gudun masu shiga da fita na gidan Ummitan ta rage fitowa falon idan ya so duk abinda take so a kai mata daki. Ga biki ya matso amma sun kara neman alfarma an ɗaga bisa hujjar kayan dakin da ba a kammala haɗawa ba na Ummitan. Wannan abu mai yiwa iyayen Sahabi da shi kansa dadi ba, ga raɗe-raɗin da aka kawowa uwar Sahabi wai Ummita na da juna biyu, ko kadan ba ta ji ta amince da zancen ba, da hakan ne ai ta san iyayen Ummitan masu dattako ne ba za su ɓoye musu ba. Wannan yasa inda ta ji zancen anan wurin ta bar shi kuma a cewarta ai ciki ba ya ɓuya, idan har akwai to fa zai fito. Mami ta yi nasarar samun wayar WIZZY. Wayarsu ta farko ya nuna bai ma san zancen da take yi ba don gaba daya hankalinsa ba a nutse yake ba gani yake kamar an hada baki ne don a kai musu cafka. Sai da aka kwashi lokaci mai tsawo sannan ta kara nemansa a waya ganin dai cikin dake tattare da Ummita ya ƙi fita uwa uba ga wani irin kulawa da Mubarak ke yiwa Ummita wacce har gobe ba ta da walwala. Wannan abu ya tashi hankalinta ya kuma jefa ta cikin rudani da tsoro. Ya tabbata kenan idan ciki bai fita a cikin Ummita ba za ta iya zama rabon ɗanta nan gaba. Ta kuwa gwammace gwara ta sanar da Wizzy cewa Ummitan na dauke da cikinsa har na watanni hudu don su ga matakin da za a dauka a kai. Cikin sa'a ya ɗaga wayar. "Wai Malama ba mun gama aikin da kika sanya mu ba? Kiran da kike yimin na mene ne bayan kin jaza mana asarar maƙudai?" "Kaga Wizzy, kar ka yimin rashin kunyar banza da wofi! Ni na jazamaku asara ko kuwa ku ne kuka jazamin? Da na ba ku aiki na ce ku ketawa yarinya haddi ne? Shegen halin akuyancinku ya sanya kun afkamata yanzu yarinya tana dauke da ciki har tsayin watanni hudu." Wizzy ya kantamo wata ashariya ya saki. "Ciki kuma?!! Don uwarta ita din akuya ce daga yi sau daya sai ciki!" Mami itama ji tayi tamkar ta sakar masa ashar, da kusa da ita yake a yadda take ji za ta iya shaƙar wuyansa har lahira. "Ko mece ce ni ba wannan ne ya sa nayi kiranka ba. Mafita nake so, idan kuma babu to lallai kuɗina ya dawo. Sadik shi ne sunanka na gaskiya, kai din haifaffen Katsina ne. Ina da kaf tarihinka na kuma san inda zan sameka, wallahi muddin ka bani matsala sai na yi maganinka." Shiru ya ɗan biyo baya tamkar ba zai ce komai ba don ba karamin dauremasa baki ta yi ba, ita kuwa Mami ta san komai bisa shawarar Hajiya Lubna, tun ma basu kai ga ba da aiki ba sai da suka sanya aka nemi dukkan bayanan sirri na wadanda suka ba aikin sannan suka amince. "Hajiya bai kai ga nan ba. Ni dai yanzu kudi mun ci ubansu. Kawai dai abin da ya kamata a bar ta ta haihu, ni kuma zan zo na dauke gudan jinina na kai garinmu." "Me kake so ka ce?" "Eh ina so nace maki ni Sadik Wizzy ina son abina. A bar min ciki ta haihu na karɓi abina." Mami ta yi shiru tana nazari. Idan har Ummita ta haihu ya karɓi abin da ta haifa watarana asiri zai tonu, ita kuma ta rantse ta gwammace gwara abin da za ta haifa din ya mutu da dai wannn gurguwar shawarar ta Wizzy. "Ya ne wai kika yi shiru Hajiya? Ba ki ji nace maki ina son abina ba? Toh ina son abina, duk wanda kuma ya yi yunkurin aika shi lahira nima zan sanya shi dogon bacci. Ina fatan kin fahimta? Idan na karɓe abina ba sai ta je ko uwar ina za ta je ba mu raba gari?" Zufa sosai ya rufe Mami, gaba daya kanta ta ƙulle ta kuma rasa mafita. Dole haka ta amsa da toh suka yi sallama. ***  *LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* 09034973645 Ganin lamuran bana ƙare ba ne, ya sanya a dole suka rungumi ƙaddarar cikin Ummita. Babu yanda suka iya don a gaban idanunsu an yi dukkan wani kokari don a zubar amma hakan bai yiwu ba. Hankalin su Abba da ma kansu su Humaira ya ɗan kwanta ganin yadda Ummitan ta samu nutsuwa don sosai take kokarin ɓoye nata damuwar saboda samarwa ƴan uwannata nutsuwa musamman Mubarak wanda kullum kokarinsa ya kyautata mata. Shi ne siyo banza siyo wofi, kunna mata fina-finai a wayarsa da ma bidiyon sanya nishadi da dariya, tun ba ta dariyar har ta zo ta ɗan soma murmushi. Ranar da abin ya ishi Mami sai da ta tunkari Abba a siyasance tana ba shi shawarar ya dace Mubarak ya dinga fita kasuwa kafin lokacin da zai tafi bautar ƙasa. Abban ya nuna hakan daidai ne sai dai ya kara da fadin.   "Amma na so ace ya hakura da kasuwarnan ya cigaba da daukewa yar uwarsa hankali ta hanyar hirar da yake taya ta. Naji dadi kwarai da na ga murmushin fuskarta jiya, na kuma sani hakan yana da alaƙa da shi. A duniya yanzu bani da burin da ya wuce na ganin farin cikin yarinyarnan. Ina kuma cike da fargabar yanda yan uwan Mahaifiyarta za su karɓi batun cikinta." Wannan magana ta Abba ko a fuska ba ta yiwa Mami ba. Ta fakaici idanunsa ta watsa mishi harara sai kuma da ta ga ya kalleta ta gyara fuskar sosai kai ka ce gaba daya damuwar duniyarnan ita aka ɗorawa. "Ni kaina hakan yana yimin dari bisa dari, sai dai kuma hakan fa ba mai ɗorewa ba ne tunda wataran din dole ne ya wuce bautar ƙasa. A yi hakan dai yanzu, na maka alkawarin in sha Allahu zan tsaya tsayin daka wajen ganin ba ta faɗa cikin ƙuncin baya ba. Ga yar uwarta Humaira ma kullum tana nan tare da ita." Sai da ta ambaci Humaira sannan Abba ya ce. "Af, kinga zan manta, mun yi magana da iyayen Fadeel, mun kuma yanke nan da watanni shida zuwa sadda shi Fadeel din ya kammala gini za a tsaida zancen aurensu." Wani irin jiri ya nemi kwasar Mami daga zaune, ta hadiyi miyau sannan cikin yaƙe ta ce. "Wannan abin farin ciki ne sosai Abban yara, amma kuma ba ka ganin kamar zai zama mun zalunci yarinyarnan? Har wannan lokacin fa Humaira ba ta kula shi, ba ta kaunarsa." Abba ya dan daure fuska. "Bar ja'irar yarinya marar wayo. Ai ba ita ta haife mu ba. Ni na gaji da wadannan mugayen dabi'unnata na korar samari da wulakantasu. An kawomin ƙararta ya fi a ƙirga, a yan watannin nan da fitowarsu dalilin da yasa ban tayar da maganar manemanta ba saboda halin da yar uwarta ke ciki ne, amma ko sati ba a yi ba akwai wanda ya same ni bayan na fito daga masallaci cewa ɗansa ya gani kuma yana so. Hakuri dai na bayar. Ni ba zan biye mata ba. Aure ne dai sai ta yi, idan ba ta son shi Fadeel din ta zo ta kawo wani." Tsaki Mami ta ja a ƙasan ranta, kamar ta shaƙo wuyan Abba haka ta ji. Kamar yanda ta saba kuma sai ta shanye bacin ran, fuskarta a ɗan daure ta ce. "Aa fa Abban yara, nikam ba wanda zan yarda ya yiwa ɗiyata dole. A dai bi abin a sannu. Yanzu dai ya muka kwana batun kai ta wurin mai magani." Girgiza kai Abban ya yi, wato dai Mami ba ta taɓa ganin laifin ƴaƴanta. "Duk sadda ku ka shirya zuwa Mamin Humaira, ni mene nawa a ciki zan mata dole ta je ne?" Ya fadi cikin gatse da kuma zolaya hakan sai ya ba Mamin dariyar da bai kai ciki ba, ta ɗan dara ɗin tana mai farr da idanunta. "Naji din, ko ma me za ka ce hakan ne kawai. Yau dai muna da baƙi, yaran Abba zasu kawo mishi ziyara. Zuwa gobe sai muje." Abba murmushin shima ya yi, ya gane Tasleem da Futuha take nufi. "Toh Allah ya kawo su lafiya." Ta amsa da amin. Humaira ce ta yi girkin gidan a ranar, ta dawo da aikinta tuƙuru na shiga kicin ganin hakan yana ɗebemata dukkan damuwa sai dai kuma har gobe masu neman ta karɓi odar su ta kasa, ko Mami ba ta sanarwa ana neman odar abinci ba saboda a ganinta ba ta da nutsuwar da za ta yi abin da ya dace. Bayan ta kammala komai ta zuba a kuloli, ta bar Ladidi da gyaran kicin din ta koma nasu dakin. Kamar dama jira yake, sai ga waya ta shigo. Koda ta duba Fadeel ne, wani irin ɓacin rai ta ji ya danne wani sashi da ke kokarin sanyayamata rai, ta kasa fahimtar yanayin da take ji akan Fadeel tamkar dai guda biyu ne. Farin ciki da bakin cikin da ya danne wannan farin cikin. Babu walwala ta amsa da sallama. Shima ya amsa sallamarta. "Ina fatan ban takuraki ba? Fatan kuna lafiya?" Ta tsuke baki, tsiwa take son ace ta yi amma sai ta ji tamkar wani ɓangare na zuciyarta na kwaɓarta. Ta kai duba ga Ummita da ke kwance idanunta a kan Humairar. Sai ta ji dagaske ta kasa tsiwar a gabanta don haka murya ciki-ciki ta amsa. "Lafiya muke. Fatan kaima haka?" Daga ma muryarsa za ka fahimci ya ji dadin yanda ta amsa ba kwanaki da take balbale shi da faɗa da bakaken maganganu ba, shi kuwa bai ma san zafi biyu ne suka hade mata a baya ba, ga na halin da cikin jikin Ummita ya jefata, ga kuma na wani ciwon kai da bacin rai da muryarsa ke haifar mata marar dalili. "Lafiya kalau nake. Ina neman ɗan wata alfarma wajenki Boddo." Sarai ta san me yake nufi da wannan sabon sunan da ya raɗa mata, wato kyakkyawa. Sai ta zaɓi ta basar ta hanyar fadin. "Ina jinka." "Zan iya shigowa mu gaisa?" Ta ɗan yi jim, ba komai take tunawa ba sai zuwansa na karshe a watannin baya da har Mami ta ji babu dadi. Yanzu idan ta ce ya zo kuma fa? Ta ji wani abu na tafasa zuciyarta, bakin cikk na saukar mata da ba ta san na mene ne ba. Wani bangare na jan ta da kokarin ta furta ya zo din, amma wani bangaren na kwaɓarta da nuna ta tsane shi, ta tsani ganinsa to me zai zo ya yi mata? "Toh." Ta ji lebbanta kawai sun ba da wannan amsar. Shi kansa sai a ya ji wani shock don bai zaci wannan amsar zai ji ba. Ya yi makamancin tambayar ya fi a ƙirga amma kullum amsar aa, karshe ma ta kashe wayar da hujjar ya dame ta.  Ya yarda addu'a tabbas na tasiri akan Humaira, don duk sadda ya dage iya dagewa a kan lamarinsu sai ya ga sauyi tattare da ita, ya kuma soma yarda da hasashen Hannatu kanwarsa da kafin ta koma Yola da ta ji irin yanda Humairar ke yi da komai ta ce ba yin kanta ba ne a nema mata magani. "Nagode Boddo, sai na shigo." Yana fadin haka ya katse kiran, itama Humaira ba ta ce komai ba ta sauke wayar daga kunnenta. Ta dubi Ummita da ke kallonta cikin murmushin da ba ta san dalili ba. "Mene ne?" Ta tambaya. Ummita ta girgiza kai. "Ba komai, ina dai ganin wani abin mamaki ne a saman fuskarki. Idan ban yi karya ba kina mutuwar son Fadeel amma na rasa meke danne wannan son." Humaira ta dan harareta da wasa. "Ni ba sonsa nake ba. Mu bar zancen don Allah kafin raina ya ɓaci." Murmushin dai Ummita ta ƙara yi, ba ta ce komai ba ta lumshe idanu tana ci gaba da jan carbin dake hannunta. Ita kadai ta san tunanin da take yi, Humaira ta dube ta. Tausayinta sosai ta ji, Sahabi har ya gaji da zuwa hira don ba fita take ba, hakanan ta daina daukar wayarsa. Kullum zancenta guda daya ne, ba za ta yaudari Sahabi ba, ta fi kaunar ya san ita din ta haramta aurensu koda kuwa bayan ta sauke nauyin cikin dake jikinta ne. Ba za ta aure shi ba sam. Ba ma za ta yi auren a duniya ba kamar yanda ta ke faɗamusu a yanzu. Shigowar Raihana ɗakin ne  da sallama ya sa Ummita bude idanun, itama Humaira ta kauda dubanta daga gareta zuwa ga Raihanar. Wannan ne ya katse tunanin dukkansu. "Mami ta ce ku fito ku gaisa su Tasleem sun zo." "To." Shi ne amsar da Humaira ta bayar ba don tana kaunar ganinsu ba domin ta gama sanyawa a ranta su din ba masoyansu ba ne. Ba kuma zasu kaunace su ba har gaban abada. Sai da Raihana ta kara maimaitawa sannan Humaira ta mike, Ummita daman tuni ta yi gaba. Cikinta bai da girma bai fito ba. Tasleem wacce daga makaranta ta shigo gidan sanye take cikin uniform dinta ga tirtsetsan cikinta dan watanni takwas sai faman taunar aya take yi suna hirar makarantar da Mami, watanni shida kawai ya rage ta kammala karatun gaba daya. Ba ta yi ko mintuna uku ba sai ga Hajiya Futuha ta shigo tana ta faman shan ƙamshi. Tasleem ta harareta ta gefen idanu ta kauda kai tana ɗan huci, fatar Futuha ta kara kyau kamar ka taɓa jini ya fito, kamshin turarenta kuwa ya buɗaɗe falon gaba daya. Ƙasim na rike da jakarta yana take mata baya, babban burinsa shi dai ta ba shi na kashewa. Yassar ya dube ta. "Ka ga manya matar Alhaji naku daban da nasu. Irin wannan ƙamshi haka? Gaskiya zan zo a sammin turaren." Ta karaso ta zauna jikin Mami tana dariya. "Har ka bani kunya ɗan uwa. Idan dai turare ne, ko direba zan aiko ya kawomaka na siyo su kala-kala a Dubai." Aka sa dariya Dawud na fadin. "Inyeee! Ka ga Hajjaju mutan Dubai." Mami dake murmushin jin alfahari ta ce. "Ya ishe ku hakanan toh." Tasleem dai ba ta tanka ba sai dariyar yaƙe kamar bakinta zai rabe biyu amma ƙasan ranta ji take tamkar ta kurma ihu. Shigowar Ummita da su Humaira ya sanya hirar ta tsagaita, suka gaishe su, Futuha ta amsawa Humaira faram-faram don tsakani da Allah so take ta wuce da ita gidanta ko don girki. Tana da mai aiki amma ko kusa ba ta iya abincin da Alhaji Yakubu ke so ba kullum sai ya yi mita wannan dalilin ne ya sanya take son tafiya da Humaira gidan koda na kwanaki ne ta nunawa yar aikinta yanda take sarrafa tukunya. "Humaira sannu, bayin Allah har kun dawo hayyacinku wallahi." Fadin Futuha, sai kuma Raihana ta sanyo wani zancen gudun kar a tada abin da zai sosa musu inda ke ƙaiƙayi. Yassar da sun riga sun samu labarin komai kuma har a zuci ba su yi farin cikin ƙaddarar cikin Ummita ba sai ya sanyo hirar abinci yana kiran a kawo a ci ya kwaso yunwa daga kasuwa. Tasleem kuwa ƙuri ta yi da idanunta akan Ummita ba ta ko ƙiftawa musamman ma da Ummitan ta mike tsaye ta sauya wurin zama. Da ta kammala tabbatar da zarginta sai ta ga ta nan a tsaye ta miƙe har ayar da take ci na zubewa a saman kafet. "Kut! Me nake shirin gani Mami?" Ta yi furucin har a sannan idanunta na kan Ummitan. Gaba daya suka dube ta, Ummita kuwa ganin idanun Tasleem a kanta ya sanya ta ɗago me take son fadi, wato dai itama ta gane tana da ciki don haka sai ta mike da sauri-sauri ta shige daki saboda kukan da ya tahomata na tsantsar damuwa. "Me aka yi kike mana ihu? Ita kuma wannan me aka yi mata ta miƙe?" Futuha ta jero tambayoyinta lokaci guda.  Tasleem ta cafe zancen tana kara hura hancinta da ya buɗe saboda ciki. "Ciki na gani jikin yarinyar nan." A razane Futuha ta buɗe idanunta ta dubi Humaira da kuma Raihana sannan ta maido hankali ga Tasleem. "Wa kenan?" "Ummita mana. Mun shiga uku, shikenan yarinyarnan za ta ɓata sunan gidanmu, image din gidanmu zai lalace a idanun duniya. Meyasa ba a zubar da cikin ba Mami?" Humaira wani tururi zuciyarta ke yi na ɓacin rai, wato ita Tasleem ba ta ko tausayawa halin da Ummitan ke ciki ba balle tayata jimami. Kamar ta tofa sa kuma albarkacin Mamin dake zaune a wurin ta ja baki ta kuma zuba idanu ga Mamin don ganin me za ta ce. Mami kuwa ta gefen idanu ta ga irin duban da Humaira ke mata don haka nan da nan ta daure fuska. "Idan ita ba ta ɓata mana suna ba, ke gashinan ai kina ihun da makwafta za su ji su fahimci halin da muke ciki! Wannan wane irin rashin tunani kike aikata mana? Kina haukar tonawa yar uwarki asiri?" Jin haka sai Tasleem ta koma ta zauna, ta ja guntun tsaki ba ta ce uffan ba. Ita wannan duk bai dameta ba kamar yanda kawayenta da dangin miji da ma abokan hulda da ake kunya za su samu labarin cikin Ummita ya zamar musu abin habaici da zagi. Futuha kuwa, babu abin da take hangowa sai irin yanda labarin zai karaɗe social media alhalin ta gama karaɗe ko'ina da nuna hotunan su Ummita tana shaidawa duniya su din kannenta ne. Yanzu idan zancen nan ya fita ai ta shiga uku. Yassar ne ya basu labarin duk fadi tashin da aka yi don ganin an zubar amma abu ya faskara. Tasleem ta ja tsaki karo na biyu. "Ba dai abi hanyar da ta dace ba. Ni wallahi da tun farko an faɗamin da kaina zan zo na yi mata alluran da na tabbatar sai cikin ya zube. Amma yanzun ma ai ba ta ɓaci ba, me zai hana a markaɗe shi?" "Wai Sis Tasleem meyasa ba ki da imani ko ƙanƙani? Kina magana babu ruwanki idan an yi ko Ummita ta mutu ta rayu." Tasleem ta harzuƙa da zancen Raihana. "Da wannan abin kunyar ba gwara ace ma mutuwar ta yi ba! Ai gwara mu lulluɓe ta cikin sutura a kai ta kabarinta da dai ta haifa mana shege." "Sai dai ke ki mutu! Ai dama wanda bai sonka ba zai taɓa sonka ba. Na kuma gama gasƙatawa ke din azzaluma ce da ba kya kaunar naki. Ciki kuma ƙaddarar Ummita ce da bai wuce faɗawa kan kowa ba koda kuwa matar auren ce. Nawa aka yi? Yanda ba kya kaunarmu har abada ba zamu taɓa kaunarki ba, yanzun ma albarkacin masu albarkar kika ci da ban ɗaga yatsuna na watsa a saman fuskarki ba." Humaira ce ke wannan zantukan cikin tsananin rufewar idanu jikinta har tsuma yake yi. Tasleem ta yi laƙwas, ina za ta mance shaƙar da ta yiwa Anti Jannat, me ya yi mata zafi da za ta yarda ta yi katoɓarar da itama za a shaƙe ta ga tsohon ciki. Falon gaba daya aka rasa mai tankawa Humaira, su Yassar wadanda sun soma hankali sun ragewa zuƙatansu ƙiyayyar Humairar ba wanda ya goyi bayan zantukan Tasleem din. Mami kuwa kamar yanda ta saba danne bakin cikinta da soyayyar yarannata a lokuta barkatai don siye zuƙatan yaran wannan karon ma haka ta yi. "Koda wasa kar na ƙara jin makamanciyar wannan magana daga bakinki. Kina kiran mutuwa ga yar uwar da ke ganin girmanki. Ban san me yarannan suka tare maki ba. Kina dai kan gaɓar haihuwa ki ji tsoron Allah." Mami na kai wa nan ta mike tana ɓata rai ta kama hannun Humaira suka yi daki wurin Ummita. Itama Raihana ta mara musu baya. Tasleem ta ja tsaki. "Ni ban ga amfanin abin da Mami take yi ba. Duk lalacewar naka, naka ne. Ta guji ranar da wadannan mutanen za su yi mata butulci." "Uwar biyu kenan, sai kin zauna da su sosai za ki fahimci ba su da kowace matsala. Ni kaina a farko rashin ba Humaira dama ya sanya ni tsanarta amma yanzu da na dan zauna na saki jiki da su na fahimci kirkinta. Wallahi sosai na tausaya musu sadda suka yi nesa da mu, na kuma gane ina kaunarsu a jinina, ba zan iya fasalta yanda labarin cikin nan ya jefa ni ba. Duk da ban kai Yaya Mubarak shiga damuwa ba." Fitowar wannan zancen daga bakin Dawud ya ba Futuha da Tasleem mamaki, dama akwai ranar da Dawud zai fadi mai kyau akan su Humaira? Yassar wanda shima bai jin ƙinsu ko kuma kaunarsu a zuciyarsa, dariya ya yi. "Kai babban yaya ai ya faɗa, rannan Anna ke fesamin wai son Ummitan yake yi. Tana ta masifa da tsinewa zancen ta ce ko bayan ranta ba da yawunta ba." "Wallahi ba za ta saɓu ba. Tab! Me Yaya Mubarak zai yi da sauran ƴan ta'adda?" Futuha ta yi furucin a zafafe. Tasleem kuwa ta ma kasa cewa komai ji take kamar abin da ke cikinta zai fito idan ta ƙara magana saboda tsabar takaici da ya yi mata lulluɓi a ƙirji. "To sai me? Ni wallahi don ya riga ni furtawa ne amma na ƙudurta ni zan aure ta matukar wancan Sahabi ya guje ta." Cewar Dawud. Kiran sallar azahar ne ya tashi mazan, Tasleem ta dubi Futuha. "Me kike tunani akan maganar cikin nan?" Futuha ta yamutse fuska. "To me zamu iya yi tunda an binne zancen ba a sanar da mu ba sai da ya fito?" Tasleem ta yi ƙwafa. Ta ciro wayarta ta kira Jannat ta fesamata abin da ke afkuwa. Jannat ta feshe da muguwar dariya. "Dakyau! Ki ce abu ya yi dadi? Toh ai wannan maganar ba abin a ɓoye ba ne. Ke ban da abinki tunda har ya afku ai zai fito. Kawai mu juya zancen mu yaɗa cewar dama karuwancinsu suka tafi, itama Humaira an keta mata haddi. Idan har duniya ta yarda ta amince kinga ai shikenan? Ban da Abbanku da DPO akwai wani da ya san an gan su kafin a kama su sun gudu?" "Aa." Tasleem ta furta da sauri. "Toh kinga idan ma an bada wannan hujjar zamu ce a kawo shaida, wacce kuma babu ita ba za a same ta ba." Shiru dai Tasleem ta yi, Futuha ta zubawa Tasleem idanu, so take ta kammala wayar don ta labarta mata abin da Antin ta ce. "Anti toh dan jira zan kiraki." Daga nan suka ajiye waya, ta labartawa Futuha yanda suka yi. Tun ma kan akai aya Futuha ta hau girgiza kai. "A'a, a'a, Tasleem kar ku yi haka. Nidai Futuha babu hannuna ciki. Ba fa sunansu kadai za a ɓata ba kenan har da na gidanmu. Nikam ba za'a yi haka da ni ba gaskiya, count me out!" Tasleem ta harareta kawai sai ta yi shiru ba ta ce uffan ba. Futuha ta zubamata idanu, ta san halin muguntar Tasleem, shirunta na nufin abubuwa da dama. "Ina fatan dai ba kina son cemin za ki haɗa kai da Anti Jannat ku aikata wannan babban kuskuren ba?" "Sai aka ce maki bani da hankali ko? Mtsw." Ta ja mata tsaki ta mike ta nufi dakin Anna amma ta gama ƙudurtawa a ranta babu fashi. Idan har ƙimar ita kanta ƴar tiktok Futuha zai taɓu a zage ta a idanun duniya toh wannan daidai ne. Gwara ma su yi hakan kawai. *** Mami ta taushi Ummita dakyar ta samu ta yi shiru, ta yi musu ƴar nasiha sannan ta fito. Kai tsaye dakinta na nufa ta dauki waya ta kira Hajiya Lubna. Komai dake afkuwa ta zayyane mata. Ta kara da faɗin. "Yarannan sun tada hankali lallai sai dai a zubar da cikin Ummita, kinsan dai yadda muka yi da Sadik Wizzy. Ina tsoron su kwatanta wani mugun abun." "Haba Maryam, sai ka ce ba ke kika haife su ba. Ba za ki yi musu jan ido ba? Wai ni Maryam duk ba wannan ba, ina aka kwana batun kai Humaira wajen Babandi?" Mami ta sauke ajiyar zuciya gami da ƙara gyara zaman wayar. "An kashe wannan zancen, gobe zan kai ta. Na fi so a yi a ƙare, na gaji ba zan iya ci gaba da wannan pretending din ba. Idan an hana ta auruwa a tura ta bariki kawai mana ba shikenan ba? Na tsani wannan Fadeel mai baƙin nacin tsiya, Babandi ya tabbatarmin muddin dai bai fice a rayuwarta ba to lallai shi zai rusa komai. Mun kasa jefa mata ƙiyayyarta a zuciyarsa kamar yanda ita muka jefamata, ba na nasa kaɗai ba har na dukkanin wani namijin da zai furta mata kalmar so. Kamar kuma yadda muka yi wa FATIMA har ya zamo silar rabuwarta da Yusuf. A ƙarshe kuma muka zama ajalinta ta hanyar yi mata turen aljani ya kashe ta." Wannan zancen ne ya yi dirar mikiya a kunnuwan Futuha wacce ta nufo Mami don sanar da ita yanda suka yi da Tasleem, ta tsaya cak a ƙofar ɗakin cikin wani irin kakkarwar jiki da zufa. Juyowar da  Mami za ta yi ta ga mutum tsaye cak a bakin ƙofa, ba ƙarama razana ta yi ba wannan ya sanya ta ajiye wayar cikin rawar murya ta ce. "Ke kuma me ya kawoki nan?" Futuha ta karasa shigowa dakin sosai har lokacin bakinta a hangame saboda tsananin mamakin da ya gama baibayeta. "Mami, duk ke kika aikata waɗannan abubuwan?" Cikin sauri Mamin ta ƙarasa ta rufe ƙofar ɗakin, ita dai Futuha bin ta take yi da kallo har lokacin kamar a ranar ta soma ganinta a duniya. Cikin kausasshiyar murya ta amsa. "Eh ni ce, na aikata kuma ina kan aikatawar, ina kuma gargadinki da babbar murya! Bar ganin kin fito daga tsatsona na rantse maki matukar kika yi gangancin tonan asiri koda a wurin yan uwanki ne sai na manta da ni na haifeki, zan iya daukar kowane irin mataki muddin dai buƙatana za ta biya." Futuha ta jinjina kai ta kasa ma cewa uffan don gani ta yi tamkar wata Mamin ce daban a gabanta. Sai kuma ta daure ta hadiye fargabanta ta ce. "Mami, kenan duk wannan kauna da muke gani kamar kin fi yiwa su Humaira a kanmu duk ba gaske ba ne? Har fa kidnapping din da aka yi naji kin ce ke ce." Ta juya tana wani mugun murmushi ta karasa ga madubi tana kallon kanta. "Wawaye, ina ku ka taɓa gani ko ji uwar da ta so ɗan wani sama da nata? Babu ita kaf faɗin duniyarnan. Idan ma akwai toh ni Maryam ba na cikinsu." Sai ta ƙara sakin murmushi mai haɗe da ƴar dariya. "Tun auren Yusuf da Fatima, nake ƙunshe da baƙin ciki a zuciyata, kakkarfan shaidar da aka yimin a garinmu da ma makwaftan da muka zauna da su a garin nan kafin rasuwar mahaifina na cewa ina da baƙin kishi kuma har akan kishin ne na taɓa marin (wani ɗan uwana da mahaifina ya so na aura) a bainar jama'a, na zazzagi uwa da ubansa kawai don ya ambatamin sunan tsohuwar budurwarsa kuma yar uwata da aurensu bai yiwu ba yana mai yabonta a kan idanuna. Tun daga wannan ranar ne na fasa aurensa. Ba shi kadai ba, na rabu da mutane da dama saboda kishi, saboda tsanar da na yiwa kishiya, mahaifina ya taɓa neman aure na wanki ƙafa har gidan da ya je nema na ɓata sunansa kuma aka fasa auren. Baƙin shaidar da na samu sanadiyyar zazzafar kishi ya sanya da Yusuf ya shigo rayuwata matsayin saurayin da bai taɓa aure ba, ya shiga zuciyata sosai. Na sa a raina ba zan taɓa nunamasa zazzafar kishina ba saboda a lokacin labarin komai da na aikata a baya ya je kunnensa ta wurin munafukai, wannan ta sanya ya yimin gwaji kala-kala kamar ya yimin wasan yana da mata auren haɗi, yana da budurwa da dai sauransu. Ni kuma na danne bana nuna masa ɓacin raina har sai da ta kai ya ƙaryata zantukan mutane a kaina. Amma fa duk radda ya yimin irin wannan idan na koma gida ranar ko tsinke ba zan ɗauke da sunan aiki ba, kuka kuma zan yi shi. Babu wanda ya isa ya taɓa ni a ranar ya sha. Mahaifina ya rasu dab da aurena da Yusuf. Bayan aurenmu babu irin faɗi tashin da ba mu sha ba saboda rashin kuɗi. Soyayyar da nake yiwa Yusuf ta sanya ban taɓa gujemasa ba daidai da kwayar zarra. Kasuwanci iri iri babu wanda bai yi ba har siyar da kayan miya, gwanjo, da dabino. Kowanne sai an fara rimi-rimi sai lamarin ya ɓaci." Mami ta haɗe girar sama da ta ƙasa ta juyo tana duban Futuha dake tsaye tana sauraronta ta cigaba da magana. "Mahaifin Ummita ya fi mijina rufin asiri sosai, shi mutum ne mai arziƙi, matarsa duk sabgar dangin miji ta fi kowa gayu da kuma kyauta saboda mijinta yana da kuɗi. Ba ta da taƙama balle wani abu wai shi girman kai, wannan kyawawan ɗabi'unta da na tsana, da su ne ta siye zuƙatan uwar mijina kafin ta rasu, ta yi bake-bake a wurin yan uwan Yusuf, ba a ganina da mutunci sai ita. Duk yawan kirkina saboda mijina ba shi da kudi sai na zama tamkar mujiya. Eh uwar mijina tana sona amma soyayyar da take yiwa Jamila ya wuce gejin nawa. Saboda tsabar yanda tsanar Jamika ya rufemin idanu har gani nake yi ba a nunawa yarana kauna a lokacin alhalin ita ko haihuwar ba ta samu ba daga ta samu cikin sai ya ɓare. Haka na jero yara biyar Mubarak,Yassar, Dawud, Ƙassim da kuma Ke. Wannan  lokacin ne kuma Yusuf ya zo min da labarin ƙara aure bayan mutuwar mahaifiyarsa, a sannan kuma ba laifi asirinmu a ɗan rufe yake. Yusuf har shago yake da shi a kasuwa yana siyar da kayayyakin agogo wanda ƙaninsa Muntari ya buɗe mishi. Wannan ma ya ƙara tsananta tsanar Jamila da Muntari a zuciyata ganin wato dai arzikinsu muke ci, da azumi haka Muntari ke sauke mana kayan abinci, da sallah, Jamila ke zuwa ta kawomana kayan fitar sallah wannan abu ya tsayamin a ƙahon zuci. Maijidda ita ce macen da ta soma lura da tarin ƙiyayyar da nake yiwa yar uwarta, akwai sadda ta taɓa ganina muraran ina yiwa Jamila barbaɗen magani a abinci wanda daga shi ne ta tsane ni ta kuma ce Jamila ta yi hankali da ni.   Toh zuwan da Yusuf ya yi da batun ƙara aure ya yi mugun ɗagan hankali amma damuwa ko ta ɗigo ban gwada masa ba, a farko da na ɓata rai, sai ya rude da rarrashina, sai kawai na fashe da dariyar baƙin ciki na nunamasa tsokana ce kawai amma nikam bani da matsala da aurensa. Da wannan ya auro Fatima wacce ya haɗu da ita a kasuwa ta rako Dadarsu siyayyar kayan auren dan uwanta Umar. Shikenan soyayyar ta kai su ga aure. Anna ba ta tare da ni a sannan saboda mijina ba shi da kudi babu wurin da zamu ajiye ta, ita kanta a sannan zagina take yi wai don me zan maƙale nace sai Yusuf da ba shi da ko keken hawa. Nidai son da nake yi masa ya hana ni karɓar ƙorafe ƙorafenta. Ba ta damu da zuwa gidana ba a lokacin. Aka yi auren Fatima da Yusuf, jininta ya hadu da Jamila. Madadin ni da muke dan shiri da Jamilar a baya, sai suka dinke da Fatima suka zama tamkar wasu ƙawaye, a sannan ina da cikin Tasleem, na kai zuciyata nesa na danne da taimakon shawarar sabuwar ƙawata Lubna da muka hadu a wurin wani bikin tsohon ubangidan Yusuf na kasuwa, mijinta mai arziki ne lokacin yana rike da matsayin Chairman. Da taimakonta na san Boka Babandi, muka niƙi ƙafa daga nan har Katsina wajensa ba tare da sanin Yusuf ba. Na samo magungunan hana Fatima daukar ciki muka dawo. Cikinta na farko kuwa ya bi rariya, ni ce mai jinyarta da nuna mata ƙololuwar kulawa. Dadarta koda ta zo ta dinga sanyamin albarka da yabona. Yusuf kuwa tamkar ya haɗiyeni ganin a lokacin ko arba'in din Tasleem ban yi ba na haihuwa amma ina fama da kula da Fatima, wannan dalili ya siyomin sabuwar kauna a zuƙatan yan uwan Yusuf.   Kamar kuma a mafarki ina dauke da karamin cikin Raihana sai ga Fatima da ciki har watanni biyar ya soma fitowa a jikinta, ba karamin firgita nayi ba da na gani saboda ko kadan ban ga wasu alamomi ba. Kuma na rasa yanda aka yi ko a hira ba ta sanar da ni ba. Hankalina ya yi mugun tashi, sai da na kai zuciyata nesa sosai kafin na iya danne damuwata. Ga wani irin soyayya da Yusuf ke nunawa Fatima har a gabana wanda nake ji kamar na shaƙe su duk biyun na huta. Ganin haka ni da Lubna muka ƙara miƙar hanya wurin Babandi, anan ne na je masa da buƙatar jefa tsanar Yusuf a zuciyar Fatima yanda ko sunansa aka ambata sai ta ji haushi. Babandi ya ban tabbacin ba ma Yusuf ba, kowane namiji sai ta tsane shi a rayuwarta muddin ya haɗa ta da wani arnen aljani. Da wannan na tattaro duka chanjina na ajiyemasa. Muka rabu da zummar zan ga aiki da cikawa, ya kuma ban wani hayaƙi yace duk sadda ta shiga halin ƙunci da kuka marar iyaka na yi mata hayaƙin. Wannan zai ƙara tasirin tsanar a zuciyarta. Da wannan muka rayu, Yusuf ya shiga tashin hankalin sauyin Fatima. Akwai radda ta taɓa shaƙe masa wuya dakyar aka ɓamɓare ta sai da na nemi taimako a waje, daga wannan ne kuma ya aikawa Dada saƙo ta zo takanas daga Nijar aka tafi da Fatima saboda ta rantse muddin aka bar ta ta cigaba da rayuwa a gidan za ta kashe shi ko kuma ta kashe kanta. Na yi kuka sosai kamar raina zai fita a gabansu, na ce su kyale ta ayi mata magani a nan idan har larura ce, Dada ta dinga rarrashina ta ce gwara ta tafi da ita. Daga wannan ranar ne na rabu da Fatima, rabuwar da har gobe ba ta ƙara tako Nijeriya ba. Wannan abu ya yimin masifar dadi, cikina nada watanni shida, Jamila ta haifi ɗiyarta mace mai sunan mahaifiyar Jamila, Rahina suke kiranta da Ummita. Sun yi gagarumin sunan kashe kudin da naji tamkar na dora hannu a ka nayi ihu da kuka  ina ji inama Yusuf keda kudin Muntari. Da wannan na soma tunanin duk runtsi sai dukiyar Muntari ta zama rabon Yusuf watarana." Mami ta numfasa ta karasa ta zauna gefen gado, ganin haka Futuha itama ta nemi wuri ta zauna, wasu abubuwan za ta iya tunawa wasu kuwa ba ta da wayo. Ta dai san Mubarak na yawan yabon mahaifiyar Humaira da kaunar da ta nunamasa, yayinda su Yassar suka tsaneta saboda tsanar da ta yiwa Abbansu. Maganar Mami ya katse tunaninta. "Haka rayuwar ta cigaba har na kusa haihuwa, Yusuf gaba daya ya rame ya tashi hankalinsa saboa Fatima, ya kai mata ziyara har sau biyu daga nan ne hankalina ya yi mugun tashi, wato soyayyar da Yusuf ke yiwa Fatima ya ninka nawa kenan? Ban yi ƙasa a gwuiwa ba, ban kuma damu da cewar tsohon ciki gareni ba, na bi shawarar Lubna na niƙi ƙafa na koma wurin Babandi. Nan na nemi a yimin aikin da zai sa a raba Fatima da abinda ke cikinta da duniyar ma baki daya. Ya nunamin yanzu haka da muke magana Fatima naƙuda take yi, ya tabbatarmin zaa turamata baƙaƙen aljanun da za su yi sanadin rayuwarta. Na yi murna kwarai, amma abin baƙin ciki ya cemin abin da za ta haifa dole zai rayu a doron ƙasa, nidai ban wani damu sosai ba. Koda ya gama dubansa ya ce aikin zai yiwu haka na tattara na tafi da farin cikin Fatima za ta bar duniyar baki ɗaya. Za ta bar mijina. Sati uku da haihuwar Fatima, labari ya zo mana na rasuwarta. Zo ki ga kuka a wurina kamar zan shiɗe. Na nuna zan je gaisuwa, amma Yusuf ya hana ni saboda cikina ya shiga watan haihuwa, da wannan hujjar ya tafi har ina ce masa ƙafarsa ƙafar jaririyar Fatima ya kawomin ita zan riƙe. Wannan ya sa Yusuf ya ji dadi sosai ya dinga yimin godiya bisa kaunarsa da nake. Har a zuciyata addua nake kada a ba shi Humaira ya kawomin. Aikuwa haka ya dawo babu ita ya cemin wai Dadar ta daukarwa Fatima alƙawarin kula da Humaira, ya yi hakuri. Daga nan fa rayuwa ta dawomin sabuwa fil a gidan mijina. Daga ni sai yarana, na haifi Raihana bayan Jamila ta haihu da kusan watanni shida, Humaira na da watanni hudu itama lokacin. Shekaru suka tafi har aka shekara biyar, zuwa lokacin rayuwar kunci da talaucin ya ishe ni, samun Yusuf ya ja baya sosai. Gaba daya ya zamana hatta kudin makarantar yara daga aljihun Muntari yake fita, wannan ya kara sanyamin ƙiyayya mai tsanani na Muntari da Jamila. Ban samu sukuni ba har sai da na biya wasu yara suka haɗa gobarar da ba a fitar da komai a gidan Muntari ba sai Ummita." Idanu waje Futuha take duban Maminta wannan karon. "Ma..ma.." Ta ma kasa magana taabar firgicin da ta shiga da tsananin ruɗani. Tana kara tabbatar da nisan da mahaifiyarta ta yi a fannin da suke ganin sun fi ta. Mamin ta yi yar dariyar mugunta. "Yes, ni na sanya aka ƙona iyayenta, aka kashe jaririyar da Jamila ta haifa da Jamilar ma. Ban san ya aka yi shegiyar yarinyar ta tsira ba. Haka labarin gobarar ta zo mana, hankalin kowa ya tashi ciki har da ni da na nuna ban san komai ba. Shegiya Maijidda tun a sannan ta nuna ita wallahi ba ta amince gobarar gaske ce ta kashe Jamila ba. Ta ce a bincika amma kowa ya yi burus da ita ga tunaninsu kawai zafin mutuwar Jamila ne saboda irin shaƙuwar da suka yi da juna. Da nayi wani tunani akan dukiyar Muntari sai na shawarci  Yusuf akan ya ɗau riƙon Ummita kar a raba ta da dangin mahaifinta. Nan fa ya amince, ya kuwa dage akan lallai shi sai an ba shi Ummita. Sun so yin fada da Maijidda wacce ta dage lallai ita za ta dauketa, a karshe dai da Kawunnansu suka sanya baki dole ta hakura ta kuma kalleni ta bini da Allah ya isa. Na fashe da kuka ina nunawa jama'a Maijidda ta tsane ni, nan aka hau rarrashina har yan uwan Jamila ana ganin baƙin Maijidda. Yusuf har kusan faɗa ya yi da Maijidda a kaina dakyar dai komai ya lafa. Wannan shi ne silar dawowar Ummita hannuna, daga baya kuma Humaira ta zo wannan kin sani." Futuha ta ja dogon numfashi. "Tab! Mami kina da abubuwan mamaki sosai. Wallahi ba don ke da bakinki kike fadamin ba, da ace a wani wurin na ji dukkan wadannan zan ƙaryata ko waye ya faɗi." Murmushi Mami ta yi. "Ku ne ba ku san rayuwa ba, yanzu da ace wani mugun halin na nuna a zahiri, kuna zaton Abbanku zamu kai yanzu da shi ba tare da mun rabu ba? Ko kuwa kuna tsammanin a baya ida  kishi ya kwashe ni na kashe Fatima da hannuna yanzun zan cigaba da rayuwa a duniya? Ai hakan ba zai taɓa afkuwa ba, komai ɗan hakuri ne da bi sannu-sannu. Ka yi siyasa a komai, ka shanye komai ka danne sai ka ci riba. Ina dab da cin ribar kwace dukiyar Yusuf saboda na faranta maku, na ba yarana maza jari su huta daga maƙon da Yusuf ke yi musu, na kuma nunawa Anna ba Firdausi Jannat ce kaɗai ɗiya ba, nima na san yanda zan iya kwatar kaina a wurin miji, wannan ne dalilin daya sa na sanya aka sace yarannan, sai dai kuma kuɗaɗen su na dab da samuwa, komai ya rushe saboda zuwan ƴan sanda. Amma ban saduda ba, ban kuma karaya ba, har gobe ba zan fasa yunƙurin ƙwatarwa yarana haƙƙi ba tunda ubansa marowaci ne mai shegen maƙo." Fuska a sake Futuha ta rungume Mami kafin ta saketa ta ce. "Wai Mami ashe daman kina kaunarmu?" Harararta ta yi. "Wa ye ba ya kaunar nasa? Na fadamaki ai duk duniya wanda za ki ga ya nuna ba ya son nasa ya fi kaunar wasu toh ƙarya yake yi, munafuki ne." Jinjina kai Futuha ta yi tana washe baki. "Hakane, Mami na kara sonki wallahi. Kin wanke tunanin dake zuciyata na ganin bakya kaunarmu. Ni fa lallaɓa Humaira nake yi so nake ta zo gidana ta koyawa yar aikina girke-girke. Shiyasa kika ga ina ta janta a jiki da kissa." Mamin ma dariya ta ce. "Sai ki bada himma." Sai kuma ta daure fuska sosai. "Ina kara jaddada maki, koda wasa kika yi yunkurin sanar da wani ko wata labarinnan wallahi zan iya kashe ki." Sosai furucin ya tsoratar da Futuha, ta yi saurin rike hannunta. "Aa Mami, wallahi na rantsemaki babu wanda zai ji. Ai ina sonki, ba zan so hukuncin shari'a ko yaya ya hau kanki ba." Sai anan ta saki fuska ta shafa kan Futuha. Daga haka suka bar zancen suka koma falo inda Tasleem suke zaune da su Mubarak ana cin abinci. Ko kallon Futuha ba ta yi ba, tsanarta take ji a zuciya, wato saboda tana da kudi shiyasa har wani shiga daki suke su rufe su na kwasar hira ita da Mami. A duniyarta ko a mafarki aka ce Futuha za ta samu miji wanda ya fi nata za ta ƙaryata. Ga Hamza yanzu ya sauya mata, zamansu gaba daya babu dadi hatta a bangarenta da uwar mijinta da ma yan uwansa. Albarkacin cikin jikinta kawai take ci ta san da wannan. Don ma dai Anti Jannat ta ce ta kwantar da hankalinta har ta haihu sannan su san yanda za su ɓullowa lamuran. Wannan ne kadai ya sa ake ganinta cikin nutsuwa, kuma ita dinma ba ta ragawa Hamzan. ***   Da yammacin ranar daidai lokacin da su Futuha suka fito da zummar tafiya gida har da Tasleem wacce za ta sauke nata gidan sanadiyyar Hamza da ba  zai samu zuwa daukarta ba, sai ko Humaira wacce a dole ba don ranta ya so ba bisa umarnin Mami za ta bi Futuha gidanta ta yi zaman sati biyu kawai don ta koyawa yar aikinta girke-girke, su Raihana sun yo musu rakiya farfajiyar gidan. Humaira tana tuno Fadeel wanda ya ce yana hanya, tana son ta dakata ta jira shi amma wata zuciyar na kwaɓarta da nuna mata babu amfanin sauraronsa tunda ba aurensa za ta yi ba. Suna nan tsaye, tana sanye da yadi mai taushi maroon colour wanda ya fiddo tsantsar kyawunta da hasken fatarta, ta ɗora karamin mayafi a kanta golden colour. Babu kwalliya ko na ɗigo a fuskarta amma kuma sosai kalar ta karɓe ta, zama wuri ɗaya babu fita ya sanya har wani sheƙi fatarta ke yi. Daidai sadda Futuha ta bude ƙofa tana shirin shiga, daidai lokacin maigadi ya wangalewa Fadeel ƙofa ya turo da hancin motarsa ciki. Bisa umarnin Abba, Fadeel ya zama ɗan gida, duk sadda ya zo yana da damar da zai yi parking a farfajiyar gidan. Ya kuma shiga idan an mishi izni su gaisa da mutane. Shi din ne dai ya zaɓi rashin zuwan akai-akai saboda gudun kada ya baƙantawa Humaira ta ga kamar yana neman shigarmata hanci da ƙudundune alhalin gidansu ne. "Wannan motar kuma fa?" Fadin Futuha tana karewa motar kallo, lexus Ls blue black sai sheƙi take yi, daga gani ba a moreta sosai ba don ba ta nuna alamun tsufa ba. "Wannan motar Fadeel ne. Na gane, ya taɓa zuwa da ita sau ɗaya wurin Abba." "Fadeel?" Tasleem da Futuha suka nanata sunan a zahiri. Aikuwa kafin su rufe bakunansu haɗaɗɗen matashin nan mai sa numfashin yan mata tsayuwa na wucin gadi ya fito daga cikinsa. Sanye yake cikin maroon tshirt da baƙin wandon jeans kamar da hadin baki shi da masoyiyartasa. Ya rufe idanunsa da baƙin gilashi yana wani murmushi mai ruɗar da zuƙata. Duhun kayan da ma motar da yake jingine a jikinta sai suka kara fiddo da tsantsar farinsa na usulin bafalutani ɗan asalin garin Yola.  Gaba daya Tasleem ta yi wani shock, suka yi mutuwar tsaye. Idanunta har wani ruwa-ruwa yake yi saboda tsabar kallonsa da ta shagala yi ga wani irin so da kauna dake fisgarta har ta mance da wasu igiyoyi masu ƙarfi da suke nannaɗe da ita suka yi mata shamaki da dukkan wani ɗa namiji da ba muharraminta ba. Shi kuwa Fadeel idanunsa a saman na Humaira har dai su Yassar suka karaso aka yi musabaha. Humaira kuwa ta yi wani irin dauke kai daga kallo daya ba ta ƙara ba. "Wajenki ya zo ne?" Futuha ta wurga mata tambayar tana ɗan murmushin yaƙe, a ranta kuwa jinjinawa Mami ta yi, tabbas ba karamin kokari tayi wurin danne abin da ke ƙasan ranta ba, akwai masifar wahala. Sosai itama ta ji kishin ace Humaira ce ta samu wannan kyakkyawan matashin kuma mai rufin asiri. "Ban sani ba." Amsar da Humaira ta bayar kenan tana ƙara tamke fuska. Tasleem kamar ta shaƙe ta, yarinyar ta samu dama amma tana nuna girman kai. Ita da ace itace da wannan damar ai sai inda ƙarfinta ya ƙare. "Assalamu alaikum." Sallamarsa ta katse musu tunani, Raihana ta jingina jikin Humaira dab da kunnenta ta ce. "Ki riƙe wannan bawan Allahn sosai idan kuwa ba haka ba ni zan maye gurbinki." Ba ta san ya aka yi ba sai tsintar idanwanta ta yi da wurgawa Raihana wata muguwar harara mai nuni da tsantsar kishi, Raihana ta sa dariya tana riƙe kunnuwa gami da ɗan jujjuya kai alamun ta tuba. Tana kuma kara gasƙatawa Humaira na son Fadeel, ba kuma ta san abin da ya danne wannan soyayyar ba. Tasleem ta amsa sallamarsa ciki ciki yayinda Futuha ta saki fuska sosai aka gaisa sannan ya dubi Humaira da shanyayyun idanunsa bayan ya cire gilashin. "Boddo, barka da yamma." Ya fadi yana mai ɗan dunƙule hannu da ɗan ranƙwafar da kai kaɗan tamkar wani basarake. Nan fa gaba ɗaya idanun ya koma kansu ana ganin ikon Allah. *LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* 09034973645 Ba ta ce uffan ba sai idanuwanta da ta sauke a cikin nasa. Ya ji kallon har a ƙasan ransa. "Sauri fa muke yi." Tasleem ta furta cikin ɗaure fuska, gaba ɗaya wani irin mugun kishi ke cin zuciyarta. Fadeel bai ko kalle ta ba ya dubi Futuha. "My sis, ko za ki ban aron ƙanwartaki for just 5mins?" Murmushin da bai kai zuci ba Futuha ta yi. "Ba ka da damuwa. Humaira jeki." Humaira da ke jin kamar ta shaƙo wuyan Fadeel amma sai ta kasa yi mishi musu ta bi bayansa sadda ya yi gaba zuwa inda ya ajiye motarsa. A jikin motar suka tsaya su na hangen su Futuha da ke hira sai ko Tasleem da ta zubamusu idanu tamkar makauniyar da ta samu ido. "Ka kirani kuma sauri muke za mu tafi." Ya ji babu dadi daga yanayin muryar da ta yi mishi magana, ya dai daure ya haɗiye kamar koyaushe. "Humaira kina addu'a sosai kuwa? Kina nafilfiloli da sallar dare? Kina mayar da hankali wajen yawan karatun Alkur'ani?" Ta yi shiru kamar ruwa ya cinye ta, ta sani tana sallolinta biyar akan lokaci, tana kuma addu'a daidai gwargwadon yinta, amma yawan karatun Alkur'ani da kuma sallolin dare da ma nafila ba za ta iya buɗe baki ta ce mishi aa a kansu ba, kawai sai ta ji hakan ya yi mata nauyi a saman harshenta. Ya tsinci amsoshin tambayarsa daga shirunta, don haka ya cigaba da magana a nutse ba tare da ya dauke idanu daga saman fuskarta ba. "Salollin farillah wajibi ne Humaira, amma su Nafiloli neman ƙarin lada ne da kusanci ga Ubangiji. Za su buɗemaki ƙofofin rahma wadanda ba ki taɓa zato ba. Hakanan shi kansa karatun Alkur'ani, yawan tilawarsa da yin azkar safe da yamma zai ba ki kariya daga shaiɗanu da ma jinnu. Babu wani ko wata ko kuma wani abun da zai cutar da ke. Ina roƙonki ki yawaita addu'a, ina kuma ba ki shawarar yawan hailala, istigfari da salatin Annabinmu s.a.w. Ki ɗauka tamkar wani ɗan uwa ne gareki na jini yake ba ki wannan shawarar. Kin yarda kin amince za ki amfani da ita?" Ba ta taɓa jin wani irin sanyi da nutsuwa tattare da kasancewarta da Fadeel ba sai a yau kuma a yanzun da yake kwararo mata waɗannan shawarwarin. Sai gaba daya ya tuno mata da Kawunta da ma Dada, ta tuna da kalar rayuwarta a Nijar, koda wasa idan ta idar da sallah, Dada ba ta barinta ta bar saman darduma sai ta yi nafila ta kuma tsaya ta ga ba ta yi wasa da addu'a ba, hakanan tilawar Alkur'ani, duk juma'a Kawunsu na tattara su har yaransa su yi tilawa, kowacce ta biya inda ta iya. Shaiɗan kwarai ya yi tasiri a zuciyarta da har ya sanya ta yi watsi da dukkan wannan, ta zama daga ta idar da sallar asuba sai bacci ba kamar a farkon zuwanta Kano ba da ma rayuwarta a Nijar inda koda wasa ba ta isa ta koma shimfaɗarta ba har sai rana ta fito bisa koyarwar Dada. A farko tana yi daga baya duk ta watsar. Ummita duk ta fi wannan kokarin. Ita kuwa kasala ya mata yawa. "Kinji? Please." Ya kara nanatawa. Ta dube shi sai ta yi murmushin da rabon da ya gan shi saman fuskarta har ya mance. Ta gyada mishi kai. "Naji, nagode sosai da tunatarwa kuma zan kiyaye in sha Allah." Ai sai ya ji tamkar an jefa shi wata duniyar ta nishadi da farin ciki, sai kawai ya rasa me zai ce ban da leɓe da ya ɗan lasa yana maida mata martanin murmushin. Ƙarar hon da aka danna da ƙarfi ya sanya suka dubi wajen, har ga Allah shi Fadeel ya ma mance adadin mintocin da aka yi mishi alfarmarsa, balle kuma Humaira da ta lula tunanin sakancin da take yi da addu'a tun zuwanta garin. Tasleem ce da wannan aikin ranta a mugun ɓace. "Nagode, kije suna jiranki. Sai mun yi waya ko?" Ta ji tamkar ta ce eh, sai kuma ta fasa ta juya kawai ta kama tafiya, ya bita da kallo sai kuma ya buɗe motarsa ya shiga, ya sani Abba ba ya nan balle ya shiga su gaisa. Don haka ya yi ribas aka buɗe gate ya fice. Itama tana shiga gaban motar kusa da direba, direban ya ja suna ɗagawa juna hannu ita da Raihana. Tasleem da Futuha a bayan motar zaune sai yare suke yi. Ita kuwa duk ta tsargu amma ta haɗiye ɓacin ranta. Tasleem ke mitar dole ne ma Humaira ta rabu da Fadeel tunda har ita ba ta same shi ba to kowa ma ya rasa. Yayinda Futuha ta ce ta kwantar da hankalinta soyayyar babu inda za ta kai. Haka suka yi ta gulmar Humaira ba tare da ta tsinci ko harafi ba. Ba ta da haɗi da buzaye balle ta fahimci akan abin da suke tattaunawarsu. Har aka sauke Tasleem, ba ta da walwala, ganin haka itama Humaira ta ja jikinta ko ki gaida gida ba ta ce mata ba. A gidan Futuha, ɗakin dai da ta taɓa sauka wannan karon ma shi ne ya kasance masaukinta. Ta ajiye jakar kayanta ta faɗa ta ɗauro alwala ganin ana dab da kiran sallar magriba, sai a lokacin ta jawo waya ta kira yar uwarta Ummita. Suka ɗan taɓa hira don ta ƙara kwantar mata da hankali, cikin ikon Allah ma sai ta ga ko a muryarta babu wata damuwa. Koda ta ajiye ta kara tsunduma da tunanin Fadeel, wai me ya yi mata ne ma da har ta tsaneshi hakan? Oho, ta ba kanta amsa, sai kuma ta ja tsaki cikin jin zafin rai, to meye nata ma na tsayawa tunaninsa? Don haka sai ta miƙe ta shimfiɗa darduma jin an soma kiraye-kirayen sallah. Koda ta idar sai da ta yi nafila sannan ta yi salati da istigfari. A karshe ta yi addu'a sosai. Sai kuma ta tsinci zuciyarta da yin wani sanyi tamkar an yayemata wata damuwar. Sabuwar wayarta ƙirar Huawei da Abba ya damƙa musu bayan fitowarsu daga hannun ƴan ta'adda ta yi ƙara sauti mai dadi shaidar shigowar saƙo. Ta ɗauka ta duba. *_Babu wata damuwa ko baƙin ciki da Allah ba zai iya magancewa ɗan adam ita ba. Ki miƙa dukkan lamuranki gareshi, ki kusanceshi, zai kusanceki. Allah yana son masu ambatonsa safe, rana da kuma dare. Ina miki fatan alheri koyaushe._* Ta karanta fiye da sau uku, ya yi mata dadi sosai, ta kuma kasa barin murmushi. Fadeel ne, koda babu suna a lambar tana da haddarta saboda kira na yau da gobe da yake yi kuma duk da ita ne. Ta sauke ajiyar zuciya, kwankwasa ƙofar da Futuha ta yi da shigowarta da sallama ya sanya ta ajiye wayar ta dube ta. Murmushi Futuha ta yi mata. "Yauwa Humaira idan kin huta ki fito ki ɗebi abinci a kicin. Daga gobe za ki soma gwadawa Hafsatu yanda kike tsara abinci da komai, yau kinga sai ki huta ko? Ni zan shiga ciki ba lallai kuma mu haɗu ba sai da safe." Ita dai ta amsa da toh kawai, bayan fitar Futuhar ta girgiza kai. Mamakin wannan rayuwa ta yaran Mami take, tabbas albasa ba ta yi halin ruwa ba, da ace sun biyo Mami hatta da girkin ba su da matsalarsa. Ta rasa menene ribar ɗiya mace idan ta zauna har ta yi aure ba ta iya girki ba. Banda shiriritar Futuha, ta gwammace a koyawa Hafsatu girki ta cigaba da yi mata bauta ita kuwa ta zauna ta miƙe ƙafa. A ƙarshe dai ta watsar da tunane-tunanen da ta tabbatar ba za su yi mata wani amfani ba ta cigaba da ambaton sunayen Allah har aka kira sallar isha'i ta gabatar ta kuma haɗa da nafila ta yi addu'a anan ma sannan ta ninke dardumar ta fita, abincin sam bai yi mata ba. Shinkafa ce dafaduka ta dai ji kaji wadanda daga ka kai saman hancinka sai ƙarni ya bugeka, da sauri ta mayar ta ajiye. Sanin da ta yi idan ta zauna sai ta kwana da yunwa ne ya sanya ta daukar indomie kanana biyu ta dafa ta ci ta sha ruwa. Saita alarm ta yi ya tashe ta karfe uku, dakyar ta tashi saboda ba ta saba ba ga bacci dake neman fin ƙarfinta, sai da har uku da rabi ta buga sannan ta iya miƙewa firgigit tana ambaton sunan Allah. Hakan ya ba ta wani ƙarfi ta kuwa ɗauro alwala ta dawo ta yi nafiloli ta karanta alƙur'ani bacci na ɗaukarta, dakyar ta daure ta yi sallar asuba sannan ta kwanta anan bacci mai karfi ya kwashe ta. Sai wuraren takwas na safe ta tashi ta yi wanka ta shirya tsaf ta dora hijabinta ta nufi kicin. Ta sani mutanen gidan ba sa tashi da wuri, maigidan kansa sai ya kai goma bai fita ba. A kicin ta tarar da Hafsatu na zaman jiranta har ta yi gyara ta wanke kwanuka. Suka gaisa fuska a sake, nan suka shiga haɗa kayan kari, kasancewarta babbar mace kuma mai basira tana hankalta kwarai da yanda Humaira ke sarrafa girkinta. Suyar dankali da agada suka yi sai ko sauce da ta haɗa, sai ruwan shayi da ya ji citta da kanumfari. Sai ko farfesun nama da ta yi da ya ji kayan lambu. Kicin din ban da ƙamshi ba abinda ke tashi, komai ta yi daidai gwargwado yanda ta tabbatar ba za'a yi almubazzarancinsa ba. Hafsatu ta fita da shi zuwa dinningtable na Futuha, ita kuwa Humaira bayan ta zuba wa Hafsatu ta ɗebi nata ta yi ɗaki don ba za ta iya jurar har sai su Futuha sun tashi ta karya ba saboda yunwar da ya addabe ta, a ranar kuma ta tashi da wani irin karfin jiki da walwala. Ta ƙara gasƙata cewar Fadeel, babu abin da ibada ba ta ɗaukewa na daga damuwa da ma ƙuncin zuciya. Hamdala kawai ta ke yi bisa yanayin da ta tsinci kanta a ciki. *** A ɓangaren Fadeel kuwa, sosai suke shirin bikin Ibb da Dakta Salma wanda bai fi sati ya rage a yi ba. Abokansu duk wanda ya ji zancen auren Ibb sai ya tambaya ko an yi na Fadeel? Amsar dai bai wuce nan kusa shima zai yi ba. Kamar koyaushe a kwanakin nan, yau ma su na tare bayan ya raka Ibb wurin Dakta Salma jin tsarin events din da za ta gudanar, Ibb sai faman mita yake yi mishi akan kawai ya kai kudi a sanya aurensu lokaci guda shi kuwa murmushi kawai ya ke yi. Girgiza kai Ibb ya yi. "Fadeel na sanka, kana da ƙoƙari sosai gun ɓoye damuwa, ba ka fiye son ɗorawa mutane nauyin damuwarka ba, amma ba yanda ka iya, mun taso tare kuma kai ɗin aminina ne dan uwana na maka sanin da wani mafi kusa da kai ɗin bai yi ba. Yanzu a ture zancen wasa, please and please ka yi abin da muke da tabbacin yiwuwarsa, idan yin a yi, idan barin a bari." Tuƙi yake yi amma sai da ya ɗan juyo ya dube shi. "Ban fahimceka ba. Me za a bari?" Ibb ya kauda fuska yana ɗan shan ƙamshi. "Auren mana, ko dole ne sai ita? Lamarinta ya fara kai ni bango, ita ba ƴar kowa ba a ƙasarnan sai ji da kai da taƙama. Matan da suka fi ta sun nuna su na yi da kai sun kuma nuna sun ji sun gani kowane yanayi ma a tafi da su amma ka nace mata, ka maƙale sai ita. Haba Fadeel, yaushe duk wannan zai wuce? Har yanzu kana da hope din cewa za ta amince da aurenka da bakinta?" Fadeel bai ce komai ba, amma zuciyarsa zafi take. A duniya bai taɓa yin so ba sai akan Humaira, kuma da son ya tashi kama shi, sai ya yi mishi wani irin kamun dabaibayi wanda ko ya ƙi ko ya so, hakanan zai rayu da shi. Bai dai san abin da gaba za ta haifar ba. "Ban iya ƙiyayya ba, kamar yanda ban iya soyayya ba ka san da haka ko? Meyasa ka ke tunanin akwai ranar da zan iya haƙura da Humaira alhalin ba ta yimin laifin da zan ƙi ta ba har yau? Ko ka yi zaton ta taɓa wulaƙantani ko zagina? Toh Humaira ba ni ta wulaƙanta ba, soyayyar da na furta ina yi mata ta wulaƙanta, amma na yi mata uzurin kasancewarta daga jinsin Dan Adam wanda muka riga muka san ajizancinsa. Ka yi hakuri, na sani kana jin babu dadi yadda ake maka ƙorafi akan aurena har da masu nemana da sharri. Please ina son ka toshe kunnuwanka daga garesu. Duk radda ni Fadeel na furta maka cewa na bar Humaira, toh ka sani ina nufin rabuwa ta har abada, amma yanzu bana jin ko ɓurɓushin hakan a zuciyata. Ba na jin kuma wannan mafarki naka mai tabbatuwa ne saboda ba ta yimin kamun wasa ba. Ka bi wannan ɗan uwannaka da addu'a Ya Sheikh, komai zai zamo tarihi fa in sha Allahu." Harara Ibb ya wurga masa jin ya ambace shi da sunan zolaya, Fadeel kuwa murmushi ya yi mishi yana ƙara yi mishi kirari da Angon Salma. Nan kuma ya saki fuska aka bar maganar gaba ɗaya. *** Cikin hukuncin Allah, a kwana a tashi har tsawon lokacin da su Abba suka ƙara roƙar alfarma a yi bikin Ummita da Sahabi ya kusa cika, a sannan Humaira ta tattara ta bar gidan Futuha adalilin mijin Futuhar da ko kallo suke sai ya dinga kiran Humaira wai ta fito su yi kar ta ƙumshe a ɗaka. Ko kuma ya yi ta santin girki yana fadin ai kaf gidan su Futuha ta fi su iya girki, Futuha tun tana yaƙe har ta zo ta kasa jure ɓacin ranta ganin tashi guda ya siyo wani rantsetsen leshi dan dubu arba'in ya kawo wa Humaira matsayin ladan girki da take yi musu. Anan ne gaba daya ta sauya fuskarta ta ce Humaira ta tattara ta koma gida, ta sa direba ya kai ta bayan ta karɓe leshin. Ba tare da sanin cewa ita Humaira hakan ya fiye mata komai dadi ba don dama ta gaji da zaman gidan, dadinta daya bai wuce na ibadar da take yawan yi yanzu ba sosai, kuma abin mamaki koda Fadeel ya kira ta ta rage jin wannan tsanar da ɓacin ran sai dai ba yabo ba fallasa. Tashin hankalin daake gudu dai shi ne ya afku, Abba ya zaunar da Sahabi da wani Kawunsa a dakin baƙi ya sanar da su abin da ke faruwa. Sahabi da yake jin wai wai a gari bai yarda ba ji ya yi har wani jiri na neman kwashe shi daga zaune. Kawunsa kuwa ya jinjina lamarin, ya kuma yi addu'ar Allah ya sauki Ummitan lafiya a karshe ya ce idan ta haihu ta yi aure ban da Sahabi don tuni dama sun yi mishi mata ganin ana ta yawo da hankalinsu akan Ummita. Sahabi ya kasa cewa uffan, idanunsa sun kaɗa. Tsakani da Allah yake son Ummita, ya kuma so aurenta, amma bisa gargadi iyayensa ga Kawu, matukar idan sun je ta tabbata ciki ne a jikin Ummita toh lallai su faɗi hakan. Sun kuma yi barazanar saɓawa Sahabi muddin ya musa zancen. Da wannan aka ƙulle mishi baki ya kasa cewa komai. Sai ma da zai tafi ne ya roƙi arziƙin ganin Ummita, nan Abba ya ba shi hakuri gami da nunamasa ba za ta iya jure ganinsa ba. Ya yi hakuri dai ya bi umarnin iyayensa. Daga wannan Sahabi ya ja jikinsa suka bar gidan bayan Abba ya damƙa musu dukkan wani abu da suka kawo da sunan aure. Ummita na ɗaki ban da kuka babu abin da take yi, Humaira wannan karon ta ma kasa rarrashinta, ga ciki ya fito ras ana gani kasancewar bai fi watanni biyu ya yi mata saura ta haihu ba. Ta shiga watanni bakwai cif. Ita kanta Humairar hawayen take yi tana gogewa. Ta dai tabbata shikenan Sahabi ya rabu da Ummita duk kuwa da irin dogon wayar da suke yi da soyayyar da suke nunawa juna. "Kaddararki ce Ummita, kiyi hakuri mu rungumeta da hannu bibbiyu. Watarana komai zai zama tarihi." Ta girgiza kai. "Humaira na sani ƙaddarata ce, amma wallahi Humaira na tsani cikin jikina da abin da ke cikin. Ba zan taɓa sonsa ba. Humaira duk sadda cikina ya yi motsi ji nake kamar na ɗauki wuƙa na caka a cikin abin da ke cikin ya mutu gaba daya koda ace nima nawa ajalin kenan. Allah ya isa, Humaira ba zan taɓa yafewa azzaluman nan ba. Har gobe mummunan fuskokinsu na nan a kwakwalwata, wallahi yau idan Allah zai nunamin su, sai na raba su da numfashinsu." Hawaye sosai itama Humaira take yi, balle kuma Raihana wacce shigowarta kenan dakin sanye da Uniform ta dawo daga makaranta ta tsinci labarin fasa auren Sahabi da Ummita kwata kwata a bakin Mami, kuka sosai take yi sanin irin kaunar da suke yiwa juna. Ta karaso ta rungume kafadar Ummita tana kuka tamkar ranta zai fita ta ma kasa magana. Sai Humaira ke aikin rarrashinsu cikin ƙarfin hali duk da itama hawayen ne ke zubomata. "Humaira! Raihana!! Kuna ina?!" Jin muryar Mubarak yana kiran sunansu murya a sama ya sanya su duban juna kafin su fito zuwa falon gaba daya ban da Ummita da ko motsi ta kasa. Kirjinta ne kawai ke dukan tara-tara, zai wahala ta yi mafarki bai afku ba, tana tsoron kuma yanzun ace mafarkin nata ne ya tabbata. Sai ta hau ambaton Innalillahi a ƙasan ranta. Ba Mubarak ne kaɗai a falon ba, har da Mami da Abba wanda bai je kasuwa ba saboda lamarin fasa auren Ummita sosai ya taɓa ransa, dama kuma ya san da zuwan ranar, amma babu yanda iya. "Kai Mubarak, mene ne haka kake ihu a gida?" Mubarak da idanunsa suka kaɗa gaba daya ba cikin nutsuwarsa yake ba, daga shi sai singilet da wando three quarter, fuskarsa ta yi jazur abinka da farin mutum. Waya kawai ya miƙawa Abba, Mami da su Humaira har su na rige rigen zuwa leƙa saman wayar. Rubutu ne a ka yi dogo, headline din rubutun mai jan hankali sai ko rubutun. _*GASKIYA TA YI HALINTA..._* _*Rahina Sani da Humaira Yusuf wadanda kwanakin baya ake tunanin sace su aka yi, a yanzu gaskiya ta yi halinta._* _*Yan matan sun bi samarinsu ne yawon sharholiya inda a karshe har ɗaya ta zubar da cikin da ta yi yayinda ɗayar kuwa Allah ya tona asirinta cikin ya ƙi zubewa tana nan yanzu haihuwa yau ko gobe. Bincikenmu ya tabbatar da cewa ba sace su aka yi ba, dama ƴan hannu ne suka bi abokan watsewarsu ganin asirinsu zai tonu ne ya yi sanadin da suka haɗa baki suka yi ƙaryar an sace su._* *_Tabbas inda ranka za ka sha kallo da mamaki._*  Sakin wayar Abba ya yi har yana taga-taga zai fadi, da taimakon su Mami dake kusa da shi ya samu ya zauna a kujera mafi kusa saboda rawar jiki. Humaira kuwa zuciyarta ke wani irin tafarfasa ranta idan ya yi dubu ya ɓaci, waye wannan ke kokarin ɓata musu suna a idon duniya? Mene ne ribarsa? "Wannan wace irin rayuwa ce? Daga wannan sai wannan? Waye da wannan aikin? Kai Mubarak a ina ka samo mummunan labari haka?" Duka wannan zantukan Abba ke yinsu lokaci guda cikin rawar murya mai nuni da zallar ɓacin rai. Mubarak da ya dauki wayarsa ya amsa. "Abba ina zaune naga an turo group din da nake har da masu bibiyata ta inbox su na tambayar ko dagaske ne. Da na duba naga an yi forwarding sama da sau hamsin. Wannan ya sa na fahimci koda ace ba a jima da baza labarin ba, toh ya samu karɓuwa ainun." "Innalillahi wa inna ilaihir raaji'un! A duniya ba ka sanin cewa kana da maƙiya sai irin hakan ta kasance. Ina so maganar nan ta tsaya iya mu da wadanda suka sani a gidan, koda wasa kar a faɗawa yarinyarnan ko don yanayin da take ciki. Mu rufe duk wata ƙofa da za ta tsinci labarin. A karɓe wayarta, ku kuma ku kiyayi tayar da zancen a gabanta. Ni kuma in sha Allahu sai inda ƙarfina ya ƙare wajen ganin an bi maku hakkinku, koda ace abin da na mallaka zai ƙare sai na sanya an bincikomin me wannan aika-aikar an hukuntashi ya kuma faɗi dalilinsa na aikata wannan abu." Kowa a wurin ya gamsu da batun Abban, Mami kuwa tunani kawai take yi na waye wannan da ya fi ta nuna ƙiyayya ga yaran? Fatanta kar ya kasance wacce take zargi. Ta sani tunda har Abba ya ci akwashin ɗaukar mataki akan al'amarin to fa babu fashi. Da wannan aka kashe zancen amma fa ran kowa a ɓace, koda su Humaira suka koma ɗaki, sun tarar Ummita ta shiga bandaki wannan ya sanya da sauri ta ɗauke wayarta ta kashe ta jefa a sif, da Ummitan ta fito ma babu wani a cikinsu da ya nuna mata komai. Ita ɗin ma ba ta lura da yanayinsu ba balle ta mayar da hankali, damuwar rashin Sahabi ya rinjayi komai. Tana buƙatar ganin ta samu nutsuwa ko ya ya ne, tana tsoron ciwon da damuwa za ta haifar mata. Wannan dalilin ne ya sanya ta jin tsoron tambayarsu dalilin kiran da Mubarak din ya yi musu, sai ta zaɓi yin shiru gami da kwanciya ta hau jan carbi. *** Wasa-wasa sai ga zance ya yaɗu a duniya. Abinka da soshal midiya masu jran ƙiris sai ga labari salo-salo ana juyawa har da masu fitowa su na ƙara nasu gishirin su na ƙara yaɗawa. Abin mamaki da tsoron shi ne har asalin su Humaira da Ummita na kasancewarsu yaran riƙo a gidan da suke haka aka dinga yaɗawa ana faɗin watakila musguna musu ake yi ya yi sanadin shigarsu karuwanci yayinda a wani gefen wasu ke cewa mai yiwuwa son duniya ne ya kai su ga faɗawa halin da suka tsinci kansu. Har da kuma wadanda suka ce koda ace ba karuwancin suka fita da zummar yi ba, zai iya yiwuwa sun yi ne domin su samu maƙudan kuɗaɗe amm a ƙarshe abokan ta'addar nasu suka cutar da su ta hanyar yi musu fyaɗe. Labaru dai iri-iri akan bayin Allahn nan biyu Humaira da Ummita babu irin wanda bai yaɗu ba. Mafi rinjaye sun fi aminta da cewar da haɗin bakinsu aka sace su hakan ta kasance. Ƙalilan ne masu tsoron Allah wadanda ba su yarda da wannan labaran ƙanzon kurege da ake ta fafutukar yaɗawa ba.   Tsintar wannan labari a wurin dangin Ummita da ma Humaira sam bai zo musu ta daɗi ba. Hankali tashe Anti Maijidda ta diro Kano, ko kaɗan ba su da labarin wai Ummita na da ciki, a hakan ma ba ta amince ba sai da ta zo don kanta ta ga Ummita da tulelan ciki, wannan baƙin ciki yasa har suma ta yi ta kuma tiƙe lallai sai dai Abba ya ba ta Ummita su tafi. Mami kuwa tashin hankalinta bai wuce na wayar da Wizzy ya ƙara yi mata bayan bayyanar labarun da ake ta yayatawa ba akan lallai Ummita na haihuwa ta ba shi ɗansa yana so zai kai wa gyatumarsa idan kuwa ta saɓa zai iya tona asirinta. Wannan dalilin ne yasa itama ta kafe akan Ummita ba za ta tafi ba. Anti Maijidda ta fusata ainun ta dubi Mami da hawaye jage-jage saman fuskarta tana kai nunata da yatsa. "Ke Maryam! Ni ba sakara ba ce ki dube ni dakyau! Idan idanun kowa ya rufe ba a ganin aibunki ni kuwa Maijidda ko ruwan teku za ki shiga ki wanke jikinki ki fito ba za ki taɓa sauyawa daga yanda nake kallonki ba. Don haka tun wuri ki fita idanuna na runtse, idan kuma ke kika yi naƙudar Ummita a yau sai ki hana ni tafiya da ita mu gani!" Jin haka sai kawai Mami ta sa kuka sosai, Abba ransa ya ɓaci yayinda Ummita ta kwantar da kai a kafaɗar Humaira tana nata kukan. "Hajiya Maijidda ina ganin ƙimarki kuma albarkacin Jamila da abin da ta haifa ya sa ban taɓa ɗaga idanu na faɗamaki maganganu ba. Ko ba komai kina ganina da wannan girman, amma fa ba zai yiwu ace koyaushe ki zauna kina kushe Maryama ba. Haba, duk ƙoƙarin da take yi akan Ummita bakya gani? Meyasa kike nema ki yanke zumuncin da ke tsakanina da ɗiyar ɗan uwana? Ke a ganinki idan ace yau Maryama na cutar da ita zan zuba idanu ne nayi shiru? Ni ga sakarai?" Mami ta ɗan dube shi ta gefen idanu kawai, yayinda Maijidda ta ji zafin maganganunsa. "Alhaji Yusuf, na ji Maryam ba ta cutar da Ummita, amma yau idan har ni na isa da Ummita matsayin yaya ga mahaifiyarta ina neman alfarma a wurinka ka bar ni na tafi da ita Bichi. Ka ga dai yadda abubuwa suka rincaɓe, sunanmu gaba daya ya gama ɓaci, ba naku ba, ba kuma ga namu ba ƴan uwan mahaifiyarta. Don haka ina  roƙon arziki ka bar ni na wuce da ita." Ummita ko kusa ba ta gane ɓacin sunan da Antinta ke magana a kai ba, sai ta yi tunanin ko don cikin dake jikinta ne kuma ga shi nan an soma sani a gari. Abba kuwa, ya yi shiru yana nazarin maganganunta, da alama sun yi tasiri a zuciyarsa. Ganin haka da sauri Mami ta dube shi. "Yau kenan kana ƙoƙari ka nuna ba ni na haifi Ummita ba? Kokari ka ke yi ka sallamawa Maijidda Ummita ta wuce da ita ko? Kana son nunamin ba ni na haifeta ba, ashe Raihana idan ace ita hakan ya faru a kanta ba zamu yi hakurin duk abin da zai je ya zo ba mu bar ta karkashin kulawarmu ba? Lallai ka sani Yusuf, a yau idan ka amince da dauke Ummita daga hannuna toh ka sani cewa ta tafi kenan har abada ba za ta dawo wurina ba. Na kuma gode da nunamin iyakata da ku ka yi." Tana kai wanan ta juya ta soma tafiya cikin zubar hawaye, wannan ya tashi hankalin Abba da ma su Ummitan.  Abban na kiran sunanta ta yi banza da shi, ita dai Anti Maijidda na tsaye riƙe da hannuwa a kirji tana kallon irin salon makirci na Mami mai ban mamaki. Ummita cikin sauri ta miƙe ta riƙo hannun Mami tana kuka  kamar ranta zai fita lokaci guda tana girgiza kai amma kalma ɗaya ta kasa fita daga bakinta. Mami ta dube ta cikin hawayen sai kuma ta shafi gefen fuskarta ta yi murmushin yaudara. Cikin karyar da murya ta ce. "Kar ki damu Ummita. Da nan din da can duk ɗaya ne." Sai a sannan Ummitan ta magantu. "Aa Mami, kiyi hakuri. Wallahi babu inda zan je, ke din tamkar uwa kike a gareni. Idan har a duniya za iya barin mahaifiyata toh kuwa zan iya rabuwa da ke. Kin rungumeni a sadda na buɗi idanuna babu iyaye, kin maida ni tamkar ɗiyar cikinki, kin kaunace ni ta kowace fuska. Ni kuwa me zai sa na zama mai butulci a gareki? Kiyi hakuri da kalaman Anti Maijidda, ta yi su ne saboda tsantsar tausayi da kuma ganin kamar zan fi samun kwanciyar hankali a can, amma na tabbata ita kanta ta sani kina nunamin kaunar da ba don kar nayi wauta ba, zan ce ta fi na Raihana da su Anti Tasleem." Anti Maijidda ta kasa cewa komai tayi gum sai kallo, Abba kuwa sai kalaman Ummita suka kashe mishi jiki, shakka babu gaskiya ta fadi kuma ba zai so a yiwa Mami butulcin nan ba. Ya dai so a farko ya amince da batun Anti Maijidda idan har sauya wurin zai dawo da walwala da farin cikin Ummita. Humaira sosai ta ji dadin kalaman da Ummita ta yi ga Mami, ta tabbata hakan ne kawai zai sanyaya zuciyar Mamin, sai kawai ta ji Anti Maijidda ta sire a ranta. Ita a duniya yanzu ba ta da maƙiyi irin mutumin da zai kushe Mami da ƙoƙarinta a kansu, abin da dai ta fahimta shi ne, ba a iyawa DAN ADAM, wannan sai mahaliccinsa. Ba ta san mene ne ribarta na aibata Mami ba. Murmushi Mami ta yi tana dubanta kafin ta dubi Anti Maijidda da ta yi mutuwar tsaye. Sai a lokacin Anti Maijidda zuciya ta tunzurota ta soma magana tana duban Ummita. "Yau kin watsamin ƙasa a ido ko Ummita? Ni kika nuna bani da wani matsayi ko ƙarfin iko a wajenki? Wa.." "Anti please. Ki duba yanayin da take ciki mana ki rabu da zancen nan haka. Ina haɗa ki da Allah ki bar komai har ta rabu da abin da ke jikinta lafiya idan har dagaske farin cikin kike nema mata." Mubarak ke wannan tun soma zancen ya shigo yana kuma sauraronsu. Ransa ya ɓaci ba kaɗan ba da yanda Anti Maijidda ke kushe masa uwa kuma mahaifiya amma ya fi jin zafin yadda take neman haifarwa da Ummita wai sabon ɓacin ran na daban. Jinjina kai Anti Maijidda ta yi, ta hadiye ɓacin ran nata kamar yanda ya nema. Dagaske ta fi kaunar samun lafiyar Ummita a yanzun da kuma kwanciyar hankalinta wannan yasa ta taka zuwa ga Ummita ta janyota ta rungume. Yadda Ummitan ke kuka hakanan itama take yi. "Kiyi hakuri ya isa hakanan, shikenan magana ta wuce. Kiyi zamanki anan zamu dinga waya kin ji?" Ummita ta gyada mata kai, daga haka kuma aka kashe zancen. Abba da Mubarak suka fita don haɗuwa da D.P.O don tsaurara bincike akan wanda ya yi wannan aika-aikar da ma neman alfarma gurin D.P.O akan ya fito gidajen yaɗa labarai ya faɗi abin da ya sani kan satar su Ummitan zuwa yanda aka kaya sadda aka je kwato su. Mami kuwa ta ƙara jifan Anti Maijidda da murmushin cin nasara sannan ta juya ta bar falon zuciyarta fari ƙal yayinda ta bar Anti Maijidda da ɗumbin takaici da cizon yatsa. Ta sani addu'a babu abin da ba ya magani, za kuma ta dage da kai kukanta ga Allah, watarana halin Mami zai bayyana ƙarara a idon duniya. *** Anti Amarya ta dubi Alhaji bayan gama nuna masa jita-jitar da ake yaɗawa akan su Humaira ta ce. "Yanzu Alhaji wannan magana ko ƙarya ne a yanda sunan gidannan ya ɓaci fisabilillahi sai ka aminta da auren Fadeel da Humaira?" Nan da nan Alhaji ya ɗaure fuska ya ajiye wayar. "Me kike son ki cemin? Sai na tauyewa ɗana farin cikinsa akan ƙaryar da maƙaryata suke yamuɗiɗi da shi?" Ta tari numfashinsa. "Saboda farin cikin ɗanka mu kuma za ka zubar da namu ƙimar gidan a idon duniya? Ka san wannan ɓacin sunan kuwa ba iyaka Nijeriya ya zagaye ba? Allah kaɗai ya san inda lamarin ya tsaya. Alhaji ya kamata ka buɗe idanunka sarai ka dubi lamarin da idanun basira, ni ban taɓa ƙin Humaira ba saboda ban ga abin ƙi tattare da ita ba kamar yanda babu wani aibu da ta taɓa yi gareni ba. Amma ana magana ne na haɗa zuri'a, idan ya kasance sai bayan mai afkuwa ya afku maganar duniya ta tabbata gaskiya sai ka sa hannu a kumatu ka ce za ka yi tagumi da nadama?" Shiru Alhaji ya yi, maganganun Anti Amarya suka shiga tasiri a zuciyarsa. Dagaske yanzu idan har zancen duniya ya tabbata shikenan ya haɗa iri da ɓata gari? Anti Amarya ganin ya yi shiru sai ta yi ɗan murmushin mugunta, ko babu komai dai alamu sun nuna kwalliya za ta biya kuɗin sabulu, alƙawari ne ta ɗaukarwa kanta yanda Fadeel bai auri Murja ba ya yi sanadin barinta gidan, toh shima har abada sai ta raba shi da Humaira. Sai ta ga iya gudun ruwansa. "Shikenan Antin yara, zan dai duba zancen. Mu yi addu'a mu kuma jira mu ga ta inda gaskiya za ta yi halinta." Ta sauke ajiyar zuciya ganin ta yi nasara. "Hakane, Allah ya bayyana gaskiyar." Ya amsa da amin. Ɓangaren Fadeel kuwa har tsawon kwanaki uku da al'amarin ya fasu yake cikin wani irin tashin hankali da baƙin ciki. Soyayyar da yake yiwa Humaira ta yi ƙarfin da ko daidai da ƙiftawar idanu ba ya zarginta da fasiƙanci balle kuma ya aminta da jita-jitar da ake yaɗawa. Wannan ya sanya a ɓangarensa shima ya sanya aka soma bincike akan al'amarin don a gano bakin zarensa. Ga bikin babban amininsa nan da kwanaki uku amma hakanan damuwar yanayinnan ya gusar da murnar bikin a zuciyarsa. Ta yaya mutanen da aka ceto su cikin wani hali na maye da kuma muguwar rama da baƙi ace yawon duniya suka shiga? Har abada ba zai yarda da wannan ba. Da taimakon wani abokinsu na makaranta wanda yake babban ma'aikacin sirri na SS, bincikensu ya dinga zurfi. Ibb dai ya zuba idanu kawai yana ƙara mamakin wannan irin zazzafar kaunar ta Fadeel akan Humaira. Har shakka yake yi kada bayan aure ya zame mata mijin tace saboda shi kam abin ma ya shallake tunaninsa. *** Tasleem tsaye tana safa da marwa a ƙuryar ɗakinta daga ita sai vest wacce ta ɗage mata saboda girman da cikinta ya yi sai ko ƙaramin short, waya ne a kunnenta, burinta kawai Antinta ta ɗaga domin ta ƙagu ta ji labari. Har sai da ta kusan katsewa sannan Jannat ta ɗaga muryarta a sake. Ko gaisawa ba su yi ba ta gangara inda yake ci mata tuwo a ƙwarya. "Anti, ina ta neman wayarki a kashe na ƙagu naji daga bakinki. Kin ji labarin da ke yawo a media akan su Humaira ko? Anti hala aikinki ne?" Wata dariya Jannat ta yi daga ɓangarenta tun ma kafin ta ce komai Tasleem ta samu amsar tambayarta, sai kuma ta magantu. "Ni ce nan my daughter, ai ban fanshi marin da munafukar ƙanwarki ta yimin ba. Idan sunansu ya ɓaci a idanun duniya wa kike tunanin zai aminta da auren ɗaya a cikinsu? Ko a zatonki wancan sakaran Fadeel ɗin zai ƙara kallonta? Tasleem ki kwantar da hankalinki, yanzu na san na gama ɗaukar fansa akan Humaira don uwarta. Ita kuwa Ummita kinga cikin dake jikinta ya taimaka wurin da jama'a za su yi saurin aminta. Ke tun sadda al'amarin ya faru nake bibiyar kalaman jama'a ina dariya. Huumm muje zuwa." Tasleem ta yi murmushi sosai. "Na ji dadin rabuwar Fadeel da Humaira, na sani ko ya nace akan sonta zai wahala iyayen da suka san mutuncin kansu su yarda ɗansu ya aure ta. Amma Anti naji fa wai Abba zai sa ayi binciken wanda ya fara yaɗawa don a gano gaskiyar magana. Bakya tunanin idan aka kama shi asiri ba zai tonu ba?" Tsaki Jannat ta ja. "Nawa aka yi irin haka Tasleem, kin taɓa ganin waɗanda aka yi nasarar cafkewa?" "A'a." "Toh ki sa ranki a inuwa tawan, babu abin da za su iya. Yanzu ai na kira Abbannaku na jajanta masa har da kukan shegantaka, shi kuwa sai faman godiya da ban hakuri yake." Suka yi dariya Tasleem har tana riƙe cikinta da ya ɗan motsa saboda dariya. "Ina yinki sosai Antina." "Nima haka yar uwa. Maminki ce dai ta matsamin da tambayoyi tun ranar farko shiyasa nake ta kashe waya, wai ita ga mai wayo, bugar cikina take yi don ta gane ko ni ce na sanya a yi amma na nunamata ban san komai ba sai ma da ta faɗamin. Kema ina jan kunnenki koda wasa kar ki kuskura kiyi maganar da kowa." Tasleem ta amsa cikin jin dadi da walwala. "Kar ki samu damuwa Anti. Ba ki da matsala da ni." Daga haka suka yi sallama zuƙatansu cike fal da annashuwar ƙuntatawa bayin Allah. ***   A kwana  a tashi babu wuya cikin ƙudurar Allah, har dai jita-jitar da ake ga su Humaira ya kai watanni biyu, a wannan lokacin ƙura ta lafa sosai sakamakon shaidu daga D.P.O har ma da shi kansa Abba da ma waɗanda Abban ya yiwa tayin gidansa don ceto yaran nasa, likitocin da suka taimaki rayuwarsu da ikon Allah,  da dai sauransu sun bayyanawa manyan gidajen jaridu abin da suka sani akan zancen har ma da irin gudunmuwar da suka bayar a lokacin. Wannan ya sanya jama'a suka gasƙata hakanan waɗanda suka aminta sai suka rinjayi masu kushe da ƙaryata zancen. Da wannan aka rufe babin Ummita da Humaira aka shiga kuma wani labarin daban ya zama abin tattaunawa a sosha midiya. Amma a ɓangaren Fadeel, magana ba ta mutu ba don yana nan a kan bakansa na sanya wa a binciko mai wannan aikin  duniya ta san shi kuma ya ɗanɗani yadda ake ji idan aka ɓata wa mutum suna. A ƙarshe ma da ya ga ba a samu haɗin kai daga jama'a ba, sai ya sanya kuɗi har dubu dari biyar ta hanyar tsohon abokin karatunsa ma'aikaci a SS,  ga duk wanda ya kawo labari ko kuma ya ke da sanayya da wanda ya aikata laifin. Nan fa jama'a kowa ya yi ca, burinsu kawai su samu wadannan kuɗaɗe, a yanda rayuwar ta yi zafi sun san ba ƙaramin taimako zai musu ba. Lokacin da Mami ta ci karo da wannan sanarwar a wani group dinsu na hamshaƙan mata wanda Hajiya Lubna ta buɗe, sosai ta ji hankalinta ya tashi. Ta ji ta ƙara tsanar Fadeel musamman da ya kasance zuwa lokacin Jannat ta gaji da ƙaryata cewa ita ta aikata a wajenta ta fito fili ta faɗamata cewar ita ce kuma fansa ta ɗauka. Ta sani, muddin ya kasance Fadeel sun ci galabar gano mai laifi to fa sunan Jannat zai ɓaci kamar yadda ƙimarta zai zube a wurin Abba. Wannan ne yasa ta fita a whatsapp ta kira Jannat, ringing bai fi sau uku ba ta ɗaga. Mami ba ta jira komai ba ta hau magana. "Kin karanta labarin dake yawo?" Cikin rashin ba abin muhimmanci ta amsawa yar uwar. "Yes, na gani na karanta. Sai me?" Mami ta danne jin zafin ire-iren magana gatsal da Jannat ke yawan yi mata a lokuta mabambanta ta ce. "Sai ki girbi abin da kika shuka tun da ke ba kya shawara da  uban kowa idan kika tashi ɓarna. Shi dai Fadeel da kike yiwa kallon tara saura gashinan yana shirin ba ki mamaki. Ko kina zaton ƙarfin kusancinmu ya kai ya hana shi daukar fansa a kanki?" Tsaki Jannat ta ja. "Ni babu wanda ya isa ya kama ni balle kuma ya ce zai yimin hukunci.  ki ga kwantar fa hankalinki kawai, ni abin ya shafa kuma nawa hankalin a kwance yake don haka ba abin da zai faru." Ƙwafa Mami ta yi. "Shikenan, kiyi kuka da kanki duk abin da ya je ya zo." Daga haka ta katse wayar tana sauke numfashi cike da ɓacin rai. Ta rasa yaushe Jannat za ta yi hankali. Ita komai ba ta iya bin sa da sauki ba sai ta yi garaje? Ai sai ta je ta ji da kunyatar da za ta yi a idon duniya da ma su Abba. *** Yakubu ya dubi Futuha da murmushin yaudara bayan ta nutsu tana sauraron abin da zai ce ya soma magana. "Na lura sam zamanki da Uwargida tun farko ba ra'ayinki ba ne, nawa ra'ayin ne. Hakan yasa na siya maki gida daban a can kusa da yar uwarki Tasleem. Kinga ke kadai abinki babu takura. Hakan ina fatan ya yi maki?" Wani dadi ya kashe Futuha har ta kasa ɓoyewa ya bayyana saman fuskarta, dagaske aikin da ta sa aka yi ta hanyar abokiyar karatunsu Anti ba karamin ci yake yi ba tunda har gashinan ya soma tunanin kawo mata sauyi cikin rayuwa ta hanyar keɓance ta da abokiyar zamanta da nuna bambanci. Ta yi farr da idanu bayan ta rungumeshi ta sakar masa sumba a lebba. "Hakan ya yimin sosai fiye ma da zatonka. Yaushe zan koma?" Wani dadi da sanyi suka lulluɓe zuciyar Yakubu ganin ya shawo kanta cikin mugun sauki. Ya san da ace ta san dalilinsa na tashin wannan zancen sauya muhallin da ba ta fara aminta da hakan ba. "Nan da sati ɗaya an kammala komai sai tariya. Yanzu ana aikin ƙarasa haɗa kayan wutar solar ne." Dadi ya ƙara ƙume ta. Ta ji sosai kaunar Yakubu na ƙara mamayarta. Ɓacin ranta na hotunan auren Ibb da matarsa Dakta Salma da aka turo group din makarantarsu ya wanku a zuciyarta. Batun karatu dama tun tafiyarta Dubai da dawowarta ta watsar, Yakubu ya nuna ba ya so zai wadatar da ita da komai da take so, hakan ya sa ko a kanta ba ta damu ba balle kuma Abba da dama shima ya fi kaunarsu da zaman auren sai dai ya so ace ta kammala. Mami kuwa itama ganin ɗiyarta na samun dukkan abin da ya dace na jin dadin duniya sai ta share zancen karatun. "Allah ya kaimu lokacin." Ya amsa da amin, daga haka ta miƙe ta na fadin bari ta kawo mishi abu mai sanyi, shi kuwa ransa ƙal ganin nan da sati biyu Ƴar Snow za ta zama mallakinsa matsayin matar aure. *** _Sosai Ummita ke ihun daya cika kunnuwanta tana ambaton sunan Allah iyakar ƙarfinta, wannan ya sanya ta nufarta a guje ba ta damu da jinin da ke yawo a tsakar ɗakin ba tamkar ruwan famfo ta damƙo kafaɗunta tana jijjigawa tana fadin._ _"A'a Ummita kar ki mutu ki bar ni, zasu kashe mu idan suka riske mu a nan. Kinga ki tashi mu gudu!"_ _Rigarta Ummita ta damƙa da ƙarfi tana hawaye take fadin._ _"Innalillahi..Kai...Kai..Humaira anya zan rayu? Humaira ko na mutu kar ki bari a jefarmin da gudan jinina. Kar ki bari su yi nasarar rabaki da ɗana._ _Ki kira shi da suna Ahmad sannan ki kularmin da shi tamkar ina raye._ _Wayyo Humaira ga Wizzy nan!"_ _Wai sai ta juya ta dubi Wizzy, riƙe yake da ƙaton adda a hannu yana kiran sai fa ya raba Ummita da jaririn. Kawai sai kuma ta ga jariri a hannunta, Wizzy zai karɓe ta shige gabansa kawai sai ta ga  Mami ta zo ta tureta ta fisge jaririn a hannun Ummita ta damƙawa Wizzy._ "Humaira! Humaira!!" Sunanta da Raihana ke faman kira tana jijjigata iyakar ƙarfinta ne ya sanya ba shiri ta miƙe daga nannauyen baccin da ya kwashe ta a saman darduma. Gaba ɗaya ta haɗa zufa sharkaf duk kuwa da iskar fankar dake kaɗawa a ɗakin. Ta damƙe hannun Raihana manyan idanunta suka ƙara girma har hakan ya yi mugun kaɗa ƴan hanjin Raihana, tsoronta kada dai aljanun Humairar ne suka tashi, cikin rawar murya ta ce. "Lafiyarki kuwa?" "Ina Ummita?" Ta nuna mata ƙofar banɗaki. "Wanka ta shiga." Sai a lokacin ta sauke doguwar ajiyar zuciya cike da tunanin irin wannan mafarkin, me kuma ya haɗa Wizzy da Mami? Ta yi ɗan nisa a tunani muryar Raihana ta ƙara katse ta. "Mami ta ce ki shirya ku yi abin kari sannan ki ɗorawa Sis Tasleem farfesu ta haifi ɗiyarta mace suna asibiti. Yanzu zamu wuce da Mamin, idan an kammala tace ki ba Yaya Ƙassim ya kawo." Humaira ta gyaɗa kai. "Toh, Allah ya raya. Ki gaidamin ita." Raihana ta amsa ta fita a ɗakin, daidai lokacin Ummita ta fito daga banɗakin. Baiwar Allah duk ta rame sai ciki da ya ƙara fitowa, bai fi sauran sati biyu ta shiga watan haihuwarta. Hancinta duk ya buɗe. Ta dubi Humaira tana ɗigar da ruwan wanka. "Anti Tasleem ta haihu? Naji kamar haka Raihana ta ce." Gyaɗa kai Humaira ta yi jikinta a sanyaye cikin tunanin mafarkinta, Ummitar cikin mafarkinta tana so da kaunar abin da za ta haifa har tana ba da amanarsa, amma kuma wannan ta tsani ma a yi mata batun abin da za ta haifi duk kuwa da rayuwar da take gudanarwa maƙale da shi a jikinta. Ummita dake tsane jikinta tana kallon Humaira ta madubi wacce ta zubamata idanu ta yi ɗan murmushin yaƙe. "Kallona kike kamar irin kina bankwana da ni zan mutu wajen haihuwa ko?" Maganarta ta girgiza zuciyar Humaira sosai, ta ji nan da nan hawaye sun cicciko mata ta kauda kai daga dubanta. "Allah ya kiyaye, hakan ma ba zai faru ba da yardar Allah. Don Allah ki daina yawan irin waɗannan kalaman basu da dadi. Ke dai ki yi addu'ar rabuwa lafiya da abin da ke cikinki." Murmushi kawai Ummitan ta yi wanda hausawa ke kiransa da yaƙe daga nan ba ta ce uffan ba, itama Humaira ba ta son zancen don haka ta miƙe ta dauki zani da brush ta yi banɗaki. *** Yarinyar Tasleem sak mahaifinta har duhun fatar, haka dangin mijinta suka dinga zarya a gidanta don tuni aka sallameta a yammacin ranar da ta haihu wato Asabar domin lafiya lau ta haifi ɗiyarta. Ta so kwarai ta je gida wanka amma Mami tana sanar da Abba ya ce sam aa, babban dalilinsa kuma kada a je a yi ta zuwa ana ganin Ummita ana ƙara mata wata damuwar ta daban. Wannan ya sanya hakanan ba don ta so ba ta zauna sai Ladidi ce ta je mata zaman wanka don dama bazawara ce mijinta ya rasu sai ko marayun yaranta da ta bari wajen tsohuwarta. Humaira ba ta leƙa ta ba sai da aka yi kwanaki uku, kullum dai ita ke girki ana kai wa. Sai da Mami ta yi magana sannan ta shirya ta je. Raihana na makaranta su na rubuta jarrabawar mock daga nan kuma ba jimawa za ta soma WAEC. Fuska a yatsine Tasleem ta amsa gaisuwar Humaira gami da fadin. "Sai yau kika ga damar zuwa kenan? Ai da ma kin bar shi gaba daya." Ta kuwa ji zafin maganar ta ji dama sam ba ta zo ba. Wato ba ta ga bautar girkin da take yo mata ba ana kawo wa ba sai kawai ƙorafin ba ta zo ba. Don haka ta ƙi tankawa ta miƙawa Ladidi jaririyar don a yi mata wanka. Ba ta wani jima ba ta fice abin ta. Tare suka wuce da Ƙasim a mashin ɗinsa don yanzu sam Abba ba ya kaunar shigarsu Ɗan sahu. Adalilin haka ne ma yake ƙoƙarin siyar ƙaramar motar fita unguwa bayan tasa ta amfaninsa dake gidan. Wannan haihuwa ta Tasleem ita ce ta yi sanadiyyar zuwan Jannat garin Kano da kyakkyawan albishir na dawowar da zasu yi Kano ita da mijinta da ma yaransu a dalilin sauyin aiki da ya samu ta zo wa Tasleem. Ta kuwa ji dadi don har tsalle ta yi ta rungumeta har sai da ta yi mata tsawa akan ta bi a hankali.  Futuha ma ranar da Jannat ta zo itama ranar ta ƙara zuwa na biyu, nan take ba su labarin gidan da Yakubu ya gina mata a sama kaɗan da su Tasleem. Ko kusa Tasleem ba ta yi wani murna ba sai murmushin yaƙe saboda baƙin cikin cigaban da Futuhar ke ta samu a rayuwa, ita kuwa Anti Jannat sosai ta ji dadi ta taya ta murna. *** Fadeel ya ƙurawa matashin da ya ci suna Joshua idanu, siriri kuma dogo baƙi wuluk. Kallo ɗaya za ka yi mishi ka san ya ƙare saboda tsabar shan sigari da kuma kayan maye. Sarƙa mai tambarin cross ce a wuyansa. Ya dubi Ridwan ya ce. "Wannan dai shi ne wanda ya yaɗa rumours akan su Humaira?" Ridwan ciki da tabbaci ya gyaɗa kai. "Shakka babu shi ne, komai na shaidun da muka samu daga abokansa ya nuna hakan kuma shi da  bakinsa ya gasƙata ya kuma ce sanya shi aka yi amma a yi hakuri." Mamaki ya ƙara kama Fadeel. "Amma kuma Yallaɓai alamunsa sun nuna tamkar bai ma jin Hausa gaba daya." Ƴar dariya Ridwan ya yi. "Haka kowa zai yi zato, amma shegen ko wani Bahaushen ba zai nuna masa Hausa ba. Hatta karatunsa a kwalejin ilimi na Kano abinda ya karanta kenan Hausa da English. Ko ba haka ba?" Ya watsa tambayar ga Joshua da ya yi tsuru da idanu yana jinsu. Jiki a sanyaye ya amsa. "Hakane Sir." Fadeel ya daure fuska. Ya ji tamksr ya shaƙe wuyan Joshua ya huta, ba iyaka haushinsa kawai yake ji ba akan abin da ya aikata aa, har ma da ɓatancin sunan da ya kusan haddasawa ya rasa Humaira gaba ɗaya a wurin Alhajinsa domin ya tabbatar masa idan zargin da ake yi ya tabbata to fa sai dai ya haƙura da Humaira. Ba shi kuma ya samu nutsuwa ba sai da shaidun da suka tabbatar da satar suka rinjayi masu ƙaryatawa. Wannan dalili kuma ya sanya Alhaji ya sauko akan  bakansa ya kuma ce nan da wata ɗaya za a yi aurensa da Humairar muddin dagaske iyayenta suke za su ba shi ita. Shima ya aminta da hakan, hakanan Abba ya san da zancen amma ko kadan bai sanar da wani a gidan ba. "Yanzun ka shirya faɗa mana wacce ta sanyaka aikata hakan?" Tambayar da Ridwan ya watsa masa kenan. Ya sunkuyar da kai kirjinsa na dukan tara tara amma gwara ya tona asirin ya huta don bai ga hanyar tsira a hannunsa ba. Miyau ya haɗiye maƙwat sannan ya ce. "Wata ce ta haɗa ni da wata mata mazauniyar ƙasan Egypt ta ce tana da wani zazzafan aiki wanda idan har nayi mata komai ya tafi yanda take so za ta yimin kyautar dubu dari biyu." Ridwan da Fadeel suka dubi juna sannan suka maida hankula gareshi. "Ya sunanta? Ka ba mu labari tiryan-tiryan don mu san abin da ya faru." Joshua ya kasa cewa komai sai zufa. "Look Joshua, ba wani abu muka ce zamu yi maka ba, muna son mu je root din matsalar ne don mu magance ta. Ka fito ka faɗamana su waye ke da hannu a ciki." Ya jinjina kai cikin aminta da zancen Ridwan ya soma magana. "Nidai ina tare da Babana ne a nan Kano, Mamana asalinta ƴar ƙasar Ghana ce. Toh tana aiki a Misra ne gidan wasu larabawa ne kamar ban dai sani ba. Toh matar ce ta ba wa Mamana aiki kan ta nemo mata wanda ta san zai iya yaɗa labarin ƙarya akan case din Ummita da Humaira kuma itama ba aikinta bane sanya ta aka yi ta nemo wanda zai yi a biyashi. Wannan dalili ne ya sa Mamana kirana ta yimin bayanin komai, nan da nan batare da dogon tunani ba na aminta zan karɓi aikin nan. Tun daga nan magana ta koma tsakanina da ainihin matar da zan yiwa aikin ba Madam din da Mama ke aiki a gidanta ba, ta instagram oage dinta muka soma magana na lura sabon buɗewa ne shafin nata, anan ne ta ke yimin bayani sosai na aikin har ma da ƙara jaddadamin wadannan kudaden da za ta bani. Toh shi ne na shirya labarin na aikamata ta lambar da ta turon na can Egypt ta ce da zarar na kammala na aikamata ta whatsapp, hakan kuwa aka yi nantura mata, sai da ta tabbatar komai ya yi kafin ta yimin umarnin samun lambar da ba a san ni da ita ba na yaɗa. Ta sanya na buɗe shafukan media sababbi da ba a sanni da su ba, har sai da labarin ya yaɗa yanda take so sannan ta bani umarnin rufe dukkan akawun din. Kuskuren da nayi sai na sanar da abokaina su huɗun nan da ku ke gani, suka goyamin baya amma suka ce sai na ba su kasonsu a kuɗin da za'a ban, akan kuɗin mun samu matsala da su. Sai kuma da aka sa kuɗin da ya ninka na aikin da aka bani cewar ana neman wanda ya aikata laifin shi ne suka ci amanata suka fallasa. Kun ji yanda abin ya kasance. Ita kuma matar tun bayan lamarin ta yi blocking dina bayan ta sallame ni. Mamana ta ce kada na ƙara tayar da zancen bisa umarnin Madam dinta, kuma kada na bari Babana ya sani. Sannan ni ko sunan wacce ta sanya ni bansani ba, Maman ba ta taɓa ambatonta da sunanta ba. Wannan shi ne abin da ya faru Yallaɓai. Ku gafarceni." Fadeel ya dunƙule hannunsa bai ce komai ba, Ridwan ya yi umarni aka mayar da Joshua ma'ajiyarsa sannan ya dubi Fadeel. "Ita kuwa wannan mene ne dalilinta ko ribarta na aikata hakan? Abu ɗaya dai da na fahimta, ko wace ce tana da relation da su biyun nan. Hakanan kawai ba za ta sanya a yaɗa rumours akan su ba." Fadeel ya jinjina kai, tabbas hakane amma kuma shi a iya tunaninsa kamar dai ba su da wani dangi a ƙetare. "Hakane Yallaɓai. Yanzu mene ne abin yi?" "Abin yi ɗaya zuwa biyu, zamu karɓi lambar ita Matar da ma Mamansa idan ta kama. Idan binciken zai kaimu har can gidan su Humairar toh sai a je." "Shikenan hakan yayi. Zan yi waya da Abbansu na sanar da shi komai." "Ok ba damuwa. Nima nan zamu yi kokarinmu." Daga haka suka yi sallama Fadeel ya bar ofishin. *** Ranar sunan ɗiyar Tasleem yarinya ta ci sunan mahaifiyar Hamza wato Asma'u suke kiranta da Husna. Sunan da kusan rigima aka yi tsakanin Tasleem da Hamza don ta rantse sai dai ya sanya sunan nata uwar shi kuwa ya rantse ba zai fasa sanya Husna ba. Hakanan aka ci suna idanun Mai jego duk a kumbure saboda kukan baƙin cikin da ta yi, uwa uba sai ga tsohuwar budurwar Hamzan kuma yar uwarsa ta kawo mata kayan barka. Ta ci uban kyau da rantsetsan leshinta ruwan ƙwai an mata adon stones. Black beauty da ita fuskarnan ta sha make up sai ƙamshi take yi. Bisa shawarar Jannat ne Tasleem ta danne ɓacin ranta sai yaƙe. Tana ji dangin Hamzan na tsokanar budurwa da sunan Amarya amarya amma sam ba su kawo komai ba. Jannat na dariya ta ce. "Toh kin gani ma ashe ta kusa aure kike wani tada hankalinki." Sai a lokacin itama Tasleeem din ta ɗan saki ranta. Gwara ta tattara ta yi auren ko ta huta da jarabar bibiyar mijinta da take yi. Futuha kuwa a tsaisaye ta leƙa sunan ta kuma wuce da Humaira da Raihana don su taimaka mata da tattara kaya saboda kaurar da zata yi sai wani rawar kai da ƙafa take yi. Hakanan suka tattara sannan ta ce su yi gaba a mota a kai kayan tare da su don tuni an kai dukkan kayan katakonta an kuma jera, sai na sanyawarta a jiki suka rage. Wannan duk budurin da ake yi ba ta ga gida ba. Humaira da Raihana suka bi umarninta zuwa gidan, yayinda ita kuwa ta wuce gyaran gashi don ta ce gwara mutan unguwar su ganta tsaf ba raini don Yakubu ya ce mata unguwar ƴan gayu ne. *** Ummita zaune ita ɗaya a falo tana biyawa su Muhsin karatun hadda da aka yi musu a islamiyya, haka Mubarak ya shigo ya risƙeta. Kallo ɗaya kawai ta yi mishi ta maida kanta ƙasa tana gaida shi don a yanzun kwata kwata ba ta kaunar ganinsa ba don komai ba sai irin kallon da yake bin ta da shi da kuma manufarsa na soyayyar da yake nuna mata, koda bai furta ba alamominsa sun nuna. Madadin ya wuce sashin Anna wurin Mami kamar yanda Waleed ya sanar mishi cewa tana can, kawai sai ya ɓige da zama a falon yana duban Ummita cike da wani irin kauna mai tsafta ga kuma tausayi. "Beauty." Ko kusa ba ta gane da ita yake ba sai bayan ya ƙara maimaitawa. Ta ɗago idanunta fuska ba walwala ta dube shi. Ya yi mata sanyayyar murmushinsa, kamanninsa da Abbansa ya ƙara fitowa. "Gobe fa zan tafi Camp, baki da labari?" Ta girgiza kai tana maida hankalinta kan littafi mai tsarki. "Ban sani ba. Allah ya kaika lafiya ya sa a kammala lafiya." Ya lumshe idanunsa ya bude da murmushi saman fuskarsa. "Amin beauty, nagode. Sai dai zan yi kewarki." Fadin hakan da ya yi hatta Waleed sai da ya dube shi, nan da nan ya daure fuska ya ce su je su cewa Mami ya zo. Suka kuwa mike har su na rige-rige suka bar falon. Ita kuwa Ummita ta kasa cewa komai sai faduwar gaba fat fat. "Sun watse sun barki ke ɗaya ko?" Gyaɗa kai ta yi. "Beauty ba magana?" Ta dago ta dube shi da idanunta wadanda suka cicciko da hawaye. Ba ta son har abada abin da zai tuna nata da Sahabi wanda tuni aka ɗaura aurensa da yar uwarsa. "Yaya Mubarak, don Allah ka kirani da Ummita. Bana jin dadin sunan da ka sauyamin." Ya taso ya ɗan yi durƙuso a gabanta. "Ba zan iya dainawa ba Beauty. Sai dai zan yi kokarin danne abin da ke zuciyata har Allah ya rabaki da cikin jikinki lafiya. Bana son na furta yanzu amma yana nema ya rinjaye ni. Kiyi hakuri da ni zan ƙara danne zuciyata har zuwa lokacin da ya kamata komai ya bayyana a zahiri. I am so sorry." Wannan karon da hawaye saman fuskarta take dubansa cike da tausayinsa. Bai san masifar da yake shirin jefa rayuwarsa ciki ba. Ban da abin Mubarak me zai yi da ita, Ummitan da sunanta ya gama ɓaci a idanun jama'a? "Mubarak!" Tsawar da Mami ta dakamasa ya sanya gaba daya suka dube ta, ranta a tsananin ɓace take dubansu. Ta ɗan jima kaɗan da shigowa falon amma sam ba su lura ba. Kaf kalaman Mubarak din na karshe a kan kunnuwanta ya yi su. Ummita ta sha jinin jikinta da irin duban da Mamin ke watsa musu.*LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* 09034973645 Duk iyaka kokarin Mami ta kasa danne zuciyarta saboda abu ɗayannan ba za ta iya ɗaukarsa ba, haɗa zuri'a da ɗiyar Jamila wato Ummita. Mubarak ya miƙe yana dubanta hakanan Ummita tun duban farko sai ta yi ƙasa da kanta kirjinta na dukan uku uku don gani tayi ma kamar Mamin cetonta ta yi daga kalaman Mubarak wadanda suke shiga kai tsaye cikin zuciyarta tamkar mashi. Ko kusa ba ta kawo komai ba face kyakkyawan zato ga Mamin. "Mene ne haka ne? Kar ka kara yimin wannan sakarcin. Ka riƙe abin da ke ranka kuma ka kauda shi don ba zai taɓa yuwuwa ba." Mamaki ya cika Mubarak, itama Ummita ta ɗan ji maganar a ranta amma kuma ta basar. To me zai dame ta ma tunda dama ita ba soyayya ce gabanta ba? Ita ta fi kaunar ma ta mutu yayin haihuwa ko ta samu shahada ta huta da baƙƙan cikin duniyarta. Mubarak har ya buɗe baki zai ƙara magana Mami ta dakatar da shi ta hanyar ɗaga mishi hannu. "Kar ka cemin komai. Fice harkar gabanka, kai da kake da tafiya a gaba mene ne za ka tsaya kana ɓatawa kanka lokaci kana ɓatawa yarinya itama?" "Ma.." "Nace maka bana son jin uffan daga gareka ko? Don haka ficemin a nan." Ya jinjina kai kawai bayan ya kara duban Ummita da aka yi sa'a itama ta ɗago kai suka haɗa idanu ta mayar, sannan ya fice yana ƙara ƙudurtawa a ƙasan ransa in sha Allahu mallakinsa ce muddin dai ta amince da aurensa. Bayan fitarsa Mamin ta karaso ta zauna sosai a saman kujera har lokacin fuskarta ba walwala ta soma magana. "Ke yanzu idan ma wani yace maki ki yi soyayya sai ki dube shi? Yanzu ai babu abin da ya fi maki alheri face ki kula da kanki da abin da ke jikinki har Allah ya rabaki da shi lafiya. Ummita na fi kaunar farin cikinki sama da na Mubarak, yau kika biyewa yaron nan sai ya kaiki ya baro. Ni na haife shi na kuma san ra'ayinsa da ma ɗabi'unsa, ba shi da ra'ayin auren bazawa.." Sai kuma ta yi ɗif jin hasalalliyar zuciyarta za ta sa ta yi katoɓara. Ummita kuwa ta fahimci tsaf abin da Mamin ke ƙoƙarin faɗi, sai ta shiga kokwanto akan anya dagaske Mamin da kanta ke wannan batun ko kuwa dai, don haka ta ɗago ta dube ta ita kuma ta kauda kai karshe ma  ta miƙe ta bar falon.  Shakka babu ita ɗin ce da kanta, maganar ta tsayawa Ummita a rai. Bazawara fa take kokarin kiranta? Mami da kanta? Sai kawai ta ji wasu sabbin hawayen sun kwaranyo. Zuciyarta na ce mata eh ga kuma zahiri na idanunta na kara tabbatarmata da haka ɗin ne amma wani ɓangaren na zuciyar na kokarin kare Mamin da tunanin ajizanci na kowane ɗan adam, mai yiwuwa itama suɓutar baki ne saboda ɓacin rai ba hakan ta so faɗi ba. Wannan dalilin ya sanya ta share hawayenta ta tattara kur'anan su Muhsin ta maida kowanne a jakarsa sannan ta kwashi jakunkuna zuwa ɗakinsu. *** Ƙaramin gida ne wanda ya ji fenti daga waje ya sha kyau, ciki kuwa kana shiga, babu batun farfajiyar gidan saboda wani tsukakken wuri ne sai famfo a gefe ga bishiyu ƙananu an mishi ado da su. Daga ciki kuwa kai tsaye falo za ka faɗa, ba shi da girman da zai cinye manyan kujerun Futuha sai raba su aka yi wasu aka kai safayar ɗaki falle guda dake  a ƴar tsakar gidan. Ɗaki ɗaya ne a ciki sai store da kicin ɗinta ƙarami wanda hatta da freezer dinta bai shiga ba sai a zagayen baya gefen kicin aka sanya shi. Hakanan babu matsugunin kayayyaki da yawa na wuta na amfani kicin dole hakanan suka cuccusa su da taimakon ma'aikata tsohon gidan da suka kawo kaya. Gado dai ya shiga ɗaki amma fa ya cinye kusan rabin ɗakin. Raihana da Humaira sai kallon kallo da mamaki, ita dai Humaira ba ta tanka ba sai Raihanan da ke ta jajen lamarin da hango rikicin da zai faru idan Futuha ta ga gidan da take ta yiwa rawar ƙafa har Tiktok ta yi na bidiyo tana a tayata da addua za ta tare a sabon gidan da mijinta ya gina mata, har da alƙawarin za ta yiwa followers dinta bidiyon gida kamar yanda suka buƙata su na ɗokin su gani. Ana kammala jeran komai wadanda ba su samu wuri ba aka sanya su a store, bayan fitar masu kawo kaya Humaira ta dubi Raihana. "Nifa gaskiya binsu zan yi a sauke ni a gida ba zan zauna har ta zo ba." Ganin haka wuf Raihana ta dauki mayafinta. "Balle kuma ni, ta ina zan zauna a yi borin nan a gabana? Wallahi ba da ni ba. Mu ba su muƙulli idan ya so su yi mata waya ta faɗi inda za su kai mata ko kuma ai za ta koma tsohon gidan ta yiwa Uwargidanta sallama, kinga sai ta karɓa a can." Murmushi Humaira ta yi, har ta tausayawa Futuha ganin yanda ta ke rawar ƙafar shiga gidan da a yanzu ko na Tasleem ya fi shi tsari da wadatuwa. Tana ji koda suka kama hanyar tafiya gida bayan sun bada muƙulli sai da ta ƙara kiran Raihana ta gama masifar dalilin da yasa ba su jirata a gidan ba salon ace ta shiga babu ɗan rakiya kafin ta hau tambayar yanda girman parking space din gidan yake wai ko zai iya cin mota biyu. Raihana ta amsa da ita dai idan ta dawo ta shiga ta ganewa idanunta daga hakanta kashe wayar baki daya. Duk yanda Humaira ta kai ga son riƙe dariyarta sai da ta kufce mata, Raihana ta taya ta. "Allah kuwa ta ban tausayi kuma ta ban dariya idan na tuna yanda take ta wani jijji da kai da ɗora bidiyo wai a taya ta murnar tariya a sabon gidanta." Humaira cikin faɗaɗɗan murmushi ta amsa. "Kin ga illar son a sanin da ta ke yi a idanun duniya kenan, yanzu da ace asirinta a rufe yake ba ta sanar da kowa ba shikenan babu mai ji balle gani. Ba ki ji ta ce washegari za ta yi walimar tariya ba har fa abinci kina dai ji a gabanmu ta ba da odarsa tana cewa akwai sabuwar mai abincin da ake yayinta a bukukuwa." Takaici sosai ya kama Raihana. "Ai shikenan, sai ta shirya naɗe tabarmar kunya da hauka." Haka suka yi ta hirarsu har suka ɓullo gidan Tasleem inda anan za su wuce tare da Jannat wacce ta maida gidan wajen yininta. Wannan karon ba ta zo da yaranta ba saboda makaranta ta bar su can hannun kanwar babansu dake aure a Misra. Gargadin Abba ne bai aminta su kara shiga ɗan sahu ba idan har ba wasu kwakkwaran dalilai ba ne da ya yi zafin da sai an nema an shiga. Wannan ya sa suka yanke hakuri da zaman jiran Jannat ta gama ta wuce da su a motarta gudun kar su je Abban ya yi musu faɗa. Su kansu tsoron shigar suke yi yanzu musamman Humaira. Sun zo dab da gidan Tasleem har su na hangowa ne wayar Humaira ta dauki ƙara. "Idan ita ce please ki ce mata muna abin hawa mun ma yi nisa." Humaira dai murmushi take don ita abin ma dariya yake  ba ta, gyaɗawa Raihana kai kawai ta yi kafin ta fiddo wayar a jaka ta duba. Fadeel ne. Madadin ɓacin rai ko baƙin ciki da haushi, sai ta ji ranta ya yi wani irin sanyin da ba ta yi zatonsa ba. Raihana da ta leƙa ta ga waye ta kuma ga yanayin dake kwance a fuskar Humaira sai ta ji tamkar da daka tsalle tsabar farin ciki, amma sai ta ƙarawa murnar armashi da ambaton sunan Allah gami da yin hamdala. "To sai ya katse? Ki ɗauka mana please." Ta kuwa amsa sannan ta kara a kunnenta da sallama. Fadeel daga ɓarinsa ya amsa. Ji ta yi muryarsa na sanyamata wata irin nutsuwa da sanyin ruhi, ta kasa hasko meke shirin faruwa da ita har sai da maganarsa ta katse tunaninta. "Boddona, nayi kewarki sosai. Kin ji bawan Allahn nan shiru a waya kwanaki biyu amma ba ki nemi ki san ko lafiya ba ko?" Sunan Boddona ya sanya ta dan lumshe idanu ta buɗe su da wani ɗan guntun murmushi a saman leɓɓanta, Raihana dai kallon ikon Allah kawai take yi tana washe bakin jin dadi na wannan sauyi da aka soma samu daga Humaira. "Ka yi hakuri, nima ban samu nutsuwar zama ba ne balle har na kira na ji ko lafiya. Fatan komai lafiya? Ya mutanen gidan ya wajen Maman Husna?" Sai da Fadeel ya yi wani irin dauke wutan da har ta yi tsammanin yankewa wayar ta yi, Raihana ma mutuwar tsaye ta yi domin cak ta tsaya daga tafiyar da suke yi baki a buɗe sai kuma ta sa hannu ta rufe. Ganin haka Humaira ta fidda wayar a kunnenta ta kalla, sannan ta ɗan juya kadan tana kallon Raihana. Wayar ta maida kunnenta tana murmushin yanayin mamakin fuskar Raihana ta kara magana. "Ba ka ji ba?" Wata doguwar ajiyar zuciya ta ji ya sauke da ƙararta sai da ta ji a kunnenta. "I am with you Boddo, na ji komai. Dukkansu lafiya kalau, nagode sosai da wannan." Ta yi ɗan murmushi ba ta ce uffan ba har suka tsaya cak a ƙofar gidan Tasleem, Raihana sai ba ta kwankwasa ba tana jiran su kammala wayar bayan ta yi mata raɗa akan ta taimaka ta sa a loudspeaker don ta ji. Ba musu Humaira ta yi hakan. "Kin yimin iznin shigowa yau? Kiyi hakuri, ina kewarki a idanuna. Na jure Boddo, amma hakurina na neman gazawa da aski ya zo gaban goshi. Please kin min izni na shigo yau mu gaisa koda na mintuna biyar ne?" Ta ji wani tausayinsa da ba ta taɓa tsintar kanta a ciki ba ya kama ta. Meyasa wai ta ke ba shi wahala har haka? Me ya taɓa yi mata don ya baƙanta ranta? Ta ba kanta da kuma zuciyarta da amsar a'a, wato babu shi. Ta ɗaga kai ta dubi Raihana, da hannu yake roƙonta akan ta ba shi damar. Lumshe idanu ta yi sannan ta amsa. "Ba damuwa. Ka shigo ka ɗebi lokacin da ya yi maka sannan ka tafi." Nan ma Fadeel sai da ya ɗauke wuta har ya ba su dariya suka gimtse. "Kamar a mafarki. Alhamdulillah. Ki yi hakuri da shirun da nake yi Boddo, in sha Allah ana yin Magrib za ki gan ni. Nagode." "Nima na gode. Allah ya kawo ka lafiya. Sai anjima." "Ba ki ji ba." "Me?" "Ba zan gaji da ce maki ina sonki ba." Yana fadin haka ya katse kiran. Kalaman sun shige ta kwarai, ta ji ta tamkar an yaye mata kaso tamanin na damuwarta. Ba ta sani ba ko tana son Fadeel ba, amma tana matuƙar tausayinsa idan ma tana tunano wulakancin da ta yi mishi a rayuwa da ma wadanda ba su ji ba su gani ba sai ta ji tamkar ta tsire kanta don ɓacin rai. A kwanakin nan dai ta sani tana nadamar abubuwa da dama data aikata a baya, babban tunanin dake cin zuciyarta bai wuce na dalilin aikatawar ba amma ta kasa tuna koda guda ɗaya. Dariya da rungumar da Raihana ta kai mata ne ya farkar da ita daga zurfin tunanin da ta faɗa. "Son so yar uwata. Allah ya nunamana aurenku da Yaya Fadeel. Ya sauki yar uwarmu lafiya ya ba ta dukkan farin ciki itama." Ta kasa amsawa sai dan murmushi kawai, tuna Ummita duk sai jikinta ya yi sanyi a kasan ranta ta ce amin din. "Malama mu shiga ciki kar mu zama abin kallo." Tana fadin haka ta ture ta ta yi gaba tana kwankwasa ƙofar itama ta bi bayanta tana dariya. Koda suka shiga da nishaɗinsu, tana ji Jannat na hirar ɓatancin sunan da aka yi musu amma ta yi banza da ita musamman ganin har da rainin hankali a zancen don tana yi tana dariya har da cewa wai wa ya sani ma ko dagaske ne tunda abu a duhu babu wanda ya san gaskiya sai su biyun da abin ya faru da wadanda aka kira da suna kidnappers din. Duk yanda ta shiga da walwala sai da Jannat ta rushe wannan farin cikin, shiyasa ta dinga kaucewa haduwarsu tun da aka ce ta zo amma yau gashinan zamansu inuwa guda ya janyo tana gasa mata zantuka marasa kan gado. Haka ta kai zuciyarta nesa ta danne. Tana ji su na hirar gidan Futuha inda Raihana ke ta labarta musu yanayin gidan, Tasleem me za ta yi ban da dariya? Ta dinga kyakyacewa son ranta har sai da Jannat ta yi mata magana. Raihana kuwa duk yanda ta kai da yiwa Futuha dariyar gidan sai da ta ji haushin farin cikin da Tasleem ta hau yi har da ambaton Allah ya ƙara. Jannat ba ita ta tashi tafiya ba sai dab da magriba, Humaira da Raihana har suka gaji ga tunanin Fadeel da zai zo bayan Magriba. Tuƙin ma yinsa ta dinga yi da gadara da yanga kamar ba ta so sai ka ce ta san da zuwan Fadeel din amma ko kusa ba su sanar mata ba. Don kanta kuma daga baya ta ware hannun sitiyari ta shiga gudu har suka isa gidan. A gurguje Raihana ta sanya Humaira shiryawa. Ummita na daga kwance tana kallonsu sai murmushi kaɗan a fatar bakinta. Inda ta ga da buƙatar gyara za ta yi magana. Duk da halin da take ciki ta yi farin ciki kwarai da wannan sauyi na Humaira akan al'amarin Fadeel. Humaira ta kammala shiri cikin wani rantsetsan yadinta mai adon maroon da yellow ta yi kyau sosai musamman da ta yafa mayafi yellow sai tashin ƙamshi take yi. Raihana ta so ta yi mata kwalliya amma ta nuna ba ta ra'ayi, ita duk kaffa kaffar da take yi kada ta motsawa Ummita wani lamarin akan Sahabi, ba ta san cewa Ummita kwarai take jin dadin yanda ta sauya ba. "Masha Allah kin yi kyau sosai." Fadin Ummita tana dubanta. Ta maida mata martanin murmushin amma ba ta ce uffan ba can kuma ta dubi Raihana. "Kinga ban sanar da Mami ba, na rasa ta yanda zan faɗamata." Cikin basarwa Raihana ta ce. "Kar ki wani damu, tana wajen Abba, ke idan ma ta tambaya zan fadamata." "Toh." Shi ne kawai amsar Humaira ta ba. *** Wannan karon madadin ta gan shi tsaye a farfajiyar gidan, sai ta same shi a ɗakin saukar baƙi na Abba. Ashe Mubarak ne ya kai shi can, shi suka yi karo ya sanar mata inda yake. A kunyace ta sunkuyar da kai ta nufi ɗakin kai tsaye. Da sallamarta ta sanya kai ciki bayan ya amsa. Suka ɗan dubi juna ta kauda kanta, ya sha adonsa cikin yadinsa mai tsada fari ƙal ga kuma hula ya ɗora wanda ya yi matuƙar hawa da kayansa. Kallonta kawai yake yi ba ƙaramin kyau ta yi mishi ba. Ta ƙaraso ta nemi wuri ta zauna can nesa da shi kaɗan tana gaishe shi. Ya amsa mata zuciyarsa tamkar ƙanƙara. Sai kuma ya rasa ta inda zai fara, sai ya ji kamar an ɗaure mishi bakin saboda tsabar shauƙi, ita kuwa ta baza kunnuwanta don son ta ji me zai ce. Can ta tsinkayi muryarsa a tausashe. "Kin yi kyau." Ta kasa cewa komai sai murmushin da ta ɗan yi. Jin lamarin ta ke banbarakwai, wai ita ce ke yin zance. Abin dai kamar a mafarki. "Boddo." Ya kira sunan da take matukar jin dadinsa amma koda wasa ba ta taɓa gwada mishi ba. Sai da ya ƙara maimaicin kira kafin ta amsa a hankali. Fadeel ya yi hamdala a ransa, tabbas babu wani abu mai girman da ya fi ƙarfin addu'a. Komai idan ka sanya Allah ciki kuma ka dage da addu'a to fa zai zo ya zama tarihi. Hakan kuma yake fata, wannan ƙiyayyar ta Humaira gareshi ta koma tamkar ba ta taɓa yinta ba. "Nasan za ki ce Fadeel ya fiye naci da takura. Kiyi hakuri, haka Allah ya yi ni, yadda ban iya ƙin abu ba haka nake idan na so ba, ba na mishi son da nake jin zan iya haƙura da shi yau, gobe ko jibi. Kina daga cikin abu mafi girma da tsada da na taɓa samu a rayuwa, a zatonki zan bari ki suɓucemin?" Ta kasa tankawa, jikinta ya yi la'asar, sai ta ji ya yi matuƙar ba ta tausayi kwarai har ta ɗago idanu kaɗan ta dube shi, kwayoyin idanunsu suka sarƙe, ya harɗe tafukan hannuwansa guri guda ya tallafa haɓansa gami da ɗan karkata kai kawai yana dubanta. Ta janye ƙwayoyin idanunta gami da sadda kai tana wasa da zoben azurfar yatsarta. So ta ke ta ce ka yi hakuri Fadeel, na sani ban kyautata maka ba ka yafemin. Amma ta ji ta kasa, da wane idanun ma za ta dube shi har ta iya bayan shafi-shafin rashin mutuncin da ta sauke a kansa. "Aa Boddona, in sha Allahu sai mun kasance a inuwar aure. Sai kin zama mallakina nan ma ba da jimawa ba." Ya ƙarashe zancen da murya ƙasa-ƙasa. Abin mamaki idanunsa a saman fuskarta, ko kallonsa ba ta yi ba balle ya tsammaci kallon hararar da ya riga ya yi sabo a shi. Wannan sauyin da take yi sai ya ji zuciyarsa n kasa ɗauka, ba kuma wai rashin aminci da shi ba. Ko kusa, sai dai kawai ya kasa sakin jiki yana ganin kamar na ɗan lokaci ne. Duk da haka yana kokarin tunasar da kansa cewa addu'a ce ta kai su ga wannan munzalin ba kuma ya tunanin akwai abin da zai sauke su a kanta. Ya miƙe ya ɗan matso kujerar da take kai ya zauna, tana can ƙarshe kujerar kasancewar mai zaman mutum uku ce, shi kuwa yana gefe ya ba da tazara tsakaninsu. Magana mai muhimmancin da ya kasa sanar da ita ne ya ke ganin ya dace ta sani yanzu. Kirjinsa na bugu saboda fargabar kada ta tada bori kan tsarin bai mata ba. Amma da ya ambaci sunan Allah sai ya samu ƙwarin gwuiwa don haka ya karya bille ya soma magana. "Humaira, iyayenmu sun yi magana sun kuma tsayar da ranar aurenmu." Ta ji tsiƙar jikinta ya tashi, ita da aure? Babu wani yanayi da ta ji da ya wuce na sanyin jiki kamar wacce aka yi wa duka. Har wani zufa ne ya yankomata, sai ta shiga maimaita sunan Allah a ƙasan ranta. Shirunta ya haifarwa da Fadeel wata irin fargaba har sai da ya ji inama bai ce uffan a kai ba. Har ya fidda ran za ta tanka sai ta ƙaryata tunaninsa ta hanyar magana tana dubansa fuskarta na nuni da damuwa. "Amma ta ya ya zan yi aure na bar Ummita cikin wannan halin?" Ya sauke ajiyar zuciya jin abin da ta ce, cikin ƙarfafa gwuiwa ya ce. "Kar ki damu Boddo, idan har wata ɗayan da su Abba suka sanya ya cika, matuƙar aka ɗaura babu wanda zai takuraki da zancen tariya har sai lokacin da kika aminta don kanki. Hakan ya yi maki?" Ga mamakinsa sai ta gyaɗa kai da ɗan murmushi kaɗan a fatar bakinta. Ai sai ya ji inama yana da damar haɗa jikinsa da nata. Hakan ma da ta aminta da aurennasa ya yi mishi sosai, muddin dai ta zama mallakinsa to sauran duka mai sauki ne. Hakan ya ayyana a ransa. Bai ja ta da hira ba gudun kada kuma a zancen ta yi wani tunanin ta sauya ra'ayi don haka ya zaɓi su yi sallama a wannan gaɓar, yana da tambayoyin da zai so ace ya yi mata na dalilin ƙin shigar ta makaranta ta zaɓi girki da ma dai son jin duk wani abu da ya shafe ta amma ba ya son kwaɓarsa ta yi ruwa sai ya haɗiye kwaɗayinsa ta hanyar yi mata sallama ya miƙe, itama ta miƙe suka fito tare ta ja ƙofar ta rufe. Hannuwansa cikin aljihu ya ke dubanta kamar ya haɗiye. "Sai mun yi waya. A gaidamin yan uwana." Ta gyada kai. Har ta soma tafiya sai ta juyo, yana tsaye cak kawai yana kallonta da shanyayyun idanunsa so na fisgarsa. Ta ɗan kauda kai daga dubansa ta ce. "A gaidamin su Baba, idan kun yi waya da Maman Husna ace ina gaida ta." "Ko na turo maki lambarta? Saƙonnin sun min yawa kada na manta." Ta ɗan murmusa. "Shikenan sai ka turo." Ta juya za ta tafi ya dakatar da ita. "Boddo." Tsayawa ta yi ta juyo, murmushinsa ya yi har gefen kumatunsa na lotsawa. "Ina ji da ke." Ta yi saurin juyawa ta nufi ciki, sai da ya ga shigewarta kafin ya fice zuwa inda ya adana motarsa yana shafar sumar kansa duniyar na mishi dadi. *** Mami kuwa ta cika ta yi fam, abu biyu ne suka haɗe mata, ga hotunan gidan da Futuha ta aikomata da kuma wayar da suka yi tana rusa uban ihun kuka tana cewa gida za ta taho yanzun a daren, ga kuma labarin auren Humaira da Fadeel da take ji a wurin Abba sai aka yi katari a ranar kuma Humaira ta fita hira wajensa. Wannan ranar ta fi kowacce baƙin ciki a wajenta. Suna falo zaune har Anna da ta fito saboda tashin hankalin akurkin gidan da ta ga Futuha ta koma da kuma batun yajin da ta dako har ana batun tana hanyar dawowa gida, sai yare suke bugawa a falon Jannat tana yi itama Annar na yi, Raihana da su Mubarak dai sai tausarsu suke yi inda Mubarak ya dage akan lallai idan Futuha ta tako yau sai ta juya ta koma gidanta acewarsa ba za ta tayarwa Abba hankali ba ga shi yana fama da hawan jini. Anna kuwa ta dage lallai sai Futuha ta dawo gidan tunda ba haka aka yi da Yakubun ba, a wannan yanayin Humaira ta shigo falon fuskarta dauke da murmushi sai baza uban ƙamshi take yi mai sanyi. Ganin yanayin mutan gida sai da ta ji dam saboda ta yi zaton ko wani abun ne ya kuma faruwa. Idanunsu a kanta, ga Anna da Jannat harara ne, Mami kuwa ba za ka tantance ba sai dai fa fuskar a haɗe take tamau. Humaira ta dake ta ƙarasa ta gaida Anna. Ba ta ko kalle ta ba balle ta amsa, ganin haka ta mike za ta nufi ɗaki Mami ta yi mata tsawar da kowa a falon sai da ya dube ta. "Ke! Da iznin uban wa ki ka fita wajen Fadeel?!!!"Kamar an ɗinke mata baki sai ta kasa cewa uffan yayinda Raihana ta yi caraf ta amsa. "Mami na fadamaki fa kuma Abba yace Yaya Fadeel ya zama ɗan gida tunda zai auri ƴar gida. Kiyi hakuri please ki daina jin haushinsa yanzu tunda har Sis Tasleem ma ta yi aurenta ta manta da shi." Wani kallon banza Mamin ta watsamata, Anna da Jannat dai idaunsu kawai suka zuba ga Mamin saboda sun kasa yarda ita ce, a zuƙatansu basu taɓa jin sanyi cikinsa ba kamar yanzun musamman Anna da take ganin fuskar tsohuwar Mamin da ta sani a Agadez a na wannan. Mami kuwa kamar ta yi shiru sai ta yi tunanin watakila shirun nata ya tona ainahin abin da ke ranta musamman ma ga su Jannat ga Mubarak da suka zubamata idanu cikin hankalta. Don haka ta sauke ajiyar zuciya. "Shikenan wuce ki shiga ciki ki sauya kaya. Anjima zamu yi magana." Humaira wacce idanunta suka cicciko da hawaye ta gyaɗa kai gami da miƙewa ta bar falon tana ji kamar an muzanta ta. Haka ta koma ɗakinsu cikin mutuwar jiki. "Ke da Mami ko?" Ummita ta wurga mata tambayar da ya sanya ta dubanta, tana daga zaune saman darduma bayan ta idar da salatin Annabi s.a.w. Kaf abin da ya faru tana ji daga inda take. Ɗan murmushin yaƙe ta yi mata. "Ban san kuskuren dake cikin nagartar Fadeel ba, watakila kuma sai yanzu da idanuna suka soma ganinsa da ƙima wata silar za ta raba mu ta nisanta mu da juna idan har hakan zai faranta ran Mami." Girgiza kai Ummita ta yi. "Ban ce ki bijirewa dukkan wani umarni na Mami ba, amma ki sani, ba Mami ce kaɗai me iko a kanmu ba. Abba shi ne mafi ƙarfin ikon zartarwa. Idan har Allah ya ƙaddara aure tsakaninku babu wani mahaluƙi da zai iya dakatar da faruwar hakan. Mami hujjarta ba karɓaɓɓiya ba ce, akan wane dalili don bai auri wata ba wacce dama tun farkon fari ba dominta ya ƙulla zumunta da gidannan ba, ace za a haramtawa wacce ba ta ji ba kuma ba ta gani ba abin da Allah bai haranta ma ta ba? Anan dai na raba fahimta da Mami." Humaira ta sauke nannauyan ajiyar zuciya har a lokacin ba ta dauke idanu cikin na Ummita ba ta ce. "Bana son saƙe-saƙen da zuciyata ta soma yimin akan Mami, iyakar ƙarfina nake ƙoƙarin ƙaryata tunanina Ummita sai dai hakan na nema ya faskara." Ɗan murmushi mai ciwo Ummita ta yi mata. "Na fahimceki, ba kuma na son saka Mami a jerin masu son zuciya idan nayi haka kamar ban mata adalci ba duba da yanayin riƙon da ta yi mana na nuna fifiko akan yaranta na ciki. Sai dai a wannan gaɓar bana goyon bayan hakan, ki toshe kunnuwanki Humaira. Fadeel mutumin kirki ne, a duniya ban da soyayyar iyayenki, zan iya rantse maki Fadeel ne masoyinki na gaske bayansu don ko mu ba lallai mu nuna mishi sonki ba. Ya sadaukar da lokacinsa duk a kanki, shekara da kusan watanni ya jure dukkan wulakanci da baƙaƙen maganganun da sauran mazan da suke sonki da aure suka kasa jura suka kama hanyar gabansu, Fadeel ya cancanci ki aureshi. Ba fata nake maki ba amma muddin kika zama mai juya baya a gareshi da ƙin yarda da shi, wallahi Humaira haƙƙinsa ba zai bar ki ba." Daidai wannan gaɓar hawaye suka wanke fuskar Humaira, ta sani gaskiya ɗaya ita ce Ummita ta faɗamata. Har haushin kanta take ji idan ta tuna yanda ya dinga ya bibiyarta a bainar jama'a tana yanƙwana shi. Ya jure dukkan wannan ya kuma sadaukar da lokacinsa don kawai ya ga ta sauko don kanta ta aminta da shi, ita kuwa me zai sa ta butulce masa? Daga haka Ummita ba ta ƙara ce mata uffan ba, ai ruwa cikin cokali ya ishi mai hankali, don haka ta bar ta da tunani iri-iri a ƙasan ranta. *** A falon kuwa da fitar Humaira sai Jannat ta kwashe da dariya. "Mamin yara kenan, yau kuma marainiyar Allahn ƴar gaban goshinki da ba ta laifi ita kike yiwa wannan ɗibar albarkar?" Mami ba ta ce uffan ba don har lokacin zuciyarta a zafafe take musamman da Jannat ta alaƙanta Humaira da sunan ƴar gaban goshinta. Wannan ko a mafarki ba ta hangen haka. "Mami, don Allah ki bar Humaira da Fadeel haka, idan har yanda Raihana ta ce sanadiyyar Tasleem ne. Yanzu Tasleem igiyoyi uku ne a kanta har da ƙaruwar Baby da ta samu. Ni ban san dalilinki na hana ta kula matashi mai kirkinsa ba." Waɗannan zantukan su na fitowa kai tsaye daga bakin Mubarak, kafin ta tattaro amsar da za ta ba shi sai ga Futuha ta bankaɗo labulen falon ta shigo a haukace tana wani irin kuka da sheshsheƙa, ta ci uban ado an shafe fuska da Foundation amma sanadin kukan da ta sha duk sai ta koma kamar wata aljana. Ganin Mubarak a zaune bai sa ta bar ihu da kukan da ta fasa ba, gaba daya suka miƙe ita kuwa kai tsaye jikin Antinta Jannat ta faɗa gami da ƙara sautin kuka da ihu. Wannan ya yi sanadin shigowar Abba falon don tun ɗazun yake tsinkayar muryoyi a sama amma na yanzu ya fi duk na baya shiga kunnuwansa don haka ya shigo falon a hargitse. Ganinsa sai Anna ta ɗan ja jiki ta koma ladabin ƙarya kamar yanda ta saba yi a gabansa. Tsawa ya dakawa Futuha ba shiri ta kame bakinta ta yi shiru, Mami sam ba ta so zuwan Abban ba don zai iya lalata shirinta ya sa Futuha komawa dakin mijinta a yau. Ya kuwa jefowa Mamin tambayar abin da ke faruwa idanunsa ma ko kan Anna bai kai ba saboda tsoro da fargabar da ihun Futuha ya haifar masa. Mami ta ɗan gyara murya ta ce. "Ke Futuha sai kiyi masa bayani, waƙa a bakin mai ita ta fi dadi ai." Futuha ta dubi Mami sannan ta maida kai ga Abba amma ta kasa cewa komai tsabar fargaba. Jannat ta yi kundunbala ta soma magana muryarta dauke da salon makirci, nan ta labartawa Abban ƙarya da gaskiya akan ginin da Yakubu ya yiwa Futibar ya maida ta. Abba ya tamke fuska tamau, Jannat ba ta taɓa ganin ya dube ta da tsantsar ɓacin rai da rashin walwala ba sai a ranar. "Shi ne me?" Tambayar ta sa Jannat kasa cewa uffan, sai Mubarak ne ya yi caraf ya amsawa Abban. "Shi ne ita kuma ta dawo gida ta ce ba za ta rayu a cikinsa ba." Abba ya nuna Futuha da yatsa. "Ke, ki saurare ni dakyau, ni dai ubanki Isuhu ina raye a kan idanuna ba za ki maida ni mutumin banza ba da bai san me yake yi ba. Kai Mubarak ka dauki mota ka maida ta ka kuma tabbatar ta shiga gidan aurenta kafin ka dawo gida. Ba zan ɗauki wannan sakarcin wofin ba." Anna tana so ta yi magana amma tana gudun zubewar girmanta a idanun Abba, girman da ta ɓoye ainahin zuciyarta ta danne komai ta shekara da shekaru wajen gina shi a idanun Abban don haka ta ja bakinta ta yi shiru, Jannat kuwa ta ƙulu iyakar ƙuluwa. Balle kuma Mami da take jira Abban ya koma ɓangarensa ta je su buga wacce za su buga don bai isa ba sai ya ƙwatarwa diyarta ƴanci. Hakanan Futuha tana kuka ta bi bayan Mubarak suka tafi, a mota ganin ta cika shi da ihu ya dakamata tsawar da ta hargitsa ta, ya koma Mubarak ɗinsa sak da suke shakka, dole ta haɗiye sauran kukan ta koma yinsa a ciki ciki yanda ba zai ji ba. *** Ya kammala shirin baccinsa tsaf zuciyarsa duk a ɓace saboda takaicin Futuha, haka Mami ta shigo tana ɗaure masa fuska, ya dube ta kadan kuma ya ba kansa cewa damuwar ce itama ke cinta wannan ya sa bai ce mata uffan ba. Sai da ta mula don kanta sannan ta magantu. "Abban yara wane irin hukunci ne ka zartar akan al'amarin da ba ka ganewa idanunka zahiri ba?" Da ɗan mamaki ya juyo daga barin chajin da yake ƙokarin sanyawa a wayar ya dube ta. "Kika ce me?" Ta kauda kai har lokacin fuskarta a daure ta amsa. "Ai ka ji abin da nace. Fisabilillahi ta yaya yarinya za ta tashi cikin gida babba kamar haka, miji ya yaudareta ya soma kai ta wuri mai kyau daga baya kuma ya sauya mata muhalli zuwa ƙasƙantaccan wuri sannan ta dawo da kokenta ta sanar da mu amma mu kasa magance mata mu ƙwatar mata haƙƙinta? Wannan yanzu daidai ne a wurinka?" Abba ya dan yi jim yana duban Mami, ya lura tun lokacin da suka tattauna a ɗazun dangane da batun tsaida ranar auren Humaira da Fadeel take tattare da rashin walwala ya kuma fi kyautata zaton rashin sanar da ita kan lokaci ne ya jawo hakan amma kuma sabon zancen da ta yi a yanzun shi ya sa shi tunanin damuwarta kala biyu ne. Wato har da lamarin Futuha. Uzuri ya yi mata ganin bai taɓa samun matsalar ja in ja da ita ba har kuwa a shekarun baya da ya je mata da batun ƙarin aure. Can dai ya nisa ya ce "Idan dai muhallin da diyarki take ciki shi ya zama dalilin ɓacin ranki shikenan, gobe zan je naga gidan bisa adalcin da kika nema." Duk da haka ba walwala ta dora ƙorafinta na gaba. "Sai na biyu, idan har ni Maryam kana yimin kallo na matsayin Uwa a wajen Humaira ba mariƙiyarta ba, ka janye batun auren Fadeel da ita saboda ina da wanda na zaɓa mata ya kasance abokin rayuwarta." Maganar ta shiga kunnuwan Abba a bazata, sai da ya yi ɗan shiru na lokaci kaɗan yana jin muryar Mamin na masa amsa kuwwa cikin dodon kunne. "Maryama, kinsan abin da kike faɗi kuwa?" Ta dube shi tsakar idanu, ta koma Maryam dinta ta Agadez sak wacce ba ta ragawa kowa balle kuma ganin kowa da ƙima ta ba shi amsa kanta tsaye. "Yes Isuhu, ni Maryam na faɗi na yiwa Humaira mijin aure. Idan kuma kana son nunamin ni ban isa da ita ba saboda ba ni ce uwarta ba toh bismillah." *_Aikinki akan yarinyar ya ɓaci gaba ɗaya kuma ba komai ya jaza hakan ba face samun tsayayyen matashin da yake tsananin sonta kuma ya jajirce wajen yi mata addu'a da ma koyamata yanda za ta ƙarfafa ibadunta.*_ *_Ina mai tabbatar maki Hajiya Maryam matukar kika bari auren Fadeel da Humaira ya afku toh ki tabbata rushewar dukkan tubalin ginin da kika dauki tsawon lokaci kina ginawa zai afku._* Waɗannan maganganun na Babandi su ne suka ƙara assasa wutar ƙiyayyar Fadeel a zuciyarta, har shi din waye? Me ya taka da zai iya ɓata mata ɓoyayyen shirinta? Yau dai gashinan a sanadiyyar baƙin nacinsa ya soma maida mata hannun agogo baya, ta soma fiddowa Abba ainahin kalar Maryam din da bai taɓa sani ba. Daga sama ta ji muryar Abba. "Ki faɗi ƙwakkwarar hujjarki koda kuwa guda ɗaya ne tak, ni kuma idan na duba ƙarfinta na maki alƙawarin zan yi yanda kika ce koda kuwa zan ji kunyar mutanen da bani da tamkarsu a yanzu wato iyayensa." Kai tsaye ta ce. "Saboda na yi mata miji, sannan ita kanta Humaira ba ta sonsa." Cikin ɗan haɗe gira Abba ya ce. "Wannan biyun da kika lissafo ba su da matsuguni Maryam, eh tabbas ke kike riƙe da Humaira kuma kin yi abin a jinjina maki kuma a ƙara sonki dominsa kamar yanda wannan ya ƙara siya maki daraja da ƙima da ma kauna a zuciyata, amma fa ki sani, ni ke da haƙƙin yiwa yarana zaɓin miji kaf dinsu, soyayya kuma ina da tabbacin soyayyar da yaron ke yi gareta zai isa su rayu cikin aminci da kyautatawa. Ina kuma da tabbacin in sha Allahu koda a baya ta furta ba ta sonsa, a yanzun ko don irin halaccin da yake kan nuna mana shi da iyayensa, ta sauko daga dokin..." "Ka ga Yusuf ya ishe ni hakanan! Na rantse maka muddin ba ka janye kudurin aurawa Fadeel Humaira ba ni Maryam ba zan ƙara kallonta da idanun rahama ba saboda ka nunamin ba ni na haife ta ba kuma ban isa na zartar da hukunci a kanta ba." Ran Abba ya ɓaci, yau duniyar gaba daya ta yi masa ƙunci. Wannan wane irin tashin hankali ne haka kuma daga wajen wacce bai taɓa zato ba, wacce koyaushe sai dai ta kwantar masa da hankali idan ya shiga irin wannan yanayin. Meke faruwa ne haka? "Wace irin ƙiyayya kike yiwa Fadeel haka Maryama da har kika kasa tankwara zuciyarki ki san da wanda kike magana?" Mami ta kasa tankawa saboda ɗacin zuciya, ji take yi kamar ta shaƙo wuyansa ta kashe shi ko ta huta da wannan zazzafar ƙiyayyar da ta kwashi shekaru tana dannewa a ruhinta har sai da tura ta kai bango. Amma sai ta zaɓi ta miƙe kawai ta fice ta bar masa dakin. Ranar dai haka suka kwana kowannensu a ɓangarensa rai a ɓace. Ga Abba mamaki da al'ajabi ne suka lulluɓe shi, to ma waye mijin da take ikrarin ta yiwa Humairar? Shi ɓacin rai ma bai sa ya tambaya ba saboda bai ga amfanin tambayar da amsarta ba lallai ya aiwatar ba. Ga Mami kuwa haka ta yi ta zarya a daki ga dare ya tsala babu damar kiran Hajiya Lubna don kai mata kokenta balle kuma Babandi da take shakkar kira kar ya ƙara sanar da ita wani abin shiga ruɗanin da fargaba. Don haka sai ta ci alwashin sauyawa Humaira ko a fuska, a ganinta ko don kaunar da ta nuna mata a baya zai sa zuciyar yarinyar ta russuna ta hakura da Fadeel ita kuma za ta yi tunanin wanda ya dace ya yi daidai da Humairar su haɗa kafaɗa a wurin aure amma ba tsara ko fiye ma da mazajen da yaranta ke aure ba. *** Abba kuwa ya cika alkawari domin duk da irin bacin ran da Mami ta ƙunsa mishi a daren jiya sai da washegari ya wanki ƙafa bayan sanar da Yakubu mijin Futuha (wanda ya cilla Abuja saboda yasan za a rina) ya yiwa gidan diyartasa tsinke tare da Mubarak da ya yi masa jagoranci. Ya tarar da mata kusan su biyar cikin shiga ta alfarma sai baza ƙamshi suke su na ta bugu amma ko gezau kamar babu rai a gidan. Ganin dattijon mutum bai sa sun damu da gaida shi ba, gogaggun ƴan duniya ne daga kallo daya sai faman yatsina fuska suke ana taunar cingam har ɗaya na fadin kodai ba nan ne gidan Futuhar Tiktok ba? Sunan da Abba ya ji sun fadi ya yi matuƙar ba shi mamaki, wato dai Futuha har yanzu tana sharafinta a sosha midiya kenan duk da ya hana? Mubarak kuwa da yake tun sadda zai yi jarrabawar karshe ya raba kansa da soshal midiya ya sa ko bayan dawowarsa bai damu da leka Tiktok ba kamar yanda bude buden status ba ɗabi'arsa ba ce hakan ya ƙara dalilin da bai san me Futuhar ke shukawa ba. Kai tsaye Abba ya kira ta a waya, ta amsa da murya ciki-ciki don sosai Abban ke ba ta haushi. Ya ba ta umarnin lallai ta zo ta bude masa ƙofa yana tsaye a bakin kyaurenta. Jin haka hankalinta ya tashi, ga kuma matan Tiktok da suka yi cirko-cirko a gaban gidanta su na jira ta bude, ta rasa uban wa ya ba su adireshin gidanta kuma cikinsu har da Ƴar Snow don ta dauki muryarta ta kuma ji an ambaci sunanta. Babu yanda ta iya hakanan ta bude kyauren cikin rawar jiki. "Don ubanki shi ne kika shanya mu muna ta buga maki ƙyauren gida? Lallai ai dole ki kasa buɗe mana ƙyauren saboda kin gama cika shegen baki kin yi mana kurin gida. Toh bari mu shiga mu ga uwar dake cikin gidan mu yiwa jama'a bidiyo." Duk wannan zantukan na fitowa daga bakin Ƴar Snow kuma kishiyarta mai zuwa, da kissa da kisisina ta samu Yakubu ya ba ta kwatancen gidan da zummar za ta je taya ta murna. Abba ya yi shiru ya kasa magana kamsa har wani sarawa yake yi, wannan tashin hankalin har ina? Ƴarka ta jawo an zageka a gaban idanunka? Mubarak kuwa da ya zo wuya ya daka musu tsawa da ba su umarnin barin wajen tun suna shaida juna. Kasancewarsu tsageru suka hau duramasa ashariya yayinda Ƴar Snow ta bude motarta ta shiga tana masa zagi na uwa da uba, Abba ne ya dakatar da shi daga tankawa har suka ja motarsu suka bar wajen. Futuha kuwa kuka sosai take yi, duk rashin kirki da mutuncinta ba za ta so a zagi iyayenta ba. Yau gashinan sanadiyyarta an zage Abbanta tas a kan idanunsa. Abba ya dago ya dubeta da idanunsa da suka kaɗa, sai kuma ya kada kai ya juya ya nufi mota bayan ya ba Mubarak umarnin ya zo su wuce kar yace mata komai saboda makwafta da kuma masu wucewa duk sun fito gulma har da matan aure. Tun a hanya kirjin Abba ya yi wani irin nauyi da zafi, nan da nan kuwa idanunsa suka soma kakkafewa hakan ya yi mugun tashin hankalin Mubarak kai tsaye ya nufi asibiti da shi. Sai da aka shawo kansa ya dawo hayyacinsa kafin ya kira gida ya sanar da Mami. Hankalinta ya tashi, ko babu komai duk da irin guma mata da ya yi tana son abinta, dalilinsa ne ta aikata duk abin da ta aikata a rayuwa hankali tashe ta sanar da mutan gidan ta yi shirin tafiya. "Mami ina iya binku?" Wani banzan kallo Humaira ta samu daga Mamin wanda ya kara sanyata shan jinin jikinta amma tana ji a ranta duk runtsi duk wuya ba za ta iya rayuwa babu Fadeel ba. Ta kara jinsa a rai musamman da ta yi istihara a kan lamarinsa bisa shawarar shi kansa Fadeel din da ya kirata a daren ta kara jin ta samu nutsuwa da lamarinsa. Wannan ya sa ta nufi dakinsu ta a hawayen ciwon Abba da addu'ar Allah ya tashi kafaɗunsa. A ɗaki kuma ta iske wani tashin hankalin, wato Ummita ce cikin halin naƙuda, duk da ba ta san ya ake haihuwa ba amma daga yanda ta ganta tana ta juyi da rike riken baya tana kirarin mutuwa ya sa hankalinta ya yi mugun tashi. Babu wani abu da ya zo mata a lokacin sai mafarkinta. Ta shiga kwala ihun kira amma ina! Gidan an watse an tafi ga Abba don haka a guje ta fito zuwa sashen Anna neman ɗauki cikin rufewar idanu saboda tsabar tashin hankali. ©Rufaida Umar.Tana shiga ta iske Annan tare da Jannat su na ta hirarsu cikin yare. Ganin yanda ta faɗomusu sai da ta tsorata su. Cikin tsawa Jannat ta ce. "Baki da hankali ne za ki faɗo mana ɗaki ba sallama babu komai?!" Humaira ta durkusa a gabanta tana kuka. "Don Allah ki taimaka mu kai Ummita asibiti, haihuwa zata yi kar ta mutu." Maganar ta ɗan shigi Jannat, ko babu komai Ummitar ta yi mata bautar da wani a yaran Mamin bai mata ba, ta kuma fi Humaira yin biyayya a gareta. Anna ta yatsine fuska. "Ke har kin gane haihuwa ce za ta yi? A ina kika san wata naƙuda? Watakila ma juyi ne." Jannat ta dubi Anna cikin yare take ce mata ai Ummita cikinta ya haura takwas, daga nan ta bi bayan Humaira bayan ta yafa mayafi saman kanta da ko dankwali babu, Humaira dai da ta gaji da maganganunsu ne ta kuma fitowa don tunanin kiran wayar Mamk da ya faɗo ranta. "Ke! Ina za ki je? Muje ki taimaka mata ta fito, bari na sanya a nemo mana abin hawa." Tana kai wa nan ta fita farfajiyar gidan, motarta su Mami sun wuce asibiti wurin Abba da ita. Dawud ta yi karo da shi wanda shigowarsa kenan gidan bai ma san wainar da ake toyawa ba don wayarsa na kashe babu chaji. "Yauwa maza nemo abin hawa Dawud, Ummita ke naƙuda yi sauri." Ai jin haka a gaggauce ya juya, can kuwa Humaira na kukan halin ciwon da ta ga Ummita ciki ya zo ya kuma lafa mata kaɗan a haka ta daure ta zuramata hijabi ta taimaka mata ta miƙe suka fito ko takalmi Ummita ta kasa sanyawa sai salati take yi da kiran ta tuba a yafemata, Humaira ta nema mata gafarar kowa da ta ke mu'amala da shi. Wannan ba ƙaramin tada hankalin Humaira ya ƙara yi ba. Har sun shiga abin hawa Jannat ta maida ta tace ta dauko kayan da aka haɗa na tarbar haihuwa, itama sai lokacin ta tuna. Mami ce ta haɗa komai ta ajiye a ɗakinta saboda ba a son Ummita ta gani balle har damuwarta ya ƙara ninkuwa. Da saurinta kuwa ta fita ta koma ɗakin Mamin tana lalube saboda tsabar ruɗewa  ba ta ma gan shi a gefen madubi ba a ajiye cikin karamin akwati, dole sai Jannat ce ta je ta dauko bayan ta balbale Humaira da masifar ruɗewar banzar da ta yi, acewarta. A cikin ɗan sahun ma haka Ummita ta dinga salati da nanata kalmar a nema mata yafiya har Jannat ta gaji ta ja tsaki wai ta fiye raki da yawa. Dawud na gefe kusa da ɗan sahun shi kansa sai dai Ummita ta ba shi tausayi ya ji dama haka haihuwar take? Tun su na tafe Jannat ta yi waya ta sanar da Mami nan da nan ta ce su taho da ita asibitin da Abba yake don shima ya warware kawai dai maganin bacci ne bai sake shi ba acewar likita yana buƙatar hutu. *** Gadan-gadan aka karɓi Ummita don har ta soma  zubar da ruwan naƙuda, gaba daya ahalin gidan hankalinsu tashe idan ka jira Jannat dake ta chatting abinta. Tashin hankalin Mami bai wuce na fatan Allah yasa abin da za a haifa ya mutu ko don ta huta da bibiyar da Wizzy yake mata musamman yanzu da Ummita ta shiga watan haihuwar kusan koyaushe sai ya yi mata wani shegen gajeran saƙo a whatsapp cewar KAR KI MANTA. Wannan kalaman su kadai yake ce mata daga su ba ya ƙara koda harafi ɗaya. Ga Mubarak kuwa, babban burinsa Ummita ta rayu kar ya rasa ta. Gaba daya ya kasa sukuni sai safa da marwa yake yi, Raihana dai na gefe tana danna counter tana jan salati yayinda Humaira take zaune shiru.   Kafin a kai ga fitowa a sanar musu ta haihu suka ji kukan jariri ya karaɗe inda suke, nan da nan duk suka nufi ƙofar suka yi cirko-cirko. Jimawa kaɗan ɗaya a cikin Nurses din dake ciki ta fito fuskarta a sake tana kallonsu ta ce. "Alhamdulillah, ta sauka lafiya an samu ɗa namiji." "Nos ya Ummitan?" Tambayar da Mubarak ya cilla kenan. "Tana cikin ƙoshin lafiya sai dai da alama ƴar shagwaɓa ce sai kuka take mana tun bayan da ta haifo santalelan saurayin." Wani guntun tsaki Jannat ta ja, su kuwa babu wanda ya ce uffan kowa da kalar tunaninsa. Humaira dai ko ma mene ne, ko wane irin tabo ne da yaron ita ta godewa Allah da har Ummita ta sauka lafiya ta kuma rabu da cikin da ta tsana lafiya. Hakanan ma tunanin Raihana. Babban burinta na kasancewar lafiya yar uwarta ta sauka. Ga Mami kuwa ba su iya sun fahimci halin da ta ke ciki ba sai dai ga dukkan alamu akwai wata damuwar da take ciki don gaba ɗaya fuskarta ta nuna. Sun fi kyautata zaton kuma saboda lamarin haihuwar Ummita ne. Wa zai yi murna da haihuwar ɗan da aka same shi ta fyaɗe? Babu shi kam, amma kaddara ce babu yanda suka iya. "Ku je gida zan zauna a wurinta. Ke Humaira ki yo mata abu mai ɗan ruwa da zafi wanda za ta ci ki kawo." Ba ta so tafiya ba tare da ta ga fuskar Ummita da ba amma sai ta daure ta amsa da toh ganin kamar har a lokacin fushi sosai Mamin ke yi da ita ba ta huce ba. Bayan tafiyarsu idan ka dauke Mubarak da Mami ta kora don dubo ko Abba ya farka, babu kowa a asibitin sai ita (Mamin). Tana zaune ta yi shiru cikin tunani, toh yanzu idan ta kasance za ta kai wa Wizzy jaririn nan wa za ta sanya wannan aiki? Kuma ma a ina za su haɗu? Ta dai san ba za ta taɓa iya raba Ummita da abin da ta haifa a asibitin nan ba saboda babban asibiti ne kuma mai tsaro sosai ga kyamarori (CCTV) ta ko'ina don haka sai ta zaɓi neman shawarar abokiyar shawararta a ire-iren waɗannan gaɓoɓin. Wato Hajiya Lubna. Miƙewa ta yi ta fice can farfajiyar asibitin ta danna mata kira, ringing hudu ta ɗaga ana biyar. Ko sallamar da dama ba ta wani ɗaɗa su da ƙasa basu yi ba Mami ta tare ta da sauri. "Lubna ina cikin tashin hankali, ga dai yarinya ta haihu an sami namiji amma kaina ya ƙulle. Yanda yarannan suka sanya idanu a kan jaririn nan ta ina kuma ta wace hanya zan soma dauke shi na kai wa wancan ɗan shegiyar?" "Kai Maryam, wannan ai abu ne mai sauki duk kin bi kin wani sanya ni fargaba. Kar ki yarda ki sanar da shi an haihu ki bari har sai an kwana biyu yanda idanu ba zai dawo kanki ba. Duk lokacin da kika samu wata wawakekiyar damar ba sai ki fiddo da shi ba ko da haɗin bakin wani amintaccen ma'aikacinku ba? A ɓoye dai aka fitar da shi ni na tabbatar ba za a zargeki ba, toh ke wa ma kike tunanin zai zargeki bayan wannan halin iya wuyar da kika gwada musu a rayuwa tsawon zama?" Sauke ajiyar zuciya Mamin ta yi na samun ɗan sauƙi daga damuwarta. "Shikenan, zan yi iyakar kokari na ganin bai samu labarin ba zuwa lokacin da  zan aiwatar da shirina." Daga haka suka yi sallama bayan Hajiya Lubna ta ƙara jaddada mata lallai ta yi kokarin aikata hakan ko ba komai ƙimar gidan nasu zai dawo idan ya so sai su san me za su yi a gaba don cimma sauran manufofinsu wadanda babu ɗigon alheri. *** Dakyar Ummita ta iya tsaida kukanta, sun gyarata tas an kuma yi mata sauyin ɗaki amman ko ɗaga kai ta kalli abin da ta haifa  da ya kwaso kamanninta tamkar an tsaga kara an karya  ba ta yi ba. Ya yi kukan har ya haƙura ya tura yatsa baki yana tsotsa a haka ya yi bacci.   Itama gajiya ta sanya bacci mai nauyi ɗaukarta. Koda Mubarak ya shigo haka ya iske su, ita bacci jaririn ma haka. Fuskarta ta yi wani fayau kuma ta ɗan sauka ba kamar ɗan kumburin da ta yi a fuskar ba kafin ta haihu. Ya kai duba ga jaririn, kamannin da yaron ya yi da Ummitan sai ya ji ya shiga ransa sosai. Tausayinsa kuma ya mamaye shi, ire-irensa su na nan birjik a faɗin duniya waɗanda ƙaddarar samuwarsu ta hanyar da ba ta sunna ba ta faɗamusu musamman ma a yanayi irin na Ummita ta hanyar fyaɗe. Amma hakan ba ya wanke tabon da suka riga suka goga daga ubansu, sai a dauki tsangwamar duniya a ɗora a kansu alhakin da ace son ransu ne su ma za su fi kwadayin a haifesu ta hanyar aure. Ya ƙara kai duba ga Ummita, ya tabbata ko ganin jaririn ba ta son yi saboda tsana, fatansa Allah yasa watarana zuciyar wannan Uwa ta russuna har hakan ya jawo mata kaunar ɗanta. A hankali ya sa hannu ya ɗauki yaron ya yi mishi addu'a har ma da yi mishi huɗuba bisa umarnin Abba wanda ya samu lafiya bayan Mubarak din ya shaida masa abin da ke faruwa ya sanya shi yiwa yaron huɗuba da suna Ahmad. Abba kuwa ya tsaya domin rama sallar da ta kubce masa. Yana nan tsaye bayan ya shimfiɗa jaririn haka Mami ta shigo, ganinsa a nan sai ta haɗe girar sama da ta ƙasa, ba ta son abin da zai sanya Mubarak ɗin raɓar Ummita da ma abin da ya shafe ta gaba daya. So take kawai ya tattata ya bar garin zuwa Camp kafin ya ɓallo mata wani abin da ba za ta iya ɗauka ba. "Kai kuma me kake yi anan?" Ya dubi Ummita gudun kar Mami ta ɓaro wani batun har ta yi sanadin tashinta daga bacci sai bai ce uffan ba ya juya ya fita, Mami ta ɗan dubi inda suke kwance sannan ta juya ta rufe ƙofar ta bi bayansa. Ya sanar da ita saƙon Abban da ma huɗubar da aka yiwa yaron da suna Ahmad. "Sai kuma a rasa wanda zai yi sai kai? Meyasa zai yimin haka? Ina ruwanka da sabgar yaron da ba a san asalinsa ba?" Mamaki ya ƙume Mubarak. "Mami, wai lafiya kwanaki biyun nan ranki duk a ɓace? Haba Mami, don Allah ki bar faɗin hakan kada ki faɗa gaban Ummita abin babu dadi." Kamar ta kifa masa mari haka ya ji, shi kuwa sosai ransa ya ɓaci. Ga damuwar da Futuha ta jefa Abbansu ciki ga kuma wannan haihuwa da ya tabbatar za a sha daga da Ummita akan duk abin da ya shafi ɗan. "Toh ubana, sai ka faɗamin abin da ya kamata da wanda bai ma dace ba ka ga ai zan ji tunda kai ka haife ni. Mubarak tun muna mu biyu ina mai ƙara gargadinka akan ka fita hanyar yarinyar nan ka kuma gaggauta cire ta a zuciyarka don na rantse ni dai Maryam muddin ni na haifeka kai ma ba shegen bane ba za ka taɓa aurenta ba." Ya ji kansa ya yi wani irin sarawa, a duniya ko misƙala bai taɓa fuskantar zai samu matsala daga Mami ba akan Ummita, ya fi tunanin zantukan su Anna da Jannat ne ya sanya ta zama haka amma ba wani abu daban ba. Madadin ya yi magana sai kawai ya ba ta hakuri ya bar wajen don ba ya so su haɗa wata diramar a asibiti. Da ficewarsa sai ga wayarta ta dauki ƙara, dubawar da za ta yi ba kowa ba ne face Wizzy. Sai da ta yi taga-taga za ta fadi da sauri kuma ta dafa ƙofar ɗakin. Ganin mutane a wajen sai ta yi tunanin shigewa dakin da Ummita take, ta ji Nos ta ce za ta jima tana bacci wannan ya sa kanta tsaye babu shakkar komai ta shiga amsa wayarta. "Mene ne? Kiran na meye ka ke yimin? Ba nace maka kar ka kuskura ka kirani har sai ta haihu ba?" Ya yi ƴar dariya. "Hajjaju kenan, kina tunanin za ki yanke alaƙa da ni da wuri alhalin kina tare da abu mafi soyuwa a rayuwata? Ina! Ai ba zai yiwu ba, koda ace yau gudan jinina ya fito a duniyarnan ki sani kin samu jikan da zai kiraki da kaka ko da kuwa daga bangon duniya ne. Ni kiran da nayi shi ne, ya ake ciki? Ina magana a whatsapp sai wani you no care kike nunamin, to idan ba so kike nayi eh yane ba wato na yi dirar mikiya a gidan ki gaggauta sanar da ni halin da ake ciki. Ta fesar da cikin ko kuwa ya na nan a dunƙule?" Wani irin zufa ya karyowa Mami. Ta ji hatta da jikinta ya ɗau rawa, ta juya inda Ummita ke kwance ganin ta ɗan motsa ya sanya da sauri ta bude ƙofar ta fita ba ta ce masa uffan ba har sai da ta ƙarasa ficewa zuwa farfajiyar asibitin. A ɓangare Ummita kuwa, tsaf ta ji muryar Mami tana yiwa abokin wayarta magana akan me zai kirata, sai dai ko alama ba ta tsinkayi abin da ya ce ba. Motsin da ta yi na farkawa tana kokarin tashi ya sanya Mamin ficewa a dakin, ta buɗe idanunta tarr ga wani jiri dake kwasarta daga kwance tsabar yunwa. Tunanin maganganun Mamin take son yi amma lokaci guda kukan da jaririn dake gefenta ya tsala ya sanya ta dan karkata kai ta kalleshi. Kallo na ƙurillah, burinta ta hango kamannin Ubansa ko ta samu shaidar da za ta nuna domin a binciko inda yake a cafke shi, sai dai kuma ban da su din waye ya taɓa ganinsa? Kukan yake yi tana jin wani iri a zuciyarta, yanayin da ba ta taɓa hangensa akan yaron ba yana zuwar mata a sannu sannu. Ta kasa miƙewa zaune balle ta samu*LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* 09034973645 Ta kasa miƙewa zaune balle ta samu damar kai masa tallafi a haka su Humaira suka shigo ɗakin suka risƙeta. Ganinsu sai ya sanya ta komawa ta kwanta sai kawai ta soma kuka a hankali, da sauri Raihana ta ƙarasa ta ɗ an rungume ta tana kokarin maida ƙwallar da ta cika mata idanu. "Ya isa hakanan don Allah. Kiyi hakuri tunda Allah ya raba lafiya yar uwa." Humaira kuwa sai ta ajiye kwandon kayayyakin da suka taho da su ta shiga haɗa mata bisa umarnin Mami da suka yi karo da ita za ta fice da waya a kunne, ta dai katse kiran ta musu magana kusan ba a nutse ba sannan ta sa kai ta karasa ficewa zuwa farfajiyar, su kuwa suka yo ciki. Raihana ta saki Ummita ta karasa ga Bebin da ya ɗan jinkirta da kukan ta ɗauke shi ta zuba masa idanu. Can kuma ta kalli Ummita, kamar ta ce kun yi kama sai kuma ta ji tsoron kar ta ji haushinta. A haka aka kwankwasa kofar dakin da sallama suka amsa aka shigo,  Baba Amina ce ƙanwar Abba sai ko Abban da kansa a bayansa kuma Mubarak. Abban da kansa ya yi kiranta ya sanar da ita zancen haihuwar wannan ya yi silar zuwanta. Ita ta taimakawa Ummita ta sha shayin ta ci abinci kadan, anan kuma Abban da ita suka hadu wajen yiwa Ummita nasiha da nunamata muhimmancin yarda da ƙaddara. Sosai kuma maganganunsu suka shige ta, sai anan ma take ji Mamin ta je gida ta dawo a bakin Abba. Bayan fitar su Abban da Mubarak ne kuma Baba Amina ta zage wajen taimaka mata ta yi wanka ta shirya tsaf, shima yaron ta wanke shi ta sanya mishi sabbin sutura, wankewar da ya sanya kamannin mahaifiyarsa ya ƙara bayyana muraran a fuskarsa hatta da ɗan baƙin tabon da Ummita keda ahi a gefen kumatunta haka jariri Ahmad ma. Ta yi ta satar kallonsa cike da sha'awa ga wata iriyar ƙauna da ta yiwa zuciyarta ƙawanya. Ba zato ta ji Baba Amina ta miƙa mata shi har ya kusan faɗuwa ba don Allah ya sa ta tarba da hannunta ba. "Daure kiyi hakuri ki ba shi ya sha Ummi, in sha Allahu wataran zai zamo maki abin alfahari. Kar ki duba hanyar da kika same shi, kiyi hakuri ki yarda wannan wata jarrabawarki ce da ba ki isa kin kufce mata ba. Watarana sai labari da yardar Allah." Kwalla suka cicciko mata, nan Baba Amina ta taimaka mata yaron kuwa ya cafka ya soma tsotso kamar zai tsige mata fata, haka yana sha tana jin wani irin ciwo a mara ga zafin fisgar da yake yi har hawaye ta soma tana jujjuya kai. Humaira da ta zuba musu idanu sai ƙarar wayarta ta katse ta. Ganin sunan Fadeel na yawo saman screen ya sanya ta fita a dakin fuskar dauke da ƙaramin murmushi. Da sallama ta ɗaga wayar, ya amsa mata a sake. "Boddona wato idan Fadeel ayyuka suka hana shi kiranki, ba za ki dauki waya ki kirashi ba ko?" Ƴar dariya ta yi kaɗan da har ya tsinkayo sautinta, ita sau da dama yanayin shagwaɓar da muryar da Fadeel kan yi mata na ba ta mamaki da kuma dariya, shi dai a lallai ta ji tausayinsa koyaushe. "Oh, dariya ma na baki? Toh aikuwa yanzu zan bar dukkan abin da nake yi ki gan ni da yammacin nan." Ta dan rausaya idanu kaɗan tana murmushi. "Ka yi hakuri toh, ni ba na ma gida, Ummita ta sauka lafiya muna asibiti." "Allah Sarki, me aka samu?" Da sanyin jikin tausayawa yaro Ahmad ta amsa. "Namiji ne, an masa huɗuba da Ahmad." Ya yi addu'ar fatan alheri gareshi kafin kuma ya ƙara kwantar mata da hankali da nunamata su ne suke kusa da ita, su kasance masu jarumta su dinga ƙarfafa mata gwuiwa. Kamar dai sun haɗa baki da Baba Amina, haka ya yi ta yiwa Humaira nasiha. Hakan ya sanya tsantsar so da kaunarsa wadanda ba ta san mafarinsu ba suka shiga ratsa ta sosai. Ya karashe zancen da fadin. "Yauwa, kuma bana son kina yin asarar hawayenki musamman da yake bana kusa." Ta ɗan russunar da idanun kamar yana kallonta saboda jin nauyin maganarsa. "Bari na kyaleki ma yi magana anjima in sha Allah." "Toh, na gode a gaida mutan gidan." "Zasu ji, nace ba?" "Naam?" Ta amsa gami da tattara nutsuwarta don a sautinsa ya nuna ko ma mene zai fadi nada matukar muhimmanci. "Ina matuƙar kaunarki." Sai ta sauke ajiyar zuciya har tana jin tsikar jikinta na miƙewa, tana son furta masa ita din ma hakan ce a wajenta amma wani kunya ya hanata aikatawa. Sai kawai ta ji ɗif ya yanke kiran. Ta numfasa kafin ta ja ƙafafunta zuwa ciki duniyar na mata wani irin dadi ga kaunar Fadeel dake ƙara tsuma ta. *** A ɓangaren Fadeel kuwa, ajiye wayar ya yi jikinsa duk a mace saboda shauki da kewar Humaira da ya mamaye shi lokaci guda, har yanzun yana shakkar kada wani abu ya sauya zuciyarta daga gareshi, sati ukun da kwanakin da suka yi saura jinsu yake tamkar shekaru duk kuwa da cewar a zahiri ga Ibb na ta faman tashi faɗi wurin ganin an haɗa dukkan abin da ya dace dangane da lefe da ma kuma list na wadanda zasu gayyata. Fadeel din shima sosai ya maida hankali ga ginin gidansa wanda an kammala komai sai kayayyakin furniture da yake sanyawa don alƙawari ne ya daukarwa kansa da yardar Allah sai dai Humaira kawai ta shigo gidansa amma ba ya bukatar a yi mishi hidimar da babu wanda zai mora sai shi sai kuma matarsa. Ita din yake so da kauna ba komai ba. A wannan lokacin ma zaune yake a falon Ibb din wanda yake amsa wayar Daddy, ya yi shiru cikin tunanin Humaira yana mai murmushi idanun a rufe ruf. Ba zato ya ji an wurgo mishi filo, ba kowa ba ne sai Ibb. "Allah ya sauwaƙe maka kai kam Romeo. Ina ce shirin aurenka ake yi da yarinyar nan? Toh mene ne kuma na wannan dogon tunanin kamar ba yanzu ku ka gama waya da junanku ba?" Fadeel wanda tun jifa da filon ya wartsake, ɗan harara ya wurga masa. "Toh sannu, kai me za a kiraka idan ka kira ni da Romeo? Mutumin da hatta da gabatar da lakca ba ta hana shi amsa wayar Madam kamar ba daga gidan ka fito ba." Murmushi Ibb ya yi kaɗan. "Ni yanzu ba wannan ba, ya ake ciki kai da mutuniyar taka?" Shi din ma Fadeel martanin murmushin ya maida masa gami da kwantar da kai jikin kujera. "Alhamdulillah, akwai cigaba kwarai ba kamar baya ba. Kai ba ka ga alamu ba?" Jinjina kai Ibb ya yi. "Na gani tabbas. Amma ba anan gizo ke saƙar ba, mu dai fatan Allah yasa ba ɓangare guda ke so ba." "Ina da yaƙini da tabbacin yanzu tana sona, sai dai ta kasa furtawa ne saboda dalilinta. Kai ni koda babu son daga fanninta, zan koyar da ita na tarbiyyantar da ita soyayyata. Har yanzu kana tantamar irin kaunar da nake yi mata wai?" Ibb na ƴar dariya ya girgiza kai. "Ko kusa, na san ai kai tuni ta shafe babin kowace mace a zuciyarka. Hakan nada kyau. Allah dai ya sanya alheri." Fadeel ya amsa yana sannan ya sanar da shi haihuwar Ummita. Sosai Ibb ya tausaya mata. "Ya ake ciki batun binciken can?" Ɗan yarfa hannu ya yi. "I dnt know, ban yi waya da shi ba, kuma bai kirani ba. Amma a satin da ya wuce ya bani tabbacin da alamun nasara don suna bincike akan accounts din da aka bude na whatsapp da instagram har da facebook da sunan Feedy Baby. Ya kuma ce an soma samun bayanai akan ta don ba ta rufe akawun din ba na instagram ta cigaba da amfani da shi a ɓoye, hakanan whatsapp, yanzu dai su na monitoring kowane motsinta." Ibb ya yi fatan nasara, haka suka yi ta tattaunawa har dai Salma ta shigo ta sanar musu abinci ya kammala wannan ya katse su suka miƙe. *** Mami gaba daya ba a nutse take ba, Wizzy ya jaddada mata cewar sai ya dauki fansa a kanta ko kuma ya tona mata asiri matuƙar ta hana shi gudan jininsa saboda yana tambayarta ko an haihu ko aa ta yi mishi ihun ya rabi da ita babu ruwansa. Wannan ne shima ya fusata shi har ya kaifafa harshe a kanta ya yi mata munanan kalamai. A karshe dai dole haka ta bar asibitin ta kkma gida don samun damar yin tufka da warwara. *** Ummita kuwa kwanansu ɗaya aka sallamo ta. Ko ta ya ya? Oho, sai ga makwafta na ɓullowa ganin jariri, aka rasa wanda ya sanar da su. Jannat kuwa ko dakin su Ummitan ba ta shiga. Tasleem zuwanta daya ta koma, dalilin jego ne ya sanya Abba bai yi mata faɗan rashin nuna kulawa ga ƴar uwarta ba. Ita kuwa Futuha Abba ya yi rantsuwar kada ta sake a nan kusa ya ga ƙafafunta a gidansa, kuma ya tabbatar mata muddin ba ta goge dukkanin shafukanta na kan yanar gizo ba zai saɓa mata. Dolenta babu yanda ta iya duk da irin tara jama'ar da ta yi a kafafen musamman Tiktok hakanan ta shafe su don Mubarak na lurar wa Abba ko ta aiwatar ko a'a. Anti Maijidda ta zo bayan Ummita ta cika sati da haihuwa, ta ɗan ji dadi ganin yanda ta kwantar da hankalinta ta ke kuma ba yaron kulawa, idan an ce mata kafin haihuwar za ta yi haka ba za ta yarda ba. A ranar Anti Maijidda ta tattara ta bar gidan domin ta rantse ba za ta kwana a gidan da Mami ke cikinsa ba. *** Mami ce zaune a falon Abba cikin amsa kiran da ya yi mata don su yi magana mai muhimmanci. "Ina sauraronka." Ta yi furucin ciki-ciki, tun sadda Abban ya ce ba zai taɓa hana Fadeel auren Humaira ba ta ke jin haushinsa ga uwa uba takurar da ya soma yiwa yaranta. Babu dama Yassar ya kai sha biyu a waje sai ya bude masa wuta kamar ya ari baki, wai ina yake samun kudaden da har yake shigar tsadaddun kaya yake yawon fita taɗi? Ga Futuha da gaba daya ya yi mata geji da gidansa, hakanan Dawud shi ma ya hana shi mu'amala da wasu abokansa ɓata gari. Ƙassim kuwa koyaushe yana gidan makwafta wurin abokansa yaran gidan, haka zasu ja shi yawo wuraren shaƙatawa iri iri na masu kudi a yi ta kashe masa kudade yana shigar kece raini, a yau din ma ganinsu da Abban ya yi da matasan gidan uku wadanda aka yiwa tambari marar kyau har ana zarginsu da shaye shaye da abubuwa barkatai, Abban har marinsa ya yi a gaban Mamin, wannan ma ya taɓa zuciyarta kaca-kaca don haka take cika da batsewa ƙiris ya rage ta fashe. Ga Abba kuwa bai damu da yanayin dake saman fuskarta ba ya soma magana. "Sanin kanki ne auren Mamana ya zo sai dai yanayin da muke ciki ya hana a yi abin da ya kamata na shirye-shirye, ita dai a satinnan za ta je Nijar ta yi musu sallamar aure, iyayen yaron da shi kansa sun jaddada min ba sa buƙatar koda tsinke daga wajenmu, za su yi mata komai na gidan aure iyaka a kai musu ita amma matsayinmu na masu mutunci ba zamu naɗe hannuwa hakan ta kasance ba, ko ya ya mu yi mata wasu kayayyakin kamar daga na kicin da dai sauransu. Ku ne mata, kun fi sanin abin da ya kamata a yi. Abu na gaba kuma ƙarshen satin nan mai kamawa za su kawo lefe." Zantukan suka shiga tafarfasa zuciyar Mami, ji take yi tamkar ta yi fiffike ta dira a jikin Abba ta shaƙe wuyansa har lahira. Daukaka dai ɗaukaka wanda ta sani shi ne abin da ya iso rayuwar Humaira? Toh wai tana mene ne haka? Kai jama'a. "Da sake!" Ta furta a fili tana wani irin tsuma kamar na zakanyar da ta wuni ta kwana ba ta ci ba. Abba cikin rashin fahimta da yi mata uzurin ɓacin ran da take tattare da shi a yinin ranar ya sanya shi kai zuciya nesa ya jefamata tambaya. "Ban fahimceki ba." Ta dube shi tsakar ido, fuskarta muraran ta bayyana abin da ke cin zuciyarta murya a sama ta ce. "Eh nace da sake! Ba za ta saɓu ba wallahi! Muddin ina raye ba zan bari Humaira ta auri dan iskan yaron nan ba mazinaci!" Kalmar mazinaci ta yi matukar girgiza Abba har sai da ya ji wata iriyar faɗuwar gaba. Salati ya yi da karfi yana nuna Mami da yatsa dake kakkarwa. "Maryama ki tsoraci Allah, kar tsanar yaron nan ya kai ki da daukar hakkinsa? A ina kika gani da idanunki yana aikata zina? Wai Maryama meke damunki? Wannan sauyin da kike nunawa na menene?" Ta ɗan yi jim tana girgiza ƙafafa kamar ta karya ta, so take ta ce masa sauyin na ubanka da uwarka ne amma kuma tana tanƙwasar kanta gudun lalacewar aikin shekara da shekaru, don haka sai ta rasa mafita, bakinta kuma ya ɗinke, kawai sai ta fashe masa da kuma. Humaira dake tsaye a ƙofa riƙe da jug wanda ta yiwa Abba lemun cittar da ya sanya ta, tun sadda Mami ta soma ambaton kalmar Da Sake! Take tsaye kamar an ɗaure mata ƙafafunta ta kasa motsawa. Komai ya shiga kunnuwanta hatta da kiran Fadeel mazinaci da Mami ta yi. A yau ɗaya kuma karo na farko da ta ji a ranta Mami ta ba ta haushi dagasken gaske. 'Mami lokacin da aka nunawa abu tsana, lokacin zuciyata take tafarfasa saboda kaunarsa. Kiyi hakuri, Fadeel koda mazinaci ne zan jure tarayya da shi, ballantana kuma zuciya da ruhina su na karyata kalamanki gareshi.' Wannan duk zantukan zuci ne da Humaira ke yi lokacin da ta juya ta soma tafiya da nufin maida haɗin firij har zuwa sadda za su kammala tattaunawa. Haka ta koma ɗakinsu zuciyarta a ɓace, Raihana da Ummita da kuma Sa'ade bazawarar ɗiyar Baba Amina dake kula da Ummita suka zubamata idanu. "Lafiya Humaira?" Har su na haɗa baki wajen tambayar, sai kawa ta girgiza musu kai da murmushin yaƙe bayan ta yi dabarar dauke ruwan hawayen da ke kokarin zubomata. "Ba komai." "Haba Amarsu, tun ma ba'a yi komai ba?" Fadin Raihana cikin son kawar mata da damuwa da bagarar da zancen. Su Ummita suka ɗan dara. Ita dai ban da murmushin dole babu abin da ke saman fuskarta. *** Mami kuwa sosai suka fafata da Abba don ta rantse ita dai ba zaa yi auren ba, wannan ya sa Abba ransa ɓaci suka samu mummunan saɓanin da har sai da ya kira Baba Amina a waya da zummar ta zo ya sanya ta hidimar auren Humaira. A cewarsa shima yana da ƴar uwa. Mami ta wuce dakinta a fusace ta rufe ruf, kanta take duba ta madubi ta yi kwafa. "Lokacin da za ka mutu yarana su mallaki arzikinka ya yi Yusuf. Idan hr tsafi gaskiya ne sai na kashe ka." Ta furta a kaifafe. @Rufaida UmarMami ta ga abin na Abba dagaske ne, a gefe ga Humaira dake shirye-shiryen tafiya Nijar sai ɗoki take yi saboda tsabar jimawar da ta yi ba ta je ba. Abba kuwa kamar yanda ya ce ne, Baba Amina ya kira suka yi magana ya ba ta ragamar siyayyar kayan kicin wanda a farko ta nuna sam ita ba za'a yi haka ba idan an yi ba'a yiwa Mami adalci ba. Sai da Abban ya ɓata rai ya zayyane mata yanda suka yi, da kanta ta samu Mamin da zancen amma Mami ta buɗe mata wuta da zummar babu abin da ya shafe ta da auren Humaira da Fadeel. Jiki a mace da kuma ɗumbin mamaki Baba Amina ta dawo a dole ta karɓi wannan ragamar ta kuma taushi Abban akan ya yi mata uzuri tunda hakan ba ta taɓa faruwa tsakaninta da yaran riƙonnata ba. Humaira kuwa sosai Mami ta dauke mata wuta, gaisuwarta ciki ciki take amsawa, hakanan ko tsinke ta bar sa Humaira dauke mata balle ta sanya ta aiki. Raihana da Ummita lamarin duka ya dame su. Humaira ma tana jin zafin hakan, duk ta bi ta rame amma ba ta jin za ta iya yiwa Mami alfarmar rabuwa da Fadeel alhalin ba ta da kwakkwarar dalili ba. Idan har a yau ta yi yanda Mamin ke so tana da tabbacin alhakin Fadeel sai ya kama ta. Ba kuma za ta taɓa samun rayuwar jin dadi da walwala ba a duniyarta. A  yau ma tana zaune tana gyara kayanta cikin jaka tana yi tana sauraron Raihana da Ummita dake faman zantawa akan lefen da za'a kawo washegari wanda ita kuwa ana kawowa da kwana ɗaya za ta wuce Nijar. Ba ta ce musu uffan ba, sai bayan fitar Raihana ne Ummita ta dube ta. "Ya kamata ki je ki sami Mami kuyi magana Humaira. Haka za ki tafi tana fushi da ke?" Ta ajiye set din kayan da take shirin sakawa a akwati a saman cinyarta bayan ta zauna gefen gadon jiki a sanyaye. "Toh ya zan yi Ummita? Kina gani fa Mami ko gaisuwata ba ta amsawa." Ummita ta girgiza kai. "Hakanan za ki mayar da komai ba komai ba ki je ki kara ba ta hakuri ki lallaɓa ta. Mun yi mata uzuri saboda sanin da muka yi cewar kowane DAN ADAM ajizi ne. Mu kara yi mata mu gani." Sauke nannauyan ajiyar zuciya ta yi. *"Shikenan, bari na je na gani ko za ta saurare ni." Ɗan murmushi Ummita ta sakar mata na karfafa gwuiwa. Wannan ya sanya ta mikewa ta nufi dakin Mami. Ta shiga da sallama a bakinta amma babu amsa, don ta tabbatar ko ba ta dakin ne ya sanya ta ɗaga labule ta shiga. Mamin hankali kwance tana zaune gefen gado sai faman danna wayar hannunta take. Abin bai ba Humaira mamaki ba, ko ba komai zuwa yanzu dama ya ci ace ta saba da hakan. Don haka ta daure ta karasa ta durkusa a gefe, Mami kuwa tun shigowarta ba ta ko kalleta ba sai ma fuskarta da ta tamke tamkar hadari ya haɗo. "Mami ina sane da cewa har yanzu kina fushi da ni, na zo ne domin na ƙara ba ki haƙuri akand laifin da ban san na aikata ba." Wani kallo ta ɗago ta watsa mata wanda ya sa Humaira sunkuyar da kai gami da yin shiru. "Kin zo ne don ki nunamin ke din ba ki da mutunci kuma butulu ce?" Jin haka sai abin ya daure mata kai. "Mami har ga Allah ban san taƙamaiman laifin da nayi ba." "Dakyau! Ai idan ba ki yimin wannan butulcin ba, ba ki cika ɗiyar Fatima ba." Maganar ta daki zuciyar Humaira da har sai da ta ƙara buɗe idanunta wurin kallonta sosai. Mami me yawan yabon halayen Mahaifiyarta, yau kuma ita ce saboda son zuciya irin nata ta ke kushe ta? "Kiyi hakuri Mami, kiyi hakuri idan har da abin da na maki mai zafi amma domin Allah kada laifina ya ture kyawawan yabon da Mahaifiyata ta samu a wurinki. Babu abin da take buƙata a wurinmu face fatan alheri." Muguwar harara ta watsa mata, kamar ta ce fatan alherin uwarki sai kuma ta danne zuciyarta dakyar. "_Kar ki yi saurin rushe komai don ba alheri ne gareki ba._ _Nace maki mu bi komai sannu har mu cimma gaci._ _Aure dai ki kwantar da hankalinki ba zai faru ba kamar yadda Babandi ya tabbatar mana._" Maganganun Hajiya Lubna ke yawo a ƙoƙon ranta, don haka sai ta yiwa Humaira nuni da ƙofa. "Ficemin a ɗaki tun ban kwaɗa maki mari ba. Ke har kin kai ki faɗamin abin da ya dace da ma wanda bai kamata ba? Ko kin ga ni Maryam na shiga shirgin aurenki da wancan lalataccen? Toh kamar yanda ban shiga ba ki je can ku ƙarata ke da shi, ai kowa ya san abin da za ku aura daga ke har shi." Ɗan shiru Humaira ta yi tana nanata kalaman ƙarshe na Mamin a zuciyarta idanunta kuwa ƙurr a kanta, to me take nufi? Gaba daya ta kasa fahimtar manufarta da kuma inda ta dosa. Sai da Mamin ta yi mata wata tsawa kan ta fice mata a ɗaki sannan ta miƙe gwuiwa a matukar sanyaye ta fita tana fidda hawayen bakin ciki. Tunanin ba Ummita kadai ce a ɗakin ba saboda lokacin yi mata wanka ya yi sai kawai ta shige kicin ta zauna tana kuka sosai. Tana kara gasƙata cewa dai wasu sabbin halayyar Mamin da ba ta sani bane suke bayyana a muraran. Lallai ta fara shaƙar ƙamshin gaskiya a kalaman Anti Maijidda, za kuma ta so tasan ko menene ta sani akan Mamin har ta kasa aminta da zuciya ɗaya take zaune da Ummita da ma ita kanta. Sai da ta kammala kukanta ta share hawaye ta koma sashinsa bayan ta wanke fuska amma ina, duk da haka Ummita da Raihana dake zaune riƙe da Ahmad a hannu wanda ya sha wanka suka fahimci akwai ta yi kuka sakamakon sauyin da fuskarta ta yi. "Lafiya Humaira? Me aka yi? Kin bar waya tun ɗazu angonnaki ke faman kira." Ta yi murmushin yaƙe kafin ta amsawa Raihana. "Babu komai, ina wayar?" Ta miƙa mata tana mai ƙara jefamata tambaya don ita sam ba ta yarda ba, a ƙarshe ta ce. "Mami ce ko? Don nasan ba kya shiga sashin Anna balle nayi tunanin ko..af ko kin haɗu da Anti Jannat ne? Ba ta jima da fita a dakinnan ba ko kun haɗu?" "Ke dai Raihana ko ma wacece kuma ko mene ne tunda dai ya faru ba shikenan ba?" Ta ɗan yatsine fuska. "Allah ya kyauta dai." Ummita ta amsa da amin. Sai da Raihana ta bar wurin ne ta kwashe duka yadda suka yi da Mamin ta sanar mata. Ummita yarinya mai kaifin basira da kwakwalwa tsaf ta fahimci manufar zantukan Mami amma sai ta ɓoye ga Humaira duk kuwa tana tunanin watakila itama ta fahimta kawai dai ba ta son fassara zancen yanda zai yi mata ƙuna a zuciya ne. *** Washegari kuwa ya kama ranar da za'a kawo lefen Humaira, tun safe Baba Amina ta iso sai shiri take yi don ma dai an ce maza ne za su kawo. Mami kuwa sai cin magani take yi ta ƙi kula koda gaisuwar Baba Amina balle ta sa ran samun maganar arziki. Raihana ya je makaranta don sun soma zane jarrabawa, su Muhsin ma duka ba sa nan. Mami ce zaune a galo sai Baba Amina a gefe ita da Jannat wacce duka ranta a ɓace yake sakamakon wayar da ta kammala da mijinta da ya rufe ta da faɗan lallai ta dawo kda ta ƙara koda kwana ɗaya don tare zasu yo ƙaura zuwa Nijeriya baki daya amma firr ta ƙi saboda bikin Humaira da ya tsaya mata a rai, burinta ta ga tsiyar da za a kawomata ga aikin da bokanta ya bayar take son aiwatarwa akan Humairar wanda zai sa ko bayan aurenta da Fadeel ta kasa samun kwanciyar hankali a gidansa, an tabbatar mata auren babu fashi hakan ya sa ta ɓullo da wata hanya daban na musguna mata duka don ta faranta ran Tasleem dake haukar son Fadeel amma ba ta samu aurensa ba. Kayan Humaira kawai za ta dauko saiti ɗaya ta kawo masa ya yi aikin da idan har ta sake ta yi amfani da kayan za ta tsani zaman gida kullum tana hanyar gantali koda kuwa ba za ta aikata wani shirme na banza ba. Tana da tabbacin muddin aikin ya ci toh fa Fadeel da ma yan uwansa za su tsane ta kuma ya rabu da ita. Suna nan zaune Mami da Jannat sun cika sun yi fam saboda Baba Amina dake kiran wayar sauran yan uwan Abban da ba su ƙaraso gidan ba akan su yi da jiki an kusa. A haka wayar Mami ta dauki ƙara, dubawar da za ta yi ba kowa ba ne sai Wizzy, ta dan saci kallon Jannat dake gefenta, ganin hankalinta na ga waya tana dannawa ya sanya da sauri ta mike ta shige ɗaki ta rufe kafin ta sa wayar a kunne. Cikin kwantar da murya kamar ba Mami ba take magana. "Haba Wizzy, meyasa kake son yimin azarɓaɓi a lamura ne? Ban fadamaka ka kwantar da hankalinka a soma sabgar biki ba idan ya so sai na sato maka shi na kawomaka?" A kausashe ya ce. "Ke Hajiya kina fa kawomin rainin hankali iri-iri, sai wani hankadomin hotunan yaro kike yi kina sanya soyayyarsa samun matsuguni a zuciyata toh kuma don me za ki wani ja min lokaci don za'a yi bikin ƴar dabar da ta kusa kashe ni?" Ta dan goge zufar goshin da ya karyo mata tana mai sauke ajiyar zuciya. "Ka dai yi hakuri, ni ai Maryam ba na daukarwa mutum alƙawarin da na san cewa ba zan iya cika shi ba. Ka kara hakuri zuwa lokacin komai zai tafi yadda kake so." "Shikenan! Kin ci darajar jikanki da na nunamaki ko ni ɗin waye. Zan ba ki daga nan har sati uku." "Babu damuwa. Amma don Allah ka bar kokarin kira koda ta whatsapp din ne, ka dinga hakurin na yi maka magana." Ya yi wata shegiyar dariyar shaƙiyanci. "Shikenan amma dai yanzu ki je ki daukarmin sabon hoton yarona ki turo na gani. Kar ki turon kala ɗaya." Ta ja guntun tsakin da take da tabbacin ba zai shiga kunnuwansa ba sannan ta amsa da ta ji. Bayan sun ajiye wayar ta soma jin haushin kanta, ko ta yaya za ta shiga yiwa yaron hoto, wannan yawan hoton da take yi har Ummitan kan iya gano wani abin muddin dai ba ta yi da gaske ba. Yarinyar akwai kaifin tunanin. Ta dai yi shahada ta fito zuwa dakin. Ba ta ko dubi Jannat ba da ma wasu baƙin da suka shigo ta nufi wurin Ummita. Ummita ta tarar ita ɗaya adalilin fitar da Humaira ta yi bisa rakiyar Raihana zuwa kasuwa siyayyar tsarabar da za ta kai Nijar, motar Abba ta kai su. Ganinta sai Ummita ta ɗan saki fuska. Kuka yake ta yi tana tsaye tana faman jijjiga shi ya ƙi yin shiru. "Ya aka yi me ya same shi haka yake kuka?" "Nima ban sani ba Mami, tun ɗazu ya ƙi ya yi shiru." Mami ta sa hannu ta karɓe shi. "Ina madararsa?" Kasancewar Abba ya siyo madarar gwangwani biaa shawarar Baba Amina tun a farko don ta ce nonon ba ya isar sa. Ta ƙarasa wajen feeder da ta haɗa madarar ciki saboda zafi sai ta sanya a kofi mai dauke da ruwan sanyi ta bar shi ta miƙawa Mamin haɗe da bif na sanyawa a wuya gudun ɓata jiki. Mamin ta shiga ba shi tana dan murmushin da bai kai zuci ba, can a ƙasan ranta ban da tsinuwa babu abin da take jifan Wizzy da shi. A cewarta duk shi ne ya cuce ta. Ummita ko ta yi shiru kawai amma jikinta ya yi sanyi, hakanan ta ji ba ta aminta da wannan kulawar daga Mami ba, Mamin da ko kallon arziki ba ta fiye bin Ahmad din da shi ba duka saboda ganin da ta yi tamkar ɗanta na soyayya da ita Ummitan. Wannan sabon sauyi da kuma hoton da ta ke dagewa wurin yiwa yaron sai yake ƙulle mata kai. Na farko dai Mamin ko status ba ta taɓa ɗorawa ba na yaron hakanan ba ta ga wani ko wata da Mamin za ta aikawa hoton ba balle har a kai ga ɗauka. Haka ta yi ta saƙe-saƙen zuci, can dai ta miƙe zuwa bandaki sanadin fitsarin da ya matso ta, koda ta fito hoton dai ta tarar Mamin na ɗaukar Ahmad, tana ganinta kuma sai ta wayance ta hanyar nunamata hoton. "Kinga wannan ɗa wato ya san Camera, ya yi ƙuri yana kallo kai kace ya san hoton za'a yi." Ta dan yi ƴar dariyar yaƙe amma ba ta ce uffan ba. Can kuma kamar an mintsili Mamin ta miƙe tsaye sannan ta miƙawa Ummita yaron. "Maza sanya shi a kafaɗa ya yi gyatsa. Ni bari naje daki naga wadannan ƴan karɓar lefen sun soma cika gida." Da sauri Ummita ga magantu. "Mami don Allah kiyi hakuri hakanan ki sanya hannu a auren Humaira." Ta tamke fuska. "Humaira ta nunamin ni ban isa da ita ba, ba ni ce uwarta ba. Me kike so kuma na ce mata? Ai shikenan, ni dai idan a tunaninta baƙin ciki nake yi don ba nawa aka aura ba to tabbas ta cutar da ni ta kuma dauki alhakin riƙon da nayi mata a ɗan shekarun nan. Ta je, aure dai ta yi shi ga tanan ga Fadeel din." Daga haka ta sa kai ta bar dakin. Ummita ta bi bayanta da kallo, sai take ɗan jin kalaman Mamin na shigarta, kodai dagaske akwai wani aibun na Fadeel wanda ba su da masaniya da shi? Haka ta yi ta saƙe-saƙen zuci akan ƴar uwarta da wanda za ta aura, wannan ya yi sanadin da ko zancen hoto ba ta ƙara tunawa ba balle ta yi. *** "Nifa ina ji a jikina ba wani abin arziki zai samyo wa yarinyar nan ba, ita da ake zargin ma ba cikakkiyar mace ba ce? Ki kwantar da hankalinki ai sun zo kayan su na can sashin Abbanku yanzu za a yo nan da su. Zamu ganewa kwarkwatar idanunmu." Jannat ke rarrashin Tasleem a waya da wadannan kalaman. Gaba daya ta hargitse wai ita dai Antin ta san yanda za ta yi Hamza ya rabu da ita ta zo ta auri Fadeel. "Hum, Anti kenan, bana jin a yadda yake mutuwar so da kaunarta zai iya yin karamin lefe." "Mtsw, ke kam akwai wauta wallahi. Toh an faɗamaki shi son daga lefe ake ganewa? Ke dai ki bari na aiwatar da abin da zan yi, koda ta shiga gidan na rantsemaki sai dai ta gaji ta nemi saki." Haka suka yi ta tufka da warwara akan baiwar Allahr da ba ta ji kuma ba ta gani ba. Guɗar da Jannat ta ji yo daga can falo ana rangaɗawa ne ya sanya ta fitowa daga dakin Anna da ta shige zuwa falon wanda tuni Annan ke zaune itama tana jiran ta sha kallo. Sai dai kuma nan da nan kallo ya kuma sama ganin yanda aka shiga shigo da akwatina daga daya biyu har sai da aka sauke set uku reras na kaya! Toh fa!! Zo ka ga idanun Mami wacce ba da son ranta ba ta fito sai domin Annan da ta yi mata magana kan ko yaya ta danne abin a ke ranta, ga kuma Jannat wacce tsabar bakin ciki da hassada sai da ta ji kwalla sun cicciko a idanunta. Ga Anna kuwa, jikinta har wani irin tsuma yake yi balle kuma a je kan uwa uba Mami wacce ta mike a mugun razane ta dakawa matar dake guɗa wata irin tsawa wanda sai da wuri ya yi tsit aka zubamata idanu.*LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* 09034973645 Da sauri kuma cikin yare Anna ta yiwa Mami magana. Nan da nan ta saita kanta. Ta juya zancen. "Ni na fada, yaron nan mugu ne, wannan kayan bai yi kama da na yaron arziki ba. Duka-duka nawa yake da har zai ci ace ya tara wannan uban dukiyar? Toh idan ku idanunku sun rufe ni Maryam babu tsiyarsa da za ta burgeni!" Wata mai kaudin bakin ta tare ta. "Haba Hajiya Maryam, babu kyau shaidar abin da ba ki da tabbacinsa. Ni wallahi ban taɓa jin an kushe wannan yaron ba sai daga wajenki." Mami ta dubi mai magana, wata abokiyar tsokanar Abban ce ana kiranta da Larai. "Ke Larai! Ki tsaya iyaka matsayinki. Dama irinki mai kwadayin abin duniya mai jiran ƙiris ai babu ta yadda za'a yi Fadeel ya taɓa laifi a wurinki. Inace har da ke ya kai wa ziyara a satin can ya sauke maki buhun shinkafa da mai? Toh bari ki ji na fadamaki, wallahi matukar ina raye ina wannan gidan babu mai aurawa Humaira ɗan yankan kai! Ashe kenan son da nake mata na banza ne matukar ba zan yi mata yaƙin abin da nake da tabbacin gaskiya ne ba. Yadda zan tsayawa Raihana hakanan zan tsaya tsayin daka akan ganin rayuwarta ta inganta." Jikin da yawa a wurin ya yi sanyi, wasu na tauna maganganun Mami su na shinshino ƙamshin gaskiya a ciki, idan ba gaskiyar ba ne, akan wane dalili ne zai sa yaron da aka ce bai ko haura arba'in ba zai mallaki maƙudan kudaɗen da zai haɗo gagarumin lefe akwati har saiti biyu. Wasu kuwa suka tafi akan zargin ba komai Mami ke gwadawa ba sai abin da ke ranta ƙarara wato hassada da baƙin ciki. Ai tun da take babu wata ɗiyarta da ta more irin wannan miji ga kyau ga kudi uwa uba kuma ƙuruciya. Baba Amina ce ta tari numfashin Mami gudun kada ta kawo musu abin da ba shi ba don da alama har zatukanta sun samu matsuguni a zuƙatan wasu. "Kiji tsoron Allah Maman Mubarak (Kamar yanda take kiranta), tun farkon soma munanan kalamai a kan Fadeel da kike yi, sai da Yaya ya sanya aka yi bincike sosai kuma aka tabbatar da komai nashi daidai da wurin aikinsa sai da ya tura aka kara tabbatar da shi din managarcin mutum ne mai kokarin kyautatawa na ƙasa da shi. Don Allah ko mene ne a ranki kada ki kawo mana shi anan, kar ki sanya a zargi abin da ba shi ba. Yadda aka fara komai lafiya a ƙare lafiya." Maganganun Baba Amina sai suka shafe zargin da wasu suka fara a zuƙatansu, suka kuma haskaka ko mene manufar Mami, wato dai ba komai ba ne face hassada. Mami za ta ƙara magana cikin azama Jannat ta rike hannunta gami da yi mata raɗa cikin yare a kunne. "Kar ki sake ki bada kanki a gabansu, za a tafi ana zunɗenki. Ki bar komai za mu samu mafitarsa." Ita kuwa Anna sai ta hau yiwa Mamin faɗan gangan, karshe ta goyawa Baba Amina baya, ita dai Baba Amina jinta kawai ta ke yi don ta san Anna ba kaunar Humaira take yi ba. Ta sha jin yanda yanayin mu'amalarsu take a bakin yaranta da kuma Ummita. Amma a yau matar ke cewa wai Humaira ba ta da miji sai Fadeel. Idanun Mami ba su raina fata ba sai da aka shiga fiddo tsadaddun lesuka da atamfofi har ma da mayafai, komai da komai da ake so a lefe babu ne kawai babu a ciki. Kayayyaki masu mugun tsada dai gashinan a gabanta tana gani kuma ba na kowa ba sai Humaira, yarinyar da ba ta taɓa jin ɓurɓushin kaunarta a ruhi ba. Guɗar Larai da ta cika wajen kusan ma da gayya take yi tana ambaton Allah ya sanya alheri, Humaira ta yi goshi. Mami fuu ta mike ta bar wajen, duk dauriya irin ta Jannat kasa daurewar ta yi, tun tana yaƙe har fuskarta ta koma ta ɗauru tamau kamar ƙullin goro. Ba don Anna ta dakatar da ita daga tashi cikin yare ba, da tuni itama ta bi sahun Mami. Sai bidiyon dole da ta dinga yi, koda aka kammala gani sai ta tura wa Tasleem da Futuha domin su sha kallo. *** Habawa! Ai wannan bidiyo ba karamin kaɗa ƴan hanjin Tasleem ya yi ba. Kuka da sheshsheka haka ta dinga yi tana kururuwar wallahi Humaira ba ta isa ta auri Fadeel ba. Cikin wannan yanayin Hamza ya risƙeta a ɗaki. "Tasleem lafiyarki kuwa? Anyi wani abu?" Gaba daya yana tambayar ne kirjinsa na dukan tara-tara, tsoronsa kada dai har wani ya yi masa shigar sauri ya fesa mata labarin aurensa. Dama da niyyar da ya shigo dakin da ita kenan, Hajiyarsa ta ce lallai ya sanarmata kafin wani magulmacin ya fesa mata. Ta fisge hannunta daga rikon da ya yi mata ta miƙe tsaye idanunta gaba daya sun rufe ta hau bambamin faɗa. "Kai Hamza! Kai ne silar rushewar mafarkaina, ka yi sanadin da na kasa samun cikar burina don haka na rantse maka ba za ka ƙara ɗanɗanar farin ciki daga gareni ba muddin ba ka sauwaƙemin igiyar aurenka ba!" Hantar cikin Hamza ta kaɗa , ya rasa meyasa yake ɗan shakkar Tasleem a wasu lokutan, ya dai aminta cewa duk inda masifaffen mutum yake ana ɗan shayinsa. Daga kalamanta ya ƙara tabbatar da zarginsa, wato wani munafukin ya kawo mata tsegumi. Zufa ta karyo mishi, ya mike a rude ya hau zuba kamar famfo. "Kiyi hakuri Tasleem, wallahi auren da zan yi ba don na ci amanarki zan yi shi ba. Ramlat ta jima tana zaman jiran..." "Dakata Hamza! Dakata! Wai wane yare kake yi? Na kasa gane komai! Yi yaren da zan ji na fahimta sosai! Uban waye zai yi aure sannan wace Ramlat ka ke magana akai?!" Ta yi maganar cikin fita hayyaci, ko kaɗan ta kasa fahimtar komai. A farko sai da razana ta sanya ta dauke wutar dole, ta ji wani dumm a kunnenta, ta dinga kallon Hamzan tamkar wani sabon halitta a gabanta. Kai tamkar a ranar ne ta soma ganinsa a duniya. Shi kuwa ya rasa me zai ce, ya aminta da cewar dai ya yi katoɓara, wato dai ba batun auren take yi ba. Sai ya sauke ajiyar zuciya. "Shikenan, abar zancen, meke faruwa ne kika..." "Anƙi a bar zancen! Wallahi sai an yi shi!!! Waye zai yi aure! Ka fadamin nace!!" Yanda take maganar cikin ihu da ƙarfi ya sa ɗiyarsu farkawa daga bacci a razane tana kuka, ko kallon inda take Tasleem ba ta yi ba balle ta kai mata agaji, shi ko Hamza da ya yunƙura da nufin zuwa ya ɗauke ta, ta yi sauri ta shiga gabansa ta cakumi wuyan rigarsa har necktie dinsa na zugewa ya fadi a ƙas don shigowarsa kenan ba jimawa daga asibiti, wurin Hajiyarsa kawai ya shiga kafin ya yo nan. Ya sa hannu ya fisge ta ya wancakalar. "Kina hauka ne Tasleem? Don nace aure shi ne kike yimin wannan borin? Ki tsaya fa ki ji, umarnin Hajiya ne wannan auren kin fi kowa sanin dai ni ba ni da  ra'ayin mata biyu." Ai kuwa wani tsautsayi za a ce ko suɓutar baki da ya kwashi Tasleem, sai ga ta nan ta narko wata ashariya ta narka ga Hajiyar Hamza, shi kuwa da ya ke yunkurin nufar Bebinsu dake kuka sai ya tsaya cak yana mai jin wani gingirim a kai. Tasleem dai ke zagin uwarsa mahaifiya da ta haifeshi? Da wata wawuyar zuciya ta kwashe shi bai san lokacin da ya nufe ta ba gadan-gadan ya hau jibga, tun tana ihu tana ƙunduma masa ruwan ashar har dai ta rasa bakin magana saboda kumbura mata baki da ya yi har yana fidda jini. Cikin sa'a sai ga wata goggwonsa ta shigo da zummar a gaisa ta ci karo da wannan mummunan abu, dakyar ta samu ya bar jibgar Tasleem. Amma ina da wata zuciyar ta kwashi Hamza sai ga bakinsa na furta kalmar saki ga Tasleem. Ta yi matukar razana don ba ta shiryawa hakan ba bagatatan! Duk irin ban baki da hakurin da Gwaggo ƙanwa ga Hajiyarsa ke bayarwa bai ko saurare ta ba, itama ta ji laifin na Tasleem ya girmama amma ba ta so sam ya kai ga saki ba musamman ma kasancewar a gabanta ne. Sai da ta ji dama ba ta shigo ba. *** Sai yamma likis Humaira da Raihana suka shigo gidan, wadanda suka yi saura  ba su wuce gida ba su na ganinta aka hau guɗa. Ita kuwa sai ta ɓoye fuskarta a kafadar Raihana suka ƙarasa ɗakin. Kuka sosai take yi, babu abin da ya fado mata a rai irin Ummita, irn hakan ce ta kusa faruwa tsakaninta da Sahabi amma al'amura suka rincaɓe. Koda suka karasa, Ummita ta rungume ta cikin wani irin murna na taya ƴar uwarta farin ciki. "Toh wai meye abin kuka don Allah?" Ta furta tana rarrashinta. Raihana ta yi dariya. "Ke kuwa na murna ne mana." Ita dai ba ta tanka musu ba, a karshe ma ta shige bandaki bayan ta ajiye ledar dake hannunta don ta kama ruwa. Wannan daren raba shi ta yi suna hira da Fadeel da ke faman zayyane mata irin kewarta da zai yi ba kadan ba. "Boddona, ba za ki iya ɗaga tafiyar har bayan aurenmu ba sannan muje tare?" Ta yi murmushi tana dan lumshe idanu domin dagaske ta soma jin bacci, sai hirar da shi ta ɗan kawar mata da damuwar maganganun Mami akan matukar ta auri Fadeel toh ta tabbata ta yi asarar ingantacciyar rayuwar farin ciki. Ita kuwa yanda take jin kaunar Fadeel ta amince da duk kalubalen da za ta fuskanta a dalilinsa. "Kin yi shiru." Ya furta cikin son jin abin da zai fito daga bakinta. "Ka yi hakuri, na faɗamaka ba jimawa zan yi ba, sati kawai Abba ya ɗibarmin." Sauke ajiyar zuciya ya yi. "Shikenan Boddo, amma lallai fa zan yi kewarki." "Kwana nawa ne zan zama mallakinka?" "Me kika ce?" Sai da ya faɗi hakan ne ta ankarar da suɓul da bakan da ta yi. Kawai sai ta rufe ido da tafin hannunta na hagu tana dariya ƙasa-ƙasa, ashe dai za ta iya mayar masa da martanin magana mai dadi? Shi kuwa a bangarensa fasalta irin farin cikin da kalamanta ya jefa shi ciki ba zai yiwu ba, koyaushe shi ne mai amayar da abin da ke ƙasan ransa ita kuwa ko oho sai dai ta bi shi da Hum, um, eh ko aa. Sai hakurin da take yawan ba shi idan ya yi wata ƴar ƙorafin ko ya ya. Haka suka raba dare su na hira a karshe ya dinga magana ya ji shiru sai hucin numfashinta da ke amsa kuwwa ta cikin wayar, anan ne kuma ya fahimci  bacci ya yi awon gaba da ita. Dole hakanan ya hakura shima ya katse kiran. *** Bisa shawarar Mami, Tasleem ta ƙi zuwa gidan saboda tsoron haɗuwa da Abba sai kawai ta sauka a gida Futuha. Tun zuwanta babu abin da suke zantawa sai lefen Humaira da ya bi ya tsone musu idanu. Futuha ta yi kwafa.   "Ki rabu da yar iska, yanzu za ta soma yiwa mutane fiffika tana ganin duka ta fi mu. Ni fa wallahi zan so ace yanda kika fito daga gidankin nan ke kika aure Fadeel din ko ba komai mu ga ta tsiya." Fadin haka ran Tasleem ya ɗan yi sanyi. Ta ji ashe Futuhar na kaunarta da alheri ba kamar ya da ta zata ba a baya. "Hum, bari ke dai yar uwa. Nima dai zan so hakan ta kasance amma Abba kinsan shi zai toshe dukkan wata kafa da mutum zai yi wancakalarsa a rayuwa. Ni wallahi a baya Mami nake zargin ba ta sonmu amma yanda ta hakikance akan ba ta son auren Fadeel da Humaira yasa na ƙaryata zargi. Abba shi ne mugun." Futuha cikin yanayi na suɓutar baki da kuma dadin zance ta taso. "Ke! Inji wa? Wallahi toh kf duniyarnan ba mu da masoyiyar da ta wuce Maminmu. Kinsan irin sadaukarwar da ta yi duk don mu samu rayuwa ingantacciya?" Ba ta jira jin ta bakin Tasleem ba ta shiga ɓaro zance babu ƙaƙƙautawa. Sai da ta ba Tasleem labari kaf na irin abubuwan da Mami ta yi a rayuwa sannan ta yi shiru. Dama zancen ya jima yana cinta a rai, ita ta tsani ka ba ta sirri don sai da ta yi dagaske ta ke iya riƙeshi. Tasleem ta ji zantukan tamkar a mafarki har dai sai da ta ƙara matsawa kusa da Futuha. "Idan wasa kike yi kinsan Allah bana son irin wannan." Tsaki Futuha ta ja kafin ta rantsewa Tasleem cewa dagaske ne kuma Mami da bakinta ta faɗa mata. Wani ihun murna mai cike da al'ajabi Tasleem ta yi, tana mai ji a ranta cewa dole ta fesawa Anna da Jannat ko don su bar ganin laifin Mami sannan Anna ta ƙara samun tabbaci akan babu abin da ya sauya daga Maminta. Jin Futuha kawai take yi tana jaddada mata kada ta sanar da kowa komai ta rike sirrin Mami, ita dai ta bi ta da toh, tana kuma da yaƙini akan ai Jannat da Anna masoya ne ga Mamin, lamarin sosai zai yi musu dadi. *** Washegari tun da asuba Humaira ta yi wankanta tsaf ta shirya cikin wata atamfar super da Mami ta ɗinka mata. Sai da ta kammala shiri tsaf su Ummita na zaune da Raihana cikin jimamin tafiyarta ta bar su, ta karasa ta dauki inda Ahmad ke shimfide ta ta sumbaci goshinsa sannan ta gyara masa lulluɓi. Suka kara yin sallama da su Ummita, daga bisani suka yo mata rakiya. Mami na sashin Abba, Abban yana falon Mami yana jiran Humaira ta fito ya je ya sanya ta a mota. Sai da suka gaisa sannan ya ba ta umarnin su tafi. "Abba zan yiwa Mami sallama." Ya girgiza kai. "Bacci take yi kwa yi a waya." Ko kadan ba ta so haka ba, tana da tabbacin akwai abin da ke faruwa. Maganar Abba karo na biyu akam ta kama hanya su tafi ya sanya dole ta bi umarninsa ta yi gaba bayan sun kara yin sallama da su Ummita tamkar kada a rabu. *** Mami dake kallonsu ta windon Abba ta saki labule cikin huci ta furzar. Wayarta ta fiddo ta dannawa Wizzy kira. "Kana buƙatar ɗanka, ni kuma ina buƙatar ka cikamin wannan aiki da na sanyaka ya kasance na ƙarshe." Ya yi wata muguwar dariya yana hangen motar Abba da aka buɗewa ƙyaure ta fito. "Ai ki sha kuruminki Hajjaju, a yau babu su babu kwanan duniya." Ta jinjina kai tana murmushin mugunta. "Dakyau! Sai na samu kyakkyawan labari." Daga haka ta katse kiran, Raihana dake yunƙurin shigowa ta ja baya tana mai riƙe kirjinta da ya tsananta bugu, kalmar innalillahi shi ta shiga ambato domin kunnuwanta sun kasa gasƙata abin da ta ji na fita a bakin Mami. A cikin sakanni kadan ta dawo hayyacinta, da wani irin azama da gudu ta bar wurin zuwa dakinsu hannunta har kakkarwa yake yi wajen danna waya. Ummita na tambayarta ko lafiya sai dai ina! Babu baka sai kunni. Wayar Abba ta kira, ringing biyu ya ɗaga da sallama. Yana tafe tana tuƙi lokacin har ya fita zuwa babban titi. "Ab..ba..ba.." "Lafiya Raihana? Meyafaru?" "Abba za a kashemin ku, ka tsaya ka juyo gida." Madadin ta ji razani a muryar Abban sai ta ji kamar ko a jikinsa. "Kar ki damu Raihana, babu mai tsallakewa kaddararsa. Amma ki sani, ina da labarin da kika tsinta ko kuma kika ji a yanzu tun a daren jiya ya risƙi kunnuwana. Na sanar da D.P.O tun a daren jiya ya kuma bani shawarar da ta dace. Ina tare da rakiyarsu. Kin ji ko?" Humaira dake gefe ta kasa gane zantukan da Abba ke yi, kirjinta sai duka yake. Abba kuwa bai jira cewar Raihana ba ya katse kiran. Tun daren jiya ya tsinci wayarbda Mami ke yi da wani inda take ba shi umarnin kashe shi da Humaira gaba daya. Har gari ya waye ya kasa tufka da warwara, ga mamaki mai tsanani da ya kewaye zuciyarsa. Ya ka sa gasƙata cewa Maryam ce da wannan yunƙurin. *** Can ɓangaren Wizzy kuwa, yana tafe a bayan su Abba sannu da sannu don ya cimma su a inda ya gama dukkan wani tanadi da shiri, har a lokacin duhun asubahi bai gama washewa ba. Kallon da zai yi ta mirrow ya hangi motar dake biye da shi a baya, ganin da ya yi duk inda su Abba suka kurɗa a mota shima ya kurɗa ana biye da su ya sanya shi buga sitiyari, ya tabbata ko wace motar ce ba zai wuce na masu tsaro ba, zarginsa bai gama tabbata ba sai da ya ga yana shan wata wawuyar U turn an bude gilashi an bishi da harbi sai da aka fasa gilashin motarsa ta baya. *** Mami ta fito afujajan daga bandaki daure da zani jiki duk kumfa da azama ta nufi wayarta dake faman ƙara, ganin Wizzy ya sanya ta murmusa don ta san haƙanta ya cimma ruwa. Sai dai me? Wani wawan ashariya ya jefa mata. "Kin janyo an kusa kashe ni a madadin na kashe?! A gidan uban wa ƴan sanda suka sami labarin nan?" "Me kake nufi? Ban fahimta ba?" Ta jefa masa tambayar a rikice, ya yi mata bayani yanda za ta gane. Ya kara da fadin. "Ke Madam, na baki nan da gobe ki gaggauta kawomin ajiyata idan kuwa ki ka yi wasa da hankalina zan zo har cikin gidan na ga uban da zai hana ni ɗaukarsa! Useless kawai!!" Daga haka ya katse mata wayar, Mami kuwa ai sai ta ji kafafunta sun dauki rawa, toh waye ya san da zancen da har maganar ta isa kunnuwan ƴan sanda? Ta ya ya hakan ta kasance? Duk iyaka tunani da zarginta ta kasa fahimta, a iyaka saninta sadda take waya a falon Abba yana dakinsa yana bacci, koda ta kammala ta shiga yanda ta bar shi hakan ta tarar da shi. Toh waye wannan da ya ji sirrinta? Sai ta zaɓi shigewa banɗakin don ta ƙarasa wanke jiki a gaggauce ta je ta duba mutanen gidan ko za ta samu wata shaidar. *** Fadeel ya ƙurawa hoton da Ridwan ya aikomasa idanu, hoto ne na wacce ake zargi da yin ɓatanci ga Ummita da Humaira, kamar ya san fuskarnan sai dai ya kasa tuna inda ya santa. Sai ya zaɓi buɗe ɗayan hoton na bayanin da Ridwan ya turo masa. Sunan ya sanya shi miƙewa tsaye babu shiri. JANNAT MOHAMMAD AGADEZ. Tabbas idan idanunsa ba su gane mishi ƙarya ba, ita ce dai ƙanwar Mami daya taɓa gani a gidan su Humaira har ta ke jajanta masa lamarin ɓatan su Humaira. Kai ya sha ganinta ma ba sau daya ba ba biyu ba. Wannan shi ne ana zaton wuta a maƙera...*LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* 09034973645 "Abba lafiya?" Tambayar da Humaira ta yi mishi hankali tashe jin ƙarar bindiga ga kuma juyin da motar dake bayansu tayi babu shiri. "Kwantar da hankalinki. Babu komai." Yana fadin hakan ya gangara gefen titi ya tsaya, motar su D.P.O su dinma fakawar suka yi don sun tabbatar ba za su samu damar cafke mutumin ba. "Ina zuwa." Abin da Abban ya ce kenan kafin ya bude motar ya fita. Humaira dai har wata zufa ke karyowa a goshinta, kirjinta kuwa bugu yake yi ba ƙaƙƙautawa, babu abin da ya faɗo ranta sai waɗancan mugayen masu garkuwar da suka kama su. Waigen Abba kawai take yi tsaye da wanda ta tabbatar ɗan sanda ne don ta gan shi ba sau ɗaya ba kuma ba biyu ba a gidannasu duk da cewar bai sanya kakin aikinsu ba. Hakanan sauran mutane biyar da ke tare da shi babu kayan aiki a jikinsu. D.P.O Alhussain ya dubi Abba dakyau. "Kar ka damu Alhaji, in sha Allahu zai zo hannu. Mun kwafi lambar motar zamu tsaurara bincike ta yadda komai za ya bayyana a zahiri. Amma Alhaji a shawarce ina so ka ɓoye batun kawo maku harin nan da aka yi koda kuwa ga iyalinka ne sannan abin da ka fito da niyyar yi kada a fasa shi yin hakan zai bada wata ƙofar da za a ƙara yin wani shirin nan gaba. Zamu yi bincike sosai har mu gano waye." Abba ya jinjina kai har a sannan cike yake da ɗumbin mamakin Maryam wanda ko a mafarki ya ga za ya aikata makamancin hakan zai ƙaryata a yayin da ya farka. Dakyar ya daurewa zuciyarsa suka yi sallama da D.P.O sannan ya koma ga motarsa ya shiga. Murmushin ƙarfin hali ya sakarwa Humaira wacce wayarta ke ta ƙarar shigowar kira daga Fadeel amma tsabar ruɗani ya sanya ba ta ko fiddo ta a jaka ba ballantana ta kai ga ɗagawa. "Abba mu koma gida don Allah. Na fasa tafiyar." Kallonta ya yi, sosai sai ta ba shi tausayi, ko ya za ta yi idan ta ji abin da ke faruwa ko kuma ya yi nufin afkuwa garesu kuma daga wacce suka yi amannar har abada ba za ta taɓa cutar da su ba? Sai ya girgiza mata kai cikin murmushi na ƙarfin hali ya amsa. "Aa Mamana, babu inda za mu juya. Muje na sanyaki a mota, kada ki damu nasan direban kamar yanda na faɗamaki ɗa ne ga tsohon Maigadin ɗan uwana. Yana da amana, na kuma sani sai dai abin da Allah ya riga da ƙaddarawa zai afku toh wannan babu wani mahaluƙin da ya isa ya tsallake. Ki kwantar da hankalinki in sha Allahu lafiya kalau za ki je ki dawo kinji ko?" Da kalaman Abba masu ƙarfafa gwuiwa kuma lokaci guda masu karya zuciya ta ɗan samu sassauci, ko ba komai ya tunasar da ita abin da ruɗani ya so ya mantar, wato ambaton Allah. Abba kuwa tuƙi kawai yake yi amma gaba ɗaya yanayinsa ya nuna yana cikin damuwa mai ɗumbin yawa. Humaira dai hankalinta ya rabu kaso barkatai, abin da ya faru yanzu da kuma yanayin Abba sai ko kirjinta dake faman bugu tun faruwar al'amarin. Abba kuwa ya damƙa ta a hannu na amanan, Rabe. Mazaunin gaba ya zaɓar mata ita ɗaya yadda ba za ta takura ba, duk kuma yadda ya so Raben ya karɓi kudin motar ƙi ya yi saboda karamci da kuma albarkacin Marigayin da ma shi kansa Abban wanda zai wahala su kai mishi wani kuka nasu ya ƙi yi ba idan da halin yin. Sosai Humaira ta yi kuka da suke sallama da Abban domin sai da ta ji tamkar kada su rabu. Sai dakyar Abba ya samu ta nutsu ya yi mata ƴar nasiha har da zolaya kafin ta saki ranta. Bayan tafiyar Abban ta fiddo wayarta don ta kira su Raihana sai ta tarar da missedcalls har goma sha, wasu daga Raihanar wasu kuwa Fadeel ne. Kafin ta kai ga wani yunkurin sai ga Fadeel ya ƙara kira. Tana ɗagawa da sallama ya rufe ta da faɗa. "Meyasa Boddo! Meyasa za ki tsoratar da ni wai?! Raihana ta kirani a ruɗe ko na yi waya da ke nace aa, mun gwada kiran wayoyin Abba a kashe. Ina kike yanzu ganinan a hanya." Ta tuna dagaske wayar Abban a kashe take tun amsa wayar Raihana da ya yi tana ganin sadda ya kashe ta gaba daya. Ko kusa faɗan Fadeel din bai yi mata zafi ba, ta sani damuwa da lamarinta ne ya yi silar hakan. "Ka yi hakuri, wayar tana cikin jaka, ina tasha har na shiga abin hawa." "No ki jira, ni zan zo na kaiki." Cikin sauri ta girgiza kai tamkar yana gabanta. "Aa wallahi, ka yi hakuri dai tunda har Abba ya san direban kuma sun gama magana." "Wace tashar ce?" Abin da ya nemi sani kenan kawai, ta faɗamasa sunanta daga nan ya katse kiran sai lokacin ne kuma ta samu damar kiran Raihana. Jin muryar Raihanar a shaƙe ya sanya ta tabbatar da ta san komai. "Raiha, kiyi hakuri wayar tana jaka." "Babu komai, Abba ina ta kiran wayarsa a kashe. Lafiya ku ke?" Ta yi tambayar cikin kokarin kwantar da murya da ɓoye damuwa bisa shawarar Ummita. "Ba mu jima da rabuwa ba, ya juyo ya taho gida." "Toh, Allah ya tsare ya kiyaye hanya. Zamu yi kewarki ko ince har mun fara." Ta dan yi murmushin ƙarfin hali. "Nima haka Raiha, a gaidamin Ummita da Ahmad. A sanya mu cikin addu'a." Daga bisani suka yi sallama, tana nan zaune har ya yi saura bai fi mutum biyu motar ta cika ba sai idanunta ya sauka kan Fadeel dake tsaye ya yi shigar tshirt fara ƙal da maroon wando na Adidas. Sumar kansa idan ka ƙura idanu za ka fahimci ko tsayawa taza bai yi ba. Sai rarraba idanu ya ke yi a tashar, sai ya ba ta tausayi da kuma murmushi lokaci guda. Ta dan yunkura da zummar buɗe ƙofa ta fito idanunsa suka shiga cikin nata, da azama ya ƙarasa ita kuwa tuni ta bude murfin ƙofar. Ya sa hannu ya riƙe murfin gami da durƙusawa su na fuskantar juna, ta kauda idanunta ta maida ga kallon gaban motar. "Barka da asuba." Abinda ya fito daga bakinta kenan. Madadin ya amsa sai ya yi shiru yana ƙaremata kallo. Can dai ta juyo, daidai lokacin Rabe ya karaso. "Ranki ya dade kin san shi ne?" Fadeel ya kalle shi sai kuma ya miƙa hannu suka yi musabaha. "Eh na san shi." Sai a lokacin ya dan murmusa. "Waye shi?" Ya tambaya, Rabe dai na tsaye kallon ikon Allah, ya dai fahimci ko waye daga yanayin kallonsa da nata, ita din cike da jin nauyi da kunya, yayinda shi kuwa kallonta yake morewa, ga duk wanda ya kalle shi kuwa zai gane ba ƙaramin nisa ya yi a kaunarta ba. Ta ɗan bishi da hararar wasa, Rabe kuwa ya yi ƴar dariya. Fadeel ya dube shi. "Aurenmu nan da sati biyu in sha Allahu. Ina gayyatarka." Nan da nan ya ƙara washe haƙoransa wadanda yawan yin asuwaki ya sanya ba su dafe ba. "Sai Oga, ina taya murna. Allah ya nunamana lokacin." Daga haka ya yi gaba ya bar su. Fadeel ya harareta kadan, ta yi mishi kyau, fatarta ta ƙara gogewa sakamakon mayukan gyara fata marasa haske da Baba Amina ta kawomata har ma da na wanka da take amfani da su. "Kin yi kyau. Sai dai meke faruwa ne naji kamar Raihana na cewa an yi attacking ɗinku? Ban fahimci komai ba." Sai a lokacin ta tuna tashin hankalin da suka tsallake cikin ikon Allah. Tunaninta kuma ya tafi ga son gano yanda aka yi Raihana da ke zaune a gida ta san da wannan magana, toh waye? Ko dai na gida ne? Ɗan ƙas da ya yi da yatsunsa saitin fuskarta ya maido ta hayyacinta. "Kin wani zubamin idanu ina tambayarki. Kwana nawa ne zan zama mallakinki?" Ya karashe da wani kalar kallo da ma murmushi. Ita sam ba ta ma san cewa idanunta a kansa ta tsayar ba. Sai ta ɗan yi wuri wuri da idanunta tana kallon mazauna bayan motar, macen ma hankalinta na ga wanda ta ke da tabbacin mijinta ne su na kwasar hirarsu. "Ki bani labari idan wani abin ya faru da ku a hanya." Nan da nan ta labarta masa komai da ta ji kuma ta gani, ya dan yi shiru yana nazarin zantukan, akwai dai alamar tambaya babba. "Antinku Jannat na gida ko ta tafi?" Tambayar da ya watsa mata kenan, shi gaba daya yanzun bai yarda da Jannat din ba, matar da son zuciyarta zai sa ta yi yunkurin munana sunan wadanda ba su yi mata laifin komai ba, toh za ta aikata abin da ya fi hakan. Ga Humaira kuwa jin tambayar ta yi wani bambarakwai, da ace ma Fadeel din nada labarin takun saƙar da ke tsakaninta da Jannat toh za ta kawo dalilin da yasa ya ambace ta a wannan gaɓar kenan, amma sanin da ta yi koda wasa ba ta taɓa buɗa masa sirrikan cikin gidansu ba ya sanya ba ta kawo wani abu a ranta ba sai dai ta yi mamakin tambayar. "Eh tana nan sai bayan biki za ta koma." Ya jinjina kai. "Alright, hakan ya yi daidai. Ba don Abba ba, ni da kaina zan kai ki wurin su Kawu. Amma babu komai, wannan ne tafiya ta ƙarshe da za ki yi ke ɗaya ba tare da ni ba a rayuwarki in sha Allahu." Ta ɗan yi ƙasa da kanta tana wasa da zoben hannunta. Zuciyarta ban da soyayyar Fadeel babu abin da ke yawo cikinsa. "Inda muke bai dace mu cigaba da hira a haka ba. Zan dinga kiranki har zuwa lokacin da wayarki za ta daina shiga sai dai please kina isa ki sanya layin can ni ki yimin koda flashing ni kuma zan kiraki. Kinji?" Ya ƙarashe a raunane, ta ɗan kalle shi, rabuwa ko yaya take ba ta da dadi. Ta kawar da kai. "In sha Allah." Abin da ta ce kenan kawai, ya miƙe gami da fiddo ƙaramar envelop a aljihin wandonsa ya ɗora saman ƙaramar jakarta dake kan cinyoyinta. "Bon Voyage." Daga nan bai ba ta damar cewa komai ba ya rufemata ƙofar ya yi gaba. Ta bishi da idanunta da suka cicciko da kwalla, kamar ta ce masa tana sonsa ko hakan zai saukaka masa dumbin kewarta da take da tabbacin zai ji, sai kuma ta ji harshenta ya yi nauyi, a hankali kuma cikin zuciyarta ta furta 'Ina sonka sosai Fadeel.' Amma a fili juwa envelop din kawai ta ɗauka ta sanya a jaka ba tare da ta duba abin da ke ciki ba. Mintuna bai fi uku ba fasinjojin suka cika motarsu ta tashi bakinta dauke da addu'a. *** Ummita ta fito daga banɗaki idanunta sun ɗan tasa sai dai ba su kai ga na Raihana ba wacce har lokacin kuka take yi tamkar ranta zai fita duk kuwa da wayar da ta amsa na Humaira ya ci ace ta samu sassauci amma ina abin ya fi ƙarfinta ya shallake dukkan tunani. Ta ƙarasa gefenta ta zauna. "Ya isa haka Raihana, kinga ɗazu kin daure da Mami ta shigo ba ki yi wani abun da zai ɗagamata hankali ba asalima baccin gangan kika yi. Yanzun kuma kin kasa nutsuwa, tambayar duniya nayi maki akan ki faɗamin wanda ke kokarin kashe su Abba kuma a ina kika ji amma kin ƙi. Lafiya lau muka yiwa Humaira rakiya amma yanzu kin hargitse. Kin tayarmin da hankali, daure ki faɗamin ko ma me ake ciki please." Raihana sai ta ji kamar Ummitan ta ƙara mata giyar kukanta, ta ina? Kuma da wane bakin? Kai wane hankalin ne ma zai dauka alhalin nata hankalin ma ya kasa, sosai take faman ƙaryata kanta amma wata zuciyar na kwaɓarta da ƙara haska mata al'amarin sakamakon kunnuwanta dake mata amsa kuwwa da muryar Mami wacce ke ƙara jaddada cewa a kashe Abba da Humaira. Toh idan ita ta kasa ɗauka, ta ya ya za ta fara yiwa Ummitan bayani ta gasƙata ta? Ta ya za ta ce mata ai Mamin da ta riƙe su matsayin ƴaƴa na cikinta ita ke barazanar kashe musu uba da kuma ƴar uwa? "Shikenan Raihana, tunda ba za ki yi magana ba. Kuma ba za ki bar kukannan ba zan je na sanar da Mami, ba za ki bar ni cikin tashin hankali da canki canka ba." Ummita tayi maganar cikin fidda tsammani da kuma yunƙurin miƙewa don aiwatar da abin da ta ce. Cikin sauri Raihana ta riƙo hannunta tana mai girgiza mata kai. Ummita ta fahimci ko mene ne ba ƙarami bane, za ta iya rantsewa rabon da ta ga Raihanar cikin wannan yanayin tun sadda suka kuɓuta daga hannun ƴan garkuwa. Kai ba ta jin ma tashin hankalin ya yi kamar wannan. Gaba daya fuskarta ta yi ja ga kuma jijiyoyin goshinta da suka fito raɗau, kuka sosai da majina. Cikin dusasshiyar murya ta ce. "Kiyi hakuri zan fadamaki komai amma sai da iznin Abba. Ko kuma ki bari kya ji daga bakinsa. Kar ki faɗawa kowa komai." Ta karashe tana ƙara fashewa da kuka, Ummita cikin hawayen ta ce. "Shikenan, amma na rantse idan ba ki bar kukannan ba zan je yanzu na kira Mami." Raihana jin zafin sunan Mami da Ummitan ke faman ambata ya sanya ta mikewa tsaye cike da jin wani ƙarfin da ta nema ta rasa a mintocin baya. "Na daina, nace ki bar ambaton sunan kowa, kiyi hakuri Abba yace kada zancen ya fita. Bari na wanko fuskata." Daga haka ta yi hanyar bandaki, ita kuwa Ummita bin ta da idanu ta yi baki a hangame, yanayin yanda ta bada amsa a fusace ne ya sanya ta kallonta. Ta sauke ajiyar zuciya gami da share nata fuskar. Za ta yi hakurin ji daga bakin Abban ko mene ne. *** Anna da Jannat su na kwance su na bacci jin an bankaɗo kofa da ƙarfi ya yi sanadin farkawarsu a ɗan razane. Tsaki Jannat ta ja ganin Mami tsaye sannan ta juya kai ta ƙara lulluba da ƙaton bargo. "Maryama lafiyarki kuwa? Anyi wani abu ne za ki shigo a haukace?" Mami wacce ke bin su da kallo cike da nazari gaba daya ta fita hayyacinta, ita dai hankalinta ya kasa kwanciya. Toh uban waye ya sanar da ƴan sanda ƙudurinta idan aka ce duk jama'ar gidan bacci suke yi? Ta sauke ajiyar zuciya na wahala. "Babu komai." Daga nan ta sa kai ta fice ta maida musu ƙofar ta rufe, kafin ta bar wajen sai da ta tsaya jikin ƙofar ta kasa kunne shiru tana son ji kodai za su ce wani abu amma ba ta ji komai ba wannan ne ya sanya ta nufar dakin samarin yarannata don nan din ne kadai ba ta leka ba. Kwankwasa kofar ta yi niyyar yi sai ta fasa gudun kada wanda ya yi wani yunkurin ya ji motsinta, ta bude ta leƙa kadan, bacci suke yi daga Yassar har Dawud, hankalinta ya kai ga Kassim wanda ya juyawa ƙofar baya, ta ɗan yi ƙuri da idanu don son tantance abin da ya dauke masa hankali a waya yake kallo. Muraran ta hango mummunan abu na yawo a kan wayar, bidiyo dai na haramtacciyar zina na jinsi shi yake kallo, hankalinsa sosai yana ga abin da yake yi har sai da gigitaciyar ƙarar da ta saki ya farkar da Dawud da Yassar, Ƙassim kuwa da wani irin firgici da rawar jiki ya yi cilli da wayar. Ya yi daidai da shigowar Abba gidan, yana tsaye da jami'an tsaro na SS da suka zo tafiya da Jannat su na magana ta fahimta, Abban na cikin muguwar kaɗuwa na jin wannan sabon al'amarin, suka tsinci ihu da kururuwar Mamin. Gaba ɗaya suka nufi ciki da gudu-gudu har Abban don ganewa idanunsu abin da ya faru kasancewar ɗakin samarin dab da waje yake.*LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* 09034973645 Yassar ne ya yi kan wayar da Ƙasim ya yi cilla da ita ya dauka, shi kuwa Ƙasim da gudu ya tafi don ɓuya a bandaki jikinsa na mugun kaɗawa tsabar firgici cikin sauri Mami ta karasa ta rike shi gami da watsamasa mari hagu da dama. "Innalillahi wa inna ilaihir raajiun! Kassim mene haka nake gani?" Yassar ke ambato hannunsa da yake rike da wayar har rawa yake yi, Dawud ya karasa ya karɓa ai kamar wanda aka jonawa wutar lantarki sai ya yi jifa wayar. Ya yi daida da fadowar su Abba ɗakin. Mami idanunta sun rufe ruf ta cakumi vest din dake jikin Ƙassim tana girgiza shi tana kuka take fadin. "Don ubanka sai ka faɗamin inda ka koyi kallon banzan nan?! Kana neman jinsi ne? A gidan uban wa ka ke yi?!!" Maganar ta saukarwa Abba kamar wata kibiya a ƙahon zuciya. "Ke Maryam, me kike magana a kai ne?" Sai a sannan ta san ma da Abba a ɗakin, ta dube shi cikin rufewar isanu har ma ba ta tuna tare ya ke da wani balle ta tuna tashin hankalin da take ciki na rashin cikar muradinta ta soma magana. "Ka cuce ni Yusuf! Tsaurin daka yiwa yarannan na hana su abin kashewa shi ya janyo Kassim kalla-kallacen bidiyoyin luwaɗi. Ni dama na jima ina zarginsa da matasan yaran gidan Alhaji Tsalha! Ance yaran ba su ji kuma abin da suke aikatawa kenan amma nayi magana ya ƙaryata ni, kuma ka hana shi mu'amala da su ya ." "Ke! Ya isa hakanan!" Abba ya tsawatar ganin kamar ba a hayyacinta ma take zantukan ba ga Ridwan da ya tsaya cike da jinjina wannan lamari. Sai kuma ya ɗan kalli Ridwan din sannan cikin karfin hali ya ce. "Ki bar zancen zan san ta yanda zan ɓullo masa, yanzu dai ki shiga ki kira Jannat ina son ganinta." Mami ta ji wani malolon bakin ciki, wato yana nufin dai ba zai matse bakin ƙassim din ba ta ƙarfi a ji ko me kenan da har ra'ayinsa ya tafi ga kallon zina? Sai kawai ta sa kai ta bar ɗakin, Abba ya bi ta da kallon kin ban mamaki kafin ya mayar da hankali ga Ridwan wanda cikin nutsuwa yake yiwa Ƙassim tambayoyi kai ka ce don shi ya zo. Nan Kassim cikin zubar hawaye ya soma magana bayan ya yi rantsuwar bai taɓa aikatawa ba ya ƙara da fadin. "Sosai suke kashemin kudade don son na saki jiki da su na bi sahunsu, ni kuma na nunamusu ba zan aikata hakan ba shi ne ni kuma bisa zugar su Usha na soma kallon bidiyoyin don na ga abin da suke aikatawa. Abba don Allah ka yafemin, wallahi tallahi ban taɓa aikata kowace kalar zina ba balle kuma ta jinsi." Kuka sosai ya sanya a ƙarshe dukkan gaɓoɓin jikinsa babu inda ba ya kakkarwa. Abba dai ya kasa magana saboda tsananin kunyar Ridwan da kuma baƙin cikin gurɓacewar zuri'arsa da ya rasa ta inda aka haihu a ragaya. Ya dai san cewa jarrabawarsa kenan. Ridwan ne ya dinga yiwa Ƙassim nasihohi masu ratsa jiki. Kassim sai da a karan kansa ya yi nadama ya kuma yi alƙawarin fita a hanyar su Usha da yan uwansa. Da wannan Abba ya ce Ridwan su ƙarasa ciki aiwatar da abin da ya kawoshi. *** Jannat ko a kanta ba ta taɓa zaton wani abu ne ba don Abba ya yi kiranta, saboda Mami ranta a ɓace yake ne da batun Ƙassim da kuma rashin nasarar da ta yi sai ta ma kasa tsayawa yi mata wani bayani dogo, tana isar da saƙon ta fice ɗakinta don tunanin mafita. *** Ta karaso falon, Abba dai kallonta kawai yake. Ga ta dai mutum har mutum a fuska, matar da yake yiwa kallon kanwarsa Amina, koda alama babu wani abu wai wasan ƙanwar mata tsakaninsu face girmamawa da nuna damuwa ga dukkan wani abu daya shafi al'amarin iyalinsa. Bai manta ba, faruwar lamarin na ɓacin sunan su Ummita takanas ta kira shi a waya tun daga Misra ta jajanta masa har da yin Allah ya isa ga duk wanda ya aikata laifin. Ita kuwa Jannat ta bi mutanen da kallo sannan ta mayar kan Abba, gaba daya sai kuma ta ɗan sha jinin jikinta. Da murmushin yaƙe ta gaida Abba. Madadin ya amsa sai ya ce. "Ga baƙinki nan." Ta gaishe su, ta kara da fadin. "Toh, sannunku. Sai dai ban gane fuskokin ba." Ridwan ya murmusa yana mai fiddo Id card dinsa na aiki ya nunamata. "Sunana Ridwan Bello Jafar, ma'aikacin SS ne. Mun zo tafiya da ke bisa kama ki da laifin ɓata suna." Ai sai ta ji kamar ta saki fitsari a wando, iyakar dakiya ta dake wajen ɓoyo razanarta. Ta dubi Abba wanda idanunsa ke tsaye ƙurr a cikin nata sannan ta dubi Ridwan da yanayin basarwa ta ce. "Ɓata suna kuma? Me kake nufi? Sunan wa na ɓata? Sannan waye ya baku iznin kama ni?" Ya nunamata shaidar izinin kafin ya amsa. "Ga shaidar iznin tafiya da ke Madam, ɓatancin sunan da nake nufi ba kowanne ba ne sai wanda kika yi ga Ummita da kuma Humaira. Muna da evidences da muke da tabbacin komai da kika aikata, sauran bayanin idan mun je can za ki ji. Ki bamu hadin kai kawai ki bi mu mu tafi." Shikenan! Ta faru ta ƙare wai an yiwa mai dami ɗaya sata. Zufa ya shiga yankowa Jannat ta ko'ina a fuskarta, ta hau girgiza kai cikin tsananin ruɗewa da tashin hankali bisa kokarin ta ga ta kare kanta amma banda kalmar ƙarya ne babu abin da bakinta ke iya furtawa. Ga Abba da ya yi mata ƙuri da idanu yana dubanta, har lokacin jikinsa a mugun mace yake. Wannan wane irin zuri'a ne ya yi aure a ciki? Daga Maryam har Jannat sun jefa shi cikin ɗumbin mamaki da kuma tsoron halayyar DAN ADAM. Ban da kalmar Innalillahi...babu abin da yake ambato a can kasan ransa. Ummita dake tsaye riƙe da ɗan ƙaramin kofi mai murfi da ta haɗowa Raihana shayi ta tsaya cak cikin razani da jin abin dake fitowa daga bakin wanda ya kira kansa ma'aikacin SS kuma mai suna Ridwan. Ban da Allah ya taimaka tana dab da bangon shiga kicin ɗin babu abin da zai hana a yanda jiri ya kwashe ta ta zube a nan. Sai da ta ga Ridwan ya miƙe tsaye cikin ba wa Jannat umarnin ta ba su haɗin kai su tafi da kuma ihun da Jannat din ta fasa akan Abba ya taimake ta sharri ne aka yi mata ya sanya ta jin wani mugun ƙarfin zuciya ya taho mata. Ummita mai haƙuri da kawaici, mai yawan murmushi da tausar wanda aka ɓatawa, nan da nan ta rikiɗe ta juye ta koma wata kalar Ummitan mai ban mamaki a inda ta yi fatali da kofin hannunta wanda ƙararsa ya dauki hankalinsu suka dube ta, ba ta damu da radadin zafin da ya tsirga saman fatar ƙafarta ba ta tsallake ta yo gaba jikinta har wani mugun rawa yake yi na ɓacin rai. Babu abin da take tunawa sai muggan kalaman da aka yi amfani da su wajen ɓata musu kyakkyawar tarbiyyar da Abba ya gina su akai shekara da shekaru. Ta tuna sanadin dukkan haka ne ya sa gaba daya aka janye aurenta da Sahabi da a yanzu ya koma ainahin garin iyayensa wato Zamfara da matarsa. Kallon Abba ta yi ya kauda kansa daga dubanta zuciyarsa cike da tsantsar tausayawa sannan ta maida kai ga Ridwan. "Domin Allah abin da kake fadi akan wannan (ta nuna Jannat) gaskiya ne?" Ridwan ya gane ta kwarai, ita ce Ummita don ba ta sauya ba, ya dai ga ta ma fi yarinta a fili sosai fiye da yadda aka yawo da hotunanta. Kawa sai ya ji ta burgeshi ta kuma ba shi tausayi kwarai. Madadin ya amsa da baki sai kawai ya ɗan gyaɗamata kai. Ta juya ga Jannat daidai lokacin da su Yassar suka shigo har Mami da Anna da ma Raihana wacce dama can a gigice take sakamakon ƙarar da Jannat din ta yi ba na wasa ba ne. "Anti Jannat, ke da kanki? Ke ce kika ɓata mana suna? Me muka yi maki? Wace kalar bautar ce bamu yi ba da har kika zaɓi yi mana mummunan ƙazafin da duniya za ta bar ganinmu da ƙima?" "Ummita kin yarda zan aikata wannan?" Ta fadi tana kokarin riƙo kafadun Ummitan, kamar wacce za a jonawa wutar lantarki cikin mugun sauri ta ja baya. Za ta ƙara gangancin matsawa domin ta taɓa ta aikuwa ga mamakin kowa Ummita ɗaga yatsunta biyar ta yi ta sauke saman fuskar Jannat hagi da dama. Za ta ƙara ne da sauri Abba ya riƙeta, kuka sosai take yi kamar ranta zai fita. "Ya isa, ya isa, kiyi hakuri hukuma za ta yi maganinta da ma dukkan wani azzalumi." Ya ƙarashe yana duban Mami wacce ta yi mutuwar tsaye jin abin da ƙanwarta ta shuka ya fito muraran. Ta kuma dan sha jinin jikinta bisa kallon da Abban ya watsa mata sai ta yi saurin wayancewa da matsowa ta dubi Jannat. "Kin bani mamaki, ban yi zaton za ki aikata hakan ba. Me suka tare maki a rayuwarki?" Jannat dake kuka sosai ta ji kamar Mamin ta sokamata mashi a ƙahon zuciya, ba kuma domin akwai su Ridwan a wurin ba za ta shaƙe wuyan Ummita ne ta aika ta lahira saboda marin da ta yi mata. Ba don jirginta da ya kasance na dare ba da tuni a safiyar yau ɗin ta tashi zuwa Misra inda za su tattaro su dawo Nijeriya gaba daya. "Yallaɓai zamu wuce lokaci ya ja. Kiyi hakuri Ummita, za ta girbi abin data shuka maki kinji ko?" Ya ƙarashe yana yiwa Ummita kallon da shi kadai ya san ma'anarsa. Daga haka wani ma'aikacinsu ya matso ya ba Jannat umarni akan ta yi gaba su je, nan fa Anna ta hau bori da ashariya duk cikin hausarta da bai irin na Bahaushe sak. Hatta da Abba sai da ta zage wai ya bari za'a tafi da autarta saboda ya nuna son kai. Abba dai mamaki bai bar shi ba, kenan duk wannan son da kaunar da suke nuna mishi da yarannan a fatar baki ne? Ya lura Mami sai kokarin janye Anna take yi tana mata yare akan ta yi shiru amma ina idanunta ya rufe ita za a tsfi da gudar jininta kuma mafi soyuwa a ruhinta. Raihana ba ta ce uffan ba, zuwa yanzu lamarin na su Jannat ba ya girgiza ta, ko babu komai ta ga wacce ta fi su iya tsari da kuma makirci. Na su ba komai bane. Ana wannan abu kallon Mami kawai ta ke yi yadda ta dage har da jan Ummita a jiki tana rarrashi. Ba ta sani ba akan Ummitan ko abin nata ya kai zuci ko aa, kawai sai ta kasa aminta da hakan sai ta juya ta koma ɗaki saboda wani sabon kukan da ya yunƙuro mata. Haka aka wuce da Jannat tana kuka da ihun a yafe mata don gaba daya kuma da ta ga al'amarin dagasken gaske ne sai ta shiga tashin hankali. Abba kuwa ana ficewa da ita ya fice zuwa dakinsa, tun a falon ya sanya mukulli ya kulle don ba ya buƙatar ji ko ganin Mami a wannan yanayin. Yana buƙatar samun hutun da zai yi tunanin da ya dace. *** Duk wannan budurin da ya faru su Futuha ba su da masaniya a kai sai washegari labarin ya riskesu daga Dawud da ya yi waya ya zayyane musu komai da komai. Zo ka ga kuka da sheshsheka wurinsu musamman Tasleem da ta ji tamkar an tafiyar mata da wani sashe na jikinta don za ta rantse shaƙuwa da kaunar dake tsakaninta da Jannat ta shallake nata da na Mami. Ita mai shirin fita zuwa makaranta inda suke shirye-shiryen zana jarrabawar ƙarshe sai ta fasa suka ɗunguma har Futuha zuwa gidan. Ba su iske Mami ba don tun ranar da aka tafi da Jannat suke asibiti sakamakon faduwar da Anna ta yi, ita ta kwana a wurinta bisa iznin Abba don shi dama ba shi da buƙatarta yanzun. Ta riga da ta gama sirewa a ransa. Raihana suka soma cin karo da ita kwance a falon da casbaha a hannunta tana ja. "Ke ina suka kai Anti Jannat?" Tambayar da Tasleem ta soma jifanta da shi cikin zubar hawaye ko zama ba ta yi ba. Guntun tsaki Raihana ta ja a ƙasan ranta a fili kuwa dakyar ta ce. "Nima ban sani ba." "Uhum, nikam tun farko dama sai da na nuna rashin goyon bayana ga wannan.." Idon da Futuha ta yiwa Tasleem ne ya sanya ta yin shiru, dagaske dai suɓutar baki ta so yi, sai ta ji tsoron kada Raihanar ta fahimci komai. Ita kuwa Raihana koda ta fahimtar ma ba ta nunamusu komai ba, ta fi damuwa akan al'amarin kashe ran da uwarta ta so a yi. Har yanzu ta kasa kwantar da hankalinta, abin ya jefa ta cikin matsanancin damuwa da tunane-tunane. "Kin je asibitin wajen Anna ne?" Cewar Futuha, girgiza mata kai kawai ta yi. Futuha ta ja tsaki. "Duk dai abinki duk wani guje-gujenki ba ki da sama da Annar da kuma mu, aikin banza kawai. Wato wai ke an taɓa ƴan uwanki shi ne kika dauki gaba da uwar uwarki. Dakyau." "Rabu da ita dai Futuha, duk dai lalacewar naka naka ne. Tashi mu wuce asibitin don ni ko wajen Abban ba zan shiga ba. Ai yana ji yana gani aka titsa ƙeyar Antin amma ya ƙi hanawa saboda ya nuna son kai da fifiko tsakanin wasu can da mu." Tasleem ya fadi tana huci gami da gyara goyon da ke kokarin kunce mata. Sai a lokacin Raihana ta mike zaune a zafafe ta shiga ba su amsa. "Su din dai jininmu ne koda kun ƙi ko kun so. Kuma wallahi da ace ni ce ku zan ji da rayuwata ne ba na tsaya kallo da kushe ta wasu ba. Ke kuma da kike kiransu da wai ƴan uwana, to ki goge kalmar wai din, yes jinina ne su kuma wallahi sun fiyemin ku nesa ba kusa ba. Kin tsaya ganin kuskure a rayukan wasu, kina nan mijinki har lefe ya kai na Ƴar Snow zai aure ta. Mtsw! Nonsense!" Tana kaiwa nan ta juya a fusace ta bar su a tsaye kamar an wawushe musu ƴaƴan hanji. Ba zagin da ta yi musu ne ya taɓa su ba don dama batun raini to fa Raihana ta yi musu shi, ko kadan ba ta wani ba su girma tun a baya, yanzun ma da ya ragu sun sani ko sun ƙi gaskiyar hakan ne albarkacin zama da su Ummita ne. Batun kai lefen Ƴar Snow da Yakubu ya yi shi ne ya fi komai sanya su cikin razana. Lefe gagarumin da suka gani yana yawo yau kusan sati kenan aka ce na Ƴar Snow ne, shi dai? "Tasleem wai kodai ni ce ban ji daidai ba?" Futuha ta fadi da wani irin ruɗani, ita kuwa Tasleem ta ɗan ji sanyi a ranta, kl babu komai idan har hakan ya tabbata ga Futuha zai kasance ba wai ita ɗaya ba ce ke shaƙar bakin cikin ɗa namiji ba. "Kai ta ya za ki biyewa wannan mahaukaciyar? Kema kin sani dai don ta shaƙa maki baƙin ciki ne ta tayar da hankalinki." Sai Futuha ta hau girgiza kai cikin mugun tashin hankali, Tasleem ganin haka ta ja hannunta suka fice tana fadin. "Dallah Malama kar abin da ta fada ki bari ya yi wani tasiri a zuciyarki. Yakubun da ke Dubai yau kusan sati uku kike wani tunani na daban? Toh ina ce ɗazun ma ya kiraki kun sha hira?" Jin haka sai Futuha ta dan samu nutsuwa, sai kuma ta yi kwafa. "Shegiyar yarinya kai, wallahi ta jefa ni cikin ruɗani na ɗan lokaci. Zan yi maganinta ne bari mu dawo." "Atoh, ko kefa. Ni so nake Anti Jannat ta fito, don ba ma za'a kwaso kayana ba sai ta fito idan ya so na siyar mu haɗa kuɗin ta kai wa Teacher dinta ya karkatomin hankalin Fadeel." Ta fadi Teacher gudun kar wani ya ji. Futuha dai jinta kawai take amma har a ƙasan ranta ta san da wuya aikin ya ci. Yaudarar kai dai Tasleem ta ke yi, amma da aiki na cin Fadeel da Ibb da tuni wani labarin ake ba wannan ba. *** Mami zaune a gefen gado bayan ta gama ba Anna abinci dakyar ta yi loma biyar ba ta ƙara marmarin ci ba. Sai kuka take yi tana tsinewa Abba kai ka ce shi ne ya sanya a kama Jannat. A wannan yanayin su Tasleem suka shigo dakin, haɗa su tayi gaba daya ta rungume tana kuka wai an tafi da shalelenta. Mami kuwa sai ta mike ta bar musu gadon ta koma saman kujerar dakin cike da dumbin tunani. Toh wai waye ya sanya aka cigaba da bin ƙwakkwafi har aka binciko gaskiyar al'amarin? Ta san dai Abba tuntuni ya bar maganar. Sai ta ɗan ja tsaki, ita ba ma wannan ba, ta kasa gane wanda ya sanar da ƴan sanda har aka kai wa su Abba ɗauki, ga kuma wani sauyin da take fuskanta daga Abban, wannan kuma ta fi danganta shi da Jannat wacce asirinta ya tonu. Watakila fushin da ya yi da jin zancen ne ya shafe ta. "Saki kuwa ni Hansatu?! Shi Hamzan ne ya sake ki?!" Furucin da Anna ta yi ne cikin dafe kirji ya sanya Mami maido hankalinta ga hirarsu. Ta mike tsaye cikin mugun firgita tana duban Tasleem wacce ko a jikinta, haka ma mikewar Mamin ba ta wani razanata ba, ɗan shakkar Mamin da take ji a baya yanzu duka ya kau adalilin jin wacece ainahin Mamin da ta yi daga bakin Futuha sai ta gane cewa ashe ita da ma su Jannat ba su yi komai ba kuma ba za su taɓa shuka irin abin da ta shuka ba a rayuwa. "Wa aka saki?" Mamin ta ƙara tambaya don gani ta yi tamkar ba ta ji daidai ba. Tiryan-tiryan Tasleem ta ba su labarin abin da ya faru ta ƙara da fadin. "Nifa Mami wannan abun ya yimin daidai kuma ya zo kan gaɓar da nake da buƙata. Ya je ya auri uwar Ramlatun ma ina ruwana. Ni yanzu Fadeel nake so na aura." "Za kuwa ki mutu ba aure! Ke shashashar ina ce?! Waye ya faɗamami akwai ranar da tsinannen yaron can zai aureki?! Wallahi na rantse maki har abada ba za ki taɓa aurensa ba! Tun muna shaidar juna ki tashi ki koma ɗakinki ko kuma yanzu na saɓa maki!" Ta turo baki. "Nidai Mami bana son aurensa. Dama wallahi da nasan matsiyaci ne babu abin da zai kai ni ga aurensa. Ai kowa yana auren ne don ya samu gida hutun da zai ci karensa babu babbaka, idan ma mutum bai samu ba sai ya ɓullo hanyoyin da ya san hakansa zai cimma ruwa. Toh ni dai ba zan iya aikata abubuwan da kika aikata ba amma zan iya yaƙi da namiji har ya sauwaƙemin na fito na samu cikar burina." Maganganunta sun sa Mami ta yi ɗif na wucin gadi, ta kuma kalli Anna wacce ke kallonta itama cikin rashin fahimtar komai sannan ta maida duba ga Futuha da alamar tambaya. Futuha kuwa ta kauda kanta tana ɗan taka yatsun ƙafar Tasleem, tana bin ta da kallon ya za ta yi mata haka? Ita kuwa Tasleem kafaɗunta kawai ta ɗaga kaɗan gami da kauda idanunta don ta rantse ta shirya yaƙi da duk wanda ya ce sai ta koma gidan Hamza. Yanzu dai Mami ce za ta yi mata yaƙin da za ta wanku a idanun Abba ko kuma ta yi barazanar tonamata asiri a wajensa. Wannan shi ne ƙudurinta.*LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA.* *5407827015* *FCMB* *Farida Abdullahi* 09034973645 "Ke! Ni sa'arki ce? Ni kike yiwa wannan maganganun?" Mamin ta fadi cikin zafi da kuma son sanin ainahin manufar Tasleem din. "Nasan komai Mami, na san wace ce ke da abubuwan da kika aikata. Wallahi samun da za ki yi na rufamaki sirrikanki nayi shiru da bakina guda daya ne, ki wanke ni a wurin Abba ya amince na zauna a gidan ba tare da kwaɓa ko wata tuhuma ba. Wannan kaɗai za ki yimin ni kuma na maki alƙawarin zan ɓoye komai." Gumi ne ya tsirfowa Mami a goshi, kirjinta har wani tagwayen lugude ya shiga yi. Wane irin suɓul da baka ta yi har ta zayyanewa Futuha komai da komai ba tare da tunanin hakan kan iya haifar mata matsaloli a gaba ba? Yanzu gashinan wa gari ya waya? Kai! Wai Tasleem dai ɗiyar cikinta ke yi mata barazana ko kuma ta tona mata asiri? Ta kara ɗaga idanu ta kalli Tasleem din wacce Anna ta damu da tambayar mene ne shi din da Mamin ta aikata amma ba ta ce uffan ba itama idanunta a kan Mamin tarr babu shakkar komai. Wannan ya ƙara firgitar da Mamin, sai kawai ta sanya kai ta bar ɗakin ta fice ba ya ko tsaya amsa kiran da Anna ke kwala mata ba. "Kai bana son iskanci kun ji ko? Ku faɗamin abin da Maryam ta aikata na san matakin dauka kafin itama wannan mugun uban naku ya sa a ficemin da ita." "Haba Anna, duk fa lalacewar uba uba ne." Futuha ce ta fadi don har ga Allah ta ji sosuwar rai bisa kiran Ubansu mugu da aka yi. Tsaki Tasleem ta ja. "Sai ki yi ai, uban da bai damu da namu farin cikin ba za ki shigarwa don an fadi aibu a kansa? Anna bari kiji abubuwan ban mamakin da ɗiyarki ta aikata." Tana fadin haka ta kwashe dukkan wasu labaran da Futuha ta ba ta ta fesarwa Tasleem, inda ta yi kuskue Futuha ta gyara, idan ma mantuwa ce ta yi sai ta tuna mata. Anna wani irin murmushi take yi sosai. Sai da suka kai aya sannan ta girgiza kai. "Ban yi mamaki ba. Maryama dai da na baku labari akan zafin kishi za ta iya aikata komai, ban yi mamaki ba. Sai dai na cika da al'ajabin yanda har ni ta ɓoyewa wadannan labaran. Kai an gaida Maryama. Muna mata kallon biri tana mana kallon ayaba." "Uhum, ai ni kaina Anna na sha mamaki. Farko na yi zaton duk don soyayyarmu ce ta sanya amma kuma zuwa yanzu na fahimci son zuciyar Mami ne. Kanta kaɗai ta sani ba ta damu da mu ba." Tasleem ta furta a zafafe. Futuha ta girgiza kai ta bude baki za ta yi magana Anna ta tari numfashinta. "Shashasha kawai, ke ba ki san Maryama ba. Son kanta ai ku din ne kan nata. Ni na sani tabbas dagaske domin ku samu jin dadi da walwalar ta aikata hakan, amma shi ne don ranki a ɓace yake kike neman kwaye mata zani a kasuwa ko?" Tasleem dai turo baki tayi kawai tana kokarin fiddo nono ta ba bebinta. Sai kuma aka koma jimamin Anti Jannat, Futuha ta kira Yakubu ta sanar masa komai saboda sanin da ta yi yana da manyan mutane watakila su shiga rigar alfarma a saki Jannat. *** NIJAR Humaira cikin ƴan uwanta da abokan arziki a garin na Maine. Gaba daya a kwanaki uku da ta yi ba ta da wata damuwa sai farin ciki da annashuwa. Kawunta sosai yake hidimar kawo mata dukkan wani abu da take so. Matarsa Tanti Hafsatu da suke kira da Hajjo kuwa ita da wasu cikin yan uwan Mamanta tun zuwanta aka soma yi mata gyare-gyaren aure. Ci wancan sha wannan, wasu kuwa tana ji sai dai su ce ba yanzu ba sai a ranar da za a kai ta. Wannan gatan da take samu ya sanya har hawaye takan yi, ta sani ba don Mami ta dauki fushi da ita kan lamarin Fadeel ba, babu abu daya da ba za ta samu daga gareta ba. Amma fushin ya kore komai. Sun gaisa da Abba a wayar Kawu amma koda wasa bai yi mata wani bayanin game da abubuwan da ke faruwa ba. Hakanan Fadeel da su Ummita, su din ma babu wanda ya ce komai. Shi Fadeel batu ne na Jannat, koda wasa bai bari ta ji ba don ba ya son abin da zai ɗaga hankalinta. A rana ta hudu Kawu ya kawo mata magungunan tsarin jiki sai rubutuka da ya yi mata. Tun soma shan da ta yi ta soma jin sauyi daga gangar jikinta. Ya ba ta addu'o'i masu ƙarfi ya ce ta dinga yi kullum safe da yamma sai kuma tashin dare da ya lura tana yi har ya zame mata jiki, nan ma ya bata wasu addu'o'in. Ya kuma ce ta dinga karanta la'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin ƙafa arba'in duk sadda ta shiga wata damuwa. A kwanakin da ta yi ta ga soyayya da kauna matuka, har ta cika sati cif bata da wata damuwa ko na ɗigo. Ana gobe za ta wuce su na zaune su na shan hira da Kawu yana mata nasiha akan zaman aure da kuma irin kyawawan halayyar mahaifiyarta sak ta dube shi cikin nutsuwa. "Kawu, don Allah mene ne maƙasudin rabuwar Mamana da Abba?" Ya ɗan yi shiru, toh meye amfanin ɓoyon tunda har Fatima a yau babu ita? Shi kansa akwai al'amarin da ya ɗaure masa kai a labarin wanda har yanzu bai fahimta ba sai dai ya yi karfin halin ba Humaira dukkan labari. Daga na irin soyayya da kaunar da Abba suka yi da Fatima, da ma kuma yanda a karshe ta zo ta tsane shi mugun tsana wanda sun sha tambayarta ta ce musu ita dai ba ta sani ba kawai ta tsane shi. Ya ƙara da fadin. "Wannan tsanar har Fatima ta mutu ba mu gano silarta ba, idan ya taso mata sai ta dinga riƙe kanta tana ji yana mata ciwo tamkar ya fashe, wani lokacin kuma ta yi kuka mai yawa daga bisani bacci ya ɗauke ta. Mun bar shi akan iskokai ne. Sadda za ta rasu kuwa, lafiya lau ta haifeki sai bayan ma har ƙanwar Dada, Inna ta mata wanka ta shirya ta tsaf kawai aka shiga aka ga fuskarta da dukkan jikinta ya yi baƙiƙirin kamar wacce aka ƙona. Aka tattaɓa aka ji babu rai, gaba daya lokaci guda ta komaɗe ta koma tamkar babu jini a jikinta." Humaira da tun soma labarin take kuka sosai ga wani irin fargaba da ya shigeta da kuma tausayin Mahaifiyarta ta ce. "Kawu kenan nima idan na haihu zan mutu ne irin yanda Mammana ta rasu?" "Haba Humaira, wa ya ce maki haihuwa mutuwa ce?" Ta girgiza kai. "Kawu nima na yi fama da makamancin wannan halayyar na Mamma akan Fadeel. Ni tsana ce na yiwa kowane ɗa namiji da zai ce yana sona." Ya yi shiru yana kallonta da mamaki, ta cigaba da koramasa bayanin duk yanayin da ta tsinci kanta a ciki da ma hayaƙe-hayaƙen da Mami ke yi mata don taimakonta. Sai wani tunani ya zo masa, tabbas Fatima ta ce itama a lokacin Mami ta taimaka mata da hayaƙi wanda nan da nan ta ke jin kanta na juyawa bacci mai nauyi ya dauketa kuma idan ta farka muddin ba Abban ta gani ba to fa tsanar ba ta ƙara dawowa. Ya tuna har hayaƙin ta ba su akan su cigaba da yi mata. "Ya aka yi kika daina jin tsanar?" Ya yi mata tambayar cikin sauri. Nan ta kwararo masa bayani, ita dai tun maida hankali sosai da ta yi ga ibada shikenan kuma sai komai ya sauya. Ta ba shi labarin abin da ke damunta wato tsanar Fadeel din da Mami ta yi. Hatta da farkon zuwan Fadeel din gidan wanda Tasleem ta yi zaton wajenta ya zo ta shirya sai da ta ba shi labari. Kawu ya yi shiru yana sauraronta cikin wata irin fargaba da tunani. Kada dai a baya sun tafka kuskuren yarda da Maryam? Ya tuna tabbas Fatima mai yawan ibada da nafilfilu tun sadda ta dawo gida Nijar suka lura gaba daya ta bar yin ibadunta yanda ya kamata. Hatta da sallah sai Dada ta yi magana take tashi ta yi. Idan ma ta idar babu wata doguwar addu'a take miƙewa. Ya ambaci kalmar Innalillahi zuwa karshenta a zuciya, bai mance ba akwai sadda wani Malami tun lokacin Fatiman ya ce asiri ne aka yi mata kuma da sanya hannun abokiyar zamanta amma sai suka yi biris suka ji haushi suka ƙaryata shi, a tunaninsu ta ya ya za'ayi matar da take zaune da su da zuciya daya ta aikata wani mummunan abu ga Fatiman? Jikinsa sai ya yi mugun la'asar. "Kawu akwai wani abu ne naji ka yi shiru?" Sai ya yi mata murmushin yaƙe. "Babu komai Humaira, maza je ki kwanta dare ya yi kinga gobe sammako za ku yi." Ya fadi hakan ne saboda tare za ta wuce da su Hajjo sai budurwar ɗiyarsa sa'ar Humairar, wato Safina. Sauran masu zuwa ɗiyoyin Inna ƙanwar Dada sai ana bai fi sauran kwana biyu biki ba za su taho da Kawun. Miƙewa ta yi ba don ta gamsu da yanayin fuskar Kawun ba ta yi mishi sai da safe ta bar wurin. Hajjo dake gefe tana damawa Kawun fura tana jinsu ta mike bayan ta gama damawa Kawun fura ta ajiye masa da ludayi, cikin harshen fillanci ta ce. "Komai da ya faru ya riga ya faru sai dai a kiyaye gaba. Yanzu tunda har ka gano bakin zaren sai a yiwa abin tufka ta hanyar cigaba da kula da yarinyar da dora ta bisa turbar addu'a da kuma nema mata abubuwa tsarin jiki duk da cewa babu tsarin da ya fi addu'ar." Kawu ya numfasa cike da jimami da taraddadi. "Mamaki da tsoron halayyar DAN ADAM ya ƙara shiga ta Hafsatu, yanzu ke kya ce wannan baiwar Allahr za ta iya cutar da ko mage ne balle kuma mutum?" Murmushi Hajjo ta ɗan yi. "Meye abin mamaki anan? An fa yi wanda ya fi haka. Kuma kar k manta zargi ne.." "Ko kusa bana kokwanto ko zargi a kan haka, wannan gaskiya ce da na jima da ji kuma na ƙi yarda sai yanzu da komai ya bayyana a zahirance. Ba zai yiwu ace hayaƙin da Maryama ta ba Fatima shekarun baya ba irinsa take hayaƙawa Humaira kuma yanayin da Fatima ke shiga dalilin hayaƙe-hayaƙen ace iri guda ne da na ɗiyarta. Wannan ai ko akwai ban mamaki, ban da kuma toshewar basira irin tamu a lokacin, mun kasa tunanin akwai cutarwa a ciki ba? Kowannenmu ya shaida da irin kaunar da Fatima da Isuhu ke yiwa junansu ba amma rana ɗaya ta yi masa tsana wadda da bakinta ta furta mana ba ta san dalilinsa ba? Kai Hafsatu, nikam ba zargi nake yi ba, na riga da na tabbatar da sa hannu wannan makirar." Hajjo ta jinjina kai yayinda kwalla suka cicciko mata na tuna yanda Adda Fatima (kasancewar yaya take a wurinta koda babu aure tsakaninta Kawu, don yar uwarsu ce ta fannin Baffansu) ta sha fama kafin rasuwarta. "Amma idan har hakan ne toh wallahi matarnan ta jira sakayyar Ubangiji don ta dauki alhakin wacce ba ta ji ba kuma ba ta gani ba. Matar da ta yarda da ita tsakani da Allah mu ma haka. Ni babu abin da ya ban tsoro sai wannan bori da tada jijiyoyin wuyan da Humaira ta ce tana yi akan ba ta kaunar aurenta da Fadeel. Toh a zatonta yarinyar za ta yi ta zama babu aure? Ai ni tun da naji cewar wai Humaira ba a sanyata a makarantar boko ba sai da na yi maka magana idan ba ka manta ba, nace maka ko ƴar gidan Iyagana da ta girmi Humaira da suka koma can Katsina da zama an maida ta boko kuma yanzu gashinan har ta kusa kammala kwalejinsu. Ka hau ni da faɗan ai wannan ma gata ne za ta yi mata. Eh gatan ne, amma yanzu wa aka cutar? Za ta shiga rayuwar miji ɗan boko fisabilillahi daga shi har danginsa na san sun ci sun tada kai da biro da takarda yarinya babu faransancin babu turanci." "Hafsatu don Allah abar maganar tunda dai mai afkuwa ya riga da ya afku. Ki yafemin faɗan da nayi maki a lokacin, amma ki sani ko Humaira ba ta yi wata aba boko ba, mu godewa Allah tunda ta tsira a hanyar tsirar, wato na islama da ba a hanata ba. Sannan karki manta duk fa yanda Allah ya tsarawa bawa a rayuwa hakan ne zai tabbata. Yanzun ba gashinan ba nan da ta yi mana girki kamar kunnuwanmu za su tsinke don dadi? Ai DUKAN RUWA BA ZAI HANA GWARJE AMO BA! Mu je zuwa muna nan dake wataran yarinyar nan sai ta zama tamkar farin wata mai haska darare a cikin yan uwanta. Babu abin da zai hana zakaran da Allah ya so ya yi cara." Ta ji karfin gwuiwa bisa maganganunsa har sai da ta murmusa. "Allahu ya nunamana wannan ranar." Kawu ya amsa da amin yana jawo ƙwaryar furarsa. *** ©Rufaida Umar.Mami sosai ta cika da mamakin ganin Abba bai ce uffan ba hame da dawowar Tasleem gidansa matsayin bazawara. Koda ta kalallameshi banda Allah ya kyauta babu abin da ya ce. Tunanin shirye-shiryen bikin da ya sa a gaba shi ya dauke hankalinsa ne ya sanya ba ta kawo komai ba amma a kaifin basira irin nata ta sani akwai dai abinda ya sauya Abban, ko fara'arsa ta daina gani. Ɓangaren jannat kuwa ranar da ta kama na dawowar Humaira, a ranar ne aka gurfanar da ita gaban alƙali, a ƴan kwanakin da ta yi gaba daya ta fita hayyacinta duk kuwa da cewar babu duka balle zagi amma fa wahalar zama a inda ba ta sama ba ya sauya ta. Tasleem koda ta ganta fashewa tayi da kuka, sai kuma a lokacin ne suka san Fadeel ne ya ƙarfafa binciken har mai afkuwa ta afku. Wannan ya ƙarawa Mamin tsanar Fadeel, itama Tasleem sai da ya yi mugun ɓata ranta. Mami tana ganin an shige ciki domin shari'ar ta koma da baya ta fidda waya ta kira Wizzy. Tuni ta shiryamasa cewar ya aika mace gidan ta daukar masa Ahmad tunda babu kowa sai Anna da Ummita. "Ka gaggauta wanzar da shirin don bana son a samu wata matsala, ka kuma tabbatar da komai ya tafi daidai." Daga haka ta katse kiran ta shiga dakin shari'ar. A gabansu alƙali ya yankewa Jannat hukuncin biyan tara na ɓata sunan da ta yiwa su Ummita, miliyan biyar ga kowaccensu. Sai kuma ƙaryata kanta a gidan jaridu da ma rediyo da kuma soshal midiya kan cewar ita ce ta sa aka yi wannan mummunan aikin da kuma ba da hakuri. Hakanan shi ma Joshua. Tun daga lokacin ya hau kuja da roƙon gafara don ya sani ba shi da maƙudan kuɗaɗen da zai biya don wake kansa a gaban alƙali. Ya shiga tsinuwa ga Jannat wacce ita ce ummul-aba'isin na shigarsa wannan hali. Shi da ya yi aikin akan kuɗaɗe ƙalilan sai ga shi ya jawowa kansa, ga mahaifinsa da ya ce babu shi babu hannunsa a ciki. Daga haka aka ƙara titsa ƙeyarta aka tafi da ita har sai lokacin da aka biya tara sannan. Haka suka fito bakin kotun su Tasleem da Mami na kuka, ga Anna can a gida ta baza idanu tana jiran ta gansu tare da ita. Mami kuwa zuciyarta cike take da zullumin ko Wizzy ya aiwatar ko kuwa an samu akasi. Ta duba ta ga dukkan yaranta idan ka cire Mubarak da ke can Sokoto a camp babu wani da ba ya tare da su. A iyakar saninta babu wata matsala da za a samu da shigar mace cikin gidan tunda dai babu kowa. *** A daidai wannan lokacin motar su Humaira ta tsaya a tasha, suka fito ita da Hajjo a take aka samar musu abin hawa da zai kai su har gida sakamakon lodin kayan da suka taho da su. Suna hanya zuciyarta cike taf da farin ciki, ba ta kira kowa ba da zummar sai dai kawai su ganta. *** Wizzy ya bude motar gami da duban matarnan, matashiyar budurwarsa da yake ji da ita a lokacin, sai da suka kai ruwa rana kafin ta aminta da buƙatarsa har sai da ya yi nata alƙawarin da ta jima tana son ji, wai aure. Ta sha zabgegen hijabi da niƙaf. "Nusy, kar ki bari a samu wata matsala. Ki bi komai daki-daki yanda muka tsara." Ta yi mishi farr da idanu bayan ta ɗage nikaf din. "Wannan ba damuwa ba ne Guy, komai zan yi dominka." Ya jawo fuskarta ya sumbaci goshin sannan ta sauke nikaf din ta dauki jakarta ta fita. Yana daga can tsallaken ya ga shigarta gidan ba tare da dogon zance da maigadin ba. Sai ya sauke ajiyar zuciyar, ribas ya yi da motar ya koma daga can bayan gidan ya tsaya gudun kada a gan shi duk kuwa da cewa motar tinted ce amma ita ce dai motar da ya kai wa su Abba hari. *** Ummita dake zaune a falo ga Ahmad a gefenta yana bacci cikin net dinsa. Hankalinta gaba daya ya yi zurfi a tunanin yanda aka kaya a wurin shari'ar amma ta kasa kiran koda Raihana ce don ta ji meke faruwa. Sallamar budurwar ta katse tunaninta, ta dubi ƙofa gami da amsawa. Ganin mace da nikaf ba ka ganin komai sai idanunta ta dan yi jim, ba don ba ta saba ganin mai irin shigar ba sai don kasancewar abu ne mai wahala su yi baƙuwa da irin shigarnan. Kamar Nusy ta san zargin da take yi, sai ta ɗage nikaf din, kyakkyawar fuskarta ta bayyana da murmushi mai bayyana haƙorinta na makkah. "Sannu, nan ne gidan su Futuha Yusuf?" Ganinta har da haƙorin makkah da kuma yanayi na kamala sai ta ɗan saki jiki, itama cikin ɗan murmushin ta amsa. "Yauwa, eh nan ne. Ƙaraso ciki mana." Nusy cikin tabbacin samun nasara ta ƙarasa ta zauna idanunta ya sauka kan wanda ta zo dominsa, wato Ahmad. Yaron tubarakAllah, da alama goyo mai kyau yake samu don yana da kumari sosai fatarsa kuma ta ƙara gogewa. "Ba ki sanni ba ko? Ni makwafciyarta ce ta Kuntau ana cemin Maman Suhail, mun yi da ita dama zan yi mata rakiya wata unguwa shi ne ta yimin kwatancen gidan nan ta ce na zo mu hadu anan mu tafi." Ba wani sanin gidan na su Futuha na yanzu ta yi ba balle ta fahimci gaskiyar lamarin, ta ba da gaskiya sosai akan zancen Nusy. "Allah Sarki, eh sun dan fita ne amma na tabbatar sun kusa dawowa yanzu. Bari na kawomaki ruwa." Tana fadin haka ta miƙe, an zo daidai wajen da Nusy take so, tana ganin shigar Ummita kicin ta yi saurin miƙewa ta bude net din Ahmad ta daukeshi. Ta ɗago suka yi ido hudu da Waleed da ya shigo daga bangaren Anna rike da ball a hannunsa. Ya gaida ta don bai mance sadda Ummita ta yi baƙuwa ba ya ƙi gaishe ta Antinsa Humaira ta yi mishi tsawa. Ta amsa tana dan wayancewa da jijjiga Ahmad kai kace kuka ne yake yi. Waleed kuwa dama ruwa ya fito sha sai kawai a guje ya yi kicin yana wasanninsa na yara. Ta sauke ajiyar zuciya da sauri ta ɗaga zumɓulelan hijabinta ta sanya Ahmad a ciki ta rufe, ta kama hanya ta fice bayan ta sauke nikaf din ya rufe fuskarta. Har ta fice daga farfajiyar gidan, Allah ya taimaka Maigadi ya ɗan mike wannan ya sa ta ƙara ɗaga kafafunta ta fice a gate din. Daidai lokacin motar su Humaira ta tsaya suka fito, idanunta akan matar dake ta baza sauri ga kukan jariri na tashi cikin hijabinta. Kafin ta yi wani tunanin sai ga Ummita a haukace ta banko kyauren gate din ta fito. "Ahmad! Wayyo jama'a ku taimakamin ɗana!!" Jin haka ai sai wasu samari da ma ita kanta Humaira dake tsaye suka nufi matar a guje, daidai sadda Wizzy ya yo gaba da zummar kawai ta bude motar ta shiga daga ta iso, sai dai ina, wata irin raruma da wani ya kai mata sai ga ta nan yiff a ƙasa, yaro kuwa ya ji buguwa ya fasa ihun da ya fi kukan da yake yi a baya. Da rawar jiki kuma a haukace Ummita ta hau ɗage hijabinta sai ga Ahmad, Wizzy kuwa tuni ya yi wata muguwar ribas ya bar wurin a miliyan, duk iyaka kokarinsu na ganin sun damƙeshi abin ya ci tura. Nusy dai ta zo hannu tana kuma ji da gani wanda ta aikata dominsa ya juya ya bar wurin. Nan da nan Ummita ta damƙe Ahmad tana kuka har lokacin jikinta na kakkarwa. Samarin nan kuwa suka shiga kokarin bugun Nusy wani dattijo ya hana ya bada umarnin a damƙa ta a hannun ƴan sanda. Ana nan ba a kai ga tafiya da ita ba sai ga motar su Abba ta sanyo kai. Mami tun daga nesa ta hangi cincirindo ai sai da ta ji wani mugun jiri daga zaune yana son kwantar da ita. "Meke faruwa haka kuma? Waccan ba Mamana ba ce?" Fadin Abba yana ɗan ƙara ƙurawa wurin idanunsa. Mami dai ta kasa ce masa uffan sai Raihana daga baya ta amsa da su ne har da Ummita. Sai kawai ya ja burki ya tsaya ya fito, Mami dai ta kasa motsi balle ta fito daga motar. Suna fita wayarta ta hau ƙara. Ganin sunan Wizzy sai da ta ji wani guntun fitsari ya kufce mata ya zubo, ta ɗaga ba tare da cewa uffan ba. "Ke tsohuwar kilaki! Ki saurare ni dakyau! Na rantse maki tunda har aka kama min farin cikin rayuwata sai na salwantar da rayuwarki! Sai na kasheki da hannuna muddin asiri ya tonu! Kuma yanzu na gaji da bibiyar ɗana ta hanyarki! Zan tunkari ita banzar gyatumarsa ta ba ni ɗana ko ta halin ƙaƙa ne! Ke kuma ki saurari abin da zai biyo baya! Ba ki san waye ni ba! Labarina kawai kike ji!" Yana kai wa nan ya datse kiran, wasu hawaye masu ɗumi na bakin ciki ya zubo saman fuskar Mami, ta yi saurin kauda su ta bude murfin mitar ta fito. Duk wannn abu da take yi akan idanun Hajjo wacce tun fitowar su Abba ta lura da Mamin da kuma yanayinta, tana ganin wayar da ta amsa. Mamin na fitowa itama idanunta ya sauka cikin na Hajjon, ta gane fuskarta sarai, matar Kawun Humaira sai ta kauda fuska ta daure ta tamau. Abba ya dubi Ummita da neman ba'asin yanda lamarin ya faru. Cikin kuka ta labartamasa komai, Futuha tunda ta ji an ambace ta da ma sunan unguwar da take sai ta zaro manyan idanunta waje gami da dafe kirji a mugun firgice. Kafin ma Ummita ta kai aya ta hau rantse rantse. "Na rantse da Allah karya take yi, ke a ina kika san ni? Wallahi Abba karya ne ni tunda naje wannan unguwar ma ban taba shiga kowane gida ba don ba class dina ba ne su. Wallahi sharri take yimin." Nusy kuwa dai ba ta tanka ba sai jin ciwon gudun da masoyinta ya yi ya kyale ta a nan, idan wani ya ce mata zai aikata hakan gareta za ta ƙaryata. Mami kuwa tana gefe ta yi gum ba ta ce uffan ba. Hajjo dai ba ta bar kallonta ba har sai da Abba ya ba su umarnin duk su shige ciki shi zai juya a miƙa Nusy hannun hukuma. Da wannan gaba daya suka yi cikin gidan, Raihana ta rungume Humaira ta fashe da kukan da Humairar ta ba kanta ko don abinda ya kusan faruwa ne. Tun tana rarrashinta har dai kukan ya soma karyar da nata zuciyar. Dama ta lura da irin muguwar ramar da Raihana ta yi. Tasleem ta tsallake su gami da jan tsaki ta shige ciki don yanzu ta koma ainahin dakinsu kuma tsohon gadonta. Futuha kuwa ɓangaren Anna ta yi don ta kwantar mata da hankali bisa hukuncin da aka yiwa Jannat. *** A ci da hakuri. Lol.Ta fakaici idanun jama'ar dake falon ta shige ɗakinta ta sanya muƙulli. Waya ta fitar ta dannawa Hajiya Lubna kira. Ƙara uku ana hudu ta ɗaga. "Lubna ki taimakamin, komai ya lalace." Tana maganar ne cike da tashin hankali. "Kwantar da hankali ki sanar da ni a nutse. Meke faruwa ne?" Nan da nan ta zayyane mata komai ta ƙara da fadin. "Muddin waccan yarinyar ta buɗe baki ta yi wata maganar toh ki sani akwai babbar matsala. Nikam ban san kuma me zan yi ba." "Wannan ba damuwa ba ce Maryam, yanzu dai abin da nake so ki yi kokarin sanin station din da aka miƙa ta ni kuma zan nemi Alhaji don ya yi magana su sake ta. Ai harka ce ta kuɗi kwantar da hankalinki komai zai tafi daidai." Ta dan ji sassauci kaɗan. "Shikenan, bari Abban yaran ya shigo. Amma lallai muddin wannan yarinya ta fito zan dauki mummunan mataki akan ɗan iskan yaron nan." "Ko kefa, ki kwantar da hankalinki komai zai tafi yanda muke so. Ai ko ba ko faɗa ba dole Wizzy ya ci ubansa. Ya batun can kuma na baya, kin gano wanda ya sanar da ƴan sanda? Na fadamaki Maryam koda yaranki kar ki sake ki aminta da su." Wannan ya tunasar da Mami tashin hankalin da ke gabanta. "Uhm, bari kawai Lubna. Ai yanzu an yanka ta tashi domin babu wani abu cikin sirrina da ƴar banzar nan Tasleem ba ta ji daga bakin Futuha ba wai har ni ta ke yiwa barazana akan maganar? Wancan batu kuwa har gobe na kasa fahimtar komai, karshe na zargi Abbansu ko shi ya sanar toh idan haka ne kuma meyasa har yanzu bai dau mataki ba? Nidai na ga y sauyamin, babu hira da ni balle a sakarmin fuska." "Toh kuwa lallai ki zauna ku yi magana da shi sosai ki fashe da kukan kissa ki nuna sauyin nan da ya yi maki sam bai maki dadi koda dai duka wadannan ba sai na koyamaki ba ke dinma Malamata ce a wannan fannin. Yaranki ko zan yi waya da Babandi mu sanya a ƙulle musu baki ta yanda babu inda maganar za ta ƙara fita." Sanin da Mami tayi Anna ba matsala ba ce ya sanya ba ta ma kawo ta a rai ba, ita idan ta sani ba wani abun bane. Tun kuma safiyar yau din sai yanzu ta yi wani murmushin da har zuciyarta ta ji daɗin wannan zantuka na aminiyarta. "Ina yinki sosai Aminiya, Allah ya kara doraki kan Alhaji da maƙiyanki." Suka yi dariya, nan kuma suka koma batun Jannat wanda tuni ya baza gari, Hajiya Lubna ta jajanta mata da tambayar yanda za su yi da batun kudaden. Ta taɓe baki. "Motarta dai ta ce a siyar sai sarƙoƙinta da mijinta zai taho da su. Ya ce dai babu hannunsa a ciki don haka ko sisin kwabo nasa ba zai yi kuka ba." "Shegen sama, shiyasani, ko me ake ciki dai sai ta fito. Sai kuma ta kiyayi gaba tunda yanzu idanun duniya duk a kanta suke." Mami ta numfasa. "Atoh, kinga bari naje ga waccan kafaffan mijin nawa ko zan iya tankwara zuciyarsa na gano dalilin sauyamin da ya yi." Suka yi dariya ransu ƙal kafin su yi sallama. *** Hajjo ta yi wanka ta fito ta dubi Ummita baki buɗe. "Wai har yanzu ba ki bar wannan kukan ba? To maganin me zai maki?" "Kema dai kya faɗa Tanti, ni wallahi ban ga amfanin kukanki ba. Mu godewa Allah ma tunda ya yi mana maganin komai." Cewar Humaira dake kokarin kauda nata hawayen, Raihana ko tana zaune shiru ba ta ce musu uffan kwakwalwarta cike da tunani iri iri. Tasleem ba ta dakin suna can bangaren Anna ana maida zance. "Don Allah ki bar tunanin komai ki godewa Allah. Ai babu babban makami a yanzu irin addu'a kuma Alhamdulillah gashinan ta yi maganin komai." Da wannan Ummita ta hakura da kukan ta share hawayenta, ita babban tashin hankalinta bai wuce kuma abin da zai ƙara faruwa a gaba ba. Ko ba a fada ba ta san azzalumin mahaifinsa ne ke biɗarsa. Ita kuma idan duniyarnan za ta haɗe babu mai raba ta da Ahmad. "Wayarki tana ta ƙara tun ɗazu, Yaya Mubarak ne ke kira amma kin ƙi ki ɗaga." Fadin Humaira tana mai miƙa mata wayar, ta sa hannu ta karɓa ba ita kuwa ta faɗa bandakin don gyara nata jikin. *** Bayan dawowar Abba daga miƙa Nusy hannun hukuma inda akai akai ta faɗi wanda ya sanya ta ta ƙi, yana zaune yana amsa wayar Alhaji mahaifin Fadeel dake jajanta al'amarin Jannat da kuma kwantarwa da Abban hankali ganin dole ya shiga damuwa tunda kanwar matarsa ce, kasantuwar hakan kuma ya jawo kananun magana iri-iri a kafafun yada labarai kowa na cewa watakila ma ita ta sa aka sace su. Abba ya yaba sosai da samun surukin da ya rikiɗe ya zame masa abokin kuka a rayuwa ya dinga godiya. A haka Mami ta shigo falon ta iske shi. Ganinta bai sa Abba fasa wayar ba, tana ji yana bada labarin abin da ya faru bayan dawowarsu daga kotu amma sam ba ta fahimci da wanda suke wayar ba sai daga baya. Ta matsu sosai ta ji ya kai gaɓar da take so wato sanin hannun da Nusy take, ba ƙaramin girgiza ta yi da jin wai tana hannun Ridwan ba. Wata irin zufa ta karyo mata. Ridwan dai da Jannat ta zama karkashinsa a can ofishin SS, kai kai kai, ita kuwa ta san zai wahala Hajiya Lubna ta iya wani abin a kai amma dai za su gwada sa'arsu. Har Abba ya kammala wayar ba ta sani ba sai da ta ji ya yi magana. "Hajiya Maryam lafiya?" Ta ɗan yi firgigit gami da dan muskutawa da tattaro dukkan damuwar duniyarnan ta ɗora saman fuskarta. Dama ya lafiyar kura? "Ina fa lafiya Abban yara, kana tunanin zan zauna cikin nutsuwar ruhi bayan abubuwan da suke biyowa baya? Wallahi idan aka ce wani nawa zai cutar da jininka zan ƙaryata hakan. Wai Jannat dai da kanta ta aikata wannan mummunan abu ga yarannan? Haba Abban yara, ni gaba daya kunyarka nake ji. Don Allah ka yafemin kar ka hukuntani da laifinta. Tabbas ta aikata wauta." Sai ga Mami ta soma kuka da hawaye, Abba ya ɗan yi shiru kawai yana kallonta. Ba don da kunnuwansa da kuma idanunsa ya ji ya gani tana bada umarnin a aiwatar da kisa a kansa da gudan jininsa ba, zai iya dafa Alkur'ani dukkan abin da take faɗi kuma take nunawa a zahirance da zuciyarta ɗaya ta ke yinsa. Sai dai ina, Maryam ta gama sirewa a ransa, kullum kuma kodayaushe cikin addu'a yake akan Allah ya kara buɗa idanunsa ya nunamasa gaskiyar matar da yake rayuwa da ita kuma ya rayu da ita tsawon shekarunnan cikin rufewar idanu da rashin sanin haƙiƙaninta. Mami ta ɗan yi turus jin babu wani sauyi ko kuma yanayin da zai nuna maganganunta ya shige shi a saman fuskarsa, ta dube shi da dan mamaki kirjinta na ɗan dukan tara-tara, kada dai zarginta yake yi? "Abban yara kodai kana tunanin da sanya hannuna cikin abin da Jannat ta aikata?" Ya numfasa gami da girgiza kai da riƙo yatsun hannunta. "Ko kusa Maryama, ni ba na zarginki da komai. Idan na zargeki na ce na zargi wa? Matar da muka rayuwa tsawon shekaru sama da ashirin cikin so da kauna ta gaskiya? Ko kuwa wacce ta riƙemin amanar gida da na yara har ma da wadanda ba ita ta haifa ba cikin kauna da aminci? Har abada ke ba abar zargina ba ce." Mami ta ɗan yi yaƙe, a karan kanta sai ta ji tsarguwa, ba ta gamsu da zantukan Abban ba. Shi kuwa idanunsa ƙurr cikin nata, danne zuciyarsa yake yi sosai don ya fi kaunar tafiyarsu a hakan har zuwa sadda zai kama ta dumu-dumu. "Kawai dai lamuran ke dauremin kai, waye ya aiko a sace Ahmad? Idan kuma ba aike bane, ita din wace ce da ta zo tafiya da shi? Akwai dai lauje cikin naɗi wanda na tabbata Ridwan zai tsaya tsayin daka wajen ganin ya warware wannan ƙulli." Kirjinta ya ba da dam! Bayan sunan Fadeel, a yanzu Ridwan shi ne suna na biyu da kaf duniya ta ji ta tsana. Wato shi ga ɗan iska, ya shigo rayuwarta don ya wargaza ta, toh kuwa bai isa ba. A fili kuwa jinjina kai ta yi cikin nuna damuwa ƙarara da mamaki. "Tabbas nima abin ya ɗauremin kai Abban yara, koma wace ce wannan yarinyar da ta kira kanta da Nusy, akwai wani sirri tattare da zuwanta da bincike kadai zai tona shi. Ka kwantar da hankalinka gaskiya za ta bayyana." Murmushi ya yi sosai. "Nima gaskiyar na fi son ta bayyana. Zan so abin da yake ɓoye ya fito fili. Na dai yanke shawara da zarar an kammala bikin ƴar uwarta zan maida ta hannun Hajiya Maijidda na ɗan wani lokaci mu gani. Ba don saboda bikin ba ma tun yanzun za ta wuce, toh amma ba na son na yanke mata wannan farin ciki." Mami ta daure fuska tamau. "Wace irin magana ce wannan kake yi? Wato ka raina dukkan kulawar da Ummita ke samu a wurina?" Shima nan da nan ya ɗaure nasa fuskar. "Nayi zaton ke ce farkon wacce za ta yi amanna da wannan shawarar Maryama, idan har dagaske kwanciya da nutsuwar hankalin Ummita ki ke buri, toh fa babu abin da ya fi wannan  samar mata nutsuwa." Sai ta gane tana shirin kwafsawa da sauri kuma ta gyara zancen ta hanyar raunana murya da fuska. "Na sani Abban yara, amma kewarta na fi tunani da zan yi. Shikenan dai Allah ya kawo karshen komai." Abba ya amsa da amin, ba shi da tabbacin ko dagasken take yi akan lamarin Ummita, ya dai bi ta da hakan ne kawai. Sai da Abban ya fice zuwa masallaci don gabatar da sallar la'asar sannan ta samu damar kiran Hajiya Lubna ta sanar da ita. Hajiya Lubna ta tambayi cikakke sunan Ridwan din, nan ta sanar da ita, sai kawai ta ja tsaki. "Aikin banza kai, ai wannan ɗan Hajiya Fa'iza ne, matar Late General Mukhtar AbdurRashid. Sai dai yaron a yanda na san shi yana da wani irin kafiya akan ra'ayi da taurin kai. Za dai mu gwada sa'ar mu. Kar ki samu damuwa. Idan ma ya ƙi bada haɗin kai ai sai mu biyo mishi ta sama." A farko zantukan Hajiya Lubna sun ɗan sa jikinta mutuwa, amma jin ƙarashen sai ta samu kwarin gwuiwa. Suka rabu akan duk yadda ake ciki za su yi waya. Daga nan Babandi ta dannawa kira ta labarta masa komai, ya ce kada ta samu damuwa zai yiwa abin tufka. Sunan Ridwan kawai ya tambaya cikakke daga nan ya ce zai mata aiki a kansa. Haka ta sallame wayar zuciyarta fari ƙal. *** Matashin ma'aikacin dogo mai ƙira, baƙi ne, irin baƙin da hutu ya ratsa. Yana da cikar sumar kai, ya na sanye cikin ƙananan kaya ya tsaya gaban tebur gami da ƙurawa Nusy idanu babu wasa ko kaɗan a cikinsu. Ita kuwa tana binsa da kallo tamkar ta lashe shi, a baya tana yiwa Wizzy kallon wani haɗaɗɗe kuma jarumi musamman a fagen bariki, amma a yanzun da Ridwan Mukhtar AbdulRashid ke tsaye a gabanta sai ta nemi sauran ruwa a jikinta ta rasa. Sai dai ta sani wannan ba sa'anta ba ne, ko za ta mutu ba zai auri ƳAR BARIKI irinta ba da ba ta san adadin wadanda suka ci moriyarta ba. "Idan za ki yiwa kanki adalci, ki faɗi gaskiya ki huta kuma hukuna ta huta. Ke din wace ce kuma mene ne dalilinki na shiga gidan Alhaji Yusuf da niyyar satar ɗan mutum?" Ta ji idanunta sun cicciko da ƙwalla amma ta yi shiru babu amsa. Idan ta fadi ba amanar Wizzy kadai ta ci ba, har da na kanta don ta tabbatar za ta yi biyu babu, wato dai babu auren Wizzy balle kuma samun wani ƴanci na rayuwa. Ridwan ya ɗan kwankwasa tebur, ta ɗago idanunta ta kara dubansa. Fuskarsa kaɗai ta isa sanya matarsa samun nutsuwa da bacci mai dadi. Ko wace ce ta same shi ta huta. "Ba ki shirya magana ba kenan? Ki sani Nusaiba akwai hanyoyi da dama da zamu sanya ki magantuwa, idan kin zaɓi ta hanyar tsananin hakan ce za ta faru. Idan kuwa kin shirya sanar da mu ba tare da ɓata lokaci ba, wannan ma kin kyautawa kanki." Wani tunani ya faɗomata sai ta yi saurin magana ba tare da hango matsalar abin da take shirin faɗi zai jawo ba. "Nidai ba satar ɗanta na je da niyyar yi ba. Babansa ne ya ke da buƙatar ganinsa ya nemi alfarma na kawomasa shi ƙofar gidan koda kuwa na mintoci ne sai na maida musu shi." Ya ji zuciyarsa ta yi wani irin tuƙuƙi. Babansa? Shi dai da ya ke da alhakin keta alfarmar macen da a yau yake jin babu ya ita a zuciyarsa? Shi din dai da ya yi garkuwa da ita? Nan da nan jijiyoyin kansa suka fito raɗau, idanunsa suka kaɗa. Ya murza yatsun hannunsa suka yi ƙara ƙas ƙas. "A ina zamu same shi domin mu tabbatar da abin da kike magana a kai?" Sai kuma ta hangi wautarta, nan da nan ta soma zufa. Ya dakamata tsawar da sai da ta miƙe tsaye tsabar firgici. "Ki sanar da ni!" Wayarsa dake gefe ce ta katse shi, ganin mahaifiyarsa ce ya sanya shi saurin ɗauka ba tare da ya ɗaga ba ya fita a dakin da sauri, a duniyar Ridwan ba shi da abin girmamawa sama da ita. Mutum ne mai matukar gudun zuciyarta. Ya samu kyakkyawar shaida ta girmama uwa a wurin mutane. An kuma ci sa'ar da ya kasance ba ta fiye yi mishi katsalandan kan aikinsa ba. A wannan karon da Hajiya Lubna ta shaida mata alfarmar da take nema na sakin Nusy bayan ta roƙi alfarmar ta sirranta sunanta. Sai ta yi kiran ɗan nata don jin taƙamaiman wace ce Nusy din. Ridwan jin tambayarta ya yi mamaki, koda wasa bai sanar da ita komai game da Nusy ba amma lamari an Jannat da ma su Ummita babu wanda ba ta sani ba. Kasancewar ba su yi zaman hira ba ne ya sa koda wasa zancen Nusy bai haɗa su ba. Bai nata tambaya kan tambaya ba, sai ya zaɓi labarta mata dukkan komai. Hajiya Fa'iza ta amsa masa bayan gana sauraro. "Ka cigaba da bincikenka, ina fatan Allah ya baka nasarar magance komai. Allah ya yi maka albarka. Ya nunamin cikar burina kafin mutuwata. " Ya yi murmushin jin dadin wannan addu'a, ya sani ba ta da buri sai na son ganin aurensa, shi kuma ya sani kukanta ya zo karshe da yardar Allah don ya riga da ya gama samun wacce yake jin zai iya ƙare rayuwarsa da ita. *** Labarin Jannat ya karaɗe ko'ina, mijinta ya samu zuwa ya kuma kawo sarƙoƙinta da aka nemi ya kawo, an siyar an haɗa da motarta amma duk da haka su na buƙatar cikon wurin miliyan hudu da rabi. Anna ta tattara nata ajiyar da bai cike miliyan ba ta bayar, Mami kuwa dakyar ta sanya dubu dari takwas inda ta rantsewa Anna su kadai gareta, duk da haka dai da sauran rina a kaba. Futuha ta bada dubu dari uku, Tasleem ko ba ajiye ba balle ta bayar, sarƙarta ɗaya ta gwal da ta mallaka ta yi shiru don ta san ba lallai ta samu ta mayar ba. Akan haka har Futuha sai da ta yada mata magana, wai duk tsananin kusancinta da Jannat ta kasa bada ko biyar da za'a haɗa a biya don a samu ta fito. Ita dai ba ta biyemata ba ta banzatar. Anna da kanta ta taka har zuwa gaban Abba da ya yi burus da batun Jannat sai shirin bikin Humaira da yake gudanarwa, roƙonsa ta shiga yi da kuka sosai akan ya taimaka ya sa hannu ko iyaka hakan a bayar don Jannat ta fito. Abba ya bata hakuri ya nunamata babu abin da zai iya yi a kai tunda dai magana ba a hannunsa take ba. A hannun hukuma da kuma yaran da aka ɓatawa yake. Wannan al'amari ya yi mugun dasa haushin Abban a zuciyar Anna. Ta kuma daɗa roƙonsa toh ya taimaka ya cika koda bashi ne idan ya so bayan fitowar Jannat din sai ta biya shi. "Kiyi hakuri Hajiya, a yanzu dai ba zan ce akwai su ba, na tattara abinda ke hannuna na bada odar kaya na shaguna na, abin da ya rage kuma shi nake amfani da shi wajen fita kunyar jikarki da bikinta ke tafe." Ina wuta Anna a jefa Abba don kiran Humaira da sunan surukarta da ya yi. Kamar ta dura masa ashariya haka ta ji sai dai ta daure ta haɗiye ɓacin ranta. Shi kuwa Abba miƙewa ya yi yana gyara zaman babbar rigarsa don ya kammala shirin fita kasuwa a ladabce cikin danne ɓacin rai ya ce. "Ni na fita Hajiya, lokaci na tafiya. A yi hakuri za a samu mafita in sha Allahu." Yana kaiwa nan ya sa kai ya bar falon sai ƙamshin turarukansa da suka bi bayanshi suka shige kofofin hancinta. "Kai wannan Isuhu an yi ɗan duniyan ƙarshe, yanzu a dubi tsabar idanuna ya shirgan uban ƙarya duk don kar ya taimaki auta? Oh ni, yau naga abin da ya fi karfina. Aikuwa duk muguntarka sai yarinyarnan na fito tunda kai azzalumin mutum ne, sai baƙin mugunta kamar wani arne a cikinsa." Ita kaɗai dai ta dinga bambamin nan har ta kai aya babu wani a falon da zai taya ta daga karshe ta yi kwafa ta miƙe ta bar falon. *** A yau Raihana ta ƙudurta sai ta bincika wayar Maminta, duk irin kwaɓar da zuciyarta ke yi mata ta kasa hakura. So take ta ga da wanda Mamin ke waya har ta kai ga ba shi umarnin kashe Abbansu. Idan har ta yi nasarar samun lambar mai shi, toh kuwa ta yanke Abban za ta kai wa don ya bayar a kamo mutumin. Wannan ya sa a yammacin yau ranar Talata tana dawowa daga jarrabawar da suka soma na WAEC ta dinga fakar idanun su Tasleem da Yassar dake zaune a falo ana hira ta mike ta bi bayan Mamin zuwa dakinta da ta shiga. Ta kudurce idan har suka yi kiciɓus za ta wayance da tambayarta maganin ciwon kai wanda gajiya da kuma damuwa suka haifarmata, idan ko ba su hadu ba to wayarta za ta durfafa. Cikin iko na Ubangiji kuwa ko kyallin Mamin babu sai motsin ruwa da ta ji a banɗakin. Hamdala ta yi jiki da hannu na rawa ta dauki wayarta dake saman gado ta bude don ta san lock din. Kai tsaye ta shiga Call log ta hau dubawa har ta kai kan na kwanan watan da Humaira ta tafi, tana yi tana kallon ƙofar bandakin, har idanunta ya kai ga lambar da aka yi saving da WZY wanda lokacin kiran hya kasance da asubahi. Buɗewa ta yi ta karanta lambar har sau uku nan da nan ta ji ya zauna a kanta don babu laifi tana da hadda, da sauri ta fita ta kashe wayar ta bar dakin tana maimaita lambar a ƙasan ranta, Allah ya taimake ta su Tasleem ba su ankara da ita ba, kai tsaye dakinsu ta shiga su Humaira na mata magana ba ta amsa ba don kar ta mance lamba sai da zare wayarta daga chaji ta shigar da lambar ta yi saving sannan ta dago ta dubi Humaira. "Yi hakuri kina magana hankalin yana nan, kaina ke ciwo kinga har yanzu bai bar sarawa ba." Humaira wacce Hajjo ba ta jima da yi mata gyaran jiki ba fatarta sai kyalli take yi don tun a Nijar aka soma ta ce. "Wayyo sannu, bari na samo maki magani wurin Mami." Daga nan Humaira ta mike ta fice, dama tana son ganin Mamin su gaisa sosai, tun zuwanta har yanzun ba su wani gaisa ba. Sun dai gaisa da Hajjo itama sama-sama, ko me Mamin za ta yi a ganinta uwa ce a gareta. Tunda dai aure za ta yi gwara a rabu lafiya. A falon ƙamshinta ne ya bayar da zuwanta, Tasleem ta kuramata idanu kamar ta shaƙo wuyanta ta mutu, cikin dogon hijabi take amma sai wani kamshi da kyalli jikinta ke yi. Ta gaishe da su Yassar wadanda a yanzu babu komai... Innalillahi wa inna ilaihir raajiun! Allah ya yiwa Kakata rasuwa dazu. Ina barar addu'o'inku. Kuyi hakuri da ni na wannan takaitaccen kwanakin. Ayi hakuri da typing errors.A falon ƙamshinta ne ya bayar da zuwanta, Tasleem ta kuramata idanu kamar ta shaƙo wuyanta ta mutu, cikin dogon hijabi take amma sai wani kamshi da kyalli jikinta ke yi. Ta gaishe da su Yassar waɗanda a yanzu babu komai tsakaninsu face mutunci. Kai ka ce ba su taɓa tsangwamarta a rayuwarsu ba. "Ina kike tunanin za ki je?" Ta ji muryar Tasleem a kanta, ta juya ta dubeta. Wani irin duba na ke a wa? Tasleem ta bude baki don mamakin hararar da Humaira ke yi mata, kafin ta samu abin faɗi sai kawai gani ta yi yarinyar ta sa kai a ɗakin. "Amma wannan yarinyar ta mugun rainamin wayo. Don uwarta har ina ma ta magana ta harare ni ta yi gaba?" "Ke dai za ki ji tsoron Allah ki bar takura rayuwar ƴar mutane. Haba Tasleem, kina girma kina cin ƙasa. Nifa dama can kawai taya ɓera ɓari ne amma idan za a titse ni ba zan nuna laifi guda da yarinyarnan ta aikata gareni ba." Cewar Yassar kenan. Tasleem ta kara kufula. "Ai ba za ka gani ba saboda kai babu abin da ka sani." "Sanar da mu." Faɗin Dawud. Ita kuwa sai ta basar, ai da kunya ta ce musu wai kwacen saurayi Humairar ta yi mata, ita a karan kanta ta san zance ne kawai ba hakan yake ba. Su ma kuma sun san komai. Sai ta zaɓi waskewa ta hanyar nunamusu irin fifikon da Abbansu ke nunamata a kansu amma tamkar dai maganganunta ba su samu wani matsuguni ba. Shi Yassar idan dai bushasha da arziki ne, babu irin wacce ba ya yi a dukiyar Abba. Ya zama ɗan karya da kashewa mata kudi. Dawud ma yakan yafici rabonsa amma ya fi Yassar tsoro wannan ya sanya na sa bai fito fili ba. Toh idan dama don kudin ne suke jin haushi da ganin kamar an fi kyautatawa Humaira, ai dai yanzun su ma suna yagar na su. Wannan ya sanya ko a jikinsu. *** Humaira da sallama a bakinta ta tura kai dakin Mami, ta iske ta tsaye riƙe da wayarta tana dannawa amma ganinta sai ta yi saurin juyowa tamkar wata marar gaskiya can kuma ta basar ta hanyar saita kanta ta ajiye wayar ta nufi gaban madubi don goge jiki. "Mami ina wuni." Ciki-ciki ta amsa. "Lafiya." Shiru ya ɗan biyo baya, ita ba ta ce uffan ba hakanan Mami dake shafa mai a jiki. Wayar Mamin ce ta yi ƙara Humaira ta mike da zummar ɗauka ta miƙa mata, amma kafin ta kai ga wayar ta ji Mami ta dakamata tsawa. "Kar ki kuskura!" Tana fadin haka ta taso da wani mugun sauri ta kai hannu ta dauki wayar, WZY ne ya kira. Humaira dai tana tsaye kamar an shuka icce tana kallon Mamin har lokacin kirjinta duka yake don ba kaɗan tsawar da Mamin ta yi ta tsorata ta ba. Mami ta ɗan saci kallonta sannan ta katse kiran, a karshe ma ta danna Airplane mode yadda ba zai kara kira har ya same ta ba. "Ina ruwanki da wayata? Bana son iskancin wofi, kin wani shigo kin min tsaye a ka, toh kin gaishe ni ba ina ce shikenan ba sai ki juya ki tafi?!" Ta numfasa. "Kiyi hakuri Mami, Raihana na zo karɓarwa maganin ciwon kai ya matsa mata kuma daga nan na..." "Kiyi me?! Raihana ni baƙuwarta ce da ba za ta iya zuwa ta karɓa da kanta ba? Har akwai wani shamaki tsakaninmu ina uwarta mahaifiya?!" Kalaman sun daki Humaira da har ba ta iya ɓoye mamakinta ba ta dubi Mami dakyau amma sai ta ji miyan bakinta ya kafe ta kasa cewa uffan. Tsakin da ta ji Mami ta yi ne ya maido ta cikin tunaninta. "Kiyi hakuri nayi zaton da kai da kaya duk mallakar wuya ne, ban ɗauka akwai bambanci tsakani ba. Amma zan kiyaye tunda an ankarar." Tana kaiwa nan ba ta jira me Mamin za ta ce ba ta yi gaba da sauri ta fice ta bar kofofin hancin Mamin da shaƙar ƙamshin da ta bari. Bayan fitarta Mami ta ɗan dafe goshi, meyasa? Meyasa ta ke kasa sarrafa kanta a kwanakin nan, gaba daya ta kasa hakurin ɓoye abin da ke ranta. Amma ta sani adalilin wannan daukakar da ta zo ga Humairar ce alhalin nata yaran na watangalili a gidan mazajensu sun kasa samun jin dadi da walwalar da ta so musu. "Ya zama dole na kula kada taɓarɓarewar abubuwa su fi wanda nake fuskanta a yanzu." Ta yi furucin a fili, ta kalli wayarta ta ƙi fitar da ita daga plane mode ba don komai ba sai gudun abin da Wizzy zai fesar mata. Ta san ba za ta ji mai kyau da kuma dadi ba don haka ta yi watsi da lamarinsa. *** Futuha ce kwance a falonta tana danne-danne a waya kamar yanda ta saba, sai ta wuni gida a ƙazance idan har ba yarinyar da ke mata aiki ce ta zo ba. Ba ta kauda ko tsinke, girki ma hakanan take hakuri da yanda yarinyar ke jagwalgwalawa ta kawomata. Kira ne ya shigo wayarta, sunan ƙawarta Aina'u da ta gani ya sanya ta ɗagawa. "Marar mutunci, sai yau kika tuna da ni?" Cewar Futuha cikin walwala. Tsaki Aina'u ta ja. "Ba dole ba, ke yanzu don wulakanci da daukata da kika yi ƴar iska kika kasa sanar da ni abin bakin cikin da ya sameki, koda dai na ji muryarki ma babu wata alama na ɓacin rai." Sai tunanin Futuha ya ba ta ko batun Anti Jannat take yi, kasancewar Aina'un ta san Jannat sadda suke gida.  "Toh banda abinki wannan ai ba abin yayatawa ba ne, don ma dai kudaden da aka buƙata babu wani yawa, just 10millions fa." Wani uban ashariya Aina'u ta saki ta wayar kafin ta ce. "Kada dai ki cemin ba ki da labarin auren da Yakubu mijinki zai yi da Ƴar Snow?" Ai sai ga Futuha a tsaye kirr saman ƙafafunta. Kirjinta wani dukan tara-tara ya shiga yi. "Wannan zancen banza ne kike yi, Yakubu fa yana Dubai. Wace Ƴar Snow din kike maganar zai aura?" Wata dariya Aina'u ta saki. "Lallai Futuha wayonki ya tashi a banza. Toh ita Ƴar Snow din kika san ina take? Wallahi tana tare da shi a can ma suka hade lefen nan da kika ga hotunansu, ina maki magana ba cikin satin nan ya ce maki zai dawo ba? Toh tare za su taho da ita kuma yana zuwa aure za'a daura. Gidan da ya fidda ki a ciki, nan zai ajiye ta har an ƙara yi mata wani mahaukacin gyara ya yi kyau." Ihu mai karfi Futuha ta saki har sai da ta razana Aina'u. "Ƙarya kike yi! Ba dai mijina ba! Ke uban wa ya fadamaki duka wannan?! Aina kar ki kashe ni, kirjina zafi yake ina ganin dishi-dishi." Aina'u ta hau rantsuwa da Allah akan dagaske take yi, kuma ta ce tunda har ba ta aminta ba za ta hankaɗo mata hotuna ta sha kallo. Ko sakanni biyar ba su yi ba da ajiye wayar Aina'u ta aikomata hotunan da Ƴar Snow ke ɗorawa tana rufe fuskar Angonta. Gaba daya Yakubunta ne a hoton. Ta kuwa buga wayar jikin talabijin dinta gami da fasa uban ƙara. A haukace ta shiga daki ta dauki mayafi sai gida. *** Raihana bayan da ta lura hankalin kowa ya tafi akan Humaira da Hajjo ke yiwa gyaran jiki kasancewar yaran Baba Amina sun zo itama tana dakin, sai ta mike ta nufi bangaren Abba. Mami ta fita unguwa, cikin sa'a ta iskeshi zaune shi ɗaya ya kammala shan fura. Ganinta ya sanya shi ɗan zubamata idanu da amsa sallamarta. Ta ƙaraso ta zauna a gefe. "Rahane (sunan da ya ke kiranta a wasu lokutan), ba ki da lafiya ne kwana biyun nan?" Ta sunkuyar da kai gami da bude baki cikin sanyin jiki ta amsa. "A'a Abba, lafiyata kalau." "Kin kasa cire maganar can a ranki ko? Meyasa ba kya jin nasiha? Nace maki ki bar komai a hannuna tun da na riga da na ankara toh da yardar Allah hakan ba zai ƙara kasancewa ba. Ai wataran za a kuma kwatawa, kinga sai ya kasance muna da shaidu ba kamar yanzu ba." Raihana da tuni hawaye sun jiƙa fuskarta ta gyaɗa kai da ɗan jan majina. "Toh Abba, dama na dauki lambar wanda Mami ta kira a ranar ne shi ne nace bari na kawomaka nasan zai taimaka wajen bincike." "Ya aka yi ta bari kika taɓa wayarta? Na sha gwada yin hakan amma ban samu nasara ba." Ya fadi cike da jin dadin wannan nasara, ko ba komai za'a bincika a kamo shi yaron da aka sanya ya aikata laifin. Ta ba shi labarin yanda aka yi ta dauka sannan ya fiddo wayarsa ta sanya masa lambar. "Kiyi hakuri Raihana, na sani daga ni har ke mun kasa yarda da abin da yake a zahiri saboda inda ake zatonsa ba anan aka iske shi ba. Abin ya zo da daure kai da al'ajabi, ina fatan wannan ba zai hana ki cigaba da yin biyayya gareta ba, kema kuma ina fatan da zarar kin kammala jarrabawa ki yiwa shi yaron can magana ya fito a yi magana." Gyada kai kawai Raihana ta yi, ita yanzu komai ma na duniyar ji take ya sire mata, har kullum fargabarta bai wuce da idanun da za ta dubi Humaira idan wannan ɗanyen aikin na Maminta ya fito ba. Daga haka suka rabu da Abban. Shi ko Abba kai tsaye ya tura lambar zuwa ga D.P.O sannan ya kirashi suka yi magana. D.P.O ya tabbatar masa da yardar Allah za su bincika har su cafke mai wayar. Da haka suka yi sallama. *** Babandi kenan, baƙin kuma gabjejan ƙato mai tumbi zaune saman kujera ya ci uban rawanin da ko zafi bai yi masa. Mami na daga gefensa a zaune, falon tsaf sai iskar fanka ta ko'ina domin gidan Malam Babandi solar ce ke aiki. Tsohon Malami ne kuma babba da ya ci ya hantse da haram. Ya dubi Mami dakyau. "Gaskiya Hajiya Maryam akwai matsaloli sosai. Na farko kin yi saken da yaranki suka san komai dangane da abin da kika shuka, wannan idan ba ki manta ba yana daga cikin sharuɗɗan da na taɓa gindaya maki a baya, wato kar ki kuskura a yanda kika faro mu'amalarki da kowa, ki bada ƙofar da wani ko wata zai ji. Idan ban manta ba kwanaki can kin faɗamin kin sanar da ita babbar yarinyarki, koda muka bincika muka ga ba zai haifar da matsala ba amma duk da hakan ai na kwaɓe ki. Yanzu dai ita wannan yarinya taki ta biyu, Yasmeen take ko?" "Tasleem." Mami ta gyara masa da muryar da ta fito daga can ƙasan maƙoshinta, a duniya ba ta son rashin nasara a kan komai ma ba wai iyalinta ba. Babandi ya cigaba da zancensa. "Yauwa Tasleem, yarinya ce mai taurin kai da kafiya a yanda na gani, zai wahala ta iya bar wa cikinta komai." "Nidai don Allah Babandi a yi dukkan abin da ya dace idan har kwalliya za ta biya kudin sabulu, sannan batun auren ita Humaira da yaron can, kiyi hakuri, ban hango wani katanga da zai yi sanadin rushewarsa ba. Sai dai abu ɗaya, ki zaɓi ta ɓangaren da kike son a musgunawa rayuwarta mu gani ko zai yiwu. Abu na gaba kuma wato mijinki Isuhu, ba zan ce maki ga abin da na gani ba, amma wacece Maijidda? A zuri'arsu akwai wata mai suna hakan ne?" Gaba daya abubuwan da yake faɗi tana jinsa ba don tana fahimtar komai ba, ba ta tashi dawowa hayyacinta ba a gigice sai da ya ambaci Maijidda. Ta ji dam! Wata iriyar faɗuwar gaba. Idanu waje take dubansa. "Me..me kake son ka ce?" Babandi ya girgiza kai. "Tambayarki nayi ko akwai Maijidda? Ai ban ce ba tukunna." "Babu, ba mu da wata Maijidda hakanan shi kansa Alhajin." Babandi ya yi wani irin murmushi gami da girgiza kai. "Toh ai shikenan." Ta dube shi cikin fitar hayyaci. "Me zai faru da shi Isuhun da Maijiddar?" Ya ɗan zubamata idanu sai kuma ya numfasa. "Duhu na hanga, ban gane komai ba. Na dai ga wata an kuma cemin Maijidda ce. Ban san manufar hakan ba." Gumi ne ya shiga kwaranyo mata. Maijidda dai? Toh don uwar Maijiddan me za ta yi a rayuwar mijinta? Kada dai waccan tsohuwar kilakin da duk mijin da ta aura mutuwa yake yi ita ce Maijidda da Babandin ke nufi? Toh ma da take tunanin aure ne zai faru tsakanin shi Isuhun da Maijidda? "Ina!! Wallahi na rantse maka idan ni Maryama ina raye Babandi ba ka isa ba! Ashe dama kai macucin banza ne?! Wato aure ka hanga tsakanin baƙar annobar can da mijina shi ne za ka yimin na ƴan bariki?! Lallai kai cikakken marar hankali ne da tunani! Ni Maryam kake tunanin ina raye san bari Isuhu ya auri wata bayan ni?!" Babandi ya ji zafin maganganunta. "Hajiya Maryam kar ki sake ki zage ni. Ni nace maki na hangi aure ko zama tsakani? Har yau duk da irin shekarun da muka kwashe da ke ki iya kallon cikin idanuna ki kira ni da marar hankali kuma macuci?!" Idanun Mami sun rufe ruf akan baƙin kishin da ya tasar mata, ji ta yi kamar Abban take gani zaune a gabanta. Babu abin da take haskowa sai tabbatuwar aure tsakanin Maijiddan da Abba. Jikinta kuwa har rawa yake yi don haka a harzuƙe kuma cikin kururuwa ta daka masa tsawa. "An kiraka ɗin! Nace ka yi uwar da za ka yi Isuhu! Ni ce ma banzar da na zauna sauraron tatsuniyoyinka marasa kan gado. Yo mutumin da yake da mata har huɗu hakan bai isheka ba kana neman almajiranka maza kai zan tsaya ka magancemin matsalolina alhalin kodayaushe lalacewa yake! Ni nan na ishi kaina! Zan yiwa kaina komai! Daga yau idan ka kara ganin ƙafata a inda ka ke kirani da wani sunan ba Maryam ba!" Tana kaiwa nan ta yi gaba tana ji yana fadin sai ta yi muguwar nadamar zageshin da ta yi amma ba ta ko juyo ba balle ta ji nadamar kalaman da ta yi mishi. *** Kamar tare suka isa cikin gida da Futuha wacce ke faman kwara ihu tana kiran wayyo. Mami duk da yanayin tashin hankalin da take ciki sai da ta ji cikin ya yi mugun ɗurar ruwa, idan akwai wani abu da ta tsana a rayuwarta bai wuce ta ji ko ta ga wata masifar ta afkawa yaranta ba. Yaran da ta ci kwakwa wajen ganin rayuwarsu ta inganta. Ta ɓoye ainahinta ga duniya domin ta samu kyakkyawar shaidar yaudarar mutanen da take tare da su duk don ingancin da ta ke son rayuwar yaranta su yi. "Ke! Meye haka? Wannan wane irin hauka kike yi kina neman tara mana jama'a?" Futuha cikin kuka take sanar da Mami labarin auren Ƴar Snow da Yakubu. Ta ƙara da faɗin. "Ni wallahi Mami ba zan zauna da ita ba, na fasa aurensa dama ai bakin cikin abin da ta aikata min na ɓata sunana a soshal midiya ne ya sanya na aureshi. Toh wallahi na gama aurensa!" Jiri sosai ta ji yana nema ya kayar da ita, daidai lokacin kuma aka buɗewa Fadeel katon ƙyauren gidan ya shigo ya yi parking, ganin Mami ya sanya shi fitowa sai baza ƙamshi yake har wata ƴar ƙiba ya ƙara saboda kwanciyar hankali da murnar samun farin cikinsa. Ya ci ado cikin shaddarsa coffee da hula kalarta. Mami kallonsa take yi, kallon kai ne silar rugujewar rayuwar ɗiyata Tasleem, kai ne kuma silar da aka kama ƴar uwata Jannat. Shi kuwa a kunyace da kuma ban girma ya ɗan russuna ya gaisheta. Madadin ta amsa sai ta buɗe baki da zummar gasa masa baƙaƙen magana amma ta fasa hango Yassar da ta yi ta baya yana mata alama da hannu, alamar roƙon ta yi hakuri ta bar wa cikinta. Yana jin duk yanda suka yi da Futuha, ta harari Fadeel kawai ta ja hannun Futuha da ta ɗan danne kukan ganin Fadeel din zuwa ciki. Bai yi mamakin hakan da ya gani tattare da Mamin ba don ya lura tun a kotu take shaƙe da shi saboda kama Jannat, amma a zatonsa tunda har dai kauna ta don Allah ta ke yiwa su Humaira ai ya ci ace ta ji dadin tonuwar asirin wanda ya ɓata musu suna. Sai Yassar ne ya ja shi zuwa masaukin baƙi. *** Suna shiga falon suka yi karo da Humaira ta yi kyau shar da ita cikin lemon green din leshi ta yafa baƙin mayafi. Ba ta yi kwalliyar a zo a gani ba amma fa fatarta ta gogu tas. Ganinsu ya sanya ta gaida Mami gami da yi mata barka da zuwa bayan ta ɗan kula da yanayin tashin hankalin dake saman fuskokinsu har ita Futuhar. Mami ba ta amsa mata ba sai ta yi gaba, itama Humaira ganin hakan sai ta soma tafiya domin ta fita. "Ke!" Ta tsaya gami da juyowa ga kallon Mamin. "Ki yimin farfesun nama yanzu ina jin yunwa." Humaira ta ɗan yi turus, ta mance rabon da Mamin ta sanya ta koda tafasa ruwan zafi ne. Sai yanzun da Fadeel ya zo sannan za ta kirkiro aiki? "Ko ba za ki yi ba?" Tambayar Mamin ya katse tunaninta, jiki a sanyaye ta ce. "Zan yi." "Toh wuce ki je." Daga nan Humaira ta kama hanya ta nufi kicin. Wannan ya faranta zuciyar Tasleem dake zaune har da kyakyacewa da dariya. *** A can kuwa Fadeel da ke zaman jira shiru, yana kokarin kiran wayar Humaira sai ga Abba ya shigo. Bayan sun gaisa ya ce "Ba ta fito ba ne?" Fadeel yana ɗan sosa ƙeya amma bai ce komai ba. "Shikenan." Abin da Abban ya furta kenan ya nufi ciki. *** *Assalamu alaikum yan uwana.* *Nagode da sakonninku na gaisuwa da masu kira da ma whatsapp.* *Nagode Allah ya bar zumunci.* ©Rufaida Umar.*DUKAN RUWA* _Ba zai hana gwarje amo ba._ Da Raihana ya soma kiciɓus ta fito daga kicin inda ta tarar Humaira ta kama aiki ranta duk a ɓace don ta yi duk iyaka yinta ta bar mata aikin ta tafi amma ta ce sam tunda Mamin ta sanya ta za ta iya yi ta je ta ba wa Fadeel hakuri ya tafi kawai. Ganin Abban itama sai ta ji sanyi ba ta ko gaida shi ba ta tafi kai tsaye kan abin da ke cin ranta. "Abba ga Humaira ta bar Yaya Fadeel ya.." "Ya isa, kiramin ita." Abban ya katse ta, ya yi daidai da fitowar Mami daga dakinta. Ganinsa sai ta haɗe girar sama da ta ƙas, kallo daya ya yi mata ya kauda kai shima ta sa fuskar a ɗaure sakamakon fitar da ta yi ba da izninsa ba a yau, wani abu da ya zame masa baƙon abu wanda ba ya jin ta taɓa yi masa hakan. Humaira ta shigo falon tare da Raihana, hawaye kwance saman fuskarta kafin ma ta kai ga cewa wani abu Abba ya tari numfashinta. "Shirya ki je kin bar mutum zaune yana ta jiranki." Jiki a sanyaye ta dauki mayafinta dake saman kujera, Mami itama zuciya a sama ta ce. "Ni kuma ban miki iznin fita ba! Aiki na sanya ta ai, don me shi ba zai iya jiran ta kammala ba tunda ganinta a yau din ya zame masa tamkar rubutu a saman dutse?" Humaira sai ta yi turus, Mami dai ba za ta daina shayar da ita mamaki ba. Ƙiyayyarta a fili na wannan auren ta ke nunawa ba ta ko iya ɓoyewa. "Duk ikonki akan ta bai kai ya ni ba, daga ita din har ke din karkashina ku ke, babu dalilin da zai sa na zuba idanu a mayar da ni sakarai a gidana. Don haka Humaira kar ki yarda na ƙara ba ki umarni na biyu, ki wuce yanzu." Ambatonta da Humaira da Abban ya yi wanda bai taɓa kwata hakan ba ya sa ta fahimci abin ba mai sauki bane don haka sum sum ta sa kai ta bar falon tana jin Mami na bambamin faɗan wai Abban ya nuna dagaske ba ita ta haifi Humaira ba kuma ba ta ita ta ce mata ta yi, ta yi din ba. Ita dai ta fice da sauri tana share fuskarta. Abba ya dubi Mami dakyau, kamar zai ce wani abu sai kuma ganin Raihana a wurin. Juyawa ya yi zuwa bangarensa can din ma bin bayansa ta yi. "Diyarka ta dawo gida saboda maci amanan mijinta zai auri abokiyar faɗanta. Nima kuma ina goyon bayanta don ban ga wani dalilin da zai sa ya yi mata wannan tozarcin ba a idon duniya." Cikin al'ajabin wannan sabon labari da ma rashin fahimtar inda aka dosa Abba ya kalleta kallon tsanaki. "Wane tozarcin? Wa kuma kike magana a kai?" Ta harareshi kamar idanunta za su zazzago. "Matan da ka aurar har su nawa ne? Ina magana ne kan ɗiyarka Futuha. Shi Yakubun ko sanar da ita batun ƙara auren bai yi ba saboda ya san auren cin amana ne. Kuma ni dai Maryam yanda ba zan dauka a yimin ba hakanan ba zan zuba idanu a halakar da kuruciyar yarana ba a hana su walwala da jin dadin zaman gidajen mazajensu. Tana nan gida na kuma hana mata komawa, ta yi zamanta har sai ya zo ya janye batun auren can da zai yi. Ya rasa wacce ma zai aura sai yar iskar Tiktok da ta yi mata ƙazafin zina a baya?" Tsananin ɓacin rai da baƙin cikin da ma nadamar kyawawan shaidun halayyar da ya yiwa Mami a baya suka bi suka lulluɓe shi, ga kuma zafin da maganganunta suka haifar a cikin ƙirjinsa. Ya miƙe tsaye jijiyoyin kansa sun fito raɗau tsabar ɓacin rai. Wayarsa kawai ya fiddo ya danna lambobin Futuha, umarnin ta zo ya yi mata, ba jimawa ta shigo tana ɗari-ɗari ta zauna can gefe kusa da Mami. Shi kuwa Abba har lokacin yana daga tsaye yana safa da marwa, sai bayan zaman Futuhar ya soma magana murya a kausashe. "Maryam! Idan har na isa da ke da kuma ɗiyar da kike tutiya taki ce, ni Isuhu ba zan lamunci zamanta a gidana ba alhalin da igiyar aure a kanta. Ke kuma na rantse maki kika yi gangancin kwana a gidannan sai na nunamaki ni Isuhu na haifu kuma babu wata ɗiya ko ɗan da zan haifa a cikina ya yi tunanin zan biyewa son zuciyarsa na banza!" Mami dama a ƙule take don babu abin da ke yawo a kwakwalwarta sai maganganun Babandi, wani mugun haushi Abban ke ba ta. Ta kuwa miƙe itama a zafafe ta ce. "Ni kuma nace babu inda za ta je! Ba zan yarda da auren cin amana ba! Idan kai ba ka san darajar abin da ka haifa ba har ka nema mishi ƴanci, ni nan Maryam ban haifar yarana ga wasu ƙattin banza don su tozartamin su ba! Ai ba su tashi sun ga uwarsu da kishiya ba!" "Ba zan yi mamakin kalamanki ba Maryam saboda a yanzu ne nake sanin ainahinki ba lulluɓin da kika yimin ba a baya, yanzun kike nunamin ke wace ce. Toh ki sani, ni dai gida nawa ne, ban ginashi da kwandalar kowa a cikinku ke da yaranki ba. Wallahi a yau sai Futuha ta koma gidan mijinta ba za ta kwana a gidana ba, idan kuma kika taka umarnina sai dai ki sa ƙafa ki bita duk inda za ta je amma na yi rantsuwa babu kaffara yarinyarnan ba za ta kwana a gidana ba. Ba kuma tsoronki nake ba da kike tutiya da fankamar wai ba su buɗi idanu sun ganki da kishiya ba! Amma ki sa a ranki zan nunamaki ni din namiji ne ba MIJIN MACE DAYA ba." Kirjin Mami ya buga dam! Maijidda ita ta faɗo ranta. "Me kake nufi?" Ta tambaya a rude, madadin ya ba ta amsa sai ya sa kai ya shige dakinsa. Futuha kuwa kuka sosai take yi jin irin yanda iyayen ke musayar yawu. Ta miƙe tsaye ta kama hanya. "Ke, na fa ce babu inda za ki je. Ki shiga cikin dakina kiyi kwanciyarki." Za ta so hakan amma fa ba za ta iya ba don ta tsorata da yanayin Abban. Ta sani mutum ne dama tun can mai zafi idan an taɓo shi sai dai kalar ɓacin ran yau da ta gani ba irin wanda ta saba ganinsa ciki ba ne a ire-iren lokutan da aka taɓo shi ba. Wannan ne dalilin da ya sa cikin sheshsheka ta ce. "Aa Mami, zan koma amma na rantse idan Yakubu ya dawo sai ya bani takardata ba zan iya cigaba da rayuwa da shi ba." "Don ubanki ni za ki watsawa ƙasa a ido?" Futuha ba ta amsa ba sai kawai ta yi gaba ta fice da gudu gudu. Mami kam zama ta yi ta fidda dankwalinta tana yiwa kanta firfita saboda ji take ma iskar dake wulwulawa a dakin kamar feshin iskar wuta ce ba ta yi mata yanda ya kamata. Yau dai Abba da kansa ya iya kallonta ya faɗamata maganganun cin fuska son ranshi? Wato rigar mutuncin da ta ara ta yafa ya fiye mata alheri akan zahirin ita a idanunsa? Dama ba mallakarsa ce ta yi ba yake shakkarta kawai albarkacin wancan kyawawan halayyar da ta ke nunawa ta ci? Toh wai ita ba ta ma fahimta ba, aure yake nufin zai yi? "Wallahi Isuhu ba ka isa ba! Ka yi kaɗan!!" Ta yi furucin cike da hargagi da ɗaga murya, babu wani da zai ba ta amsa don haka ta kwashi jiki ta yi bangaren uwarta, yau ce ranar farko tun bayan aurenta da ta ji tana buƙatar shawararta wajen waɗannan ƙullace-ƙullacen da take yi. Shakka babu idan gininta na tsawon shekaru ya rushe ko kuma ya karasa rushewa za ta kwashi kashinta a hannu. *** Fadeel ya yiwa Humaira duba na tsanaki, tana cikin wata damuwar da duk iyaka kokarinta na yin murmushin yaƙe sai da ya ɗago ta. "Ka yi shiru." Ta furta a sanyaye ganin sun kwashi mintoci cikinsu babu alamun wani zai ce uffan. Ita tunanin sabuwar Mami da manufofinta ke dukan zuciyarta shi kuwa damuwarta ce ta haifar da ta sa. Tun da ya ga yanayin da Mami ta tarbe shi ya san akwai wata a ƙasa, ya kuma fi tunanin rashin nutsuwar Humaira saboda ganin Mamin cikin wani yanayi ne. Bai kawo komai bayan wannan ba. "So nake ki gama tunaninki." Ta girgiza kai. "Ni ba tunani nake yi ba fa." "Boddo please. Ko meke damunki kiyi hakuri ki cire shi a rai idan ba haka ba zan samu Abba da Alhajina yanzu kawai a daura auren na wuce da ke gidana." Ya ba ta dariya dagaske, ta ɗan bishi da hararar wasa. Shi ma murmushin ya yi mata gami da ɗan ɗaga gira kaɗan. A ƙarshe suka sha hirarsu sosai da ta mantar da ita Mami da sabgarta. Sun ɗan jima kafin su yi sallama ya fice. *** Anna ta muskuta tana kara tamke fuska, ai ita yanzu kam a duniyarta babu abin da ta tsana sama da Abba da wadancan yarannasa biyu da suka yi sanadiyyar kama autarta. Ta sanya gonarta ɗaya babba ta can Agadez a kasuwa yanzu haka an samu mai siya duk da akwai faɗuwa sosai a yanda aka taya amma ita dai burinta a samu abin cikawa a fiddo Jannat wacce mijinta ya yi ƙememe ya kuma rantse ba zai ba da ko biyar ba tunda ba shi ne ya sanya ta aikata ba. Dama yana cike da jin haushin yawon da ta ke yi bini-bini idan abu ya tashi sai ta matsa mishi za ta zo Nijeriya. Ga rashin ɗaukar yan uwansa da daraja, ganinsu take ƴan ƙauye futuk. "Ke Maryam, idan za ki buɗe zuciyarki ki fito ki nunawa wancan sokon mijinnaki Maryam ce da ba a nunamata ɗan yatsa ba ta karya ba. Ai ni da ace tun farko ma nasan wautar da kika yi kenan na wannan makircij da bai kai ki ko'ina ba da ba zan bari ba. Ai gwara mutum ya sanka da halinka amma yanzu zai dinga yi maki wani kallo saboda ba haka kika nunamasa a farko ba. Yanzu dai ki jira ƴar uwarki mu samu ta biya wadancan karnukan kuɗinsu sai a san me za a yi." "Yanzu Anna sai Jannat ta fito za ki duba matsalata?" Mamin ta furta cike da takaici. "Ke ba kya tausayinta ashe? Ita tana can a garƙame cikin yanayin a tausayawa ke kuwa ai naki mai sauki ne. Ki tashi tsaye ki ƙwatarwa yaranki ƴancinsu ta ƙarfin tuwo idan ba haka ba dama na fadamaki tun ba yau ba, Isuhu zai iya tattara rabi da kwata na dukiyarsa da sunan na Ummita ne yake juyamata." Annar ta yi mata wani tuni mai ƙarfi da muhimmanci, tabbas akwai dukiyar Ummita a hannun Abba, duk kuwa da cewa shima Abban ya samu gadonsa a dukiyar ƙanin nasa. Tana tsoron Ummitar ta tashi aure ya ce zai tattara komai ya damƙa mata abinta da mijinta, idan kuwa hakane ita ya dace ta samarwa Ummita miji ba kowa ba. Mijin da za ta iya juyashi son ranta ba wanda zai gagareta sarrafawa ba. Mijin da ba zai zama ɗan da ta haifa da cikinta ba. Toh wa za ta samu haka? "Ina magana kin yi shiru." Kalaman Anna suka katse tunaninta. Miƙewa tsaye tana wani murmushi mai tarin ma'anoni. "Zan san abin yi." Daga haka ta fice ba tare da ta ƙara ba Anna amsar tambayarta na me za ta yi ba. *** A kwana a tashi cikin hukuncin Allah har ranar sanya Humaira a lalle ya gabato. Ana gobe za a soma shagalin bikin sai ga yan uwanta daga Nijar sun dira a gidan. Mami duk shige da ficen da Baba Amina ke yi da ma wasu a ƴan uwan Abba da kuma Hajjo babu ko ɗaya da ta sanya hannunta ciki. Ita kuwa Humaira ta tattara batun Mami ta ajiye gefe bisa shawarar Hajjo da Baba Amina. Ta bi Mamin bi bana wasa ba amma Mamin ba ta ko sauraronta. Ga Tasleem a dakin da babu damar a yi wani abin sai ta tanka ta faɗi baƙa, a ƙarshe ma ta tattara ta koma ɗakin Anna da kwana. Hankalin Tasleem ya yi masifar tashi ganin dagaske dai bikin Humaira da Fadeel za'a yi, wannan na nufin za ta tashi a tutar babu kenan? Ta iske Mami hankali a mugun tashe tana kuka kamar ranta zai fita ita fa lallai Mamin ta san abin yi don zuciyarta ba za ta iya zama ta yi haƙurin ganin hakan ya kasance ba. Mami ta dafe kanta dake tsananin sarawa, kwana biyunnan ba ta iya bacci saboda damuwa. "Don Allah Tasleem ki rabu da ni da wannan koke-koken naki. Na samu tabbaci daga Babandi aurennan fa sai an yi babu makawa. Wannan borin naki zai tashi a banza." Tasleem ta dora hannu a kai wani sabon kukan na kwace mata har da majina. Ashe haka baƙin ciki yake? Haka radadin kishi yake? Toh ita yau duk biyun take ɗanɗana, ganin Humaira kamar wata sarauniya ya sanya ta ji inama ta kashe kanta ta huta saboda baƙin ciki da azabar kishi. Har ji ta yi wasu ƴan uwan Abba na ce mata ranki ya daɗe don hauka, acewarta. Mami da ta ƙuramata idanu gaba daya sai ta ba ta tausayi, Fatima ta haifa mata baƙin ciki ta kuma bar duniyar ta bar ta da shi, gashinan tana ƙunsa. Can ta nisa ta ce. "Toh ko za ki je wajen Babandi, dama ya ce ko bayan auren na fadi abin da nake son a yi musu amma saboda takaicin abin da naji gami da Abbanki da Maijidda sai idanuna ya rufe na ci mishi mutunci. Ki je ki ce nace ya yi hakuri ya dubi lamarinki ya samar maki da mafitar da ta dace. Zan biyashi ko nawa ne." "Mami ki kirashi a waya toh." Harararta ta yi ta ja tsaki. "Kiran me zan mishi bayan na ce maki ga yanda muka yi da shi? Ke dai zan ba ki lambar da kwatance ki je." Ta amsa da toh, a take kuwa Mami ta dauki waya ta turanmata lambar ta whatsapp dinta ita kuwa ta yi mata sallama ta fice bayan ta bi umarninta na shiga banɗaki ta wanke fuskarta. A wajen Anna ta bar ɗiyarta ta fice bayan ta sa facemask ta rufe hanci da bakinta yanda babu wani da zai gane ta a hanya. *** Babandi ya kalle ta tsaf, ya buga wani murmushi mai tarin ma'ana bayan gama sauraronta da kuma jin daga inda ta zo wajensa. 'Kin tafka kuskure babba Hajiya Maryam. Kin kashe ɗiyarki da hannunki.' Ya yi furucin a ƙasan ransa. *RUFAIDA UMAR*Ya nisa kafin ya ce. "Haƙiƙanin gaskiya ba don ina ganin mutuncin Hajiya Lubna da ta zama silar haɗuwata da Mahaifiyarki ba, da babu abin da zai sa na ƙara karɓar wani aikin da ya shafe ta da ma wani nata. Amma tunda har ta fahimci ni Babandi ba za ta iya gudanar da rayuwa yanda take so ba tare da taimakona ba (Waiyazubillah) toh shikenan zan taimaka maki albarkacin hakan." Tasleem ta saki wata doguwar ajiyar zuciya tana ɗan murmushin da ya ƙara kwaɗaitawa Babandi ita. Ya lashi leɓɓansa gami da mayar mata da martanin murmushi kafin ya hau buge-bugen ƙasarsa sannan ya ɗago ya dubeta "Gaskiya Malama Tasleem yau dai kin zo a sa'a domin kuwa koda na ƙara bincikawa na tabbatar za a iya fasa auren Humaira da Fadeel, akwai kuma gagarumin sa'a da ke nuni da cewar za ki zama mallakinsa nan gaba. Sai dai kuma wani hanzari ba gudu ba, aikin da za ki yi hakan ya faru ba mai sauki ba ne."" Da sauri ta tari numfashinsa. "Na rantse kowane iri ne aikin zan iya yinsa muddin zan auri Fadeel." Ya jinjina kai yana shafa gemunsa. "Sai mu'amala ta shiga tsakaninmu har na tsawon wata ɗaya kafin aurenki da Fadeel. Ita ko Humaira a yau zan fara aiki a kanta zuwa ranar da ki ka ce za'a ɗaura auren ina mai tabbatar maki ba zai yiwu ba. Idan dai kika ba da haɗin kai yanda ya dace kuma kika yi gum da bakinki ma'ana kika ɓoye cikinki hatta ga wacce ta turoki nan, toh shakka babu za'a dace. Za ki yi mamakin irin mahaukacin son da Fadeel zai soma yi maki har sai kin ce ya yi yawa." Tasleem ta ɗan yi dum, ga ƙoshi ga kwanan yunwa. Tsaf ta karanci me yake nufi da mu'amala amma sai ta ji kamar dai hausarta akwai gyara a jikk wannan ya sanya ta ƙara neman ya yi mata ƙarin bayani. Nan fa Babandi ya buɗe mata komai ta tabbatar dai saduwar ita yake magana a kai ba komai ba. Ta ƙare mishi kallo, jibgegen ƙato mai mummunan fuska daidai gwargwado. Sai dai ga dukkan alamu yana amfani da manyan turaruka masu ƙarfi marasa dadin kamshi. Ba dai za ka ce yana tashin hamami ba. 'Kar ki sake ki cuci kanki, mene ne a ciki don kawai dai saduwa? Fadeel fa ne za ki aura ya zama a ƙarƙashin ikonki.' Wani sashi na zuciyarta ke mata tuni, nan da nan ta ji ta yi na'am musamman da ta ƙara hasko kanta cikin wannan katafaren gidan da ta samu labarin ya danƙara na Humaira. Ga kuma kayan alfarma na lefe wanda zai dawo mallakinta. Duniya ta yiwa idanunta rumfa ruf, ba ta hangen komai sai ɗaukaka da shaharar da ke gabato ta. Wannan ya sa ta dubansa a tsanake.   "Na amince amma da sharaɗin sai na yi tsarin iyali gudun daukar ciki." Ya yi wani murmushi na mugunta, a ransa faɗi yake.  'Ashe ba ma fansar nayi niyyar ɗauka akan Hajiya Maryam ba. Ai sai kin haifa mata ƙaramar bokanya ko kuma boka.' A fili kuwa sai cewa ya yi. "Ke da kike gaban Babandi, ai ba ki da matsala akan tsarin iyali. Akwai layar da zan ba ki, muddin kika sanya a bakinki yayin komai, ina mai tabbatar maki babu ke babu samun ciki. Ba ma a kaina kawai ba, ko tsakaninki da sabon Angonki Fadeel idan har ba ki shirya ki haihu da shi da wuri ba wannan laƙanin zai maki aiki da ma wasu na sirri. Mallakarsa kuwa kin yi kan gama." Wani dadi ya ratsa zuciyar Tasleem, ta kara samun ƙwarin gwuiwar da ta ji ko rai aka ce ta kashe akan ta samu cikar burinta za ta iya saboda kwaɗayin duniyar da kuma daukakr da ta ke hasasowa kanta muddin ya kasance Fadeel ya zama mijinta. "Shikenan, Malam nidai na shirya komai ma a yi tunda za'a dace. Sannan nidai koda ace Humaira an raba ta da Fadeel, bana son ta auri mijin da ya fi shi ko nan gaba. Na fi kaunar ta auri ƙasƙantaccen da za ta dinga zuwa wurina da ƙoƙon bararta na neman taimako." Babandi ya jinjina kai, ai barewa ba za ta yi gudu ba ɗanta ya yi rarrafe. Ya san ba a ƙas ta tsinci wannan muguntar ba. "Burinki zai cika. Ina zuwa." Ya miƙe ya shiga ɗakinsa kafin ya fito ya miƙa mata laya da umarnin ta tura bakinta. Ta bi umarninsa sannan ta mike suka nufi dakin kirjinta na harbawa amma hakanan ta daure, ba ita ta bar gidansa ba sai kusan goma da mintoci na dare. Babandi ya bi ta da kallo bayan ta fice ya kyakyace da dariyar nishadi, wa ya ƙi banza a rayuwa? Ai wannan lamarin karɓaɓɓe ne ba kuma ya jin zai bar rayuwarta ta sarara. Hakika Tasleem ta faɗi hannunsa. Daga nan ya mike ya gyara jiki ya bada umarnin kada hadiminsa ya bar wani ko wata su shigo ganinsa a sanar da kowa ba ya nan. Aiki sosai ya zauna yi na mallake Tasleem da kuma sa mata tsoronsa ta yanda ba za ta taɓa iya tsallake umarninsa ba saboda ba kadan ba ya ji ya kamu da matsanancin buƙatarta kuma yana son hakan ya ɗore ko don ya gwadawa Maryam ita ba komai ba ce. *** Hankali tashe Mami ta ja Tasleem zuwa dakinta ta rufe. Dubanta take yi a tsanake. Jikinta banda ƙamshin turarukan da Babandi ke amfani da su babu abin da ke tashi. Ta kara shinshinarta sosai, Tasleem ji ta yi kamar ta saki fitsari a wando. "Me ya yi maki?" Ta tambaya cikin tsananin ruɗani.  Girgiza kai Tasleem ta yi. Ta tuna gargaɗin Babandi cewa muddin ta sake bakinta ya furta abin da ya faru ga kowa wane ne toh ta sa a ranta aikin ya lalace har abada kuma ba za ta samu koda rabin mutum  irin Fadeel ba balle a kai ga shi da kansa. Wannan ya sanya ta samarwa kanta nutsuwar dole ta fisge hannun Mami daga jikinta. "Mami mene haka wai? Me kike tunanin ya yimin? Babu fa abinda ya yimin, kawai dai ya ban wasu turaruka na shafa ya ce na zauna ya dinga yimin wasu karatuka bayan ya kammala kuma ya ce naje na jira zan soma ganin sakamako. Gobe ma yace na koma zai ban wani garin magani da zan barbaɗa a makwancin Humaira." Ajiyar zuciya mai karfi Mami ta yi har da kama jikin madubi. Sai bayan tafiyar Tasleem ta dinga tunanin anya ba ta aikata kuskure da ta tura ta wajensa ba musamman da ta tuno yanda suka kwashe. Ta kira wayar Tasleem din ya fi a ƙirga amma ba ta ko ɗaga ba hakanan na Babandi ma sai a ce mata a kashe. Tana niyyar zuwa da zummar kai mata yarinyarta dake faman kuka sai ga Tasleem din ta shigo gidan. "Shikenan, ki wuce ki je kin bar yarinya tana ta kuka." Itama ajiyar zuciyar ta sauke ganin Mamin ta yarda da zantukanta na bogi. Har ta kai ƙofa Mamin ta dakatar da ita hakan yasa ta waigo. "Ki kula sosai da duk wani abu da Babandi zai sanya ki yi, idan har kanki ya ƙulle a kai ki sanar da ni kafin ki aikata." Gyadamata kai kawai ta yi kafin ta juya ta nufi dakin Anna don gaba daya ma ta tattara kayanta daga ainahin dakinsu, ba za ta juri ganin wannan rawar ƙafar da ake yi akan auren Humaira da Fadeel ba. *** Ɓangaren Humaira ba ta da ko ɗigon damuwa game da komai. Idan ka ga yanda ta yi kyau za ka rantse ba ta taɓa sanin wata aba wai wahalar rayuwa ba. Ummita ita kanta ta bar damuwa da yanayin kaddararta, gaba daya ma babu mai yi mata tuni a kai, yanda ƴan uwan Humaira ke haba-haba da ita da nunawa Ahmad kauna sai ta ƙara sakewa da su. A yanzu babu abin da ke damunta dangane da abin da ya faru da ita na baya sai ko yanzun da Ridwan ke neman takurawa rayuwarta da kira da ƙara fallasa mata zahirin zuciyarsa. Ga kuma Mubarak a gefe wanda ya ce babu gudu ba ja da baya don ya samu labarin Ridwan daga bakin ƴan uwansa. Ita kam gaba dayansu babu wanda ta ke jin ma kaunarsa a ranta sai tausayi da suke ba ta ganin su matasa su na neman daukarwa kansu abin da bai dace da rayukansu ba. A cewarta. Safiyar ranar Juma'a su na zaune a daki, Humaira sai yatsine fuska take tana kallon kwanon da Baba Amina ta dire a gabanta na kazar da aka dafa da sinadaran gyaran mata. "Ki kalla dakyau Humaira, hakanan za ki ci shi ko bakya so." Fadin Baba Amina kenan, yanmatan dake dakin aka kwashe da dariya har Ummita da Raihana wacce ta saki ranta saboda murna da farin cikin ganin auren Fadeel da Humaira na niyyar tabbatuwa, abin da ta jima tana son gani. "Nikam Baba idan ta ƙi ci a miƙomin yanzun nan na tashi da shi." Cewar Raihana tana ƴar dariya. "Aa Raihana, wannan kam na matan aure ne. Ki jira zai zo kanki ke da Ummita nan ba da jimawa ba kuwa sai mu gani ko cika baki ne ko kuwa dagasken za ki iya ci." Aka yi dariya, Ummita ko murmusawa ta yi, ita ba ta fiye son ana sanya ta a layin waɗanda za'a aurar ba. "Allah kuwa Baba cikina ya cika, dazunnan fa na gama shan wani..." "Toh marar sirri, a gaban ƴan uwan naki za ki tona abinda aka baki?" Hajjo ta katse zancen Humaira, anan kuma sai Baba Amina duk ta sa aka fice a dakin aka bar Humairar sai ko Ummita da Hajjo. "Kinga Humaira, wadannan abubuwan da nake sanyaki sha da ci, suna daga cikin abin da za su ƙara siyamaki daraja a wurin mijinki. Ba ki da wanda ya wuce mu da zamu tsaya don ganin rayuwar aurenki ta inganta da taimakon Allah. Abu kuma na gaba da nake son faɗamaki, bai wuce akan Maminki ba. Kar ki ga don ta sauko kamar ta sauya fuska ta shiga cikin sha'anin bikinnan na jiya ki yi zaton babu sauran ɓurɓushin hassada da bakin ciki a ƙasan ranta. Ta riga ta fiddomaki da kuma mu da zahirin wace ce ita wannan kadai ya isa ki kula koda bayan aurenki ki yi kokari kada ki bada wata ƙofar da za'a ji kanki keda mijinki. Ki godewa Allah, samun miji irin Fadeel a zamanin nan sai a tona. Mutumin da tun kina gwada masa tsana da kyara yake bibiyarki da nuna maki kauna ta gaskiya, wallahi Humaira koda wasa kika cutar da shi a zamantakewarku sai Allah ya yi masa sakayya. Kar ki yi amfani da wannan dumbin kaunar da yake gwadamaki wanda hatta a dangin Mahaifinki akwai wadanda suke nuna adawarsu da shi ki yi tunanin cutar da rayuwarsa. Ki yiwa kanki karatun ta nutsu, ki yi hakurin zama da mijinki kar ki yaɗa matsalar da za ki fuskanta da shi ga kowa ba ma fatan matsalar ake maki ba, amma ki kula ki san me kike yi." Haka Baba Amina ta yi ta yi mata maganganu masu ratsa zuciya har sai da jikinta ya yi sanyi. A karshe ta soma cin kazar su na zolayarta. Hajjo ta mike ta fice zuwa wurin yan uwansu da suke ɗakin baƙi. Itama Baba Amina ta fita wannan ya ba Raihana damar dawowa ta zauna gefen Humaira tana yamutsa fuska. "Wai kun ji labarin an yiwa Sis Futuha kishiya kuwa?" Dagaske ba su da wannan labarin, Humaira dai ta ganta tana kuka ranar da Fadeel ya zo amma ba ta samu damar cewa uffan ba saboda umarnin da Mami ta ba ta a lokacin. "Kai Raihana, dagaske kike?" Fadin Ummita. Taɓe baki ta yi. "Allah ko dagaske, Ƴar Snow mijinta ya aura." "Ƴar Snow fa kike ce?!" Fadin Ummita idanunta waje. Humaira ko sai da ta ɗan yi jim don ta na tunani kamar ta san sunan kamar kuma ba ta sani ba. Can ta tuna wace ce, wacce dai ta yiwa Futuhar mummunan ƙazafin da ya yi sanadin aurenta da Yakubu ba Ibb da take mutuwar so ba. "Ita dai, yau ma za ta tare kuma a gidan da Futuha ta fito. An mata gyara sosai. Hum, ta tashi hankalinta ita kuma, dazu har rotse ta yi mishi a goshi dakyar ya kwaci kansa ya bar gidanta. Abba ma ya je ya yi mata kaca-kaca da barazanar saɓa mata muddin ta ƙara gangancin kashe rai. Ba don Abban da abokin Yakubun ba ai da tuni itama ta dawo gida zawarci." Raihana ta karashe zuciyarta a karye har kwalla sai da ta cika idanunta. Rashin sa'ar ƴan uwa mata da ma rashin sa'ar uwa ta gari yana mata zafi a ranta. Me suka ɗauki duniya ne haka? Kowanne cikinsu dogon buri ya ke ci mata kai ka ce shi ke da alhakin ƙayyadewa kansa lokacin da zai mutu. Futuha a zahiri ta nuna kwadayin abin hannun Yakubu, yau gashinan ya nuna mata halin maza ire-irensa. Tasleem ko ba ta ma san a layin da za ta jera ta ba. "Allah ya kyauta. Ya tsare. Amma ta bani tausayi gaskiya. Ai ko ni duk hakurin ba na jin zan iya zama da wacce ta yimin ƙazafi ba a rayuwa." Fadin Ummita kenan da ya katse tunanin Raihana. "Amma a ganinki tun farko laifin waye? Laifinta ne da ta zaɓi duniyar Tiktok akan zahirinta, Allah dai ya tsare." Suka amsa da amin. *** Misalin karfe biyar na yamma aka shirya Humaira cikin wani arnen leshi mai daukar idanu kalar yellow ochre, ta yi wani irin kyau da ta fito tamkar a matar wani hamshaƙin. Ummita kanta ta ci ado sosai cikin wani leshi golden da suka yi ankonsa da Raihana. Su biyu kacal suka yi shi, Ahmad kuwa Hajjo ta karɓe ta ce wajenta zai zauna ita ce mai rainonsa. Duk kuwa ta yi hakan ne don kar ya hana Ummita sakewa a wurin biki, tana fatan itama Allah ya fiddo mata da miji ta yi aure. Gidan gaba daya aka fice har Mami wacce Hajiya Lubna ta yi ta yiwa famfon kar ta bari a kwace mata ragamar gida. Wato ta zuba idanu Baba Amina ta yi mulki a gidan mijinta alhalin ita ya dace komai ya ɓulla ta hannunta. Anti Laila kuwa ƙanwa ga Hajiya Lubna, wato matar da ta koyawa Humaira girke-girke. Takanas ta zo har da ƙatuwar ledarta na taya murnar aure da ta tahowa da Humairar. Ita kam da zuciya ɗaya ta ke sonta. Ta kuma iso da ƙaramin akwati mai dauke da agogo mai dankaren kyau daga Kabir dan Hajiya Lubna ya ce a ba Humaira. Humaira duka ta amsa ta damƙawa Raihana. Ita ko ta je ga Baba Amina dake zaune ta nunamata. Mami na kallon wannan diramar, haushin Raihana tamkar ya kashe ta, wato ba ta ma dauketa komai ba don tun zuwansu wurin yinin komai aka bada na Humairar wajen Baba Amina take kai shi. Ko inda Mamin take ba ta kalla, Mamin dai ta haɗe itama cikin wata shaddarta sabuwa da ta sa aka yi aikinta daga can Mali amma ba ta taɓa sanya ta ba sai a yau ta yi mata rana. "Hajiya Maryam wallahi sai mun tashi tsaye, nikam ina tsoron kar wannan abu ya tabbata. Kiga yarinya duk ta fi yaranki more aure? Duba kiga yan uwan mijinta babu na raini a cikinsu. Suturarsu masu tsada ne na ƙarshe ina faɗamaki." Hajiya Lubna ke wannan bayanin tana karewa su Anti Amarya da su Hannatu ƙanwar Fadeel kallo. Mami ta cika ta yi fam, ta ji kwallar baƙin ciki sun cika idanunta. "Bar ni haka Hajiya Lubna, wallahi kuka nake son fashewa da shi. Wannan ranar baƙa ce a gareni kuma ba don kin matsa akan zuwan ba da babu inda zan tako don ban ga wani abu cikinsa bayan baƙin ciki ba. Yarana su na can cike da tashin hankali, amma wadannan hotihon banzan ba su kishin yan uwansu sam, ji yanda ita waccan ke zirga-zirga ke kya ce bikin kanin ubanta ake yi, ji don Allah yanda wancan soloɓiyon ya wage baki yana zubawa Humaira kudi." Ta karashe tana duban Yassar da ya ke tiƙar rawa yana yi wa Humaira karin kudi da take tsaye a fili. "Sai hakuri, farin cikinnan zamu san yanda zamu yi daga baya ya koma baƙin ciki." Kallo bai tashi komawa sama ba, sai da aka yi kiran uwar Amarya ta fito, Mami da Baba Amina suka fita a lokaci guda. Wannan abu ya yiwa Mamin ciwo amma hakanan ta danne ta dinga zuba murmushin da bai je zuci ba. Humaira kuwa har hawaye ne suka zubomata, babu wanda ya fado a ranta sai Dada da mahaifiyarta. Baba Amina ta dan ja ta a jiki ta a goge mata fuskar da handkerchief sai hoto da liƙin ya koma kansu wannan ne dalilin barin Mami hall din gaba daya don hatta da MC din idan ya ambaci sunanta sai ya ambaci na Baba Amina. Raihana ta fito don kai wa wasu ƙawayensu na makaranta kati dake waje, ta ji wayar Ummita dake jakarta na ƙara. Kafin ta ciro ya zama missedcall, ta ga ba ma kira daya ba ne, kira ne wurin goma sha wani abu daga Mubarak, Ridwan da kuma wata lambar da ta dauki hankalinta matuƙa kuma ta girgizata. Tana nan tsaye bayan ta ba da katin sun shige ta rasa abin yi sai kakkarwar hannu da jiki, wayar ta ƙara ringing. Lambar ce dai dagaske, lambar da ta gani a wayar Mamin har ta tura wa Abba. Ta yi saurin ɗagawa kirjinta na harbawa. Kafin ta yi magana ya riga ta. "Blackbeauty, ina fatan kin dauki muryata? I am the Wizzy the father of Ahmad." Ai ba ta san lokacin da ta durƙushe a cikin fararen duwatsun dake wurin ba, Wizzy da ya yiwa Ummita fyaɗe? Shi ne Wizzy da Mami ke waya da shi? Ta kara fiddo wayar a kunne ta duba dakyau, tabbas lambar ce ba ƙarya ba ne. Ta katse kiran ta ciro wayarta tuni hawaye sun gama wanke fuskarta ga wayar har tana faɗuwa a kan duwatsun ta buɗe ta fiddo lambar Wizzy dake wayarta, ta ƙura idanu tabbas ita ce dai lambar. Mami wacce ke tsaye tare da Hajiya Lubna su na jiran direban Hajiya Lubnan da aka nema aka rasa ya kaɗa yawo, ta hango Raihana cikin halin ruɗani. Ta dubi Hajiya Lubna. "Raihana kuma? Meyafaru da ita?" Hajiya Lubna ita dinma sai lokacin ta ankara da ita, cikin sauri suka hau tafiya zuwa inda take.Kafin Raihana ta kai ga daukar kowane mataki, wayar Ummita dake hannunta ya ƙara ringing, Mami daidai lokacin suka karaso ita kuma ta ɗaga wayar tana fadin. "Waye Wizzy? Mene dalilinka na kiran Ummita?" Kirjin Mami ya bada dam, suka dubi juna da Hajiya Lubna cikin tsananin kiɗima. Wizzy kuma? Kiran Ummita? Ai sai kafafun Mami suka hau rawa, dakyar ta karasa ta zagaya gaban Raihana, ita kuwa Raihana ganin Mami ya sanya ta ƙara nanata tambayar da ta yiwa Wizzy don ta ga yanayin da za ta shiga. Ai kuwa zaro idanu ta yi waje, hannu ta kai ta fisgi wayar. "Bani mu ji waye?" Haka kawai ta fadi ta sa wayar a kunne ta dan yi gaba acewarta wai ƙarar sautin da aka sanya a cikin hall ya sa ba ta jin abin da yake fadi. Hajiya Lubna cike da dabara ta riƙe hannun Raihana. "Ki kwantar da hankalinki, ko waye za mu sani. Me ya ce maki ne naga duk kin shiga ruɗani har da su kuka?" Raihana ta bi matar da kallon munafuka mai ƙara tunzura uwarta. Ai dama sai hali ya zo ɗaya ake ƙawance. Ta sani sarai don kada ta bi bayan Mamin ne ya sa ta ke siyasance ta. Sai ta kauda kai ba tare da ta ce mata uffan ba. Hankalinta na kan Mamin da ta ba su baya ta kuma yi can nesa da su. Mami kuwa ta saurari kalaman dake fitowa a bakin Wizzy. "Ke wace ce? Ki ba wayar ga mai wayar uwa ga yarona ita nake son magana da ita kar ki bari na wulakanta rayuwarki kema." "Wizzy." Ya ji muryar Mamin cikin kunnuwansa, sai kuma ya kyakyace da dariya. "Oh, ki ce wayar fasin fasin ake da ita, daga hannun wannan sai na waccan, Hajjaju kenan. Kin yi mamakin jin na kira lambar Uwar yarona ko? Ki. Yi zaton zan zuba idanu na biyewa shirme da shiriritarki? Kin kasa cika umarnina ma fiddo Nusy har jami'ai sun fara farauta ta saboda ta ba da kwatancen inda nake, ta ci amanata. Yanzu haka na yi nesa da Kano da ma duk inda aka san za a gan ni na koma ainahin ƙauyenmu. Toh ki sani, a duk radda na tashi dawowa zan yi zuwan a mutu ko a rayu, ba Ahmad kadai ba har uwar Ahmad zan dauke ke kuma haɗuwarmu dama na faɗamaki ai ba za ta yi kyau ba. Ki shirya tonan asirikanki." Gumi ya shiga tsirfowa Mami, ta dan juya ta dubi  su Raihana, ta kuwa kuramata idanu babu ko kiftawa. Ta kauda kai ta ce. "Shikenan, ka yiwa Allah kar ka kara kiran wayar Ummita. Zan maka yanda kake so kafin a kammala bikin auren nan." Ta dinga magiya har sai da ya ce ya ji. Da haka suka yi sallama ta goge lambar bayan ta yi blocking dinta. Kasancewar wayar Ummita babu wani lock da ta sanya hakan ne ya ba ta damar yin yanda ta so kafin kuma ta koma ta ba Raihana wayar. Har lokacin kallonta kawai take yi hawaye na zuba a saman kuncinta. Wai wannan matar da Allah bai raga da komai na kyawun fuska ba sai ko munanan ɗabi'unta ita din mahaifiya ce gareta babu yanda kuma za ta yi ta sauyawa tuwo suna. "Innalillahi wa inna ilaihir raajiun! Raihana kin ji masifar dake shirin tunkaro mu? Wai uban Ahmad ne yake son karɓar ɗansa? Lallai ki kiyaye furta wannan zancen ga Ummita, mun samu ta dawo cikin nutsuwarta yanzu, idan wannan magana ta fito bamu san halin da za ta shiga ba kuma." Mami duk ke wannan zantukan har da fidda hawaye itama ta a share su. Hajiya Lubna  ko sai ƙara jinjinawa irin salon kisisinar Mami take. Gaba ɗaya ta rikiɗe zuwa ta Allah, wanda bai santa ba ma zai ce har zuciyarta dagaske ta ke. Raihana ta kauda kai tayi murmushi mai ciwo lokaci guda tana sa yatsunta ta share fuskarta. Allah ya taimaka ba ta yi kwalliyar hodar foundation ba, babu kuma irin nacin da Ummita ba ta yi mata akan ta yi din ba ta ce ba ta ra'ayi hakan ya ba su mamaki kwarai game da ita don ta fi su ma son kwalliyar sosai. "Shikenan, ba zan fadamata ba. Ni bari na koma ciki kar a neme ni." Daga haka ta juya ta bar su a tsaye, suka bita da ido. "Hajiya Maryam, jikina yana bani akwai wani abu da diyarki ke ɓoyewa." Cewar Hajiya Lubna. Mami ta girgiza kai tana wani murmushi. "Ko kusa Lubna, ban gan shi ba. Na san Raihana sarai, da ace akwai abu a ranta ba za ta iya yin shiru ba. Haka take, ba ta ɓoyon abin da ke ranta." Hajiya Lubna dai ta ji ta amma ba ta yi na'am ba. Daga nan suka rankaya zuwa wurin motar inda direban tuni ya dawo yana jiransu. Hakuri ya dinga bayarwa da Hajiya Lubna ke mishi fada kafin su shiga ta ba shi umarnin ya jira a waje sai ta mishi iznin shiga motar. Dole haka ya bi umarninta ya samu can gefe ya tsaya yana kallon masu shige da fice ƴan biki. Sai lokacin Mami ta labarta mata yanda suka yi da Wizzy, ta kara da fadin. "Na riga na yanke zan sa Bala (wanda ya haɗa ta da Wizzy tun farko) ya yi amfani da damarsa wayar yaron nan ta shiga hannunsa ya kai wurin masana kwamfuta a yi resetting ta dawo kamar sabuwa. Wannan damar zai sa ya rasa komai da muka yi tsakaninmu. Kinga koda asirinshi ya tonu wanda nake ji a jikina zai tonun tunda dai an kama budurwarsa an kuma fara harinsa, babu wata shaidar da zai nuna gaban kotu da za'a ce har da ni a ciki. Abin godiyar ma, bai taɓa yin ido hudu da ni ba ballantana ya ce ya san ni. Nima a bangarena zan fidda komai nasa daga wayata." Murmushi sosai Hajiya Lubna ke yi. "Tabbas wannan babbar dabara ce. Nima dai akan ta wa matsalar na auren da Honarabul ke shirin ɗaukowa na waccan shuwa arab din dole na je na ga Babandi. A baya ya yi aikin kamar za a fasa amma kinga ashe magana tana nan kuma yan banzan danginsa sun nuna goyon bayansu. Kinsan duk yanda ka kai ga kyautatawa dangin miji tsinannu sai sun ga aibunka. Koda dai bana tsinana musu hatta uwarsa bai isa ya yi mata ba sai da iznina. Watakila wannan ƙarfin da ya bani na iko a gidansa da kuma kaunar da ya nunamin ce ta yi sanadiyyar da suke nunamin hassada da bakin cikinsu." Fuska Mami ta yamutse. "Hum, ba ki ga waccan balbelar ba?" "Wa kenan?" "Wace ban da yar iskar bazawarar can Maijidda? Nifa ko zan yi yawo tsirara ba zan aminta da aurenta da mijina ba." Dariya Hajiya Lubna ta yi. "Kai kai kai Maryam, yanzu ke da bakinki kin ce Babandi bai tabbatar maki da aure tsakaninsu ba. Toh na meye za ki yi wannan irin yanke hukuncin da gaggawa haka?" Girgiza kai Mami ta yi. "Uhm uhm Hajiya Lubna. Babandi shegen kansa ne. Ni jikina yana bani zai wahala idan ba dangantaka ta auren yake nufi ba. Sai yanzu ma nake ganin wautarmu na tsayawa kan mutum daya don yi mana aiki. Yanzu gashinan abubuwa ba sa tafiya yanda muke so, ya kamata dai ki lalubo mana wani gwarzo kuma babban malamin da ya shahara da zai iya yi mana aiki." "Nima nayi wannan tunanin Hajiya Maryam, lallai mu tsaya mu nemi wata mafitar, akwai masu taimakon jibgi guda suna nan. Shi kuma Bala ki yi maza ki kirashi yanzu, ai da zafi akan bugi karfe, gwara ki ba shi wannan aikin da alkawarin manyan kudade idan ya aiwatar kada lokaci ya kure." Bisa wannan shawarar Mami ta fiddo waya ta kira Bala, ta ci sa'a ba ta sha wuyar samunsa ba. Suka yi magana ya kuma ji daɗin kudaden da aka yi mishi alƙawari ya ce zai yi yanda ta ce. Da haka suka yi sallama. Sai da suka gama ƙulla-ƙullarsu kafin Hajiya Lubna ta kira direbanta ya zo ya ja suka bar farfajiyar wajen taron. *** Tasleem kuwa tun da aka sa ƙafa aka tafi wajen biki, ta zari mayafinta jikinta har rawa yake ta wuce gidan Babandi. Ta rasa meke janta zuwa gareshi. Kiranta kawai ya yi ya sanar da ita ta zo yana jiranta ta ji nan duniya idan ba ta je ba akwai matsala, ko makaranta ta kasa mayar da hankali kan jarrabawar karshe da take yi. Haka Babandi ya more ta sannan ya ba ta wani ƙullin magani akan ta yi yanda za ta yi ta sanya a abin ci ko shan Humaira, sai ko wani turare da za ta shafe a kayan da ta tabbatar shi Humairar za ta sanya ranar daurin aure. Da wannan murnar ta dawo gidan. Koda Mami ta tambayeta daliin jimawarta, cewa ta yi layi ta tarar. *** Washegari ya kama ranar ɗaurin aure da kuma yinin cikin gida sai ko kai Amarya duka. Tun safe jikin Humaira a sanyaye yake, kewar yan uwanta da tunanin sabuwar rayuwar da za ta shiga na aure sun tsaya a ƙoƙon ranta. Tana gani ana ta shige da fice ana shiri, masu wanka nayi masu karyawa suna yi, ita ko ta kasa sa komai a bakinta balle ta samu ta ji faɗan Hajjo ta miƙe ta shiga wanka. Da ta kalli Ummita sai ta ji hawaye na ƙara zuba kamar famfo a fuskarta. Ummitan ma daurewa kawai ta ke yi, ita ko Raihana ma gaba daya ta dunkuke cikin bargo tana kuka. So take ta je ga Abba ta fayyace masa komai amma kuma ba ta son raba masa hankali gida biyu. Ta san yana ta hada-hadar fita zuwa daurin aure. Wannan dalili ne ya sanya ta bar komai a cikinta. Ɓangaren Anna kuwa, murna har da su rawa saboda kudaden da aka turo mata ya yi daidai da wadanda aka suka rage ta cika wajen fiddo autarta. Ta yiwa Mami magana, suka dunguma har Futuha da ta shigo gidan da safe  zuwa inda Jannat din take. Tasleem ko ba ta bi su ba sai tunanin ta inda za ta shiga dakin ta shafa turare a kayan Humaira alhalin babu ko tsinkenta a dakin. Ga mutane an cika a ciki, gaba daya kanta ya ƙulle. Ta fito falon goye da ɗiyarta a baya wacce ko wanka ba ta yi mata ba ga famfas ya cika sai tashin zarni take yi. Ƙazanta na ɗaya daga cikin halayyarta. Ƙazamar gaske ce har ma fiye da Futuha kai ka ce ba Nos ba. "Ladidi don Allah yi da jiki ki miƙawa Amarya wannan shayin yarinyar ta ƙi cin komai, ni bari naje na ga ko masu kai kayan can gidanta sun tafi." Baba Amina ke maganar ba ta ko lura da Tasleem ba, ta fice da sauri Ladidi na amsa mata da toh. Wani irin sauke ajiyar zuciya ta yi tana jin wani sanyi a ranta. Ta yi sauri ta fada kicin din. Suka gaisa da Ladidi. Ta dubi tire din mai dauke da filas da kuma kofi sai kayan shayi da plate wanda aka soya kwai aka rufe. "Ladidi don Allah dubamin akwai ragowar fulawa." Ta amsa da toh sannan ta shige store din dake jingine da kicin din tana fadin ba za a rasa ba bari ta duba. Tasleem a gaggauce ta fiddo ƙullin maganinta cikin zanin goyon, ta kunce ta bude kwan ta barbaɗa kadan a sama, ta rufe ta kara bude murfin filas din shayin ta zuba ciki kadan ta rufe ta jijjiga ta ajiye, ganin Ladidi na shirin fitowa ta yi saurin tura maganin cikin zani ta saita tsayuwarta. Ladidi ta fito rike da karamin buhun fulawa ta ce. "An ci sa'a kin samu ba yawa, haka mutumin naki kike son ci?" Tana nufin danwake. Tasleem ta dan yi dariya ranta fari sol ganin a saukake ta aiwatar da guda daya saura ɗaya. "Kamar kin sani, don Allah taimaka ki yimin idan kin miƙa saƙon Humairar." "Ya akai kika san an Humaira ne?" Tambayar da Ladidi ta jefomata kenan, ta dan ji faduwar gaba kadan, ashe fa ba ta riga da ta shigo kicin din ba sai kuma ta basar. "Ah, na ji Baba Amina na baki saƙo tana fita." Sai a sannan Ladidi ta saki fuska. "Auho, toh bari na kai sai na zo na ɗoramaki." Daga haka ta dauka ta fice zuwa dakin su Humaira. Ajiyar zuciya mai karfi Tasleem ta saki, murmushin jin dadi ta yi har da ɗan buga tsalle. Lallai idan Humaira ta ci a yanda Babandi ya ce za ta ji nan duniya ba ta son auren Fadeel. Shi kuwa turaren da za ta fesa a kayan da Humairar za ta sa, zai yi sanadin da za ta haukace ta bi duniya. Da wannan farin cikin ta fice a kicin din. Sai dai me? Bayan awa guda ta shiga dakin don ta ga irin sauyuwar fuskar da Humaira za ta yi da borin ba ta son auren Fadeel, amma ta tarar ma waya take yi da Fadeel din tana doka murmushi yanmatan dakin na tsokanarta. Wani zafi da jiri ta ji a kirjinta da kuma jikinta. Jiri har yana so ya kayar da ita. Tana da tabbacin Humaira ce ta ci ta sha shayi da kwai, don har  shigowa ta yi da zummar neman wani mayafinta a sif din Raihana ta tarar Humairar ta a yagar kwai tana loma a baki amma ya akai bai yi tasiri a jikinta ba? "Ke Tasleem lafiyarki kuwa?" Ta dubi mai tambayar, Sauda ce diyar Baba Amina dake aure a Zaria. "Babu komai, kaina ke ciwo tun safe da shi na kwana." "Ayya, ai sai ki nemi magani. Sannu." Ta amsa da yauwa tana murmushin yake da kallon Humaira. Ta sa kai ta fice za ta nufi dakin Anna. Sai ta hangi kaya a hannun Raihana za ta shiga falon Abba da su wanda ba ya nan ya fice zuwa wajen daurin aure. "Kayan waye wannan?" Tasleem ta tambaya da dan sauri. Raihana ba ta ko kalleta ba don haushinsu take ji su duka ta amsa. "Na Mrs Fadeel in sha Allah." Wannan Mrs Fadeel din ya baƙanta ranta sosai, ta ja tsaki, Raihana ta fice tana waƙar.  "Ko anƙi ko an so, aure zai ɗauru.." Ta sani da ita take, ba ma haka waƙar take ba amma don ta ƙo a ranta ya sanya ta juya shi, wallahi ban da da wayonta aka haifi Raihana za ta rantse ba jininsu ba ce yanda ta fifita Humaira sama da su. Wata ƙwafa ta yi, tana gani Raihana ta shige bangaren Abba ta ajiye kayan ta fito bayan ta jawo kofar, key kawai ta murɗa amma ba ta zare shi ba ta wuce dakinsu da zummar taso Humaira da ta yi wanka ta je ta shirya a can saboda mutane sun yawaita a dakinnasu. Cikin sa'a kuwa ta yi sauri ta afka ciki ta daga kayan ta fiddo kwalbar turaren ta fesa a jikinsu sosai ta mayar yanda ta gansu ta ajiye. Ta bude kofar ta fita ta rufe ta fada sashin Anna tana dariya. "Ai idan kinsan wata ba ki san wata ba. Babandi ya cemin sai kin haukace kin bi duniya, wannan ranar nake jira. Maza jeki Mrs Fadeel ki sanya kayanki. Uniform dinki na asibitin dawanau." Tana kaiwa nan ta feshe da dariya. Sai a lokacin ne ta samu nutsuwar shiga wanka, yarinyarta can ta jefa ta wajen Ladidi don a yi mata wanka. Zuciyarta fari ƙal za ta zama matar Fadeel. *** Gama wayarsa da Humaira ya shiga wanka, bayan ya fito ya kammala shirinsa tsaf cikin shadda ruwan goro da ta sha aiki, kyau iyaka kyau ya yi. Dogo mijin doguwa, ga cikar zati ga kyau da haiba. Fadeel kenan. Ya fito falonsa inda Ibb da su Idris abokansu ke jiransa. Nan suka sanya mishi ihu da zuzuta haduwar da ya yi a yau. "Ka ga angon Humaira." Ya yi wani murmushinsa haɗadɗe. "Ku tashi muje dama shi muke jira, yana so amma yana ɓatawa mutane lokaci." Ibb ya fadi yana harararsa don tun dazu suke zaman jiransa sai da ya shiga kawai ya ganshi ya yi daiɗai a kan gado yana waya da Humaira. Fadeel ya yi dariyar da fararen hakoransa da dimple suka fito. "Sorry, muje toh." Daga nan suka fito gaba daya, ba su ko shiga bangaren Anti Amarya ba saboda cunkoson jama'a suka bari akan sai sun dawo. A kan idanunta ya shiga mota suka fice daga gidan, ta ji saukar hawaye a kuncinta. Ta saki labulen dakin Antinn nata ta juya zuwa ciki. Zama ta yi ta shiga kuka kamar ranta zai fita. Wato Fadeel ya rantse ba zai aure ta ba, Humaira ya zaɓa sama da ita? A wannan halin Rabi yayarsu ta iske ta. "Haba Murja, wai sai yaushe za ki sa wa zuciyarki dangana?" Ta dago fuskar tana dubanta, gaba daya tayi wata iriyar rama da baƙi, dama rabin farin na mayuka ne, har wani ja take yi kamar na soyayyen ƙosai. "Anti wallahi ina son Fadeel." Rabi ta zauna a gefenta. "Amma shi kuma ba ya sonki. Wannan bai isa sanya ki hakuri da shi ki rungumi mai sonki ba? Anas ƙanin mijina sai binki yake kina wulaƙantashi." "Anti shaye-shaye yake fa." "Sai me? Kar ki manta ya fi mijina kudi sosai. Kedai ba burinki ki yi auren kudi ki hutawa ranki ba? Mu din ma ai fatan da muke yi maki kenan. Ki rungumi kaddara ki aminta kawai a daura maku aure. Kina haifar namiji shikenan mu burinmu zai cika kin zama matar gida. Wallahi a yanda halittar fatarki ta kara munana Fadeel ba zai taɓa kallonki ya ji sonki na aure ba balle sha'awa. Ki yi hakuri ki lallaba rayuwarki da auren Anas kar ki yi saki na dafe. Watakila ma sai kiga sanadin soyayyar da yake yi maki Allah ya shirya shi. Sai kiga ya sauya daga yanda kika san shi. Mu dai ki zama Matar Gida, ki haifar masa ɗa namiji dukiyarsa ta zama ikonki." Rabi ta dinga yi mata famfo, har a karshe ta ji ta saduda ta amince da hakan. Da wannan murnar da farin ciki ta kira Anas ta yi mishi albishir cewa ai Murja ta aminta da batun aurensa. Shima ya yi farin ciki sosai ya kuma ce a ba shi Murjar ya ji ta bakinta. Nan ta sanar da shi eh hakane ta yi na'am har feeto ya yi mata a kunne ta cikin wayar tsabar farin ciki. Ita dai ta yamutsa fuska. Ai gwara ma ta yi kudin ta nunawa Fadeel ba shi kadai ke da arziki ba. *** Ta shirya tsaf cikin leshin da Raihana ta tanadar mata. Raihana na kokarin miƙa mata sarƙa ta ga Humaira ta yi wani dumm, lokaci guda kuma idanunta suka kaɗa. Ta rike kanta ta shiga tari. "Lafiya Humaira?" Ta tambaya hankali tashe.Ta yamutse fuska gami da neman wuri ta zauna dalilin jiri da take ji yana kwasarta. "Raiha wannan wane irin turare ne? Warinsa babu dadi, kinga jiri nake ji ga amai na yunkurin tahomin." Da sauri Raihana ta mike. "Ya Salam, naji, ai nayi zaton ko Baba Amina ko Hajjo ce suka fesa, ban ma ankara da ƙamshin ba sai yanzu. Cire kayan kar ya ja maki wata matsalar." Ba shiri Humaira ta cire da taimakon Raihanar, ta karasa ta ware mata fankar falon ta bude labule don ta samu iska sosai, kayan kuwa ta kwasa ta fice tana ce mata ta jira tana zuwa. Humaira ko hijabi ta zura saman zanin da ta ɗora a kirjinta ta kwanta a can wata kujerar don turaren wani karfi ne da shi da ya mamaye kujerar da ta bari. A hankali kuma ta shiga ambatar sunayen Ubangiji har hakan ya haifar mata da nutsuwar zuci da na jiki. Tana a kwancen tana salati har Raihana suka shigo tare da Baba Amina da Hajjo sai ko Anti Maijidda wacce tun shigowarta a safiyar yau gidan ta faɗa cikinsu ake ta hada-hadar girki da ma dukkan ayyuka da ita kasancewar dama can za'a ce ƙawa ce ga Baba Amina duk kuwa da ta bata shekara guda hakan bai hana ƙawance wanzuwa ba. Rashin yar uwarta Jamila ne ya sanya ƙawancen ja baya sai ko idan abu ya tashi suke haɗuwa, sai kuma waya. Humaira ta tashi zaune. Kayan ne sai a hannun Raihana sai dai yanzu ƙamshin turaruka masu daɗi suke yi na wuta da aka dora kayan saman kabbasa aka turara su. "Ke Humaira, tashi ki sa kaya. Wane irin turare haka naji na kayan dazu? Ina yake?" Cikin daurewar kai take duban Baba Amina sai ko ta girgiza kan. "Wallahi Baba nima kawai dai na ji yana ƙamshin, na ma yi zaton ko ku ne ku ka fesa." "Aa ko kaɗan, Raihana ma ba ta fesa maki komai ba, ina ce har da kwalin turaren ta shigo da shi a jaka. Ai ba a kai ga fesawar ba." Nan dai aka hau jimamin wannan abu, Raihana kuwa iyaka tunaninta ya tafi ga Tasleem sai dai ba ta da kwakkwarar hujjar da za ta ce ko ita ce. Nan da nan ta shiga istigfari. "Yanzu dai duk a ture wannan tunda dai ya wuce. Ta yi sauri ta shirya ta fito mutane sun soma cika gidan." Cewar Anti Maijidda. Daga haka suka fice aka bar Raihana kawai sai Humairar, Raihana ita har Humaira ta kammala jikinta a mugun sanyaye yake. Can kuma sai ga mai kwalliya ta iso, Ummita ta rako ta har bangaren Abban, aka shiga yi. Ganin haka ita kuma ta fice zuwa sashin Anna wajen Tasleem. Ta iske ta zaune tana tsantsara kwalliya a fuskarta, rabon da ta ce ta ga Tasleem cikin irin wannan kwalliyar tun lokutan amarcinta. Ta tsaya tana kallonta lokaci guda kuma tana ɗan waige-waige cikin ɗakin wai ko za ta ci karo da turaren. Tasleem na ganinta ta miƙe tsaye cikin sauri. "Lafiya na ga fuskarki wani iri?" Tambayar kawai da ta jefawa Raihanar kenan, Raihana ta yi murmushi gami da ɗaga kafaɗarta. "Lafiya ƙalau ma kuwa, watakila kewar rabuwa da yar uwata ne ya soma dukana." "Humaira?! Me ya faru da ita?" Ta tambaya idanu waje cikin zaƙuwar son jin amsar da zai fito a bakinta. Ita kuwa idanu ta ƙuramata cike da zargi ta ce. "Babu abin da ya faru da ita sai alheri, yanzu haka ma kwalliya ake yi mata. Kin yi zaton wani abun ne?" Ai Tasleem ba ta san lokacin da ta yi wurgi da eyeliner din dake hannunta ba. Idanunta suka cicciko da hawaye. Ta hau girgiza kai murya na rawa ta ce. "Ƙarya kike yi! Wallahi ƙarya kike! Ta sanya kayanta ne? Bari naje, nasan kin sauyamata wasu munafuka kawai!" Tana kaiwa nan ta kama hanya za ta fita, Raihana cikin zafin nama ta tura ta baya har tana buguwa da gado sannan da sauri ta karasa ta rufe ƙofar da mukulli. Ba ta sa lokacin da ta soma zubar hawaye ba, lallai zatonta ya kasance gaskiya, dama ta san a rina! Da walakin goro a miya, shigarta falon Abban babu wanda ya gan ta sai Tasleem, ta ajiye kaya iyakar tunaninta ta tuna hancinta bai shaƙar mata wani ƙamshi ko wari na turare a sadda ta ajiye ba, sai daga bayan nan ta tuna tabbas mukullin a jiki ta bar shi bisa mantuwa ta fice kiran Humaira. Sai kuma yanzun ta gama tabbatarwa dagaske ba kokwanto zuciyarta ke yi ba, ɗazun a farko babu wani wari ko ƙamshin turaren da ta ji. Yanayin Tasleem ya fayyace mata komai. "Kina zaton wani abu zai faru da Humaira ne idan ta sanya kayan da aka tanadar mata? Ko kuwa don kin fesa wani ƙaramin kayan asirinki kin yi tunanin za ta mutu ne ko kuma ta samu wata illar? Toh babu ɗaya Tasleem, babu daya da zai faru. Ko kin mance ita ɗin Allah ta sanya a gaba? Wajenshi ta ke kai dukkan kokenta? Kin mance tana tare da Mai Kariya daga dukkan sharri? Wallahi kin shayar da ni mamaki! Ban taba zaton son zuciyarki ta kai har haka ba da za ki iya gwada shirka don samun abin duniya! Waye Fadeel da har za ki kauce hanya ki rushe dukkan kyawawan ɗabi'unki saboda shi? Anya kina da hankali?" Tasleem da ke kuka sosai, kukan baƙin ciki da takaicin yaudarar da Babandi ya yi mata ta juyo a fusace tana kallon Raihana cike da tsantsar tsana. "Ke ce dabba jaka marar hankali da ba ki iya taya ƴan uwanki kishi da son abin da suke so ba! Banza mai kwakwalwar kifi! Eh! Na so ace na illatar da rayuwar Humaira kuma koda ace aikina bai ci ba ai idan ta sa wata ba ta san wata ba! Raihana ki rubuta ki ajiye sai na illata rayuwar Humaira!" Raihana a wannan gaɓar kalaman bakinta ma dakyar suke fita. "Ke wace iri ce Tasleem? Ki ji tsoron Allah. Ba a yiwa Allah haka, har abada ba za ki ga daidai ba. Humaira ta fi karfinki da tsafinki har abada ba za ki yi nasara a kanta ba. Muna nan dake kina ji kina gani abubuwan alheri za su dinga faruwa gareta sai dai ko baƙin ciki ya kashe ki." Wani wawan mari ta kai wa Raihana tana kuka itama Raihanar na kuka, ba don zafin marin ba sai don bakin cikin wannan masifu da take ta gani su na yawo a rayuwar ƴan uwanta da ma mahaifiyarta wadanda son zuciyarsu ce kawai ta ke neman kai su ga kogon halaka. "Banza yar iska da ba ta san ciwon nata ba! Daga ke har Humaira daidai nake da ku!" Ta na kaiwa nan ta ja mayafinta ta bude dakin ta fice. Fitarta kuwa ta yi mugun gamo, don wata tsohuwar gwaggonsu ce ta ɓangaren Abba ta ji tana rangaɗa guɗa tana hamdala wai an ɗaura auren Humaira da Fadeel. Ai ba ta san sadda ta saki wani ihu mai ƙarfi ba da sai da mutanen falon hankulansu ya yi kanta sai ganinta aka yi ta zube ƙasa a sume. Nan fa aka shiga yarfa mata ruwa, ya yi daidai da faɗowar Mami gidan. Zuciyarta abubuwa uku ne ke dagule ciki, ga farincikin kuɓutar Jannat wacce suka sauka a can gidan Futuha don ta kimtsa kuma kada ta zo ta tarar da jama'a a yi mata caa, gefe fa Bala da ya kira ya tabbatar mata an samu an goge komai na wayar Wizzy an maido ta tamkar sabuwa fil kuma an mayar masa an ajiye kamar yanda itama a nata ɓangaren ta goge dukkan wani abu da ya shafi Wizzy har lambarsa babu ɗaya da ta bari ga kuma baƙin cikin albishir da Yassar ya kira ya yi mata cewar an ɗaura auren Humaira da Fadeel har sai da ta ɗura masa ashariya ta wayar. Shigowarta ta hangi Tasleem a sheme a ƙasa ana yayyafa mata ruwa a fuska. Ta karasa kirjinta na dukan tara-tara. "Lafiya? Meke faruwa ne haka?!" Ta tambaya a hargitse tana tura jama'a tana nufar inda Tasleem din take. "Ina zamu sani? Fitowa ta yi kawai a firgice sai ta saki ƙara ta zube." Cewar wata ƴar dattijuwa cikin dangin mijin Baba Amina. Tsaf Mami ta fahimci dalilin, kafin a yi abin kunya ta yi saurin cewa. "Watakila mutanenta ne suka tashi, ɗan kama min ita zuwa ɗaki don Allah." Ta fadi tana duban dattijuwar, wasu dai suka hau ƴar dariya da kananun magana, a gefe kuma wata ta shiga rangaɗa guɗa tana cigaba da fadin wai ina Amaryar take ta fito. Har tana rerawa Humaira kirari. Mami ta bita da harara kamar ta shaƙo wuyanta, ta dai danne suka yi dakinta da Tasleem. Tasleem hatta da ajiyeta da aka yi tana ji ba ta son ma ta bude idanu ne gudun kar ta faɗi abinda za a ji kunya. Ba ta ma san ya aka yi baƙin cikin ya haifar mata da faɗuwar ba. Sai da ta ji ta kuma fahimci Mamin ce kaɗai a kanta sannan ta bude idanun, Mami ta bar jijjigatan da take faman yi gami da sauke ajiyar zuciya. "Wane irin abin kunya kike son janyo min? Yanzun ma ya aka ƙare ballantana kin nuna baƙin cikinki a fili? So kike a tafi da mu a baka ana zaginmu?" Jin haka ai sai ta ƙara sakin wani sabon kukan. "Mami zan mutu wallahi. Fadeel shikenan ya auri Humaira. Babandi ya..." Sai ta ji kamar an sa gam an ɗinki leɓɓanta, ta kasa ƙarasa abin da ta yi niyyar sanar da Mamin game da Babandi. "Babandin me ya yi?" Mamin ta tambaya kirjinta har wani lugude yake yi, ta tattara dukkan hankali da tunaninta ga diyarta don neman ƙarin bayani. Sai Tasleem ta kasa cewa uffan sai kukanta da ya karaɗe ɗakin. Mami ta ƙara jijjiga ta. "Tambayarki nake!" "Ba komai Mami. Aikin da ya bani ne bai ci Humairar ba." Sai ta sauke ajiyar zuciya tana mai jan tsaki. "Har kin tsoratar da ni. Toh ai dama ni na riga da na dawo daga rakiyarsa. Ganin kin damu ne ya sanya na bari mu ƙara gwada shi mu gani ko za'a dace. Amma yanzu ai bakin alƙalami ya riga da ya bushe. Sai ki cire komai a ranki ki mayar kan jarrabawarki kinga dai zangon ƙarshe ki ke. Wannan fadi tashin da nayi maku don ku samu karatu idan ita waccan (Futuha) ta watsar saboda romon baka na banza na ɗa namiji ke dai tunda kina ƙarshe gwara ki mayar da hankalinki. Sannan don Allah kada a gane kina cikin halin bakin ciki, nima kinga dai daurewa zan yi na dan shirya na fita a yi da ni. Kema hakan nake so, ki daurewa zuciyarki, idan ma ba za ki iya ba ki fice zuwa gidan Futuha, Antinki tana can tare da Anna sai dare idan an ragu za su dawo." Tasleem dai ba ta ce mata uffan ba, ta dai ɗan ji sanyi jin Jannat ta kuɓuta amma tuna Fadeel da Humaira sun zama mata da miji yana baƙanta zuciyarta sosai. Haka tana ji da gani har Mamin ta miƙe ta shiga wanka. Ita kuwa wayarta ta hau lalubawa, ba ta fadi ba daga aljihun doguwar rigar atamfar dake jikinta ta zaro ta danna lambar Babandi da zummar ta ci mutunci sai dai kuma nan take reshe ya juye da mujiya. "Ya aka yi Tasleem? Kamar kinsan ina shirin kiranki. Nasan zuwa yanzu kina tunanin kin yi rashin nasara a aikinki ko? Kar ki damu, ki shirya yanzu ki zo ina son ganinki komai zai yi daidai." Sai ta kasa cewa komai bayan kalmar Toh. Ta miƙe jikinta har rawa yake yi ta yafa mayafinta ta fice daga gidan. Ba ta damu da taron jama'ar falon ba cikinsu kuwa har da Humaira da ke tsakiyar ƙawayensu da yan uwa ana hoto ana kuma tsokanarta. Ta bi Tasleem din da kallo yayinda itama ta kalle ta har ta a tuntuɓe. Ta kasa cewa komai ban da ta cigaba da tafiyarta, gani take yi ko mintuna kadan ida ta ƙara toh za ta ɓata ran Babandi kuma zai hana ta zuwa wajensa. Wani mugun tsoronsa take ji a zuciyarta. Ba ta ko damu da matasan da suka soma cika farfajiyar gidannasu ba ta fice. *** Fadeel kuwa daga sadda aka ɗaura auren, ya samu wuri ya yi nafila raka'a biyu gami da nuna godiyarsa ga Allah da ya ba shi abin da ya jima ya kwana da wuni cikin bege da kaunarta. Duk yanda ya so ya keɓe domin ya yi kiranta abu ya gagara, jama'arsa ta ko'ina ga yan uwan Mahaifiyarsa ma daga Yola ta ko'ina. Babu damar wayar dole hakanan ya hakura har zuwa sadda aka dunguma don zuwa gidan su Humaira gaisuwar iyaye. *** Cikin wani ikon Allah da kuma rabon a yi, ya yi shiga ta kamala ya bi tawagar Ango zuwa cikin gidan Amarya Humaira ba don komai ba sai don ya yi dacen ɗauke gudan jininsa Ahmad koda kuwa cikin babbar rigarsa. RANA DUBU NA ƁARAWO...."Masha Allah, ga nan Ango da tawagarsa nan shigowa." Faɗin wata mata, nan aka hau gyara hanya, suka shigo da sallama dauke a bakunansu kowannensu cikin gayu. Matasa masu jini a jika ga ruwan arziƙi. Ummita ta kauda kai daga kan Ridwan tun ganin da ya yi mata ya zubamata mayatattun idanunsa kamar ya haɗiyeta. "Wancan guy din fa ke yake ta kallo, ke kuwa kin ƙi ba shi dama." Raihana ta faɗi ƙasa-ƙasa, tuni ta gyara fuskarta ta fito, baƙin cikin halayyar yan uwanta ba zai sa ta kasa nunawa Humaira murnarta da samun miji ɗaya tamkar da dubu ba. Harararta kadan Ummita ta yi. Humaira ko tun da wata abokiyar tsoƙanarta ta sanya hannunta cikin na Fadeel ta yi ɗif ta kasa magana, duk iyakar kokarinta na ganin ta zare amma gogan sai ya tamke su tam a cikin nasa. Nan fa aka shiga hotuna bayan kammala gaishe-gaishe. Fadeel ya matsu ko kallonsa ne Humaira ta yi amma ina, kunya ba ta bar ta ba. Zuciyoyinsu sai wani zillo yake yi na farin ciki. Wizzy na tsaye daga baya yana ƙarewa gidan kallo da mutanen dake ciki, bai san Mami ba a fuska hakanan ita din ma balle ya yi tunanin za ta gan shi ko kuma shi din ya gan ta. Yana kuma da tabbacin zai wahala wani cikin su Humaira da Ummita su iya gane shi, a ganinsa abu har an shekara zai wahala su gane shi. "Ke Ummita, yaron nan dai ɗuminki yake son ji." Faɗin Hajjo tana mai miƙo mata shi bayan ta je sun kammala hotuna da su Fadeel an gaisa. Hankalin Wizzy gaba daya ya yi kansu, Ummitan ta ci wani irin kwalliya da blue lace ta yi kyau tsaf. Ahmad din ma shigar ƙananun kaya aka yi masa, ya yi ɓulɓul abinsa. Yana kallonsu cike da wani irin kauna da bai san daga sadda ta faro ba. Ya bi Ummita da kallon sama har ƙasa, ta ƙara zama wata yarinya sharr da ita. Daidai sadda wani ya karasa kafin Humaira ta kai ga sa hannu ta karɓi Ahmed, ya ce Hajjo ta miƙa masa shi. Wani ƙululun bakin ciki ya tokare a wuyan Wizzy, wannan wane ɗan iskan ne haka? Dama ya kula da irin shishshigin da yake yiwa Ummitan, toh kuwa bai isa shiga tsakaninsa da ɗansa ba. A yau zai raba su da wannan farin ciki ya ɗauke jininsa idan ya so daga baya ko Ummitan ya dawo ya sace. Shi ya ji ma zai iya aurenta su rayu tare. Ummita ta dubi Ridwan. Ya kashe ta da wani sassanyan murmushi, ta yi ƙasa da kanta. Ganin haka Hajjo da murmushi ta juya ta bar musu wurin tana mai fatan alheri a can ƙasan ranta. Ta tabbatar idan har wannan aure ya tabbata toh shakka babu Ummita ma tana cikin layin masu dace a rayuwa. Tana da labarinsa a bakin su Raihana da Humaira a sadda suke koɗa shi duk don su nemi kafa shi a zuciyarta. "Ni ake ta yiwa yanga? Ɗan nawa ma rowar ganinsa ake yimin?" Duk sadda ya kira Ahmed da ɗansa wani daɗi take ji amma ta ke kannewa. Yanzun ma ba ta ce komai ba sai kauda kai gefe. Ya taka zuwa inda ta mayar da fuskarta. Idanunsa ya kai ga Wizzy, ganin haka Wizzy ya kauda kai da sauri yana kallon wani ɓangaren, shima sai ya ɗan share amma tun sadda aka shigo yake lura da shi, gaba ɗaya zuciyarsa ba ta yarda da shi ba. "Mama tana tambayar yaushe za ki je ta ganki? Kinsan fa na ce mata sa ranar kawai ya yi saura. Kin amince." Ya karashe da ɗan ɗaga gira, ta zaro ido gami da ɗan dafe kirjinta. "Ni da bakina na ce maka na amince?" Ya ɗan bi bakin da kallo yana murmusawa kafin ya maida idanunsa kanta. Ta kauda kai, ta rasa dalilin da idanunsa ke mata wani irin kwarjini. "Ko ba ki furta ba ai idanunki sun fallasa sirrin dake cikin zuciyarki." Ta kasa cewa komai sai giftashi da ta yi ta wuce murmushi dauke a fuskarta. Shi dinma bin bayanta da kallo ya yi cikin murmushin har sai da Idris ya ɗan buga kafaɗarsa. Ya basar gami ga miƙa Ahmed ga ƴar yarinya kuma jika ga Baba Amina dake ta faman miƙa hannu wai ya ba ta shi. Ta karɓe shi kuwa ta yi gaba tana masa  wasa. Dukkan wannan abu akan idanun Wizzy suka faru. Ya gama shaƙar baƙin cikin wannan soyayyar da Ummita ta samu, ya kuma ji kwarin gwuiwar ganin wata ƴar albarkar ta rage masa aiki ta hanyar karɓar Ahmed da kuma nufar hanyar ƙofa da shi inda ƙawayenta yara suke tsaye ana wasa. Ya faƙaici idanun jama'ar dake wurin ya yi saurin yin baya. A wannan fakar idanun Ummita idanunta suka kai kansa, har abada ba za ta taɓa mance wannan mummunan fuskar ba duk kuwa da irin shigar manyan kaya na kamala da ya yi ba a can da yake shigar ƙananan kaya, kayan ma na ƴan duniya irinsa. Kirjinta ya hau bugu, ta ga ya juya zai fita, ta kasa sukuni ta bi bayansa, ta kasa magana saboda ta fi buƙatar tantance komai da idanunta kan ta yanke hukuncin ihu za ta yi ko kuwa gudu za ta yi. A yayinda hankalinta ke kan Wizzy, shi ko Ridwan nashi hankalin ya koma kanta ganin ta zo ta tsakiyarsu inda za'a yi hoto ta wuce ba a hayyaci ba. Ya juya da sauri ya bi bayanta daidai sadda Wizzy ya sa hannu ya karɓi Ahmed da yaudararriyar murmushi da ya sakarwa yarinyar gami da fadin ta ba da shi ya ga wannan fine boy din. Daga haka ta ga ya nufi wajen falon da shi yana ɗan yi mishi wasa. Ihun da ke maƙale a fatar bakinta shi ta saki gaba ɗaya iyaka ƙarfinta. Wannan ya ankarar da Wizzy, da wani irin sauri ya zura Ahmed cikin babbar riga ya soma  gudu zai fice. Ai cikin wani irin zafin nama Ridwan ya bi shi da sauran mazan dake a wurin. Waɗanda ke waje kuwa suka yi nasarar cafke shi, Ummita kam tuni ta fita hayyacinta kira take "Shi ne! Wallahi shi ne! Ya zo ya ɗaukemin ɗa!" Humaira da Fadeel da sauran jama'a hankalinsu ya tashi, Fadeel ya riƙe Humaira gam ganin yanda jikinta ya hau wani irin mazara, aka fita gaba daya zuwa farfajiyar gidan inda Ridwan ke riƙe da Wizzy gam! Ahmed ko yana hannun Dawud. Ummita na zuwa ta karɓi Ahmed ta rungume tana ja baya sosai daga Wizzy, kallonsa take yi a mugun tsorace jikinta na ɓari, Anti Maijidda da Hajjo suka riƙe ta sosai. Wizzy kuwa idanunsa sun raina fata, Humaira ta bishi da kallon tsaf. Tabbas shi ne. Ta hau nuna shi da yatsa itama. "Fadeel wallahi shi ne ya ketawa ƴar uwata haddi! Shi ne baƙin azzalumin da ya cuci rayuwarmu!" Sai ta fashe da kuka mai tsuma zuciya, Fadeel ya rungumeta sosai cikin alamun rarrashi. Nan dai Ridwan ya yi waya ga abokan aikinsa akan su iso da gaggawa.  Abba da jama'arsa dake zaune a falonsa na saukar baƙi jin wannan labari suka fito, ya nufi Wizzy ya bishi da maruka hagu da dama. "Yanda ka shigo hannu da yardar Allah ƙarshenka ya zo. Muje ni da kai shari'a yanzu aka fara. Azzalumi!" Wizzy dake cika da batsewa yana hura hanci kamar tsohon salansa sanadiyyar marin da ya sha na Abba ya tari Abban da sauri. "Ka dinga yin jam'u ai Yallaɓai! Azzaluman ai biyu ne ba ɗaya ba! Akwai azzaluma irin matar mai wannan gidan?! Ita ce ta sanya muka aikata wannan mummunan aikin don ta samu ta mallaki dukiyarka!" Ana ga wata ga wata! Nan fa kallo ya koma sama! Jama'a suka yi caa ana maganganu, kowanne da abin da yake faɗi. Abba kuwa ai sai da ya ji duniyar na juyamasa, yana ji abokan Fadeel suka yi caa a kansa akan ya ƙara shirga wata ƙaryar sai sun fasa bakinsa. Shi kuwa Wizzy ya dinga rantse-rantsensa cewar har da hannun matar Abba. Daidai lokacin motar ta iso aka titsa ƙeyarsa aka tafi. Su Fadeel ma babu jinkiri suka tafi, shi kam a son ransa ya so a ba shi matarsa kawai su fice tare don ya tabbatar wannan lamarin sai ta dinga kuka a kansa. Ibb ne ya nunamasa ba a haka tunda dai su na cikin rashin nutsuwa ya ƙyale su samu hankula su kwanta. Magana dai har yamma ana ta yi, kallo sai ya koma sama. Madadin hirar da ta shafi biki da kuma sabga ta mata sai gulmar Mami. Da yawa sun cika da al'ajabi sun kuma yi rantsuwa kan cewar za ta aikata. Wasu kuwa sun ce sam! Mami ta riƙi yaran da zuciya daya, kawai dai akan auren Humaira ne aka yi yaƙi da ita don a fili ta nuna ba ta ra'ayin Fadeel, zai kuma iya zamtowa akwai dalilinta. Anti Maijidda kuwa kuka sosai ta shiga yi tana hamdala da Allah ya nunamata ranar da kusan kowa ya gane wace ce Mami. *** Wai ina Mamin? Tun shigowar su Fadeel tana ɗaki, ta yi wanka sai dai ta kasa fiddo kaya balle ta sanya. Baƙin cikin wannan gidan arzikin da Humaira za ta shiga shi ya tsaya a ƙoƙon ranta, ƙarshe ma kuka ta shiga yi. Abin mamaki, kuka na baƙin ciki da jin inama ta mutu kafin wannan rana. Wai ɗiyar Fatima ce kishiyarta, ita ce dai ta samu wannan ɗaukaka ta ko'ina. Ita kuwa nata yaran daga bazawara mai ƙananun shekaru sai ko wata can da aurenta ke gantali, su kansu mazan sun ƙare karatunsu babu aiki. Kasuwar ma Abba ya dakatar da su daga zuwa saboda irin ɓarnar da ya ce suna yi masa. Yassar da Abban yace zai samar masa koyarwa ya rantse ba zai yi ba, shi kam Allah ya kiyaye a ganshi yana koyarwa. Wannan ya hasala Abban har ya fita hanyarsa ya ce ya yi duk yanda ya so. Tana nan kwance ta ji ihun Ummita da ya karaɗe gidan. Ta mike har zaninta na faɗuwa tana ja tana ɗorawa. Jiki na rawa ta ɗauki dogon hijabi ta zura. Saɗaf saɗaf ta bude ƙofar ta fita lokacin hankulan jama'a duka ya yi waje an fita an bi Wizzy. Ba ta fahimci wa Ridwan ya riƙe ba sai da kunnuwanta suka ji muryar Humaira na sanar da Fadeel  wai shi ne mutumin da ya keta haddin yar uwarta. Ai cikin Mami sai da ya yi wani irin kaɗawa. Jiki na rawa ta nemi hanya ta koma ɗakinta ta datse gam! Gumi fa ko ta ina ya shiga tsastsafo mata. Tana nan ta dauki waya amma rawar da hannunta ke yi ya sanya ta kasa koda bude wayar balle kuma ta kira. Ta yi wurgi da wayar sakamakon cikinta da ya shiga murɗawa ai sai ta nufi bandaki ta hau gudawa. Can ta ƙara fitowa ta yi jim a jikin ƙofar ɗakinta don jin me ke gudana, wani sabon al'amari ta ji, Anti Maijidda ke kuka da hamdala wai Allah ya toni asirinta. Yau gashinan Wizzy ya ce tare da ita ce suka haɗa baki suka yi garkuwa da su Ummita. Ai Mami sai ta sulale a wurin ta zauna daɓas! Wannan tashin hankalin da me ya yi kama? Duk da ta sani babu wata hujja da Wizzy zai nuna ya ce har da ita ciki amma wannan furucin nasa babban barazana ce a gareta. Haka ta wuni ta ƙi fitowa a ɗakin, duk irin bugun duniya da kiran wayarta da aka dinga yi amma ta yi biris ko kallon wayar ta kasa balle ta ga mai kiran. Tana ji wasu na rantsuwar tana ciki wasu kuwa cewa suke yi ga dukkan alamu dai ta fice a gidan tunda akwai wadanda suka ce sun ga fitowarta sanye da hijabi. Raihana kuwa a ranar asibiti ta kwana saboda tsananin ciwon kai da zazzaɓin da ya yi mata dirar mikiya. Hakanan a wannan daren Abba yace babu abin da zai sa a jinkirta kai Humaira ɗakin mijintaz da wannan tashin hankalin suna kuka suka rungume juna ita da Ummita tamkar kar su rabu. Ga ƴar uwarsu can a asibiti kwance, haka aka tsitsa ƙeyar Humaira bayan sun yi sallama da Abba ya yi mata nasiha zuwa gidanta na aure. *** Washegari kuwa tun asuba Mami ta shiga wurin Abba, yana dawowa daga masallaci sai ganin mace ya yi a zaune tana faman kuka. Ya kalle ta bai ce uffan ba ya kama hanyar shiga ɗakinsa. Ta tare shi da sauri ta rike kafafunsa tana kuka kamar ranta zai fita. "Abban yara, kada dai ace ka yarda da wannan baƙin ƙazafin da aka shiryamin? Innalillahi wa inna ilaihir raaji'un! Wallahi Abban yara muddin aka ce kai ma ka mara wa masu zargina baya nikam ban ga wanda zan kama ba. Ni Maryam me marayun Allah suka yimin da zan cutar da rayuwarsu?" Abba kallonta kawai ya ke yi da idanunsa da suka tasa ga dukkan alamu bai samu wani baccin kirki ba. Murmushin yaƙe ya bita da shi. "Ni kin ji na ce maki ina zarginki ne Maryama? Kin ji wani abu daga bakina?" Sai ta mike tsaye suna duban juna. "Ba ka faɗi ba, amma shirunka ya nuna ka aminta da zargin masu zargi." Ya kauda kai don wallahi ji yake yi a duniya a yanzu babu abin da ke mishi muni ya kall sama da fuskarta. "Maryama, abar zancen. Tunda shi wannan baƙin azzalumin ya shiga hannu, gaskiya za ta yi halinta ai yanzu. Ki kwantar da hankalinki masu zarginki za su bari muddin komai ya bayyana." Yanayin da ya yi zancen sai ba ta gamsu babu komai a zuciyarsa ba dangane da ita. Ta dai matsa mishi kamar yanda ya buƙata ya faɗa ɗakinsa. *** Ina labarin Humaira da Fadeel? ***Afuwan zuwa gobe zan ɗora in sha Allah. Kuyi hakuri Dukan Ruwa saura ƙiris ya yi maku bankwana in sha Allah. ***Kukan Humaira ya ƙi ci ya ƙi cinyewa. Abubuwa da dama ne ke ƙara mata ƙarfin kukan. Wannan tashin hankalin na jin wai da sanya hannun Mami a garkuwa da su ya tsaya a ranta. Ta dinga tunano kalar rayuwar da suka yi da ita a gidan tsawon shekarun da ba su da yawan da za a kasa ƙirgawa, irin kulawa da nuna kaunar da ta dinga yi mata. Ita kuwa komai da Mamin ta ke mata ta ɗauke shi da zuciya ɗaya, ba ta taɓa kawo wani abu na mugun zato a kanta ba idan aka cire sanin da ta yi Mami ba ta farin ciki da aurenta da Fadeel. Sai yanzun abubuwa da dama suke mata yawo a kwakwalwa, wai dama ya za'a yi macen da ta haifi yara da kanta ace ta fi kaunarsu akan abin da ta haifa? Kenan ta tabbata batun Hajjo da ta ce da biyu Mamin ta dakile ta daga karatun boko? Toh idan ita din ta kasance ɗiya ga tsohuwar kishiyarta da ta rasu, me Ummita ta tare mata? Me ta yi mata a rayuwa da har sa ta nakasta rayuwarta har haka? Ta maida ita ƙaramar budurwa kuma bazawara? Tayi sanadin da aka keta alfarmarta har wannan masifa ke bibiyarta wato Wizzy. Ta yi sanadin da aka fasa aurenta da masoyinta Sahabi. Mene ne ribar Mami da ta shuka dukkan waɗannan munanan ayyukan. Shin kodai Raihana ta sani ne? Tambayar da ya shiga kwakwalwar Humaira kenan. Ta ɗan muskuta ta share fuskata. Anya Raihana ba ta da wani labarin dangane da Mami? Yarinyar a yan kwanakin nan ta sauya gaba daya ba ta rabo da kuma da damuwa? Sai an matsa da tambaya sannan ta ke saita kanta ta shiga harkokinta? Kai gaskiya tana da tabbacin akwai abin da Raihanar ke ɓoyewa. Sai tausayin ƙanwarta ta ya mamaye zuciyarta, ita ɗin ba ta da wani aibu a yanzu, ta tsarkake zuciyarta daga dattin ƙiyayya da hassada irin wanda yan uwanta Tasleem da Futuha suka ɗorawa kansu. Tana kaunarsu tana kuma zaune da su da zuciya ɗaya babu wani abu bayan hakan. Turo ƙofar da aka yi gami da sallama cikin tausassan murya ya katse tunanin Humaira, ta ƙara sunkuyar da kanta tana ɗan sakin numfashi irin na wacce ta ci kuka kuma take kan yinsa. A can ƙasan zuciyarta ta amsa sallamartasa. Ya ƙaraso cikin dakin sosai, ya yi wanka ya sauya sutura zuwa jallabiya fara ƙal wacce ba ta ɓoye kyakkyawan tsarin halittar da Allah ya yi mishi ba. Sai baza ƙamshi yake yi ta ko'ina. Ya ɗan bi ɗakin da kallo kaɗan yana murmushi da alfahari da zaɓin da ya yiwa Humairar na kalar da ta fiso wato kore. Sai adon ɗakin ya kasance farin da kore. Zama ya yi a gefenta har kafaɗunsa na gugar nata. Fadeel kenan, shigowarsa babu aboki ballantana ɗan rakiya. Hannu ya sa ya yaye rufin fuskarta. Ganin hawaye kwance ya sanya shi saurin riƙo haɓarta da ɗago kan suka dubi juna, ai yanda ya ga idanunta sun kumbure sun yi ja sai ya ji wani sabon tashin hankalin na daban. "Boddo, kukan kike ta yi? Ya Salam, sai ki janyowa kanki wani ciwon?" Ya shiga taɓa goshinta da gefen wuyanta don ya ji ko jikinta da zafi, ita kuwa sai noƙewa take shi ko zuciyarsa daya yake yi. Gaba daya ganinta cikin wannan halin bai masa dadi ba ko kaɗan. "Please ya isa hakanan. Kinga yanzu babu zafi jikinki. Kiyi hakuri tunda komai yanzu yana hannun hukuma. Idan kuma don kin ji ya ambaci Maminki ne kar ki bari wannan ya yi tasiri a zuciyarki. Tunda har ya gan shi a hannun hukuma to zai iya ƙirƙirar kowane sharri ya faɗi. Ki kwantar da hankalinki koma mene ne bincike zai bayyana." Ta gyaɗa kai, ya lalubo tafukan hannunta ya sanya cikinnasa. Rashin sabo da hakan daga shi din har ita sai da suka ji wani yarr. "Kina da alwala?" Shi ne tambayar da ya yi mata, nan din ma kan ta gyaɗa ta a kokarin zare hannunta. A hankali ya saki sannan ya faɗa banɗakinta. Can kuma ya fito ya yi mata umarnin zuwa su yi nafila. Ba musu ta miƙe ta gyara zaman laffayarta. Bayan sun idar ya dafa kanta ya yi mata addu'o'i. Daga nan ya kama hannunta ya miƙar suka fita suwa falo. Ta ɗaga kanta a hankali tana kallon falon, hamdala ta shiga ui a zuciyarta, yau ita dai Humaira ita ce ta mallaki wannan irin falon da sai dai ta gani a soshal midiya su na yawo don ko gidan Futuha da ake ta santinsa bai kai rabin nata tsaruwa da kyau ba. Komai a falon adon skyblue ne da fari, iyakar kyau da tsari ya yi. Jan hannunta da Fadeel ya ƙara yi ne ya maido ta hayyacinta, ta ɗan yi saurin janyewa tana ɗan tura baki. Da alama ita ba ta son wannan baƙon halin nasa na riƙe mata hannu. Ya yi murmushi ya matso dab da ita gami da sa hannunsa saman ƙugunta ya matse ta gam har fuskokinsu na haɗuwa wuri guda. Idanunsu a lumshe ba ka jin komai sai bugun da kirjin kowannensu ke yi. Daddaɗan kamshi babu ko digon wari shi ke fita daga bakunansu. "Kin zamo mallakina Humaira, babu sauran wata ƙofa da ke buɗe tsakaninmu. Babu kuma sauran sharaɗin da ya yi saura. Ki taimake ni ki bar kokarin yimin iyaka da dukkan inda hannuna ya sauka a jikinki." Ya yi maganar da muryar da ta rasa na Fadeel ne ko kuwa, har sai da ta buɗe idanunta, aka yi sa'a shi ɗinma kallonta yake yi a lokacin, sai dai ga mamakinta, hawaye ne kwance saman kumatunsa. Ta yi kokarin ja baya a ɗan ruɗe, ya yi saurin ƙara riƙe ta sosai. "No Humaira, bar ni na ji ɗuminki, na ƙara samun tabbacin Fadeel ba mafarkin da zai iya farkawa yake yi ba. Alhamdulillah Ya Rahman." Ya furta zuciyarsa da wani irin nauyi ga farin cikin da yake lulluɓe shi. Sabuwar soyayyar Humaira na ƙara huda dukkan wata ƙofa ta jikinsa tana shiga tana mamayarsa. A ɓangaren Humaira kuwa ba ta san sadda yatsunta suka sauka a kuncinsa ba, dauke masa hawayen ta yi yayinda itama nata su ke zuba. Ita ya kamata ta koka ba shi ba, ta wahalar da shi iyaka, ta kuma yi mishi cin fuska kala-kala, sai dai dukkan wadannan bai sa ya juya baya ya haƙura da ita ba. Sanadinsa za ta iya cewa ta samu warakar zuci da gangar jiki daga cutar da ake tunanin iskokai ne masu sanya ta tsanar dukkan wani ɗa namiji a rayuwa. Ya riƙe yatsunta idanunsa a cikin nata gami da kai su baki ya sumbata. Ta runtse idanun tana jin kamar ta kwace yatsunta amma kuma roƙon da ya gama yi mata na kar ta yi mishi kowane iyaka ne ya sanya ta daurewa. Tana jinsa ya dinga yin yanda ya so har sai da suka nemi faɗuwa sannan ya bar ta. Ta yi saurin zama a kujera mafi kusa da ita. Shi kuwa durƙuso ya yi a gabanta gami da riƙo dukkan yatsun hannayenta yana dubanta kai ka ce ranar ya soma ganinta a rayuwa. Murmushi sosai yake yi yana kallonta yayinda ita kuma ta kauda kai zuwa gefe guda, kallonsa na haifar mata da yanayi mai kashe kuzarin jiki. "Nagode, nagode da kika aminta da aurena. Ina mai miki albishir da cewa kin dace in sha Allahu, kamar yanda dama ni tun tuni na sa a raina samunki a rayuwa shi ne dacewar da zan yi. Alhamdulillah. Yau ga Fadeel ga Humaira. Kin ga ranar haƙuri ko?" Ta ɗan yi murmushi. Ya kai hannu ya shafi leɓɓanta. "Soyayyata kaɗai ta isa mu rayu cikin farin ciki da aminci. Nidai na san koda ace har yau ba a wani sona, toh ana ji da ni." Ta yi ƙasa da kanta, shiru ya biyo baya, shi bai bar wasa da yatsunta da kuma bin ta da kallo ba, ita kuma ta kasa furta abin da ke yawo a zuciya da saman leɓɓanta. So ta ke ta ba shi tabbacin cewa itama fa tana so da kaunarsa wanda ta san ya sani kawai so yake yi ya ji daga bakinta. Miƙewa ya yi ta bishi da idanu har ya je fa ledojin da ya shigo da su yana fadin shi yunwa yake ji saboda tun safe bai ci komai ba murnar an ɗaura aurensu. Suka ci har ta miƙe ta bar shi, yana jinta tana masa sai da safe ya gyaɗa kai kawai yana bin ta da murmushin da shi kaɗai ya san ma'anarsa. Ɗakinta ta shiga ta ɗan tura ƙofar, laffayar jikinta ta warware ta ninke ta buɗe sif  dake manne jikin bango ta sanya. Rigar da ta ji Hajjo ta ce mata ta sanya shi ta fiddo, warware shi ta yi, doguwar riga ce mai hawa biyu kalar maroon. Gefenta wani gashi ne mai laushi. Ta shiga bandaki ta sauya shiga sannan ta fito ta nemi wuri ta kwanta bayan ta kashe fitila. Ba ta fi mintoci da kwanciyar ba ta ji shigowar Fadeel, kirjinta ya hau bugu tara-tara, wai yana nufin anan zai kwana? Shi ne tambayar da ta yiwa kanta, ta runtse idanunta tamau alokacin da ya hau gadon sosai, fitilar ya kunna haske ya karaɗe ɗakin, da kallo ya bi fuskarta, ya sani ba bacci take yi ba, runtse idanun na dole ne. Ba ta yi aune ba ta ji ya yaye gaba ɗaya bargon, da sauri ta dora hannuwa saman fuskarta. Ya yi murmushi ya kashe fitilar kafin ya maida bargon ya rufa musu. Janyo ta jikinsa ya yi sosai, ya fidda hannuwanta saman fuskarta, duk kuwa da cewar dakin da duhu ba ganin idanunta zai yi ba. "Please faɗamin koda sau ɗaya ne naji. Kinji?" Ya na maganar tamkar mai raɗa. Ta yi shiru sai bugun kirjinta da yake ji, yanayin maganarsa sai ya ba ta tausayi, ta tuna dukkan gwagwarmayar da ya sha a kanta. A hankali ta bude baki ta ce. "Ina matuƙar so da ƙaunarka Fadeel." Ya yi ɗif na lokaci ƙalilan, ita kuwa ta samu wani irin kuzarin da sai da ta ƙara maimaitawa, kaunar tasa take ji yana fisgarta sosai. Ai ba ta yi aune ba ta ji sauran kalaman bakin nata sun maƙale adalilin toshe nata bakin da ya yi da gurbin nasa. Daren dai sun raya shi tamkar ba za su yi bacci ba. Washegari suka tashi zuciyoyinsu cike da walwala da soyayya mai tsafta. Humaira kuwa jikinta ya yi mugun sanyi don tuna ƴar uwarta Ummita. Wannan abun shi Wizzy ya kwatar mata da ƙarfin tuwo. Wannan dai ƴancin da Fadeel ke ta cin alwashi da alƙawarin kyautata mata saboda shi? Dakyar ta samu lamarin ya fice a ranta sakamakon kulawar da Fadeel ya dinga ba ta tamkar ya haɗiye ta. Sun kira waya ta gaisa da Raihana ta kuma tabbatar da samun saukinta, hakanan da su Hajjo suka zo yi mata sallama sun ba ta tabbacin Ummita ta ɗan saki ranta har Abba na fadin zai haɗa ta da Anti Maijidda su wuce Bichi. Hakan ya yiwa Humaira dadi kwarai domin ita kanta ba ta kaunar ganin Mami a wannan gaɓar, zuciyarta ba ta amince da ita ba kamar a baya. *** Kafin su Hajjo su kai ga dawowa gidan Mami, sai ga Jannat sun dawo gidan har da Futuha gaba ɗaya. Sun samu labarin komai dangane da zargin da ake yiwa Mami na satar su Ummita. Futuha da Tasleem waɗanda suka san da zancen hankalinsu ya tashi ainun domin sun san komai ba kuma zargi ba ne. Jannat kuwa ashariya ta dinga zundumawa gami da yiwa Mamin Allah ya ƙara. "Kin fifita su akan yaranki na cikinki ai ga sakamakon abin da kika yi nan kina gani." Ita dai Mami ba ta ce uffan ba, Tasleem ko da tun a gidan Futuha take fama da lemun tsami a baka saboda tashin zuciya, wani amai ne ya taho mata da ya yi sanadin miƙewarta a guje ta faɗa banɗakin Anna. Gaba ɗaya suka bi ta da kallo. Mami kirjinta ya yi wani irin duka da ƙarfi. "Wannan tashin zuciyar da kike ta yi dama tun a can ai nasan ba a banza ba. Sai ki tattara ki koma gidan Hamza tunda akwai sauran rabo tsakani." Mami ta juyo a ruɗe ta ƙara bin Anna da kallo mai maganar hankalinta kwance. Futuha da Jannat babu wanda ya dara don gaba ɗayansu zuciyoyin ba dadi, ga Futuha, baƙaƙen maganganun da ake yi mata da habaici a Tiktok ya fi ƙarfin kanta. Ga kuma Yakubu da ya ɗauki Ƴar Snow zuwa Saudiya inda daga nan za su wuce Dubai sai ko London. Kuɗin da ya bar mata a wannan tafiyar shi ne rabin abin da yake ba ta kyauta a wata, gaba ɗaya ya rufe bakin aljihunsa sai dan abin da bai taka ya karya ba yake ba ta. Ta kuma fahimci azabar da yake son gana mata muddin ta yi sake za ta dame ta shanye irin kalar na uwargidansa. Jannat ma dai rigima ce ake ta yi da nata mijin, inda mahaifiyarsa da danginsa suka dage akan lallai sai ya rabu da ita ko kuma ya yi aure. Zafi biyu ya haɗe mata ga tunanin inda za ta fara samu ta tattaro kan kudadenta da ta yi asararsu. Miƙewar Mami ce ya sa duk suka dube ta, kai tsaye banɗaki ta je ga Tasleem, suka yi kiciɓus sadda take fitowa tana share baki. "Ke, yaushe rabonki da al'ada?" Tasleem ta ɗan yi shiru, ita dai ta san koda ta dawo daga gidan Hamza tana jego ne ba ta yi wanka ba,  tun da ta yi wankan kuma ba ta ƙara ganin jini ba. "Ina magana kin mayar da ni sakara! Nace yaushe rabonki da al'ada?!" A firgice Tasleem ta amsa. "Tun farkon dawowata da na yi wankan biƙi. Amma Mami ai shayarwa nake yi, shi ne dalilin rashin ganin al'adata." Mami ta ɗan yi jim tana lissafawa, kai ba za ta taɓa yarda ba, hankalinta ba zai kwanta ba idan har ba bincikawar ta yi don kanta ba. Wannan yasa ta yi kiran Ƙassim a waya ba shiri ya zo. Su Jannat dai sun yiwa Mami caa wai akan me take zarginta ita dai shiru kawai ta yi. Har Ƙassim ya shigo ta ba shi kudi ya amso mata Pt-strip ba ta ko sauraron zantukan su, Anna har da su zaginta wai tana zargin ɗiyarta da bin maza alhalin tana idda? Ita dai ba ta tanka ba, Tasleem kuwa shiru ta yi ba ta ce uffan ba. Suna nan hira na gudana tsakanin Anna, Jannat da Futuha har Ƙassim ya kawo aiken. Mami ta karɓa ta ce ya fice, da kanta ta titsa ƙeyar Tasleem har bandaki. Tasleem a dole ta bi umarnin Mamin don itama tana son tabbatarwa, ana yi kuwa sai ga ranƙwalelan shaidar positive ya nuna a jiki. Mami ta kusan sakin ihu a bandaki, ciki dai ciki?  Toh uban waye ya yiwa Tasleem din ciki? A haukace ta ƙara tambayarta cikin fita hayyaci. "Don ubanki wani abu ya shiga tsakaninki da Babandi ne?" Ta kasa magana, jikin Tasleem ya hau rawa, dama ta soma zargin cikin ne ashe ko ya tabbata. Wannan ruɗewar ta Mami ya sa tsoronta ya daɗu. Ita kam ta shiga uku idan ciki ne ya shiga jikinta. Shirunta kuwa ya tabbatarwa Mami cewa eh, wani abu ya gifta tsakaninta da Babandi. Ai sai ta shiga duka Tasleem kamar an aiko ta, Tasleem har ta fito daga bandakin a guje Mamin na biye da ita har cikin ɗakin. Tana dukan tana tsinewa Babandi. Sai da su Jannat suka riƙe ta gami da yi mata inkiya kar mutane su dawo su ji. "Wai waye Babandi? Me kike magana a kai? Ciki kuma?" Anna ta nemi ba'asi a ruɗe. Nan Mami ta kora musu bayanin bokannata da yanda suka yi kaca-kaca akan aikin Humaira da Fadeel da ma yanda ta tura Tasleem wajensa har mai afkuwa ta afku. "Maryama baki da hankali! Ke mahaukaciya ce ashe ina maki kallon mutum mai hankali? Ta ya ya za ki samu saɓani da mutum ki yi mishi zagin uwaka ubaka kuma ki tura ɗiyarki wajensa?! Shikenan! Yanzu dai ta tabbata ɗan Bokanki ne a cikin Ɗiyarki." Wannan kalma ta ƙarshe na Anna ya mugun jijjiga zuciyar Mami. Ai sai ta fashe da wani irin kuka, Jannat masoyiya ga Tasleem itama kukan ta sanya gami da zuwa ta ɗago Tasleem tana rantsuwar ita dai wallahi sai ta kai ta an zubar da cikin. Nan da nan Tasleem ta ture ta. "Aa wallahi! Ba wanda ya isa ya zubarmin da ciki, Babandi ya ce idan na tabbatar ciki ne da ni toh yana son abinsa idan na haihu na kai masa!" Tana maganar kamar ba Tasleem ba cike da faɗa idanunta tsaye kai ka ce ba ita ta gama kuka yanzu ba. Gaba daya suka bi ta da kallon mamaki. Kiran da Dawud ke kwalawa Mami iyakar ƙarfinsa ya yi sanadin da suka ɗunguma cikin tashin hankali zuwa waje. A falo suka yi kiciɓus da shi, lokacin su Hajjo sun dawo ba su kai ga shigewa masaukinsu ba. Wasu kuwa sun fice zuwa kasuwa ƙarasa siyayya. "Meyafaru Dawud?" Ta tambaya jikinta a mugun mace. Kan ya kai ga cewa komai sai ga Ridwan cikin kayan aikinsa da abokan aikinnasa su uku, biyu mata sai ɗaya namiji. Fuskarnan tamkar ba shi ne mai fara'a ranar bikin Fadeel ba. Ya ɗaure ta tamau, ya fito a jami'in aikin na gaske marar son wasa. Arrest warrant ya buɗe ya nunawa Mami. "Hajiya mun zo tafiya dake bisa zargin da ake yi maki na garkuwa da yaran maigidanki. Hukuma ta bamu damar shigar da ƙara kotu." Wani razanannen ihu Futuha ta saki tana ƙunduma uban ashar wai ƙarya ne. Shi kuwa Dawud hawaye kawai yake fitarwa don dama labarin da ya zo kawo wa Mamin kenan. Su Hajjo suka yi cirko-cirko suna kallon ikon Allah har matan nan suka nufi Mami da zummar tisa ƙeyarta a tafi. "Me kuke nufi? Ina ku ke zaton za ku kai ni?! Yanzu a ganinku zan cutar da yaran da nake yiwa so fiye da yara a da na haifa?" "Hajiya wannan duka shari'a ce za ta bayyana. Yanzu dai ki bamu haɗin kai mu yi aikin da ke gabanmu." Wannan ranar ta zo musu da tashin hankula iri-iri. Futuha ta ɗauki waya ta yi kiran Abba, koda ta sanar masa ban da Allah ya kyauta gami da kashe wayar babu abin da ya ce. Nan Futuha ta hau fadin wai dama Abba ba sonsu yake ba, ya fi so ya ga sun watse sun bi duniya! Mami kadai ke son su tsawon shekarun nan komai da take yi don su take yi. Ganin Futuha na kokarin yin suɓul da baka ne ya sanya Mami dakamata wata tsawar. "Ke! Ya isa hakanan! Nace ki bari haka! Ai ƙarya fure take ba ta ƴaƴa. Idan ma an yi hakan don a ɓatawa uwarku suna ki kwantar da hankalinki babu inda ƙarya za ta je. Duk inda za su kai ni zan fito." Abin da Mamin ta ce kenan sannan ta yi gaba ma'aikatan suka mara mata baya. Ridwan sai da ya tsaya ya ɗan waiga, rashin ganin Ummita a wurin sai ya ji hakan bai masa dadi ba. Kawai sai ya sa kai ya fice. Nan fa yaran Mami kamar su yi hauka. Suka kira Mubarak suka labarta masa, hankalinsa ya tashi. Ya kira Abba, Abba ya kwantar da hankalinsa ya ce ya yi hakuri ya nutsu tunda satika ya rage ya kammala ya dawo, ya bari zai kula da komai. *** Kamar da wasa sai ga Mami har tsawon sati a hannu hukuma, babu duka balle zagi, ta kafe akan ita ba ta san Wizzy ba kuma ba ta san ma a inda ya santa ba. Wizzy ma an tambaye shi yace shi bai taɓa ganin wacce suke waya ba, amma ya riƙe muryar. Ya kuma sani matar uban su Humairar ce. Sai da Mami ta cika sati aka shiga kotu, duka wannan Abba yana asibiti adalilin ciwonsa da ya tashi. Raihana ko ta dawo gida amma Abba ya bata umarnin tattarawa ta koma gidan Baba Amina don ta ƙarasa jarrabawarta. Ummita kuwa tana Bichi amma sanadin shari'ar sai da ta dawo. Ita da Humaira aka nemi su bada bayanin komai da ya faru da su, haka kowaccensu ta yi magana zuciyoyin cike da rauni babu kamar Ummita dake ƙara jin tsanar Sadik Wizzy  da su Baaba wadanda duk aka titso ƙeyarsu ta hanyar Wizzy din, kowannensu ya amsa eh ya aikata laifin idan ka cire Mami da ta dage akan ita sharri da ƙage akai mata. Lauyar da Hajiya Lubna ta ɗaukar mata ta tsaya tsayin daka wurin yi mata wannan yaƙin. Aka yankewa su Wizzy hukunci daidai da laifukansu yayin da kotu ta wanke Mami daga zargi bisa duba da rashin hujja koda ƙwaya ɗaya da za'a kama ta dominsa. *** Ta dawo gidanta hankali kwance, yaranta gaba daya su na cike da farin cikin kuɓutar mahaifiyarsu da kuma wanke ta da kotu ta yi idan ka cire Raihana da ba ta gidan kuma ko labarin ma ba ta kaunar ta ji. Ummita da Humaira kuwa har abada ba su jin  za su ƙara aminta da Mami. Ballantana kuma Abba da yake ji a jikinsa lallai da saka hannunta. Ya kuma kara yarda da kalar zalunci na matar da yake aure. Ta iske Abban a falonsa zaune yana kallon labarai, ga dukkan alamu hankalinsa ma ba ya kan talabijin din, ya zurfafa cikin tunani. Gaba daya ya rame kamar wanda ya yi cutar watanni. Ita kanta Mami ta rame saboda tashin hankulan da ta gani a wannan ƴan watannin. Zama ta yi gefensa. Ya ji zuwannata amma bai ko kalle ta ba. Kafin ta kai ga magana ya riga ta cikin shaƙaƙƙiyar murya. "Maryam, zaman me Jannat take yi a gidana?" Ta yi turus, ta yi zaton zai ce wani abu a kanta amma sai ta ji ba ma ta itan yake ba. Cikin ƴar borin kunya ta ce. "Ina za ta iya tafiya gidanta alhalin yar uwarta na garƙame a wajen jami'an tsaro? Adalilina ne ya sanya ta ke zaune." Ya miƙe zaune sosai daga kishingiɗar da ya yi. "Ta tattara ta bar min gidana, ba na buƙatar ganinta. Abin nufi, koda wasa kada ta ƙara gangancin takowa cikin gidannan! Gida dai nawa ne, ni ke da iko da shi! Toh daga yau ba na buƙatar ta ƙara zuwa." Sulhu take nema, tana so ta shawo kansa don ta san meke tafe a ransa a kanta don haka sai ta yi saurin amsawa. "An gama Abban yara. Zan sanar da ita ba za ta ƙara takowa ba." Bai ce uffan ba ya na ta tufka da warwara har sai da ya ji ta kwantar da kai saman kafaɗarsa. "Abban yara kana kaunata, naji ance har kwanciya asibiti ka yi sadda aka tafi da ni. Nayi mamakin wannan ƙazafin da wannan baƙin azzalumin ya so ya yimin, ya kusa raba ni da rigar mutuncina." Abba ya yi wani murmushi mai ciwo. "Kika ce rigar mutunci Maryama? Ina rigar mutuncin naki yake? Ai a yanzun ma da nake tare da ke, DARAJA ƊAYA kawai kike ci. Ban da wannan kusan zan iya cewa babu komai da ya rage a tsakanina da ke." Yana kai wa nan ya zame kanta daga kafaɗarsa, ta yi wani irin zama tana kallonsa satoto. "Bangane nufinka ba? Daraja ɗaya kamar ya? Igiyar auren fa?" Ta yi tambayar zuciyarta na duka da karfi, kallonsa take yi kawai tana lissafo ire-iren tashin hankulan da ta jefa kanta ciki duk a sanadiyyarsa da yaranta. Toh me Yusuf ke shirin ce mata?Abba ya yi ɗan murmushin takaici. "Aure? Ai ba ki ɗauke ni miji ba. Nima rashin sani ne ya kai ni ga ɗaukar mace irinki a matsayin matar aure, uwa ga yarana. A iyakar zaman da nayi da ke, ki faɗamin abu guda da na tauye maki na haƙƙoƙinki dake rataye a wuyana Maryama. Abin da ban taɓa zato ba, ashe wayona da hankalina bai min rana ba tunda har na rayu da mace irinki mai fuska biyu har na tsawon shekarunnan ba tare da na ankara ba. Kura da fatar akuya, kin cutar da ni kin cutar da ahalina. Na riƙe ki da zuciya daya, na kula da ke da kuma naki. Wannan wane kalar sakayya kika yimin? Ni dai Yusuf kika so a kashe? Kika gurɓata rayuwar yarana? Da me na rage ki? Wace buƙatar ce da ta zame min wajibi ba na kokari wajen sauke shi?" Mami sauraronsa take yi amma fa gaba ɗaya ya gama kashe mata dukkan wani kuzari. Kirjinta ya hau bugu fat! fat! Wato ta tabbata dai Abba da kansa ya sani ta yi yunƙurin kashe shi da Humaira? Ashe dama kurum ya yi yake bin ta da kallon shashasha? Dama rigar mutuncinta ya jima da kecewa a idanunsa? Wani gumi ya shiga tsirfo mata, tana sauraronsa amma ba ta iya fadin ko harafin A ba har ya kammala ya mike ya fice zuwa ɗaki ya bar ta da nanata zantukan ƙarshe da ya yi. "Ki nesanta kanki daga zuwa ɗakina Maryama. Ki zauna a naki ɗakin har zuwa sadda mai yiwuwa ko zaman ya ƙare ko wani abun daban saɓanin tunaninmu ni da ke." Mikewa tsaye ta yi gwuiwoyinta a sake, ashe dai har yanzu akwai sauran rina a kaba, a tunaninta ta gama rufe bakin tsanyar tunda har shari'a ta wanke ta ba tare da kawo hujja ko daya zai nuna akwai sa hannunta ba. Lallai kafin Abba ya ankare da abubuwan da ta shuka na baya, ya kamata ta san mafitarta. Da wannan ta miƙe ta koma ɗakinta. *** Kwanaki uku, abu dai kamar wasa ta ga dagaske ne, tsakaninta da Abba sai idan ta gaida shi ya amsa, babu sakin fuska balle har ta samu damar wata maganar. Zai shirya ya yi ficewarsa ko abincinta ba ya saurara. Jannat kuwa ta tattara nata ya nata ta bar gidan. Anna abin ya taɓa ranta ta kuma rantse sai ta yiwa Abba magana akai. Mami dai ta hana ta amma ina! A rana ta huɗu ne da tafiyar Jannat, ta tsaya a hanyar da ta san cewa dole ta nan din yake zuwa ya fice. Yana fitowa kuwa ya gan ta. Ɗan durƙusawa yanda ya saba ya gaishe ta a mutunce. Ta amsa tana cin magani gami da gyara tsayuwa sakamakon ƙafa da ta matsa mata. "Isuhu, na yi shiru ne saboda ban sani ba ko Maryama za ta iya kokarinta wajen ganin ta sa ka janye dokar da ka kafawa Auta na zuwa gidannan sai na ga hakan ya faskara. Wannan ne ya sanya ni zuwa da kaina domin na ji ba'asi. Haba Isuhu, duk wani abu da yarinyar nan ta aikata sharrin shaiɗan ne, ta ba da haƙuri ta kuma nemi gafarar yarannan (acewar Annar kenan), toh na mene ne za ka hana ta zuwa inda uwarta take fisabilillah idan dai ba ni ɗin ka yi shirin kora ba?" Abba sosai ya yi mamakin son zuciya irin na wannan matar, wato don ba nata aka yiwa ba? Kai shi yanzu dukkanin dangin Maryama ma tsoronsu yake domin su na shayar da shi mamaki. Yanzun ne ya ƙara fahimtar cewa ashe dai ba tsanarsu wasu a danginsa suka yi ba, ashe Hajiya Maijidda ba a banza ta tsani ganin Maryama ba. Ita din ta jima da sanin ainahin fuskar Maryama. "Isuhu ka yi shiru ina magana?" Anna ta buƙata a ɗan zafafe, abin da bai taɓa gani kenan a tare da ita ba. Koda dai ya sani cewa duk tafiyarsu guda. "Kiyi hakuri Hajiya, ni dai Isuhu idan har wannan gida ikona ne, toh Jannat ba za ta ƙara shigarsa ba. Ban raba maku zumunci da ita ba tunda taku ce, amma idan dai a wannan gidan ne toh sai dai ku yi hakuri. Duk sadda kike da buƙatar zuwa wajenta in sha Allahu mota da direba ba zai gagareni samar maki ba." Anna ta saki baki galala, yau Isuhu da kansa ke yi mata musu? Wato dai ba a shaidar ɗan kuturu sai ya girma da yatsa. "Ai shikenan, tunda dai hakanan ka ce nima yanzu dole zan haƙura da zaman gidanka. Allah ya bamu alherinsa." Abba ko a jikinsa ya miƙe. "A gafarceni Hajiya, amma ni dai na gama yanke magana. Ban ce ki bar gidana ba saboda ba ki yimin komai ba.." "Aa, wannan dai kora da hali ne. Ba Auta kaɗai ka kora ba, nima dama watakila kana da niyyar kora ta tunda iyakar saninka ai ba zan rayu a gidan nan babu Auta ba. Nima dai watakila kana ƙullace da ni, babu yanda ka iya ne shiyasa." Abba ya ɗan yi murmushi mai ciwo jin abin da ke fita daga bakin ƊAN ADAM mai mance halacci, mai son kai da son zuciya. A yau dai Anna ita ke korar kanta daga gidansa saboda son rai irin nata. "Ni dai Allah ya sani, ban kore ki daga gidannan ba saboda na dauke ki tamkar uwa a gareni. Ina mai baki hakuri bisa abin da na yi idan bai maki dadi ba. Ki yi hakuri hakan ba zai sauya komai ba." Daga haka ya sa kai ya fice, yana jin Anna na salati da kiran wai dama can ya gaji da ciyar da ita amma bai ko juyo ba sai murmushin baƙin ciki da tausayin kansa da ya ke ji na zaɓen tumun daren da ya yi tun a farko. Kewar iyayensa ya ji na mamayarsa, ashe dai iyaye ba za a rabu da kewarsu ba musamman ma irin nasa nagari masu halayyar dattako. Ya yi musu addu'ar samun rahmar Ubangiji kana ya shiga mota. Madadin zuwa kasuwa sai kawai ya fice zuwa gidan ƙanwarsa Baba Amina. *** Ya iske ta zaune, Raihana ba ta nan ta fice jarrabawa, hakanan sauran ƴanmatan yarannata su biyu su ma sun fice. Ita daya ya iske. Tana ganin da yanayin da ya shigo nan da nan hankalinta ya tashi, ta kira sunan Allah a zuci da kuma fili. Bayan ya zauna ta gaidashi. Kawai daga tambayarsa ko lafiya, ya soma zubar da hawaye. Baba Amina mace mai saurin kuka don har Abba na cewa su Humaira ita suka biyo, nan da nan ta soma kukan itama. "Yaya lafiya? Ko mene ya yi zafi maganinsa Allah." Ya jinjina kai. Ya ba ta labarin dukkan abin da ya sani a yanzu game da Mami har da yanda suka yi da Anna. Ya kara da fadin. "Amina na yi zaɓen tumun dare." Baba Amina zuwa lokacin kuka take yi sosai. Tausayin Abba da kuma tashin hankalin da ta ji na wai Mami na neman rayuwarsa ya sanya ta wannan kukan. Abban da ya zo don ya samu a rarrashe shi, sai shi ne ya koma rarrashin. Ta mike ta hado masa kayan shayi da abinci, ta yi mamakin yanda ya zage ya ci kuwa, tausayinsa kwarai ta ji, har ta kasa hakuri ƙarshe ta dube shi. "Toh yanzu Yaya hakanan za ka yi zaman rayuwa da ita? Nikam hankalina sam bai kwanta ba, shikenan ka haramtawa kanka cimar gidanka saboda Maryam?" Ya dan yi murmushin yaƙe bayan ya kora ruwan shayi mai dumi a cikinsa. "Amina kenan, wallahi ganinta ma bana son yi. " Takaici ya kama Baba Amina. "Toh Yaya ka yi aure mana." Ya ɗan yi jim sannan ya jinjina kai. "Tsoron matan nake Amina, ba zan iya auren kowa ba a yanzu." "Ba duka aka taru aka zama ɗaya ba Yaya, ni wallahi dama na jima ina yi maka sha'awar auren wata baiwar Allah, da ace za ka bani dama ni zan san yanda zan shawo maka kanta ta amince." Ya yi murmushi. "Wato dama kin dade kina so na yi auren kenan." Ta yi murmushin itama. "Eh toh, gaskiya kusan hakan ne. Tun da na soma gane wace ce ainahin Maryam na ji haka kawai ina son zamanka tare da wata bayan ita." Abba ya girgiza kai. "Mutum abin tsoro ne Amina. Kedai kawai Allah yasa mu dace." Ta amsa da amin tana mai kara tausayawa rayuwar Yayannata. Haka ya yi mata sallama ya tafi bai ko damu da sanin ko sunan wacce ta zaɓar masa ba. Kusan ma bai dauki lamarin da muhimmanci ba. Ita kuwa ta dauke shi da matukar girma, ta kuma dauki ɗamarar dagewa da addu'a har kafin ta tunkari ɗan uwan mahaifinsu Baffa Tukur da zancen, tana son ta ga tabbatuwar lamarin ko don samar da farin ciki ga yayanta da kuma ganin yanda Maryam za ta ƙara bayyana munanan ɗabi'unta kowa ya ankara da shi. Ai tunda har Raihana da kanta ta bude baki ta ce dama Abbanta ya kara aure, ta san cewa lamarin babba ne. *** Tafiya ta yi tafiya har aka kwashi watanni biyu, Humaira cikin ikon Allah ta samu juna biyu, wani irin tarairaya na musamman ta ke samu daga Fadeel, a wannan watanni Abba ya hana ta taka koda harabar gidansa da sunan ziyara, acewarsa ta yi hakuri da zuwa gidan zuwa wani lokaci. Ita kuwa zuwa lokacin ƙarshen damuwa ta shige shi domin so take yi ta ga Abbannata saboda ta sani tabbas yana cikin damuwa. Ta ji komai daga bakin Raihana. Ganin wannan ne yasa Abba amincewa da zuwanta, ranar ko da ya kasance na zuwannata bai fita kasuwa ba, zamansa ya yi a gida. Yana zaune a falonsa Tasleem ta shigo gaishe shi, ya mance rabon ma da ya ganta don har mantawa yake yi ta a gidan, ya bita da kallo sosai ta sha zumɓulelan hijabi tana ta kare cikinta wanda bai kai ga fitowa ba amma hakanan take tsarguwar kada Abban ya ankare da shi. Shi kuwa ramar da ta yi yake bi da ido. Ya amsa gaisuwarta a daƙile ya kauda kai. "Abba don Allah ina son ɗan wani abu zan siya kayan sanyawa na ciki." Ya ɗan yi jim, tabbas yanzun ya sani tana da hakki a kansa, idan bai mata ba yana tsoron ɓacin zamanin nan. Ya dan kara dubanta, sai ta ba shi tausayi. Yarinya ƙarama ta haɗu da zawarci saboda kishin banza da ta ɗorawa zuciyarta har ya kai ta ga marin uwar mijinta. Hannu ya sa a aljihu ya fiddo kudi ya ƙirga dubu goma ya miƙa mata. Ta yi mamaki sosai don ba ta ma zaci za ta samu kamar hakan ba. Ta yi godiya, har za ta tashi sai ya kira ta, dawowa ta yi ta zauna jiki a mace. Zuwa yanzu ta gaji da zuwa wajen Babandi sai dai ta rasa dalili idan har ya dauki waya ya kirata toh ko me take yi ba ta kammalawa tana rawar jiki za ta je wajensa. Nasiha mai ratsa jiki Abba ya yi mata game da rayuwa da kuma faɗa akan rashin alfanun zaman mace babu aure. Ya nuna mata hakan ba zai ƙare ta da komai ba, yanzu idan babu shi a duniyar wa za ta tambaya? Abba dai sosai ya yi mata faɗa akan ta tsoraci Allah a lamuranta, kada ta bari son duniya da abin da ke ciki ya rufe idanunta. Tasleem jikinta ya ƙara mutuwa, ita fa dama yanzu ta gane dama kyau ba ya kawowa mace miji mai arziki balle kuma surar jiki. Kawai ta gane kaddarar mutum ce komai dake faruwa, yanzu ta bar yiwa kanta hangen miji irin na Humaira don ta san ba za ta samu ba, ita babban abin da ke ramar da ita bai wuce cikin Babandi dake jikinta ba wanda ta ƙi ta zubar saboda tsananin tsoron abin da zai biyo baya tsakaninsu idan ta zubar. "Ƴar uwarki tana nan shigowa yau za ta kawomana ziyara. Ki sa Ladidi ta samar mata wani abin." "Abba wa?" Ya dube ta. "Humaira." Ta ji kwalla sun cicciko mata, ta sani Humaira ta zama hajiya, ko ba ta ganta ba ta san za a ganta cikin kwanciyar hankali da nutsuwa ba kamar ita ba da ta rasa hakan. Gatanan ba wan ba ƙanin, ƙarfi da yaji ta zama kwartuwar Boka. Kullum cikin aikata zina take yi babu ji babu gani. "Toh." Abin da ta firta kenan ta mike ta tafi.