YAKANAH!- Agogon ‘alarm’ da ke gefen makeken gadon ya buga karfe shidda dai-dai na safe, Dr. Hadizah wadda ke kwance a gadon doguwa ce ba can ba, irin tsayin nan gare ta mai tsari da ban sha’awa. Tana sanye cikin rigar barci mai santsi fara sol. Ta yi mika a hankali tare da koro addu’ar (Alhamdulillahil lazee ahyana, ba’ada ma amatana wa ilaihin nushour). Ta mika hannu side din da maigidanta ke kwance, wayam! Tayi hanzarin mikewa daga kwanciyar don a zatonta, ta makara. Daga can kitchen ta jiyo motsin mai aikinsu Goggo Alti tana karakaina da kwanuka. Tana shirin mikewa ta ji motsin maigidanta Sulayman a shower, don haka ta yi ajiyar zuciya mai sanyi, a kalla ko ta makara kadan ne. Ita ma ta fada bandakin don ta taimaka mishi wajen wanka. Suka fito kowane daure da towell, shi iya kugun shi ita iya cinyoyin ta. Jiki ne da ita lukui-lukui kamar atafa. Jiki ne da shi na MANYA, kuma kasaitattun maza, wadanda suka dama, suka kutsa cikin ilimummuka daban-daban. Yana da duhu, amma duhun mazan Marocco ne. Dogo ne sosai ma’abocin karfi da kyawun sura ta ko’ina. Idan baka san asalin shi ba, za ka yi tsammanin ya fito ne daga Sirreleone, amma a zahiri Bakatsine ne dan asalin garin Bakori. Wadda Bakorin ta bi sunan shi, ta boye Sulayman-Sulayman din, ake kiran shi Dr. Bakori. Ta bude wardrove ta dauko mishi bakaken Spanish-Suit mai hade da farin tie mai santsi. Ita kuma ta fiddo wata atamfa super shudiya mai ratsin rowan hoda da_ hasken – sararin samaniya, riga, zane da kallabin su, ta dora da farar rigar su ta likitoci. Tuni ta fito a Dr. Hadizarta. Tana tsuke mishi tie ya ja zankalelen dogon karan hancinta in appreciation din (cike da jin dadin) irin kulawar da take mishi. Yace “Allah ya bar min ke Dr. D.Z”. Ta ce “‘…Ya bar min kai nima, likitan zuciyata…..”.. Ta manna mishi kyakkyawar sumba a kirji, kasancewar ya kere ta a tsaho, ita iya kirjin shi ce. Ta dauko tashi rigar likitocin ta zagaya ta bayan shi ta rufa mishi, ya zura hannun shi kana a hankali ya janyo ta ya rungume ta. Sun dau tsawon lokaci a hakan, suna sakin ajiyar zuciya mai sanyi cike da matsananciyar kauna wadda biro ba zai iya rubutawa ba, kamin su saki juna ba don sun so ba, sai don tunanin dimbin al’umma masu larura da suka yi sammako suke jiran su. Sai da suka gama kammalawa tsaf sannan suka fito, tana rike da gilashin idonta a hannu, ya yin da shi yake rike da jakarta da brief case din shi. Kai tsaye dakin yaransu suka nufa, inda suka tarar tuni Alti ta shirya su tsaf, kasancewar yau garin an tashi da lullumin sanyi mai tsanani ya sanya ta sanya musu rigar sanyi mai kauri a ciki, ta sanya musu fararen socks ta rufe musu kafafu cikin farin cambas. Yaran su biyu ne mace da namiji, namijin dan kimanin shekaru hudu, macen ‘yar kimanin shekaru biyu da kadan. Dole in ka gansu sai ka sake marmarin kallon su, sun kuma baka sha’awa. Munib sak Babansa, yayin da Muniba komi nata na Dr, Hadiza ne. To ba Mamin ba, ba Daddyn ba, kowanne ji yake da kyau tamkar shi ya yi kansa. Akwai shakuwa, fahimta da soyayya mai yawa a tsakanin wannan family. Hadiza ta rage tsawo ta russuna ta rungume Muniba, “Gud morning my dear……. “Morning Mummyy….”. Munib ma ya ce “Gud morning Daddy…..”. Ya amsa da “Morning my Munib, an tashi lafiya?” Su dukka suka nufi tebir domin yin kalaci. Goggo Allti ta fito daga kitchen za ta wuce bangaren ta, daga Hadiza har Sulayman suka gaishe ta, kamin ita ta gaida su. Wannan dabi’arsu ce da ke karawa dattijuwar jin dadin zama dasu, saboda yadda suke ba ta girma kamar ba a karkashin su take ci ba. Hakan ne yake kara mata himmar kula musu da yaransu saboda Allah. Hadiza ta bude ma’adanan abincin ta soma serbing kowannen su da abinda yake so. Sinasir ne da miyar ganye, sai farfesun kayan ciki, sai kuma soyayyen dankali da kwai domin su Munib da bazasu iya cin mai nauyin ba. Ga al’adarsu sun fi cin abinci mai nauyi da safe, don ba za su kara ci ba sai dare in sun dawo aiki, sai ‘yan ciye-ciye da ba a rasa ba a office. Hankalin Dr. Sulaiman yana kan ‘ya’yan shi, sai da ya tabbatar sun koshi sannan ya ci nasa. Zuwa bakwai da rabi sun gama komai sun fito, suka yiwa Goggo Alti sallama suka wuce rumfar adana motocin su. Akwai motoci har guda uku, daya ta Sulaiman, daya ta Hadiza, daya ta amfanin gida. Sai da suka aje yaran a makarantar su (Maitama Sule) da ke dab da asibitin da suke, wato (AKTH) sannan suka karasa cikin asibiti, kowanne ya nufi bangaren sa. Dr. Sulaiman-Sulaiman Bakori shi ne consultant na (cardiology), yayin da Dr. Hadiza Ja’afar Mai-Yadi take likitar mata wato (gynaec) a labour ward take. Sai da ya fara sauke ta sannan ya wuce ofishinsa, ya soma attending dimbin cases din da ke gabansa. Karfe sha biyu na rana ya zame ya je ya debo yara ya kai ma Goggo Allti, sannan ya dawo. Wannan shi ne tsarin rayuwar su a kullum. AK S hekarun su biyar kenan da aure, amma har zuwa inda yau ke motsi, babu abinda ya canza na daga soyayyar da suke yiwa juna, sai ma abin da ya karu. Hadiza dalibar shi ce irin yaran likitocin nan da ake koyarwa a (teaching hospital). Ya fahimce ta yarinya ce mai matukar kwazo a tsakanin tsararrakin ta. Wani abin mamaki da ya fara bincike a kanta ‘yar talakawa ce likis, amma iyayenta sun tsaya tsayin daka wajen daukar nauyin karatun ta, duk da tsadar shi kuwa, da dukkan iyawarsu. Soyayya ce mai tsabta irin ta wadanda suka wadata da ilimi suka gudanar kamin aure. Ga Hadizah ba karamar sa’a ba ce, kuma ba karamin abin alfahari bane samun mutun kaman Sulayman (as a husband). To haka shi ma. Hadiza ta tara duk wasu kualities da yake nema ga diya mace, ga dai kyau ga kyan hali, ga addini da kyakkyawar zuciya, sannan uwa uba ta samu ingantacciyar tarbiyya daga_ iyayen kwarai. Iyayenta suna nan a_ unguwar Karkasara dake cikin birnin Kano, sana’ar mahaifinta shi ne yadiddika yake sayarwa, yana da shago a nan kantin Kwari. Hadiza ita ce ta biyu a cikin ‘ya’yan gidansu, akwai Yayanta Mukhtar wanda ke aiki da (Zenith Bank) a Kaduna, kusan da tallafin shi ne Hadiza ta samu ta kammala karatun ta. Duk da haka shi ma mahaifinsu a tsaye yake a kan karatun su, don yaga amfanin da karatun yayiwa Mukhtar. Sai kanwar ta Fati, budurwa ce ‘yar ki manin shekaru sha bakwai, a bana ne ta kammala karatun sakandire. Sai Hamza da Yusuf, da dan autan su Abdulyassar. Duk cikin kannenta Hadiza ta fi son Fati, wata irin yarinya ce mai sanyin hali, sanyin kyau da sassanyar zuciya. Akwai wata irin shakuwa ta musamman tsakanin Hadiza da ‘yar uwarta Fati. Jininsu ya hadu sosai ta yadda Hadiza ba ta iya shawara da kowa kan al’amuranta kamar Fati saboda hankalin ta. Fati yarinya ce mai tsananin son addini da nutsuwa, ba ta da rawar kai ko kadan irin na ‘yammatan zamanin nan, komi nata cikin hankali da nutsuwa yake. Ita da Hadiza kamar an tsaga kara, sai dai Hadiza fara ce sol, yayin da Fati ta kasance wankan tarwada. Amma hatta yanayin tafiyar su da murmushin su iri daya ne. Ss ulayman Bakori, mutumin — garin Bakori ne ta jihar Katsina, daga kallo na farko mawuyaci ne ka bambance daga kabilar da ya fito, wani irin mutum ma’abocin cikar zati da kamala da duk wani nau’in daidaito na rayuwa, ga dimbin ilimi a cikin fannonin kiwon lafiya daban-daban. Ya ci sunan mahaifinshi ne don haka a gidan su ake kiran shi mai sunan Malam. Mahaifin shi Malam Sulaiman, Malami ne mai karantarwa, yana baiwa magidanta anguwar su karatun buzu. Duk wani da ya kwana ya tashi a garin Bakori ya san Malam Sulaiman Mai-Gafaka. Mutum ne da al’ummarsa ke matukar ganin girman sa, kuma ya yi fice a garin Bakori baki daya saboda ilimin da Allah ya ba shi, kowa yana daraja shi. Shi ne da na biyu a gidansu, yayar shi Jummai ta rasu wajen haihuwar fari, sai kannen shi Ramatu, Saude da Ruma, duk suna gidan aure. Sai Khalid wanda ke karatun sakandire a halin yanzu. Sulaiman ya yi dukkan karatun shi ne da taimakon gwamnati da mahaifiyar shi Inna Halima, wadda duk lokacin da hidimar karatun ta tashi take fitar da kadararta ta siyar ta yi masa. In dan ta Malam ne sakandire ma kawai ta isa. Burinsa Sulayman ya zauna a gida ya tallafa mishi kasuwancin shi na fata, ya yi aure ya haifa mishi jikoki shi kuma zai yi masa komai. Amma Sulaiman ya ki, ya dage ga son cimma burinsa na son zama likita. Ba abin da yake so a rayuwar shi irin yau ace ya zama likita yana yiwa mutane allura. Irin yaran nan ne gifted tun suna kanana, wato ‘yan baiwa. Wata irin kwakwalwa gare shi da ba duk mutane Allah yake baiwa ba, duk inda yayi karatu malaman shi sai sun san shi, sun kuma ja shi a jiki, sun so shi saboda hazakar shi. Ya yi gaba dayan karatun shi daga jami’ar Najeriya (NSUKKA). Bayan ya kammala MBBS din shi ya yi nasarar samun_ scholarship zuwa jami’ar (Manchester) inda ya yi specializing a kan zuciya da duk abin da ya shafe ta. Bayan kammalawar shi da dawowar shi ya soma aiki da federal, hakan ne ya sa ake yawan canza mishi wajen aiki. Ya fara ne da aiki a babbn asibitin koyarwa na Ibadan, daga baya suka mai da shi ABU Teaching Hospital. Nan din bai dade ba suka dawo da shi nan AKTH na Kano, inda Allah ya hada shi da Hadizah. Haduwar su haduwa ce _ special kuma haduwa ba ta dadi ba. Yana tare da patient da ya yiwa aiki satin da ya wuce, Hadizah Ja’afar, da wasu abokan karatun ta suka shigo domin daukar lacca. Ko kallon su bai yi ba, balle ya tantance kamannin su, kasancewar Allah bai dora mishi lalurar yiwa mata kallon kurilla ba. Tsakanin shi da kowacce diya mace, kallo daya ne, da kau da kai. Suka samu_ kujeru. suka zauna, kowacce da jotter din ta da biro a hannu. Yana ta yi musu bayani cikin lafiyayyen turancinshi na _ Birtaniya mara surki, wani zubin ya yiwa mara lafiyar tambaya ta ba shi amsa. Wata amsa da patient din ta bayar ta sanya su murmushi dukkanin su (ban da Hadiza), cikin kalaman ta za ka fahimci kwakwalwarta ta tabu sakamakon bacin zuciya da damuwa. Ta ce, “Likita nifa ‘yar sarauta ce ba mara lafiya ba!”. (Wannan ne ya sanya su yin murmushi). Ya ce, “Wacce sarauta gare ki don mu fara girmama ki?” Gaba daya daliban suka yi dariya don yadda yake biye ma shirmen matar dole ya baka dariya. Ta ce, “Sarautar Kano gare ni”. Yace, “Wacce ke nan?” Ta ce, “Nice ‘yar ruwatan Kano”. Gaba daya suka yi murmushi, wannan karon ma ban da Hadizah, wadda a lokacin hankalinta baya tare dasu, yana ga halin da ta baro Mamansu a ciki na rashin lafiya mai tsanani. Ba zato Dr. Bakori ya jefo tambaya, “Mene ne delusion?” Ya kuma nuna Hadiza da ya lura hankalinta ba ya tare da shi matsayin wadda za ta amsa mishi tambayar shi. Ya yi mata magana ya kai sau uku ba ta san yana yi ba. Hadiza ta damu da Mamanta sosai, kasancewar ta jarumar Uwa mai hidimtawa rayuwar su, tun daga yarinta har a girman su. Yaya, (Sa’adatu), ba ta huta da dawainiyar su ba. Don haka jin ciwon ta suke tamkar a gangar jikin su. Duka kawayen ta babu wadda ta zungure ta, don sun san da ta ji za ta ba da amsa a yabe ta kamar yadda manyan likitoci suke yabon ta a kullum saboda kokarin ta. Ya buga tebir din gaban shi da karfi har ta razana, ya nuna mata hanyar waje ya ce, ‘You can go out….. in kin gama tunanin kya dawo”. Ta mike sumi-sumi ta fita, murna gun su Hafsat kamar su yi yaya, yau Allah ya nuna musu likitan da ya yi maganin ‘yar gaban goshin likitoci. Ya yi (referring patient) din zuwa psychiatric, su kuma ya sallame su. Ya koma gida a wannan ranar, bayan ya gama duk abubuwan da ya saba na al’adar rayuwar shi kamin ya kwanta, kamar shan fruit da edcercise saboda shi da daddare yake edcercise din sa kasancewar da safe ba shi da lokaci. Amma abin mamaki ya kasa runtsa idonsa, tunanin fuskar dalibar da ya kora a yau ke gilma mishi, ya hana shi sakat, ya hana shi sukuni, ya yi duk kokarin da zai yi don ya samu barci amma hakan ya faskara. Ya ko kasa runtsa idon sa, wani bakon al’amari ne mai takura zuciya da bai taba tsintar kansa a ciki ba. Hadiza ba wata muguwar kyakkyawa ba ce cancan, tana da kyau dai-dai nata, sai dai kuma yarinya ce mai aji na karshe. Fuskarta zagayayya mai dauke da dara-daran fararen idanu masu sheki da walainiya, hancinta kamar an sanya ruler an ja shi an daidaita shi a kan (obal -shaped) fuskarta. Bakinta dan karami kamar cokali baya shige ba. A kan tsinin hancinta tawwadar Allah ce da aka haife ta da ita, fara ce sol! Irin farin nan da wadataccen ilimin boko ke taimakawa wajen zahharar sa. Bai taba ganin yarinyar da (lab-coat) ta yi ma kyau kamar Hadizah ba. Ba Sai ya tsaya wahalar da kanshi wajen tunanin abin da ke faruwa da shi ba, ya tabbata son Hadiza ne ke ratsa kowanne sako a jikinsa. Abin haushin ko sunan ta bai sani ba, zuciya ta kwashe shi ya yi abin da ya zo ya dame shi. Bai taba tsintar kansa a kwatankwacin irin wannan yanayin ba, a kan diya mace. Sai dai shi a ce ana son sa yana hura hanci, kada hakan ya janyo raini, baya fatan hakan ya kasance sakayya ce Allah ya yiwa dimbin matan da ke binsa agindi-agindi don ya so su yana yakice su. Tare da yi musu wulakancin da ko a hanya suka ganshi bazasu yi fatan ace sun san shi ba. Ya fahimci dalibar (obstetric and gynaecology) ce, daga (ID Card) din ta. Yadda ya ga rana haka ya ga dare, ko na second daya bai runtsa ba. So da kaunar student (daliba) Hadiza na narkar mai da zuciya. Abin kamar sihiri, daga ranar bai kara ganin Hadiza ba, bai kuma san ya zai yi ya tambaya ba, tunda ko sunanta bai sani ba. A matsayinsa na babban likita, mai juya sauran likitocin bangaren su, ba karamin zub da kima bane a ji shi yana tambayar wata yarinya cikin masu daukar darasi a wurin su. Duk da haka bai fidda rai ba, yana da yakinin watarana Allah zai sake hada shi da yarinyar ko da a mafarki ne. Ita kuwa Hadiza ba ta dawo TH ba sai bayan sati uku, tana gida tana Jinyar Maman su da suke kira Yaya, da ke fama da ciwon hanta. Tana ganin likita a Murtala, har suka kwantar da ita sati guda. Kawarta Surayya ke daukar musu Jacca tana kuma sanar da ita duk abin da ke faruwa ta waya. Ranar monday Maman su ta ji sauki sosai, don haka ta shirya ta dawo. Ba zato babu tsammanin shi, yana ganawa da wata patient din suka shigo ita da Surayyah, ya zare gilashin idonsa a hankali, ya saki wata sassanyar ajiyar zuciya irin ta wanda ke neman abu, ya wahala ya dade, kamin ya samu. Duk hankalin sa da attention din sa sai ya koma kanta, ya manta abin da ke gabansa, ya samu kansa da rudewa. Abin da bai taba yi ba a kan diya mace, akwai wani sassanyan kallo cikin kwayar idon Hadizah, da ba duk mata Allah ya mallakawa ba. Suka gaishe shi cike da girmamawa, sannan suka samu kujeru suka zauna. Hadiza dai a darare take, ko kanta ba ta dago ba. Daga gefe-gefen idon ta take satar kallon likitan da ya hargitsa mata tunani ‘yan kwanakin nan. Tunda ya kore ta ba ta kara samun nutsuwar zuciyarta ba, har zuwa yau da ta sake tozali da shi a karo na biyu. Ta tambayi kanta, shin ko mutane nawa ne a duniya irin Dr. Bakori? Yana da wasu ilhamomi na musamman a tare da shi da ba ta taba ganin su a da namiji ba, ko yadda yake duban mutane daban ne da na sauran likitocin da ta sani. Tsarin maganar sa cikin seriousness shi ne babban abinda ke burge ta da shi, ga kamun kai da sanin mutuncin kai, hadi da rashin son wasa ta ko’ina. Dr. Sulayman Bakori, ya shiga cikin rukunin wasu mutane da take ganin matukar kima da mutuncin su, sannan kuma ya bi ya manne a zuciyarta, ta yadda dai-dai da minti daya ta kasa manta shi cikin satittikan da ta yi tana jinyar Mamanta. A gurguje ya basu laccar ya kuma sallami mara lafiyar da suke tare da ita. Suka mike da nufin su tafi, baya fatan wannan damar da kubuce masa, don haka bai yi kwauron baki ba, ya yi ta maza (in ji mata) ya ce da Hadiza cikin wata irin lallausar murya da ya kasa yarda cewa tashi ce. “Wato fushi kika yi? Kika daina halartar karatun ki sabida na kore ki a kan kin yi min laifi?” Ta yi ajiyar zuciya a hankali ba tare da ta juyo ba, ta ce, “A haba Doctor! Wane ni in yi fushi? Mum dina aka kwantar a_ hospital kuma ni nake jinyar ta sai jiya aka sallame mu”. Ya nuna tausayi tsantsa a_ kan kyakkyawar fuskarsa, ya ce, “Ayya! Ta juyo ta yi mishi murmushi, suka yi ido hudu da dan Inna Halima, wani chemistry yayi aiki cikin ‘yan dakikai, ya kimsa wani al’amari mai GIRMA a zuciyoyinsu mai wuyar bayyanawa. Gwiwoyinta suka yi sanyi, zuciyarta ta karye, duk wata soyayya da Allah ya halitta a zuciyarta ta hadu ta tattare waje daya. To haka shi ma. Jikin shi ya ba shi wannan ita ce matar auren shi, wadda za ta samar mishi da ‘ya’yan da zai yi alfaharin fitowar su daga tsatson ta. Ya ce “A bani address zan zo in duba Mamar mu”. Daga ita har Surayyah sai suka yi mutuwar tsaye, domin abune da ko da wasa basu taba kawowa ba. Kowa ya san shi da halin ko in kula da yake nunawa a kan mata, wanda ke burge kowa. Don haka sun sha mamaki. Ita Hadiza ta kasa magana, sai Surayyah ce ta rairayo mishi adireshin Hadiza. Ya ce, “Idan na zo wa zan ce?” Ta ce, “Hadizah!””. Ya ce, “Hadizahh, am I welcome?” Ta yi murmushi ta ce, ” You are welcome!!”. Tun daga ranar kakkarfar soyayya ta kullu, kullum suna tare, a gida ne ko a ofis. Abin ya soma bayyana ga abokan aikin shi da abokan karatun ta, da manyan likitoci mata da ke yi mishi asirtacciyar soyayya. Wannan ya janyo ma Hadiza hassada karara a wajen mafi yawan abokan karatun ta, to ita ma sai ta share su, saboda ta san Surayyah kadai ke kaunar ta saboda Allah. A uren su, wani abu ne da ya bar dimbin tarihi a asibitin Malam Aminu Kano, domin mafi akasarin likitocin cardiology kabilu da Hausawa sun halarta. Ba a taba ganin daurin auren da ya tara ‘yan boko tsantsa, likitoci ziryan a unguwar Karkasara irin na Hadiza ba. Suka tare a gidan Sulaiman da ke cikin asibiti, cikin wata irin soyayya mai wuyar fassarawa. Aure ne auren soyayya mai tsabta, wanda babu ha’inci, yaudara ko karya a cikin ta. Ya sha mamakin samun Hadizah a cikakkiyar mace (birgin) musamman in aka yi la’akari da matakin karatun ta. Ba gaskiya bane zargin da ake yiwa ‘yammatan (medicine), kawai dan iska dan iskan kansa ne, amma da yawa abin da ya kai su shi ne a gabansu. Cikin shekaru uku da auren su ta yi mishi tukuicin kauna da Munib da Muniba, wannan ya kara sayowa Hadiza matsiyaciyar kauna a zuciyar Sulaiman. Daga baya ne da ya kammala ginin da yake yi a Janbulo suka koma, daga nan ne likitocin aka rufe bakin mahaifa ruf, aka _ fuskanci cigaba. Hadiza ta kare karatun ta cikin nasara, da taimakon mijinta. Ita ce (oberall) a year din su. Da gudu aka rike ta a (labour room) wato dakin haihuwa. Sannan ba ta tsaya a nan ba, ta ci gaba da halartar kwasai-kwasai a akan bangaren ta. Har kawo matakin da ta ke kai a yau, na cikakkiyar likitar mata. 2K 2K OK Karfe hudu na yammacin ranar litinin aiki ya tsagaitawa Dr. Hadiza, babu yawan marasa lafiya, don haka ta soma hada ‘yan komatsanta don barin asibitin. Tun safe yau kanta ke damun ta da ciwo, gida kawai take so ta Je ta huta. Amma dole sai ta fara ganin Sulaiman tukunna, akwai wasu kudi da take son karba a wajen sa za ta biya ta kai ma Fati tayi (registration). Ta bude motar ta kenan ta zuba shirgin hannun ta, wata Nurse ta karaso da gudu tana haki tana kiran ta, “Dr. Hadizah!” Ta juya tana kallon ta har ta karaso. ” leeees Don Allah ki taimaka, wata ce aka kawo yanzun nan da alama ba za ta iya haihuwa da kanta ba, sai bleeding (zubar jini) take”. Ta kama kanta dake sarawa ta ce, “Lokacin tashina ya yi, yanzu Dr. Surayyah za ta Zo……… ” Nurse din ta katse ta, “Ki ceci rai kamar yadda kika saba, sakayyar ki na wajen Allah! Daga matar har Babyn suna cikin hadari, ga shi babu likita ko daya duk sun shiga meeting. Sannan Surayyah babu wanda ya san lokacin da za ta karaso”. Hadizah mai sanyin zuciya, matar ta kashe mata gwiwa da tausasan kalamanta. A take ta manta da ciwon kanta, ta rufe motar ta koma gun mai haihuwa. Wannan halayyar ta ce da ta sha banbam da ta sauran likitocin labour room da kowa ke kuka dasu. Zuciyarta mai laushi ce, shi ya sa daga likitocin har Nurses zuwa labourers ke son ta, suke jin dadin aiki da ita. Hadiza is simple, komi nata a saukake yake. Da gaske ne matar ba za ta iya haihuwa ba. Ta kai matuka wajen galabaita, ta soma ba ta dukkan taimakon da ya dace. Tana cikin aikin Dr. Surayyah ta iso, suka tsaya a kan matar nan. Cikin dan lokaci sun yi nasarar fitar da jaririn amma ba rai. To alhamdulillahi an samu uwar. Tana zare safar han nunta ta ce da Surayyah, “Ko da ban zo gobe ba, don Allah ki kular min da matar nan, haka kawai nake jin tausayin ta, dube ta yarinya karama, ga dukkan alamu ba ta isa auren ba suka yi mata. Allah ne ya taimake ta sun zo asibiti da wuri, da babu mamaki BBF ya same ta”. Surayyah ta ce, “Matsalar mutanen karkararmu kenan, ban san yaushe za su hankalta ba. A kullum fadakarwa ake a radio da talabijin, amma kamar ana kara zuga su. Allah ya kyauta. Balle ma me zai hana ki zuwa idan da rai da lafiya?” Ta girgiza kai ta yi dan tsaki, ta ce, “Bana jin dadi ne”. Surayyah ta ce, “To Allah ya kawo sauki, a shafa min kan Munib”: Da haka suka yi sallama ta fita. Da yake yau kowa a motar shi ya zo, wato itada Sulaiman, kasancewar lokutan ayyukan nasu sun banbanta. Akwai tazara sosai daga inda ta yi parking zuwa cardiology. Tana tukin tana duba agogon ‘gucci’ da ke daure a damtsen hannun ta na hagu. Yau Dr. Sulaiman aikin kwana gare shi, kudin Fati sun tsaya mata a rai, ga shi jakarta (is empty). Sannan is too late ta je banki ta fitar da kudi (lokacin ba ATM). Ba al’adar ta ba ce tambayar Sulaiman kudi ba, saboda duk wata yana cika mata account ba tare da la’akari da albashin ta ba. Ita da kudin ta sai dai ta yiwa iyayen ta da ‘yan uwanta hidima, amma duk wani nauyin rayuwar ta Sulaiman ya dauke shi. Sau tari, ta kan ji kawayen ta da ba suyi aure ba irin su Dr. Surayyah, na tattaunawa a kan abinda ya hana su yin aure, su kan ce da ka yi aure shi ke nan ka shiga matsalar da namiji (wulakanci, rashin tsayawa ga mace daya, rowa da sauran su). To ita dai yau shekaru biyar cif, ba ta ga ta inda nata da namijin ya kuskuro ta ba; Matakin iliminsa bai sa shi ya zamo cikin kowanne irin aikin ashsha ba. Bai sa shi ya zamo mai tauye mata hakki ba, bai sa shi ya zamo mai girman kai a gare ta ba. Kullum tambayar shi, “No problem Haddizah (babu matsala Hadiza)?” Ta kan tambayi kanta, yadda neman mata ya zamo ado ga akasarin mazan wannan zamanin, masu matakin rayuwa irin nashi, mai ya sa ban da Sulaiman? Duk da kasancewar shi mutun mai tsananin bukatar diya mace. Ta yadda duk juriyar ta wani lokacin har ta kan nuna gazawar ta. Ta taba tambayar shi cewar, “Don me ba zai kara aure ba?” Sai ya kankame ta. Ya ce, “Haddizah you are okey for me, in dai ba za ki yi min rowar, ni’imtaccen jikin ki ba……… ” Ta ce, “Doctor gani nake ina kwarar ka, you seem not o.k…….. ” A hanzarce ya ce, “Ni na gaya miki?” Ta girgiza kai. Ya ce, “To kar ki kara yi min wannan zancen, silly girl kawai”. Ta yi murmushi, da tunanin ta ya zo nan. Dai-dai lokacin da ta iso cardiology, ta yi parking a inda aka tanada don adana motoci ta fito rike da jakarta. A nutse ta karasa (male ward) inda office din Sulaiman yake, ta tura kofar bayan ta murda tare da sallama. Da alama aiki ya kacame masa, yana ta rubutu cikin file-file dake gabansa, ya daga kai yana duban ta duba na so da kauna, kuma na nutsuwa kamar yana son karanto ainihin damuwar da ke fuskarta. Ya mike ya baro kujerar sa ya zauna a masangalin kujerar da ta zauna, ya zare mata gilashi, ya ce, “Ya ya ne Dr. Hadiza, you look edhausted!” (Da alama kin gaji likis). Ta lumshe zara-zaran gashin idonta ta ce, “Migraine ke damuna (ciwon kan barin kai guda)”. Ya kai lallausar tafin hannun shi goshinta, har sai da ta ji wani shock kamar yau ya fara taba ta. Ta yi saurin ture hannun sa, za ta yi magan Dr. AbdulJahi ya turo kofar ya shigo, da sauri ya koma yana “edcuse me plzzz……. {” Duk suka yi murmushi. Ya ce, “Kin sha magani?” Ta girgiza kai, “Ina so in je Karkasara ne”. “Amma lafiya na gaba da komai ko?’ Ta ce, “Zan biya emergency in amsa kamin in wuce”. Ya kai hannu cikin rigarta wai zai ji temperature na jikin, ta yi saurin rike hannun ta ce, “Haba Sulaiman…….” Shi ma ya ce, “Haba Hadizahbh….! Ni kadai zan kwana fa, babu dumin jikin ki Hadizah…..?” Ta yi murmushi ta rusunar da kwayar idon ta cikin jin kunyar furucinsa, domin dai ita mace ce mai tsananin kamun kai a gaban mijinta da jin kunyar sa, kai ka ce basu haihu tare ba. Yace “Ke kwanta in duba ki, ban yarda dake ba, har yanzu ba ki cire wannan loop din ba”. Ya soma laluben ta. Ta rike hannun shi ta ce, “Wallahi na cire”. Ya ce, “To ko ke fa? “Ya’ya nake so Haddizah, ki yi ta cika min gida dasu. Bani da harshen da zai iya bayyana hakikanin son da nake miki, you are my life Hadizah….., kada Allah ya rabamu……. ” Ya shiga nuna mata son, practically, (a aikace) irin yadda bai taba yi ba. Murmushi tayi. Ta ce, “Sulaiman naka son ka sani, amma baka san nawa ba. Sannan ban san yaya zan yi in fassara ba. All I can say (abinda zan iya cewa shine) ina son ka Sulaiman son da nake yiwa raina……’ Ya kai hannu ya toshe mata baki, wayar shi ta yi kara ya juya yana amsa call din amma bai saki hannunta ba. Ya gama ya kashe ya maida aljihun shi, yana yi mata wani sassanyan kallo ya ce, “Ki yi min alfarma ki taya ni kwana ko hira ce ki dinga yi min ina aikin”. Ta ce, “Ka yi min afuwa Baban Munib, Fati zan kai ma kudi za ta yi registration gobe”. Da sauri Ya ce, “Registration din Fati ya fini?” Ta bude baki ta rufe da hannun ta, ta kasa cewa komai. Ya tsare ta da sedy eyes din sa, masu kassara ta, ba shiri ta sunkuyar da kai, don ba ta iya jure kallon idanuwan nan na Sulaiman din ta, masu rikirkita kowacce lafiyayyar diya mace, balle ita matarshi ta sunnah, data fi kowa sanin sirrinsa na zahiri da badini. A raunane ta ce, “Ban so ka yi min wannan fahimtar ba”. “Sai wacce kike so in miki?” “Irin wadda ka saba, understandable (ta fahimta)”. Ya yi murmushi ya mike daga kujerar ya koma mazaunin shi, duk ya shafa mata mayataccen kamshinsa na _ turaren ‘Chris Adams’. Nutsuwar matarshi da haibarta na burge shi, magana take cikin nutsuwa da haiba, kamar ba daga bakinta furucin ke fitowa ba, dauke da matsananciyar kauna a cikin kwayar idanun ta. Son ta da kaunar ta na kara kwarara a zuciyarsa, ya rasa inda zai sa kansa. Ya kama kanshi da hannuwan shi biyu. Ya ce, “Hadiza bana so ki tafi ne, sai in ji ni lonely kamar maraya…….. !” Ta ce, “Alfarma za ka yi min Sulaiman, muna tare muddin rayuwar mu”. Ya mika mata hannu ta kama, ta isa gare shi. Ya miko mata kumatun shi yace, “Kiss me plzzzz……772”. Ta ji kunya sosai, ta boye kanta a kafadun shi, ita ba ta iya wannan keke-da-keken ba. Ta ce, “Kudin da zan kai mata za ka bani Su laiman, ba kudi a waje na”. Ji yake in zai iya ba ta ranshi, to zai ba ta. Balle duniyar da abin da ke cikinta. Bai tambaye ta me za ta yi dasu ba, ko adadin da take so, ya kwaso duk abin da ke cikin aljihun shi ya zuba a jakar ta. Allah sarki! Kamar ba za su rabu ba, a lokacin har duhun dare ya shigo, likitoci uku ne da ke karkashin sa suka kwankwasa suka turo kofar suka shigo. Dole Hadiza ta dau jakarta da lab-coat hadi da gilashinta ta fita, yana kara jaddada mata ta yi tuki da kula. Dan banzan go slow ne ya tare ta a titi, ba ta isa gidansu ba sai tara da rabi, Maman su da suke kira Yaya, tana zaune a tsakar gida da rediyo a hannun ta tana sauraron Jakar Magori. Autan su Abdulyassar yana gefe yana hada motar kara. Yaya Babar su Hadiza ba wata tsohuwa ba ce cancan, don irin auren wurin nan aka yi mata, shekarun ta arba’in kenan. Hadiza ta yi sallama Yaya ta amsa, Abdulyassar ya watsar da _ kayan wasan shi da gudun shi ya kwaso ya rungume ‘yar uwar shi, kasancewar ta mai jan su a jiki tare da nuna musu kauna. Yana tambayar ta ina Munib? Daga can dakinta na ‘yammatanci, wanda a yanzu ya zan mallakin Fati, sautin Abdurrahaman Sudais ke tashi a hankali cikin suratul Al-Imran, wannan ya tabbatar mata Hafiza Fati Ja‘afar na gida. Ta samu gefen Yaya ta zauna, Yaya ta mike daga kwanciyar da ta yi bisa tabarma. Kai da ganin kyakkyawar fuskarta ka san ta ji dadin ganin diyar tata, ta ce, “Da daddaren nan Hadiza?’ Ta ce, “Wallahi Yaya, Dr. ne ya tare ni, na kawo ma Fati kudin ne”. Ta ce, “Amma kin kyauta, don da ta yi ma Yayan ku maganar ta waya ya ce ba zai samu zuwa Kano wannan satin ba, ga shi baban ku kwanan nan kasuwar ta ja baya, kuma ta ce daga wannan satin za a rufe”. Ta ce, “Baba bai dawo bane?” Yaya ta ce, “Ya dawo tun yamma, ya tafi dubiyar dan gidan Malam Abdu ne babur ya buge shi dazu”. Ta ce, “Allah ya sauwake, Fati na ciki ko”. Yaya ta ce, “Yanzu ta gama cin abinci ta shige ciki tana rehearsal, jibi za su yi musabakar jiha kuma ita za ta wakilci jihar Kano, kin san Fati ba daga nan ba”. Cikin alfahari da kanwar tata a zuciyarta, Hadiza ta tura kofar dakin cikin sallama, Fati ta diro daga gado ta rungume ‘yar uwarta tana yi mata oyoyo. Hadiza ta dubi Fati sama da kasa, ta zama cikakkiyar budurwa sosai. Ta kama baki “Fati girma haka?” Fati ta yi murmushi, kumatunta duka suka lotsa gwanin sha’awa, wushiryarta ta fito siririya da ita. Hadiza ta ce, “Wane course aka samu?” Ta ce, “Course din da na nema ne (Islamic Studies)”. Ta ce, “Masha Allah, da an je kuma sai a Samo saurayi, irin wannan girma haka Fati?” Ta ji kunya ta boye fuskarta cikin tafukanta, ta ce, “Ai hijabi zan ke zumbulawa irin mai hannun nan, kada ace ana so na”. Hadiza ta ce me za ta yi ba dariya ba, duk girman Fati baka raba ta da wauta. Ta kirgo kudi a jakarta naira dubu ishirin ta ba ta, Fati ta yi godiya ta ce, “Allah Yaya Hadiza kwana biyu ba’a kawo su Munib ba”. Ta ce, “Makaranta ta boye su, amma da anyi hutu suna nan tafe insha-Allah”. Sai sannan ne ta ga hakoran Fati. Ta ce, “Ashe kuma musabaka za a yi Fati ba labari? To Allah Ya ba da sa’a”. Ta yi murmushi ta ce, “Ameen”, Tana shirin fita Baban su na shigowa, ya ce, “A’ah, manyan likitoci ne yau a gidan namu? Ina matas da abokin?” Ta yi murmushi ta tsuguna har kasa ta gaida tsohon ta, ta ce, “Suna nan lafiya basu samu hutu bane, da sun samu za su ZO”. Yace, “Kinga kafar nan tawa kwanan nan bana jin dadin ta, har na gaji da hadiyar magani”. Ta ce, “Wane magani ne Baba? Likita ne ya rubuta?” Ya ce, “A‘a, maganin ciwon kashi ne kawai nake saya a wajen masu talla”. Ta kama baki, “Baba irin wadannan magungunan ba masu kyau bane, yawanci ma sun yi edpiry don Allah ka daina sha. Yanzu bari in rubuta maganin Fati ko Hamza su je su siyo”. Yace, “To na gode”. Ta baro Karkasara karfe goma daidai na dare, dauke da tazbihi a bakinta domin ba abu ne da ta ke so ko ta saba ba, wato (night dribing) tukin dare. Ta biyo ta titin Court Road ta hawo titin Gandu, ta yi kwana ta hau titin B.U.K Road. Ta iso Kabuga ta dau titin New-site wanda zai sadata da Janbulo. Babu wadatar motoci a titin. Daga gefen ta wayarta ta yi kara, sunan Sweetypie ya soma yawo a screen din. Ta yi murmushi ta mika hannun damanta ta dauka, ta rike sitiyari da hannun hagu cikin sanyin sauti ya ce, “Ya ya? Hope for now kina gida?” Ta yi ajiyar zuciya cikin karyayyar murya ta ce, “Na kusa dai, ina kan Iya abin da ya ji ke nan sai wata irin kara da ta fi kama da fashewar taya, ya yi kira “Hello!…..Hello….Hadizah!” Amma ba amsa. Motar ta hantsila ta shige karkashin wata trailer da ke cike da buhunhunan abinci, duk da kokarin da direban ya yi wajen kauce mata hakan bai samu ba, motocin da ke gabansu da bayan su duk suka yi birki cikin salati, tsirarun mutanen da ke gefen titi suka runtumo don kawo agaji. T a hanyar katin shaida (ID Card) jami’an tsaro suka gano ko wace ce Hadiza. Don haka ba su sha wahalar samun nombar wayar mijinta ba, wanda ke can cikin gigicewa. Nan asibitin aka taho da ita cikin jinni, rai a hannun Allah. Likitoci biyar ne a kan Hadiza, sai Sulaiman cikon na shida, wanda ya manta wani abu wai shi karatun likita, komawa ya yi tamkar bai taba halarta aji ba. Shi da Hadiza da ke kwance babu maraba, illa shi a tsaye yake, sai dai jingine da garu (bango), wanda ya taimaka masa wajen daukar nauyin gangar jikinsa. A lokacin da za ka tsaga ba za ka samu ko digon jini a cikin jikinsa ba. Tashin hankali ba a sa maka rana! Haka wannan mummunan labari ya iske iyayen Hadiza da ‘yan uwanta ta hanyar Dr. Surayyah. A daren Mukhtar ya baro Kaduna zuwa Kano, a daren suka dungumo baki dayan su suka taho, sai dai basu samu ganin Hadiza ba. Har zuwa lokacin likitoci na tsananta bincike a kanta, haka suka kwana a barandar asibiti cikin tsananin sanyi. Fati sai kuka take kamar ranta zai fita tunda suka taho, Yaya na lallashin ta. Sai washegari da safe result din Hadiza ya iske Sulaiman da iyayen ta, bayan raunuka da ba za su kirgu ba, babu karaya ko daya a jikinta. Babban tashin hankalin wanda ya _ girgiza kowa shi ne, jijiyar bayanta wadda ta hada daga wuya zuwa bayan ta (spinal cord) ta tsinke, wanda ke nufin Hadiza ba za ta kara iya mikewa ba, ba za ta kara iya tafiya ba a gaba daya sauran rayuwar ta. Dr. Sulaiman ya mike tsaye ya nuna Dr. Samson da dan yatsa, “Ka san abin da kake fada, ban san cewa baka san aikin ka ba sai yau. Kuma shi ke nan daga yin accident sai ka nakasta min mata? Uwarka ce ba za ta kara iya mikewa ba, amma ba Hadiza ba……” Kai da ganin yadda yake maganar, kwayar idanun shi a juye, ka san ba a hayyacin sa yake wannan furucin ba. Samson ya sunkuyar da kai, duka likitocin babu wanda ya kara magana. Tausayi ne fal a zukatan su. Dr. Hadiza abar so ce ga kowa, suna jin dadin tarayya da ita, marasa lafiyan ta na yaba kokarin ta. Wannan accident da ya yi mata karan tsaye da kuruciyar ta, ya zamo nakasu ga dimbin taimakon da take bai ma al’umma. Malam Ja’afar mahaifin Hadiza da ke gefe shi ya soma tausar Sulaiman da kalami masu dadi da sanya imani, yana tuna masa muhimmancin yarda da kaddara. Sulaiman ya yi shiru, ya koma ya zauna a kujerar sa. Ya kifa kai cikin cinyoyin sa, amma har yanzu ya kasa yarda da abin da kunnuwan sa suka jiye masa. Wai Hadiza ta zama sai dai a kwantar a tayar ba za ta kara amfanuwa ba, ba za ta kara moruwa ba. Balle ta amfanawa kanta komai. Ita da ‘ya’yanta da mijinta sai dai gani da ido. Abin da suke gani kullum yana faruwa da al’umma yau Allah As-Samadu ya juyo da shi kansu. Dimbin ilimin su, karfin aljihunsu da tunanin su babu abin da zai iya a kai, domin ita wannan jijiya ba ta doruwa. Sai ya fashe da kuka. Malam Ja’afar ya mike daga kujerar sa ya isa ga Sulaiman, ya mikar da shi tsaye ya rungume. “Haba Sule! Kamar ba namiji ba? Namijin ma, likitan likitoci. Ba ka yi kuka a kan sauran al’umma da kuke kwana da yini kuna fama dasu ba sai a kan matar ka kadai? Su Allah ba ya son su ne yake dora musu lalura? Allah da ya halicci Hadiza ya fi mu son ta, shi kadai ya san dalilin sa na hukunta hakan a gare ta. Yau in Hadiza mutuwa ta yi me zamu iya ban da mu yi mata addu’a? Amma tana raye, a kalla muna ganin ta muna jin dadi, ka yi tawakkali ka barwa AIlah, ka zamo mai YAKANAH, sai ya yi maka tukuici da abin da baka zata ba. Kai za ka ba ta kwarin gwiwa, ta rungumi kaddarar da Allah ya dora mata. Amma idan ka fita karaya, wane ne zai karfafa wani?” Ya mika hannu yana share masa hawayen da suka kasa daina ambaliya daga kyawawan idanun sa. Dr. Ruth ta yi gyaran murya, ta dubi Dr. Sulaiman ta sunkuyar da kanta, kana ta dago ta ce, “Ina ganin idan Dr. Hadiza ta ji sauki, za ta iya ci gaba da aikinta ta hanyar amfani da wheel chair, idan har za’a samu wanda zai juri kawo ta da mai da ita”. Kiris! Ya rage ya lailayo ashar ya antaya mata, amma da ya tuna Malam na wajen Sai ya balla mata harara, a zuciyar shi ya ce, “Uwar ki za a sa a wheel chair ba uwar Munib ba”. Samson ya ce, “Shawarar Ruth abar dubawa ce, hakan zai debe mata kewa fiye da ta zauna a gida ba abin da take yi. Ko ba don zuwa aiki ba dole za a nema mata wheel chair ko da a gida ne”. Ba shi da abin cewa, don duk likitocin abin da suke cewa kenan. Malam dai baya ji saboda cikin harshen turanci suke maganar. Sulaiman ya tashi ya fita ya nufi ICU inda aka kwantar da Hadizah. A bayan kofa ya tsaya ya rabe, yana leken ta, ya kasa karasawa, ya kura mata ido yana ta’ajjibin yadda kwana daya rak! Allah ya_ jirkitar da kyakkyawar fuskar Hadiza, ko ina a jikinta rauni ne, nan plasta can plasta. Barci take sadidan, sai dai da gani ba na Allah da Annabi bane (na karfin allurai ne). Rabin fuskarta nade cikin bandeji, wadda ta kumbura ta yi sumtum kamar an hura (baloon). A hankali ya soma taku ya isa ga gadon da take kwance, ya ja kujera ya zauna dai-dai fuskarta yana fuskantar ta. Ya kai hannu bisa goshin ta wanda ke nade cikin bandeji, kamar an ce da ita bude idon ki. Suka yi ido hudu da Sulaiman din ta, ta dubi dakin ta dubi kanta, ta tabbatar a kwance take a gadon asibiti. Ta maido duban ta ga Sulaiman wanda ke binta da ido, da zuciya, ta ce cikin kankanuwar murya, “Accident na yi ko?” Ya daga mata kai. Ta dora hannunta mai rangwamen raunika bisa nashi dake goshin ta, ta sauke, don ji take kamar ya dora mata Dala da Gwauron Dutse. Ta yunkura da niyyar ta tashi zaune amma ta ji kamar ba jikinta ba, ya mike ya kama ta ya mikar da ita zaune. Ya janyo pillow ya tusa mata don ta ji dadin jinginar, ya tabbatar dai da gaske ne Hadizar shi ta zama disabled (nakasasshiya), sai jikinsa ya soma kyarma. Duk dauriyar da yake yi abin ya ci tura, da sauri ya rungume ta, cikin shesshekar kuka ya ce, “Cikin kowanne hali, INA SON KI HADIZAH”” Kuka suke dukkanin su babu mai rarrashin wani, don ita Hadiza ta tabbatar abin da zai sa Sulaiman kuka, to tabbata ba karamin abu bane, wannan shi ya gigita ta, ita ma ta fashe da kuka. Fati a gaba, Yaya, Malam, Hamza da babban Yayan su Mukhtar suka shigo, daga Hadiza har Sulaiman babu wanda ya san da shigowar su, shessehekar kukan Fati ne ya ankarar da Sulaiman cewa akwai mutane a dakin. A hankali ya zare jikinsa daga na Hadiza ya juya ya fita daga dakin ba tare da ya iya hada ido da surukansa ba. Malam Ja’afar ya karasa jikin gadon Hadiza ya kama hannun ta inda babu ciwo, ya ce, “Ki yi tawakkali Hadiza, ki zamo mai YAKANAH a dukkanin al’amuran ki, ki zamo mai godiya ga Allah a duk yanayin da kika tsinci kanki. Wannan ba shi ne karshen rayuwar ba, yarda da kaddara dole ne ga duk musulmin kwarai”. Cikin kuka mai tsanani ta ce, “Na ji Baba, amma don Allah ku fada min me ke faruwa dani? Sulaiman bai gaya min komi ba, sai kuka yake yi, kukan shi ya daga min hankali, ku fidda ni a duhu. Wani abu ne ya faru dani?” Malam ya sa habar babbar rigar sa ya share hawayen da suka ciko mishi ido cikin dabara wai kada Hadiza ta ga shi ma kukan yake, amma ta ganin. Hadiza ta musamman ce ko a cikin ‘ya’yansa, yana son ta son da bal yiwa su Mukhtar, ganin Babanta yana kuka sai ta kara tsananta kukan ta. Cikin tausasawa Mukhtar ya ce, “Cool down Hadiza, take it easy……. Ya shiga rattabo mata al’amarin da ya samu rayuwarta, ya kare da cewa, ““Wannan shi ne ya dagawa Sulaiman hankali, amma kamar yadda Baba ya ce ne, ki yi tawakkali, ki zamo mai YAKANAH! Wannan ba shi _ ne karshen rayuwar ba!” A matsayinta na cikakkiyar likita, tuni ta gano mummunan nakasun da ya samu rayuwarta wanda babu wani likitan duniya da zai iya maganin shi. Ta nemi hawaye a kwayar idonta ta rasa, ta nemi miyau don ta hadiya a kan harshen ta ya kafe karaf! Kamar Fati a gaba, Yaya, Malam, Hamza da babban Yayan su Mukhtar suka shigo, daga Hadiza har Sulaiman babu wanda ya san da shigowar su, shessehekar kukan Fati ne ya ankarar da Sulaiman cewa akwai mutane a dakin. A hankali ya zare jikinsa daga na Hadiza ya juya ya fita daga dakin ba tare da ya iya hada ido da surukansa ba. Malam Ja’afar ya karasa jikin gadon Hadiza ya kama hannun ta inda babu ciwo, ya ce, “Ki yi tawakkali Hadiza, ki zamo mai YAKANAH a dukkanin al’amuran ki, ki zamo mai godiya ga Allah a duk yanayin da kika tsinci kanki. Wannan ba shi ne karshen rayuwar ba, yarda da kaddara dole ne ga duk musulmin kwarai”. Cikin kuka mai tsanani ta ce, “Na ji Baba, amma don Allah ku fada min me ke faruwa dani? Sulaiman bai gaya min komi ba, sai kuka yake yi, kukan shi ya daga min hankali, ku fidda ni a duhu. Wani abu ne ya faru dani?” Malam ya sa habar babbar rigar sa ya share hawayen da suka ciko mishi ido cikin dabara wai kada Hadiza ta ga shi ma kukan yake, amma ta ganin. Hadiza ta musamman ce ko a cikin ‘ya’yansa, yana son ta son da bal yiwa su Mukhtar, ganin Babanta yana kuka sai ta kara tsananta kukan ta. Cikin tausasawa Mukhtar ya ce, “Cool down Hadiza, take it easy……. Ya shiga rattabo mata al’amarin da ya samu rayuwarta, ya kare da cewa, ““Wannan shi ne ya dagawa Sulaiman hankali, amma kamar yadda Baba ya ce ne, ki yi tawakkali, ki zamo mai YAKANAH! Wannan ba shi ne karshen rayuwar ba!” A matsayinta na cikakkiyar likita, tuni ta gano mummunan nakasun da ya samu rayuwarta wanda babu wani likitan duniya da zai iya maganin shi. Ta nemi hawaye a kwayar idonta ta rasa, ta nemi miyau don ta hadiya a kan harshen ta ya kafe karaf! Kamar bai taba gudana a cikin bakinta ba. Ta runtse idonta da karfi, tsawon mintuna biyar ba ta bude ba. Ita kadai ta san radadin da take ji a zuciyarta, ita kadai ta san azabtuwar da ruhinta ke yi, al’amarin ya shallake tunanin ta. Ba ta yi tsammanin al’amarin ya yi kamarin haka ba, lallai dan adam ba a bakin komai yake ba. Yau ne kake mai rai, gobe ne kake gawa. Yau ne kake da amfani, idan Ubangiji ya so, gobe ne ka zama tarihi. A rayuwar Hadiza ba ta taba tsammanin wata kaddara makamanciyar wannan za ta taba shafar rayuwar ta ba. To ina ruwan Allah! Ta bude idon a hankali tana kallon iyayen ta da ‘yan uwanta wadanda dukkanin su ke sharar hawaye, sai ta soma lallashin su cikin muryar ban mamaki, tamkar ba ita ba. Ta fi su karfin zuciya, ta fi su tawakkali, ta fi su YAKANAH. Ta karbi kaddarar ta da hannu bibbiyu, tana fatan Allah ya sa hakan ya zamo kaffara a gare ta, in kuma jarrabawa ce ya sa ta cinye jarrabawar ta. 36 KOK Dole kanwar naki, Sulaiman ya sayo ma Hadiza wheel chair ana i gobe za a sallame su daga asibiti. Don duk raunin dake jikinta ya kame sai karfin jiki da dan abin da ba a rasa ba. Yaya ta so Sulaiman ya ba ta Hadiza ta wuce da ita gida inda za ta fi samun kulawar iyaye da ‘yan uwa, amma sai ya sa musu kuka. Da me zai ji ne? Da lalurar da ta kashe masa rayuwa, ko da rashin Hadiza a cikin gidan, wadda ta zamo wani bangare na rayuwar sa, kundin farin cikin sa, sannan barin jikinsa? Dole suka kyale shi da matar shi, amma sun ce Fati ta koma gidan ta zauna tare dasu, don ta dinga taimaka masa kula da Hadiza, musamman kasancewar sa ba mazauni ba. Sulaiman bai so ba, don shi tun fil’azal Allah bai sa mishi son Fati ba, saboda son da Hadiza ke mata. Yana kishin Fati, a ganin sa Hadiza ta fi son Fati a kanshi. Sannan zubin ta na zuhudu (gudun duniya) ya yi yawa, bai fiya son mutane irin ta ba, kasancewar shi (sociable). A tsarin halittar dan adam (personality), tana cikin rukunin al’ummar da ake kira (introbert). Ba ta iya hada ido da shi, kai da kowa ma, saboda kunya. Da wuya ka ga hakoranta, sai dai in guri ya kure ta yi murmushi, ‘dimple’ din da ‘cleft’ su lotsa, wanda shi ne muhimmin al’amarin da ke daukar hankalin dubban maza a kanta, sai dai kuma bai isa ya tsallake hukuncin da Yaya ta yanke ba. Haka Fati ta hado kayan ta tsaf, ta dawo gidan ‘yar uwarta da zuciyar ‘yan uwantaka. Zuciyarta cike fal da so da kaunar ‘yar’uwar ta, karatun da ta taso shekara da shekaru da burin yin sa, gashi ta samu, amma ta jingine shi ta sadaukar da rayuwarta kacokam da lokacinta ga rayuwar, ‘yar uwarta. Sulaiman ya ciccibo Hadiza ya fito da ita daga mota, Fati ta bude (boot) ta fiddo wheel chair a nade, cikin sauri ta warware, Sulaiman ya sanya ta a ciki ya tura a hankali zuwa cikin gida. Fati ta fiddo kayansu daga cikin motar ta rufe motar, ta soma diban kayan daya bayan daya tana shiga dasu cikin gida. Malam Ilu maigadi, ya yi sallama a falon, a lokacin Sulaiman na kici-kicin aza Hadiza a daya daga cikin kujerun falon, ba tare da ya juyo ba ya amsa masa. Ya zube har kasa yana jajantawa iyayen gidansa kaddarar da ta same su. Yana magana yana sharar hawaye, saboda yadda yake matukar kaunar Hadiza, saboda karamci da kyautatawar ta gare shi. Haka Goggo Allti ta fito daga kitchen, ganin Hadiza yau nade cikin kujera sai ta fashe da kuka, Sulaiman ya yi saurin ficewa a falon ya dau mota ya fita don dauko yara a makaranta. Hadiza ta dubi Alti ta yi dan murmushi, “Alti wane ne ya halicce mu?” Ta ce, “Allah (S.W.A)”. Ta ce, “To kinga in haka ne ke nan bamu da iko da kanmu sai abin da ya ga damar hukuntawa a gare mu, mu kuma dole ne mu zamto masu godiya idan har muna so imanin mu ya cika”. Alti ta jinjina kai tana mai jinjina karfin imani irin na uwargijiyarta. Hadiza ta juya ga Fati ta ce ta kal kayanta dakin ta, kasancewar a tsarin gidan likitocin babu wani edtra room, ita za ta yi amfani da na Sulaiman. Fati ta ce atafau ita dakin su Muniba za ta zauna tare dasu, ta kada ta raya amma ta ki, ta ciccibi jakarta ta yi dakin su Muniba. Fitar ta daga falon ke nan su Munib suka dira a falon, Baban su na biye dasu yana rike da jakunkunan su da food flasks din su. Suka tafi da gudu suka rungume Mamarsu, Munib da yake shine mai wayo ya ce, “Mummy yaya jikin ki? Daddy ya gaya mana kin yi accident kin ji ciwo kina asibiti ana yi miki allura?” Ya kai hannu ga tabon ciwon goshinta, “Sannu Mummy, kin ji?”. Ta shafa kansa ta yi masa murmushi bata ce komai ba. Ita kuwa Muniba bin jikin Mummyn ta yi ta lafe kamar mage, dama ita ba ta fiya magana ba. Zuciyarta kal da ganin mahaifiyarta da ta jima ba ta gani ba. Munib ya soma jan hannunta wai ta taso suje su yi kwallo (ball) kamar yadda suka saba, Sulaiman ya kau da kai, bai son ganin wannan abin tausayi, ya mai da hankali ga lallatsa wayar sa, baya son su ga hawayen sa. To ita ma Hadizar duk dauriyar ta sai da hawayen suka tsatstsafo, ta sa yatsun ta biyu ta dauke su, ta kama dukkan ‘ya’yan biyu ta rungume a kirjinta. Kukan zuci take wanda ya fi na fili soya zuciya. Ta ce, “Ku tafi wurin Anti Fati tana dakinku ku yi kwallon tare, har yanzu bani da lafiya”. Da gudu suka mike daga jikinta suka nufi dakin su suna murnar zuwan Antin su da suke tsananin so. Alti ta yi sallama dauke da tray kanta a sunkuye ta ce da Hadiza, “Na ce sai na daina daura abinci a tebir?’ Hadiza ta yi murmushi mai hade da wani irin huci mai zafi, ta ce, “Idan maigidan yana son hawa tebir din fa?” Ta fada tana kallon Sulaiman. Bai dago ya kalle su ba, haka bai tofa musu ba, duk da ya lura ta bakinsa suke son ji. Alti ta ajiye katon tray a gaban Hadiza ta juya ta fita. Tana ba da baya ya suri Hadiza a kafadar shi sai dakin barcin su. A hankali ya sauke ta a makeken ‘family bed’ din su, ya koma toilet ya cika baf da ruwa mai dumi, ya zuba dettol kadan ya dawo ya soma warwarewa Hadiza kayan jikinta, ya nade ta cikin towel ya sake sungumar ta ya yi toilet ya sanya ta cikin ruwan da ya hada. Ita karfin Sulaiman mamaki yake bata. Ya yi mata kyakkyawan wanka da kamsassan sabulun Zest, ya nado ta ya fito da ita. Yawancin kayanta a dakin suke, don haka ya shirya ta cikin riga da wandon pakistan ruwan goro (orange), ya dauki (kumb) ya soma sharce mata gashin kanta wanda rashin gyara kwana biyu ya sa shi duk ya cukurkude. Ta ce, “Da ka bari Sulaiman Fati za ta yi min”. Bai saurare ta ba ya ci gaba da abin da yake, amma da a ce ta kalli fuskarshi a lokacin, data lura da yadda ya dan hada rai, saboda ambatar Fati da ta yi, wato ta fi son Fati ta kula da ita fiye da shi. Ta yi murmushi ta ce, “Amma tunda ka hada ruwan wanka ka yi mai wuyar, zan iya wanka da kaina,sai Fati ta shirya ni koda yake ma zan iya shiryawa da kaina……. ” “Is o.k Hadiza, ba tun yau ba na san kin fi son kanwar ki fiye dani. In ba haka ba ni amfanin me ke gare ni? Da ba zan kula dake ba a lokacin da kike cikin lalura?” Ta kama baki, don ba ta ji dadin maganar shi ta farko ba, amma sai ta share ta ce, “Yau da gobe ne sai Allah Sulaiman……. “. Can kuma ta yi rau-rau da ido kamar hawaye za su zubo, “Me ya kawo maganar na fi son Fati a kanka? Ban ji dadin nagetive response din ka ba”. Ya ce, “To ai ke ce Hadiza da wani irin batu, amma ina so ki yarda da cewa, idan zan gaji da hidimar ki Hadiza, to zan gaji da_ hidimar Kaina…… ” Ta ce, “Amma Sulaiman…… Ya kai hannu ya toshe mata baki, “Kina shakka da abin da na ce miki?” Ba ta son jan zancen da nisa, har ya yi tsayin da zai zamo bacin rai, sai ta ce, “Bana shakka Sulaiman, Allah ya bamu rai da lafiya”. Ya turo ta cikin kujerar ta suka dawo falon don cin abinci. Munib da Muniba suka shigo, fes dasu cikin kaya ‘yan kanti (pink colour) har Fati tayi musu wanka ta shirya su ta feshe su da turare. Suka saki baki cikin mamaki, ganin Daddy yana tura Mummy cikin kujera, abin ki da yaro, sai ba su kawo ma ransu komai ba, ko wani abu ne ya faru da Maman nasu, sun dauka haka nan dai yake tura ta don bata da lafiya. Sai suka sa rigimar ta tashi suma Daddy ya tura su. Haka Sulaiman ya sauke Hadiza a seater, ya dauke su su duka biyun ya aza a kujerar, ya yi ta zagaya falon dasu suna jin dadi, sai kyalkyatar dariya suke. Hadiza ta juya ta dube su, ganin abin nasu ba na kare bane ta ce, “Oya! Food is ready, maza ku zo ku ci kafin malamin lesson ya zo, ko kuna so ku yi latti ya yi muku bulala?” Suka diro daga kujerar suka nufo abincin, Sulaiman ya zauna tsakanin Hadiza da Muniba, kafadun su na gugar na juna. Ta sa murya ta ce, “Fati!” Ta fito sanye da hijab, da alama sallah ta idar, kallo daya Sulaiman ya yi mata ya dauke kansa, ya ci gaba da cin abincinsa. Daga can bakin kofa ta tsaya ba ta karaso cikin falon ba, son addini irin na Fati yana matukar burge Hadiza ba kadan ba. Ta ce, “Taho mu ci abinci in kin idar da sallar”. Ta yatsina fuska ta ce, “Na ci tun dazu, Alti ta zuba mini”. Don jikinta ya yi sanyi da hararar da Sulaiman ke zabga mata, bayan ita ko da gida da mota aka hada ta dama ba za ta ci abinci da shi ba, don ta ki jinin mutum mai halin GIRMAN KAI. To a ganin ta halin Sulaiman kenan, babu wanda ke ganin walwalar shi sai ‘ya’yan shi da matarshi, duk ilimin da ya ke takama da shi a ganin ta girman kai ba hali ne da ya dace da likita ba. Ba ta san cewa shi ma bekenta yake gani ba. Hadiza ta ce, “Don me ba za ki bari mu ci tare ba? Kada ki sake yin haka”. Fati ta ce, “Haka nan na saba, ba zan iya cin abinci da mutane ba”. Sulaiman ya balla mata harara, “Su waye mutanen? Bakauya kawai, saboda ni ne ba za ki ci ba. Na yi kama da rubabben saurayin ki ne? Dube ta da Allah kullum da zumbulelen hijabi kamar takari, gara ma ki rage wannan zuhudun ko kya samu mashinshini, don ko ni din nan aka bani ke ko da sadaka ne ba abinda zan yi da ke wallahi-wallahi ko mata sun kare a duniya”. Fati ta harare shi ta zumbura baki kamar ta yi kuka, ta ce da Hadiza, “Kina jin shi ko?” Hadiza ta yi dariya ta ce, “Rabu da shi Fati na, Allah na tuba ko mutuwa nayi ai ya yi miki tsufa, me za ki ci da dan late thirty? Sai yaro sabon jini kamar ki”. Daga Fati har Sulaiman, kalmar “mutuwa” da Hadiza ta ambatawa kanta, ta taba zuciyar su. Sulaiman ya tsame cokali daga plate ya aje gefe yana bin Hadiza da wata irin harara da ita kadai ta san ma’anar ta. Ita kuwa Fati ba ta kara tofawa ba, ta koma daki tana cewa cikin ranta, “kada Allah ya nuna min wannan ranar…., Yaya Hadiza sai dai ki yi min makoki, ba dai in yi miki ba’. Kwana bakwai cif Sulaiman yana gida cikin iyalinsa bai je ofis ba, yana kula da lafiyar Hadizar sa. Ta fuskar shan magungunan ta a kan lokaci, hidimar ta da walwalar ta, tare da ba ta karfin gwiwa na karbar rayuwa a duk yadda tazo, yana nuna mata kaddarar da ta same ta ba ta shafi ko kankani na daga soyayyar da yake yi mata ba. Ta yarda, ta amince Sulaiman mai son ta ne, kuma irin mazan da da wuya a samu kamar su a wannan zamanin wajen rike alkawarin soyayya da sanin darajar diya mace. A ‘yan kwanakin ta kara samun karfin jikinta, don haka ta kirkirowa kanta abubuwan debe kewa da _ dama, wadanda a da ba ta da lokacin su, kamar karatun jaridu da mujallu, “browsing’ da kuma kasancewa full-time da ‘ya’yanta suka kara shakuwa. Abu na hudu da take ganin zai taimaka ainun wajen debe mata kewa shi ne, rubuta tarihin rayuwar ta a matsayin story-writing cikin harshen Hausa. Da Sulaiman ya fahimci damuwar Hadiza ta ragu da 80%, sai ya samu kwarin gwiwa da jarumtakar fuskantar aikin sa. Ya koma aiki ranar monday cike da tausayin Hadiza, yana mai tuno lokutan zirga-zirgar su cikin asibitin don ceton al’umma, da matsalar ta mai magantuwa ce ba ya tsammanin in zai rasa duk abin da ya mallaka zai gaza wajen nema mata magani. A wani bangaren kuma yana tunanin shawarar su Dr. Ruth ne da suka ce Hadiza za ta iya komawa aikin ta a haka. Da ya tuntube ta, ta nuna ba ta yi naam da shawarar ba, don ba ta yanke kauna da rahmar Ubangiji ba, za ta zauna a gida ta yi zaman aure, wanda a da ba ta yi ba. Ta ga shi kuma wace irin riba ce a cikin sa, tunda ta yi aikin, ta ga ribarsa da rashin ribar sa? A wautar Hadiza, tunda wannan lalura ta same ta shikenan Sulaiman ya daina sha’awar ta, wato ya daina mu’amalar aure da ita, tunda ta nakasa ba ta da abin da za ta ja hankalin sa. Ba ta yi la’akari da cewa soyayyar ta a cikin jinin Sulaiman take ba, ba’a abun jan hankali ba. Kwata-kwata sati biyu cur da fitowar ta daga asibiti, sai labari ya sauya, Sulaiman soyayya har ta fi ta baya, kamar wanda ya je ya kara yin course a kan (lobe-making). Watakila da da hali da ya tsaga kirjinsa ya sanya ta a ciki, mai yiwuwa sannan ne zai zamo (contented). Sai da komai ya lafa ya fahimci Hadiza kuka take, ba kuma kukan komi take ba, ….kukan rashin yarda da kai ne. Amma shi duk sai ya rikice, kukanta da hawayen ta ba karamin daga mai hankali ya yi ba. Ya tarairayo ta ya dora a kan kirjin shi, cikin sassanyar murya yake tambaya, “Did I hurt you Hadizahh?’ Ta girgiza kai, cikin shesshekar kuka ta ce, “Sulaiman kai ne?” “In bani bane wane ne?” Sai ta yarfar da hawaye da hannun daman ta, ta ce, “Ni dai ka kara AURE!” Sai ya janye jiki daga jikinta cikin mutuwar jiki da sagewar gwiwa, “Kafin in baki amsa Hadiza, ko in bi umarnin ki, ina so in san mene ne dalilin ki na cewa hakan?” “Saboda Hadizar da, ba ita ce yanzu ba, wannan nakasasshiya ce, ba ta cancanci wannan dimbin soyayyar ba”. Ya dade yana kallon kyakkyawar fuskarta a dan hasken asubahi da ya soma keto shara-sharan farin labulen dakin, kamin ya yi murmushin takaici ya zauna sosai ya ba ta baya. “Hadiza tafiyar ki ce ta sa na aure ki? Ko ko yanga da kwarkwasa kika yi min na ji ina son ki?” Ta girgiza kai, “babu ko daya. Amma son da nake maka Sulaiman, ba zai barni in kware ka ba, idan ka ci gaba da zama dani ni kadai, na kware ka, a matsayin ka na _ lafiyayye kuma cikakken namiji. Idan ka kara aure zan ji dadi, zuciyata za ta sake. A kalla ina da tabbacin baka cikin kwaruwa, amma yanzu sai nake ganin, na kware ka…….. ” Ya daga mata hannu ya ce, “Ya isa, ya isa Hadiza….” Ya ma rasa me zai ce don takaici, sai ya karkada kai ya fita ya bar mata dakin. Kwanaki uku suna kan wannan takaddamar. Hadiza ta dage ta ja tunga a kan bakanta, in ya yi fushi sai kuma ya sauko ya yi dariya don mamaki. Ba ya son duk wani abu da zai bata ranta a dai wannan lokacin da_yake angwancewa da kuma yin la’akari da halin da take ciki. Don haka a rana ta biyar da ya ga ba zai iya jure wannan horon da ta tsiri yi mishi ba, don ba shi da juriyar a wannan fannin ta inda take samun weakness din sa kenan. Sai ya cafki hannayen ta ya langabar da kai kamar karamin yaro, idanuwan nan sun juye sun rikide zuwa…….. Ya ce, “Hadiza na baki wuka da nama, ke ce mijin ke ce matar, ki zabo min duk yarinyar da kika ga ta dace dani, don bani da idon kallon wata diya mace, tun daga lokacin da Allah ya mallaka min ke……” Ta cira kai a hankali ta dube shi, sai ya ba ta tausayi, don numfashi kanshi a wahale yake furzar da shi da sauri da sauri. Ganin yadda jidalin ta ya ramar da shi kwanaki biyar kacal, sai ta kara jin tausayin sa. Amma jan ajin mu na mata, sai ta balla masa harara wadda in ka lura ba komi ne cikin ta ba face tsananin son mijinta da matsanancin KISHI, ganin daga karshe ya sauko ya bi ra’ayinta kamar yadda take so. Kamar ta yi kuka ta ce, “Nice ma zan nemo maka matar? Ashe you are not serious…!” Ta juyar da kai, sai ga hawaye sharrr! Sun zubo a kan kundukukin ta. Kiris ya rage dariya ta kubce masa, amma ya danne kada ya kara laifi. A gicciye ba tare da ya dube ta ba ya ce, “Wai ko a cikin student din ward din ku, irin ‘yan yara-yaran ‘yammatan nan? Ko rikakkun ‘yammatan likitoci irin su Dr. Surayyah”. Haushi ya kama Hadiza, don ta lura ya mai da abin zolaya. Ta yi shiru ba ta ba shi amsa ba. Ya rungumota ta baya, ya dora kan shi a kafadun ta, yana sakin ajiyar zuciya mai nauyi. A sanyaye ya ce, “Ko kin daina sona ne Hadizahh? Kike neman kai dani? A da ko kallo na wata ta yi, kallon da bai yi miki ba, sai kin kwana bakya yi min magana, amma yanzu duk kin daga hankalin ki wai in yi aure. Which mean……. na gundire ki…. kina neman mataimakiya don ki huta….. Ni ina ruwana da wasu kafafun ki tunda ba su nake aure ba? Inda nake aure zam-zam yake. Da aka yi accident din ma, kamar an kara masa armashi. Kafafu? Ni ba ina da su ba? Kuma ba ina daukar ki dasu ba? To meye damuwar ki? In gaya miki gaskiya, ba zan iya sharing kaina ba, saboda ina da kyama, ba kowacce mace zan iya hada jiki da ita ba. Babu, ban taba ba, bana fata, kada ki tursasa ni, don ba zan iya ba, ba zan iya adalci ba. An ce kuma in ba za ku iya adalci ba, to ku zauna da daya. Amma in kin gwammace ranar kiyama in tashi da shanyayyen barin jiki, all the same, sai in auri Surayyah! Kinga daga nan sai ku kara dankon zumunci…….. Ta ture shi da sauri, duk da jikinta ya yi sanyi da maganganun sa, ta tabbatar iya gaskiyar shi yake fadi, don shi bai fadin abin da ba haka bane a zuciyar shi. Don kaji dadi, ko don ya faranta maka. In haka ne kenan Sulaiman da gaske za ka iya auren Dr. Surayyah?” Sai hawaye suka zubo. Magana take a zuci, ba ta san cewa a fili ta yi ba. Ya sauka daga gadon ya zauna dabas a kan kafet, ya dauki hannu ya rafka uban tagumi, “Ni SuJaiman na shige su, duk yadda na yi, ban iya ba. To ki fadi yadda kike so, ni kuma mijin ta ce ne!” Idon ta fal hawaye ta dube shi cikin ido, abin da bata yi sai rana ta kure, “Ka gaya min gaskiya Sulaiman, Surayyah kake so?” Ya yi murmushi ya shafi siraran lebbansa, “Ya ya ba zan so ta ba tunda tana son ki, tana son ‘ya’yana?” “Ni ba wannan son nake nufi ba…….. Ya mike tsaye ya bata baya zai fice, “Koma wanne kike nufi shi ne, yarinyar nan rikicinki ya ishe ni, son ta nake na soyayya, soyet. Ki yi kulikulin kubura dani, ko ki yi ta kuka, har hawayen ya kare…….. ” Duk da kuka take ba ta san sanda ta yi dariya ba, ganin kuma ya dawo ya cafko ta yana son a sauya hirar da irin wacce ya fi so ayi, mai ma’ana da tsayawa a zuci, hadi da dimbin lada. Ba ta da zabi (she habe no choice) ban da ta rungumi mijinta, mai son ta, mai kaunar ta. Ta nuna mishi son shi kawai ya sani, bai san nata ba. Duk hasashe take, amma ita ma ta san ba za ta iya raba Sulaiman din ta da kowa ba. 2K OK D a wannan Sulaiman ya kashe bakin Hadiza da maganar ya kara aure, saboda ita ta nakasa. Don ta san cewa zai yi zai auri Dr. Surayyah, ita kuma in da abin da ta tsana ya fito daga bakin sa, to bai wuce wannan furucin ba. Surayyar ba ta watsar da Hadiza ba, ta kan zo in ta samu sararin aiki kuma suna yawan yin waya. Tayi-tayi Hadiza ta koma aiki in ya so sai Fati ta dinga kula da zirga-zirgar ta amma ta ki. A ganin ta ita Fatin zaman ta kenan ba za ta yi nata auren ba? Ko ko haka za ta karar da rayuwar ta wajen hidimar ta alhalin bata kai ga cimma komai a rayuwa ba? Gara ita ta kai ga matakin da duk dan adam ke burin samu; tayi ilmi, tanada kwali, tayi aure, ta hayayyafa. Don ta zauna gida a halin yanzu babu komi. Ta ce, “Surayyah mune bamu gane ba, ko da yake mu namu aikin mai tushe ne daga addini. Amma ba abin da ya kai mace ta zauna a dakin mijinta ta yi biyayyar aure dadi da kwanciyar hankali, amma ina amfanin da auren ki da mijin ki da ‘ya’yan ki amma kin watsar dasu kin barwa mai aiki kullum kina titi, bayan mijin ya tsare miki dukkan bukatun ki na rayuwa?” Surayyah ta ce, “Ke din ce dai kawai kin yi sa’a Hadiza, amma ba ko wadanne maza ne irin Dr. Sulaiman ba”. Kishi ya motsawa Hadiza ta hadiye shi mukut, amma ta san Surayya gaskiya ta fada, Sulaiman is unikue, akwai wani simpleness a tare da shi wanda maza da yawa basu da shi. Hadiza ba ta samu kwanciyar hankali ba sai da Dr. Surayyah Yahya ta kawo mata katin auren ta da Dr. Bashir Bunza, cike da shakiyanci ta nunawa Sulaiman. Ya karanta ya ciji yatsa, “Shege Bunza, ya kasa ni”. Ta kyalkyace da dariya ta ce, “Eh, to kai ne ka tsaya sanya”. Ya harare ta da idanun kauna, “Haka ma za ki ce? Bayan ke kika kashe min gwiwa, ai da tuni na karkata hula nasa kai, wallahi da ni zan kasa shi”. Ta sake yin dariya ta ce, “Oho dai, sai abi wani sarkin ba Ado ba”. 2K KK OK A sabar ce sassanya mai dauke da wani irin lullumi mai sanya nishadi a zukatan dan adam, ana saura kwana biyar a kama azumin watan Ramadan, kamar kowacce asabar din karshen wata. Dr. Sulaiman ya zuba ‘ya’yan shi a mota suka nufi Bakori ainihin gidan iyayen shi kamar yadda suka saba, can za su wuni, wani zubin har yamma ko dare. To yau ma hakan. Gidan ya rage daga Hadiza sai Fati, don Alti ta je kauyen su Kukawa ganin gida za ta yi sati biyu tunda yaran ma cikin hutu suke. Fati ta tura Hadiza_ kitchen kamar yadda ta bukata, ita tana girki Hadiza na mata hira. Ta ce, “Fati yau shekara guda cur da faruwar al’amarin nan, nayi-nayi ki kara neman wani admission din amma kin ki, kina nufin haka za ki yi ta zama kina yi min bauta ba karatu ba aure? In don nice wallahi bana cikin matsala a halin yanzu I can take a good care of myself (zan iya kula da kaina) ko daa ce ni kadai ce a cikin gidan nan”. Fati ta sauke tukunya ta dora wata, ta yarfar da hannu don zafi. Sannan ta dubi ‘yar uwarta, “Yaya Hadiza ba zan iya barin ki ke kadai in tafi makaranta ba, ko na tafi tunanin halin da kike ciki ba zai barni in mai da hankali a kan karatun ba”. Ta yi murmushi, “Cewa_nake watarana aure za ki yi Fati?” Nan da nan Fati ta yi kicin-kicin da fuska, ta juya mata baya ba ta ce komi ba. Hadiza ta ce, “Ko baki ji ni ba? Aure za ki yi Fati dole ba da jimawa ba, don haka ki tsaya ki gina rayuwar ki kamar yadda muka gina tamu, bana so saboda amfanin kaina ke in tauye ki. Don haka na baki kwana biyu ki yi tunani, an fara sai da JAMB na wannan shekarar, don haka ki nutsu ki kama abin da zai taimake ki ranar da bani. Duk wata kauna da dan uwa na gari zai nuna wa dan uwansa kin nuna min ita, sakayyar ki na wajen Allah. Sai dai ba zan bari ki kari rayuwar ki baki dandani zakin ilimin ko auren da na dandana ba, dole in samar miki future kafin Allah ya yi hukuncin da ya So a kaina….” Fati ta yi saurin juyowa ta dubi Hadiza, domin a da ta bata baya ne. Ba ta gane abinda take nufi ba. Hadiza ta yi murmushin karfin hali ta ce, “Fati zan gaya miki wani abu, amma bana so ki daga hankalin ki, bani da lafiya Fati, amma don Allah ko Yaya ban yarda ki gayawa ba balle Sulaiman. Fati na dade ina fama da ciwon kai wanda nake yi lokaci-lokaci, Sulaiman ya sani ina yawan fama da (migrain) amma bai taba zurfafa bincike ba, don ban taba gaya masa yadda nake ji ba. Ba tare da sanin sa ba na je wajen Dr. Bunza mijin Surayyah, da ke likitan kwakwalwa ne, cikin sirri ya yi min bincike mai zurfi inda ya sanar dani ina fama da kansar kwakwalwa (brain cancer)”. Fati ta zazzaro ido ta sulale ta zauna a kasa, ta kai hannu ta dafe kirjinta, sai ga hawaye suna shatata! Hadiza ta yi murmushi ta matso da kujerar ta inda Fati take, ta dora hannu a kanta. “A‘a, Fati kada mu yi haka da ke, ama nar rayuwata nake gaya miki, wadda bani da wanda zan bawa sai ke. Ba wanda zan iya gaya ma wa Sai ke, ciwon bai yi tsanani ba, kuma ina shan magani a boye, ko Surayya ba ta sani ba. Fati abin da ya sa na gaya miki don ki tallafa min ne, Sulaiman likita ne wanda ke bukatar kwanciyar hankali don samun (confidance) wajen gudanar da aikinsa na ceton rayuwar al’umma, idan ya ji wannan maganar ba zai taba samun kwanciyar hankali ba. Fati Sulaiman yana sona, sosai, irin son da zai iya bani rayuwar shi, bana son abin da zai dagula masa lissafi, ki rike min amanata, ki rike min ‘ya’yana, ki basu tarbiyya irin taki kada ki bari Sulaiman ya tagayyara a bayana. Ina son shi yadda yake so na, na so in Ci gaba da rayuwa tare da shi, in ci gaba da haifa mishi ‘ya’ya kamar yadda yake so, amma ban san ya ya Allah zai yi dani da rayuwata ba. Ki rike min Sulaiman Fati bana so rashi na ya tagayyara shi…….. ” Zuwa wannan lokacin duka ‘yan uwan biyu sharbe suke, na hawaye da majina. Girki yana ta kauri, amma ba su kula ba. Fati ta rage sautin kukan ta, ta ce, “Shi brain cancer ba’a warkewa?” Hadiza ta ce, “Ba a warkewa gaba daya, ko ya lafa zai tashi, amma ina kula da shan magani”. Fati ta yarfe hawaye ta ce, “Wannan ba abun boyewa bane Yaya Hadiza, ki daina fidda rai da rayuwa saboda ciwo. Insha Allah ke za ki aurar da Munib da Muniba, ya kamata ki sanar da Dr. domin ya taimaka miki da addu’a, duk wani hali da zai shiga ai shi musulmi ne ya san duk son da yake miki ya san bai kai wanda Ubangijin ki yake miki ba. If the condition become worst, ba zai taba yafe Hadiza ta yi shiru tana mamakin Zurfin hankali irin na Fati, yarinyag karama sai tunanin manya. Ta ce, “Zan duba shawarar ki Fati, Allah ya kara. min YAKANAH, ya_ bawa ‘ya’yana tarbiyya irin taki. Ai dai za ki kula min dasu ko Fati?” Cikin kuka ta ce, “Yaya Hadiza ki daina yi min wannan maganar, bani da jarumtakar sauraron ta…… “, Ta ce, “Na rantse da Allah idan baki yi min wannan alkawarin ba nima ba zan bi shawarar ki ba”. Cikin makyarkyatar murya ta ce, “Eh…….eh……na yi alkawarin zan kula dasu”. Ta ce, “To nima zan bi shawarar ki, amma ba yanzu ba. Tashi sauke tukunyar can tana kauri”. Ta share idonta ta mike ta sauke, ilahirin jikinta sai rawa yake. Ta kashe komi ta maido Hadiza falo, ta yi dakin su ta rufe ta fada kan gadon su ta soma girka kuka. Ta ga kukan ba zai amfane ta da komai ba, sai ta je bandaki ta dauro alwala, ta shimfida sallaya ta soma Sallah, a kowacce sujjadarta tana yiwa Hadiza addu’ar Allah ya ba ta lafiya. Wayar Hadiza ta yi kara, a lokacin tana bisa sallaya tana azkar, don haka ba ta daga ba har ta tsinke. Sai ya yo tedt, ta dauka ta duba Sulaiman ne yake gaya mata suna bisa hanya har da Inna Halima za ta zo ta duba ta kuma za ta ga likita, don haka a gyara mata daki don za ta kwana biyu. Hadiza ta ji dadin zuwan Inna, domin Innar Sulaiman mutum ce har mutum, ma’abociyar raha da sanin mutunci. Don haka ta kira Fati a waya ta ce ta kara yawan abinci da ta aje a falo, ta kuma canza shimfidar gadon dakinta, don kullum a gyare yake Fati ba ta wasa da tsabtarsa. Tara na dare dai-dai suka shigo, Inna dauke da Muniba da tayi barci a kafadunta. Hadiza da Fati suka yi mata sauka ta ban girma. Sai lokacin kwanciya ne aka kai ruwa rana da Inna, don ta ce ba za ta zaunawa Hadiza a daki ba, sai tare da ‘yan jikokinta, dole suka kyale ta. Duk juyin da Inna ta yi a wannan dare, Fati take gani a kan sallaya, ta yi sallah, ta yi lazimi. Da asubahi kuwa ta soma rero (Suratul Yaseen) da sauti irin na Khusairi. Sannan ne ta dan samu barci. Karfe shida ta fada kitchen ta soma aikace-aikace, Inna na hankalce da damuwar da yarinyar ke ciki, ta rasa abin da ke damun ta kankanuwa da ita haka. To haka a washegari ma, har cikin kitchen wannan yarinya ba ta rabo da hijabi da carbi, tun tana burge ta har ta koma bata tausayi. Washegari litinin bayan sun yi kalaci, Inna da Sulaiman suka wuce asibiti in da za ta ga likitan ido, ba su dawo ba sai da rana ta take, yana sauke Inna ya juya. Sun fara cin abinci ita da Hadiza a kan darduma irin traditional carpet din nan na fata, an kuma shimfida ledar cin abinci. Don Fati ba ta cin abinci cikin mutane, loma ta farko, ta biyu, ta uku Hadiza ta soma kelayo amai kamar ta amayar da ‘yan hanjinta. Da sauri Fati ta shigo, Inna na rike da Hadiza, ita kuma ta kawo ruwa da roba Hadiza ta kuskure bakin ta. Fati ta sa moper ta gyare wajen, ta koma kitchen don hidimar abincin dare. Ko me take yi cikin kitchen bakinta ba ya rabo da ambaton Allah, duk a kan lafiyar ‘yar uwarta. Ita dai Inna haka nan ta ji Fati tana burge ta, tana bata sha’awa. Zahidah ce, babu duniya a gabanta, gata da dan banzan kyau da fata lafiyayya, amma ba sa gabanta, lahira take nema da harshen ta da goshin ta da gwiwoyin ta, ba ta furuci Sai wanda ya zame mata dole, ko in an tambaye ta. Amma a kwanaki bakwai da ta yi, Inna Halima babba ce mai cikakken hankali, ta lura Sulaiman ko ganin Fati a gidan shi ba ya son yi, don dai ba yadda zai yi ne, kuma bai son abin da zai bata ran Hadiza. Suna falo ita da Sulaiman misalin karfe sha daya na dare suna hira a nutse irin ta da da mahaifi, ta ce, “Wai ni mai sunan Malam me yarinyar nan kanwar Hadiza ta yi maka ko kallon ta ba ka yi? Dazu da safe ina kallo tana gayas da kai ka dauke kai ka fita, haka tun zuwana ban taba ganin ka yi mata magana ba, balle wasan nan irin na mijin ya da kanwarta. In kana wuri ta shigo sai ka tashi, in kana falo ta ganka sai ta koma ta yi ta zaman daki. Ita da ganin ‘yar uwarta sai in baka nan, mene ne manufar hakan?” Ya juyo yana kallon Inna ya ce, “Wacce yarinya kike magana?” Ta ce, “Fatima”. Yace, “Fati wai?” “Eh, ita”. Ya rausayar da kai ya ce, “Raini ne bana so, kuma ni ban iya wani wasan kanin miji ko kanin mata ba”. Ta yi sakale tana jin sa, ta ce, “Hala wani laifi ta yi maka? Har Hadiza na lura ranta yana baci da irin halin ko in kulan da kake yiwa ‘yar uwarta. Ban san ka da bakar zuciya ba, kada ka a fara a kan Fatima, domin mutum ce cikin ‘yammatan da babu irin su a yanzu, wannan yarinyar tana da halayen ‘yan aljanna, ka yi a hankali baka sani ba ko waliyya ce”. Shi abin ma sai ya ba shi dariya, ya ce, “A wannan kalatacciyar duniyar tamu dama akwai sauran waliyyai Inna?” Ta harare shi ta ce, “Dariya ma kake min?” Ya yi saurin cewa, “A’a, yi hakuri Inna”. Ta ce, “To ka gyara ma’amalar ku, zai fi kyau a ce akwai kyakkyawar alaka a tsakanin ku saboda Hadiza, in ta gaishe ka ka dinga amsawa cikin walwala da sakin fuska, wanda ya rike ibada ba ya wulakanta a duniya da Jahira. Baka sani ba ko ta fi ka matsayi a wajen Allah, ka canza takun ka a kanta, ai ba haka na ga kana yiwa su Ruma ba, to matsayin ta daya dasu a gare ka, ka ji na gaya maka”. Bai ce komi ba ya jawo wata hirar, don dai a sauya wannan. He is not interested at all (Fati is not the kind of person) wato ba ta daga cikin irin mutanen da yake son yin mu’amala dasu. Haka nan jinin su bai hadu ba, don yana son Ya, ba dole sai ya yi wata kakkarfar alaka da kanwar ta ba, bayan wadda musulunci ya ce, ai ba sa’ar wasan shi ba ce kanwar shi ce. Kwana bakwai din da Inna Halima ta yi jinyar Hadiza suke ita da Fati, komai ta ci sai ta amayar, ga zazzabi da ciwon kai mai zafi, sai ta rike kanta idan ciwon ya motsa mata tana wani irin kuka mai keta zuciyar duk mai imani. Sulaiman da farko bai sani ba, don ya dauka laulayin ciki ne irin wanda ta saba, kuma ciwon baya tasar mata da daddare lokacin da suke tare kenan. Ita ma Inna ta lura ta san laulayi ne na sabon ciki, amma wannan buga kan da Hadiza take yi a jikin bango da kukan da take yi na azaba ta fahimci akwai dai wani abun, amma tana ganin dukkan su likitoci ne sun san abin da ke damun ta, kuma ta ga Hadiza tana shan magani, sai ba ta yi magana ba, amma dai ba ta taba ganin irin wannan laulayin cikin ba. Don haka ta kara sati saboda lafiyar Hadiza wadda ta daina cin komai sai ruwan bakin lipton da ruwan tsamiya. Gaba daya ta rame ta fita hayyacin ta, ba ta taba yin cikin da yake wahalar da ita irin wannan ba. Tun Sulaiman bai gane ba har ya fahimci Hadiza ba ta da lafiya sosai, wannan ya wuce laulayi kuma wannan (migrain) yana bukatar bincike. A daren ya fito daga wanka yana tsane kanshi da dan kankanin towell, tana kwance rigingine a gefen gado, cikin doguwar rigar barci mai santsi mara hannu ruwan madara, kyawawan kafafunta da cinyoyin ta a mike sambal, a haka sai ka rantse lafiyar ta kalau ba ta tare da wata lalura. Son matarshi da kaunar ta na kara girgiza zuciyar sa, yana hargitsa gangar jikinsa. Ta kure fanka da A.C amma ba ta daina zufa (gumi) ba. Da sauri ya karasa zarga igiyar pyjamas din shi ya yiwa kanshi kyakkyawan matsuguni a bayan ta, ya daura hannu a kan goshin ta, zafi rau! Dole ya hadiye nashi bukatan ya soma ba ta kyakkyawar kulawa ta hanyar sanya karamin towell a ruwa yana goge mata kanta don zafin kan ya ragu. Sannan ya soma bin gabban jikinta da message don ta ji dadin kasusuwan ta. Ya juyo ta ya rungume ta yana furzar da numfashi da sauri da sauri, ya sake cewa, “Cikin kowanne hali, INA SON KI HADIZAH!”” Ta bude idanunta a hankali, wadanda suka kankance suka yi jawur tana kallon abin son ta, shi ma kallon ta yake kallon yaya zan yi da raina? Ya ce a galabaice, “Gobe zan dauko Dr. Bunza ya duba ki”. Gabanta ya yi wani irin faduwa, ta runtse idon ta da karfi ta ce, “Bana so, kada ka dauko shi, idan kuma har ka dage sai ka dauko shi to zan koma Karkasara’”. Ya girgiza ta da karfi ya ce, “What do you mean (me kike nufi)? In barki a gida kina ciwo ban nema miki magani ba? Ai Allah sai ya tambaye ni, tyayen ki da suka danka min ke su tuhume ni. Wannan ciwon kan bana wasa bane yana bukatar bincike”. Ta ce, “Ai ba yau na fara ba, kuma da na sha magani shi ke nan _ yake lafawa”. “Ina maganin? Dauko min in gani”. Ta ce, “Ya kare dazu, da safe nake shirin in aiki Fati ta siyo wasu”. Yace, “Wane magani ne?” Ta yi shiru. ““Tambayar ki nake yi, ina maganin? Ya ya sunan sa?’ Ta ce, “Panadol”. A mamakance ya maimaita “Panadol?” “Eh”. Ya ce, “You are silly ko in ce you are nonsense Doctor! I did not beliebe YOU… “(kina shirme, ke shashashar likita ce, ban yarda dake ba). Ya tashi a fusace ya fizgi waya ya kira Dr. Bashir, ‘consultant’ na ‘psychiatrist’, Surayya ce ta dauka, bai ko amsa gaisuwar da take mishi ba ya ce, “Ina mijin ki?’ Ta amsa “An kira shi a ‘emergency’ kuma ‘he is on call’ yanzu ya fita, ya manta wayar”. Ya kashe wayar ya cillar ya zauna a gefen gado ya dafe kai, Hadiza na kuka a hankali tana kara hargitsa shi, ya ce a fusace, “Enough…….is enough Hadizah! Ki gaya min fisabilillahi mene ne babbar matsalar ki?” Ta ce, A mamakance ya maimaita “Panadol?” “Eh”. Ya ce, “You are silly ko in ce you are nonsense Doctor! I did not beliebe YOU… “(kina shirme, ke shashashar likita ce, ban yarda dake ba). Ya tashi a fusace ya fizgi waya ya kira Dr. Bashir, ‘consultant’ na ‘psychiatrist’, Surayya ce ta dauka, bai ko amsa gaisuwar da take mishi ba ya ce, “Ina mijin ki?’ Ta amsa “An kira shi a ‘emergency’ kuma ‘he is on call’ yanzu ya fita, ya manta wayar”. Ya kashe wayar ya cillar ya zauna a gefen gado ya dafe kai, Hadiza na kuka a hankali tana kara hargitsa shi, ya ce a fusace, “Enough…….is enough Hadizah! Ki gaya min fisabilillahi mene ne babbar matsalar ki?” Ta ce, “Nifa na gaya maka laulayin ciki ne, Sai migraine wanda ba yau na fara ba, kuma ka san shi dama ina da magungunan da nake sha a kan shi, wannan zazzabin da haraswa laulayin ciki ne irin wanda na saba, zan gaya maka karya ne? Yau da bakin ka Sulaiman kake cewa baka yarda dani ba?” Jikinsa ya dan yi sanyi, ya rage sauti ya ce, “To ta ya ya zan ce zan kira likita da ya san matsalar ki ya duba ki ki ce a’a? Sai in dauka wani abu ne daban kike boye mini”. Ya yi mata wani irin murmushi da har abada ba zai gushe daga zuciyarta ba, ta dauke kai alamar ta yi fushi. Ya bi bayan ta a hankali ya kwanta, suna raba zazzabin tare. Akwai wani abu wai shi ‘hot kiss’ da Hadiza ba ta sani ba daga Sulaiman sai a yau, ya mantar da ita rashin lafiyar ta, ya dauke ta ya jefa a duniyar soyayya, ta manta cewa ita nakasasshiya ce, ta manta damuwar ta na cewa lafiyarta na hannun Allah, ta dauka cewa, tana a Dr. Hadiza ne ta baya. Ba za ta mance da wannan ranar da Sulaiman ya zubar da hawayen shi a karo na biyu a kanta ba. Na farko saboda ta nakasa, na biyu na dimbin soyayyar da yake yi mata. To wanne ne zai kasance na uku??? 2K KK OK I nna ba ta koma Bakori ba sai bayan watanni biyu, lokacin laulayin Hadiza ya ragu, tana yi mata dabaru irin na manya har ta samu sauki. A lokacin cikin ya shiga wata hudu, sannan ne laulayin ya tsaya. Sannan ciwon kanta ya jima bai tashi ba, saboda Dr. Bunza ya sauya mata magani, Fati ce ke zuwa ta karbo ba tare da sanin Sulaiman ba. Ganin ciwon ya dade bai tashi ba sai Hadiza ta watsar da shawarar Fati ba ta gayawa Yaya ba, shi dama SuJaiman tuni ta binne shi ya kuma yarda cewa migraine take. Cikin Hadiza wata bakwai, ya fito ya yi tororo kamar watanni tara. Haka za ka ganta fus! A cikin wheel chair tasa cikin a gaba tana kallo tana mamakin sarautar Allah, wanda ya ga damar ta haihu a cikin halin da take ciki. So da kulawa wurin Sulaiman kamar ya yi mata nakuda. Watan Aprilu ya kama, wanda ya yi dai-dai da EDD din ta, cikin dare wani azababben ciwon kai ya tashe ta, ta soma bubbuga kanta a jikin gado, kafin a yi haka ta yi dogo suma jini ya kece kamar da bakin kwarya. Duk wani kokari da zai iya shi ne kiran Dr. Abdullahi ko Dr. Surayyah a waya, amma hannun shi ya kasa kama wayar saboda dimaucewa. Sannan shi ya manta kansa balle ya yi tunanin wane irin taimako zai ba ta a matsayin shi na cardiologist wanda kuma ke da general knowledge a kan komai. Sai ya sunkuto ta ya nufo harabar gidan, ya shimfidar a bayan mota. Malam Ilu ya wangale mishi ‘gate’ ya fita, cikin ranshi yana cewa kai wan nan yarinya kina cikin jarrabawa kalakala, Allah ya baki lafiya. Da taimakon innalillahi…….. da yake ta ambato ya samu nutsuwar da har ya iso AKTH, aka karbe ta a bangaren ta wato dakin haihuwa, su Dr. Surayyah, Dr. Abdullahi suka rufu a kanta, ba ta san inda kanta yake ba. Suka soma ba ta duk wani taimako da ya dace don ta haihu da kanta kamin su yi bincike a kan wata matsala daban da suka hango wadda da alama dadaddiya ce. Amma duk iya kokarin su sun tabbatar da ba za ta iya haihuwa da kanta ba, don haka suka miko mishi takardu don ya sanya hannu a shiga da ita tiyata. Da kyar yake iya sarrafa ‘yan yatsun shi a lokacin da yake rattaba hannun, zuciyar shi ta riga ta bushe da tashin hankali. Yana tsaye aka turo ta a kan gadon daukar marassa lafiya zuwa dakin tiyata, bai yi tunanin gayawa kowa ba sai da safe, kasancewar ba shi da nutsuwar yin hakan. Da ya ga wannan ba za ta yi mishi ba, sai ya nufi ofishinsa ya murda kofar ya shiga, ya jingina da kofar ya soma tunanin wasu al’amura da ya lura Hadiza na boye mishi, da yawan waya da take yi da Dr. Bunza na mene ne? Sannan da kwayoyin maganin da ya gani a leda babu suna babu takardar su a karkashin gadon su. Ya yi wani irin huci mai zafi, “Akwai wata matsala wadda da alama dadaddiya ce”. Ya tuno furucin Dr. Abdullahi. A sukwane ya bude kofar ya fita ya nufi ofishin Dr. Bunza a psychiatry. Dr. Bunza na rubuce-rdubuce a file suna hira da Dr. Karaye, Dr. Sulaiman ya bankada kofar ofishin ba tare da ya yi sallama ko neman izinin shigowa ba, ya kai wa Dr. Bunza shaka ya ce, “Gara in kashe ka, kafin ka kashe ni….”. Dr. Karaye ya soma kokarin kwatar Dr. Bunza wanda ya sha_ shaka matuka, duk idanun sun yo waje. Ya ce, “Ba zan cika shi ba, sai ya gaya min abin da ke damun matata, da magungunan mene ne yake dirka mata?” Dr. Bunza ya ce, “Ka yi hakuri Dr. Sulaiman mu yi maganar cikin nutsuwa”. Ya samu ya sake shi da kyar ya koma kujerar sa yana gyara wuyan rigarshi, yayin da Sulaiman ya yi mishi kerere a kai, idanun shi a jujjuye, shi dai kawai so yake ya ji mene ne matsalar Hadiza? Dr. Karaye ya ce, “Ka yi hakuri ka zauna Dr. Bakori, Dr. Bashir ba zai cuce ka ba…… – Ya juyar da juyayyun idanunsa a kan Karaye, “Akwai wata cuta wadda ta wuce wadda ya yi min? Matata na dauke da cuta shekara guda amma bai taba gaya min ba? Ya biye mata suke yi min rainin hankali, na yi kama da wanda bai je makaranta bane Dr. Karaye?” Dr. Bunza ya ce, “Ba haka bane Dr. Bakori, ina bisa aikina ne, akwai sirri tsakanin likita da petient din sa, wannan shi ne hujja ta. Sannan Dr. Hadiza na da tata huyar, ta boye maka cewa tana da (brain cancer) don samar maka da kwanciyar hankali, ta ce idan ka ji babu kai babu sauran kwanciyar hankali, kuma nima na yarda you are not taking things easy (ba ka daukan abubuwa da sauki). Ka bini a hankali in maka bayani”. Ya kunna computer inda (record) din Hadiza yake yana nuna masa yadda ciwon ya ci karfin ta a yanzu, da irin taimakon da ya ba ta. Shi kan sa Bunza sai da ya yi hawaye balle gogan, wanda gudun jini ya katse a jijiyoyin jikinsa. 2K 2K 2 K arfe shida na safe Dr. Surayyah ta fito da jaririyar da aka cirowa Hadiza, kamar ta daya da Baban ta kamar ya yi kaki ya tofar, har duhun kalar nashi ne. A lokacin ne jama’ar gidan su Hadiza suka iso, Dr. Surayyah ta sanar da su. Fati karfe bakwai na safe ta iso asibitin, ta baro yaran da Alti ta zo a (keke-napep). Dai-dai lokacin da aka turo Hadiza za a mai da ita ICU, ya yi dai-dai da sanda Surayyah ta mika mishi jaririyar ya ki amsa, sai Fati ce ta amsa. Za a wuce da Hadiza ta rike hannun sister Magajiya ta rada mata cikin nishi, “Ina son yin magana da su…..”. Don haka sister ta dakata. Sulaiman da Fati suka garzayo gareta, kowanne ya fita hayyacinsa. Fati rungume da jaririya tsantsan tana ta tsala ihu. Itama Fatin Kukan take.Hadiza ta runtse ido hawaye na zirara, ta ce, “Fati ina alkawarin mu?” Cikin Kuka ta ce, “Yana nan Yaya Hadiza”. Ta kama hannun Sulaiman ta hada da na Fati, duk su Malam Ja’afar na kallo, ta ce, “Fati har da shi a alkawarin fa………. Ta yi sharbe ta yarfar da majina da hawaye ta ce, “In kula da shi? Yaya Hadiza ai shi babba ne?’ “Babba ba ya _ bukatar kulawa Fati…… ?” Ta ce, “Ban sani ba”. Ta ce, “To yana bukata, shi ma kamar Munib ne, bambancinsu shine shi Munib kulawar UWA yake nema, shi kuwa Sulaman kulawar MATA yake ne Ta yi murmushi ta runtse idonta, cikin azabar da take dandana. Sulaiman ya russuna ya sumbaci goshinta, “You will get well soon Hadizah…… , bana bukatar kulawar kowa sai taki, in ba taki ba na yafe, zafin ciwo yake sa ki yin irin wannan magana……… Ta girgiza kai ta kara manne hannun su ta ce, “Sulaiman-Fati………… ” Dr. Bunza ya karaso ya tura gadon da kanshi yana ta yiwa sister Magaji fada. Yaya ta karaso ta karbi ‘yar da ke hannun Fati ganin tana neman kwala ta da kasa. Dr. Sulaiman ya mai da hannun shi cikin aljihu, yana so ya yi kuka amma idanun sun bushe kamar soyayyar gyada marau-marau. Sai Malam Ja‘afar ya iso gare shi ya kamo hannun sa suka zauna tare, yana cewa, “Karbi ‘yar ka sa mata albarka”. Amma Sulaiman ya ki, sai kirjin shi da ke ta kai kawo kamar zuciyar ta ballo allon kirjinsa ta fito. Ana shigar da ita cikin computer don a yi hoton kwakwalwar ta kamin likitocin su san me za su yi a kai, ta soma ta yi salati rai bakon duniya ya yi halinsa. “Allah ya ji kan Dr. Hadizah!” Abin da dukkanin likitocin suka furta kenan, a lokaci guda suna share ambaliyar hawaye daga idanuwan su, tare da kai hannu su rufe mata idanun ta. 2K OK KK A n bawa Malam Ja’afar da Sulaiman gawar Hadiza cikin mota ambulance, zuwa nan unguwar Karkasara. Inda daruruwar jama’‘a suka yi jana’‘izar ta. Mijinta da Mahaifinta suka sanya ta a kabarin ta, suna masu yi mata addu’ar fatan alheri, yafiya, afuwa da addu’ar Allah ya yi mata masauki da aljanna, Annabi ya san da zuwan ta. Su kuma ya basu imanin jurewa. Sulaiman ya baiwa kowa mamaki, saboda yadda ya tsaya a kan jana’izar Hadizah, babu ko digon hawaye a idanunsa. Ba su san shi kansa kukan na zuwa ne idan an san abin da ake yi ba. To bai san me yake yi ba, bai san halin da kwakwalwarshi ke ciki ba. Ya san dai kawai Hadizar sa ta rasu, sun kaita makwancin ta na gaskiya, bayan wannan bai san komi ba, bai san kansa ba, bai san a ina yake ba. Ya dai bude ido ya gan shi a gidan su Hadizah, dakin Mukhtar, ba ya rintsawa, yadda ya ga rana haka yake ganin dare, ya wuni yana_ karbar ta’aziyyar ‘yan uwa da abokan arziki. Tun a ranar Inna Halima, Malam Sulaiman da sauran kannen shi suka zo Kano, da su ake karbar gaisuwa har zuwa kwana uku. Ranar lahadi suka juya Bakori cike da juyayin halin da Sulaiman ke ciki. Malam ya ce zai dinga aiko mishi da rubutu tsayin kwana bakwai. Ya ce, “To”. Wadda ta zama kalma mafi saukin fada a bakinsa, sai kuma bin kowa da ido, amma abinci da ruwa wannan kwanan shi uku bai dandana su ba. Alti ma tana gidan ita da yara wadanda suka damu kowa da tambayar ina Momin su? Alhamis aka yi sadakar uku, Alti ta koma kauyen su tana kuka da hawayen ta, ta ce sai ranar sadakar arba’in za ta dawo. Tambaye ni ina baiwar Allah Fatima Ja’afar Mai-Yadi? Tana can dakinta tana kuka, tana fama da jaririya, bini-bini ta hada madarar (SMA) ta dura mata, ta ba ta ruwan zam-zam. Ba ta barin ta tayi kuka, idan ta bata madarar da ruwan sai ta sa ta a baya ta goye, ta zauna ta yi ta jijjiga ta, har sai ta samu barci, ta sakko ta ta sanya ta a gadon ta, ta zauna a gabanta ta yi ta girka kuka. Idan kukan ya ishe ta sai ta bude littattafan addu’o’in ta, ta yi ta karantawa tana rokon Allah ya kai ladan makwancin rabin jikin ta Dr. Hadiza Ja’afar MaiYadi. Mutuwar Hadiza ta girgiza kowa a gidan nan, haka duk wanda ya santa ya koka ya gode Allah. Kada Dr. Surayyah ta ji labari, to ina ga wanda farin cikin rayuwar sa ya ta’allaka a wuyan ta? Ya ke kwana da ita yake tashi da ita, yake yi mata son da ko iyayen ta sai dai su ce su suka haife ta? Don haka Doctor Sulaiman-Sulaiman Bakori, yana cikin wani irin hali da duk masoyinsa dole ya koka masa, in har yana da imani, ya bishi da addu’ar Allah ya ba shi dangana da YAKANAH! Tuni Mukhtar ya koma Kaduna, ranar da aka yi bakwai shi ma Malam Ja’afar ya ce ya koma bakin aikin sa. Ya bishi da “To”. Kamar yadda yake bin kowa da ita. Ya tattara ya koma gidansa, shi kadai kwal kamar maye. Sai da ya gwammace da bai dawo ba, a lokacin da ya ci karo da wheel chair din Hadiza da kayan ta dake watse a dakin barcin su, a nan ne komi ya dawo masa danye, karo na uku da ya soma kukan da ya tabbatar har abada ba zai daina ba. Haka ya kulle kansa, ba shi da abinci sai ruwan lipton wanda yake dafawa a kettle ya dura a flask ya wuni yana sha, babu ko tunanin sa sukari. Cikin kwanaki ashirin da mutuwar Hadiza ya zama babu kyawun gani, kasumba ta cika fuskar sa. Duk wannan gayun ya daina shi, wanka ma ba kullum yake yi ba sai ya ji alamar jikin shi na dan wari-wari, ya kashe wayoyinsa gaba daya, ya yi sallama da aikin sa, amma bai fasa kwana yana yiwa Hadiza addu’a ba. Uwa, mahaifiya, duk ta rasa sukuni, tana can Bakori, hankalinta na Kano, ta san cikin kowanne hali Sulaiman yake yana cikin halin da yake neman matallafi. Kuma cikin halin da yake bukatar mai tausar sa, nuna masa kauna da kulawa. Don haka yau ta tambayi Malam Sulaiman cewa za ta taho Kano wajen Sulaiman. Ya ce hakan ya yi. Yana zaune a falo, daga shi sai wata dukunkunanniyar jallabiya ruwan makuba, da kofin ‘tea’ a hannun shi da ‘remote’ yana_ = kallon _tashar Saudiyyah, inda suke gabatar da sallar magariba. Aka danna kararrawa wajen sau biyar kamin ya yunkura ya aje kofin a kan side table ya bude kofar. Inna Halima ce tsaye cikin atamfa holland ta sha lullubi da koren mayafi kalar atamfar ta, har ranshi ya ji dadin ganin ta, ya ba ta hanya ta wuce cikin falon, ya tsuguna ya gaishe ta. Ba ta amsa ba sai kallon shi take cikin al’ajabi, “Haka ka lalata kanka Sulaimanu saboda Allah? To wannan rashin tawakkalin da kake shi zai dawo da Hadiza duniya ko me? Ka sani Hadiza ta riga ta koma ga mahaliccin ta, ba za ta taba dawowa ba, ka fuskanci rayuwar da take jiran ka a gaba, ka zamo mai YAKANAH cikin duk halin da ka tsinci kanka. Tsakanin ka da Hadiza yanzu addu’a ce, ba wannan lalata rayuwar ba. Idan Hadiza tana raye, ba za ta so ganin ka haka ba, ka yi hakuri mai sunan Malam. Shin yaushe rabon ka da cin abinci?’ Ya sunkuyar da kai bai yi magana ba. Ta jawo ledar da ta shigo da ita ta fiddo ma’adanan abinci guda biyu, ta bude ta tura masa, tuwon shinkafa ne lafiyayye da miyar taushe ta ji nama zuku-zuku, ta ce, “Cinye maza ka bani kwanon”. Ba musu ya dauka ya soma ci kamar Allah ya aiko shi. Inna ta mike ta soma tattare bolar falon, ta share shi tsaf, ta shiga dakunan ta gyare ko ina, ta wanke masa toilet. Sanda ta gama ya dade da yin barci a carpet, ta zauna a gefen kansa tana tofa masa addu’a. Yana tashi ta ba shi rubutun da ta zo da shi cikin jarka ya sha, ya mai da kai kan tuntun ya koma barci. Bai tashi ba sai la’asar, ta je bandaki ta hada mishi ruwan wanka cikin kwami, ta dawo falon ta same shi ya idar da sallar la’asar, ya mike kafa yana kallon ceiling, ta tsuguna a gabansa ta ce, “Tashi ka je ka yi wanka, ka shirya muje mu ga mai sunan Hadiza”. Wannan karon ma bai yi musu ba, ya mike ya je ya yi wankan, ya zubo farar shadda dinkin Mohammed, ya dora hula fara sol amma bai fesa turare ba, ya fito ya tadda Inna ta idar da sallah tana lazimi. Ta yi addu’a ta shafa, ta mike suka fito harabar adana motoci, duk motocin sun yi kura futuk! Alamar an dade ba a taba su ba. Ya sa key ya fiddo motar dai-dai inda Inna take, Malam Ilu ya karaso da sauri ya gaida Inna, ya sa ‘duster’ ya karkade motar cike da jin dadin ganin yau Ubangidansa ya fito, wanda yake kwana cikin wannan gida shi kadai ransa, sai dai yana tausaya masa, don ya san rashin matar kwarai kamar Dr. Hadiza ba karamin abu bane. Inna na baya shi kuma yana tukin suka nufi unguwar Karkasara. A dai-dai titin asibitin AKTH kamar an ce da Inna ta juya, ta hango Fati rike da hannun Munib da Muniba cikin kayan makaranta tana tare tasi, da alama ta dauko su ne daga makaranta. Da sauri Inna ta ce, “Ka ga Fati can tana tare mota, yi kwana mu dauke su”. Ya yi kamar bai ji ba, ya karawa motar shi gudu. Inna ta yi salati ta ce, “Baka ji ni bane? ‘Ya’yan ka fa ta dauko daga makaranta!”. Sai a sannan ya juya, tuni ta tare tasi suna kokarin shiga. Ya ce, “Ai sun shiga mota ma hadu a can”. Inna ta yi shiru tana mamaki, har suka iso gidan su Fati ba su shigo ba, don ba za ka hada motar gida da ta haya da ke yin tsaye-tsaye ba. Tun daga soron gidan yake jiyo kukan Baby Nana Khadijah. Ya rintse ido tsigar jikinshi na tashi. Inna ce ta yi sallama ya biyo bayan ta. Yaya suka tarar tana ta fama da Baby Nana, wadda ke ta tsandara kuka kamar ta tsaga gidan ta ki karbar madarar da take bata. Ta amsa musu sallama cikin sakin fuska da walwala, ta shimfida musu sabuwar tabarma, sannan ta mikawa Inna Baby Nana. Yaya ta dubi Sulaiman ganin yadda ya rame ya yi kasumba, sai ta ji hawaye sun ciko idon ta. Ta ce, “Me nake gani haka ni Sa’adatu? Su Da sauri Inna ta ce, “Ka ga Fati can tana tare mota, yi kwana mu dauke su”. Ya yi kamar bai ji ba, ya karawa motar shi gudu. Inna ta yi salati ta ce, “Baka ji ni bane? ‘Ya’yan ka fa ta dauko daga makaranta!”. Sai a sannan ya juya, tuni ta tare tasi suna kokarin shiga. Ya ce, “Ai sun shiga mota ma hadu a can”. Inna ta yi shiru tana mamaki, har suka iso gidan su Fati ba su shigo ba, don ba za ka hada motar gida da ta haya da ke yin tsaye-tsaye ba. Tun daga soron gidan yake jiyo kukan Baby Nana Khadijah. Ya rintse ido tsigar jikinshi na tashi. Inna ce ta yi sallama ya biyo bayan ta. Yaya suka tarar tana ta fama da Baby Nana, wadda ke ta tsandara kuka kamar ta tsaga gidan ta ki karbar madarar da take bata. Ta amsa musu sallama cikin sakin fuska da walwala, ta shimfida musu sabuwar tabarma, sannan ta mikawa Inna Baby Nana. Yaya ta dubi Sulaiman ganin yadda ya rame ya yi kasumba, sai ta ji hawaye sun ciko idon ta. Ta ce, “Me nake gani haka ni Sa’adatu? Sulaiman me ya yi zafi? Hadiza ba ta yi gaggawa ba, muma jiran namu wa’adin muke. Karbi ‘yarka tunda ta zo duniya baka taba daukar ta ba, ita kuma laifin me ta yi? Ka zamo mai YAKANAH, wannan ba shi ne karshen rayuwar ka ba!!”. Inna ta mika mishi yarinyar, ya fi karafin mintuna uku kamin ya karbe ta, ya kura mata ido yana mamakin kamannin shi da ita har sun fi nashi da Munib. Dai-dai sanda Fati da yaran suka shigo cikin sallama, tana sanye da katon hijabin ta har kasa mai hannaye, rike da lunch bod din yara da jakunkunan su. Cikin nutsuwa ta tsuguna har kasa ta gaida Inna, ba tare da ta kalli Sulaiman ba ta ce, “Ina wuni?’ Bai amsa ba, ita ma ba ta tsaya sauraron ya amsa ba ta wuce ciki. Ai Munib da Muniba suna ganin Baban su suka fada mishi suna ta tsallen murna, ya mikawa Inna Baby ya zaunar dasu duka a cinyoyin sa, suka soma ba shi labari iri-iri, duka rabi ‘AUNTY FATI’ ta yi mana kaza, ta yi mana kaza. Yana jinsu bai ce komi ba. Malam Ja’afar ya shigo hannayen shi rike da manyan ledoji yayo cefane ciki har da madarar SMA da Nana ke sha, ya kwalawa Fati kira ta fito ya bata. Sai a sannan ya lura da bakin takalma har da na namiji a kofar dakin Yaya, ya ce da Fati, “Waccan madarar ta kare ne?” Ta ce, “Eh, saura kadan”. Ya ce, “To ki dinga gaya min kafin ta kare ba sai ta kare kaf a barta tana kuka ba”. Ta ce, “Ai masassara take shi ne take kuka, amma dama gobe zan kaita asibiti”. Ya ce, “To Allah ya sauwake, ke kuma Allah ya ba ki ladan hidimar da kike yi da ‘ya’yan ki, ya sa suji kan ki kamar yadda kika ji kan su, ya kai rahama kabarin mahaifiyar su”. Ta ce, “Amin Baba”. Shi ma Sulaiman da ke can daki yana jin su ya ce “Amin”. A zuciyar shi. Malam ya daga labulen ya ce, “A’a! Ashe Inna ce, barka da zuwa kin sha hanya, ya ya aka baro Malam?” Ta amsa, suka ci gaba da gaisawa suna hirar ‘yan jikokin su, tare da kara yiwa juna ta’aziyya. Malam Ja’afar ya dubi Sulaiman sosai ya ce, “Ina maganar aiki ta kwana?” Ya yi shiru kanshi a sunkuye, can kuma ya ce, “Zan koma gobe insha Allahu”. Malam ya ji dadi, ya kara mishi da nasiha mai sanyaya zuciya. Ba su baro gidan ba sai karfe biyar na yamma, bayan Inna da Yaya sun yanke shawarar yaran za su ci gaba da zama a nan saboda ya fi kusa da makarantar su. Har za su tafi ya dubi Yaya ya ce, “Duk abin da ake bukata Yaya, don Allah a gaya min”. Yaya ta yi murmushi ta ce, “Me ake bukata ban da madara? Bayan ita babu abin da zai gagara da izinin Allah”. Ya ce, “Duk da haka ina son sanin sauran abubuwan da ake bukata, ai ragi-ragi ne”. Ta ce, “To ka tambayi Fati”. Ba don ranshi ya so ba ya nufi kofar dakin nata. hijabin a jikinta, kwayar idanun su ta hadu, ya yi saurin dauke kansa don gani ya yi kamar Hadiza, hatta digon tauwadar Allah da ke kan tsinin hancin Hadiza akwai shi a tsinin hancin Fati. Zuciyar shi ta yi wani irin mummunan bugu, don gani ya yi tana rikide mishi Hadiza sak, kasancewar bai taba ganin ta babu hijabi ba. Ya tsaya daga bakin kofar hannun shi duka biyu zube cikin aljihu. Da kyar yake magana kamar an tilasta mishi, ba tare da ya kara kallon ta ba. “Na tambayi Yaya abubuwan da yara suke bukata, ta ce in tambaye ki?” Kanta a kasa ta ce, “Sai ko pampers da madara”. Yace, “Bayan su ba wani abu?” Ta ce, “Eh, amma malamar su ta ce akwai prize gibing day ranar asabar kuma ana son iyayen yara su je”. Sannan ta dauko report card na yaran na wannan zangon ta mika masa. Garin karba hannayen su suka gogi juna, sannan suka kara hada ido a lokaci daya babu wanda bai jia jikin sa ba. Ita tsoro ta ji, shi kuma ji ya yi kamar hannun Hadiza. Bai ce komi ba ya karba ya sanya a aljihun shi ba tare da ya duba ba, bai kuma ba ta amsar zai je ko ba zai je ba ya fita. Ya tadda Inna har ta fito suka tafi, ya bar Fati cikin tunani. Ta zauna a gefen gadon ta, ta sauko Nanah wadda ta samu barci ta rungume cikin hannayen ta, tana tunanin me Hadiza ke nufi da ta ce ta kula da Baban Munib? “….Munib kulawar Uwa yake nema, Sulaiman kulawar MATA yake nema….”. Ta tuno kalaman Hadiza. To ai ita ba matar shi ba ce, ba gidansu daya ba, ta ina za ta kula da shin kada rashin Hadiza ya tagayyara shi? Wannan baudadden mijin nata dake yi mata kiyayya maras dalili? In har Hadiza na nufin ta auri mijinta ne wanda ba ta fito baro-baro ta fada ba, sai hannunka mai sanda da ta yi mata, ta hada ta da wani al’amari da ba zai taba yiwuwa ba. Ba ta fata, kuma kada Allah ya tabbatar ta yi tarayya da Hadiza a kan abin da take so, ta tafi ta bari ba don ba ta so ba, sai don hukuncin Allah wanda ya fi karfin dan adam ya yi jayayya da shi. Hakika ta dauki alkawarin da ba ta san yadda za ta yi ta sauke shi ba. kK WwW ashegari da yamma sai ga Inna ta kara dawowa, Dr. Sulaiman ya kawo ta, Hamza da Abdulyassar suka shigowa Fati da katon na madarar SMA, katon na diapers da himilin shopping na kayan masarufi da kayan biskit da choculate da su Indomie wanda su Munib ke zuwa makaranta da su. Ta adana kowanne a inda ya dace, Inna ta ce ya je sai dare ya zo ya dauke ta. A lokacin Malam Ja’afar ya iso da shi da Inna da Yaya suka kule a daki, suka sakayo kofa, me suka ce me suka ce oho, sun dai dade suna magana kafin ya dawo ya dauki Inna su wuce, kasancewar a gobe zata koma Bakonri, ya biya ta Jifatu ya yi mata sayayya mai yawa kamar yadda ya saba, ita da Malam da sauran kannen shi, suka wuce gidan sa. Inna ta tuka mishi tuwon semobita da miyar ganye ya ci, ta takura mishi ya bude wayoyinsa. Yana budewa sakonnin ta’aziyya daga |ikitoci ‘yan uwansa da sauran abokan arziki ya soma tittidowa cikin wayar. Sannan ana neman shi a ofishin (Chief Medical Director) na AKTH ranar litinin. Don haka yana kai Inna Bakori suka gaisa da mahaifin shi bai tsaya ba. Da zai tafi Inna ta ce, “Ni kuwa akwai wata magana muhimmiya da nake so mu yi, ga shi na ga alamar kana sauri”. Yace, “Gaskiya kam ina cikin sauri, sai ko idan na dawo”. Ta ce, “Shi ke nan Allah ya kiyaye hanya, ya kara maka hakuri da YAKANAH, ya shige maka gaba a kan al’amuran ka, ya yi maka musayan alheri”. Har ransa ya ji dadin addu’o’in Inna, wata nutsuwa ta kara shigar shi, son mahaifiyar shi ya kara shigar shi. Ta ce, “Ina so zuwa sanda za ka dawo in ga canji, kamar yadda ka yi min alkawari, in ganka a likitanka ba mai sunan Malam ba”. Murmushi ya yi, wanda rabon shi da yin shi tun wani karni can da ya shude. RR KK L itinin, ya isa ofishin CMD, sun dade suna tattunawa a kan wani aiki na dashen zuciya da za a yiwa ministan lafiya. Yana daya daga cikin likitocin da zasu gabatar da aikin. Ya koma office dinsa ya daidaita komai ya ci gaba da aikin sa, cikin karfin zuciya da neman rinjaye a kanta. Sai ya zamto yana jin dadin aikin sosai, don yana debe mishi kewa, yana hana shi zama shiru har maraicin matarsa ya gallabe shi. Ya tarar da tulin ayyuka da yawa, don haka ya zamo busy a satin gaba daya. Ranar alhamis ya saci jiki ya je yayowa ‘ya’yan shi siyayya ya biya ta makarantar su ya gansu, lokacin da aka fito cin abinci, a karkashin wani benci ya zauna ya rungume su suna ta labari, ya bude ‘kit-kat’ yana basu suna ci suna yi mishi hira. Tun suna damuwa da rashin Momin su har sun hakura sun dangana sun daina tambayar ta. Munib ya ce, “Daddy ba ka zo (prize gibing) din mu ba, kowa Baban shi ya zo banda mu”. Ya kama kunnen shi cikin nunawa yaron amsa laifin sa, ya ce, “I am bery-bery sorry….. aiki ne ya yi min yawa. To wa ya kawo ku?” Suka ce, “Aunty Fati, ta yi mana kwalliya ta kawo mu”. Ya ce, “Aunty Fati ta kyauta!”. Suka yi murmushi. Ya ce, “Nedt year ba zan sake ba”. Aka kada kararrawar komawa aji, suka fella da gudu suka nufi ajinsu, ya bisu da kallo yana murmushi cike da kewar su. Hakan yake yi duk sanda ya samu sararin aiki, ya daina zuwa gidan don kar ya ga Fati, tana tuno mishi da wasu al’amura msu yawa a kan Hadiza. Sannan ba ya son wata alaka take shiga tsakanin su, shi ma kuma bai san mai ya sa ba, ya danganta hakan da rashin haduwar jini. Ita kuma ta danganta hakan da wulakanci da raina mata wayo, yana ganin ta kamar ba ta san abin da take yi ba, bayan in da wanda ya san ciwon kansa a duniya to ita ce. Sai dai tsarin rayuwar su da ya banbanta, kowa da irin nashi tsarin rayuwar, don haka ita ma ta yi kamar ba ta san yana zuwa makarantar yaran ba, bayan kuma suna gaya mata. Ana i gobe sadakar arba’in din Hadizah, Malam Sulaiman, Inna Halima da Baffanin Sulaiman guda biyu, Malam Surajo da Alhaji Umar suka iso gidan Sulaiman a Kano, a daren suka bukaci ya kai su Karkasara. In da ya ajiye su da daddare ya wuce asibiti, da cewar zai dawo ya dauke su. Manya sun kule a falon Baban Hadiza, wato Malam Ja’afar suna magana ta hankali har da Yaya da Inna. Yaya ta ce, “Ni bana jin Fati sai shi Sulaiman, anya zai yi na’am da al’amarin nan?” Malam Sulaiman ya yi murmushi ya ce, “Kune baku san Sule ba har yanzu, yana da wani hali tun yana yaro, abin da zai so sai ya fara kin shi tukunna. Ga yadda mahaifiyar shi take bani labari, babu jituwa ko ya ya tsakanin sa da Fati, ita kuma ta kama kanta ba ta shiga shirgin shi. Mu dai burin mu ku bamu hadin kai, Allah ya gani muna son zuri’ar gidan nan, muna son zumunci ya ci gaba da gudana kamar yadda aka faro. Fati ita ta fi cancanta da ta rike ‘ya’yan ‘yar uwar ta, don a wannan zamanin da wuya a samu macen da za ta rike maka ‘ya’ya har uku duk son da take maka. Sannan mun yaba da hankali da tsarin rayuwar Fati, muna sa ran yara za su tashi da kyakkyawar tarbiyya har zuwa girman su. Fati ba za ta dauwama a gida tana bautar ‘ya’yan ‘yar uwarta ba, dole watarana za ta yi aure. Ranar da hakan ta faru ya ya Sulaiman zai yi da yaran nan? Ga shi suna karatun su mai kyau a nan balle mu tafi dasu Bakori. Fati ita ta fi cancanta da ta maye gurbin ‘yar uwarta a zuciyar Sulaiman. Don haka muna neman hadin kanku, yardar ku da amincewar ku Malam Ja’afar. Shin an bamu Fati? Da karfin mu muka zo, gobe muke so bayan an shafa addu’ar Hadiza a daura auren Sulaiman da Fatima”. Malam Ja’afar ya ce, “Tun kafin ku yi wannan tunanin na riga ku yin sa, kun dai riga ni furtawa ne. Tabbas duk matar da Sule zai aura nan gaba ta rike mishi marayun shi ba kamar Fati ba, wadda ta san ciwon su, tasan ciwon ‘yar uwarta. Sannan Hadizah ta yi wani abu a ranar da za ta koma ga mahaliccinta, wanda ya tsaya min a rai kwarai, ta kama hannun Sulaiman ta hada da na Fati, sai dai ban ji me suke cewa ba. Fati yarinya ce mai biyayya, ba za ta tsallake umarnin mu ba, amma kamar yadda Sa’adatu ta ce ne, da kyar idan shi Sulaiman din zai amince. Sannan ya wuce matsayin da za ace za a yi mishi aure ba tare da sanin shi ba”. Alhaji Umar ya ce, “Kubar wannan a hannun mu, kamar yadda Fati take mai biyayya, shi ma Sulaiman mai biyayya ne, iyayen shi basu taba saka mishi kara ya tsallake ba. Ina da yakinin zai yi biyayya ga mahaifin shi, kuma a daren nan zamu sanar da shi ba sai gobe ba. Ga sadaki naira dubu ishirin ga goro, daga aljihuna ni waliyyin sa. Jikina ya bani alheri ne zamu kulla, don irin wannan auren na son zuciyar iyaye ba karamar falala ake samu a cikin shi ba”. Kowa ya jinjina kai. Yaya ta ce, “Nima a daren nan zan sanar da ita insha Allahu””, Da haka taron ya tashi, ya yi dai-dai da sallamar Sulaiman a falon, dukkanin su suka amsa fuskar kowannen su cike da walwala da annuri. Malam ya ce, “Faduwa ta zo dai-dai da zama kenan, ita ma Fatiman a kirawo ta”. Yaya ta tashi ta fita don kiran Fati. Tana yiwa su Munib shimfidar kwanciya goye da Nana, Yaya ta yane labulen dakin ta ce, “Fati kin kwanta ne?” “A‘a, ina harama dai”. “To biyo ni dakin Malam yana son magana da ke”. Ta sauke goyon ta zurma hijabin ta, ta bi bayan Yaya har dakin Malam. Ta sha mamakin ganin taron dakin har da Baban Munib, wanda ke can sunkuye da kai a gefe. Ta yi sallama cikin sassanyar muryar ta dukkan su suka amsa, ban da Sulaiman wanda ya fara shan jinin jikinsa kan wannan taron domin shi aka yi. Jikinsa ya yi sanyi, gaban shi ya soma faduwa, haka nan gwiwoyinsa ya jisu kamar an rarrade su da murfin kwano. Ta samu gefen Inna ta zauna, ita ma jikinta ya soma kyarma don ba ta son a tirke ta a cikin mutane. Iyayen dai na duban su suna nazarin kowannen su, sun fahimci dukkan su a firgice suke, amma firgitar ta fi karfi ga Sulaiman. Wannan taro na mene ne? Malam Sulaiman baya _shiga kankanuwar magana. Sai da suka tabbatar sun dan samu nutsuwa sannan Malam Sulaiman ya dubi dansa ya ce, “Mai sunana wani abin alheri ne za mu yi maka, da fatan za ka karba hannu bibbiyu”. Bai yi magana ba, amma ya dago ya dubi mahaifin sa. Ya ci gaba da cewa, “Muna kara yi muku ta’aziyya, sannan muna so ku sani cewa, duk abin da Allah ya tsara akwai hikimar yin hakan a cikin sa. Mun zauna mun yi tunani, mun yi shawara mun yanke cewa, Fati za ta maye gurbin ‘yar uwarta a gare ka, ku ci gaba da raino da_tarbiyyar ‘ya’yanku kamar yadda mahaifiyar su ta fara yi musu, kuma ‘yar uwarta ta karbe ta. Allah ya riga ya hada mu, zuri’a ta hada mu. Don haka Sulaiman bana son ka da wani aure in dai ba jinin gidan nan ne ya kare ba. Za mu yi alfahari daku idan kuka taushi zuciyoyin ku kuka yi mana biyayya. Allah zai nunawa Hadiza har cikin kabarin ta cewa, ke Fati kin rungumi iyalinta, kin rungumi mijinta baki bar rashin ta a rayuwa ya tagayyara shi ba. Sannan kai Sulaiman Hadiza za ta yi farin ciki idan har ya zamto ka rungumi amanar rayuwar ‘yar uwarta ta hanyar aure, muna neman hadin kan ku, za mu samu Fatima da Sulaiman?” Da a ce Malam Sulaiman ya lura, da ya ga irin jibin (zufar) da ke ambaliya a fuska da jikin Sulaiman, yayin da gudun jini ya katse a jikin Fati, idanuwanta suka juye suka kada suka yi jazur, hanjin cikinta ya dunkule waje daya ko dan yatsanta ta kasa dagawa balle ta motsa bakinta. Tana addu’a cikin zuciyarta idan mafarki take Ubangiji Allah subhana ya yi gaggawar farkar da ita. Sai dai a bangaren shi Sulaiman, ya so a ce shi da iyayen shi ne kadai su kai wannan maganar, da a take zai ce dasu idan kasa da sama za ta hadu bai amince ba. To an ce wai ko mutuwa tana kunyar iyaye, balle iyayen Hadiza? Ya zai yi ya iya ya budi baki a gabansu ya ce baya son jinin Hadiza? Shi tunda ya rasa Hadiza bai kara tunanin nan gaba zai kara yin aure ba, bai kara tunanin wai yana da future ba, balle ya yi tunanin yin aure. Kuma a rasa wadda za a aura masa sai wannan yarinyar da bai san a matsayin da ya ajiye ta a zuciyar sa ba. Duk da yadda take hidima da ‘ya’yansa, Fati ba ta taba burge shi ba, Allah bai sa masa kaunar ta a zuciyar sa ba, sannan kuma wai auren ma daga yin arba’in din Hadiza? Sannan da shakikiyar ta? Fati ba ta taba burge shi ba balle ya so ta, bai taba tunanin irin ta a matsayin matar shi ba. Ya ya ma za ai wannan kidahumar yarinyar ‘yar sakandire ta maye gurbin Hadiza? Ta ya ya mahaifan shi suke tunanin zai iya rayuwa da kanwar Hadiza? Ya yada girman sa ya yi mu’amalar aure da ita? Kwarai ya fahimci abin da Hadiza ke nufi tsakanin shi da Fati a ranar da Allah zai dauki ranta, amma (he is sorry to say) ba zai iya cikawa Hadiza burinta ba. In don ‘ya’yan shi ne a ba shi abinsa ya rike ko ya bai wa Inna, ba sai an makala mishi auren da bai san ya ya zai yi da shi ba. Malam Ja’afar ya ce, “Duk kun yi shiru, ko da yake shirun alamar amincewa ne, To ku tashi ku je Allah ya yi muku albarka, dama mun sanar daku ne kada sai gobe ku ji an daura aure ku ce ba a sanar daku ba. In kuma akwai mai magana to ya yi, a shirye muke da mu bai wa kowannen ku hakkin sa”. Inna tana murmushi ta dubi Sulaiman ta ce, “Ni na san mai sunan Malam ba zai ki abin da muke so ba”. Jikinsa ya yi sanyi kalau, ya nemi duk wata hujja da zai bayar ya neme ta ya rasa. Zuwa lokacin Fati ta mike za ta fita, juwa na kwasar ta, da dafa bango ta samu ta bar falon. Ta yi dakinta ta dauki ‘yar jaririyar ta wadda ke ta tsala kuka a dalilin ta manta ba ta sa mata gidan sauro ba ta fita, sauro ya hana mata barci. Shi ma bai yi magana ba yana jin su suna ta kida suna rawar su na addu’o’’l, sa albarka da fatan alheri a gare shi. Gwiwa a salube ya fito jikin mota ya baro su suna ta sallama. Mu tara a littafi na 2. Kuma na karshe inshallahu. Wanda tare suke da dan uwansa. Maman Safah da Marwah ce, ke yi muku fatan alheri. c a _=> – = – —= _= —= – > Advertisements