﻿
Compiled By Umar Dalha Funtua.

Copied By Shooly





🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼

            *_YAA SHEK_*

🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼  




🌈 *kainuwa writers asso*🤝🏻

*_BY : U.K.Y for real_*

*_Dedicated to Mmn khaery_*




 ```Assalamu Alaikum yan uwa musulmi wannan littafin nawa nayishine ba Don wata ko waniba ko Don cin zarafin wani ba aa kawai sai Don nishadi ,fadakarwa da kuma wa'azin tarwa ina fatan yadda na fara lafiya na gama lafiya```



              1⃣to5⃣


Tashin kira'ar Yaa shek ne ke tashi tun kafin ka karyo kwanar islamiyar mai suna Sahsib kasancewar Allah y hore mai murya gaza'ki ga balaga, kowanna harafi yana fitarwa bisa ka ida

 d'alibai ne a zaune cikin wani aji, matasa ne maza d mata jikin su sanye da uniform maroon color suna zazzaune kowa d al'quran a hannun sa sun nutsu suna sauraran karatun


 shikuwa malamin nasu wato Yaa  shek yana kan wani benci yana ta rero karatun cikin kwanciyar hankali da nutsuwa idon shi alumshe saboda shauki, da ka yake karatun kasan cewar shi hafizin al qur'ani,

sanye yake da wani  hadaddan yadi milk color yasha guga, da wata hula brawn,kasan cewar aykin dake jikin kayan ma brown ne, kannan yasha gyara sumar nan baka kirin tayi luf luf da ita takalmin ma brown ne yasha mai sai kyalli yake wandon nan a d'age kai daka gani kasan sunna ta ratsashi ga wani gemu mai ban sha'awa yazauna das dashi sai 'kamshi yake kanagani kasan cikakken mai tsaftane,


Yana kaiwa karshe wata aya yace sadakallahul aziim kafin ya 'Dan nisa yadago kyawawan manyan idanun shi yana kallon yan ajin d'aya bayan d'aya yai gyaran  murya yace lokacin fitasalla yayi karfe hud'u da minti biyar duk Wanda bai shigoba to kuwa bazai shigoba yana kaiwa nan ya mike yafita 

Ayko yana fita mazan da matan suka hau shewa suna cewa yaaaa sheeek d'aya daka cikin yan matan ce tai magana tana cewa kunga kutashi muyi sauri mu dawo Don ni wlhy dana rasa lecture din yaa shek gara nai zazzabin wuni Don nasan idan na rasa dolene sai nayi 

Caraf wata tace ayke zazzabi ma kikace da sauki wata tace nidai wlhy idan namakara zama zanyi naita kuka har sai yace nashigo, ayko kinsan yaa shek ba cewa zai yi kishigoba Don haka kunga tafiya ta ayko  gaba daya yan ajin suka rufa mata baya,


 suna zuwa wajen sallah wasu yan mata biyar sukawo Kansu d'aya daga cikin yan matan nan tace wayyo kunji dadin Ku yau yaa  shek a ajin Ku yake wata takuma cewa kai kugayama na yau wani kalar wanka yayi d'aya tasake cewa nima abinda nakeson ji kenan d'aya daga cikin wayanda yaa shek yafito daga ajinsu tace wai saurin mekuke? nagadai zaku ganshi sai kujira yafito daga office naga kuma Idan a ajin Ku yake bakwa gaya mana Don haka kujira suna cikin haka kuwa saiga yaa shek yafito daga office,
yana takawa cike da kasaita d gayu  yana goge fiskandhi da wani Brown hankacif da alama alwala yayi ayko suka bishi da ido  





Afilin makarantar d'aluban sukeyin sallah Don haka tako ina dalubai ne suna jira atayar da sallah   



Yaa shek matashi ne mai shekaru ashirin da bakwai 'Dan gayu ga tsafta uwa uba ilimin addini da na boko masanin hadisai da littafan addinin islama ya gama degree dinshi a usman dan fodiyo university sokoto ya karanci 'bankaran hadisai da zamantakewar aura tayya hakan ne yasa hukumar makarantar suka bukaci yadinga yima d'aluban da zasuyi sauka lecture duba da yadda aure yake mutuwa da wuri a wannan zamani Don haka d'aluban keson ya shiga ajinsu saboda yadda Yaa shek yake warware musu zare da abawa ga daukar wanka, 
wasu daga cikin daluban sonshi suke wasu kuma burgesu yake ajin yan sauka guda biyu ne  Don haka yau idan yashiga daya gobe sai ya shiga daya cikakken sunan sa kuwa Abdallah Gaddafi a makaranta ne d'alubai ke ce mai Yaa shek batun aykin gwamnati kuwa yana nema saidai har yanzu shiru,




Sauri sauri suke saboda su koma bayan kowa ya hallara saiga Yaa shek yashiko yana shikowa duk suka nutsu sabada sun san bayason hayaniya kuma yana iya korar mutun  

Bayan yadai daita zaman shi ne a kan bench din ne yace kundai San dokokina ko?kuma kunsan hukuncin Wanda yasaba min Don haka ba bukatar na mai mai ta suka hada baki wazen fadi na'am yaa shek 


ya nisa ya cigaba da bayani daga inda ya tsaya jiya. 

Baki iya hiraba baki iya kwalliya ba baki iya shagwa'ba ba baki iya komai ba kuma kina korafi wai lado baya dawowa gida da wuri to taya zai dawo d wuri bayan in ya dawo d'in ma yasan kayan haushi zai gani, 
kuna kallo a tb an nuno wani dan wasan kince wai ke wannan gayan yana burgeki duk a gaban lado yo ba lado ba ko ni ne sai na shanbe ki ina mijinki kice wani yana burgeki agabana ta yaya kuke tunanin aure bazai mutuba?  


duk yana maganane yana kallon gurin d 'yan matan ke zaune Don dasu yake, kafin ya dawo da kallonsa gurin mazan yana mai cewa 


"kai kuma lado baka iya siyan brush ba baka iya shiyan acuci maza ba baka iya siyan kayan kwalliyaba inzaka shigo gida kazo rannan abace, kana tsamin daud'a kashige gansan gansan ba fara'a,tayi tayi da kai kayi wanka kace kai baza kaiba sannan kuma kazo kana mata Yar murya idan dare ya tsala" 



ayko duk d'aluban dariya suka sa kasa kasa Don kar yajisu,
  haka tsarinsa yake yayin lecture idan zai bada misali akan namiji sai yace lado idan mace ce sai yace kande ,

shikuwa ko ajikin sa da irin wannan Jan hankali da nasihohi lokacin tashi yayi yayi musu addu'a ya fita sannan d'aluban kowa ya watse,
 saida yashiga office y dauki littattafan sa sannan ya kama hanya yayi gida.
[21/04, 9:59 a.m.] Shooly: 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼            
                   
                 *_YAA SHEK!!_*

🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼


*BY:U.K.Y.       for real*😘



🌈 *kainuwa writers asso*🤝🏻

*_dedicated TO mmn khaery_*🤝🏻








                     5⃣to1⃣0⃣



Z,aune suke a tsakar gidan nasu, ummee da abdulmalik da abdul majid suna kan tabarma,


Shi kuwa yaa shek yana gefen  su akan wata katuwar sallaya,  waya ce a hannun shi  yanajin wa'azin Dr Zakir Naik, 

Ummee ce ta kalleshi tace Abdallah wai baza kaci abincin bane? 

Nace a kawo ma abinci kayi shiru,

 ummee nah zanci mana, 

 ay nazata baza kaci bane da naji kayi shiru, abdulmalik  jeka ka dauko mai abincin shi ya nanan a flas sai ka dauko cokali d flet, 


Kawo masa abincin yai gaban sa ya ajiye ya koma ya  zauna,  

dago kai yayi ya  kalli k'annan nasa wato su abdulmajid,sannan yace "wai kuwa ma kunyi hadda ne kukazo kuka zauna kuna wa muta ne surutu?"


Nidai nayi  inji Abdulmalik, shi kuwa abdulmajid cewa yayi ni saida asuba zanyi yaya Abdallah wlhy idan nayi yanzu ba zai zauna ba, 


umme ce tace bazai zaunaba?!  dama bakaso yazauna ba ne.   sai asuban tayi Ay  ta tashinka kaki tashi makaryaci,   wai saida asuba kamar da gaske,

Shidai Abdul majid bai sake cewa komai ba don bayaso a ja zancen da yawa ga ya Abdallah agurin, yasan Zane mai jiki zaiyi don ya Dade da fuskantar ya abdallah 'kyaleshi kawai yakeyi amma yasan sarai ba kararun yakeba.


Acikin su ukun Abdul majid ne yake da wasa ba shida maida kai a karatu, amma alamu sun nuna Abdul malik zai biyo hali irin na yayan nashi wato Yaa shek.

Shima Abdallah shiruyayi da kudurin zai gyarawa yaron nan  zama a zuciyar shi,


Suna zau nan ne kowa yayi shiru suka jiyo kuka a ma'ko tansu,   da suke Katanga d'aya da su, wato gidan kanin babansu baffa usman mai rasuwa



ihu take tana kiran yayyo ummee nah wayyo yaya Abdallah nah kuzo kutai makeni nidai wlhy bazan ci ba,


Ummee ce ta ce ikon Allah waye kuma yake dukan min yarinya a cikin daran nan?


Abdul majid ne yana dariya. yace wlhy ba wani duka in kin bibiya ma'kiyin ta  akace taci   wato   tuwo  shine  take  wannan ihun
 kamar ana yankata, sai kace  bakusan halin  *Jidda* ntaku ba,

Wlhy kuwa  inji Abdul malik  yana 'kyal,kyala dariya shima


To ay sai a 'kyalemin yarinya ko a dafa mata indomie din nata data keso ko? Yariyar nan da gaske take batason tuwon nan tunda idan tacima sai tayi aman sa don haka sai a kyale ta,   kai Abdul malik  jeka ka gani mene ne idan tuwan ne baza taci ba ka kawo min ita ga abincin yayan kunan tunda bai ciba sai a d'iba mata,


Yaa shek da tunda yajiyo ihun Jidda ya kasa kunne yanaso ya gane me take cewa don yasan dalilin kukan nata don in akan cin tuwo ne bazai sa baki ba ace yarin ya wai baza taci tuwo ba sai kace ba mace ba ay halin rayuwa ake gudu idan babu halin a dafa mata abinda ranta  yakeso to ayi yaya kenan?


amma duk da haka bazai iya jure jin kukan nata ba saboda bai son kuka balle ma kuma kukan Jidda Yar rigima,



Kai abdulmalik zo kazauna bari na dubo ummee,    yawwa Abdallah zeka kaji.




Yana fita ya fad'a gidan yayi sallama sai da aka amsa akai mai izini sannan ya shiga, (abunka da masu koyi da koyar war annabi Muhammad wato sunnah)



Kafin ya gama shigowa Jidda tayi maza tayi gunsa tana shashshe'kar   kuka    tana ajiyar zuciya kamar wadda akaiwa dukan kawo wu'ka,



A'a baba na Kaine kunjiyo kukan wannan ja'irar ko? 

Samu guri kazauna tana nunamai tabarma, zama yayi sannan ya gaishe ta, 

Kaga baba nah wlhy ko yatsa ban d'ora    a kantaba kawai tuwo na bata nace ta ci shine take wannan ihun tafiso idan na dafa tuwan na dinga   bi makota ina asanmin abincin na bawa Jidda ko kuma  in nemo mata wani abun, duk da ita yarinya ce amma ay kullum girma take kuma koba dad'e ko ba jima.    gidan wani zata.




Hakane mamy kiyi hakuri sai a hankali zata ci ne, yadaga kai ya kalli Jidda da ta make kafad'a ta cuno baki Dan bakin nan mitsil dashi alamun ba 
ranar da zata ci tuwan ,  

       yace ke,    to sami guri kizau na, ayko ta   bare   mai   baki   zata Dora a inda ta tsaya, 

Mamy     tace baba nah baci za tai ba kyaleta kawai kar ta Tara mana jama'a ,   haka take  cemai baban ta saboda su nan baban ta abdullahi.





To shikenan mamy bari naje dama  ummee ce  ta ce azo aduba ko lfa, 
yamike   zai tafi,


 ayko Jidda tace  batasan    zancen ba ita sai ta bishi  don  idan   yatafi   mamy   Zane  ta   za  tai,



Itadai mamy    da kallo  tabi ta don  halin  Jidda sai   addu'a.



Harta rigashi kaiwa zaure tana gaba yana ba ya yaiwa mamy sallama ya fice.


Ta  riga shi  shiga gidan don haka ya hango ta akan cinyar   ummee  tana   ta  zuba  ta'barar  ta dama  halin Jidda ne, 



Ummee nah nidai agidan nan zan kwana yau mamy  tace   saita   Zane    ni  saboda  banci   tuwo  ba, 

  kai jiddo   banda sharrifa inji Abdumajid, 

Ayko tahau shure shure ummee nah kinji wannan yaya abdulmajid din yana cemin jiddo ko? Ta karashe    maganar tana   nuna Abdulmajid da  yatsa  cike  da  shagwa'ba  da  ta'bara,


Abdulmajid banason tsokana  wlhy zan sa'ba maka akan  tsokanar yata da  kake  yi,

To nima sai na rama wool bai iya hadda ba tana nai gwalo ,


Ayko takashe bakin abdulmajid yai shiru an ta'bo maganar hadda,


Abdallah bai sa musu bakiba donshi ta'baran jiddan ma mamaki yake bashi , yafara cin abincin shi da tun dazu da aka ajiye mai,  

tsilum saiga Jidda agabanshi ,  yaya Abdallah nah  abinci  zakaci? Nima zanci, amma nidai a baki zaka bani takarasa maganan kice sa shagwa'ba 

Kallon ta kawai ya tsaya yanayi yacigaba da cin abincin sa 


Ummee kinga yace wai bazai bani ba 

Kafin ummee tai magana ya zuba mata wani razanan nan kallo mai ma'anar ki shiga taitainki fa, 

Ayko tsiiit tayi tana kallon sa kuri da ido, candai dataga ba bata zaiyi ba tace don Allah na ci?



"Jeki wanko hannun ki "

Ba musu raje ta wanko hannun ta tadawo



Yabita da kallo azuciyar  shi  yana tunanin  kai yarinta kenan wai mutun yanajin yinwa amma wai yace bazaici tuwoba  wai   sai  abinda   ya  taza'ba,  ummee ce ta katshe mai tunani tana tambayar shi Abdallah kunyi waya da abii kuwa?


Eh ummee munyi ay goben zai dawo ko ko yasake shawara ne?  


   A'a goben zai dawo dama natambaye Kane ko bai gaya maba,

"Ok ya gayamin ummee Allah y dawo da shi lfa"



"Dukansu suka amsa da amin"

Itako zuwa tai ta zauna jikinta har rawa yake tasa hannu ta fara ci,

Saida suka cinye na fleet dinne yake tambayarta ko ta koshi ,   tace,  a'a  yakara mata shikuma ya tashi yaiwa   ummee     sai da safe  ummee   tace   Allah   ya tashe  mu lfa.           

Yanufi dakinshi dake  zaure ,


Ikon Allah kai bakace  dakin matashin   saurayi  bane  kamar haka ba ,


Dakin bawani babba bane amma  tako ina carpet ne ashinfide da 'Yar durowa ajikin bango mai biyu,     sai    d'an  mirror da turarurruka  kala kala amma dai  bawasu  masu  tsada  ba , sai katifa  dai dai kwanciyar mutun biyu ya lailaye ta da bed shit  da wata anger ta  rataye kaya,   d'akin  fes fes dashi  sai 'kamshi yake kamar dakin budurwa budurwar ma mai tsafta,lol



Kayansa ya rage ya sa jallabiya  sannan ya kuma nufar cikin gida don watsa ruwa da d'auro alwala don  haka tsarinsa yake baya konciya sai da alwala ,     


koda yashiga  har su abdulmalik sun shiga dakinsu ummee ma tadauki Yar rigimarta sunshige, don anan ta bingire bayan tagama tsokanar abdulmajid tai bacci,



Bayan ya gama ne yakoma d'akinshi  ya cire jallabitar ya fesa body spree  yasa wayanshi a chage yai addu'a yakwanta   hadida  addu'ar Allah y sa kar yayi  mafar kin  nasa na  jaraba,

      shi yana mamakin wannan Abu  ace rana d'aid'ai ne ba zaiyi mafarkin yana Tarawa da   mace ba  shidai yasan  bawai yasa son mata  aransa  bane  kuma  yana  azumi litinin da alhamis  kuma  yana kokarin kauda  idon  sa ga duk abinda  zai  sashi jin  shaawa don kare  addimin sa da imanin sa don gudun sabawa mahaliccin sa  



Eh  bazaice baya son kasan cewar mace a kusa  da  shiba saboda yasan shi lafiyayyan namiji ne,


 amma yasan  ba  abu ne   mai yiwuwa ba kasancewar  bashida  ayki  kuma albashin sa na Sahsib islamiyya bawani mai yawa bane,


         kuma abii ma ba wani karfe ne dashi ba sai dai rufin ashiri duk da yasan abii mutum ne mai kokarin   yaga  yarufawa  iyalin asiri,
             

ga iyalan 'kanin shi baffa usman wato     mamy   da jadda duk shi yake dawainiya dasu duk   da  dai tasu dawainiyar ba mai yawa bace saboda mamy tana Yar   sana'arta   don    itama   taga tarufawa kanta   asiri  amma duk da haka bazai iya bijiro da zancen aure   ba   shiyasa  yake kai   zuciyar shi  nesa.




Da ire iren wannan tunani bacci yayi gaba dashi....
[21/04, 9:59 a.m.] Shooly: 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
                  *YAA SHEK!!*

🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼


*BY:U.K.Y.          for real*😘


        🌈 *kainuwa writers asso*🤝🏻


*dedicated to mmn khaery*🤝🏻



            1⃣0⃣to1⃣5⃣

Koda ya farka karfe hud'u dai dai duk da cewa ya makara tashi sallan dare, amma fa aykin gama yariga ya gama, abun dai da bayaso shi yagani,


Ya Allah wannan wace irin jaraba ce abinda ya furta kenan,

Nifa bansan ma nayi mafarkin ba amma dai gashi alamu sun nuna,    duk shi kadai yake wannan zancen  kamar wani zautacce,

Goge jikinsa yayi yana nai addu'ar kar Allah y sa ummee ta ganshi idan zai shiga wanka don kusan kullum sai ta ganshi kuma ba karamar kunya ce take kamashi ba,   don  yasan  duk  Wanda yaganshi  yayi  wanka da asuba to kuwa yasan me  ya faru d shi,don ma dai   Abii   ba mazauni bane da kunyar sai tafi haka , 

Futowa yayi yana sand'a kamar 'barawo bakin shi d'auke da addu'a,

 ya samu yai wuf yafada toilet sannan yasauke nannauyar ajiyan zuciya saboda ummee bata ganshi ba,


Saidai baisan shine bai gantaba amma ita ta ganshi, don tazo d'akinsu Abdul Malik taga ko sun tashi, tana fitowa ne ta ganshi yana sand'a,

ta koma d'aki zuciyar ta cike da tunanin wai meke damun abdallah,


 kusan kullum sai yayi wanka,to komadai meke damun shi saidai yasama ranshi hakuri don aure ba yanzu ba, shida bashi da ayki.


Bayan yafito agurguje ya shirya yanufi masallaci, 



"Abdul Malik wai bazaku fito Ku karya bane lokaci yana kurewa? Inji umme 

" ummee gamu nan zuwa"


To Ke kuma Jidda aydai yanzu kin bushe ko saikizo nashafa miki mai, 

Turo baki tai tana ma'ke kafad'a "nidai nizan shafa da kaina, wankan mafa na iya kika ce saikin yi  min"

Naji to jeki shafa kifito ki karya inji ummee, 


Suna karyawa ya shigo sai lokacin yadawo saga masallaci, ya  nemi guri kusa da ummee ya zauna yana gaishe ta,

Fuskan ta dauke d fara'a tace lafiya klau abdalah,

 kana azumin kuwa yau alhamis?

A kunyace yace 
"Eh ummee inayi"

 To da kyau madalla Allah ya muku al barka, 
"Suka amsa da amin"

Su Abdul Mali suka gaishe shi shima ya amsa yana mai cewa kuyi Sauri kun kusa makara fa, 


Kafin suyi magana sukaji sallama, mamy ce tashigo hannun ta dauke da uniform din Jidda,


 suka amsa mata, tazauna suna gaisawa da ummee ,     suma duk suka gaisheta ta amsa cikin fara'a  ta Dora da cewa amma dai waccan Yar rigimar ita tashafa wannan man?  tai maganar tana kallon inda jidda ke  zaune da daurin kirji Wanda tayi da 'Dan kwalin ummee,


Ayko su  Abdul Malik suka kyalkyale da dariya, ganin yadda fuskan jiddan take maiko



Sukuwa manyan yara wato Jidda Yar aji daya a primary an sha Vasilin a fuska sai maiko take , kuma ko ahikin ta,


 ta dago ta kalle yaa shek Wanda tunda ya gaishe da  mamy yamai da hankalin shi kan wayarshi,  tace


"  yaya abdallah batajira amsar shiba tadora da cewa gaskiya nidai  yau Kaine zaka kaini makaran ta, idan muka tafi dasu yaya Abdul malik dukana sukeyi suce wai bana sauri,kuma basa Shiga dani makaranta a bakin layi suke barina, ta'karasa maganar har da 'Yar kwallar ta.


'Dago kai yayi yana kallon su rannan abace   yace mai yasa kuke dukan ta?


Wlhy 'karya takeyi yaya idan muka tafi da ita bata sauri , taita bata mana lokaci,yaya don Allah kawai tunda makaran tarsu banisa tadinga tafiya ita kadai, tunda idan yawanta yatashi har gaba da makarantar tasuma tana zuwa,  



Many tace aykuwa dai ingun gama kuringa tafiyar ku, zanje ay gurin auntyn taku nace taringa zaneki idan kin makara,
Karbi uniform dinki ni kisaka, 

ta karba tana bubbuga 'kafa, 

Ummee tace 'karfa Ku takurawa auta ta,  zonan na sakamiki kinji,


Takarba tasaka mata tace abdallah zo kakai ta tunda tace kai zaka kaita ,

Bamusu yatashi ya rike mata hannu suka fita, suma su Abdul majid suka kama hanya, 


Ahanya ne tasa mai kuka wai itasaiya d'auketa, bayadda ya iya haka ya d'auketa,


 saboda shi fa duk 'kan 'kartar Jidda idan tana wannan shagwa'bar ta ta sai yaji wani iri kuma hankalinsa yana tashi matuka.


                 Asalin su Jidda da Yaa shek!...
[21/04, 10:00 a.m.] Shooly: 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼

           *YAA SHEIKH!!*

🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼

*BY:U.K.Y.         for real*😘

     🌈 *kainuwa writers asso*✍🏻

*dedicated to mmn khaery*🤝🏻

_Note: masoyana ina mai   ba Ku  ha'kuri don zakuga spelling d'in rubuta sunan littafin nan ya sauya daga Yaa Shek zuwa Yaa Sheikh,amma hakan ne ya kamata ya zama ,ina godiya gaduk kan masoyana, nima  aylobiyu Lodi lodi_.🤣

*Special tanx to*:

Ummy Abduol,Ummu farheen and Aunty Fauziyya.

         1⃣5⃣to2⃣0⃣

Malam Gaddafi da wato Abii mahaifin Yaa sheikh, da kuma malam Usman mahaifin Jadda, 'yan uwan juna ne uwa d'aya uba d'aya suke.

Mahaifiyar su Hajiya Laila  Shuwa ce ita 'Yar garin Borno, shi kuwa mahaifinsu Alhaji Mahi d'an 'kasar Sudan ne.

Kasancewar ba inda aure baya kai mutum ne yasa ya kai Hajiya Laila kasar Sudan ,bayan auran ne Allah ya azurta su da yara biyu wato Gaddafi da Usman, Gaddafi shine babba sannan Usman.

Usman yana da shekara d'aya Allah yayiwa mahaifin su wato Alhaji Mahi rasuwa, k'warai rasuwar ta jijjaga Hajiya Laila da 'yan uwan Mahi.



Bayan ta gama takaba ne ta shaidawa 'yan uwan Mahi  Zata koma kasar su Borno,basuji dad'i ba matu'ka,  amma ba yadda suka iya dole ne ta tafi tunda dama ba 'Yar 'kasar Sudan ba ce.

Haka ta koma Borno ita da yaran ta, da al'kawarin duk sanda ta samu lokaci zata Ke kawo musu ziyara, tana kuka haka suka rabu tana kewar mijin ta,tana mai addu'ar Allah ya ji'kan mijin ta.

Bayan tadawo Borno ne ta koma family house d'in  su kasan cewar ita din ma marainiya ce haka dai take zaune gidan, yau da dad'i gobe babu,mutun d'aya ne take gani taji dad'i  wato 'kanin ta Abdallah shine ya ke 'kwantar mata da hankali.



gidan daga daga 'kannan baban ta Sai matan su hakadai take zaune,  saboda babban burinta bai wuce taga yaranta sun sami ilimin addini da na boko ba.



Alhamdulillahi burin hajiya laila yana cika,  ta tsaya tsayin daka wajan ganin yaranta sun samu ilimi, don kuwa sun sauke al kur'ani,kasan cewar su yara masu haza'ka, inda Gaddafi yake aji shida a primary shi kuma Usman yana aji biyar, yanzu kuma abunda yake damunta bai wuce rashin auren 'kanin na taba wato Abdallah.

To kana taka Allah na tashi 'kwatsam Sai ciwan ajali ya riski Hajiya Laila,tace ga garin Ku Abdalla 'kaninta yayi kuka  haka su Gaddafi shida Usman.


Dan haka Abdallah ba shiri ya fara Neman aure saboda yasan wahala su Gaddafi zasu sha idan ya barsu a family house d'in nasu, ammafa ranshi ba dad'i yaso yayar tashi taga auran nashi.


Ba'a d'au lokaci ba yasamu yarinya Yar manyan mutane,mai tarbiyya itama shuwa ce , mai suna khadija ,bayan sun dai daita ne aka yi aure.



Bayan auran da wata biyu ya d'auko Gaddafi da Usman suka dawo gabansa inda yaci gaba da d'aukar d'awainiyar su na makaranta da kuma tarbiyyar su, kuma itama  Khadija bata da matsala tana kula dasu tsakani da Allah. 


Bayan wani lokaci itama Khadija wadda ayanzu su Gaddafi suke kira da hajiya kamar yadda suke kiran Hajiyarsu kafin ta rasu, ta haihu ta samu 'yarta mace kyakkyawa da ita,inda taci sunan Hajiya wato Laila.


Haka suka cigaba da zama cikin so da 'kaunar juna, su Gaddafi suna son   Laila shiyasa ma itama Khadija keson su.




Kwance tashi ba wuya don Gaddafi da Usman sun gama karatun su,itama Laila ta girma tana secondary.


Gaddafi da Usman sun fara kasuwanci suna saro kaya a kano suna kawowa Borno kuma ba laifi Suna samun alheri, da hakane har suka sami uban gida.

Kasuwanci su ya bunk'asa inda suka daina kawo kaya Borno Sai dai su siyar a kano, idan suka zo kano basa komawa Baron Sai 'karshen sati.

A hakane har Allah ya ha'da Gaddafi da Aysha wato  ummee, Gaddafi yazo ya sami baffan sa Abdallah da batun aure, baffa Abdallah yaji dad'i yakuma bashi shawaran ya Gina gida a can kano saboda yawo a moton yayi yawa gara su zauna guri d'aya.


Haka kuwa akayi, gadan gadan suka fara gini a kano a unguwar gandun albasa, gida biyu suka gina, d'aya na Gaddafi d'aya na Usman duk da dai shi ba auran ne a gabansa ba.


Aka daura auran Gaddafi da Aysha duk lokacin da suka samu dama kuma suna zuwa Borno. 



haka har Aysha ta haihu ta sami namiji aykuwa Gaddafi yasa ma yaro sunan baffan sa Abdallah, yaro kyakkyawa dashi ga shiga rai, Sai yafito sak kyawawan Sudan d'innan hanci har baka, baffah Abdallah yaji dad'i matu'ka,awannan lokacine kuma baffa ya takurawa Usman sai ya fito da mata, da Usman yaji baffan nashi ya matsa masa ne yafito ya fad'a mai gaskiya shifa Laila yakeso, ay kuwa wannan abu ya yiwa baffa dad'i' haka hajiya ma don tasan Usman zai ri'ke mata tilon  'Yarta ta don daga kan Lailan bata kuma haihuwa ba.




Ba 'bata lokaci akayi aure aka kawo wa Usman amaryarsa Laila.



Aysha taji dad'i sosai saboda acewarta ta samu 'Yar uwa, ayko tasamu d'in don  Laila bata da matsala kullum Abdallah yana hannunta saboda mai sunan baban tane kuma gashi kyakkyawa.


Bayan Abdallah yayi shekara Tara ne aka yi mai 'kani Abdul majid,  Abdallah yanazuwa makaranta kuma yana da ko kari, yana da shekara Taran ne ya haddace alkur'ani .




Itadai lailah shuru Allah bai kawo haihuwaba amma itada Usman sunata addu'a  suma Allah ya basu.

A haka rayuwa ta cigaba da tafiya inda Aysha wato  Ummee ta kuma haihuwa shima na miji aka samai suna Abdul malik.


Bayan wasu 'yan lokaci Allah ya amshi addu'ar Usman da Laila inda su ma Allah ya basu 'yarsu mace Inda taci suna Jidda yarinya kyakkywa son kowa 'kin Wanda ya rasa fara tas da ita kana ganinta kaga jinin Shuwa ga kyau ga gashi.




Jidda tana da shekara uku  Allah ya yiwa Usman rasuwa, kai wannan rasuwa ta gigita su musamnan Laila wato mamy da kuma Abii,haka shima baffa da hajiya ,Abdallah shima yaji mutuwarnan sosai ita kuwa Jidda bata da wayo don haka bata San ma me a keyi bama. 


 Bayan Mamy ta gama takaba baffa yace "ta koma gida" amma Sam Abii yaki Yar da a cewarsa ay ko ba matar Usman bace ita ba ay  ita k'anwar  sa ce shi mai iya rike tane kuma Dama tana 'Yar sana'ar ta gashi sun saba kawai ta zauna idan Allah ya fito mata da miji tai auran ta, haka baffa ya ha'kura ya kyale ta.


         *Cigaban Labari*
[21/04, 10:00 a.m.] Shooly: 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼

             *YAA SHEIKH*

🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼

*BY:U.K.Y.       for real*😘

       
      🌈 *kainuwa writers asso*✍🏻

*Dedicated to mmn khaery*🤝🏻

            2⃣0⃣to2⃣5⃣

Haka suka 'karasa makaranta Yana d'auke da ita a kafa'da, ya kai ta har cikin makarantar tasu sannan yace,


"Saura kuma idan antashi ki tsaya a hanya kina wasa"

"Nima bazan tsaya wasa ba ay yau Abii zai dawo zai kawo mana kayan dadi ko?"

Yace mata "eh kiyi karatu da yawa"

Ya juya ya fice daka makarantar.

Bai tsaya ko inaba sai gidansu Bilal.

Bilal abokin Yaa Sheikh ne tun suna yara haka kuma tare suke karatu saida su kazo university ne Yaa Sheikh ya tafi sokoto shi kuma Bilal Yana kano, shima Bilal yanzu haka bai samu ayki ba kuma shima malami ne a Sahsib islamiyya.


Yaa sheikh Yana zuwa ya tarar da Bilal a 'kofar gida Yana duba wani littafi, ya 'karasa shima ya zauna sannan suka yi musabaha fuskar Bilal dauke da murmushi, amma fa ta Yaa Sheikh cike take da damuwa kuma Bilal ya fahinci hakan sai dai baiyi magana ba, don yasan ko yayi ma ba lallai ne ya gaya mai abin da yake damun shi ba saboda Yaa Sheikh mutum ne mai zurfin ciki.

Zama Yaa Sheikh yayi suka cigaba da duba littafin suna muhawara irin ta masu imilin addini a tsakanin su,daga bisani suka koma hirar su ta abokai, anan ne  Bilal ya takura akan lallai sai Yaa Sheikh ya fad'a masa abun da yake damun sa.


Yaa  Sheikh ya d'ago fuskan shi d'auke da damuwa yace,

"Bilal"


Sai da Bilal ya d'ago ya kalle shi zuwa lokacin fuskan shi har ya sauya kala, kana iya karanta damuwar da Ke d'auke a fuskar tashi.

Yace "Jiddah itace damuwa ta Bilal, bani da wata damuwa da ya wuce Jidda"

Bilal ya sake kallon abokin nashi kuma Yana mamakin abin da yake cewa, taya zai ce wai Jidda ce damuwar shi, Jidda karamar yarinya? to kodai wani Abune ya sami Jiddan ?


Duk Bilal ne ya kewa kanshi wannan tambayar sai dai yasan Yaa Sheikh ne zai iya bashi amsa, don haka yace,

"Abdallah me yasami Jiddan kodai ba Jiddan Ku kake nufi ba?" 


"Ita nake nufi Bilal, Jidda yarinya CE karama sai dai ina jin wani babban al amari game da ita, kuma nima na kasa tantance mai hakan yake nufi,idan naga Jidda nakan rasa hankali na, ina shiga wani yanayi aduk lokacin da nake tare da ita, ni mutum ne mai son shagwab'a ita kuma Jidda ba abun da ya zame mata jiki kamar shagwab'a,Bilal akwai abubuwa da dama da nake ji game da Jidda, kuma banaso Ummee ta fuskanci halin da nake ciki".


Ya d'ora da cewa " nidai nasan ba wata mace da nake  jin hakan game da ita, hasali ma ni mata basa gaba na, why sai Jidda? Why?" 

"Allah kaga zuciya ta, Allah kayi al'kawarin baza ka jarabci bawan ka da abin da yafi 'karfin shi ba ya Allah ina rokon ka da ka dubeni da idon rahma"

Bilal da yai kasa'ke yana kallon abokin nasa da tausayin sa da ya cika mai zuciya kuma yana mai mamakin wannan lamari, saboda yasan abokin nasa ba mai damuwa da mata bane hasalima ko mace ce tace tana sonsa to daga ranar tsana ta shiga tsakanin sa da wadda tace tana son nasa.

Bilal ya nisa yace "Abdallah kar kasa damuwa a ranka kacigaba da addu'a nima zan tayaka,sai dai ina tunanin kawai fa son Jidda kake" 

"Nima ina zargin hakan, amma ay Jidda ba tsara ta bace taya zan fara son ta? Yarinyar da ko kanta bata sani ba, ya Allah gani gare ka"


"Kardai kasa damuwa a ran ka komai zai zo dasau'ki da yardar Allah kai dai kayi addu'a, kuma da kake cewa baka son Ummee  tasan halin da kake ciki idan bata sani ba waye kake dashi da zai tayaka addu'a? kadai San addu'ar iyaye akan 'ya'yansu daurewa zakai ka fad'mata"


"Hakane amma gaskiya Bilal ko zan gayawa Ummee ba yanzu ba zan dai cigaba da  daddu'ar"

Bilal yace "to shikenan nima zan tayaka "

Yaa Sheikh ya mika wa Bilal hannu suka yi musabaha yace "to bari na k'arasa gida yau Abii zai dawo sai mun had'u a islamiyya"

"OK to shikenan nima zan shigo nayiwa Abii sannun da zuwa"

Haka suka rabu Bilal yana tausayawa abokin sa, shima Yaa Sheikh yana tausayawa kan sa.


Yana shiga gida ya tarar da Ummee ta gyara gida ko ina fes fes itama tayi wankan ta tana jiran shigowar mai gidan ta.

Ya shiga yana murmushi yana yaba yadda Ummeen shi keda kokari tana da tsafta ga son ado, ya k'arasa kusa da ita yana mata sannun da gida tace, 
"Yawwa sannu Abdallah, kakai min yarinyar tawa ko, amma dai ka tsaya wani gun don ka dad'e?"


Ta jera mishi tambayar. 

"Eh Ummena natsaya a gurinbBilal ne" 



Ta sake cewa " 'Yar tawa kuma fa?"

"Na kai ta"

Ya bata amsa a ta'kaice don baya so Ummee ta gano wani Abu, saboda shi ko maganan jiddan tana sa shi tuna nin ta.


Tsayu war mota a 'kofar gidan sune ya dawo dashi daga duniyar tunanin da ya tafi, Umme tace

"Abdallah wannan kamar Abii ko?"

"Bari na duba "


Ay kuwa shi ne, Abdallah ya 'karasa wajen baban nashi yana cewa,
"Abii sannun da zuwa ka sha hanya"

"Wallahi kuma babana shiga da wannan sauran kuma ka barsu a but din idan su Abdul majid sun dawo saisu shigarwa Mamy"


 (Shima Mamyn yake CE mata tunda dai sunan  mahaifiyar sa gare ta.)

Abdallah yace "toh Abii"   yana mai daukan kayan da Abii din ya nuna masa.


Ummee da murna ta tari mijin ta,Abdallah ya kuma gaushe da Abii, ya tashi yana cewa   "Umme bari na Dan watsa ruwa na kwanta kafin azahar"


"To Abdallah"
Itama ta fad'a tana kokarin tashiga d'akin Abii ta ha'da mai ruwan wanka "

Karfe 12:15 Jidda tashigo tana murna don taga Motan Abii a kofar gida tana cewa,

 "yeee Abii ya dawo"

 tai hanyar dakin Abii da gudu ta fad'a dakin, aiko tana ganin sa ta fad'a jikin sa, shima da murna yace

" 'Yar gidan Abii kin dawo, ya makaranta kina dai karatun ko, ko kina nan kina kukan ki na banza?"


Ya jera mata tambaya saboda ya San mai hali baya fasa halinsa.


"Abii banayi kuma ina karatu,Abii ka kawo min tsaraba"?

" na kawo miki Jidda na idan bankawo miki ba Wa zan kawowa?"

Aiko ta washe baki tace "yawwa Abii na, na gode, sai anjima zaka bani?"

"Eh zan bawa Umme ta ajiye miki yanzu kije ki gaishe da Mamy kuma kice nima Ina gaishe ta,

" Abii to ina Umme?"

Yace"tana d'akin ta"

"To idan ta zo kace na dawo kuma kabata tsaraba ta' ta ajeye min"

Tana gama fad'a tafice da niyyar zuwa wajan Mamyn ta, sai dai tana zuwa wajen 'kofar d'akin Yaa sheikh ta shige d'akin, tana shiga ta ganshi yana bacci, yayi d'ai'dai ya kunna fankar 'kasa tana ta hurashi.
[21/04, 10:00 a.m.] Shooly: 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼



              *YAA SHEIKH*



🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼



*BY:U. K. Y.      For real*😘




   🌈 *kainuwa writers asso*✍🏻 



*Dedicated to Mmn kheiry*





_masoya na bansan irin godiyar da zan muku ba wlh nima Ina sonku na gode da kula warku kuma wadanda sukai min adduar samun nasara a exam dina to alhamdulillahi nasamu nagode sosai da sosai_





*my ANFA  ilobiyu Lodi Lodi wooo*😅😘



             *25 to30*


Jiddah Tana shiga d'akin tai wajen madubi turarukan shi ta fara feshe jikin ta dasu 

"Ay wallahi sai na fesa kowanne nima naita kamshi kamar Ya Abdallah na"

Nan dai taita fasawa sannan ta koma yimai bincike ta hargitsa komai  zuwa wannan lokacin ta gaji tulus dama ta gamo rashin jinta a makaran,  gefen shi ta kwanta itama sai bacci, 



Wani abu yaji ajikin shi kamar ruwa ruwa sannan yaji  kamar wani yazo ya kwanta abayan shi, 



 ay kuwa da sauri yafarka juyawar da zaiyi yaga Jiddah kwance cikin fitsari sharkaf tai musu don shima ajiken yake kawai kallon ta yake yama rasa mezai ce, 


 ita kuwa sharar baccin ta take ko ajikin ta, tsaki yayi kawai ya yunkura zai tashi kenan      ay kuwa baiyi aune ba kawai yaji Jiddah ta cafko shi tana magagin bacci,  



wata galabai tacciyar 'Kara ya saki yana kiran 



"ya ilahi" 





Ya jima kafin ya tattaro karfinsa, 



janye hannun ta yayi daga jikin nashi yana tunanin wai yaushe ma ta shigo d'akin nashi har ta kwanta kusa dashi? 





 sai alokacin yaga iri ayka aykan da taimasa gaba d'aya ta hargitsa d'akin, juyawa yayi yasake kallon ta tananan tana sharar baccin ta wani 'kaya taccen murmushi ne ya kubucemai ya furta

 *"inda rai da rabo"* 


ko me ya tuna oho, 


sannan ya tashi ya sake wasu kayan ya fita daga dakin, 


Yana  fita ya tarar da Ummyn su tana alwala  


"Yanzu nake cewa Abdul malik yazo ya tasoka kafin karasa jam'i"



"Wlh na tashi Ummy wannan yarinyar taki ce  wai ta rasa inda zata kwanta sai d'aki na kawai sai farkawa nayi nagan ta,  gashi tamin fitsarin kwance"

 
Dagowa Ummy tai tana tambayar sa "fitsari dai,  akan katifar kuma? "



"A wlh Ummy" yafada fiskan shi cike da takaici shi sai yanzu ma abin yake batamai rai, 
 "To ay shikenan Kayi alwala kar ashiga sallan"



"To Ummy na,  Abii fa ko ya tafi masalkacin?" 



"Eh " Ummy ta fada tana shiga   dakin ta shima ya sheikh alwala yayi ya tafi masallaci ko takan Jiddah bai biba, 




Ita kuwa Jiddah ya sheikh yana fita ta farka ganin abin da taine kunya ta hanata fita saboda tasan indai su Abdul majid sunji abinda tai tashiga uku, 






 tanajin fitarsu masallaci tai maza ta sulale tai gidan mamyn ta,  tana shiga ta tarar mamy ta tada sallah,  tasamu guri tarakube tana jiran mamyn ta idar, 



Mamy tana idarwa Bayan tayi addua ta kalli Jiddah dasai muzurai take tace "meya jika miki kaya? "




"Fitsarin kwance nayi"
Tabata amsa tana dukar da kai,  


"Fitsarin kwance Jiddah a Ina kikai? " 


"A dakin ya Abdallah "



Mamy ta sake jefa mata tambaya "a kasa ko a Ina? " 



"A katifa"



Tafada tana turo baki na borin kunya. 

*5 years*



Kuyi hakuri da wannan fans ba yawa😍😍😍
[21/04, 10:00 a.m.] Shooly: 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
  
               *YAA SHEIKH*


🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼


*U. K. Y.    For real*😘


🌈 *kainuwa writers asso*✍🏻



*Dedicated to mmn kheiry*




             *30to35*





 
*5 years*



Shekaru biyar da suka shud'e abubuwa da dama sun faru, ansamu nasarori da dama.

A halin yanzu Jiddah ta gama primary school sannan ana cuku-cukun sama mata secondary.



Jiddah idan kagan ta a wannan lokacin bazakace yarinya Yar shekara goma sha biyu bace, Jiddah doguwa ce fara siririya Mai cikakken diri da kyawun zati,       wani abun burgewa game da Jiddah shine Jiddah irin yarannan ne masu shegen iyayi ga tsafta ga son iyawa a 'bangaren karatu Jiddah nada kaifin 'kwa'kwalwa afannin Arabic da kuma boko idan Jiddah Tana magana Sai kayi mamaki  saboda tsabar iyayi kai a ta'kaice Jiddah tana da d'aukar hankali. 



A 'bangaran Yaa Sheikh kuwa a halin yanzu Yaa Sheikh  cikakken mutum ne kyakkyawa,  to dama abinka da jinin sudanawa  dole Ya Sheikh ya kasance Mai jan Hankali, 


Ya Sheikh yanada sura Mai d'aukar hankali ga nutsuwa abinka da malaman sunna ba hayaniya.


Shekaru biyar da suka wakana Ya Sheikh ya samu scholarship na zuwa 'kasar  Madina, sakamakon musaba'ka da akayi ta 'kasa ba'ki d'aya inda ya samu nasarar lashe gasar kowa yayi farin ciki da hakan, 


Ya tafi k'asar Madina inda ya cigaba da karatun masters d'in shi ahalin yanzu ya kammala. 




Sai dai sun nuna buk'atar su akan Ya Sheikh da ya zauna don yayi musu Ayki a kasar tasu wato Madina koda ba 
na din din din ba kuma Yaa Sheikh ya amince da bukatar su, Sai dai ya basu nashi uzirin cewa yanason zuwa gida nawani d'an lokaci sannan yadawo ya kar'bi aikin,  suma kuma sun amin ce.



Babban burin Ya Sheikh yanzu bai wuce yaje yaga abin k'aunar saba kuma sanyin idaniyar sa wato Jiddah,  don ba abinda ya sauya game da abin da Ya Sheikh ya keji akan Jiddah, don daga Ummy har Mamy sun gane Ya Sheikh yana tsananin 'kaunar Jiddah, Sai dai ita Jiddah bata sani ba. 




Ummy tasha yiwa Ya Sheikh magana akan ya nemar wa kanshi mafita ya samu wata cikakkiyar budurwa ya aura don ya yiwa Jiddah girma, Jiddah baza ta iya dashi ba amma kullum tazo Mai da zancen Sai ya hau yi mata magiya don Allah Ummy na kibar wannan maganar kafin Jiddah taji itama tace nayi mata girman.



Ummy dai jinshi kawai take kuma tana mamakin yadda Abdallan  nata yake mugun son Jiddah wanda ta lura ko gurin da yake Jiddah tazo Sai yanayin sa ya canja, to inaga an kaimai ita gidan sa a matsayin mata.



Mamy har yanzu Allah bai kawo mata miji ba tana zaune dai tana 'yan sana'oin ta kuma rashin auran bai dame ta ba saboda ba abunda tarasa  yadda Ya Sheikh zai yima Ummyn shi ayke haka yake yiwa Mamy ma sannan Abii ma duk abunda ya kawo Sai an kai mata, tana zaune cikin kwanciyar hankali,            
Sannan koda ta gane ala'kar Ya Sheikh da Jiddah abun ya mata dadi sosai, sai dai Tana tunanin Anya Jiddah tana son Abdallah kuwa? 





Abdul Malik da Abdul Majid suna Sokoto suna karatunsu na degree wanda shima Ya Sheikh ne ya dauki nauyin Kara tun nasu. 


Kai Sai dai muce Alhamdulilah amma dai kam an samu ci gaba.




"Nidai Mamy Allah boding nakeso kinga Nana ma can za a kaita ba Sai akaimu tare ba? "





"Oh wato ita Nanan ce ta cemiki boding za a kaita shine zakizo ki sani a gaba ko? To ni kifita a idona na rufe kina jina ko tun wuri ki cire zancen boding d'innan ma a ranki Jiddah  kinsan Abii ba yarda zaiyi ba."

Jiddah bata sake cewa komai ba saboda tasan Ya Sheikh ya kusa dawowa kuma tasan zai yarda kuma yana yarda shi kenan,


"To shikenan Mamy bari naje na gaishe da Ummy Da Abii kafin ya fita."


Mamy tace "toh ki ce ina gaishe da Abii kuma kicewa Ummyn taku nima Zan shigo anjima."


Tana fita tafad'a gidan Ummyn bayan ta gaishe su tai sauri tafita tana cewa "Ummy na tafi.....         na baro Mamy tana Ayki "

"To Jiddah na kice mata Sai ta shigo din"



Jiddah tana fita tai gidan su Nana aminiyar ta, 
Nana tana ganin ta ta hau murna don a tunanin ta Jiddah tazo gaya mata  an yarda itama za akaita boding d'in.

"Ke Mamyn ta yarda ko? "
Nana ta tambaye ta 


"Wlh bata yarda ba Nana amma dai kinga Ya Sheikh ya kusa dawowa idan ya yarda shikenan."



"Ya Sheikh ubanki ne shi da zakice Sai ya yarda? "


Wani mugun kallo Jiddah  watsawa Nana kana tace "idan shi ba ubana bane ai yaya nane shi ko kuma idan bai yarda ba uban wane zai biya kud'in makarantar?  Ko babanku zai biya min?" ta k'arasa maganar tanawa Nana kallon up and down 




"Kefa baki da M wlh yanzu me ne nasako Baban mu a ciki? "




Jiddah tace "ke kika fara ai, ni tashi muje ki rakani  kar Mamy taga na dade."


"Tom naji, shine ko ki tambaye ni mutumin naki ko? "


Jiddah tace" wafa? "


Wani kallon kinma raina ni Nana taiwa Jiddah  "oh kina nufin kice baki san wa nake nufi ba? To *FIGO* nake nufi jiya ya bani letter na baki."





"Uhmmm kanki ake ji" inji Jiddah 



"Kema anajin Naki kan.....  Yaro 'Dan gayu Kamar figo kiringa jamai aji " 




Jiddah tace" nidai ba ruwa na ina yarinya ta bazan kula namiji ba don idan Mamy tasani Sai ta zaneni"



"Nidai bari na dauko miki letter in kin gadama ki yaga"





*birnin MADINA*



Ina Sau raron comment din ku😃09032749200 what's app only.........
[21/04, 10:00 a.m.] Shooly: 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼

             *Yaa Sheikh*

🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼


*BY:U. K. Y.   For real*😘 




    🌈 *kainuwa writers asso*✍🏻


 


*Dedicated to mmn kheiry*




Wannan page din nakine my *zanna* I love ❤️ 😍 Ana tare🤝🏻



                  *35to40*





*MADINAH*


Yaa Sheikh ne ya fito daga wani hall yana ta sauri hannun shi dauke da takardu. 




Yana cikin tafiyar ne yaga wata mota ta faka  kusa da shi koda yajuya Sai yaga Nuaym ne. 


(Nuaym shine abokin da Yaa Sheikh Yayi a garin madina kuma makocin shine don haka sun saba, Nuaym balaraben misrane shima karatu ne ya kawo shi madina) 




Cikin harshen larabci suka fara magana Nuaym yake cewa Yaa Sheikh 

"Abdallah yau da safe ina jiran ka kazo mu taho makaranta ashe kai kayi tafiyar ka" 


Nuaym ya 'karasa maganar yana mai jin haushin jiran Yaa Sheikh da yayi. 




Yaa Sheikh Yayi murmushi ya na mai bud'e murfin motar Sai da ya dai-dai ta zaman shi sannan ya kalli Nuaym da ya 'bata fuskanshi wai shi Yayi fushi, sannan ya ce 



"haba abokina tun jiya na fad'ama ina so na gama komai yau a cikin makarantar nan tun 6:00 na taho nasan lokacin baka tashi ba,  amma yanzu dai kayi ha'kuri mukarasa gida "



             "  Ok " 

kawai Nuaym yace ya tayar da motor suka nufi gida. 




Koda suka isa gida Yaa Sheikh gidan sa ya shige akan  cewar da yamma zasu had'u. 




******



Su Jiddah suna fitowa Nana tace"ke ni ungo letter ki, ana so Ana kaiwa kasuwa " 



  Ita dai Jiddah  bata ce komai ba ta kar'bi letter suka cigaba da tafiya. 




"Kinga Jiddah don Allah kizo mubi ta hanyar shagon askin su Figo dama jiya da ya bani letter Sai da ya cemin ya naso ya ganki"




"Gaskiya nidai bazani ba so kike ace mana Yan iska ko? "


"Kaiii!!...... Gaskiya  ke Jiddah wlhy banza ce  ina ruwanmu da mutane? Ay wlhy dama Figo ni face yana so"



"Mtswww to Sai me?  Don Figo yace yana sonki mutumin da yake sa sar'ka yasa wando duk Bayan shi a bu'de, to ke Figo ya dama amma ni bai dameni ba"




Nana tace"to naji Kiyi hakuri Tunda bazaki ba ki tsaya naje na kirawo shi"

"Kinga Nana tunda bazaki rakani ba shikenan , nidai bazan tsaya ba"




"Kai don Allah ki tsaya haba kawata Zan rakaki har gida fa "



Da haka dai Nana ta ja ra' ayin Jiddah har ta tsaya ita kuma ta tafi kiran Fito. 



"Kaganta can Figo muyi sauri in ba haka ba wlhy zata iya tafiya" 



Bayan sun karasone Figo Yabi Jiddah da wani mayataccen kallo yana ayyana abubuwa da dama a zuciyar sa sannan yace



    "yaaa! Baby Tunda ke bazaki zoba to ni gani nazo , baby kina kofsawa da yawa fa mene a ciki don kinzo gurina"



Jiddah da ta sunkuyar da kanta 'kasa ta Dan saci kallan sa sannan ta kuma kau da kanta gefe tace. 




"Ke Nana tun da yazo to ki taho mu tafi "ta karasa maganar tana tafiya. 




"To naji muje, Figo Sai anjima bari na rakata" 
Figo da Yayi sa'kare yana shafa gefen fuskar sa yana sakin wani lalataccen murmushi gaba d'aya hankalinsa ya tafi kugin kallon Jiddah baima san me Nana ke cewa ba. 




Nana ta sake mai mai tawa da karfi


 "kai Figo mun tafi"

 sannan ya dawo hayya cinsa


 "ok tom see u leter " 



 Wane *FIGO*

Figo sunan shi na gaskiya musa matashi ne Wanda a'kalla zaiyi shekara ashirin da uku. 


Musa (Figo) yoroba ne 'Dan garin Ibadon, yazo karatu ne kano to kunsan yoroba da neman kud'i wannan dalilin ne yasa ya bud'e shagon aski a Latin su Nana Figo abokin Ali ne shi kuma Ali yayan Nana ne shi yasa suka saba da Nana, don wani lokacin ma Figo a d'akin Ali yake kwana. 



Iyayen Nana irin iyayen nan ne da basa 'kwa'bar 'ya'yan su. 



Don haka daga Ali har Nana suke abinda ransu yakeso, wai don ma Maman su Nanan tana Dan 'kwa'bar ta sabo da ita mace ce. 



Tunda Figo yaga Jiddah ya kwallafa  ran shi akan ta shine yabiyo ta wajen Nana don yasan zata taima kama sa. 




Ay kuwa hakan akayi don tun Jiddah bata kula shi har tazo ta fara duk da tai makon Nana. 


Saboda Jiddah bata da wata 'kawa Sai Nana ajinsu daya a primary. 



😍😍😍😍😍😍😍 bari nace muku see u😉👋🏻
[21/04, 10:00 a.m.] Shooly: 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼

              *Yaa Sheikh*


🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼



*BY:U. K. Y.    For real*😘




🌈 *kainuwa writers asso* ✍🏻




*dedicated to mmn kheiry*🤝🏻



               *40to45*




Tana shiga gida ta- tarar da Mamy tana sallah, itama alwala tayi ta shige d'aki. 




Bayan ta idar da sallah tafito ta sami Mamy itama ta idar, 

"Mamy wai Ummyn tana amsawa "


Mamy  ta kalleta tana zargin ba a gidan Ummyn ta zauna ba har tsawon wannan lokacin ba amma Sai ta kyale ta bata ce mata komai ba. 


"Ok nima ay yanzu Zan shiga ki tashi ki gyara min kayan miya Sai kizo gidan Ummyn ki same ni"


"Toh Mamy,....  wai goben Ya Abdallahn zai dawo ne? "



Mamy ta washa mata harara tace"kin bashi sak'o ne da kike tanbayar yaushe zai dawo? To idan ma so kike ya dawo ki mai maganar boding garama ki sake tunani don ko ya biye miki ni ba barinki zanyi ba"

Mamy tana kaiwa nan ta d'au mayafin ta-tafita. 


Aykuwa Mamy na fita Jiddah ta ciro lettern Figo ta karanta, ba komai bane illa dai abinda ya saba rubutawa wato yaushe zata fito su ha'du, ... Ta'be baki tai tace,  


"kaji da shi"

Sannan ta 'boye lettern a inda ta saba b'oyewa, sannan ta fara gyara kayan miyar. 



Bayan ta gama ne itama ta kulle musu gidan ta shige gidan Ummy da niyyar idan ta shiga zata kar'bi wayan Ummy ta kira Ya Abdallahn ta,  taji yaushe zai dawo. 


A sa'a kuwa tana shiga ta iske ya kira suna ta hira da Mamy. 


"Yawwa Ummy ya Abdallah ne ko? " 


"Jiddah na shine yanzu shima yake tambayar ki "


Ta cuno baki cike da sgagwab'a sannan tace"Hmmm ke dai Ummy kina kare shine amma nasan bai tambaye ni ba"


Dariya Ummy tayi sannan tace "Auu hakama zaki ce to ay gashi nan ya kira saiki bari idan ki kaga ya kashe wayan bai neme ki ba Sai kice haka"

Ita dai Jiddah bata kuma cewa komai ba ta cigaba da cuno baki tana jira taga ko Ya Sheikh zai kashe wayan bai neme ta ba. 


Ita dai Ummy abunma dariya ya bata kasan cewar wataran Ya Sheikh zai kira musammam don Ita amma  'kiri-'kiri zata ce baza ta karb'a ba,  haka Ya Sheikh zai hakura,... Don haka yau abun yayiwa Ummy dad'i tana adduar Allah yasa Jiddah da fara son Abdallahn tane. 



Mamy kuwa Sai hira suke ita da Ya Sheikh amma fa shi burin shi yaji tace ga Jiddahn amma shiru, hakane yasa yace "


"Mamy Ummy bata kusa ne inason na gaya mata me zata dafa min goben"


"Toh babana bari na bata"


'Kin kar'ba Ummy tai don tasan sarai so yake ta ha'da shi da Jiddah don haka tace  Ayki take don haka  Mamy kawai ta bawa Jiddah  inyaso ko anjima ne za suyi magana. 



Mamy mi'kawa Jiddah wayar tayi,  tana cewa Ummy zata koma gida. 




Koda Jiddah ta kar'bi wayar bata tsaya a tsakar gida ba d'akin Ummy ta shige, 



"Hello Ya Abdallah nah"


Wani sanyi yaji yana ratsa shi gami da wata cikakkiyar nutsuwa kice da zumud'i ya amsa mata "na'am Jiddo nah ya kike? "



Kamar yana kallon ta-ta wani cuno baki cike da tab'ara tahau bubbuga 'kafa tana cewa "shine da ka kira waya ko ka tambaya ina nake ko? To Allah nayi fushi idan ka dawo bazan kula kaba "


Ay  kuwa karkuso kuga yanda Ya Sheikh ya ru'de kamar wani wawa ko ince k'aramin yaro. 



 magiya ya shiga yi mata kamar zaiyi kuka


"please my Jiddo don't  be angry  with me,...  Jiddo wallahi na tambayi  Mamy tace ta barki a gida kina mata Ayki ki tambayi Ummy ma idan baki Yarda ba"



"Ok Toh na yarda"



"To kin hak'ura? "


"Eh na hak'ura"

Wata nannauyar ajiyar zuciya ya sauke yana jin da'di har cikin ran sa sannan yana mamakin yadda Allah ya jarabce shi da son 'yar 'karamar yarin kamar Jiddah. 




 amma ko ba komai yasan Jiddah tana da duk wani Abu da yake so a tattare da mace. 


 Jiddahn ce ta katse mai tunanin da yake da shagwa'bar ta ta fara cewa




"Toh Ya Abdallah nah yau she zaka dawo 'din wai? "


     Ya Sheikh da ya shagala da sauraron shagwa'bar ta mai sashi a wani hali a kasalan ce yace mata"Jiddah yau Zan hawo jirgi 'karfe Tara insha Allah  Kinga zuwa gobe iwar haka muna tare " 


"Kai amma naji dad'i Ya Abdallah dama Inaso in gaya maka wata magana ne sai ka dawo Zan fa'da ma"



(Har yanzu dai tananan da k'udirin ta na zuwa boring saboda Nana ta gama yima ta hud'uba) 



"Ok tom shikenan Jiddahn Abdallah,  bari na gama shiryawa Kinga lokaci yana tafiya amma kafin nan sai kin cemin kina so na"


Dariya tayi, ko ajikin ta tace ina sonka Ya Abdallah nah Kaima kana so na? "


"Kai Jiddah ina sonki mana"


Ya sake lumshe ido yanajin cigar jikin shi ha tashi saboda shauk'i (kamar wami mai magana da cikakkiyar budurwa lol) 



Sannan Ya cigaba da cewa


" ay kaf duniya bacin Mamy ba Wanda ya fini son ki "


"Yeeeee naji da'di Ya Abdallah" 


"Toh Jiddah bari na 'karasa shiryawa ko?.....  sai anjima Zan sake kira Kafin mu tashi"


Da haka sukai sallama.




9:00pm jirgin su Ya Sheikh ya 'daga sai Nigeria 🇳🇬 


I love ❤️ u all my fans🤝🏻



Khairaty 😍😘
[21/04, 10:00 a.m.] Shooly: 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼

              *Yaa Sheikh*

🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼


*BY:U. K. Y.    For  real*😘




🌈 *kainuwa writers asso*✍🏻



*Dedicated to Mmn kheiry*🤝🏻


*Note*: *naji sa'kon ku masoya na cewar bakwa so Jiddah taje boding school to amma Idan kunyi ha'kuri na d'an lokaci ne kucigaba da bina kudai kawai*🤝🏻😍



               *45to50*


 _Wannan page din nakune abokan arzik'i   😍 *Yaa Sheikh fans* 😍_



'Tun safe Jiddah take zaman jiran Yaa Sheikh amma shuru kakeji, harkusan magarib bashi ba labarin sa. 




Kallon ta Mamy tai tace "tashi ki shiga gidan Ummy ki tambaye ta kiji ko baban nawa ya kira ta?nasan dai yanzu kam sun iso".



Jiddah kamar mai jiran hakan,  ta mi'ki da sauri ta sa hijab ta fita sai gidan Ummy, 


Tana shiga ta tarar da Ummy itama tana zaune ta cab'a ado na tarbar d'an ta. 




Bayan ta gaishe da Ummynne take tambayar ta
"Wai Ummy Ya Abdallahn bazai dawo bane kodai dama bai taho Ba? "


Ta k'arasa maganar kamar zatai kuka Don har idon ta ya kawo kwalla. 




"Au kuka zakiyi saboda bakya raina abin kuka? To Abii ya tafi d'akko shi yanzunnan zaki gansu,  Dan Tun d'azu Abii ya tafi d'aukan shi "




Sai a sannan taji dad'i ta saki ranta ta hau yiwa Ummy hira. 





Suna cikin hirar ne su kaji tsayuwar motar Abii, Jiddah kawai k'urawa k'ofa ido tai tana jiran taga shigowar Ya Abdallahn ta. 



Da sallama suka shigo,....... Ido hud'u sukai da junan su ay kuwa Jiddah ta wani zabura tai kan Ya Sheikh, bai Ankara sai ji yayi Jiddah ta rungume she, 



" *YA SALAM*" 

Shine abin da ya iya furtawa saboda yadda yaji tsigar jikin shi ya tashi ga wani jiri da ya d'ebe shi, taga-taga ya fara kamar zai fad'i, Ummy da ta Ankara da halin da Ya Sheikh ya shiga tai saurin cewa "kai Jiddah bakisan kin girma Ba yanzu ay saiki kada yayan naki",


Da Wannan damar Ya Sheikh yai k'ok'arin tattaro nutsuwar shi sannan ya zame jikin shi daga na Jiddah. 



Abii ne yace" to ay sai ku samu guri ku zauna ko? "


Dukan su zama sukai sannan Ya Sheikh ya gaishe da Ummy zuciyar shi cike da murnar ganin shi a gida. 

"Lafiya kalau Abdallah ya hanya ya karatu to Allah ya sa angama a sa'".


"Amin ya Allah,  Ummy na"

haka dai sukaita gashe-gaishen su da hirar yaushe gamo,  Abii yana ta tambayar shi game da aykin da madina suka bashi, kafin daga bisani Abii ya tashi ya shiga d'akin shi. 



Ya Sheikh sai satar kallon Jiddah yake yana mamakin girman da ta k'arayi, ga wani iyayi da take kamar wata cikakkiyar budurwa, Ummy ce takatse mai tunanin da yake tace,"Abdallah  akawo ma abinci KO? "

"A'a Ummy bari dai na fara wanka"


Bayan yayi wankane ya fito cikin shirin sa, sanye yake da wata black jallabiya, kannan a gyare sai zuba k'amshi yake Idan kagan shi kamar balarabe duk dade hasken shi Ba irin na larabawa bane irin na yan sudanne ne amma Ba k'aramin kyau yayi ba. 



Zama yayi sannan yace"yawwa to yanzu Kinga sai naci abincin ko Ummy na? "



Murmushi Ummy tayi sannan face"to Abdallah bari na d'auko ma"


Tana fad'in  haka ta nufi kitchen . 


Jiddah itama mik'ewa tayi da niyyar taje ta taya Ummy d'auko abincin, da sauri Ya Sheikh ya ruk'o hannuta ya maida ta ta zauna suna kallon juna sannan yace

"Jiddah na baki ce nayi kyau ba kodai banyi ba ne? Don kefa nai wannan wankan"

Ya k'arashe maganar yana kurawa k'wayar idonta kallo, kamar mai jin bacci. 

Kallon shi itama tai sannan tace

"kayi kyau mana ka ganka kuwa kamar balarabe"

"Toh Jiddah nah nagode, yanzu to kice kina sona"

Ta kyalkyale da dariya tace"kai Ya Abdallah nace fa Ina sonka kuma kaima kace kana sona ba shikenan ba"




Zuwan Ummy ne ya hanashi sake cewa komai, Don haka kawai ya fara cin abincin da ta kawo mai. 

Bayan ya gama yace


"Ummy bari na shiga na gaishe da Mamy naga dare yana yi"



Haka kuwa akai suka tashi shi da Jiddah, Jiddah mata yiwa Ummy saida safe. 




Mamy tayi Farin ciki sosai da ganin Ya Sheikh, sun d'an tab'a hira Karin Ya Sheikh yayi mata saida safe, Jiddah tanajin haka tabi Bayan sa, a zaure suka tsaya Jiddah tayi k'asa-k'asa da murya tace" Ya Abdallah karfa ka manta nace maka zan gaya maka wata magana amma sai da safe"

"Toh Jiddah Allah ya kaimu"


Sallama sukai ya nifi gida,....  yana shiga -yayi wa Ummy da Abii saida safe, yashige d'aki yayi shinrin kwanciya Bayan ya gama duk abubuwan da ya sabayi. 



Yana kwanciya tunani yace salamualaikum, haka yaita tunani,................ Tab wai Jiddah ce ta k'aragirma haka, amma daga nayi magana Ummy tace wai nayiwa Jiddah girma baza ta iya dani ba, to ay in ita bazata iya Dani Ba ni zan iya da ita. 

Da irin wad'annan tunanin bacci yayi awangaba da shi. 




Khairaty😘🤝🏻
[21/04, 10:00 a.m.] Shooly: 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼


            *Yaa Sheikh*


🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼



*BY:U. K. Y. For real*😘




🌈 *kainuwa writers asso*✍🏻




*Dedicated to Mmn khairy*🤝🏻 😘



Surah Al-Araf, Verse 27:
يَا بَنِي آدَمَ لَا يَفْتِنَنَّكُمُ الشَّيْطَانُ كَمَا أَخْرَجَ أَبَوَيْكُم مِّنَ الْجَنَّةِ يَنزِعُ عَنْهُمَا لِبَاسَهُمَا لِيُرِيَهُمَا سَوْآتِهِمَا إِنَّهُ يَرَاكُمْ هُوَ وَقَبِيلُهُ مِنْ حَيْثُ لَا تَرَوْنَهُمْ إِنَّا جَعَلْنَا الشَّيَاطِينَ أَوْلِيَاءَ لِلَّذِينَ لَا يُؤْمِنُونَ

O children of Adam! let not the Shaitan cause you to fall into affliction as he expelled your parents from the garden, pulling off from them both their clothing that he might show them their evil inclinations, he surely sees you, he as well as his host, from whence you cannot see them; surely We have made the Shaitans to be the guardians of those who do not believe.
(English - Shakir)  

via iQuran  juma a Mubarak



*masoyana ina godiya da kulawar da kuke bani, wad'anda suka kirani da Wanda suka bini pc duk ina godiya kuma ina k'ara baku hak'uri abu buwa ne sukai min yawa*



                 
                *50to55*




'Dumin abinda ya fitar daga jikin sane ya farkar dashi daga mafarkin da yake, gaba d'aya ya had'a gumi afili ya furta "hasbunallahu wa ni'emal wa kil, why!?  Me yasa haka ne?"


Duk shi kad'ai yake surutan sa kafin daga bisani ya kalli agogon dake mak'ale a jikin bangon d'akin nasa, k'arfe 3:00 dai-dai don haka ya tashi ya nufi toilet. 






Bayan ya tsarkake jikin sane ya fara gabatar da nafilfilu yana adduar Allah ya kawo masa mafita don shi kansa wani lokacin Yana gasgata maganar Umme cewar Jiddah ta mai k'ank'anta ya nemi wata, 

To amma fa shi bashi da wani interest Akan wata mace Bayan Jiddah da ya kwallafa ranshi a kanta,  don haka dole ne ya rok'i Allah mafita, ahaka har lokaci shiga sallar asuba yayi, don haka ya feshe jikin shi da turare   ya nufi masallaci ba tare da ya shiga cikin gidan nasu ba. 





Da misalin karfe 8:00 na safe Jiddah har ansha wanka za'aje rok'ar al farman tafiya boarding school gurin Yaa Sheikh sai addua take Allah yasa ya yarda, fitowa Tayi ta iske Mamy a falo, kame kame ta fara kafin ta nemo abun fad'a. 




"Umm Mamy zanje gun Umme na gaishe ta"


Mamy tace "hmmm Jiddah kenan zadai kije gurin babana ay ba hanaki zanyi ba sai kin dawo".      


Aykuwa sim-sim ta fice ta nufi gidan Umme, 
Tana shiga bata tsaya ko ina ba sai d'akin Yaa Sheikh a cewar ta koma ina yake ai zai shigo d'akin sa, tai zamanta, Aikuwa tana cikin tunanin nan Yaa Sheikh din ya shigo, dawowar sa kenan daga masallaci don Tun fitar sa sallan asuba bai dawo ba sai yanzu. 





Tashi tai da gudu zata rungume shi Aikuwa k'irjjn shi har dukan uku-uku yake Saboda shi yasan wani  irin yanayi ya shiga jiya da ta rungume shi gashi yau yana azumi don haka yayi sauri durk'usawa ya dafe cikin sa Yana cewa"Asssshhhhh" 
 

A tsorace ta dago tana kallon sa "yaya mene? "Ta tambaye shi. 



 

      "Cikina "yabata amsa





    "To sannu yaya muje ka kwanta"




Haka ta tusa shi gaba kamar k'aramin yaro, saida taga ya zau na Sannan ta sake yimai sannu. 


Shidai a cikin ran sa Allah yake wa godiya da bata tabashi ba sannan yana tunanin ya rayuwar sa zata kasance a gaba,  ba zaiyiwu ace kullum zai dinga k'arya Saboda Jiddah kar ta tab'a shi ba, kuma ya fuskanci kamar bata da ranar daina rungumar sa, " tab akwai aiki"ya fad'a a zuciyar sa. 




"Sannu yaya kasha magani ko zai daina "


"Toh Jiddah zan sha sai anjima, yanzu dai ki fadamin abinda kika ce zaki fad'a min"
Ya k'arasa maganar yana kallon ta. 




Ita kuma ta sunkuyar da kai tana jin tsoron abinda zai biyo baya idan ta fad'a mai ko zai yarda ko bazai yarda ba. 

Cikin k'ink'ina ta fara magana"umm emm... Dama yaya so nake a kaini boarding ni banason day Saboda a boarding anfi karatu kuma inason boarding school nidai yaya "ta k'are maganar tana zuba mai shagwa'ba. 


A rud'e ya d'ago yana kallon ta duk Yabi ya susuce" kiyi shiru mana, badai kince kina so ba,  kuma zaki iya? "



"Eh yaya inaso"



"To shike nan ki bari Zanyi shawara "


"To yaya amma kar kayi shawaran da Mamy kaji"


"To naji tashi kije "

Ba musu ta fita ranta fari k'al,  don ga dukkan alamu zatai nasara. 


Shi kuwa Yaa Sheikh wata ajiyar zuciya ya sauka had'i da furzar da wata zazzafar iska. 


 "banida wani zab'i da ya wuce na bar Jiddah ta dafi school nima zan samu sauk'in abinda nake ji idan bana ganin ta, indan yaso in Zan koma madina sai nai mata transfer don har ga Allah banason makarantar kwana ko don karatun islamiyyar ta" shi kad'ai yake maganarsa kamar zau tacce. 



**************


Three weeks ago 


Komai ya kammala Mame ta amince da maganar zuwan Jiddah makaranta, haka, Abii da Umme duk sun yarda kasan cewar sunga yadda Jiddah ke so taje makarantar kwanan. 




A b'an garan  Nana har tafi Jiddah Farin ciki da jin wannan labarin sai dai  ita Nana acikin satin nan za a kaita Saboda angama mata komai, Nana bata so haka ba amma Jiddah ta kwantar mata da hankali cewar ai itama ba dad'ewa za taiba an kusa gama mata nata shirin.   



Figo baiji dad'in Nisan da masoyiyarsa Jiddah zatai ba amma acewar sa ba wani abun damuwa bane Tunda tana tare da Nana mai yi masa ban ruwa a soyayyar tasa.  lol😂




Haka akayi kuwa Nana ta tafi a satin,  inda kuma Yaa Sheikh yaketa yima Jiddah nata shirin don yace bayason ta buk'aci wani abu.





A kwana goma da Nana Tayi a makaranta ba Wanda bai santaba Saboda bak'in rashin ji da rashin kunya, hatta malamai sun gane ta. 

A yanzu Nana bata da wani buri da ya wuce taga k'awarta ta a makarantar Saboda kowa yak'i   k'awance da ita gudun kar a Shafa mai bak'in fenti. 




Yau ta Kama ranar Monday kuma yau ne Yaa Sheikh ya d'au niyyar kai Jiddah makaranta.




Keep flowing 
Khairaty😘✍🏻
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼


            *Yaa Sheikh*


🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼



*BY:U. K. Y. For real*😘




🌈 *kainuwa writers asso*✍🏻




*Dedicated to Mmn khairy*🤝🏻 😘



               *55to60*


An gama saka komai a boat din moton Abii Jiddah kawai Yaa Sheikh yake jira cos shima ya gama shirin shi.



A cikin gida kuwa Jiddah ce keta sharb'an kuka harda majina, gaba d'aya jikin ta yayi sanyi zata rabu da Mamyn ta da kuma Ummen ta suyi fad'a su shirya. 


Nasiha Umme Tayi mata sosai sannan ta kwantar mata da hankali. 


Ita kuwa Mamy cewa tai ba ruwanta Tunda Jiddah itace tace taji ta gani don  haka Tayi mata shuru,  to amma abunka da d'a da uwa cikin ranta tausayin Jiddahn ne ya bai baye ta, basu tab'a rabuwa ba  koda na Kwana daya ba don ko Borno tare suke zuwa amma sai gashi yanzu Jiddahn ta zab'i makarantar kwana.



 Mamy ta kalle ta tace "Kid'au jakar ki kije yana jiranki fa kin sani sarai kinzo kin tsaya"



Ta d'auki Jakarta Umme ta taya ta da wasu sauran kayan da ba'asa a moto ba suka nufi waje Jiddah sai shasshk'ar kuka take Ummy nata bata hak'uri. 



"Allah ya kiyaye ya kuma tsare kuma ki maida hankalin ki kiyi karatu" wannan shine abinda Mamy ta iya cewa, ta koma cikin d'aki don baza ta iya ganin tafiyar tilon "yarta-taba. 



Yaa Sheikh yana tsaye yanata kallon agogo don baison suyi rana Saboda makarantar ba a cikin gari take ba, ya shirya tsaf cikin farar jallabiya kana gani basai an gayama kud'in taba kasan mai tsadace Tayi cif da jikin sa gashi ta karb'i kalan fatar sa, wani bak'in sau ciki ne a k'afarsa shima yayi matuk'ar kyau ak'afar tasa, sanna ya kawo bakar hula irin ta larabawa yasaka sumar kanshi tasha gyara ga wani bak'in agogo daya haska hannun shi,kai gaskiya yaa Sheikh kyakkyawane gakyau ga gayu ga tsafta ga iya soyayya uwa uba ilimin addini Dana zamani,   a tak'aice Yaa Sheikh ya had'u matuk'a. 


Yana tsayenne Umme tafito rik'e da hannun Jiddah suka k'arasa jikin motar. 

"Kukan me takeyi kuma?  Kefa kikace kina so, zakiyi shuru ki shiga mota kosaina sab'a miki? "



Umme ce ta kalleshi tace"Aa Abdallah kabita a hankali banason wata magana, Jiddah ki shiga mota kutafi karku yi rana"






Jiddah najin haka ta kuma fashewa da kuka "yaya don Allah kayi hakuri Wallahi na fasa bana so"ta k'arasa maganar tana k'arasawa gun shi da gudu ta fad'a jikin shi ta rungume shi. 



Sosai yaji tausayin ta amma bakin alk'alami yariga ya bushe dole ya kaita.



"Kiyi shuru kinji Jiddah na ki daina kuka,  kece fa kikace kina so, ba komai kiyi hakuri zan dinga zuwa duba ki kinji "yan mata na? "


Da haka dai ya samu ya lallab'a ta,  Umme tana tsaye Tana kallon ikon Allah. 


Da haka yaja moton suka d'au hanya Jiddah tana ta d'agawa Umme hannu. 


Zallan so  Yaa Sheikh yake nunawa Jiddah amma da yake ita a nata tunanin 'yan uwan taka ne kwata kwata bata kawo komai a ranta ba. 




"Jiddah na tafiya zakiyi ki barni? Zanyi kewar ki Jiddah, Allah ya nuna min ranar da bazaki kuma yin nisa dani ba ranar da zan zama ke,  ke ki zama ni, Jiddah zan shar dake dad'in da baki tab'a jinshi ba a duniya , yanda ko ance kiyi nisa dani ma bazaki iya ba, Jiddah na kice kina sona please "



Jiddah da tai kasak'e Tana kallon bakin Yaa Sheikh da yake matuk'ar burge ta yadda yake motsa shi kamar bai son yin maganar, a ranta cewa take dama nata ne da sai itama ta ringa yin yanga. Lol




"Jiddah na bazaki ce kina son nawaba "ya fad'a kamar zaiyi kuka. 



Da sauri ta d'ago tace"aa yaya zan fad'a ina son ka mana, kasan wani abuma yaya Wallahi ina son wannan bakin naka"ta fad'a tana kai hannu zata tab'a yayi sauri ya rik'o hannun nata  saboda yasan saukar hannunta kan bakinsa ba k'aramar fitina zai haifar ba amma duk da haka rik'e hannunta da yayi saida yanayinsa ya sauya. 




"Jiddah kalleni"ya bata umarni ba musu Tayi yanda yace ta kalle shi suna kallon  juna amma hanunsa rik'e da sitiyari. 



"Jiddah kika ce bakina yana burge ki? "




"Eh Wallahi yaya, bakaga ba har wani iyayi kakeyi dashi"



Dariya ta bashi sosai saida yayi mai isar shi sannan ya kuma kallon ta yad'ora da cewa "Jiddah na Inama dai inada damar nuna miki wannan bakin nawa da yake burge ki mallakin ki ne, Allah ka nunamin wannan lokacin"


Batare da ta gane me yake nufiba tace "amin"


*********************"""***********************"
Sai a wannan lokacin suka iso cikin matarantar babu b'ata lokaci Yaa Sheikh yashiga bin duk wata ka'ida da zata   tabbatar da Jiddah ta zama cikakkiyar 'yar makaranta, ansha artabu sosai Kafin Jaddah ta cika Yaa Sheikh ya tafi saida malamai sukayi mata jan ido tukunna. 


Yaa Sheikh yabar Jiddah zuciyar sa cike da tausayin ta. 






Khairaty😘✍🏻
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼


            *Yaa Sheikh*


🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼



*BY:U. K. Y. For real*😘




🌈 *kainuwa writers asso*✍🏻




*Dedicated to Mmn khairy*🤝🏻 😘



               *60 to 65*



*Alhamdullah ala kulli halin am back, am really really  appreciate your  support and cares, prayers, calls, messages.... I will use this ofacunity to great all my family and friends......* 
*BARKA DA SALLAH*






Wani malami ne daga cikin malaman gurin ya daka mata tsawar don yaga da alama Jiddan shagwa'babbiya ce. 



"Ke! "


Ay kuwa a razane ta d'ago jikin ta na rawa tace "na'am"



Sake hade rai malamin yayi yace "ki fara d'aukar kayanki  one after the other kina kaiwa bakin bishiyar can kafin students su tashi daga class saiki samu mate d'inki su taya ki d'auka"

Ya k'arasa maganar yana mata nuni da bishiyar. 



Ba musu ta fara d'aukar kayan nata,  tana dana sanin zuwan ta boarding a zuciyarta......  



Nana kuwa a lissafin ta yau ne sahibar ta ta zata zo don haka take allah allah a tashi daga class...     



Yaa Sheikh tuk'i kawai  kake yanajin kamar bai kyautama Jiddahn shiba dama bai biye taba dama bai amince da zuwanta boarding school ba amma aykin gama ya Riga da ya gama saidai yasan sai ya dage wajen yak'i da zuciyar shi  don tun daga yanzu ya fara jin missing din Jiddahn, ..."fuuhhh! "Wata  zazzafar iska ya furzar yana karawa da cewa.... 

" ohhh Allah help me out,...  son 'yar k'aramar yarinya zai kashe Abdallah"


Duk shi kad'ai yake maganarsa. 


(Ayya Abdallah abun tausayi ) 



Adaddafe ya cigaba da driving din zuciyarsa cike da tunani.... 




Ba karamin dad'i Nana taji ba saboda ganin aminiyar ta don haka bakin ta yaki rufuwa...... 



"Ke wai dagaske kece Jaddah? "

A salib'e Jiddah ta kalli Nana kafin tace"to da wacece"? 


Ay kuwa sai Nana ta kwashe da dariya sannan tace "ke kinga fiskanki fa kinga yadda kike wani gwab'a fuska kamar kina gaban wannan mai jallabiyar da tashi kafiya naci?  To bari kiji in fad'a miki garama ki zama jan ido idan ba hakaba a raina ki"
......... Ta karashe maganar tana d'aga kirji sama, duk wani iskanci na yan makaranta Nana ta haddace su, kai harda karin nata ma Saboda Nana ba baya bace. 


Jiddah datai sak'are tana kallon ta,   zunbura baki tai tace "daga zuwa na zamu fara ko ?...   to Dabadan shi mai jallabiyar ba da baki ganni anan ba yar rainin wayo "



"Kedai kika sani... Bari yan jss 1 suzo wucewa su d'aukar maki kayan" 


"Gaskiya Nana ke yar rainin hankali ce kina mate dinsu kice su d'aukar miki kaya? Ko dama ana haka? "


Wata dariya Nana ta yi tace "baki da maths, to Dalla cen ay sababbin zuwa nake samu wanda basu sanni yar jss 1 bace saina had'e rai na kirasu na ayke su kuma suje ba musu, sai su zata ni senior  ce kinsan wawaye ne"


Kafin Jiddah tayi magana saiga yan jss 1 nan sun taho don da ka gansu zaka gane sabbabbine kuma yan jss 1 saboda sababbin uniform din jikin su. 

Ay kuwa ba bata lokaci Nana ta raba musu kayan tace sukai mata blue hostel kasancewar nan aka bawa Jiddah ita kuma nana a green hostel take, amma hakan bai wa Nana dad'i ba amma ba yadda zatai. 



Koda suka shiga cikin hostel Jiddah saroro tai kuma zuciyarta cike da tsoro take bin students da kallo  ganin su da tai daga mai mini skat sai mai skin tied sai mai half beast  ga Uban acuci maza Akan kowacce. 

"Tab" shine abunda Jiddah ta iya cewa. 



"Ke kema sabuwar zuwa ce"? 

Wata free Fed ta tambaye su  

"Eh sabuwar zuwa ce kuma nan blue aka kawo ta"

"Ok to zoki hau layi kafin a raba muku gado".... 



Saida Nana ta shiryawa Jiddah komai sannan tace mata "to kizo muje hostel dimu na baki ruwa kiyi wanka na ara miki kaya kafin a baku naku"


Ita dai Jiddah ba uhm ba uhm-uhm Saboda mamakin Nana take Saboda  yadda take magana tana d'aga kirji. 



A haka Jiddah tai wata d'aya zuwa wannan lokacin ta goge ta gane kan komai duk wani iskancin yan makaranta itama ta iya wani girgije girgijen k'irjji ta iya dama ga abubuwa sun fara bayya na. 



"Babyn Figgo kije ki karbo mana abinci"


Kicin kicin Jiddah tayi da rai "ke wace babyn Figgo? To wallahi bazanje ba ke kije dama kece acici"

Ta k'arasa magana tana wani daga bombom sama sannan ta fice daga class din. 


"Abdallah wai kai kuwa lafiyar ka kuwa? Kana fama da olcer sannan kace kullum sai kayi azumi?  Wlh tun wuri ka samawa kanka lafiya"


Sarai ya gane abinda Ummi take nufi amma shi dai a nasa lissafin azumin shine samun lafiyarsa da kuma maslaha agare shi. 

"Wai ni yanzu da nake wannan jiran gawan shanun shin wai Jiddah zata karbeni a matsayin miji?  kuma abokin rayuwar ta? Kuma zata soni kamar yadda nake son ta?"... ......


Duk wannan tambayoyin da bashida amsar su yayima kanshi kafin daga  bisani karar wayan shi ya katse shi......... 


Khairaty ✍🏻
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼

*Yaa Sheikh*


🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼



*U. K. Y. for real*😘

*Dedicated to Mmn khairy*🤝🏻




              *65to70*



Wayar tashi ya d'auka sunan da ya gani ne yasa shi dai daita nutsuwar shi, school authorities  ya kane rubuce kan Wayar tashi don haka baiyi wata wata ba ya d'auka....... 



Cikin gaggawa ake neman yaa Sheikh yaje Madina saboda za ayi musu exam wanda daga wannan exam d'inne idan mutun yaci za'a bashi ayki da acormadation, (muhalli) da kuma yarjejeniyar albashin da za ake bawa mutun idan ya amin ce. 




Bayan ya sha ruwa ne suna zaune da su ummy da Abdul majid kasancewar sun dawo yake shaidawa Umme abunda yake faruwa.... 




Ba karamin dad'i Umme taji ba dajin wannan labarin saboda ko ba kamai tasan zasu huta idan Abdallah ya samu aykin nan saboda Abdallah akwai taimako da kuma tausayi ita dai fatan ta Allah yasa su dace ya samu yaci exam din. 



"To Abdallah yanzu tafita kama ka keban? " 

"Wlhy kuwa Ummy nah"

"To Allah yasa adace saika kira Abii ka fad'amai, zuwa yaushe ne to suke bukatar kuje?"


Ta karashe zancen nata da tambayar shi. 


"Ummy sati biyu ne"

"Ok to Allah ya taima ka" 


"Amin"



"Ku... tunda kuma dawo ma kuwa kunyi muraja'a? Ko kuma tun da kun zama yan boko shikenan kunyi bye bye da islamiyya?"

Abdul malik ne ya danyi k'arfin halin magana yana sosa k'eya"aa yaya wlh ni inayi saidai ko Abdul majid"
                Da sauri Abdul majid ya katse shi "kai Karfa ka had'ani da ya Abdallah wlh yaya nima inayi, yanzu ay girma yazo munsan dad'in abun, idan da badon Allah yasa munada na addinin ba ay da bamu kai haka a A. B. U ba tuni zasu bugo mu. 



Murmushi yaa Sheikh yayi  yana cewa "gara da kuka gane hakan ay"


Sun d'an taba hira kad'an kafin daga bisani Yaa Sheikh yayi musu sallahma zai wuce masallaci sallan isha daganan kuma zai tsaya Saboda akwai matasan da yake wa karatu bayan sallan ishan don haka yace wa ummy saida safe sukuma su Abdallah ya jamusu kunne karsu makara a jam'i.



"wayyo Allah na Nana wlh da gaske k'asan cikina ciwo yake min"


"Ke dalla nace miki marar kice take ciwo bawai k'asan ciki ba"


"To naji mara ta tana min ciwo"



Wata uwar shewa Nana tayi ta d'ora da gud'a "ayiiriiriiii su Jiddah za'a balaga a balallage "


"Kinga bana son iskanci fa Nana wannan wani irin magana ne kike? Ni banason iskanci"



"A'a kinga ikon Allah Jiddah kefa kikace kina ciwon mara kuma ciwon mara ay na mai period ne ita kuma mai period ay baliga ce "



Wata uwar harara Jiddah ta watsawa Nana "ke kika san wannan kinga tafiya ta"


Ta mik'e tana tafiya amma kirjin nan a sama


"Babyn figo maida k'irjin mana, idan kika koma gida kina irin wannan tafiyar ay sai mai jallabiya ya cinye ki d'anya da wannan shegen kallon da yake miki"


Ko juyowa Jiddah batai ba bare ta bata amsa.... 



Yau saura kwana uku yaa Sheikh yatafi kuma gobe ya yanke shawaran dubo Jiddah don bazai iya tafiya bai ganta ba,  acewar shi wai idan ya tafi bai ganta ba bazai iya tab'uka komai ba don haka gara yaje yaga beby love d'inshi. 





Fita yayi yayowa Jiddah shopping  kaca-kaca na yan makaranta  sannan yaje ya gayawa Ummy ko tana da sak'o gurin Jiddah idan tana dashi to ya zama cikin shiri don gobe zaije dubota sannan yaje ya gayawa Mamy ma. 




Ita dai Ummy bata so wannan zuwan da zaiwa Jiddah ba saboda tana tsoron kar yaje ya gano abinda zai sa ya kasa yin abun arzik'i a exam din nashi. 






Hhhhhhh tofa wannan shine kowa da nashi tunanin. Waye mai gaskiya Ummy ko Yaa Sheikh? 🤔🤔🤔

Thank you Yaa Sheikh fans aylobiyu furnai furnai😂🤣😂😘



Khairaty ✍🏻😍❣
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
                 *Yaa Sheikh*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼


_*ina godiya masoyana aringa hakuri da spelling mistakes please 😍*_


           


*U. K. Y. For real*😍

*Dedicated to Mmn khairy*🤝🏻

             
             *70to75*


Tsaye yake gaban mirror Yana feshe jikin shi da turare kamshi kawai ke tashi akowace kusurwa na d'akin kamar anyi b'arin turare. 


Sanye yake cikin wata gezna( shadda)  light  blue tayi matuk'ar amsarshi abunka da farin fata, dark blue din takarmi sauciki yasa da agogo da hula duk dark blue ne yayi kyau sosai. 



Cikin Sauri yake komai don k'arfe 3:00 na rana kuma yana so duk inda 4:00 yake ya zama yana kusa da Jiddah. 



Abdul majid ne ya shigo d'akin yana cewa "Yaya na gama wanke motan Abii din, yaya wai Abii din dawowa zaiyi ne? "


Ko kallon sa Yaa Sheikh baiyi ba ya bashi amsa da "a'a ni zan fita da ita, sannan idan ka gama surutun naka ka d'auki wad'ancen ladojin ka samin a boat "



Ya k'arasa maganar yana nufar cikin gida ya sami Ummy ya shaida mata ya gama shiryawa zai tafi. 


  "Hmmm Abdallah kenan yanzu duk wannan shirin na Jiddah ne?"


Shidai Yaa Sheikh  sosa kai kawai yayi yana murmushi baice komai ba. 

"To Allah ya kiyaye, sannan ga kantu nan na soya mata ka kaimata kasan mutuniyar taka a wajen kwad'ayi tafi kauri"


karb'ar kantun  yayi yana murmushi yana  sak'a abubuwa iri-iri a ransa. 



"To Ummy ta gode bari naje gurin Mamy dagacen zan wuce"





Itama Mamy duk kayan kwad'ayi ta had'a mata takuma bada sak'on a gaishe mata da ita. 




***********


"Don Allah Nana kiyi sauri ki gama inada assignment ke kuma kin tsaya iyayi"


"kai ni karki cinyeni,  mu tafi". 




Jiddah Sanye take cikin doguwar riga ta morris blue ta matseta ta sama ta kasa kuma ta bud'e ga yanmatanci ya fara bayyana, wani d'an k'aramin farin hijab ne iya wuya,  ba wani kwalliya taiba amma tayi matuk'ar yin kyau. 





4:00 acikin school d'in su Jiddah tayiwa Yaa Sheikh , bai tsaya ko ina ba sai admin block yabi duk wani procedure da visitors suke bi don haka aka tura messeger ya kira Jiddah Usman. 



Yaa Sheikh komawa yayi cikin moto yana jira yaga ta ina Jiddah zata b'ullo sai wani gyara zaman hula yake yana daidaita kafad'a😂lol.


Sanda Jiddah taji wai anzo mata tasan ba kowa bane illa Yah  Abdallahn ta don haka ko takan Nana bata biba ta nufi inda visitors ke tsayawa,...  ay kowa tana zuwa ta hango moto din Abii an faka ta can k'asan wata bishya aykuwa su Jiddah harda wani sake gyara tafiya irin Yaa Sheikh yasan fa tazo boarding school ta Kara wayewa. 


Tacikin mirror ya hangota  tana takowa ko'ina na jikin ta yana motsawa tamkar cikakkiyar budurwa. 


   " Yaaa salam.... What? It's Jiddah?  I can't believe it "



Kafin ya gama mamakin nasa har ta k'araso dai-dai saitin Window d'in mai zaman banza, itama Allah Allah take taga shin Yah Abdallahn ne kokuwa. 



Ido biyu sukai da Yaa Sheikh wanda ya kafeta da ido ko k'iftawa ya kasa yanajin wani abu na bin jikinshi kamar kiyashi  yaa Sheikh bai k'ara shiga wani haliba sai da yaga Jiddah na wani irin tsallen murna gami da shagwa'ba, 

"Laah aykuwa shine wayyo dad'i"

Sa hannu tayi ta bud'e kofar tun kafin yayi mata izini, ta fad'a cikin moto din batare da ta kalli halin da Yaa Sheikh yake ciki ba ta kaimai wani wawan hug, suman zaune yayi lokaci d'aya kuma numfashin shi yana kokarin d'aukewa. 



"Kai amma naji dad'i yaya Abdallah nah yasu ummy? "

Duk tana rungume dashi take jera mai wannan tambayar.


Da kyar ya iya zame jikin shi daga nata sannan yace "Jiddah duk wannan murnan na ganina ne?  to ki tsaya mu gaisa mana"da kyar ya ke maganar kamar zai shid'e. 

"Ok Yah Abdallah nah ya kake? "


"Lafiya klau Jiddah ya karatu? "

"Lafiya lau yaya"


"Ummy da Mamy suna gaisheki"


"Ina amsawa, Allah sarki Ummy nah, me tabaka ka kawomin? "



"Abun dad'i"


"Yeee! To nagode yaya"



Shidai Yaa Sheikh kawai kallon Jiddah yake a ranshi kuma yana mamakin yadda akai ta canza gaba d'aya kamar ba ita ba. D'an saisaita kanshi tayi ya wayance da cewa


"To yanzu dai ki bani labari kafin lokaci ya kure minti goma suka bani na ganki"



"Ok tom kasan me Yah Abdallah?"


"Aa Jiddah saikin fad'a"


Shagwa'be fuska tai kamar zatai kuka sannan ta fara magana "kaga ranan nan ne naita ciwon k'asan ciki naita  kuka"ta k'arasa maganar tana shigewa jikin shi. 


Bubbuga bayanta yashiga yi yana bata hak'uri. 
"Meyasa to bakije clinic ba?"

"Naje sun bani magani amma bai daina ba"

"har yanzu? " ya tambayeta

"Aa banda yanzu"


"To idan ya kuma kiyi addua zai daina amma karki kuma yin kuka, ko kinaso nima nayi? "

Mak'e kafad'a tayi sannan tace "banaso"


"Yawwa Jiddah good girl, kinsan me nakeso dake? "
"A'a "

"So nake Kimin addua jibi zan koma madina zamuyi exam, sannan Kimin alkawari zaki ringa karatu sosai"



Ya kafeta da ido yana sauraron amsar ta, itama shi take kallo idon ta cike da kwalla. 

"Yah Abdallah tafiya zakayi, idan katafi sai Yaushe? "



"Ohh no!  Don't cry my jiddo ba dad'ewa zanyi bafa kafin ki dawo ma Insha Allah na dawo Kedai Kimin addua"

Yana maganar ne yana goge mata hawaye. 


"Nayima alkawari zan ringa karatu sosai sannan zanyima addua Allah ya bada sa'a"

"Amin jiddo nah, kinga har kocacin ya cika ki tafi class idan kun kama evening prep saiki je ki karbi sak'onki "

Idonta fall da hawaye tace tom yah Abdallah nagode ka gaishemin da Mamy na da ummy na"tana kaiwa nan ta bud'e moto d'in tafita da gudu. 
Baiyi k'okarin hanata ba saboda a halin da yake ciki komai zai iya faruwa idan yace zai tsaya rarrashin ta. 

Kansa ya d'ora kan  sitiyari yana mai mamakin kansa, lallai shi lafiyayyan namiji ne kallon kansa yayi yana godema Allah da Jiddah bata ganshi ba bare ta ga halin da take ciki. 

Da kyar ya iya lallab'awa ya kama hanyar komawa gida , yana tausayin kansa yana kuma tuna yadda yabar Jiddah tana kuka. 




_*Don Allah kuyi hakuri da spelling mistakes, ina kaunarku masoya na*_



Khairaty 😍✍🏻
[7/4, 7:50 AM] ‪+234 903 274 9200‬: 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
         *Yaa Sheikh*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼


*U. K. Y. For Real*😍


*Dedicated to Mmn Khairy*🤝🏻

     


                *76 to 80*


Ikon Allah ne kawai ya kaisa gida, yana parking aka soma kiran Sallan Magrib, yana fitowa ya shiga gida. Ummy dasu Abdulmajid yasamu a tsakar gida suna Alwala. 


Da d'an sakin fuska ya k'arasa cikin gidan, Ummy ta d'ago da fara'a tana cewa

"Sannu da zuwa Abdallah"

Da murmushi ya amsa, su Abdulmajid suma suka masa Sannu da zuwa sannan suka fita dan zuwa masallaci. Bokiti ya d'auka ya d'ebi ruwa ya shiga wanka, dan yanda Jiddah ta rud'asa dazu yasa dole yayi wanka.

A gurguje ya gama ya fito ya sauya kaya ya nufi masallaci. Ana idarwa ya dawo gida, D'akin Ummy ya shiga da Sallama ya zauna tare da fad'in

"Wash!"

Ummy tad'an kallesa cike da kulawa

"Yaya dai? Ya kasamu 'Yar tawa"

Da wani k'ayataccen Murmushi jin ta ambato Masoyiyar tasa yace

"Tana nan Lafiya lau Ummy, kinga kuwa yanda ta k'ara natsuwa"


Ummy tayi dariya tana girgiza kai. Mik'ewa tayi ta d'auko mai abincinsa ta aje tana cewa

"Nasan kanajin Yunwa"

Yayi saurin Jan Food flask din ya bude ya soma ci yana lumshe ido, Hira ya soma mata kamar bashi bah duk hiran rabi na Jiddah neh.


Kallansa kawai take cikin ranta ko kawai mamaki me na ganin yadda yaa Sheikh yake kokarin maida kansa wawa.

"Alhandulilahi ala kulli halin, wannan abuncin naki da dad'i yake Ummi ta"yafad'a yana aje Food flask d'in a gefe.

Murmushi ummy tayi,  suka cigaba da hira. 

 AbdulMalik da AbdulMajid ne suka shigo a tare da sallama, Ummy da Yaa Sheikh suka amsa masu suka zazzauna tareda musu sannu. AbdulMalik yace


"Ya Abdallah Ya Jiddo nasan tana nan tana cigaba da rashin ji da lalaci kamar yanda aka saba to wai yanzu ma wa zataiwa wannan shagwa'bar tatane? "
 Ya k'arasa maganar suna kwashewa da dariya shida Abdul majid.


Yaa Sheikh yabud'e baki neman zaiyi magana abbulmajid ya karb'e
 
"Kai kake tunanin wannan ma kamata yayi ka tambaya acen wane yake dafa mata indomei  mai yaji , yarinya sai kafurin kwadayi wai ita bazataci tuwo ba,  hala madai ba a yin tuwo a makarantar nasu"



Ya maida dubansa ga Ya Abdallah


"Ya Abdallah Halan An baka Complain d'inta a makarantar? "

 


Kasa magana Abdallah yayi saboda takaici, so dayawa su Abdulmajid na shirmansu da Jiddah na tsokana amma bai
Taba jin haushi kamar nayau bah, mik'ewa yayi fuskansa ba walwala yace

"Ummy barin shiga wajan Mamy"


"Ka gaisheta" cewar Ummy

Toh kawai yace yasa takalmansa ya fita. Da sallama ya shiga gidan Mamy, kan sallaya ya sameta tana lazumi, zama yayi kusa da ita harta gama sannan ta juyo garesa

"Aa An dawo ne baba na"


Duk'ar dakai yayi k'asa tare da gaisheta, ta amsa fuska a sake tare da tambayansa ya hanya, ya amsa da lafiya lau. Shiru ne ya biyo baya chan tace


"Ya Jiddan? Nasan tana nan tana abinda ta saba musamman da yanzu babu mai saka mata ido"


"Aa Mamy! Jiddah yanzu ta chanza ba yanda kika santa bah, tayi Hankali sosai"


"Kaiya Babana, nasan fa halin Jiddah"


Yayi saurin kauda zanchan da cewa


"Mamy Addu'a kawai zaki cigaba da mata, Allah ya bata sa'a a karatunta"


Ta sauke ajiyar zuciya tace


"Addu'a kullum ina muku ba ita kad'ai ba, Allah ya shiryeku gaba d'aya ya shige muku gaba a duk alamuran ku"


"Ameen Mamy mun gode"




                 *****

Da kuka ta k'arasa gurin  Nana ta zauna tana cigaba da sharan hawaye

"Ke wai yaneh haka mene kike ma mutane kuka? "


Tad'an d'ago kanta chab'e chab'e da hawaye


"Yaa Abdallah neh! Ni gida nakeso na koma"


Nana taja dogon tsaki tare da tureta

"Nifah na tsani Yaa Sayyadi yake ko Yaaa Sheikh? Ban gane wannan bibiyan da yake miki bah faa"


Jiddah ta sake d'ago jajayen idanunta tace

"Duk cikin yayye na babu mai sona kamarshi ya Abdallah yana matuk'ar sona koda nake da k'arancin shekaru Nasan da haka ya Abdallah bai barni nayi kukan maraici ba, kuma kema shaida ce tunda gashi kina gani inayin makaranta mai kyau kamar yadda kema me uba araye kikeyi"

Nana ta dungureta tana turo baki


"Dallah chan kedai banza ce, wani so bayan ko 'yar tsarabar d'an makaranta bai miki bah"


Maganganun Nana ne ya soma bata haushi ta d'ago tana goge hawayen fuskanta


"Ke tsaraban yan makaranta ya dama"


Ta fita ta barta nan baki bud'e cike da Mamakin yau ita Jiddah ke yab'ama magana.


Class ta koma gaba d'aya jikinta a sanyaye saboda kewar gida, ko inda Nana take bata kalla bah har aka tashi, sai da yamma sannan ta samu ta amso kayan da Yaa Abdallah ya kawo mata. Ba kunya Nana ta matso tana duba ledojin


"Haba k'awaliya romon kaza, ai nidake ba haka. Me Yaa Sheikh din ya kawo mana neh"


Jiddah dai batace mata komai bah dan Ciwon Maranta ne taji yana neman tashin mata. Tana kallo Nana ta jida abinda takeso tayi tafiyarta tana zagin Yaa Abdallah.



Bayan sun koma hostel ne Mara yace Bismillah, kuka kawai Jiddah take tana juye juye rik'e da maranta, Gaba d'aya d'akin ya rude, d'aya daga Cikin Mummys d'in makarantan neh ta shigo, da taimakonta Jiddah ta mik'e  sai yarfe hannu take tana kuka tare da turo baki gefe guda kuma tana kiran Mamy da Ummy.


Clinic suka wuce dan Kallo d'aya ta mata ta gane abinda ke damunta.





A firgice ya farka tare da dafe k'irjinshi yana kiran sunan Allah, Idanunsa ne suka ciko da kwalla murya a raunane yace



"Allah kasa Mafarkin nan ba gaskiya baneh, Allah kasa Jiddah tah na cikin koshin Lafiya"


Ya sake dafe kirjinshi sbda yanda zuciyarsa ke bugawa da sauri. Ba shiri ya fashe da kuka duk da taurin zuciya irin ta maza, kuka yake yana dafe da kirjinsa yana karanto duk addu'ar datazo bakinsa. 





Ummy Abdul/
khairaty ✍🏻
[7/4, 9:12 AM] ‪+234 903 274 9200‬: 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
         *Yaa Sheikh*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼


*U. K. Y. For Real*😍


*Dedicated to Mmn Khairy*🤝🏻

     


                *81 to 85*


Ganin kukan bazai fisheshi ba yasa ya mik'e ya saka jallabiya ya fito, Alwala yayi ya koma d'aki ya tada sallah, bai zauna ba saida yaji kiraye kirayen Sallahn Asubah.


Mik'ewa yayi dak'yar sbda yanda kansa ke masa wani irin mugun ciwo, D'akinsu Abdulmajid ya buga kamar yanda ya saba duk Asubah idan yaba gida. Yana tashin su ya wuce Masallaci.


Bashi ya shigo gidan ba sai karfe goma na safe, cikin gida ya shiga ya samu Ummy tana gyaran kayan miya, har k'asa ya tsugunna yace

"Ina kwana Ummy"


Ta d'ago suka had'a ido, ganin yanayin Idanunsa yasa ta juyo garesa dakyau tana cewa


"Lafiya Lau Abdallah, meya sameka naga idanunka haka?"


Yad'an dukar dakai k'asa yace


"Kaina ke ciwo tun jiya amma nasha magani"


"Allah ya baka Lafiya, tashi ka shiga ciki abin karinka na nan, nima sauri nake na gama Aiki dan Abby na hanya yau"


Murya a raunane yace


"Eh munyi waya jiya, Allah ya kawosa Lafiya"


Ta amsa da "Ameen"


Ya mik'e yace


"Ummy barin d'an watsa ruwa na kwanta tukun zanci abincin Anjima"


"Toh" tace dan bataso ta tsawaita magana saboda yanda ta lura da yanayinsa.



  
                  *******


Da kuka suka isa Clinic, sun samu Nurse mai Night Duty ta amshi Jiddah, kuka kawai take harda majina. Mummyn tace


"Kedai Wannan yarinya da shagwab'a kike, kiyi shiru mana ai girma ne ya sameki"


Cikin kuka ta turo baki tace


"Wallahi banasan girman na yafe"


Ta k'are maganan da sakin wani sabon kukan tana rik'e da Maran. Abu taji na gangaro mata daga k'asanta tasa hannu ganin jini yasa ta saki k'ara da karfi ta soma tsalle


"Wayyo Allah na shiga uku Jini na fitomin a gabana, na shiga uku Mamy zan mutu"


Nurse d'in ta daka mata tsawa


"Dallah yima mutane shiru"


Nan da nan ta shanye kukan ganin ba wasa a idon Nurse d'in gata K'atuwa bak'akirin da ita.

Allurah ta zuk'a a syringe Jiddah na ganin haka ta soma aniyan arcewa Mummy ta dank'ota, Nurse d'in ta mata alluran ta saki k'ara tana kuka sosai.

Nurse din ce ta d'auko Pad da sabon Pant ta nuna mata yanda ake anfani dashi sannan tace ta shiga Toilet tayi wanka sai tasa. Ba musu ta shiga dan mugun tsoron Nurse din takeji yanzu. Tana shiga Nurse din tace Mummy ta samo mata wasu kaya ta chanza, ba musu ta koma Hostel dinsu.



Nana ta samu ta zafga tagumi, ta tambayeta inda kayan Jiddan suke ta nuna mata, kaya ta d'aukan mata ta fita, koda ta koma har ta gama wankan kayan kawai take jira.


Cikin minti kad'an ta kimtsa amma har lokacin bata daina hawaye da turo baki bah. Drip nurse din tasa mata bayan ansha artabu da ita. Nan ta kwana juye juye tana kuka sai gaf da asubah ta samu Ya saketa sannan ta samu bacci.




K'arfe Sha biyu da rabi Yaa Sheikh ya farka da Addu'an tashi daga bacci, Hiransu Abdulmajid da Abby yaji Hakan ya tabbatar masa da ya dawo.


Da sauri ya mik'e dan ciwon kan ya sakesa yanzu sai jikinsa daba k'wari, A tsakar gida ya samesu suna shan iska ya k'arasa ya zauna kan tabarma kusada Abby ya gaida shi da fara'a, Abby ya amsa yana cewa


"Ya jikin Ummyn ku kecemin bakajin dad'i"


Yad'an duk'ar dakai yace


"Dasauk'i Abby"


Abby yace


"Ya Jiddah tah? Ance kaje dubata jiya"


Nan da nan ya saki lallausan Murmushi


"Tana nan Lafiya Abby, tace na gaisheka"


Abby yace "Ina amsawa, Ya shirye shiryen tafiyan naka? Gobe ne koh?"


Kai ya gyad'a, Abby ya masa Addu'a sosai sannan suka cigaba da hira. Sai bayan la'asar yaje yad'anyi siyaiya ya dawo. A daran ya shiga Yama Mamy sallama ya fito dan da asubah zai bar gida. Addua tamai sosai sannan ya fito.


Da Asubah ana fitowa a masallaci Abby yakaisa Airport da rakiyan su AbdulMalik. K'arfe Shidda jirginsu ya d'aga zuwa k'asar saudi Arabia.



K'arfe Sha biyu na dare wanda a k'asar Nigeria yake goma na dare  ya sauka a Prince Muhammad bin Abdulaziz Airport dake Madina.


Taxi ya nema yahau zuwa masaukin shi........ 






Long lasting friendship,  my in low. Ummy Abdul 😍khairaty ✍🏻
[7/4, 7:50 AM] ‪+234 903 274 9200‬: 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
         *Yaa Sheikh*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼


*U. K. Y. For Real*😍


*Dedicated to Mmn Khairy*🤝🏻

     


                *76 to 80*


Ikon Allah ne kawai ya kaisa gida, yana parking aka soma kiran Sallan Magrib, yana fitowa ya shiga gida. Ummy dasu Abdulmajid yasamu a tsakar gida suna Alwala. 


Da d'an sakin fuska ya k'arasa cikin gidan, Ummy ta d'ago da fara'a tana cewa

"Sannu da zuwa Abdallah"

Da murmushi ya amsa, su Abdulmajid suma suka masa Sannu da zuwa sannan suka fita dan zuwa masallaci. Bokiti ya d'auka ya d'ebi ruwa ya shiga wanka, dan yanda Jiddah ta rud'asa dazu yasa dole yayi wanka.

A gurguje ya gama ya fito ya sauya kaya ya nufi masallaci. Ana idarwa ya dawo gida, D'akin Ummy ya shiga da Sallama ya zauna tare da fad'in

"Wash!"

Ummy tad'an kallesa cike da kulawa

"Yaya dai? Ya kasamu 'Yar tawa"

Da wani k'ayataccen Murmushi jin ta ambato Masoyiyar tasa yace

"Tana nan Lafiya lau Ummy, kinga kuwa yanda ta k'ara natsuwa"


Ummy tayi dariya tana girgiza kai. Mik'ewa tayi ta d'auko mai abincinsa ta aje tana cewa

"Nasan kanajin Yunwa"

Yayi saurin Jan Food flask din ya bude ya soma ci yana lumshe ido, Hira ya soma mata kamar bashi bah duk hiran rabi na Jiddah neh.


Kallansa kawai take cikin ranta ko kawai mamaki me na ganin yadda yaa Sheikh yake kokarin maida kansa wawa.

"Alhandulilahi ala kulli halin, wannan abuncin naki da dad'i yake Ummi ta"yafad'a yana aje Food flask d'in a gefe.

Murmushi ummy tayi,  suka cigaba da hira. 

 AbdulMalik da AbdulMajid ne suka shigo a tare da sallama, Ummy da Yaa Sheikh suka amsa masu suka zazzauna tareda musu sannu. AbdulMalik yace


"Ya Abdallah Ya Jiddo nasan tana nan tana cigaba da rashin ji da lalaci kamar yanda aka saba to wai yanzu ma wa zataiwa wannan shagwa'bar tatane? "
 Ya k'arasa maganar suna kwashewa da dariya shida Abdul majid.


Yaa Sheikh yabud'e baki neman zaiyi magana abbulmajid ya karb'e
 
"Kai kake tunanin wannan ma kamata yayi ka tambaya acen wane yake dafa mata indomei  mai yaji , yarinya sai kafurin kwadayi wai ita bazataci tuwo ba,  hala madai ba a yin tuwo a makarantar nasu"



Ya maida dubansa ga Ya Abdallah


"Ya Abdallah Halan An baka Complain d'inta a makarantar? "

 


Kasa magana Abdallah yayi saboda takaici, so dayawa su Abdulmajid na shirmansu da Jiddah na tsokana amma bai
Taba jin haushi kamar nayau bah, mik'ewa yayi fuskansa ba walwala yace

"Ummy barin shiga wajan Mamy"


"Ka gaisheta" cewar Ummy

Toh kawai yace yasa takalmansa ya fita. Da sallama ya shiga gidan Mamy, kan sallaya ya sameta tana lazumi, zama yayi kusa da ita harta gama sannan ta juyo garesa

"Aa An dawo ne baba na"


Duk'ar dakai yayi k'asa tare da gaisheta, ta amsa fuska a sake tare da tambayansa ya hanya, ya amsa da lafiya lau. Shiru ne ya biyo baya chan tace


"Ya Jiddan? Nasan tana nan tana abinda ta saba musamman da yanzu babu mai saka mata ido"


"Aa Mamy! Jiddah yanzu ta chanza ba yanda kika santa bah, tayi Hankali sosai"


"Kaiya Babana, nasan fa halin Jiddah"


Yayi saurin kauda zanchan da cewa


"Mamy Addu'a kawai zaki cigaba da mata, Allah ya bata sa'a a karatunta"


Ta sauke ajiyar zuciya tace


"Addu'a kullum ina muku ba ita kad'ai ba, Allah ya shiryeku gaba d'aya ya shige muku gaba a duk alamuran ku"


"Ameen Mamy mun gode"




                 *****

Da kuka ta k'arasa gurin  Nana ta zauna tana cigaba da sharan hawaye

"Ke wai yaneh haka mene kike ma mutane kuka? "


Tad'an d'ago kanta chab'e chab'e da hawaye


"Yaa Abdallah neh! Ni gida nakeso na koma"


Nana taja dogon tsaki tare da tureta

"Nifah na tsani Yaa Sayyadi yake ko Yaaa Sheikh? Ban gane wannan bibiyan da yake miki bah faa"


Jiddah ta sake d'ago jajayen idanunta tace

"Duk cikin yayye na babu mai sona kamarshi ya Abdallah yana matuk'ar sona koda nake da k'arancin shekaru Nasan da haka ya Abdallah bai barni nayi kukan maraici ba, kuma kema shaida ce tunda gashi kina gani inayin makaranta mai kyau kamar yadda kema me uba araye kikeyi"

Nana ta dungureta tana turo baki


"Dallah chan kedai banza ce, wani so bayan ko 'yar tsarabar d'an makaranta bai miki bah"


Maganganun Nana ne ya soma bata haushi ta d'ago tana goge hawayen fuskanta


"Ke tsaraban yan makaranta ya dama"


Ta fita ta barta nan baki bud'e cike da Mamakin yau ita Jiddah ke yab'ama magana.


Class ta koma gaba d'aya jikinta a sanyaye saboda kewar gida, ko inda Nana take bata kalla bah har aka tashi, sai da yamma sannan ta samu ta amso kayan da Yaa Abdallah ya kawo mata. Ba kunya Nana ta matso tana duba ledojin


"Haba k'awaliya romon kaza, ai nidake ba haka. Me Yaa Sheikh din ya kawo mana neh"


Jiddah dai batace mata komai bah dan Ciwon Maranta ne taji yana neman tashin mata. Tana kallo Nana ta jida abinda takeso tayi tafiyarta tana zagin Yaa Abdallah.



Bayan sun koma hostel ne Mara yace Bismillah, kuka kawai Jiddah take tana juye juye rik'e da maranta, Gaba d'aya d'akin ya rude, d'aya daga Cikin Mummys d'in makarantan neh ta shigo, da taimakonta Jiddah ta mik'e  sai yarfe hannu take tana kuka tare da turo baki gefe guda kuma tana kiran Mamy da Ummy.


Clinic suka wuce dan Kallo d'aya ta mata ta gane abinda ke damunta.





A firgice ya farka tare da dafe k'irjinshi yana kiran sunan Allah, Idanunsa ne suka ciko da kwalla murya a raunane yace



"Allah kasa Mafarkin nan ba gaskiya baneh, Allah kasa Jiddah tah na cikin koshin Lafiya"


Ya sake dafe kirjinshi sbda yanda zuciyarsa ke bugawa da sauri. Ba shiri ya fashe da kuka duk da taurin zuciya irin ta maza, kuka yake yana dafe da kirjinsa yana karanto duk addu'ar datazo bakinsa. 





Ummy Abdul/
khairaty ✍🏻
[7/4, 9:12 AM] ‪+234 903 274 9200‬: 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
         *Yaa Sheikh*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼


*U. K. Y. For Real*😍


*Dedicated to Mmn Khairy*🤝🏻

     


                *81 to 85*


Ganin kukan bazai fisheshi ba yasa ya mik'e ya saka jallabiya ya fito, Alwala yayi ya koma d'aki ya tada sallah, bai zauna ba saida yaji kiraye kirayen Sallahn Asubah.


Mik'ewa yayi dak'yar sbda yanda kansa ke masa wani irin mugun ciwo, D'akinsu Abdulmajid ya buga kamar yanda ya saba duk Asubah idan yaba gida. Yana tashin su ya wuce Masallaci.


Bashi ya shigo gidan ba sai karfe goma na safe, cikin gida ya shiga ya samu Ummy tana gyaran kayan miya, har k'asa ya tsugunna yace

"Ina kwana Ummy"


Ta d'ago suka had'a ido, ganin yanayin Idanunsa yasa ta juyo garesa dakyau tana cewa


"Lafiya Lau Abdallah, meya sameka naga idanunka haka?"


Yad'an dukar dakai k'asa yace


"Kaina ke ciwo tun jiya amma nasha magani"


"Allah ya baka Lafiya, tashi ka shiga ciki abin karinka na nan, nima sauri nake na gama Aiki dan Abby na hanya yau"


Murya a raunane yace


"Eh munyi waya jiya, Allah ya kawosa Lafiya"


Ta amsa da "Ameen"


Ya mik'e yace


"Ummy barin d'an watsa ruwa na kwanta tukun zanci abincin Anjima"


"Toh" tace dan bataso ta tsawaita magana saboda yanda ta lura da yanayinsa.



  
                  *******


Da kuka suka isa Clinic, sun samu Nurse mai Night Duty ta amshi Jiddah, kuka kawai take harda majina. Mummyn tace


"Kedai Wannan yarinya da shagwab'a kike, kiyi shiru mana ai girma ne ya sameki"


Cikin kuka ta turo baki tace


"Wallahi banasan girman na yafe"


Ta k'are maganan da sakin wani sabon kukan tana rik'e da Maran. Abu taji na gangaro mata daga k'asanta tasa hannu ganin jini yasa ta saki k'ara da karfi ta soma tsalle


"Wayyo Allah na shiga uku Jini na fitomin a gabana, na shiga uku Mamy zan mutu"


Nurse d'in ta daka mata tsawa


"Dallah yima mutane shiru"


Nan da nan ta shanye kukan ganin ba wasa a idon Nurse d'in gata K'atuwa bak'akirin da ita.

Allurah ta zuk'a a syringe Jiddah na ganin haka ta soma aniyan arcewa Mummy ta dank'ota, Nurse d'in ta mata alluran ta saki k'ara tana kuka sosai.

Nurse din ce ta d'auko Pad da sabon Pant ta nuna mata yanda ake anfani dashi sannan tace ta shiga Toilet tayi wanka sai tasa. Ba musu ta shiga dan mugun tsoron Nurse din takeji yanzu. Tana shiga Nurse din tace Mummy ta samo mata wasu kaya ta chanza, ba musu ta koma Hostel dinsu.



Nana ta samu ta zafga tagumi, ta tambayeta inda kayan Jiddan suke ta nuna mata, kaya ta d'aukan mata ta fita, koda ta koma har ta gama wankan kayan kawai take jira.


Cikin minti kad'an ta kimtsa amma har lokacin bata daina hawaye da turo baki bah. Drip nurse din tasa mata bayan ansha artabu da ita. Nan ta kwana juye juye tana kuka sai gaf da asubah ta samu Ya saketa sannan ta samu bacci.




K'arfe Sha biyu da rabi Yaa Sheikh ya farka da Addu'an tashi daga bacci, Hiransu Abdulmajid da Abby yaji Hakan ya tabbatar masa da ya dawo.


Da sauri ya mik'e dan ciwon kan ya sakesa yanzu sai jikinsa daba k'wari, A tsakar gida ya samesu suna shan iska ya k'arasa ya zauna kan tabarma kusada Abby ya gaida shi da fara'a, Abby ya amsa yana cewa


"Ya jikin Ummyn ku kecemin bakajin dad'i"


Yad'an duk'ar dakai yace


"Dasauk'i Abby"


Abby yace


"Ya Jiddah tah? Ance kaje dubata jiya"


Nan da nan ya saki lallausan Murmushi


"Tana nan Lafiya Abby, tace na gaisheka"


Abby yace "Ina amsawa, Ya shirye shiryen tafiyan naka? Gobe ne koh?"


Kai ya gyad'a, Abby ya masa Addu'a sosai sannan suka cigaba da hira. Sai bayan la'asar yaje yad'anyi siyaiya ya dawo. A daran ya shiga Yama Mamy sallama ya fito dan da asubah zai bar gida. Addua tamai sosai sannan ya fito.


Da Asubah ana fitowa a masallaci Abby yakaisa Airport da rakiyan su AbdulMalik. K'arfe Shidda jirginsu ya d'aga zuwa k'asar saudi Arabia.



K'arfe Sha biyu na dare wanda a k'asar Nigeria yake goma na dare  ya sauka a Prince Muhammad bin Abdulaziz Airport dake Madina.


Taxi ya nema yahau zuwa masaukin shi........ 






Long lasting friendship,  my in low. Ummy Abdul 😍khairaty ✍🏻
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
           *Yaa Sheikh*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼


*U. K. Y. For Real*😍


*Dedicated to Mmn Khairy*🤝🏻

     


                *86 to 90*

*Ummy Abduol wannan page din nakine farar yarinya yar d'agwas*😍😅



Kafin Safiya Ciwon maran ya saketa haka Drip din da aka sa mata ya k'are. Saida Nurse din ta turketa tasha magani sannan ta koma hostel.


Koda ta k'arasa duk Student nata hada hadan shiryawa dan Attending Class, Da Nana taci karo tana ganinta tayi dariya tana girgiza jiki


"Su Jiddah an balaga sai aure"


Jidda ta had'e rai 


"Auren lafiya?"


Dariya Nana ta sakeyi tana tafiya tana cewa


"Barin tafi kamin 'Yan iskan Seniors din nan suzo gwara ke zaki iya bada excuse din bakida lafiya"


Bata jira cewar Jiddan ba tayi tafiyarta zuwa Assemble Ground. Sauri sauri Itama tayi wanka ta sauya Pad d'inda Nurse ta bata sannan ta shirya tsaf ta nufi Assemble ground.


Ana gamawa suka wuce aji, Maths ne First Period yau, sam Jiddah ta tsani Maths ga teachern bai iya koyarwa ba wani lokacin har gyangyad'i take, ta juya ga Nana data hakince kan kujera tana nunama wata daga cikin 'yar class dinsu Note dazata kwafar mata

"Nana naga ranar dazakiyi note da kanki"


Wani Mugun murmushi tayi kamar na Boss tace


"Allah ya kiyaye, ai shiyasa Kikaga na bud'e wuta ban bari wata shegiya ta raina ni bah"


Kan Jiddah ta bata masa Maths Teachern su ya shigo Class din tare da wasu Student su biyu kyawawa d'aya bak'a d'aya fara. Gabatar dasu yayi a matsayin sababin student, sannan yasa su gabatar da kansu


Farar ce ta soma magana cikin tsantsar Turanci tace sunanta Firdausi Ahmad, d'ayar kuma tace sunanta Amina Ibrahim. Tunda suka shigo Nana ta kafesu da ido ko kiftawa batayi. 


Teachern ya basu izinin zuwa su zauna, Ware ido suka soma dan neman inda zasu zauna, Nana ta galla ma wasu student dake kusada ita harara sukayi saurin mik'ewa ta juyo da fara'a tana cewa


"Kuzo ga wuri"


Ba musu suka nufi inda take suka zauna tare da cewa "Thanks" sai wani kaud'i suke suna jujuya ido.




               ********



A bangaren Yaa Sheikh kuwa bai samu ya shiga school ba sai washe gari
Da wuri ya shirya ya shiga makarantarsu, Direct Department dinsu ya wuce inda ya samu sauran d'alibai burjik kowa na harkan gabansa, hannu yasa a aljihu don dauko phone dinshi saboda ya kira Nu'aiym.


 Dafashi yaji anyi ko ba'a fad'a ba yasan Nu'aym dinne neh dan haka da murmushi a fuskarsa ya juyo.

Hannu ya mik'a masa sukayi musabaha cikin harshen Larabci Nu'aym yace 


"Ka dawo lafiya ya mutanen gidan"


Abdallah ya amsa da 


"Lafiya lau wlh kagafa yanzu nake shirin kiranka sai gaka "

"Banason borin kunya faa abokina kawai shige muje"

Ba musu Yaa Sheikh ya bishi. 


Cikin Hall d'insu suka shiga suna cigaba da tattauna yanda jarabawan tasu zata kasance gobe.


Ranar a library school suka yini suna karatu dukaninsu kwakwalwa tayi charji, sai dare suka koma masaukinsu.


Washe gari da wuri suka shiga makaranta cikin lumtsetsiyar Lambo d'in Nu'aym, a Parking space na makarantar sukayi Parking, kasancewar sabuwar fitowar motace yasa larabawan dake tsakar Wajan maida hankalinsu ga motar sai santin ta suke.


A tare suka fito dukansu suna sanye da doguwar jallabiya
Na Abdallah fara k'ar na Nu'aiym bak'i, dukansu suna sanye da jan rawani a kansu, sunyi kyau sosai bama kamar Abdallah dan shigar yasa kyansa k'ara fitowa kamar d'an Arab country.


Cikin department dinsu suka shiga, karatu suka d'an sakeyi sannan suka
Shiga Exams d'insu. Cikin ikon Allah basu wani d'au lokaci ba suka gama dan duk abinda suka karanta shi ya fito musu.


Suna gamawa suka sake shiga mota suka nufi wani Eatery dake kusa da makarantar tasu dan Karyawa.



                  *****


Allah Allah Nana take a tashi Break dan ta Lurah New Comers din nada d'an Maik'o Maik'o. Ana Ringing Bell Student suka Fita, Har Jiddah ta mik'e Nana tace


"Jiddah ina kuma zaki, ki tsaya mana muyi fira"


Ba musu ta dawo ta zauna tana d'an b'ata fuska


"Nifa yunwa nakeji idan ke bakiji"


D'aya daga cikin New comers din mai suna Firdaussi tace


"Ai muma yanzu zamuje muci abincin"


Nana ta soma murmushi tana kallansu


"Sunana Nana Khadija Idris amma Nana ake cemin"


Ta nuna Jiddah dake gefe tace


"Ita kuma sunanta Jiddah, dukanmu 'yan unguwa d'aya ne tun daga primary school muke tare"


Firdaussi ta yatsine fuska tana bin Jiddan da kallo sannan tace


"Ni kuma sunana Fiddy"


Ta nuna ta kusa da ita 


"Sai Sis dina Meenah, mu 'yan Kaduna neh"


Nana ta gyad'a kai tare da rik'e hab'a


"Tun daga kaduna kukazo nan makaranta"


Kan Fiddy ta bata amsa Meenarh tayi saurin cewa


"Am Tired of all this dan Allah ku tashi muje muci Abinci dan am Hungry"


Nana tayi saurin mik'ewa suka fita. Dinning sukaje dan cin abinci, Kallan kallo Meenarh da Fiddy suka tsaya yi ganin abincin dake gabansu, Meenarh ta fashe da kuka


"Wallahi Uncle Sadiq ya cucemu, ya za'ayi ma mu iya cin wannan disgusting abincin"


Fiddy ta fara rarrashinta ta  rik'e mata hannu suka bar Dinning arean, Summ Summ Nana ta bisu kamar jela, Jiddah ko binsu tayi da kallo tayi ta zauna ta soma cin abincinta.



Koda Aka koma Class mamaki ne sosai ya kama Jiddah ganin yanda Nana ke nan nan dasu Fiddy har abin ya soma bata haushi, ko kallansu bata k'arayi ba ta maida hankalinta zuwa karatun da Business studies Teachernsu keyi.



Saida aka tashi sannan Nana ta kulata, a tare suka nufi Hostel. Din su  Jiddah kasancewar cen aka kaisu fiddy ita kuwa Nana tama gaba d'aya ta koma rayuwa acen in kin ganta a hostel dinsu to saida dalili, 

Haka suka k'arasa hostel din Nana  na binsu a baya. Bayan sun natsa sun cire School uniform Meenarh ta waiwaya ta kalli Jiddah wacce ta kwanta kan gadonta rik'e da English text book tana dubawa, sanan ta maida dubanta ga Nana


"Wannan Friend din taki bata magana neh? Ni tunda muke hira banji tayi magana bah"


Nana ta tab'e baki tace


"Indai Jiddah ce ba abinda bazaki gani bah, narasa ganeta taki ta waye ta saki jikinta"



Fiddy ta kyalkyale da dariya tana kallan Jiddah sannan tace


"Dani keda kyanki dana more,...  kehh! Tab da sauranki"


Ta rik'e hab'a kamar mai tunani


"I will Ronse up wallahi"


Meenarh da Fiddyn sukasa dariya duka.


Haka dai Jiddah ta bisu da kallo har aka kad'ai c exter. 



Khairaty ✍🏻
Ummy Abdul 😍
[7/13, 5:49 AM] 0mmer Farouk: 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
         *Yaa Sheikh*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼


*U. K. Y. For Real*😍


*Dedicated to Mmn Khairy*🤝🏻

     


                *91 to 95*



Basu suka samu  zaman hira ba sai washe gari bayan an tafi break, bayan sun gama cin abinci Meenarh ta kalli Jiddah tace


"Jiddah kinada kyau wallahi, dani keda kyanki babu wanda ya isa ya raina ni wallahi"


Jiddah tad'anyi murmushi batace komai bah, Fiddy tadanyi dariya tace


"Kinga mu ada a Dambo intl school muke, Uncle dinmu ne ya chanza mana school ya kawomu nan wai saboda bamajin magana"


Ta kalli Nana wacce ta kafesu da ido tana murmushi kamar wawiya


"Wai dagaske Munada rashin ji?"


Nana tayi saurin girgiza kai Alamar

"Aa"


Fiddy ta juya tana kallasu duka tace


"Kinga a makarantar da mukayi a baya duk da mu yan primary ne amma we have class, sboda kowa ubanta yana biyan kudi mai yawa so ba raini. Kunsan meh?"


Dukansu suka girgiza kai 


Fiddy tace


"Akwai yayamu sunanta Suhaima ranan naji tana cewa Sun hada squad itada kawayenta na manyan yara, so nima inaso muyi haka a school din nan"


Meenarh ta doka tsalle tana tafa hannuwanta


"Thats why i like uh Sis, haka wallahi za'ayi"


Jiddah sai binsu da ido take kamar wacce tayi k'arya sannan tana tunanin taya haka zata faru.


                  ********


Abdallah da Nu'aym yawo ranar sukayi a cikin Riyad, Washe gari kuma suka shiga Jiddah, Shopping sosai Abdallah yayi ma Iyayensa da kuma k'annensa bama kamar Jiddah, duk abinda ya gani na mata sai ya daukar mata wani dan Bob short ya gani ya mashi kyau da kad'an yafi pant yayi sauri ya faki idon Nu'aym ya sa a cikin kayan sa . Babban burinsa yanzu bai wuce yaji result dinsa bah, dan hukumar makarantar sun shaida musu bayan Jarabawar da kwana uku result zai fito.




Ranar basu suka koma Madinah ba sai d'ayan dare, tun a k'asa sukayi ma juna sallama Abdallah ya kwashi ledojin dayayi shopping Ya Shiga lift ya nufi apartment dinsa.

Washe gari da wuri suka shirya, yauma sanye Nu'aym yake da bak'ar jallabiya wanda ya fito da kyansa da kuma hasken fatarsa. 


Yana tsaye Abdallah ya fito cikin lift, baki Nu'aym ya saki ganinsa da kaftan abinda bai tab'a ganin yasa bah.

Abdallah ya k'araso inda yake yana 'yar murmushi

 
"Yadai?"


Nu'aym ya mayar masa da murmushin yana cewa


"Ka ganka kuwa? kayi kyau sosai, ban tab'a ganinka da irin kayan nan bah"


Dariya Abdallah Yayi yana kallansa tare da girgiza kai yana tunawa da bomsort din da yasiyama Jiddah wanda idan sunyi aure zatake saka mishi, kuma ya tabbata da Nu'aym yagani da yasha nagana , Nu'aym yadan b'ata fuska yana kallanshi


"What's funny"

Ganin ya b'ata rai yasa ya k'arasa ya rik'e kafadansa yace


"Am sorry toh, mu tafi dan lokaci na tafiya."


Ba musu Nu'aym yayi gaba suka shiga motan suka d'au hanya, waya Abdallah ya zaro ya soma neman layin Abby, Ringing d'aya biyu ya d'auka tare da sallama.


Cike da ladabi ya amsa tare da d'an duk'ar dakai ya gaida shi kamar yana gabansa, Abby ya amsa yana tambayansa ya jarabawa, cikin natsuwa ya soma masa bayanin tun zuwansa har zuwa yau dazasu duba sakamakon jarabawan tasu.


Lokaci lokaci Nu'aym kan juyo yana kallan Abdallahn da d'an murmushi ganin yanda ya natsu yana wayar duk yanda akayi wanda suke wayan yanada matuk'ar muhimmanci da kuma girma a wajansa.


Addu'a sosai Abby ya masa na samun nasara sannan ya mik'ama Ummy wayan suka gaisa itama ta masa addu'a sosai sannan sukayi sallama ya kashe yana murmushi cike da annashuwa.


Har Nu'aym ya bud'e baki zai masa magana sai kuma ya fasa ya cigaba da driving d'insa hankali kwance. Cikin k'ankanin lokaci suka isa makarantar tasu, Direct notice board suka nufa, sun samu d'alibai da dama suna duba result d'insu hakan yasa suka koma gefe har saida aka d'an ragu.


Abdallah ne ya soma ganin masa, ya samu points sosai har yayi yawa, Shima Nu'aym yaga nasa shima yayi nasara dan ya samu abinda yakeso. Hannu suka mik'a ma juna sukayi musabaha saboda murna, A take ya sake kiran Abby ya sanar dashi, sunyi farinciki sosai tare da yi masa Addu'a.


Sai da yanma sannan aka samu attending d'insu, batare da wani b'ata lokaci ba aka basu takardar d'aukansu aiki, a matsayin Malaman Jami'a sai dai Jami'ar da zasu koyar ba d'aya baneh anma yana kusa da juna.


Murna wajan Nu'aym da Abdallah ba'a magana. Murnan su sam yak'i b'oyuwa. Jiddahn shi ce ta fad'o masa a rai, ya saki murmushi a ransa yana ayyana Jiddansa ta kusa zama nasa san don son zata zama tashi cos dama jiran ayki yake.




To dama haka rayuwa take wasu suyi nasara wasu kuma akasin hakan don da dama wasu basuyi nasara ba. 


Khairaty😍
[7/13, 5:49 AM] 0mmer Farouk: 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
         *Yaa Sheikh*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼


*U. K. Y. For Real*😍


*Dedicated to Mmn Khairy*🤝🏻

     


                *96 to 100*


Sai da suka fito daga office din sannan suka bubud'e lettern dan karanta abinda ya k'unsa


Bayan Abdallah ya karanta nasa ya d'ago yana kallan Nu'aym wanda shima ya maida hankali kan takardar hannunsa


"Alfaisal University Riyadh zanyi aiki"


Nu'aym ya sake kallan nasa sannan yace


"Ni kuma a Prince Sultan University, Its ok ai duka Riyadh din neh"


Suka mik'a ma juna hannu sukayi musabaha cike da jindad'i. Motan Nu'aym suka nufa suka nufi gida cike da murna. Saida suka isa sannan Abdallah ya Kira Abby ya fad'a masa abinda ke faruwa.


Abby dasu Ummy sunyi matuk'ar farinciki, d'aya d'aya Abby ya mik'a ma su Ummy wayan suka masa murna harda Mamyn Jiddah dan ta shigo gidan. Sun masa fatan Alheri sosai.



A cikin Satin sukayi bikin murnar Kammala makarantar, taro ne wanda ya amsa taro, daga Abdallah har Nu'aym sakin baki sukayi ganin manyan mutane wanda suke gani a tv. Sarkin Saudi Arabia wato Sarki Salman shima ba'a barshi a baya bah tare da tawagarsa harda babban d'ansa dayake matuk'ar ji dashi.


Anyi taro lafiya, Abdallah har kyauta ya samu na First Class daya samu. Hakan yasa tauraronsa ya haska a taron. Anyi an gama kowa ya koma gidansa lafiya. Saboda tsananin gajiya a Apartment d'in Nu'aym suka kwana, washe gari suka soma shirya kayansu dan zuwa Riyadh, Bayan sun isa Masaukin Abdallah Nu'aym ya fara saukeshi dan kowa an basa gidansa kusada makarantar dayake.



Abdallah ya masa godiya sannan shima ya wuce nasa masaukin. Ya samu ya huta asabar da lahadi, Ranar monday k'arfe bakwai a Alfaisal University Riyadh ya masa. Ba tare da b'ata lokaci ba ya nufi department d'inda xai koyar.


Tafiya yake cikin sanyinsa kamar yanda ya saba, yana sanye da Brown Jallabiya da Bak'ar hula, sosai kayan suka amshesa, duk inda ya wulga sai an kallesa har abin na basa mamaki. direct reporting yayi sannan ya aje jakansa a office d'in da aka basa ya wuce Lecture hall dan an sanar dashi yanada Class da safiyar ranar.



Tunda ya shiga ajin wasu mata su biyu dake zaune a gaba suke kallansa kamar zasu cinyesa. Guntun tsaki yaja a hankali sannan yayi musu sallama tare da gabatar da kansa, sunyi murna sosai da kasancewarshi malamin su.


Bai d'au wani lokaci ba ya soma musu darasi. Cikin kwanciyar hankali yake musu karatun, da tsantsar larafci, tunda ya fara daya d'aga kai sai su had'a ido da D'aya daga cikin 'yan matan dake gaban, a haka har ya gama musu tare da tambayansu ko sun gane, duk suka amsa da na'am. Ba b'ata lokaci ya musu sallama ya fita.



Bashi yabar makarantar ba sai K'arfe biyar na yanma, a gajiye ya tari Taxi ya nufi gida tare da kudurin siyan moto saboda irin hakan.




            *Bayan Wata Biyu*




Meenarh ce ta shigo class tana yatsine Fuska tana kallan wata d'aliba dake zaune a kan kujeranta da alama sabuwar d'aliba ce. Cikin k'asaita ta k'arasa ta rik'e k'ugu tana jujjuya ido


"Ke! Uban wa yace ki zauna min a kujera"


Cike da tsoro yarinyan tace


"English teacher ce tace na zauna"


Jiddah da Nana suka shigo a tare, Fiddy na biye dasu a baya, a tare suka k'arasa wajan Jiddah ta kalli yarinyan tace



"Ina kuma muka samu wannan"


Meenarh tace



"Wai new student ce, kuma dan iskanci a seat d'ina"


Nana ta galla ma yarinyar harara


"Ke tashi dan ubanki"



Ganin yanda suka zazzare mata ido yasa ta mik'e dasauri ta canza kujera tana kallansu a tsorace.



Jiddah ta fashe da dariya suka tafa itada Meenarh


"Kuna Burgeni wallahi" cewar Jiddah tana cigaba da dariya



"Stay were uh are!"

 Abinda sukaji kenan daga bayansu
Ko ba'a fad'aba sun san Social studies teacher neh, a daidai inda suke suka k'ame. Teachern ya shigo yana kallansu, cikin harshen turanci yace



"Dama nasani ku hud'u nan neh tsaye, Come forward and knell down"


Meenarh ta chuno baki tana gaba suna biye da ita har gaban ajin sukayi Knell down sai turo baki suke.


Malamin mai suna Ahmad Yusuf ya kalli Jiddah yana girgiza kai


"Hauwa'u Usman sanda kikazo makarantar nan uh are Calm, why do uh change?"


Jiddah Ta sake tura baki ta kauda kai tana wani jujuya ido, baice komai ba sai girgiza kai dayayi ya cigaba da koyarwa.



A haka suka tsaya har ya gama sannan yace suje su zauna, Fiddy tayi gaba tana wani turo k'irji tana b'ata fuska, baice komai ba ya fita ya koma staff room. Yana fita Nana tace


"Nifah Mr Ahmad Yusuf d'in nan ya takura mana Wallahi"


Meenarh taja tsaki


"Tsiyar Boarding school kenan"


Fiddy tayi saurin cewa


"Wallahi kuwa"


Jiddah ta amshe da cewa


"Ai yafi ma samin ido, baki maji sunana ya kiraba"


Nana tace


"Dallah kyallesu, mu chanza topic dan bansan jin wannan maganar mah"




                *******


Salati yayi ya mik'e zaune yana mik'a tare da duba Jikinsa, Gani yayi gaba d'aya ya jik'e. Ya rik'e kansa da hannu biyu yana d'an girgiza kai


Harga Allah yana matuk'ar buk'atar mace a kusa dashi, kuma ba kowa ba sai Jiddah. Kwanakin nan mafarkan dayake yana making love da Jiddah ya soma yawa.



Ya lumshe ido ya bud'e yana d'an murmushi, he really enjoy the moment he had with her on his Dream. A hankali ya furta


"Da dad'i... Balle kuma reality"

Ya saki murmushi mai sauti


"I can't wait"


Dole ya mik'e ya shiga toilet yayi wanka tare da wanke boxern ya fito. 



K'arfe Takwas ya Shiga school direct Office d'inshi ya wuce ya bud'e ya shiga. Ya zauna kenan akayi knocking, ya bada izinin shigowa. Yarinyan nan Student d'inshi ce ta shigo cikin b'akar jallabiya har k'asa tayi rolling da farin veil. Tana sanye da Butterfly eye glasses.


Tsaki yaji kad'an, gaba d'aya yarinyar ta soma takura masa, sam baya ra'ayinta shi ko sunanta ma bai saniba.


Cikin harshen larabci tace


"Zan iya zama?"



"Idan kinaso"



Tad'anyi murmushi sannan ta samu guri ta zauna. Agogon azurfan hannunsa ya duba K'arfe takwas da kwata yasan yanzu a nigeria shidda da kwata kenan na safe.


Wayansa ya d'auka ya soma neman layin Abby, bugu biyu ya d'auka tare da masa sallama, Abby ya amsa, cikin ladabi suka gaisa ya tambayi su Abdul ya amsa da lafiya lau.



Jimmm yayi har saida Abby yace


"Akwai wani abu neh?"


Ya sosa k'eya kamar yana ganinsa yace


"Dama yau ne Visiting d'insu Jiddah, Ummm... Shine...Umm"


Abby yad'anyi dariya yace


"Abdallah kenan! Kanadai ji da k'anwar nan taka".


Yad'anyi murmushi, Abby yace



"Ai Ummynku na nan nata shiri gaba d'aya zamu rankaya mu tafi zuwa anjima"


Dad'i ne ya lullub'esa yace


"To Abby, a gaida su mamy"


Abby ya masa sallama ya kashe kiran. Had'a girar sama data k'asa yayi ya maida dubansa ga Yarinyar dake Office d'insa


"How may i help uh"



Khairaty😍
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
             *Yaa Sheikh*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼


     

*U. K. Y. For real*✍🏻



Dedicated to Mmn Khairy 🤝🏻


It's your day my special friend Ummy Abdul thank you for every thing. ❤❤❤



                   *109*

Shiga falon sukai hannun yaa sheikh rike da kayayyakin su,ya kunna light din falon,  tsaf ta karewa falon kallo har yafi nasu Nu'aiym kyau ba wani tarkace kayan kallo ne sai kujeru sai kuma dinning area dake a cen gefe gidan fes dashi. 


Bayan ta karewa falon kallo tai zamanta kan kujera Cike da gajiya,  shikuma ya koma ya d'auko musu sauran kayan.


Sanda ya dawo har ta fara bacci Cike da gajiya baiso zai tashetaba saboda sunriga da sunyi Sallah isha a gidan Nu'aiym amma da yake ka'idarsa sai yayi alwala yake kwanciya to dole itama ya Dora ta akan irin tsarin sa, don haka ya fara tashin ta amma ko motsawa batayi ba. 


D'aukan ta yayi cak bai direta ko inaba sai toilet dake cikin dakin da ya kaimata kayan ta. 



"Ke Jiddah....  Jiddah bud'e idonki kiyi alwala "


Cikin magagin bacci ta farayi mai Kuka  "nidai ka kyaleni bazanyi wani alwala ba bacci nakeji"



"Aykuwa saikinyi wlh idan ba hakaba na Zane miki jiki"


dakyar ya samu tayi alwalan tana gamawa ta fito ta haye kan gadon dake dakin . 


Da kallo kawai ya bita sannan yayi mata addu'a ya kashe hasken dakin ya nufi nashi dakin. 




Wanka yayi ya d'auro alwala sannan yazo ya fara shirin kwanciya kamar wani mace  feshe jikin shi yayi da turaruka masu kanshi sannan ya hau taje sumar kansa da gemunsa masu ban sha'awa sai sheki suke,  daga shi sai dan gajeren truoser . 




Sai tunani yake bacci ya kasa d'aukar sa "yah rabbih"ya fad'a a fili "ko ya zaman namu zai kasance? "Yayima kanshi tambaya, "Allah kasani ina son ta kuma ina bukatar ta...... But dole nakai zuciyara nesa banaso ta rainani kuma inajin tausayin ta.... To amma hakan bazai yiwu ba bazan iya kauda kaina daga kanki ba jiddah Saida goyon Bayan ki"ya karasa maganar kamar tana jin sa. 

Cen yaji wata zuciyar tana  cewa" to idan kuma zargin ka gaskiya ne fa"?



"No banida wannan amsar "ya fad'a Cike da kosawar zancen zucin da yake. 


Da haka bacci yayi akwan gaba dashi cike da mafarkai kala kala. 



Da asuba yaji motsin tashin ta don haka da yafito tafiya masallaci ko kallon kofar dakin baiyi ba bare ma ya shiga don acewar sa kallon Jiddah a wannan yanayin tada zaune tsaye ne, don haka salin alin ya fice. 



Har karfe  Tara bata tashi ba zuwa wannan lokacin Yaa sheikh har ya gyare gidan yayi wankan sa yana kwance kan three sitter yana kallon Al-jazira abun mamaki sanye yake da three quieter trouser blue da armless riga yellow sosai kayan suka amshe shi. 



Sai Tara da rabi yaji motsin ta don haka ya tashi ya shi ga kitchen don had'a mata breakfast. 



Ita kuwa wanka ta shiga tayi wankanta fes da ita sannan ta fito ta tsaya gaban mirror tana kallon kitson kanta da Ummy tasa aka mata k'ananun kitso ne shuku uku mai style ba k'aramin kyau yayi ba "tab wannan kitson Ya za'ayi na iya tsefewa "ta fad'i tana karewa kitson kallo. 



Gurin da  Yaa sheikh Ya ajiye mata kayyakinta ta je ta bubbude kayan da suka siya ta dauki. Body spray ta feshe jikin ta dasu sannan ta shiga neman kayan da  zata  sa har ta bud'e kayan da ta taho dasu daga gida ta fasa. "Wannan daka siyomin su zansa "ta fada tana duba Wanda zata sa daga cikin kayan.




Egg Ya soya mata sai tea mai kauri daya hada mata a kan dinning table Ya aje mata don har yagama  bata Tito ba don haka ya dawo ya cigaba da kallon sa yana jiran fitowar ta. 




Blue Jins Ne ajikin ta  iya gwiwa Wanda yayi bala'in dameta sai handless Riga raed itama bata rufe cibiyar ta ba gashi ta kamata itama saita koma kamar yar tsana (babyn roba) 



Sosai tayi kyau ta cikin mudubii ta gama kallon kanta"wlh a haka zan fita ni nace ka siyamin wadannan yan iskan kayan"tana gama fad'in haka ta fito, hango shi tayi a kwance ga mamakin ta sai taga ba jallabiya bace a jikin saba don haka ta kuma matsawa kusa don ganin kwakwaf, "da gaske ba ba jallabiyar bace "ta fad'i a ranta sannan ta maze ta nufeshi yadda zai ganta itama. 



"Ya hayyu Ya kayyumu bii rahmatika astagisu" wannan shine abinda Ya fad'i sanda yayi ido hudu da ita. 


'Dan rintse idon shi yayi sannan Ya kuma bud'e su a kanta tana tsaye a gabansa ta kafe shi da ido, wani irin abu yaji lokacin daya yanayin sa ya sauya idon sa ya canja yayi ja sosai "ina kwana yah Abdallah? "....ta fad'a tana nazarin yanayin sa 

Kai kawai ya iya dagawa Ya kasa bata amsa, ganin haka yasa tai wani dan fari da ido tana d'aga kafad'a a lamar Ko a jikin ta sannan ta kuma cewa "yah Abdallah am hungry "

Nuni yayi mata da dinning area a karo na biyu ba tare da yayi magana ba. 


"Owk' ta fad'a tana nufar dining din, bin bombom dinta yayi da ido yanajin kamar yaje ya cafke su "NO!  Come down Abdallah "ya fadawa kansa. 



Mi'kewa yayi don bayason sake kallon ta don gudun fitinar sa zata iya kaishi ga aykata komai don haka ya nufi d'aki ko kallon gabansa bai yi tsabar sha'awa Saida Yaje bakin k'ofar batafe da ya juyu ba yace "ke Jiddah "

"Yes"

Ta amsa mai

"Karki kuma sa wannan kayan ko maka mancin su , da fatan kinji? "


"Kai yah Abdallah Sabo dame? Bayan Kai ka siya da kudin ka... Nidai gaskiya ina son su kallifa yanda sukai min kyau "ta fad'a tana nufo shi don nuna mai, ay kuwa da sauriya shige dad'i yana cewa "nidai na fad'a miki idan kunne yaji jiki ya tsira"

Ganin yadda ya shige d'aki da sauri yasata kwashewa da dariya "wlh yau na fara sa kayannan ay Bani nace ka  siya ba"tana gama fad'ar haka itama tai shigewarta d'aki saboda ta gama cika cikin ta. 


Shi kuwa taayawa yayi yana sauke numfashi kamar Wanda yayi gudu "na siyi jaraba da kudi na..  Anya zan iya jurewa kuwa? No I can't keep looking u like this   because I can't  take it anymore "yayi maganar yana kallon dick d'in shi da shima yayi tsaye yana kallon sa har wani zafi yake mai, dafe kanshi yayi yana squeezing sumar sa "Ana tausayin ki bakya tausayin kanki... Am already knows my self dat is way Jiddah,  but I promise you  duk ta yanda kika biyu ta haka zanbi dake "ya fad'a  in a assured manner.



Shigan ta d'aki kwanciya  tayi tana reversing moment dinta da Fego, Saidai tana tuno da Nana ce ta had'a su taji ranta ya baci don haka ta tashi ta hau shirya kayan ta na jerawa a  kan mirror ta jera  komai ta sashi a muhallin da ya dace. 




Sai karfe biyu ya dayo daga sallan a zahar, kitchen ya shiga ya musu boiling  nuddles, ya zuba nashi yaci yayi zaman shi a falon yana kallo yana dan daddana phone din shi, number Nu'aiym yashiga kira Bayan sun gaisa yake mai zancen ne mawa Jiddah school da kuma samun ya yar ayki don idan ya koma ayki kuma Jiddah ta fara zuwa school abun zai had'e musu. 
  


Nu'aiym shawara ya bashi akan ya nema mata staff school dake cikin makarantar da Abdallahn yake ayki don samun sauki kasancewar ya fad'a masa Jiddah a o level take. 

Sallama sukai  akan zasu had'u anjima don sake tattaunawa , batun yar Ayki kuwa yace zai sa Rauda tayima mai aykinta magana don ta nemowa su Abdallahn. 


Yana gama Waya tana fitowa sanye da hijab din datai Sallah kallo d'aya yai mata ya d'auke kansa itama dinning ta nufa ganin food warmas ba tare da tace komai ba. 



Daga cen inda take cin abincin ta ce "yah Abdallah ka kiramin su Ummy "



"Ba yau ba " ya bata amsa a takaice yana barin falon"


Da harara tabi shi sannan ta dawo cikin falon ta zauna tana d'aukar remote tudduba channels din ta fara a haka har taci karo da   wani  Channel da ake Mexicans series maida hankali tai sosai gurin kallon film din duk da ba daga farko ta fara gani ba ta fuskanci na siyayyane ganin yadda ake kisses , don haka ta kudurce a ranta zatake kallon channel din saboda yanayin  film din ya burge ta. 




Da karfe biyar Nu'aiym yazo suka tattauna inda suka yanke shawaran fara fita gobe don ganin yadda samun makarantar jiddah zai kasance, sai Bayan magrib Nu'aiym ya tafi. 


Haka kuwa akayi washe gari suka fara processing  neman makaranta gashi kuma saura kwana biyar su koma ayki don haka abun ya had'ar sumu. 



Kwana hudu kenan  Yaa sheikh baya samun komawa gida har sai Jiddah tayi bacci amma duk da haka sai ya tasheta tayi alwala sannan Kullum sai ya yi mata blending kankana da danyen dabino da milk ya bata tasha kafin ta kwanta, sosai take jin dad'in wannan lemon madaran kamar yadda tai masa suna, batun rashin zaman shi a gida kuwa bai dameta ba saboda film din tsotsan baki yana deba mata kewa Shima a cewar ta as well. 





Yau sosai yakejin kewar ta don haka yayi kokarin gama komai akan lokacin don gudun kar ya iske tayi bacci Ana idar da sallan isha ya taho gida, a falo ya tarar da ita still tana kallon wannan Mexicans channel din(film din tsotsan baki)kamar yadda ta bashi suna  ,   sanye da half beast sai wani dan karamin wando inya cinya , daga inda yake yana iya hango yan boobs dinta ga sheep din hips dinta daya fito sosai"Yarin yarnan so take ta kasheni kawai"ya fad'a a zuciyar sa, kokarin dauke idon sa daga kanta yayi  a rashin sa'a kuwa ya sauke su kan saurayi da budurwa take romancing junan su cikin film din da Jiddah ta maida hankali take kalla, sosai hankalin sa ya kuma tashi ji yayi a wannan karon bazai iya hakura ba don haka yanufe ta.


"didn't I told you don't ever wear this indecent   dress Jiddah  ... Uhmm? "



A razane ta dago don batayi tunanin zuwanshi a wannan lokacin ba amma jin tambayar da yayi mata yasa ta marairaice cikin shagwaba tana wani bubbuga kafa boobs dinta sai shaking suke ta fara magana kamar da gayya"yah Abdallah wai me kayannan sukayi nidai inaso Kuma.... Be bari ta karasa ba saboda yadda yakeji kawai ya had'e bakinsa da nata kissing dinta ya fara kamar zai had'iye lips din nata, sosai jikinta ya dau tawa amma jin yadda yake wasa da harshen sa cikin bakinta yasa itama nata lissafin ya kwance batasan sanda itama ta fara tsotsan harshen saba, sake rudewa yayi jin Jiddah na mayarmai da martani, half beast d'in  ya d'age boobs dinta suka bayyana hannunsa yakai yana tabasu wani irin laushi yaji gasu yan dadai gasu a tsaye ay tuni kafar Jiddah ya fara rawa jin hannun yah Abdallah kan nonon ta shima ji yayi kamar kafarsa baza ta iya dakansa ba don haka ya kwantar da ida kan sitter wasa ya farayi da nipple's  dinta still yana tsotsan bakin ta tuni suka fita daga hayyacin su jiddah kuwa gani take kamar a cikin mafarki ne bada gaske ba, bakin shi ya mayar kan boobs dinta ya fara sucking dinsu "oh my God "kawai yake mai mai tawa Ita kuwa jin yasa boobs dinta a baki yana sosa mata nipple's dinta da ha'korinsa sai taji kamar jizon ta zaiyi aykuwa da k'arfin ta fara ihu tana cewa"wayyo nono na karka cije ni"ta fad'a tana kokarin zamewa. 

"NO! Jiddah please stop it let me be "yayi maganar yana matso da 'kugun ta kusa sashi sosai yana kokarin raba ta da wandon ta. 


"Wayyo nidai ka bari banaso"ta fad'a tana dukansa ganin abun nashi ya wuce inda take zato. 


Baima san tanayi ba hankalinsa yakai k'ololuwa wajen tashi don ganin shafaffiyar maran Jiddah a gaban shi tuni ya fara kokarin tura yatsan shi k'asan ta amma ko alamar shiga baiyi, amma sai dad'a turawa yake saboda wani mugun d'umi da santsi da yaji yana janshi gaba daya baya cikin hankalin sa. 


Tsoro ya fara bata ga wani zafi da takeji a k'asanta aykuwa ta kara bud'e murya tana ihu"nidai kyaleni wlh bana so "


"Lefin kine jiddah Saida nace miki karki Kuma sa kaya irin wannan amma da yake kunnen k'ashi gareki bakiji ba, don haka ki kyaleni nayi yadda nake so dake "magana yake kamar zautacce. 


Ganin da gaske yake yasa ta tattaro karfinta ta tureshi had'i da gasa mashi cizo. 



A galabaice ya cika ta saboda yaji zafin cizon sosai,  ay kuwa ganin ya cika ta yasa ta tashi da gudu ko takan wondan ta batabi ba tai d'akin ta a 360. 





Sorry for the spelling mistakes  manage pls. 

Na gama exams alhmdlh nagode da fatan alkairin ku gare ni👍🏻👍🏻

*khairaty*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
             *Yaa Sheikh*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼



*U. K. Y. For real*✍🏻


Dedicated to Mmn Khairy 🤝🏻

 
                   *110*


Da gudu Yabi bayan ta amma kafin ya k'arasa har ta rufe, cikin sanyi ya fara magana "please Jiddo nah ki bud'e min don Allah  ki bud'e zan kira miki su Mamy Kinji "


 Banza tayi dashi ta cigaba da kukan ta,  gajiya yayi da bugawa ga joystick dinshi da ya dameshi da ciwo, a haka ya lallab'a ya had'o mata watermelon and  milk juice  as usual ya kawo mata kofar dakin ya shaida mata ya kawo mata sannan ya shiga  dakin sa. 


Tana ji ya shiga dakin sa ta fito ta d'auki lemon madaran ta tana cewa"Wallahi bazan daina sa kayan nan ba kuma duk maitar mutun haka zai gani ya kyale, wlh mu zuba mu gani  "


Haka taita zuba rashin kunyarta ita kad'ai harda cewa wai  ashe masu jallabiya ma sun iya iskanci. 


Tas ta shanye lemon madarar ta tana cewa "gobe da kaina zan had'a kuma nasan zaiyi dad'i "ita kad'ai taita magana daga karshe bacci ya d'auketa anan k'asan hannun ta rike da cup din lemon madara. 



Dakyar ya samu yayi shirin  kwanciya amma bacci baiyi gigin d'aukar sa ba sai tunani kalakala a bangare d'aya kuma yanawa Allah godiya saboda Jiddah  tana da duk wani structure da yake  so a jikin mace, dama tun tuni ya san da hakan amma yau ya kuma gasgatawa. "Abdallah Allah yaga zuciyarka yaga yadda ka Kai zuciyarka nesa don gudun sab'a masa shi yasa yayi maka wannan kyautar "yaji zuciyar sa na fad'a masa, kayar bacci b'arawo ya sami damar dauke shi. 



Yau Monday kuma ayau ne yaa sheikh zai koma ayki tun safe yar aykin da mai aykin Rauda ta samo musu tazo ta fara aykin ta. 



Zoya itace sabuwar mai aykin su Zoya haifaffiyar kasar  misra ce sakamakon talauci da yake damun wasu daga cikin mazaun kasar yasa sukan fita wasu k'asashen don neman abunyi to Zoya ta kasance daga cikin masu neman na kansu don rufawa kansu asiri , ta dad'e a Riyadh anan take ayki a wani company amma sai yan companyn suka bukaci sake ma'aykata  kamar yanda suka saba lokaci zuwa sukan sake ma'aykata. 




 cikin shirin office ya fito Zoya ta kaishe shi cikin harshen larabci,  ya amsa sannan ya ce ta bashi phone d'inta, jiki na rawa ta ciro daga cikin aljihun uniform din aykin ta ta mik'a mashi, phone number dinshi ya saka mata sannan ya bata yana cewa"wannan shine number na idan akwai matsala ki kira ni sannan akwai yarinya a wanan d'akin tana bacci ki kuta da ita sosai idan ta tashi ki tambayeta abinda takeso taci saiki dafa mata, " 


Da "na'am" take ta amsa masa cike da ladabi duk da a shekaru ta girme shi don zatayi sa'ar Mamy. 

Kitchen ya shiga ya nuna mata yadda ake had'a watermelon juice sannan yace mata "duk sanda taci abinci ki had'a mata ki tabbatar tasha"


Nanma amasa mishi tai da "na'am"sannan ya fita yana missing Jiddah don yasan ko Yaje bazata bud'e mai k'ofar bama bare ta kulashi. 

Jiddah Wanda ta dade da tashi tana jinsa amma sai mamaki take dawa yake magana,  tanaji ya fita amma ko motsawa batayi ba Saida taji motsi yayi yawa a falo sannan ta fito don ganin ko wane. 


Da sauri Zoya tazo ta gaishe ta cikin larabci da turanci ta amsa mata sannan ta tsaya tana binta da kallo. Ba sosai Zoya kejin turanci ba amma tayi k'okarin yima Jiddah introducing kanta sannan ta tanbaye ta mezata ci. 

Ita dai Jiddah sai kallonta take daga bisani tace batajin yinwa , amma Zoya kin yarda tayi tace lallai sai Jiddah ta fad'a mata abunda zataci idan ba kahaba ta kira Yaa sheikh ta fad'a mai. Ganin Zoya bazata kyaleta ba yasa tace ta soya mata chips. 

Haka ta soya mata ta had'o mata da lemon madaran ta. 




faking motan shi yayi a inda ya saba cikin sauri ya nufi office dinshi kasan cewar akwai class din da zaima lecture karfe tara. 


As usual a k'ofar office d'in shi ya hango ta  a zauna kan barandar kamar mai jiran gafara, k'arasawa yayi ran shi a had'e don shi yama manta da ita sai yau daya kanta. 


Da sauri ta taso ganin sahibin nata da ta dad'e bata sa shi a idon taba sosai taga ya Kara kyau da kwarjini. 

Yiyai kamar bai ganta ba ya shige office din da sauri yana banko k'ofar da k'arfi , tanaji  ya sama kofar key, bata da zab'i daya wuce ta koma class don inda Sabo ta saba. 



Kwana uku kenan Yaa sheikh yana fita gurin aykin sa yana barin Jiddah da Zoya sosai Zoya take kula da Jiddah kuma ba laifi Jiddah ta fara sakin jiki da ita Saidai Zoya ba sosai takejin turanci ba itama Jiddah bajin larabci take ba. 






Yau tun safe Jiddah kejin ciwon mara tanaji Abdallah ya fita haka ma Zoya tana ta aykin ta amma ta kasa fita, dama kuma  tun ranar da yaa sheikh ya ritsata a falo bata sake bari sun had'u ba. 



Tayi tunannin ciwon ba serious bane amma zuwa yanzu ciwon Kara karuwa yake tun tana kuka a hankali har ta farayi da k'arfi. 



Zoya dake aykin ta zata Jiddah bacci take amma jin kamar sautin kuka yasa ta nufi d'akin jiddan hankali ta a tashe. 



A kwance ta ganta rike da mara  sai murkususu take, tana tanbayarta amma ta kasa bata amsa don haka ta shiga kiran layin yaa sheikh. 



Fitowar sa kenan daga class din su Hamna yaji Ana kiran sa. 

Muryan Zoya yaji a rud'e tana cewa Jiddah ba lafiya, shima hankalin shi a tashe yake tambayar ta meya same ta amma kafin ta bashi amsa yaji Jiddah na cewa wayyo maran ta. 

Kashe wayan yayi ya nufi moto dinshi ya tayar ya nufi gida zuciyar shi Cike da jin dadin zai samu damar jagwalgwala Jiddah yadda yaga dama. 





Manage please 

*khairaty*✍🏻
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
            *Yaa Sheikh*

🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼


*U. K. Y. For real*✍🏻


Dedicated to Mmn Khairy 🤝🏻


                 *111*



Ko faking mai kyau baiyi ba da sauri ya kashe motan ya shiga cikin gidan, bai samesu a falo ba don haka ya nufi d'akin Jiddah. 



Kwance take sai kuka take rik'e da mara Zoya sai aykin rarrashi take, a haka ya same su, Zoya tana ganin ya shigo ta mi shi sannu da dawowa ta fita. 



K'arasawa kan gadon yayi kicin sanyin murya ya fara magana "Jiddo na meya sameki uhmm? "


Cikin kuka tace "mata ce take ciwo"

Hannun shi na rawa ya jawo ta jikin shi yana shafa Bayan ta yace


"To sannu tashi kiyi wanka bari naje na samo miki magani ko?! "


Kokarin zamewa daga rikon ta yayi mata tai amma saboda jikinta ba k'arfi saita kasa. 



"Ko bazaki iya tashiba ne, na kaiki toilet din?  " ya kuma tanbayar ta


"Ni dai ka kyaleni kawai, ka tafi zanyi wankan "ta fad'a cikin kuka kuma har wannan lokacin bata bar kokarin zamewa daga jikinshi ba. 



Kallon yadda take kuka yayi tadan bashi tausayj saidai kuma duk abunda zatayi ya kudurce a ransa saiya rage zafi. 



"To naji zan tafi amma bari na turo miki Zoya ta rakaki kiyi wanka kuma  kici abinci kafin na dawo"


"Naji"tace tana hararar shi ta gefen ido,light kiss yayi mata akan  lips  din ta sannan ya fita. 




Kasa motsawa tayi don saukar lips din shi a kan nata sai taji ya kuma sa jikin ta ya zama very wick. 



Zoya ce ta taimaka mata tayi wanka saidai abun mamaki koda ta duba period dinta baizo ba,  wata riga mara nauyi iya gwiwa ta saka  ko bra bata saka ba sai pant kawai , sannan Zoya  ta had'a mata tea tasha,  ta koma ta kwanta. 


Shi kuwa gogon naku gudun wuce sa'a yake don gani yake kamar bazai karasa wajen siyan maganin ba, koda ya karasa pharmacyn kasa fita yayi daga cikin motan shi saboda joystick dinshi da yake tsaye duk yadda yaso mantar da tunanin Jiddah a ranshi don yasa mu ya koma daidai  kasawa yayi don haka yayi wa wani daga cikin ma'aykatan gurin magana yayi mai bayani kan ciwon Jiddahn sannan yaje ya had'o mai maganin ya kawo mai shikuma ya bashi kudin maganin. 




Sanda ya dawo har ta fara bacci don haka ya sallami Zoya kasan cewar ta kammala aykin ta dama. 



D'akin ya koma harda sa key sannan ya koma bakin gadon ya fara tashin ta, tashi tayi  ta zauna tana dan yatsina fiska, jikinshi ya jawo ta yana karewa nonuwan ta kallo  sosai hankalin shi ya kuma tashi shafa Bayan ta ya fara sannan yace "Jiddo na! "


Dagowa tayi suka had'a ido ba tare da ta amsa ba, sannan yace "ga maganin karb'i kisha"


Ya kima mata maganin Da ruwa dake cikin glass  cup, 


Saida da ta zame daga rikon da yayi mata sannan ta karba, tsayawa kallon maganin tayi sannan ta shagwabe fiska kamar zatayi kuka, ganin haka yasa yace mata

"yadai? "

"Da d'aci? "Ta tambaye shi 


"No ba wani da'ci, kishama kiji"


Saida ta kurbi ruwa sannan ta sa tablets din a bakin ta, Dakyar ta hadiye face dinnan a dame saboda d'aci. 


"Da d'aci ne? "Ya tambaye ta yana tallafo kanta, kafin ta bashi amsa yayi kokarin had'e bakin su yana cewa
" kawo na goge miki  d'acin"


Bata bari yakai ga yin abunda yai niyyaba tayi sauriTa tashi tana cewa "nidai bana so "


Shima da sauri ya tashi ya riko hannun ta jikinsa sai rawa yake don ranshi ya gama korawa cikin sigar magiya ya fara cewa "kiyi hakuri don Allah  Jiddo na ki taimaka min ki barni na tsotsi koda bakin ki ne  I beg Jiddah "


Kallon yadda yayi kalan tausayi tayi kuma itama tana so sai dai tanajin tsoron kar yayi mata irin na ranan nan. 


"Promise? "Ta tambaye shi

"Umm"kawai ya iya ce mata ya dauke ta cak ya maida ta kan bed bakin ta ya fara tsotsa cikin kwarewa da wani salo dashi kansa baisan ya iya ba, tuni suka fice daga hayyacin su ita ma Jiddah sosai take mayar mai da martani, Saida yaga ta shagala sosai sannan ya cire mata rigar jikin ta boobs d'in ta suka bayyana a gaban shi a rud'e yace "Jiddo na nasha? "Ya fad'a kamar an fixgi maganar daga bakin shi, idon ta a rufe ta  dinga daga mai kai alamar eh, haka ya dinga sucking boobs dinta yamar karamin Yaro. 


Kokarin rabata da pant dinta yake aykuwa tuni ta fara yimai kuka "nidai to mu bari haka bana so"


"Please Jiddah"ya fad'a yana Kara jan pant d'in 


"Ni dai a'a"ta dad'a cikin kuka tana kokarin sauka daga kan gadon, Fixgo ta yayi da karfi Ganin baza taji rarrashin ba yasa yayi kicin kicin da rai cikin kakkausar murya yace "kinaso na kyaleki?  " 


Da sauri tace"eh" tana goge hawayen face dinta 


Sannan yace"then hold this "ya fad'a showing his dick to her 


Zaro idon ta tayi tana girgiza kanta had'i da yerfe hunnun ta sannan tace "I can't "


"Ok.. To kwanta ki cire "yayi maganar yana daga giran shi daya sana. 


Kukan ta taci gaba ba tare da  tayi abunda ya sata ba, ganin zata b'ata mai lokaci yasa ya jowota yana kokarin cire mata pant din, ay kuwa da sauri tace 

"zanyi"

Ta fad'a tana rintse idon ta had'i da kama joystick din. 

Wata yar Kara ya saki saboda wani abu da yaji yana ratsashi, cikin zafin nama ya kuma  had'e bakinshi d nata. A haka har ya samu nutsuwa. 




*Khairaty*✍🏻
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
              *Yaa Sheila*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼



*U. K. Y. For real*✍🏻

Dedicated to mmn Khairy 



                 *112*



Cikin mamaki take d'an Satan kallon abunda ya fitar don har hannun ta ya b'ata, shi kansa a wannan karon saida yaji kunya, sannan ya basar ya jawota jikin shi ba musu ta lafe akan faffadan kirjin shi cikin rashin  sanin yanayin da take, amma a Kasan ranta sai taji kaba d'aya tunanin abunda ya wakana ne tsakanin ta da yaa sheikh, sai dai da ta tuna abunda ya sata rikewa sai taji tsigar jikin ta ya rashi ga wani mahaukacin tsoron Abun da ya kuma kama ta a haka bacci b'arawo ya sace ta, Dama abunda yaa sheikh yake fata kanan don sai yanzu ya danji nauyin abunda ya faru tsanin shi da Jiddon Dan shafa keyar shi yayi ya dan Kalli kansa yayi murmushi sannan ya tashi ya nufi toilet din Jiddah ya samarwa kansa tsarki sannan ya debo ruwa a cikin wani roba yazo ya wankema Jiddah hannun ta da  Abun nashi ya bata mata sannan ya dan sunbaci goshinta yanajin wani shauki a zuciyarsa,  a Kasan makoshin sa ya furta *"somun tab'i* ne wannan Jiddo zaki zama expert ne"

Ita kuwa jiddah baccin ta take batasan ma yanayi ba, shima fita yayi falo ya zauna don yasan idan ya cigaba da zama kusa da ita komai zai iya faruwa.




Sai da yamma ta tashi, wanka tayi don zuwa wannan lokacin period d'inta yazo, ta shirya kanta tsaf cikin wata Turkey gown.  Mai bin jiki sai kuma ta Dora kimono a saman ta bawata kwalliya tayi ba amma tayi balain kyau ta kama gashinta guru daya sannan tai rolling kan nata da wani dan k'aramin veil, saida ta Kalli kanta a mirror sannan ta fita falo, dai dai lokacin da yaa sheikh ya fito daga bedroom din shi sanye da jallabiya, sumar kanshi tasha gyara ga wani black glass da ya saka sosai yayi kyau, satar kallonshi tayi karo na farko da taga jallabiya tayi Mai mugun kyau gani tai bazata iya hakura ba ta kuma d'ago kanta ta kuma kallon sa shima tacikin glass din kallon ta yake bata sani ba, gani tai yana matsowa inda take Saura k'iris baifi taku d'aya ba don haka a zabure ta juya zata koma daki don yanzu tsoron had'uwar su guri daya take, ay kuwa kafin takai ga shiga d'akin ya chafko ta kuma still da glass dinnan manne akan face dinshi....  hikimar shi nasa glass din don yana jin nauyin abunda ya faru ne. 



Saida ya kare mata kallo yaga gaba daya a tsorace take sannan ya sassauta rikon da yayi mata ya sassauta murya yace "Jiddo wannan kwalliyar fa? "


Shuru ba amsa saima kallon gefe da take


"Baza ki magana ba? "


Nan ma ba amsa


"To shikenan tunda bazakiyi magana ba  dama gidan Nu'aiym zan kaiki tunda kin daina magana kiyi zaman ki nace kina gaishe su"yayi maganar yana  nufar k'ofar fita. 


Ay kuwa da gudu ta bi bayan shi ta rungume shi ta baya cikin kuka ta fara magana"Nidai Allah bazan zauna ba, kai wai bakajin tausayi nane? Wlh gani nake kai kamar ba yah Abdallah na ba kadaina jin tausayi na,,, nice fa.... "tayi Mai nuni da kanta still tana kukan kuma Cike da shagwaba taci gaba da cewa"nice fa jiddon ka.. Dazu bani da lafiya amma ko ka damu shine harda sani.." Sai kuma tai shiru saboda bazata iya fada ba. 

Tsayawa yayi Yana kallon ta ta bashi dariya kuma ta bashi tausayi



Matsowa yayi ya kuma rungume ta sarai yasan yanda yake treating nata bai dace ba duk da yasan ita ta ja amma bai kamata ba, a hankali ya dinga shafa bayan ta har saida yaji ta daina Kuka sannan yace" idan kinaso na koma yanda nake to kema sai kin koma yanda kike da, rashin kunya, tsiwa duk da ba halin ki bane amma yanzu kin koya" 

Da sauri ta goge hawayen fuskan ta tace"wlh yah Abdallah na daina amma kaima ka daina kadai na tabani ka daina shiga d'akina indai kayar da tom sai mu shirya mu daina fad'a"


Wani kallon takaici ya bita dashi yaga ba gane komai take ba don haka bai kara magana ba ya fita tabi bayan sa suka shiga moto yaja suka nufi gidan Nu'aiym.


Jiddah murna fal zuciyar ta wai yau ta fita, Yana lura da ita amma baice mata komai ba har suka karasa. 


Kafin su shiga gidan ya kira Nu'aiym a waya don shaida mashi sun iso don dama ya fad'a Mai zasu zo, tare suka fito da Raudah wanda itama tayi murna ganin Jiddah ta karaso suka rungume juna kamar yanda Nu'aiym yayima yaa sheikh sannan suka dunguma suka shiga gidan suna dan gaishe gaishe tsakanin su. 


Raudah ta kawo musu kayan kwalam d makulashe, su yaa sheikh sai hiransu suke inda Jiddah ta radawa Raudah cewa"don Allah Aunty Raudah ki barni na zauna anan gidan nibanason can"cikin harshen turanci, sosai Raudah take dariya don ba k'aramin dariya Jiddahn take bata ba don wancen zuwan nasuma haka ta kafe wai ita saidai yaa sheikh ya barta, a hannu d'aya kuma Raudah tana ganin rashin wayon Jiddah da kuma kuruciyar ta don tasan  tayi missing abu da dama don wannan haddadan saurayin ba Abun a dinga gudu  bane Wato yaa sheikh. 


Dariyar da Raudah take ne ya jawo hankulan su Nu'aiym gurin ta don haka suka tsaya suna kallon ta ay kuwa Nu'aiym ya shiga tanbayar ta cikin harshen larabci wanda Jiddah baji take ba. 


Sai da tadan tsagaita da dariyan sannan ta Kalle su tace "abokin Kane yake takura mata gashi yau tace bazata koma ba kuma na goyi da bayan ta anan zaka barmana ita, don naga kai kana mantawa da yarinya ka aura zaka isheta"tayi maganar Cike da zolaya


Ayko Nu'aiym ma ya samu don haka suka taru suna zolayar shi wai ya samu yar mutane ya fitine ta don haka zasu rike ta,  shidai baice komai ba sai yar dariyar shi da yake , aransa kuwa Yana cewa "ay ko Nigeria muka koma a part dina zata ke kwana bare kuma anan madina "don shi a nashi ganin yanxu bazai iya kwana gida ba Jiddah  ba. 




Jiddah data ga sunata hiran su kuma baji take ba yasa ta maida hankali wajen cin kayan kwadayin  da Raudah ta kawo musu . 




Haka suka dinga hira saidai idan lokacin Sallah yayi su Nu'aiym su fita suyi sukuma su shiga daki Raudah tayi don Jiddah bayi take ba koda Raudah taga Jiddah ta fara al Ada saida Abun ya bata mamaki don batai tunanin ta kai ba aranta tace"yarinya anzo  gurin nan da wasu yan lokuta bazaki so abunda zai raba muku makwanci bama "


Sai bayan isha suka koma gida a hanya ya yi masu take away suna zuwa ya shige d'akin shi ita kuma Jiddah ta zauna nan falo tare da daukan remote takai Chanel dinta na film din tsotson baki. 



Nidai bani da abinda zance muku masoyana saidai na baku hakuri... Wlh inada uzuri da yawa amma ku cigaba da hkr dani, *barka da Sallah* masoyanah *AYLOBIYU*😍🤣

*Khairaty*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
              *Yaa sheikh
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼


*U. K. Y. For real*



Dedicated to Mmn khairy 



                *113*


A sa'a kuwa irin abunda take so d'in ake don haka gaba daya hankalin ta ya koma kan TVn, jawo ledan take a way din da suka siyo tayi ta fara ci still idon ta nakan TV. 


A haka yaa sheikh ya  fito daga daki ya same ta, sai da ya hade rai sannan ya shiga falon, satar kallon sa tai sannan ta dauke idon ta. 


"Jiddah kin wuce duk yanda ake zaton ki, ya kamata na taka maki burki akan kallon wadannan channels din ko kuma na ciresu gaba daya "ya fada a cikin ransa


Remote ya dauka  zai chanja channel din ay kuwa da sauri Jiddah ta kalle shi, ganin mugun kallon daya watsa matane yasa ta shagwabe fuska saidai ta kasa magana. 


Bai fasa chanja channel din ba,ya nemo aljazira tare da relaxing kan sofa sannan ya jawo ledan take a way din Shima ya fara cin abincin shi hankalin shi kwance ko ta  kan Jiddah bai Kara bi ba. 


Ita kuwa gaba daya ta dama fuska abincinma ta daina ci jira take wani abu ya hada su ta fara mai kuka, ya gano hakan sarai don haka yayi kamar baisan tana gurin ba. 



Saida ya gama cin abincin sa ya mike ya nufi kitchen, water melon juice ya hada mata as usual , 


Yanda ya barta haka ya same ta fuskannan  a dame, Saida yadan kauda kai yayi dariya sannan ya kuma yashan mur ya karasa kusa da ita sannan yace"karbi"ya fada yana mika mata cup d'in, kamar baza ta karba ba saidai don ranta yana so yasa ta karba.tana zunbura baki tana sha. 


Gurin zaman shi ya kuma sannan yace "me kika gayawa Raudah d'azu"ya fada yana binta da kallon tuhuma. 



Ba tare da ta kalleshi ba ta zun bura baki sannan tace"ni ba abinda nace mata, kawai dai ni banason gidan nan ne"ta fada hawaye na gangarowa a idon ta. 


"Saboda ina hanaki kallon bad'ala ko me? "Yayi maganar cikin neman Karin bayani




"Mene bad'alar? Naga kaima ay yi kake.. Gara Suma basa sawa a rik'e musu... Sai kuma tai shiru"still tana kukan 


Kallon mamaki yake binta dashi Yama rasa mezai ce mata "bakisan su haramun bane kallon su... Ni kuma halak ne na saki duk abunda naga dama indai bai sabawa shari'a ba, wlh Jiddah ki shiga taitayin ki indai kinaso ki zauna lafiya a gidan nan "


Bata kuma cewa komai ba ta cigaba da kukan ta, shi kuwa banza yayi da ita don ta fara kular dashi, Anan inda take bacci mai nauyi  yayi gaba da ita kasan zuciyar ta cike da tunanin bata kyautawa wanda tasan da a gida ne da tuni ya dai dai ta mata zama. 



Saida ya gama kallon labaran sa sannan ya kalli inda tai shame-shame tana bacci kamar ba ita ta gama rashin kunya ba, sannan yaje ya d'auke yasata saman kafadar shi kamar wata baby doll tana rike a hannun sa ya kashe kayan kallon da wutan palon sannan ya nufi bet room d'inta, 


Cikin toilet ya dire ta da nufin ta tsaya da kafafun ta amma ina yana ajeta ta kuma fadowa jikin sa,  sai a sanan ya fara kiran sunan ta "jiddo.. Jiddo bude idon ki  "cikin magagi ta soma magana itama "yaya don Allah ka kyaleni ni bacci ... nakeji ka kaini ... kan gado na kawai sai ka bani Bakin nasha sai nayi bacci ko? "

Wani irin yarrrr yaji har tsakiyar kwakwalwar sa jin abinda tace, 

Yana cikin wannan yanayin ya kuma jin tace"yah Abdallah nah ko bazaka bani ba?"cike da shagwaba 


"Zan baki amma kiyi alwala.. "Maganar sane yaji ya kashe sakamakon cafkar da Jiddah taima Bakin sa tana mai wani irin kiss daya ruda shi lokaci daya, baiyi wata-wata ba ya biye mata cikin so da kauna da kwarewa abinda ya kuma ruda Jiddah kenan takai hannun ta kan.......... 




Don Allah kuyi hakuri ku cigaba da bina koda kad'an kad'an na samu na gama amma ina bukatar comment don wlh shi zai samin kwarin gwiwar karasawa don wlh  banida lfa. Ina godiya sosai da kulawar ku😍 *AY MISIYU*😂😂


Khairaty ✍🏻😍
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
             *Yaa sheikh*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼


*U. K. Y. For real*😘


Dedicated to Mmn khairy 



                 *114*



"Ya salam"ya furta cikin d'imau cewa ya tureta da karfi don gudun kar ta sashi cikin wani lahi kuma ba iya biyan bukatar sa zaiyi ba saboda period da take. 


Sosai ta razana da turetan da yayi duk da cikin magagi abinda ya wakana ya faru koda ta dawo hayyacin ta wani irin yanayi ta tsinci kanta a ciki wanda ita kanta batasan me hakan yake nufi ba. 


Ba wanda yayi magana cikin su sai kallon juna da suke Jiddah sai maida nunfashi take kamar wadda tai aykin karfi, shi kuwa yaa sheikh a zuciyar shi cewa yake "in halin ki ne zaki kuma lokacin zaki gane shayi ruwa ne ba baki zan baki ba har abinda yafi shi "

Ganin shirun yayi yawa yasa ta nufar kofar fita daga toilet din, ay kuwa kafin takai bakin kofar ya fizgota "al wala nace kiyi, kuma ni bazaki k'azanta a gida naba tun yamma fat ke jikin ki zaki kwanta baki sake wata ba saboda k'azantarki ta shahara "



Wata muguwar kunyace wadda bata ta'ba jin  irin taba taji ta lullube ta, duk bakin Jiddah da tsiwar ta kasa magana tai, 

"To shige kiyi al wala"ya sake maimaita mata


Sum sum ta wuce ba shiri ta fara al walan



Fant d'in ta ya dauka a inda take ratayewa idan ta wanke,  ya janwo wata  cabinet ya dauko fat ya samata shi jikin fant din,   tana idar da al walan ya mika mata, kanta a sunkuye ta karb'a "ki tabbatar kin cire na jikin ki   ina jiran ki" yana kaiwa nan ya fita daga toilet din. 



"Haka aka ce maka bazan sake bane zaka wani samin fat ko kunya baka ji.. Ko a ina ka koya ma oho"saida taga ya fita sannan tayi maganar harda hararar kofa. 


A bakin kofar ta sameshi yana jiran nata "kin chanja ko kuwa? "



"Eh"

Kawai tace 


"Zoto na gani"ya fada a tsare

Zazzaro ido tai waje tana ja da baya, shi ma binta ya fara fiskannan babu alamar wasa. a tsorace ta fara magana"wlh yah Abdallah da gaske na chanja Allah kuwa "


"Ok shine kikemin magana kamar wata kurma"

"A'a wlh na chanja "


"Good jeki kwanta to"


Da sauri ta haye kan gado tun kafin ya karasa maganar sa. 



Saida yayi mata addu'a sannan ya ja mata kofar ya tafi nashi dakin. 





 Yau ta kama Friday kuma a yau ne jidda ta kama period din ta, kuma a yau yaa sheikh Shima ya kammala nema jiddah makaran ta a cikin makarantar dayake lecturing ranar Monday zata fara zuwa, daga Monday zuwa Thursday zata ke zuwa karfe 8:00am sai 6:pm a taso da yake Arabic ne da boko sai rananr Friday kuma a tashi 12:00,don haka ya yanke shawarar zasu dinga tafiya tare suna dawowa tare ranar Friday  din kuma idan an tashe su ta dinga zuwa office din shi idan ya gama abunda yake sai su tafi gida. Wannan shine shawarar da ya yanke.  sai dai zuciyar shi cike da tsoron kar wataran Jiddah ta hadu da Hamna don ita ma ranar Friday din tafi takura masa cos ranar lecture daya take, a take yaji shakkar Jiddahn ya kama shi saboda bai san  wani irin fahimta zatai wa hakan ba. 



Da yamma ya shigo gidan ya sameta zaune kan kujera daga ita dai wata yaloluwar riga ko cinyarta bata gama rufewa ba rabin kirjin ta kuwa duk a waje saboda wuyan rigar ya mata yawa, a kwanakin nan sosai take nai biyayya ya rasa mene dalili sai dai kuma duk fadan da yake mata akan sa kananun . kaya taki ta dai na acewar ayshi ya shiya mata da kudin sa don haka sawa ba fashi. 

Kallo daya ya mata ya dauke kai, 


Da sauri ta taso tana cewa"yah Abdallah sannu da dawowa "tayi maganar tana mika mai hannu ya bata jakar hannun shi, bai bata ba ya ajiye kan kujera dake kusa dashi yana binta da wani irin kallo na kwadayi da kai kololowa wajen hakuri, dakyar ya iya cewa"yawwa jiddo ya gida, yau Zoya ta tafi da wuri kenan? "
. saida ta zunb'uro baki sannan ta fara magana cikin shagwaba "eh mana tafiya tai ta barni da har na fara jin haushi sai kuma gaka"


Ganin sai wani shagwaba take Gashi ko ina na jikin ta sai rawa yake don bata sa komai a ciki ba sai fant,yasa ya kauda maganar bai Kara. Cewa komai ba ya shiga kicin ya hada mata juice dinta sannan ya fito , a zaune ya same ta ya mika mata "gashi ko?... "Bayan ta karba ya kuma sa hannu a  aljihun sa ya fito da wani dan boxes mai shegen kyau ya mika mata yana cewa"yau kika gama period dinki ko? "

Saida ta sunkuyar da kai saboda batayi tsammanin zai mata wannan tanbayar ba sannan ta gyada kanta alamar eh... 

"Ok.. To karbi wannan musk ne idan Kinyi wanka anjima Saiki goge jikin ki dashi... Ki tabbatar kin goge duk inda abun naki ya tab'a"

Yana kaiwa nan ya bata sannan ya dauki jakar laptop dinshi ya nufi dakin shi, kai tsaye toilet ya nufa kansa ya sakar ma ruwa shi kadai ya fara magana "ina wlh bazan iya ba *alkawarin da ciwo* bazan iya ba hakuri na ya kare wlh, Jiddah kiyi hakuri kawai amma wlh banga abunda zai hana ni aywatar da mafarki na yau a zahiri ba saidai ikon Allah" 


Haka a daddafe ya karasa wankan ya fito. 



Bayan ta gama shan water melon din itama daki ta shige, ta bude abinda ya bata kwalba mai kyau ta gani tun kafin ta bud'e taji wani hadaddan kamshi bata san sanda tace "uhmm su yah Abdallah badai gayu ba"


ganin an gusa shiga masallaci sallan magrib yasa ya tashi dakyar ya dauro alwala ya nufi masallaci. 



Jiddah kuwa wanka tayi tayi kamar yanda ya fadi mata sannan tazo ta shirya wani riga da wando marasa nauyi tasa wandon iya gwiwa rigan kuma mai hannun shimi kayan pink color ne don haka sunyi matukar yi mata kyau sai kamshi take zubawa hijab din sallan ta tadauka har kasa tasa sannan ta tada salla. 




Saida yayi sallan isha sannan ya dawo gida. 



Khairaty ✍🏻
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
             *Yaa sheikh*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼



*U. K. Y. For real* 😘


Dedicated to Mmn khairy 


                   *115*


A hankali yake tafiya kamar wanda kwai ya fashewa a ciki, Kai tsaye d'akin Jiddah ya shiga a kan sallaya ya ango ta ta idar da Sallah sanye da hijabi, wani irin mugun  tausayin tane ya kama shi shikansa yasan tamai kankanta amma ina ruwan so baya duba wannan. 

A hankali yayi sallama d'ako kai tai suka had'a ido, abun mamaki sai gashi tana mai murmushi,  abinda yaa sheikh bai sani ba shine Jiddah ta yanke shawaran zubar da makaman ta acewar ta yah Abdallahn ta bai cancanci haka ba gara ta lallaba su rabu lafiya duk randa yakai ta Nigeria tace ita bata Auren a saketa tasan idan yaga tayi hankali zai saketa amma ko ya saketa tayi alkawarin baza ta komawa su Nana ba bare kuma Fego.  had'add'an saurayi zata samu Wanda ya amsa sunan shi kamar yah Abdallahn ta amma Wanda shi baya sa jallahbiya. 




Shima murmushin yayi mata ya karasa Bakin gadon ta ya zauna  shurune ya biyo baya kafin Jiddah tace"Yah Abdallah yinwa nake ji.. Naje kitchen na dafa abinci? "


Kallon ta yayi sai yaji ta bala'in burge shi tana magana cikin salo kamar waya cikakkiyar mace


"Kaji yah Abdallah nah! "


Tai maganar cikin salon da ya kuma rudashi

da kyar ya iya cewa "jiddo nah zaki iya ne? "


" wlh zan iya tare muke shiga kitchen din fa da Zoya ina ganin yanda take girkin"


"To naji amma sai dai muje na taya ki"



"Tom na yarda amma ka barni nayi ni kadai sai Kaji kona iya"

"Ok". Kawai yace yana Kallon yadda take k'okarin cire hijab


"Ya zuljalalu wal Ikram"ya fad'a a k'asan mak'oshin sa lokacin da yaga kayan da Jiddah ke sanye dasu, ba matseta sukai ba hasali ma sun so suyi mata yawa amma saboda laushin kayan gaba daya sun kwanta a jikin ta duk wani sheep na jikin ta ya fito dama ita ba gwanar sa inner ba. 



Bata lura da Kallon da yake mata ba ta fara tafiya tana cemai "ka taho mu je" ta fada tana barin dakin




Kallon jikin sa yayi yanda Shima yace ayi girkin dashi, ya fitar da wata zazzafar iska daga Bakin sa, sannan ya daddafa ya bi Bayan ta yaso dai dai ta kansa amma hakan yaci tura don haka ya maze yana shiga ya sami stole ya zauna. 


Noodles ta dafa sai surutu take shi kuwa yaa sheikh sai binta da Kallon tausayi yake. 



"Yawwa yah Abdallah ka had'a min juice din naga yanda kake hadawa"



"To Jiddah "yace yana kokarin had'a matan


Tsaf ta gama dafawa sai kamshi take, shima ya hada mata juice din ta gani, suka fito falo, nan jiddah taci abincin ta ta koshi tana ta yabawa girkin nata sannan ta kora da watermelon. 



Shidai zumud'i ya hana shi jin yinwar ma bare yaci abincin sosai, kad'an yaci sannan yace mata taje dakin ta tai shirin kwan ciya tayi alwala zai zo suyi Sallah. 


Kallan shi tai sannan tace"yah Abdallah Sallah kuma?.... Ni ay nayi salla ay dazu daga ganni kan sallaya ay idar da sallan nawa kenan"


'Dan hade rai yayi ganin zatamai halin nata wato musu sannan yace"Sallah tana yawane? To nafila zamuyi ko ke bakya son lada? "


Sai da ta shagwabe fuska sannan tace"ina so mana "


"To oya yi abinda nace nima bari naje nayi alwalan ko? "

"Tom amma yah Abdallah naxo muyi a dakin ka ban fa tab'a shiga ba"ta fada kamar zatai kuka



Kamar me jira da Sauri yace "shikenan ma kizo to sai muyi kinga kin fara shiga daga yau ko? "



Dadine ya kama ta yah Abdallah ya fara sakar mata don haka ta tashi ta shiga dakin ta tana cewa "yanzu zakaga na fito"


Lumshe ido yayi yana cewa "Poor jiddo bazaki kuma marmarin shiga daki naba, sai dai idan kin kara wayo"


Tsaf ya gama shirin shi na kwanciya kamar Yanda yasaba yana jiran shigowar Jiddah, bata b'ata lokaci ba itama a dakin ta wankan ta sake tasa musk don dadin kamshi shi take ji a jikin ta kuma ta fesa rutare sannan ta zura wata sleeping dress mara nauyi ta wuce gwiwar ta amma bata karasa kasa ba a wannan karon ma bata sa komai daga ciki ba sai fant ta zura hijab dinta har kasa ta nufi turaka lol.



Ba b'ata lokaci ya jasu sukayi nafila, sosai yayi Addu'ar akan Allah yasa wa Jiddah sonshi sannan ya basu zaman lafiya ya kauda fitina a tsakanin su ya basu zuria ta gari duk da yasa a ranshi zaiyi taka tsantsan don kar Jiddah ta dau ciki cos tayi yarinya ga kuma makaranta. 


Bayan sun kammala Jiddah ta fara hamma don haka ta mike tsam tana cewa "yah Abdallah saida safe bacci nake ji"

Aykuwa Shima zinbur ya mike kamar Wanda aka mintsina yace"bacci kuma Jiddah?.. A'a kiyi kwanciyar ki anan kinga baki taba shigowa ba yau kiyi kwanciyar ki"

Da kallon tuhuma ta bishi don abin nashi ya wuce mutunci a wannan karon wani irin mutunci ne wannan ya Abdallah ke mata? To Kodai yana so ya jagwalgwala tane? Ta kuma tanbayar kanta. 

"To indai haka ne ay kuwa itama tana so don tayi missing din abun kwana biyu bai mata ba"ta fada a zuciyar ta 

Yanda ta kafeshi da ido Shima haka ya kafe ta da nashi 

Sim sim ta koma ta zauna a Bakin gado(ni kuwa nace" gurin kwadayi Kuda ke mutuwa") lol


A hankali ya sauke ajiyan zuciya sannan Shima yaje ya zauna a kusa da ita, kusan minti goma duk sun kasa magana,, can yayi gyaran murya yace"Jiddah kin tuna ranan nan kikace wai na baki baki na kisha? "


"Lahhh ni? Ni ban fada ba "ta fada tana zaro ido


"Ok tom shikenan na zata kin fada ne yau na baki amma tunda baki bafa ba shikenan ni bari na koma falo na barki ki kwana anan"


"Tom" tace 

Shi kuwa jin tace tom yaji gaban shi ya fadi amma haka ya daure ya kime ya fara tafiya yana ce mata sai da safe. 


Dab da zai fita tace "to ka dawo ka bani amma ni wlh ni ban fada ba" ta fada tana b'oye fiskanta cikin cinyar ta

Wani dadi ne ya kama shi  sannan ba musu ya koma Bakin gadon. Lol 


Nan ma saida sukai kusan minti biyar sannan ya matsa kusa da ita a hankali ya rada mata "ko na tafi? "

Idon ta ta dago suka gada ido sannan tai kasa da kai tana girgiza kai alamar a'a


Hannun ta ya riko yana murzawa a hankali nan take da fara sauke ajiyar zuciya a haka yayi nasarar hade lips din su.... Sosai suke kissing juna har Jiddah ta fara bashi mamaki. 


Saida ya fitar da ita daga hayyacin ta sannan ya fara k'okarin rabata da kayan jikin ta, Jiddah bata ankara basai da yah Abdallah ya raba ta da komai, kuka ta fara mai wai ita ya bata kayan ta ta mayar sai su cigaba, ganin zatamai daru yasa ya fara mata abinda ya lura da tafi so wato sucking tanjiruns (boobs) lol

Sosai ta fara shide masa don haka yayj kokarin aywatar da abinda yayi niyya kafin ta dawo hayyacin ta..... ji yayi kwata kwata ba space "ya Allah "ya furta da karfi cikin tashin hankali kamar Wanda baya cikin hayyacin sa. 

Mutsu Mutsu ta fara masa tana "ni bana so ka cikani na tafi wayyo na shiga uku wayyo Mamy ta wayyo Ummy nah Wlh saina fadawa ya abdulmajid d yah abdulmakil"


Ji yai zata zulle mashi  aykuwa yayi mata wani irin wawan riko kamar zai ballata  a kunnan ta ya rada mata "sorry *me dad'i*" hade da Addu'ar...... 


Da karfi ya shige ta..  a tare suka saki wata muguwar Kara Jiddah na ta wuya yaa sheikh na ta aka sin haka. 

Sosai ya fita hayyacin sa kuma kuka yake tsakanin shi da Allah yana fadin" Abby nah Ummy nah Jiddah zata kashe ni "kai kanaji  kasan ba a hayyacin sa yake ba


abin mamaki yaa sheikh dake tausayin jiddah duk kukan da take ya kasa daga mata kafa "ki hakuri Jiddah ba laifi na bane " abinda kawai ya ke fada kenan. 


Kafin ya kai ga gaci Jiddah ta sume tsabar wahala. 

Burinshi na cika Shima ya fadi gefenta. 

*To ko Shima sumar yayi?*


Allah ya sani iya abinda zan ita vayyanawa kenan.. masu cewa a fad'a musu komai...... Su kuma masu zagi duk wadda ta zageni ban yafe ba don ban wuce gona da iri ba. 😍😍😍

Khairaty 😘
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 
              *Yaa Sheikh*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼



*U. K. Y. For real*😘


Dedicated to Mmn khairy


                *116*

Da kyar munfashin sa ke fita wani Irin yanayi ya shiga Wanda bai taba jin Irin shi ba "wai dama abinda nake ji a mafarki ba komai bane"ya yiwa kanshi tanbaya, lallai Allah ya mishi babbar kyauta da baiwa ta samun jiddah amatsayin mata, wannan ay Irin su ne ake kira"bake ba kishiya"ya furta a bayya ne. Sai a lokacin ya samu damar iya daga hannun sa dan ko yatsansa ya kasa dagawa. 


Da kyar ya kai hannun sa kan jiddah Sai yaji ko motsawa batai ba, ya kuma ta bata amma still ba motsi,  nan take ya tuna tun sanda ya shigeta bai kuma jin motsinta ko maganar ta ba, nan take yaji ya nemi kasalar da yake ji ya rasa a razane ya tashi ya zauna ya jawo ta jikin sa face dinta face face da hawaye harda majina ga kafafunta duk sun baci d jini"la haula wala kuwwata illa billah" ya furta a razane"shikenan abinda Ummyn shi ke gudu ya afku, yanxu ni nena aykata wa karamar yarin ya haka, yanxu mene abunyi "wata zuciyar ta Ce mashi "may be suma tayi ka yayyafa  mata ruwa ".        ba tare da ya kuma wani tunani ba ya kwantar da ita ya shiga toilet ya debo ruwa baiyi wata wata ba ya sheka mata ruwan, a karo na farko ko moshi batai ba, ya kuma komawa toilet da sauri ya kuma diban ruwan ya dawo y kuma zuba mata Sai a lokacin taja dogaon munfashi ta sauke tare da sakin wani razanannan kuka, a gigice yayi kanta ya zauna gefe ya jawota jikin shi. Jikin shi Sai rawa yake. 



"Jiddo don Allah kiyi hakuri bazan Kara ba, wlh da nasan haka zai faru bazan miki ba.... Kiyi hakuri kinji? "



Kamar Wanda yake zugata ta kuma bude Baki tana tureshi cikin dashewar murya da kyar muryar take fita ta fara magana
. "wlh saina fadawa Abbey saina hadaka da Mamy nah...... Wayyo Allah bayana wayyo cinya ta wayyo kai na zai cire ni gida zan koma"ta hau lissafa duk ilahirin jikin ta Wai duk ciwo suke mata



Ganin kukan take da gaske gashi muryarta na Kara dashewa ga jijiyoyin kanta duk sun tashi alamar sosai kan ta yake mata ciyo yasa Yaa Sheikh sake janyo ta jikin sa yana rarrashin ta yanaji kamar yasa zani ya goya ta"jiddo kiyi shiru haka pls naji zan kira miki su da safe sai ki fada musu idan kuma kin fi so na maidaki gida ki fada musu toh saina maida ki"

Cikin kukan tace"eh ka maida ni din"

"Ta kwana gidan sauki.. "

Yayi maganar kamar da gaske yake,, Kasan zuciyar shi yana cewa "yanxu ay koda wasa ko hanyar airport bazaki gani ba *mai dad'i* sabon sunan da ya rad'a mata "


Anan kan gadon da take kukan ya barta ya shiga toilet ya hada mata ruwa Mai dumi ya dawo cak ya dauketa .... ba wani karfi kareta ba gashi jikinta duk yayi tsami don haka batayi yinkurin kwace kanta ba haka ya dauke ta kamar gawa. 

Cikin ruwan ya sata ayko ta saki wata siririyar k'ara tana k'ankame shi. "Wayyo nan d'ina"ta fada tana yarfe hannu. 

Sosai yake jin tausayin ta yanajin dama baiyi ba sai a lokacin ya kuma ganin yarintar ta, ba abinda yake furtawa sai"kiyi hakuri jiddoh nah... Nine ko?.... Bazan Kara ba kinji..... "




Ita kuma sai Kara narkewa take tana fadin ka wani sashi na jikin ta Wai yana mata jiwo kuma ba hakura zaitai ba sai ta fad'a. 


A haka ya gasa mata jiki ya Ce tayi wankan tsarki, saida sukakai ruwa rana sannan ta yarda tayi, ya sa mata towel ya doro ta a kafada ya nufi dakin ta a kan gadonta ya kwantar da ita zuwa yanzu kukan nata ya ragu don sosai taji kanta na ciwo dole tayi shiru ga zazzabi daya rufe ta shi kansa ya fara jin tsoro sosai a ransa, maganin ciwon kan d zaxxabi ya koma dakinsa ya d'auko 
Ya bata da kyar ya samu mu tasha yayi ta lallab'a har tayi bacci,  aransa yana cewa zuwa safe idan yaga bata koma normal ba dole ya kaita hospital. 


A hankali ya zame jikin sa ya koma dakin shi yana kuma jaddada godiyar shi ga Allah. 


Saida ya cire bedsheet don yayi staining ya wanke sannan yayi wanka yasa jallabiya sannan ya feshe jikin shi d turare yayi Sallah raka'a biyu ya kuma godiya ga Allah, sannan ya rufo d'akin ya nufi na jiddah. 


Khairaty😘✍🏻



🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
               *Yaa sheikh*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼






*U.K.Y.    for real* 😘


*Dedicated to mmn khairy* 🤝🏻



Bismillahirrahmanurrahim
   _To dai da farko godiya zan muku masoya na a gaskiya bani d kamarku, duk tsawon lokaci Dana diba bana typing saka Makon  rashin lafiya da nayi hakan baisa kun daina bibiyata ba to gaskiya naji dadi Kuma wannan dalilin yasa naji ina son ko Yaya dai nima na faranta muku ta hanyar karasa wannan novel insha Allah,da fatan zan samu goyon bayanku ta hanyar yimin comments da Kuma tayani yada wannan novel kamar yadda kuka Saba ngd_




              *117*
Kwance yasameta kan gadon tana bacci tausayin ta yasake kamashi cike da kaunarta yaqaraso kan gadon yajanyota jikinshi tafarka atsorace tare da fasa wani kukan tare dafadin "ni ka kyaleni.. bazan Kuma zuwa kokusa dakai ba" qoqarin janyota yasake ta Kuma fasa ihu "nidai don Allah karka tabani "


tsayawa yayi Yana kallon yadda take karkarwa Kuma yaga tsakani da Allah take jin tsoron sa, saida yaso yayi dariya amma ya gimtse Shi kansa yasan yayiwa jiddon shi aika aika Amma yasan ba laifinshi bane duba da yadda ya Dade  da muguwar shaawar ta ga   tarin ni'ima da wani mugun guguwar Dadi da ya debe shi don haka bada sanin shi yayi wa shalelen shi haka ba.




 tana turjiya haka ya sake  matseta gam cikin qirjinsa tare da fadin

" haba jiddon Mamy nace fa kiyi hkr bazan Kara ba Kuma nace maki idan Kika Fara zuwa school kukayi hutu zan maidaki gurin su Ummyn sai ki fada musu abunda nayi mikin ,haka ya Miki?"Ya karashe maganar tare da tanbayar ta


Tsayawa tayi tana dan kallon sa hade da dan hararar sa ta kasan ido a ranta tana tu nanin gara tace ta yarda idan yaso idan ya maida ta gidan har da sharri zata Kara har abunda bai Mata bama zata ce ya mata,....

Dan ture shi tayi sannan tace eh naji yayi min hakan Amma ka tashi ka fita to"ta fada tana kwanciya tare da juya mai baya.



Murmushi yayi ganin ya shawo kanta sannan yace "yadda Kika ce haka za'ayi ranki ya dade ya fada Yana tashi daga kan gadon sannan ya rufa mata blanket yayi mata addua sannan ya fita a ransa Yana ta sa mata albarka.


Ita ko jiddah dan tsaki tayi gami da cewa"Yana fama da wata jallabiyar sa"ta fada cike da kunkuni.

A haka bacci yayi gaba da ita kasancewar maganin da ya Bata dazu ya saukar da zazzibin da Kuma ciwon kan kawai dai kasanta ne ke mata mugun ciwo.



Yaa sheikh ma daya koma daki bacci ne Mai Dadi yayi gaba dashi rungume da filo tamkar Jaddahn ya rungume..........





Da asuba Saida yaso ya makara da kyar ya samu ya tashi ya dauro alwala bai tashi jiddah ba cos yasan bata samu wani ishashshan bacci ba,masallaci ya nufa suna idarwa ya dawo gida saboda Shima baccin bai isheshi ba,




   Kasancewar asbar ne sai   shadaya  yatashi da addua abakinsa duba agogo yayi yaga yanda lokaci yaja da hanzari yashige toilet yasakarwa  kansa ruwa, yafito daure da towel daya àqugunsa daya akansa yana goge sumarsa, jan qaramar stool yayi yazauna gaban mirror yashafa cream sannan yabi gabbansa da turaruka masu sanyin qamshi wardrobe yanufa yazabo shirt da trouser yasanya agaggauce ,kai kana ganin sa kasan Yana cikin nishadi Saida sukayi waya da Nu'aym yake Fadi mashi Jiddah ba lafiya gashi Monday zata Fara zuwa school yanzu ya zasuyi , Nu'aym yake ce Mai maybe ay kafin Monday din ta warke ,haka dai suka Dan taba Hira har Nu'aym yaso ya dago abunda ya wakana Amma yaa sheikh ya basar,Amma Nu'aym ya kudurce a ransa zai sa Raudah ta tanbayi Jiddah idan sunzo  duba ta cos yasan Jiddah yarinyace Bata San komai ba a wannan harkar ba bare Kuma tasan yadda zata Kula da kanta,Nan dai sukayi sallama sannan yaa sheikh ya fita.



A falo ya iske Zoya har tazo ta gyare gidan ta gama shirya musu breakfast kamar yadda ta Saba ,gaisawa sukai sannan ya shiga bubbube abincin yaga abinda ta dafa egg rolls ne sai toasting bread sai Kuma tea da yasha kayan kamshi.


              
Bayan ya gama dubawa ya nufi d'agin Jiddah sai a sannan yaji gaban shi na faduwa don bai san a wani yanayi zai sameta ba ,Saida yai ta Maza sannan ya tuura kofar ya shiga,a bakin gado ya hangota da alama tashinta kenan Kuma daga gani ta rasa yadda zatai ta tashi ne ,da sauri ya karasa kusa da iya Yana fadin "sannu ko jiddonah "
Ko kallon inda yake batayi ba ta kauda Kai,
Kara matsawa yayi kusa da ita yana kokarin jawota jikin sa amma ta janye jikin ta alamar bataso ya taba ta.

"Ok bakiso na taimaka Miki ki tashi?.....muje na hada Miki ruwan wanka"duk ya fada a lokaci daya ,ko motsawa batayi ba bare yasa ran zata kulashi,kallon ta ya sakeyi Yana maijin haushin abunda yayi mata sannan yace"Jiddah bazaki kulani ba...na baki hakuri fa Kuma kince kin hakura ,don Allah ko bazaki kulani ba ki tashi na kaiki toilet na hada miki ruwa kiyi wanka"ya fada kamar zaiyi kuka.


Kirmisisi tai taki ko Moshi,ganin da gaske take fushin yasa kawai ya dauketa ya sabata a kafada ,kukane me karfi ya kwace mata batare da tace komai ba haka dai ya kaita toilet ya hada ruwan da zai gasa mata jiki Amma  bayadda baiyi ba ya cire mata Kaya taki yarda, rasa yadda zaiyi da ita yai dole yasa Saida ya fito ya samu Zoya ya fadi mata Jiddah Bata da lfa ta shiga ta taimaka mata tayi wanka,ba bata lokaci ta aje aykin da take ta shiga dakin Jiddah,


Yadda yaa sheikh ya barta haka Zoya ta shiga ta sameta ,tun kallon da taimata ta fuskanci wani abu ne ya faru tsakanin su Bata tabbatar ba Saida ta Kama hannun Jiddah da zummar ta jawota taji Mai yake damun ta sai taga dakyar Jiddah ke tafiya hakan kuwa ya tabbatar mata da abunda take zargi ,kallon Jiddah tai taga yanda take share kwalla haka taita lallabata ta samu ta taimaka mata ta gasa gikin ta sosai ,suka fito Zoya ta dauko mata Kaya tasa har zuwa wannan lokacin Bata ce komai ba ita ko Zoya sai jera mata sannu take,sannan tace mata tadan kwanta bari ta kawo mata abinci ta samu taci.


Yaa sheikh dake zaune kan Dining table ko tea din ya kasa Sha gaba daya hankalin sa yana kan Jiddah, Zoya ta fito daga dakin Jiddah da sauri ya tashi Yana tanbayar yaya jikin Jiddahn ganin yadda yadda ya rudene yasa tace"sir da sauki Kuma tayi wankan yanzu zandan hada mata pepper soup ne Amma jikin ta da Dan zafi sai an Nemo mata magani"tayi maganar cike da girmamawa

"Ok "yace sannan ya dau Kay din moton shi don siyo mata maganin duk da yanada maganin zazzibin but yasan maybe sai Tasha na cire zugi sannan za taji dama dama.




Khairaty
      n
Khairatee
 😍😍😍


🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
              *Yaa sheikh*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼

*U.K.Y.for real*. 😘


Dedicated to mmn khairy🤝🏻


                  *118*


Wani pharmacy yaje yayi musu bayani ,maganin cire zugi dana zazzabi d ciwon Kai suka bashi cikin hanzari ya biya kudin ya komo gida.




A kicin ya samu Zoya har ta gama hada mata   tea d pepper soup din ta zuba cikin bowl tana kokarin Kai mata ya shigo maganin ya bata sannan ya gaya mata yadda zata Bata ,cikin ladabi ta karba har ta zuya zata tafi y kuma kiranta yace"don Allah ki kula d ita fa ki tabbatar Tasha maganin"

Cikin ladabi ta Kuma amsa Mai cikin ranta tana mamakin wannan wani irin so ne yakewa yarinya karama Wanda Sam baya iya boye wa don ita tunda ta farayi musu ayki take ganin hakan a kwayar idon sa,haka dai ta shiga dakin Jiddah tana wannan tunani .



Zuwa wannan lokacin kuwa Jiddah har ta samu bacci ya dauketa, a hankali Zoya ta karasa bakin gadon ta tashe ta.
  

    Ahankali tadan buga pillow datake kai bude lumsassaun idanuwanta tayi ta daura bisa fuskar zoya"how are you feeling now" gyada mata Kai tayi alamar da sauqi i prepare sometin for u,come  eat and take ur medicines zoya tafada mata yamutsa fuska Jiddan tayi tare da fadin "no am ok," cigaba tayi da rarrashinta hartasamu tamiqe zaune tare da jingina bayanta ajikin gadon sannan ta zuba mata pepper soup din  kadan da tea a plastic cup tare d daurawa kan qaramin tray tadauramata kan cinyarta haka tadan tsakuri kadan tace mata taqoshi tattare wurin zoya tayi tamayar da kayan gefe ballo maganin tayi tamiqa mata da kofin ruwan tasha,


 tashi zoya tayi tashige bathroom ta hada mata ruwan dumi sannan ta fito samu jiddah tayi  taqara lafewa jikin gado karasawa gurin tayi tana tabata tana fadin "kiyi haquri ki tashi ki sake dumama jikinki zakiji sauqi insha Allah "dakyar tamiqe ta taimaka mata ta rakata bakin toilet din, nan tabarta tajuya  ta tattare kayan tamaida su kitchen tare da qalqale kitchen din ......



  Gasa jikinta tai dakyau taji sauqi sosai dan zugin datakeji ma yaragu haka zazzabinma ya sauka dauro alwala tayi tafito daure da towel goge jikinta tayi tadan murza cream da dan perfume ajikinta ta zira simple gown ta tayar da sallar azahar




          A polour kuwa yaa sheikh  yakasa zaune yakasa tsaye aqage yake dason sanin halinda kyar rigimar  take ciki don Koda Zoya ta fito dazu kasa tanbayar ta yayi saboda yasan zuwa wannan lokacin ta gano abinda ya wakana, yana ta zirga zirga yaji Kiran sallah akunnenshi tashi yayi yashiga bedroom dinsa domin gabatar da alwala yafita masallaci



          Jidda kuwa bayan ta idar da sallah ta yi Yan adduoin ta sannan ta cire  hijabin jikinta,
 Ganin tadaan samu sauqin jikinta yasa  ta fita palour  ta kunna TV channel din tade wacce take matuqar so ta kamo wato Mexicans channel, tunanin abinda sukeyinne yazo kanta taja tsuka tare dafadin "ashema abinda sukeyin ba dadi gareshi ba sai kaga suna Nishi kamar zasu mutu Kai ka zata Dadi ne ya ishesu ashe dan banza azaba ne to dama dama ma  Shan bakin but Kuma shine mafarin azabar"tayi maganar tana daddana saman mararta kana taja tsaki   tare dajin haushin channel din tare da sake  fadin "amma fasa kallonku "tana cikin jarabarta ita kadai aranta saijin sallamar yah sheik ciki ciki ta amsa mai, shi kuwa shigowa yayi yasamu daya daga cikin kujerun palour yazauna yana dan satar kallonta


 mutuniyar kuwa tayi kicin kicin da rai yanke shirun nasu yayi da fadin" yajikin ..hope dai kinsha magani? "


"uhmm" 

tace tana qara tamke fuska yace" sannu yanzu mekikeso "

tace "bbu abinda nakeso ni"

"kodai nahada miki juice din kankana"

 juyowa tayi takalleshi kallon sama da kasannan sannan tace "umm kado"

      Jiki narawa yamiqe yashiga kitchen domin faranta ran jiddonshi hadaddiya juice din kankanar ya hada Mata as usual Wanda taji madara sosai ya zabga sugar don yasan halin Jiddah da son suger ,dadai shike hanata Shan Zaki but yanzu tunda so yake ya shawo kanta ya samu ya dinga samun nutsuwa da ita da wannan sihirtacciyar ni'imar Tata Dole yayi Mata duk wani abu da take so, yajuye mata a jug qarama tareda jefa er qanqara kadan domin yaqara taste kawo Mata yayi yamiqa mata ,saida  ta Dan kalleshi sannan ta tsiyaya a cup ta Kai bakin ta ta kurbi kadan wani dadi taji yaratsata har kwanyarta lumshe Ido tayi tana yaba juice din aranta shikuwa ddine yarufe shi ganin tadage sai shan juice din take cike da nishadi hakan yanuna masa cewa juice din yau y Mata Dadi fiye da kullum , nan yayta janta da hira tana dan ansa masa kadan kadan sundan jima a palour kamin ta tashi tashige bedroom tabarshi Anan




  Shigarta baidade ba aka Kira la'asar shigewa bathroom tayi domin dauro alwala shima yah sheikh bedroom yashiga yadauro alwala yaqara ficewa masallaci fitowarsa a masallaci yaji wayarsa na ringing cirota yayi a aljihun rigarsa yaga Mai kiransa .nu'aym ne ,daga kiran yai yakara akunnensa tareda yin sallama bayan sungaisane yace masa gasu a kofar gidansu yace"ok to  gashinan isowa "



Ayi hakuri van samu nayi editing ba

Khairaty😘✍🏻

Khairatee tanx alot


🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
               *Yaa sheikh*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼


*U.K.Y. for real*. ✍🏻



Dedicated to mmn khairy


                    *119*



     Da sassarfa yaqaraso kofar gidan domin kada su Nu'aym su qosa da jira samunsu yayi a farfajiyar gidan miqa masa hannu yayi yana mai hannu yayi  sukay musabaha kaida ganin su kasan akwai  shakuwa sosai a tsakanin abokan ,


yajuya Inda Raudah take tagaishesa cikin raha ya amsa Yana shigewa gaba  yana mai yimusu iso cikin gidan a palour sukaiwa kansu ma sauki
Kan sofa

Kicin ya nifa Yana Kiran Zoya cikin hanzari ta amsa ya shaida mata sunyi Baki su Raudah dake  tasan Raudah uwar dakin kawar ta (Idan baku Manta ba bace muku Yar aykin Raudah ce ta samo Zoya)




Nan Zoya ta shiga Kai musu abin motsa Baki


"Ina Mara lafiyan "Raudah ta tanbayi yaa shiekh



"Bari na Kira ta maybe bacci take"yafada Yana nufar dakin Jiddah

 Kwance ya samu   jidda yafadamata su raudha suna palour murna fal cikinta da zumudi ta tashi zata fice haka yajanyota yana fadin "to sarauniyar masu hankali aede kyasa hijabi kirufe jiki Koh"kwace jikin ta tai tana zumburar baki tajanyo hijabi datay sallah tafice Yana biye da ita a baya



a parlorn kuwa ta tarar dasu ,sallamarta ne yajanyo hankalinsu gareta yanayin tafiyarta kadai yanuna musu abinda suke zargin shi yafaru 



Karasowa tayi ta fada jikin Raudah muryanta na rawa tace :aunty shine saiyau kuke zuwa"ta karasa maganar tana Dan turo Baki ,kafin ta juya ta gaida Nu'aym duk cikin English 



 ,amsawa yayi Yana kallon ta yana Dan murmushi,yaa sheikh yayi Mai wani kallo Mai cike d tuhuma ,wata Yar dariya Nu'aym ya Kuma ,Wanda hkn ya tabbatarwa yaa sheikh da wani Dan munafur d yake cin su daga Nu'aym din har Raudahn.

Yana cikin wannan tunanin ne yaji muryar Jiddah na cewa"aunty kizo muje daki "


Wuki wuki yaa sheikh yayi da ido aransa Yana cewa wannan yarinyar fa ba Kaine da ita ba yanzu saita iya fadawa Raudah abinda ya faru ,kallon ta yake yanaso su hada ido don ya ja Mata kunne Amma Sam taki ko kallon inda yake,bai auneba kawai sai ganin wucewar su yayi Jiddah najan hannan Raudah,


suna shiga daki yaa sheikh ya Mike zaibi bayan su ayko Nu'aym ya Sha gabanshi Yana cewa "ango yanazo gidanka Amma Kai gaba daya hankalin ka nakan amaryar ka ,yanzu daka Mike dakin zaka bisu ko Yaya?"yayi maganar Yana Mai dariyar shakiyanci,

Gaba daya ya gama susucewa Sosa kyeya yayi Yana hararar Nu'aym sannan yace "malam abuna Zan dakko"


"Ok to ko bosses Dinka ka Manta ne" Nu'aym yayi maganar Yana dariya harda rike ciki


Shidai yaa sheikh basarwa yayi don ya gane Nu'aym ya gama gano shi ya hade rai Yana wani harare harare,lol



"Ok to kaga tashi kaje ka dauko takardan da muka rubuta takardun Jiddah Wanda babu a cikin makara ta"Nu'aym ya fada Yana kokarin gimtse dariyar shi.



Yaa sheikh sai yanzu d  Nu'aym ya tunamai sannan ya tuna da sanda sukaje maganar makarantar Jiddah an Basu sunan books din da babu a cikin school din don haka ya tashi ya dauko ,ko kallon inda Nu'aym yake baiba ya fita Nu'aym dariya yayi yabi bayan shi suka tafi.




A daki kuwa Jiddah suna shiga ta Fara KuKa tana cewa"ya tashi ya aure ni Wai saboda Figgo Dan iskane to ay gara Figgo dinma tunda shi saidai ya fada a Baki bai taba yimin ba" 
Raudah sakin Baki Tai tana kallon Jiddah da yake da hausa tayi maganar "dear what are you saying "Raudah ta tanbaye ta,sai a wannan lokacin Jiddah ta Fara magana da English tana kokarin Gaya mata abunda sukai da yaa sheikh , Raudah katseta tai ta Hana ta fada sannan ta Fara cewa"to ay dama wannan shine auren dear ,Kinga Abdallah Yana sonki da yawa Idan baki yarda dashi zai daina Kuma Kinga a school akwai yanmatan da suke sonsu Idan bamu kula dasu ba zasuke zuwa gurin su don haka kiyi hkr kinji ?"


Ita dai Jiddah "uhmm" tace kawai badon waazin tsuntsayen da Raudah Tai mata ya shigeta ba.


"Yawwa dear sai Abu na gaba ki dinga anfani da ruwan dumi kinji Kuma ki dinga Shan fruit sosai zaisa ki warke kinji"

"To"Jiddah ta Kuma cewa a ranta tanacewa kobadon na warke bama Zan dinga Sha ko don Dadi ma,

Haka suka shiga Hira Raudah take tanbayar ta yaushe zata Fara zuwa school taji su Nu'aym na magana akan school din nata

"Sai ranar Monday"Jiddah tabata amsa
"Ok jibi kenan" ta sake tanbaya

"Eh Idan na tafi tun safe sai 6 na yanma sai ranar Friday ne zanke dawowa 1amma Shima saina jira ya Abdallah ya gama aykinsa sannan mu dawo" 

"Ok to kimaida hankali sosai kiyi karatu kinji "

"Tom" Jiddah tace


Suna zaunen ne Zoya ta shigo dakin tayi musu sallama ta gama ayki zata tafi sannan ta sake tunawa Jiddah Tasha naganin ta na dare,Nan Jiddah ta amsa sukayi sallama,


Sai bayan magrib su yaa sheikh suka dawo Nu'aym yace Raudah ta taho sutafi a Nan Jiddah tasa rigima dakyar yaa sheikh ya samu ya shawo kanta ya sabota a kafada suka koma ciki.


A Moto kuwa Raudah ta kwashe yanda sukai da Jiddah ta gayamai suna ta dariya , sannan ya tanbayeta tadai gayamata yadda zatake kula da kanta ko ?tace mishi"eh"


Jiddah kuwa makalkale Mai tayi a kafada taki sauka sai zuba Mai shagwaba take tana kuka tana dukan sa"nidai Allah bazan sauka ba ka kaini gurin su su tafi Dani"

"To ki zamanki Nan Amma dai su sun Riga sun tafi"ya fada Yana Kara gyara Mata Zama nan kafadar shi


Nan ta shiga mutsumutsu tana zillewa cike da shagwaba shi kuwa hakan ya mishi daidai don da wannan damar da ya samu ya Fara tattabe abunda yake tsolemai ido cikin dabara


Ayko ganin ya Fara fita hayyacinsa yasa ta Ankara da sauri ta tureshi tana dutowa daga kafadar shin tayi kicin kicin da Rai ,shiko da kyaf ya ke maida numfashin sa ,wani kallo ta Watsa Mai sannan ta juya Tai shigewarta daki jiyayi kamar ya jamo ta but yasan bazasu wanye klau ba yasa ya hakura .


To tun ranar Jiddah Bata Bari sun sake haduwa ba Zoya ke kula da ita sosai har zuwa yau Monday.



Khairaty😘✍🏻


Allah ya Baki lafiya namcy🤲🏻


🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸w🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
               *Yaa sheikh*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼






*U.K.Y.    for real* 😘
  

Dedicated to mmn khairy


                   *120*

*Monday* da sassafe yah sheikh ya tashi yanufi dakin Jiddah, nannade yaganta bisa gado tana sharar baccinta murmushi yayi yana fadin" er rigima" ,tashinta yayi dakyar tabude idanuwanta ta zuba Masa a fuskarsa yace mata jiddona tashi yaufah monday kinmanta yau zaki Fara attending school ne yamutsa fuska tayi tayi narai narai da ido tana shirin sakin kuka yace makarantar ce kuma bakiso turo baki tayi cike da shagwaba tace ni baccin be isheni ba yace haquri zakiyi daure kinji dama neman ilimi yagaji haka dole kacire laziness kamin kasamu yanda kakeso bbu wanda yakwanta agida kuma ya ilimantu don haka kidage dama nasanki da hazaka kinji daga kai tayi yace yawwa bby dull Shi yahada mata ruwan wankan sannan yace mataa tashirya Shima zai je yayi wanka saisu wuce 

Zoya kuwa tun 7 taxo ta Fara aykinta breakfast ta Fara hada musu ta shirya akan dinning table sannan ta wuce ta Fara aykin gida


  Ashirye tsaf yafito da jallabiya me hula ta baya fari qal dashi yasha yasa sau ciki baqa hirami fara da er launin jan geza  abakin hiramin yanade kansa dashi yafito very neat and attractive irin wannan wankan ko a makkan ma sai Wanda ya amsa sunanshi Dan Gaye keyin shi don haka yake rudar yan mata da yawa Kai tsaye dakin jidda yashiga yasameta ashirye tasa baqin vintage gown baki da yarfin gold ajiki da hill aqafarta domin yanzu tajita garau bbu Inda yake mata ciwo tanade kanta da golden din gyale tayi kyau matuqa murmushi yasakar mata yace muuje muyi brkfst saimu wuce

   A dining suka yada zango shiyayi serving nasu yazuba mata komai kadan kadan aplate din yatura mata tare da hada mata tea shima hakan yayi yafara ci amma ita sai wasa take da abincin magana yayi mata lokaci zai qure tayi sauri amma kamar qara zugata yake saida yadaka mata tsawa tashiga hankalinta tafaraci hawaye taf idonta suna kammalawa sukayiwa zoya sallama suka fice


   Office na principal suka fara zuwa yagabatar da ita amatsayin sabuwar dalibar da suka nemawa school din  uniform aka bata kusan kala uku da Kuma na sport da zatake sawa ran Friday da sauran abubuwan da school authority ta tanadarwa kowanne dalibi na makarantar aka hadata da massinger mace takaita want room da aka tanada don sababbin student idan zasu sa uniform tanuna mata male room   tace tashiga tacanja, bata 'Bata  lokaci ba ta gama sawa ta fito,


 Masha Allah Allah yayi halitta kyawun datayi ba'a magana uniform din yakarbeta matuqa kamar wanda aka bata domin yin gasar sarauniyar kyau sanye take da farin riga tayi zanzaro da pink din straight skirt har qasa sannan da wani pink din falmara data daura bisa farar rigar da yar madaidaciyar hijab akanta farin canvas ne sanye aqafarta da bakin jaka a bayanta qare fitowa tayi  tasameshi saidayayi suman wucin gadi danjiyayi kamar yaje yarungumota beauty yace acan qasan maqoshinsa  yayinda kishi yacikasa fal ganin yanda sauran malaman suka zzuba mata na mujiya


Zuwa yayi ya kama hannun ta suka koma cen inda aka vata Kaya anan ne aka hadata da wani messenger aka fadimai class din da zai kaita ,


Kallon yaa sheikh Tai tayi narai2 da idon ta kamar Mai Shirin kuka ,Shima kallonta yake yasan ba abune Mai sauki ba shiga cikin wadan da ba yarenka ba da zummar daukar darasi but yasan a hankali zata Saba ,kara riko hannunta yayi yace"stop mn my jiddo mene ...karki damu kinji kije class kiyi karatunki kinji kafin ma 6 din tayi zanzo na jiraki kinji autar mu ,ungo wannan idan kunfito break ki sai abinci kinji"yayi makanar Yana bata riyar da yawa Wanda a kalla yakai 4k a kudin mu na Nan.

Karba Tai tana goge gawayen ta sannan tabi vayan Wanda aka hada ta d shi.



Office yaa sheikh ya ja moton shi ya karasa dayake babu Nisa tsakanin sashin baifi tafiyan minti biyu ba ya faka moton shi ya shiga office din shi da yake sai 12 yake da lecture a class din su Hamnah.


Ayki ya farayi kawai sai yaji sallamah , bakin ciki da bacin Raine a lokaci daya suka lulllube shi a ransa Yana Jin haushi da bai rufe kofar shi ba ,dakyar ya dago ya kalleta ya amsa sallamar Yana kauda idon sa itako Hamnah idonta karrr a kan kyakyawar fiskan shi.


Takowa tayi ta yima kanta wajen Zama saman daya daga cikin kujerun  dake gaban tebur din yaa sheikh tana ta murmushi fuskarta ba ko alamar fushi .


Dagowa yayi ya Kuma kallon ta sannan yace"Wai ya akayi ne ?"yayi maganar Yana Mata wani irin kallon takaici,gyara Zama tayi harda gyaran murya cikin harshen larabci da kuma yauki ta fara magana"sir dama nazo na gaishe ka ne kwana biyu bangan ka ba ,sir don Allah ka daure ka bani phone numbern naka wlh idan ka bani bazan sake shogo ma office ba"ta karashe  maganar kamar zatai kuka 

Wani bakin cikin ne ya sake turnike zuciyar yaa sheikh ya rasa wannan wace irin jaraba ce Yana mamakin rashin zuciya irin na Hamnah sannan yace"ki tashi ki fita yanzu Ni ayki nake idan nayi shawara da zuciya ta zakiji amasa  Zan iya baki number na ko bazan baki ba"
Kara muskutawa Tai zata sake magana ya xuba Mata wata razabanniyar tsawa Yana cewa" nece ki fitar min a office ko just get out "jiki na rawa ta tashi amma ko kadan cikin ranta bataji haushin abunda yayi Mata ba ,sum sum ta fice  a ranta Tana cewa anjima Zan dawo.


Jiddah har aka fita break Bata kula kowa a class din ba Kuma Maza da Mata ne amma kowa set dinshi daban,ganin inda dalubai ke zuwa siyan abinci yasa itama taje gurin Saida ta gama kallon abubuwan da ake siyarwa a wajen sannan ta Miki kudin ta ita ma tace a Bata shawarma da bugger sai drink ta karba ta koma inda taga suna Zama cin abinci itama ta zauna ,tas ta cinye abunda ta siyo ta kora da lemon ta ,kunsan Jiddah dason kwadayi.


Sai 2 suka tashi daga boko duk inda taga dalubai sunyi ita ma Nan take yi alwala tayi kamar yanda taga sunayi sannan suka nufi masallaci ,a nan ne taga dalubai mata na shiga wani daki Kuma idan sun tashi fitowa saita gansu da hijabai har kasa don hk ita ma ta shiga anan ne taga wasu durowayi kowanne da key a jikin ta da Kuma sunan ko wace daluba don hk ta shiga duba sunan ta ,ayko cen ta hango nata taje ta bude hijab biyu ta gani don hk ta dauki daya ta cire kramin na jikin ta ta nin ke tasa a cikin jakar da aka Bata uniform din ta dazu ,haka ta fito tayi sallah itama duk abinda taga sunyi shi take yi ita ma daga Nan suka Kuma cin abinci sannan suka wuce bangaren islamiya .


Yaa sheikh tunani ya shiga yi Yana cewa" wannan yarinyar so take ta zamemin matsala don duk ranar da suka hadu da Jiddah bansan mezai faru ba duk da a tunanin shi  Jiddah bazarai kishin shi ba amma yasan rigimar ta baisan ta inda zata bullomai ba,dogon nazari ya shiga yi can Kuma sai ya saki wani gayataccen murmushi Mai cike da ma'anoni Wanda shi kadai yasan me hakan yake nufi.

Kamar yanda tayi alkawari tun kafin 6 din tayi yayi kokari ya gama aykin shi sannan ya fito ya rufe office dinshi yaja muton shi zuwa side din su Jiddah har ya jira aka tashe su ,cikin student ya hanko da alama ta gaji........



Wlh indai bazan ke samun comments ba Zan bar typing din cos donku nake Amma kuyi comments Abu saiya gagara kwana ukun Nan da vanyi typing ba Wanda sukai magana sunkai 100 but idan nayi typing Wanda suke mgn ba sufi 50 ba to gaskiya na gaji idan kun gyara na cigaba idan baku  gyara ba wlh bazan Kuma typing ba.


Ina godiya khairatee


Khairaty✍🏻😍


🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
              *Yaa sheikh*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼



U.K.Y .for real 😘


Dedicated to mmn khairy




Ayi hakuri d spelling mistake cos ba editing

                  *122*





Zumbur ta Mike tanAy kallon boobs dinta"wayyo Allah na meyasa nayi  gashi na jama kaina ya tafi"ta fada tana dungurin kanta da kyar ta samu ta koma ta kwanta Amma bawai don har lokacin bacci na idon taba tunani ta shiga yi kala kala.


A daddafe ya shiga dakin shi toilet ya wuce ya sakarwa kanshi ruwa duk da sanyin da ake a Riyahd ya Jima ruwan na sauka akanshi sannan ya dauro alwala ya zo yasaka Kaya ya fara nafila ya Jima Yana gabatar d nafilar kafin ya tashi ya koma kan gado wani irin Abu yake a jikin shi Wanda shi kanshi bai San mene ba juyi ya sake yi Yana fadin"Allah gani gareka ya Allah ka bani dama akan mata ta Jiddah ta Soni da damu Dani kamar yanda nakeji game da ita"haka ya jero addua Yana dafe marar sa Nan take wata zuciyar ta shiga bashi shawara akan abinda yake ayyanawa tun dazu game da Hamnah"wannan shine babban damar da zaka samu make her jealous and prove her  u have allot of mata da suke mugun sonka then we should see"wahalallan murmushi ya saki still da hannun shi dafe da marar shi yana maijin dadin wannan shawara Amma duk da haka zai nemi shawarar Nu'aym saboda tsaro Koda Jiddah ta burkice Mai to Yana da evidence akan abinda yayi set up ne, a haka ya samu yayi bacci da tunanin inshallah ya samu mafita.


Ita ma Jiddah anata bangaren cikin tunani tai bacci.

Wata shida kenan yaa sheikh bai kai Jiddah gida ba saidai basa kwana biyu bai Kira gida sun gaisa ba Jiddah har ta Saba da makaranta saidai har yanzu batai kawaye ba sunyi exam biyu Kuma result dinta da  kyau a inda Kuma Allah bai taba hada Jiddah da Hamnah ba saidai ita Hamnah Tasha ganin Jiddah musamman ma ranar Friday day da take ganin Jiddah ta wuni a office din rabin ranta Tasha tanbayar yaa shiekh wace ita Amma baitaba Bata amsa ba haka yasa take mugun kishi da ita ganin yanzu ta samu  fiska wajen yaa sheikh har Yana Dan kulata yasa takejin baza ta bar duk wata mace ta shige mata gaba ba ,shi kuwa yaa sheikh dalilin shi na bawa Hamnah fuska bai wuce don Jiddah ta San akwai Mata masu sanshi ba Yana ganin hakan zai taimaka mishi wajen shawo kanta don yanzu ya lura gaba Daya muamalar ta ya sauya tana bashi respect sosai saidai Bata yadda ya taba ta.
Sukan kaiwa su Nu'aym ziyara Kuma Raudah Bata gajiya wajen wayarwa Jiddah Kai ,a watannin shida dasuka wakana kuwa Raudah a yanzu haka tana da cikin ta don harya Fara fitowa wannan kenan.

Yau jumaa Kuma a yaune Hamnah ta kuduri niyyar ko Yaya sai ta ga Jiddah ta samu Tai Mata kallon kwakwaf don daga nesa take kallon ta Kuma zatayi duk wani Abu da zaisa ta Gane mene tsakanin Jiddah da yaa sheikh.



12:30 Jiddah ta fito daga class inda suke siyan abinci ta nufa don tasa bada wuri zasu koma gida ba Kuma sai yaa sheikh ya sawo daga sallahn jumaa yake siyo mata abinci.shawarma d bugger da drink dasu sweet ta siya kala kala sata a jaka sannan ta nufi bangaren University din da Jakarta goye a bayanta ta nufi office din yaa sheikh,

Daga L.T.D Hamnah ta hango ta  jitai zuciyarta ta buga dama Batun yauba yarinyar ke Mata kwarjini ba Amma Nan take Kuma saita fade rai tana fadin" yaudai zansan wani Abu game dake ko Yaya ma"tayi maganar nata hararar jiddah dake shiga office din yaa sheikh kamar ko wace Friday Hala ma wannan Bata sameshi a office din ba har ya tafi masallaci Jakarta ya sauke ta jefa kan sofar dake office din sannan ta cije hijab Shima ta cillar sannan ta zauna kan sofar tana cire toms din dake kafarta mikewa tayi ta cire wandon dake jikin ta daga ita sai rigar sport   dai wani  bomp short fari kall dashi iya gwiwa sai farar  safar dake kafar ta kanta kowa a tsife Shima ta kamashi da farin ribbon a tsakiyar kanta ,komawa Tai ta zauna Tana wani lashe bakinta tana fadin"to bismillah zamu Fara cin kayan Dadi" tayi maganar tana janyo jakar ta.


Khairaty😍✍🏻

🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
             *Yaa sheikh*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼


*U.K.Y . for real*😘



Dedicated to all my fans



                  *123*




Hamnah gyara fiska ta shiga tana ta shafe shafe sannan ta feshe jikin ta da turare ta gyra rolling dinta da yake sanye take cikin abaya Mai duwatsu Masha Allah tayi kyau sosai saboda farace sosai kunsan larabawa da fari saidai Sam Bata da hanci bare ido Amma dayake fari yaci rabin kyau Sam bazaka Gane rashin kyanta ba saboda akwai ta da daukar wanka Kuma a haife zatai shekara ashirin da shida ba laifi tanada hip dinta daidai gwargwado,


Nan dai ta gama
 shafe shafenta Tana sauri taje gurin Jiddah kafin yaa sheikh ya dawo don an kusa saukowa daga masjid Kuma tafiso ta samu Jiddahn ita kadai.


A office kuwa Jiddah dai ko a jikin ta sai kwalamar ta take wani sweet take Sha Mai tsinke Amma kafin ta Sha saita tsomashi cikin madara ```Wanda duk a siyayyar ta ta siyo``` )sannan ta lashe saita tsotse madarar tass sannan ta Kuma tsoma sweet din cikin madarar 


Haka Hamnah ta bude kofar office din ta samu Jiddah dukan su kallon juna sukai a tare Kuma zuciyoyin suka buga Jiddah ce ta Fara dauke kanta sannan Hamnah cikin gadara gadara ta shige cikin office din ta samu kujerar dake kusa da tebur din da yaa sheikh ke zama ta zauna kafa daya kandaya sannan ta juyo da kujerar Tana Dan facing Jiddah dakewa kawai Tai but cikin ranta fargabane da tunanin wai mene tsakanin wannan yarinyar da yaa sheikh ,to gaskiya koma dai ba komai to komai din na iya fasuwa don kyawun yarinyar yakai Kuma Banda rainin hankali ma ya zaay ta zauna daga ita sai bomp short gata Yar yarinya Amma daga Nan inda take zaunen tana iya ganin duwaiwakan ta da hip dinta can kasan ranta  ta furta"Allah yasa bai taba ganin ta a Haka ba Allah yasa idan taga ya kusa dawowa tasa wondon ta"ta karasa maganar tana wani juya ido tare da furzar da zazzafar iska daga bakin ta daga karshe Bata San sanda ta saki tsaki ba



Cikin zafin nama Jiddah ta dago kanta ta kalle ta suka hada ido Nan take Jiddah taji Sam matar Bata kwanta Mata a raiba sannan a take tunani ya Fado Mata "kambu uwar me ya shigo da mace cikin office din yah Abdallah sannan ma ko sallama batai ba bugu da Kari tana wani Shan kamshi harda su sakin tsaki"ta fada cikin ranta zuciyarta na tsanan ta bugawa


"Rainin wayo" ta fada a fili tunawa da tai yah Abdallah fa bayan matsayin shi na Yaya a gurin ta fa mijin tane shine har wata ta samu wannan damar a gurin sa?!

"Cab" ta sake fada tana watsawa hamnah kallon banza but ita Hamnah Bata San me Jiddah take fada ba koma dai mene ne tana tunanin jirgi daya   ne ya kwaso su don da alama Jiddah ma kishin take,sake bararrajewa tai tana sake sakin tsaki sannan ta Kuma kallon Jiddah cikin English tace


 "Ina Mai wajen yake ne?"



Bakin ciki ne ya Kuma rufe Jiddah taki ko kallon inda take Tana fadin "zaidawo kuma dukan ku za kuyi Bayani" tayi maganar tana girgiza kafa Kuma har lokacin Bata fasa Shan alawar tsinken ta ba



Hamnah Ganin Jiddah bazata amsa mata ba Kuma Sarai tasan ta Bata haushine yasa taji dadi ta Miki ta dau room freshener Tana fesawa office din "ko bakya magana ne nace Ina Mai  gurin yake"ta sake Mai maitawa  wannan karon fiskarta dauke da murmushin Jin Dadin da alama ran Jiddah  ya gama baci



Ayko a harzuke Jiddah ta tashi Tai kan Hamnah ta damki hannun ta tana fadin "fita ki jira shi a waje"tayi maganar Tana Jan hannun Hamnah duk da tafita karfi itako Hamnah cikin mamaki take kallon Jiddah da take kokarin hankada ta waje ,Jiddah na bude kofar sukaci karo da yaa sheikh idanu waje ya tsaya Yana kallon ikon Allah Jiddah na Jan hannun Hamnah zata hankada ta waje.


Na samu free time ne idan kunyi comments naji mene raayinku game da page dinnan zuwa dare ma Kuna iya ganin wani page din as I said comments dinku ne ke karamin karfin gwiwa wallahi kuyi comments kuga typing🙅🏼‍♀😍😘 see you



Khairaty✍🏻😘


🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼

              *Yaa sheikh*

🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼







U.K.Y .for real 😘





Dedicated to mmn khairy



     124

_After all this tsawon lokaci Ina mai bama gaba daya masoyan wannan littafi nawa wato *Yaa sheikh* hakuri kun San ita duniya kana naka Allah na nashi ne sai yanzu Allah ya bani damar cigaba da kawo maku karshen wannan labarin fatan masoyana zasu yi hakuri kuma su cigaba da bini. I really appreciate the way you guys have shown so much love to my book sbd na samu kira ba daya ba biyu ba wasu Ina messages toh Ina mai farikin cikin sanar maku insha Allah daga yau na dawo. One love ❤️ my fans_
........


Da mamaki yaa sheikh ke kallon gaba dayan su kallon sa ya maida ga Jiddah data takarkare tana kokarin fitar da Hamnah waje kuma duk da ganin sa da tayi bai sa ta daina kokarin turata din da take ba wani irin bala’i yake hangowa cikin idonta a hankali ya furta “yah salam dama nasan hakan zai faru” kokarin riko Jiddah yake ganin gaba daya ta cire kayan jikinta nan da nan annurin fuskar sa ya dauke yasha mur ita kuwa ya dage sai masifa take zubawa Hamna da hausa dan bata ma Samu damar tsayawa mata English ba “wlh idan na kara ganin kafar ki a office din nan sai na karya ki banza kawai uban me ya kawo ki office din mijina!” Kalmar mijina data fada yasa yaa sheikh sandardan yana kallonta ganin tama korarin fizgewa ne yasa ya hankadata cikin office din kana ya tura kofa ya saka key. Kallon sa yake cikeda masifa kana ta fashe masa da wani irin matsanan cin kuka baibi ta kanta ba ya koma ya zauna tare da bude laptop dinsa ganin haka yasa ta kara karfin kukan ta amma hakan baisa ya kallesa ba ballantana ya rarrasheta Ba komai yake a laptop din ba sbd kukan da Jiddah keyi har cikin ransa yake jinsa sai dai ya dau alwashin bazai rarrasheta har sai ya dawo cikin hankalinta it’s high time ba maganar karanta ya tabbata a Islamiya an koyar dasu karatu akan hakkin aure sannan kuma ya dauki alwashin sai ta kawo kanta da kanta koda kuwa mai zai faru bazai kara rike koda hannunta ba zai daure koya ya ne.
Ganin yaki kula yasa tayi mai isarta ta gama ta koma cunno baki. Kallonta yayi yace “shiga toilet ki wanki face dinki” ganin yanda yayi maganar ba wasa yasa ta mike ta shiga ta wanko fuskarta ta fito kayanta ya bata ba musu ya karba ya saka yace “muje” ba karamin baci ranta yayi ba ganin bai kulata ba shi kuwa duk da abun ya damesa amma ba yanda ya iya.

Hamnah kuwa gaba daya dimaucewa tayi ranta ya gama baci ganin wulakancin da Jiddah ta mata yarinya karama da ita haka ta tafi tana tunanin abunda ya Kamata tayi dan ta rama itama ta tabbata itama wannan son ya sheikh take shine shima harda wulakanta ta ya shige da ita office hmm.


Sai da ya tsaya wani shago ya dan siya abubuwa kana suka karasa gida fuuuuuuu ta shige dakinta dariya kawai yayi ya shige nashi bedroom room din sai da ya dan watsa ruwa ya chanza kaya zuwa maroon armless shirt da white  3/4 trouser kana ya fito parlour dining ya wuce direct dan yau ya kwaso yunwa, Bayan ya gama ya dawo parlour ya zauna yana chanza channel.

Jiddah kuwa Bayan ta shige daki zama tayi bakin gado tare da rakfa uban tagumi komai ya kunce mata wato kenan yaa sheik yan mata garesa aikuwa bazata sabu ba ya zama dole ta taka ma kowa ce Shegiya Burke. Tsaki tayi tace “koda yake ma meye nawa tunda da mun koma gida rabuwa zanyi dashi nima na samu nawa saurayin kuma Allah sai na gaya wa abii yan mata garesa yanda ma zasu ji tausayina suce ya sake ni aikin banza mutum sai fama da jallabiya ni kuwa yaushe zan tsaya da mijin da baya wankan kananan kaya” ta mike ta shiga toilet wanka tayi tare da dauro alwala ta fito dan an kusa kiran sallah koda ta fito cream dinta ta shafa sama sama kana ta fesa turare ta saka wata simple gown Mara hannu har kasa peach colour kana ta tada sallah.

Ya sheikh ma jin kiran sallah ya saka shi mike wa ya shiga daki sai da ya dauro alwala ya saka jallabiya ya fice masjid. 

A parlour ya sameta kan tug tayi dai dai tana cin abunci kallo daya ya mata ya shige dakin sa cike da begenta ita kuwa kicin kicin tayi da fuska tana cigaba da cin abincin ta ba jimawa ya fito waya a kunne da alama waya yake yi zauna wa yayi yana kallon Tv zeeworld kuma Mehek akeyi dama series din ba dai soyayya ba ga shoria tsaye ba riga ita kuwa mehek ta dora kanta a kirjinsa tare da lumshe ido. Remote ya dauka ya fara chanza channel cuno baki gaba tayi kasa kasa tace “shikenan ba halin na kalli abunda nake so” sai rai ya jita ya share yana cigaba da wayar sa. Jin yace “Abdul majid bama ummee wayar toh” yasa ta dago da sauri tare da matsowa kusa dashi tana kai kunnenta ga wayar wani irin kallo ya jefa mata hakan yasa tadan ja baya. Bayan sun gaisa da ummee yake gaya mata “ummee fa na turo kudin yanzu kuma na kira wayar abii bata zuwa ki gaya masa sai ayi kokari a fara aikin insha Allah duk wata zan rika turo da abunda ya samu Kinga kafin mu dawo an gama idan Allah ya yarda” ummee tace “toh shikenan Allah ya dafa mana kasan harkar gina ba wasa ba” yace “haka ne ummee insha Allah zanyi kokari na gani koda iya nawa aka gama dai” tace “toh shikenan Ina yar tawa” kallon Jidda yayi tare da cewa “ummee bata kusa amma anjima zan...” bai karasa ba ta fashe da kuka da sauri ya juyo yana kallonta ummee tace “Ba kukan ta nake ji ba me aka mata kuma” yace “hmmm gata dai” karbar wayar tayi ko gaisuwa babu tace “ummee Kinga yah Abdallah ko” ummee tace “me kuma yayan naki ya maki” tace “toh ummee bashi bane yace bana kusa Bayan gani zaune a gurin waya sani ma kullum haka yake cewa” ummee tayi dariya tace “oh ni Aishatu bansan yaushe yarta zata girma ba toh shikenan zance ya siya maki taki wayar sai na dinga kiran ki” tace “yeeeee ummee na shi yasa nake kara sonki” ummee tace “toh yau ba gaisuwa” kasa tayi da kai kamar tana gabanta tace “yi hakuri ummee na Ina yini ya mutanen gida” dariya ummee tayi tace “Lpy qalau ya karatu” tace “alhmdllh” ummee tace “a maida hankali dai banda wasa” tace “toh ummee Ina mami” ummee tace “tana gida amma zan kira zuwa gobe sai kuyi magana” tace “toh ummee na ki gaida ta” ummee tace “toh zata ji bama yayan naki waya” mika masa tayi hawaye na zubo mata ita kawai gida take son zuwa taga mamin ta shi kuwa sallama sukayi da ummee tare da ajiye wayar.


Khairaty✍🏻




https://chat.whatsapp.com/CIKrWG5ATBh3WMUVsBCeK1



🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼

              *Yaa sheikh*

🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼







U.K.Y .for real 😘



Dedicated to mmn khairy & Neeshar.jay


Haka suka cigaba da zaman gidan ba abunda ya chanza kullum ya sheikh cikin azumi yake duk da yanzu Jidda ta rage yawan saka ƙananan kaya, abinda ke damun ta yanzu ɗaya ne yanda take gani ya Sheikh na sake ma yan mata fuska sosai bata jin dadi ko kadan gashi ya tsare gida ballantana ta samu damar tambayaarsa taci kudirin idan sun koma gida ba abinda zai hana bata masa sharri ba cewa zata yi kullum yana tare da yan matan sa kuma ko kallon ta baya yi harda gwada yanda zata yi a gaban Abii tayi "wlh Abii ni bazan zauna da shi ba kullum yana tare da yan matan sa ko kallo na baya yi haka ma idan yaje school din mu ɗauka na sai yayi ta kallon frnds ɗina har da cewa na basa ɗaya" yanda ta kwabe fuska itama sai da abun ya bata dariya tace " hmmm zaka sani yah Nima idan muka koma zan yi saurayi mai kyau kamar ka" ta lumshe ido shigowar teachern su ne yasa ta mai da hankali 6 nayi ya Sheikh yaje ɗaukan ta sai wani ya mutsa fuska take ta shiga ta zauna yaja suka tafi.

Bayan kwana biyu yace ta shirya zasu je gidan Nu'aym ta mike ta shige shima bedroom din sa ya shiga dan shirya wa ba jima wa sai gashi ya fito cikin shigar kaftan off-white din tissue ya saka mai zanen balls a jiki ya kwanta sosai a jikin sa har da hula ya saka yau hakan yasa kyan sa kara fitowa sosai, kusan fice mins ya dauka yana jiran fitowar ta amma shiru hakan yasa ya mike ya shiga dakin ta bakin sa ɗauke da sallama tana zaune gaban dressing mirror ta gama shafa ma ɗan ƙaramin bakin ta red lipstick suka hada ido ta cikin madubi ɗauke kai tayi tare da turo dan Karamin bakin nata kallon ta kawai yake ya kasa ɗauke idon sa a kanta, matsawa yayi kusa da ita ya daura hannunsa kan shoulder ɗin ta yana cigaba da kallon ta, ganin yana ɓata mata lokaci yasa tace "ya ka bari na shirya mana" sai lokacin ya farfaɗo sakin ta yayi yana kallon yanda take tafiya gashi towel ɗin iya kar cinyar ta yake.

Gaba daya ta gama ɗaukar hankalin sa Ita kuwa ganin yaƙi fita yasa ta jiyo tace "ya ka fita to na shirya mana" juyawa yayi ya fice gaba daya jikin sa a mace ji yake ina ma yau yayi azumin sa tsaki kawai yayi ya zauna jiran fitowar ta ba jima wa sai gata sanye da abaya army green wadda ta kara fito da hasken ta da kyan ta Abdallah can't take off his eyes on her cikin ransa ya furta "ya zuljalali wal'ikram Allah na gode maka.

Zama tayi kan ɗaya daga cikin kujerar parlourn ta na wani shan kamshi tana turo baki mikewa yayi yace "muje" yana gaba tana bin sa a baya har suka shiga Mota sai gidan Nu'aym, sun jima a gidan kana suka koma.

Kwana ki sai tafiya suke kamar yanda bawa ke cigaba da kusan to kabarin sa a yanzu shekara ɗaya kenan data wuce abubuwa da yawa sun faru ciki kuwa har da gama gidan ya Sheikh da aka yi sai dai iya party din sa kawai aka gama saura na su Abdul da ummar, Jiddarh kuma ana ss2 yanzu kuma Abdallah ya mata alƙawarin zuwa gida Nigeria idan har taci examns din ta idan kuma bata ci ba zai cire ta daga school gaba daya ya daina wahalar da kuɗin sa hakan yasa ta dage tana karatu.

Zaune take tana ta faman karatu saboda example din da zasu Fara gaba daya kanta ya dauki chaji tsaki tayi tare da mikewa tsaye riga ce kara ma mai hannun vest iya karta cinya kanta kuwa ko dan kwallon babu ba komai a jikin ta sai pant Amma fitowa tayi parlour sbd yunwar da take ji bata kula dashi  kwance a parlourn ba ta wuce direct fridge ɗin da dining table ɗauki fresh milk ta juya zata koma, tun fitowar ta yake Binta da ido mutuwar zaune yayi ganin yanda ta kara girma yau ɗin nan ganin zata koma ya saka shi kiranta "Jiddarh" jin yanda ya kirata murya a karshe yasa ta juya da hannu ya mata alama da tazo ba musu  taje mike wa zaune yayi ya nuna mata turo baki tayi tace "kai ya am busy gashi nama kasa solving wani question pls ka barni na je kai fa kace idan nayi failing zaka cire ni daga makaranta" yace "ok toh Naji jeki dauko sai na taya ki" mike wa tayi da sauri ta shiga daki sai gata da books dinta ta zauna kusa dashi ta bude kallon question din yayi tare da jan tsaki yace "yanzu wannan ne baki iya ba?" Kallon sa tayi tare da turo baki cikin shagwaɓa tace "Ni fa bawai ban iya bane kawai ban gane ba ai kaga wanda nayi" ta fada tana nuna  masa back page ɗin" yace "silly girl kawai a fili ya fara karanta question din 'solve the equation 6x-5x-4=0  kai Amma dai ke..." Turo baki tayi tace "daƙiƙiya ce ko?" 

Dariya yayi yace "Ni dai ban faɗa ba toh a haka ne zaki iya studying medicine kuwa?" Kara turo baki tayi tace "Ni dai ba daƙiƙiya bace" yace "ay ban faɗa ba kuma idan kika ƙara turo min baki zaki sani" kara turo baki tayi da sauri ya juyo da fuskanta ya hade bakin su ta fara ƙoƙarin ƙwace wa amma yaki bata damar hakan yanda yake binta da passionate kiss hakan yasa ta fara mai da masa da martani tuni ya fara kiciniyar raba ta da girar jikin ta bata hana sa ba dan ita ma tana so ɗaukar ta yayi sukutum Sai bedroom ɗin sa ganin ya fara wuce gona da iri yasa Jiddarh fara ture sa amma ina yayi nisa.

Sai da komai ya gama wakana kana ya mirgina gefe yana sauraren yanda sautin kukan ta ke fita a hankali kuma cikin disashewar murya tsam ya rungume ta jikin sa yana rarrashi its being a while tun ranar daya fara kusantar ta bai kara ba sai wannan karon "Allah ya maki albarka Allah ya biya ki da gidan aljanna" ita dai sai kukan ta take yi dakyar ya dauke ta Sai toilet ya haɗa mata ruwan zafi ya sakata sai matsara kwalla take dakyar ya samu tayi wanka ta fito. Yau kam yasan akwai rikici a gidan dan zai sha kuka. Karatun da ba'a ƙara sa ba kenan, kamar yanda ya faɗa gaba daya har dare taki bari su haɗu tun da ta shiga ɗakinta ta rufe gashi taƙi fitowa taci abinci yayi har ya gaji ganin dare ya raba sosai yasa ya koma ɗakin sa ya kwanta. 

Tana jin sa amma ta masa banza ganin zai takura mata tana karatu ne yasa ta shige toilet da book ɗinta ba ita ta fito ba sai pass 2 Shima yunwar data dameta ne yasa ta fito neman abinda zata saka ma cikin ta.

Tamar Monday suka shirya gaba daya da sauri take shan tea har ta gama ta miƙe tana jiransa  ganin yanda yake shan tea din ne yasa tace "ya exams Dina fa 8 ne and this is 7:42" mikewa yayi yace "let go" tana gaba yana Binta a baya har suka sauka ƙasa ta shiga ya Kaita school wining glass yace "karki manta da addu'a all the best" tace thanks" ta shige abunta shima yaja motar sa ya wuce.



Khairaty✍🏻







🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼

              *Yaa sheikh*

🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼







U.K.Y .for real 😘


Dedicated to mmn khairy & Neeshar.jay



125


Haka kullum Jiddarh ke fita exams gaba ɗaya yanzu ta zama busy kullum cikin karatu dan babban burinta ta gama secondary school ta fara University inasha Allah sai ta zama cikakkiyar likita kamar yanda take so kuma zata bama ya sheikh mamaki tunda tantama yake akan ƙoƙarin ta, ranar wata friday suka gama exams a gajiye ta fito dan practical chemistry sukayi yau dakyar ta ƙara sa kofar office ɗinsa tasan by now ya tafi masjid dan password 12 buɗe kofa tayi ta shiga sai kawai taga Hamnah zaune ta Hakim ce gashi tayi kyau har ta gaji cikin shigar ta long sleeve shirt red data kama ta Sai wandon ta Palazzo baki da flowers red tayi using red Vail Mai touch din black ƙafar da tayi crossing ɗaya kan ɗaya na sanye da red tomes sosae gaba Jiddarh ya faɗi ta ƙara sa cikin office ɗin fuskanta ba annur sai ta nemi gajiyar data kwaso ta barta direct kujerar ya Sheikh ta nufa ta zaune kallo ɗaya ta mata ta ɗauke kai.

Itama sai bata kula ta ba amma taci alwashin zata taka mata burki da wannan iskancin biyu mijin ta har office da take yi ko kuwa shike kiranta ne yau zai mata bayani, sai kusan 2 ya shigo office ɗin cikin sauri dan yasan cewa by this time Jiddarh na jiran sa.

Yana shiga yayi turus ganin Hamna zaune cikin wannan shigar haɗe girar sama da ƙasa yayi sai dai ganin Jiddarh zaune ya saka shi ɗan sakin fuska ya canza yare zuwa larabci yace ma Hamna "what do you want" Farrer tayi da ido tace "babu kawai dai nazo ganin ka ne" smiling yayi yace "thanks" 

Ran Jiddarh idan yayi dubu ya ɓaci wato ma dan rainin hankali a gabanta zai mata smiling itama tana masa iyaye da ido harda wani canza yare dan karta ji me suke faɗa miƙewa tayi tare da cire hijab ɗin ta ta fara unbotting rigar ta ta karasa kusa dashi ta shige jikin sa, ya Sheikh kuwa mutuwar tsaye yayi yana kallon ikon Allah mamaki bai ƙara kamasa ba sai da yaji bakin sa cikin na Jiddarh turus yayi kusa take masa cike da ƙware wa kawai ya fara mayar mata da martani harda kamo fuskar ta, kusan five mins suna a haka kana ta zare bakinta ta jiyo tana watsama Hamnah da tayi mutuwar zaune kallo kana ta maida kallon ta ga ya Sheikh tace "Are You satisfied or you need more" Sai a lokacin ya gane dalilin da yasa tayi hakan wato sbd taga Hamna ne smiling kawai yayi ta shafa gefen fuskar sa.

Gaban Hamna ta karasa tana wani yatsine fuska tace "last warning don't you ever think of coming to this office because this is my husband office, oh lemme no waste my saliva since you witness it with your own eyes so you may leave" ta juya ta fara tafiya sai kuma ta dawo tace "or do you want to watch it do the end ohh sorry poor Hamna you'll end of loosing your eyesight" ta kama hannunta sai waje tace "don't come back here if not..." Ta rufe kofar da karfi harda saka key kana ta koma gurin Abdallah da tayi mutuwar tsaye.

Tsare sa tayi da idon ta tace "dama haka kake kawo yan mata kana ajiyewa kullum what's between you and this girl da take kawo ma ziyara kullum" gaba daya daburcewa ya soma yi ta ɗaga hannu tace "enough you have nothing to tell me ya Abdallah you have" ta ɗauki hijab ɗin ta ta saka kana tace "let go am tired" kamar soko haka ya koma sai da suka je gida ya samu ya rarrashe ta dakyar.

Wayar daya siya mata  iPhone 8+ ya ɗauko ya bata ssoae tayi farin ciki ta dinga zabga masa godiya da addu'a hakan ba ƙaramin daɗi ya masa ba ganin tana cikin farin ciki nan ya mata setting komai tare da nuna mata yanda ake amfani da ita ya bata nan ta fara saka number din su ummee ta kira ta gaya mata  ta kira Abii shima sosae suka taya ta muran su Abdul kuwa harda tsokanar ta, yace "kice ma yah buɗe maki WhatsApp kinga kin huta da wahalar da credit din ki kuma zan turo maki ko din budurwa ta amma karki gaya ma yau" dariya tayi tace "toh shikenan ya Abdul majid" bayan sunyi sallama ta miƙa masa waya tace " yah ka buɗe min WhatsApp plsss" ba musu ya bude mata harda facebook sosae taji daɗi bayan Abdul Majid ya turo mata no din khadeeja suka gaisa sosae suka sha fira har khadeeja ke ce mata ta fara karatun novel tunda ba all take zuwa ba yanzu ba musu tace "toh ki turo" ai ko sai gasu rututu Sudan shigowa tayi mata godiya kawai dan tasan ba lallai ne ta iya karantawa ba.

Yanzu da wuri sabuwar mai aikin ta ke wuce wa sai ita kaɗai cikin gida kuma gashi da khadeeja kawai take chatting gashi bata online kaɗai ci da zaman shiru ya mata yawa ta dauko wayar ta ta buɗe document ɗin da khadeeja ta turo mata ta fara karanta wani book Ashwaan sosai take jin daɗin karanta book din and rashin sabo har ya Sheikh ya dawo tana kwance kan sofa tana fama dariya yayi yace "sabon shiga" 

Turo baki tayi bata ce komai ba ya zauna yana faɗin "washh Allah na gaji" 

A hankali tace "sannu" mikewa tayi ta kawo masa ruwa sosae yaji daɗi yace "Nagode" smiling kawai tayi ta zauna tana cigaba da karatun ta, hadare tana abu ɗaya sosai take jin daɗin labarin kusan iri ɗaya ne da nata sai dai bambanci Safwaan ba cousin din Safa bane ita kuma cousins ne ita da Abdallah.
Sai kusan 2 tayi bacci ai kuwa dakyar ta tashi sallar asuba tana idarwa kuwa ta faɗa gado ta cigaba da baccin ta koda Ya Sheikh ya gama shirin fita office ya leƙo ya ganta tana bacci girgiza kai kawai yayi ya mata kiss a gishiri da lips buɗe idon ta tayi ya samar Mata murmushi itama ta mayar masa yace "sleeping beauty cigaba da baccin ki Ni zan fita" lumshe ido tayi ya kara ja mata blanket ya fice.
  Sai kusan 12 ta farka wanka tayi tare da yin breakfast ta cigaba da karatu. Sabon shiga Lol😆


Ya Sheikh kuwa sai fafutuka yake saboda komawa gida da yake so suyi next week kullum ya fita a gajiye yake dawowa lilis, Jiddarh kuwa bata da aiki sai karatun novels sosae take jin daɗi tana mamakin yanda ake soyayya haka inama zata samu wanda zai riƙa mata irin wannan soyayyar da tarairaya lumshe ido tayi cike da shauki tana buɗe wa taga ya Sheikh tsaye a kanta gira ɗaya ya ɗaga mata yace "ya dai?" Mikewa zaune tayi tace "ba komai"

Hannun sa taka kama tace "have a sit yayana"  zaro Ido yayi tace "Are You surprised?" Yace "Yes" tace "hmmm yaya kenan"


*Nigeria*


Sosae ake hidima a a sabon gdan da su Jiddarh zasu zauna an saka masu komai dai dai karfin Abdullah komai na gdan yayi kyau matuƙa  su ummee sai shirye shiryen tarbar mutanen Makka ake yi.



Fans baku tambayi Nana


 Nana kam gaba ɗaya ta zama ƴar duniya duk wata wayewa irin ta jahilai Nana na da ita sosae tace sheƙe ayarta tun a Skl teachers suka fara Bintaba musu ta bada kanta wanda hakan ya yi sanadin faɗawar ta halaka dama tun farko gdan bata taso ana kwaɓarta ba hakan yasa ta zaƙe tana more rayuwar ta.




Khairaty✍🏻




🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼

              *Yaa sheikh*

🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼



U.K.Y .for real 😘


Dedicated to mmn khairy & Neeshar.jay


127

Tunda daga lokacin da Jiddarh ta gama exams ba ta da aiki sai karatun novel yanzu kam ko kallo ba ta cika mai da hankali a kan sa ba a ɗaya hannun kuma tana kwatanta duk abinda ta gani a cikin littafin data karanta sai dai har yanzu bata gama sakin jiki da shi ba kullum zaka ga ta buɗe gida da turaren wuta masu daɗin kamshi wata rana ma da kanta take saka ya Sheikh ya fita da ita ta siya duk wanda ya mata, gaba ɗaya yanzu kamar ba ita ba ta koma wata silent ga kewar gida daya cika zuciyar ta duk da kusan kullum suna makale a waya sai dai hakan bai hanata son Jin warmness na malanta ba. A zamantakewar da ya Sheikh kuwa har yanzu ta ƙi bada kai ko Dan romance ɗin nan yanzu ma ta daina bari haka kawai Allah ya saka mata kunyar sa lokaci daya idan taga ya riƙe hannun ta sai ta nema hanyar guduwa.

Ya Sheikh kuwa sosae ya ƙara zama busy gashi students dinsu sun Fara exams hakan yasa komai ya haɗe masa idan ya fita tun safe sai bayan isha.


Kwance take akan 3 seater waya a hannun ta sai faman dariya take har da rike ciki "kai aunty khadeeja zata kashe ni da dariya wlh" 

Ƙarar shigowar message ya katse mata maganar da take yi chat din su da khadeeja ta karanta bayan ta gama sai kuma tayi shiru tana wani tunani can ta mata reply da "Toh aunty khadeeja insha Allah I will try my best" daga nan ta kashe data ta miƙe, 

Wanka ta fara yi tare da ɗauro alwala ta fito riga kawai ta saka ta tada Sallah sbd lokacin ta ya ɗan soma wucewa, bayan ta idar tayi shafa'i kawai ta mike gaban mirror ta matsa sai da ta jona  hand dryer ta busar da kanta kana ta dan shafa mai sama sama ta shafa powder and hot red lipstick days ƙara fito da kyawun ta miraran cumbing kan ta tayi tare da parking ɗinsa one side ta fesa gaba daya pefs ɗin da ke kan mirror ɗin suka bada wani sihirtaccen kamshi mai sanyi da sanyaya zuciya.  Army green Egypt abaya ta saka sosae rigar ta ƙara fito da hasken fatar jikin ta dake glowing tayi simple ɗaurin turban data Ke kallo kullum a Channel ɗin Neeshar.jay, faɗa maku irin kyan da tayi ɓata lokaci ne kawai ku hango readers. 
    Kallon kanta tayi a madubi a murmushi ne ya suɓuce mata ƙasan maƙoshinta ta furta "alhmdllh" juyawa tayi yana kallon yanda ta haɗe cikin wannan shigar, bubbuga kafa ta fara yi a kasa tace "kai aunty khadeeja Allah fa ni kunya nake ji taya zan fara hugging ɗinsa Idan ya dawo" tsaki tayi tace "ugh I just have to give it a trial" ganin har kusan 9:34pm yasa ta kuma fesa turare ta  ɗauki wayar ta ta fice parlour.

Jin alama mun an zura key a main door ɗinne yasa ta miƙa da gudu ta laɓe jikin cotton ɗin da ke gurin, ya Sheikh kuwa yana buɗe kofa yaji an cikwikwuye sa ga kamshin ta gaba ɗaya ya gama cika masa hanci a hankali ya kai hannun sa saman waist ɗin ta ya kuma mannata da jikin sa sai kawai ta lafe 30sec suna a haka kana ya ɗago ta daga jikin sa sai kawai ta manna masa kiss a gefen wuya cikin wata murya tace "sannu da zuwa" 🤣 ai kusan sumewa ya Sheikh yayi a gurin gaba ɗaya Jiddarh ta gama tafiya da shi sai murmushi yake zubawa yana kallon ta ga kuma mamaki,

     Jakar hannun sa ta karɓa ta wuce gaba tana taku ɗai ɗai da ido ya rakata har ta kai tsakiyar parlour ta jiyo ta gansa tsaye farrr tayi da ido tace "ƙara so mana" kamar soko haka ya koma gaba ɗaya Jiddarh ta rikitashi ruwa  drink ɗin da ya saba haɗa mata ta zubo masa a glass cup ta bashi ya ƙarɓa ya sha , ta koma gefe ta zauna kanta a kasa mike wa yayi ya shige ɗakin sa yana dafe ciki, a daddafe yayi  wanka koda ya fito sai yaga kaya a kan bed smiling yayi ya wuce gaban mirror ɗin sa ya ɗan shafa mai kana ya saka kayan a gaggauce dan yunwa yake ji.

A dining ya hangota tana ciro wani jug daga frigde ƙara sawa yayi ba zato ya rungume ta ta baya tare da ɗaura kansa a wuyanta yana shaƙar kamshinta "wifey am hungry" turo baki tayi tace "kai yaya" yace "serious a bani abincin"  tace "kai ya Abdallah Ko kunya jifa yanda kake magana Allah kamar yaro" ta faɗa tana dariya, 
  Juyo da ita gaba yayi yace "toh ai baki yi karya ba Ni ɗin a gaban ki ai yaro ne" rufe fuskanta tayi a ƙirjinsa tace "kai ya" yace "ehh mana yanzu dai a bani abinci" sakin ta yayi ya zauna ta zuba masa abincin dai dai yanda tasan zai ishe sa ta zuba masa juice ta zuba masa ta tura gaban sa kallon ta yayi yace "me kike nufi Ni zan ci da kai na" da mamaki ta kalle sa tace "yau dai da alama rigima kake ji da ita yah toh Ni zan baka a baki ne" yace "rasss kawai ki cika ladan ki beb" murmushi tayi tace "kai yah nifa Bazan iya ba" yace "ohh really toh kuwa na ƙoshi bazan ci ba".

    Mikewa tayi ta karasa kujerar dake kusa da nashi tace "toh kar kayi fushi zo na baka" yace "yauwa ko kefa" gaba ɗaya mamakin abinda ya sauya Jiddarh a ɗan tsakanin nan yake yi lallai ya godewa Allah da kuma duk abinda ya canza masa Jiddarhn shi.
    Haka ta dinga bashi abincin a baki har ya ƙoshi ya miƙa ya koma parlour ita kuwa ta tattara gaba ɗaya kayan takai kitchen, Bayan ta gama ta dawo parlour ta zauna ya Sheikh ya kira mutanen Nijeriya suka gaisa bayan ya Bama Jiddarh suka ɓarke da fira suna dariya ita da ummee da Mami da shigowar ta kenan.
  Bayan sunyi sallama ta miƙa masa wayar sa ta cigaba da kallon ta shi kuma ya maida hankali a laptop ɗin sa suna fira jifa jifa har kusan 11 ta miƙe ta shige ɗaki dan bacci take ji yau ɗin.

Jin shiru har ya gama abinda yake yi ne yasa ya tattara kayansa ya kashe komai ya kai ɗaki kana ya koma ɗakin ta can ya hangota kwance tana bacci cikin duvet kamar wata jariri ya smiling yayi yaƙarasa cikin ɗakin ya mata addu'a tare da rage sanyin AC ɗin kana ya kashe mata wuta ya fice abunsa shima sallah yayi kana yayi shirin kwanciya cike da begen matar sa.

    Bayan sati 2

Yau tafiyar su ya Sheikh Nijeriya ya rage kwana huɗu  kuma sai yau ne yake sanar da Jiddarh sosae tayi farin ciki da murna da jin wannan maganar zata je taga mamin ta, da yamma suka shirya suka fita ya ɗan yi yawo da ita gdan frnds ɗin sa sunje masu bankwana kana suka tsaya a hanya suka fara siyan tsaraba, kullum haka suke fita har gdan su Nu'aym sanda suka je. 
    Ranar Thursday jirgin su ya ɗaya sai Nijeriya.

Abii da su Abdul Malik ne suka tafi tarbarsu su ummee kam sai hidima suke sosae a gda fuskar kowa ɗauke da farin cikin don ganin su Jiddarh.

Su Abii na tsaye har mutanen cikin jirgin suka fara fitowa har su Jiddarh suka fito itace ta fara ɗaura ido a kansu da gudu ta tafi ta faɗa kan Abii shikam bai ma gane Jiddarh ba "Abii nayi missing ɗin ka sosai Abii yeeeee" Abdul majid ne yace "ke ɗaga shi karki ƙara sa masa kafa mana katuwa dake haka" ɗagowa tayi tace "kai ya Abdul majid" kallon ta ta mai da kan Abii dake Binta da ido gaba ɗaya ta canza masa a shekara ɗaya kamar ba Jiddarh daya sani ba , ƙara sowar yah Sheikh ne yasa Abii ɗauke idon sa daga kan Jiddarh.
     Turo baki tayi tace "Abii wai baka gane Ni bane ko ka daina so na ne yanzu?" Dariya Abii yayi yace "ba haka bane kawai dai naga kin  canza ne kamar bake ba kin zama wata balarabiya. 
    Dariya suka yi gaba ɗaya yah Sheikh ya ƙara sa kusa da mahaifinsa ya ɗan masa side hug Abii yace "ya hanya Abdallah" 
  "Lpy alhmdllh Abii mun same ku lpy" 
Abii yace "Lpy qalau"

  Su Abdul sukayi hugging ɗin sa cike da shaukin ganin yayan nasu nan suka kwasa sai gida.

Ko gyara parking Abdul Malik baiyi ba Jiddarh ta fice da gudu sai cikin gida tana kwalla kiran "ummee ummeena" sai ga ummee ta fito daga cikin ɗaki kanta ta faɗa sai kuma kuka.

Ummee tace "a'a meye kuma na kuka Jiddarh"

Turo baki tayi tace "ummee nah kukan jin daɗin ganin ki ne"

Su Addul Majid da suka shigo da kaya suka saka mata dariya yace "kedai bakya girma wlh"
 Race "kai ya Abdul Malik" har ƙasa ta duƙa tace "ummee nah ina yini mun same ku lpy"

Ɗago ta ummee tayi tace "Lpy Jiddarh ya hanya" tace "Lpy"

Abii daya shigo yace "kinga ƴar taki ta koma balarabiya ko"

Dariya ummee tayi tace "aiko dai Masha Allah"

Yahoo Sheikh ma ya ƙara so ya gaida ummee cike da ƙaunar uwar ta sa" ta amsa tana tambayar hanya yace "alhmdllh".

Jiddarh tace "ummee nah mamy fa?"

Ummee tace "aiko yanzu taje gida" Jiddarh kuwa da sauri ta fice suka karata da dariya, sosae ummee taji daɗi har cikin ranta ganin yanda yaran nata suka zama kamar basu ba abun sha'awa. Yah Sheikh kuma ɗakin sa ya wuce dan watsi ruwa ya ɗan cire gajiya.



Khairaty✍🏻




🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼

              *Yaa sheikh*

🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼



U.K.Y .for real 😘


Dedicated to mmn khairy & Neeshar.jay

*END........*



Mamy Na cikin ɗaki Jiddarh ta faɗo kamar wacca aka jefo harararta mamy tayi tace "meye haka" faɗa wa kanta Jiddarh tayi tace "mamyyyyy" ke karki karya ni mana irin wannan rungumar haka" tace"kai mamy ina yini wlh nayi missing ɗinki sosae mamyna"

Mamy race "ya hanya to ina babana?"

Jiddarh tace "Lpy mamy Ni kamar ma baki ji daɗin dawowa na ba" 

Mamy tace "haka na gaya maki"

Turo baki tayi tace "toh mamy ba gashi ba Ni da nazo gurin ki bata ni kike yi ba shi yau da bai zo ba shi kike tambaya"

Tace "ke Ni bazan iya ba ya kuka baro Makka"

Tace "Lpy mamy na". Nan suka shiga fira irin ta ƴa da uwa.

       Ya Sheikh kuwa bayan ya fito gidan mamy ta shiga suka gaisa ta masa sannu da zuwa a tare suka fito gidan gaba ɗaya suka shiga gidan ummee a parlour suka baje aka ci abinci cikin farin ciki har magrib suna tare. Kiran sallah ne ya tada mamy ta koma gida su ummee ma suka mike sallah yan matan gidan kuma suka fice masjid, bayan isha ma suna parlourn ummee har Abii ya dawo shima aka dan taɓa firar dashi wanda yawan ci Jiddarh ce ke basu labarin Makka da kuma school ɗin ta har da labarin su Nu'aym gaba ɗaya sai data gaya masu sai 11 Abii yace kowa yaje ya kwanta, kallon kasan ido yah Sheikh ke bin Jiddarh dashi ganin hakan yasa ta mike ta shige ɗaki girgiza kai yayi tare da masu sai da safe ya fice su Abdul ma suka wuce ɗakin su ummee ma bayan ta gama shirya wa ta wuce ɗakin Abii.

     Washe gari sai kusan 10am ya Sheikh ya fito a parlour ya tarar da Jiddarh tana breakfast da alama kuma ummee na gurin abii, zama yayi kusa da ita ya saka hannu ya dauki dankali daya ya kai baki.
  Turo baki tayi tace "kai yaya fah" kallonta yayi kana ya maida hannun sa ya ƙara ɗaukar daya yace "ba gaisuwa" a hankali tace "ina kwana" yace "bazan amsa ba" bata ce komai ba ta ɗauke plate ɗin ta juya masa baya ya dawo gabanta ta ƙara juyawa suna haka sai ga ummee da Abii kunya ce ta kama yahoo Sheikh sae ya shiga sosae bayan kansa su kuma sukayi kamar basu gamsu ba Jiddarh ta turo baki tace "ummee nah kin ga yah ko?" Ummee tace "kyale sa ci kayan ki" zama sukayi Abii yace "Jiddarh ba tayi ne" dariya tayi tace "haba Abii Ni na isa" yace "toh ba gashi ba" miƙa masa plate da cup ɗin ta tayi yace "a'a na gode sai da na riƙa" murmushi tayi yace "toh ya karatun Saudi da daɗi ko kuwa" tace "da daɗi abii yanzu ina ganewa and Ai nama kusa gamawa" yace "hakan yayi kyau a ƙara dagewa" tace "insha Allah" .
   Kallon sa ya maida kan ya Sheikh yace "Abdallah yaushe zaku koma can gdan naku?"
  Kallon ummee yayi kana yace "gobe insha Allah"
  
Abii yace "a'a gobe yayi nisa dama da kuka dawo can kuka tare kawai yafi"
   Baice komai ba Abii yace "idan Allah ya kaimu anjima sai ka ɗauki matar ka ku tafi ai"
Yace "insha Allah" daga nan Abii ya mike ya fice ummee na bayan sa.

Turo baki Jiddarh tayi kamar za tayi kuka ta kalli ya Sheikh taga shima ita yake kallo ya ɗaga mata gira ɗaya sama sai kawai ta fashe da kuka.

Da sauri ya matso kusa da ita yana tambayar Lpy tace "toh ba kai bane zaka kuma ɗauke ni daga gurin su ummee ba" dariya ta basa amma sai bai yi ba ya fara rarrashin ta daya ga tayi shiru ya fice daga gidan itama tana gamawa ta shiga gidan su gurin Mamy, bata jima ba ta fice daga gidan bata tsaya ko ina ba sai gidan su kawar ta Nana sai dai bata tarar da ita ba tana makaranta basuyi hutu ba hakan yasa ta koma gida.

Bayan sallar isha kamar yanda Abii ya faɗa su ya Sheikh suka fito dan tafiya gidan su Abdul majid ne zai kasu a motar Abii, sosae aka sha riciki da Jiddarh akan bazata koma ba da kyar aka lallaɓata suka tafi. 

Gida me mai kyau daya ji kayan more rayuwa dai dai ƙarfin ya Sheikh sosae gidan zai burge ka idan ka kalla parlour biyu da ɗaki uku sai jiragen da store gdan safe content ne, a wannan daren ya Sheikh bai ɗaga ma Jiddarh kafa ba sai kuka take masa haka ya samu ya lallaɓata.


   *A gurguje*


Bayan sati ɗaya ranar friday ya Sheikh ya kawo Jiddarh wuni gida dan fita zai yi kuma sai dare zai dawo, sosae taji daɗi bayan la'asar ta shirya zuwa gdan su Nana tunda mahaifiyar ta tace sun kusa dawowa, a parlour ta tarar da ita suka rungume juna cike da begen ganin juna bayan sun zauna Nana ta kawo wa Jiddarh ruwa ta zauna tana rike baki tace "kawata kinga yanda kika koma kuwa kamar fa bale ba" murmushi Jiddarh tayi bata ce komai ba ita kuwa Nana sai santin kyan da Jiddarh tayi take Nan suka shiga firar yaushe rabo Jiddarh ta labartawa Nana yanda take jin daɗin zaman Makka Nana tace "ba dole ba kin huta ai gashi har kin chanza kin koma kamar larabawa" 
  Dariya Jiddarh tayi tace "lallai baki san larabawan bane shi yasa kike haɗa Ni dasu" 

Nana tace "toh ya mijin naki" 

Jiddarh tace "yana Lpy qalau"

Nana tace "uhmm su Jiddarh manya masu aure amma dai bakya zuwa makaranta ko"

Jiddarh tace "ina zuwa mana me kika gani?"

Nana tace "a toh nayi tunanin kina da ciki ne shi yasa na tambaya kin san ciki baya barin ayi karatu barin ma ke da kike secondary har yanzu kuma shekarun ki nawa ma da zakiyi ciki"

Jiddarh ta bata fuska tace "ke Ni dai bani da wani ciki kuma ina zuwa school sai ma na rigaki gamawa kin san karatun mu ba ɗaya daku ba"

Nana ta tabe baki tace "haka ne amma dai idan kika yi wasa ciki ya shige ki ke kika sani"
  Murmushi kawai Jiddarh tayi suka cigaba da fira Nana na bata shawara wasu ta ɗauka wasu kuma ta watsar.


Da dare bayan ta Sheikh ya zo ya ɗauke ta suka tafi gida, bayan sun ƙimtsa suka dawo parlour tana kallo Abdallah kuma yana aiki a laptop din sa, kallon sa tayi tace "yah" ɗagowa yayi ya kalleta sai dai bai amsa ba ta cigaba "dama nace Ni dai uhm.... dama cewa nayi..."

Yace "ki gaya min menene"

Kasa tayi da kai tace "dama zan gaya ma ne ne dai bana son  haihuwa" ta faɗa tana turo baki.
 
   Da mamaki yake kallon ta kana yace "zo nan" ba musu ta je gabansa ya zaunar da ita kusa dashi murya a sanyaye yace "Jiddarh kin san me kike faɗa kuwa haihuwa da nine bakya so ku kuwa haihuwar ce gaba ɗaya bakya so?"
  Kasa tayi da kanta ba tace komai ba yace "Jiddarh talk mana" tana wasa da hannun ta tace "haihuwar ce bana so" 
  Yace "dalili?"
  Tace "saboda school ɗina kuma kaga ai ni ƙarama ce" ta faɗa tana zuba masa idanun ta.

Ɗauke kansa yayi daga kallon ta yana jawo laptop ɗin sa yace "wani ya baki wannan shawarar?" 

Tace "a'a"
Yace "kin san bana son ƙarya nasan hankalin ki bazai kai kiyi wannan tunanin ba dole a kwai wanda ya raɗa maki wannan maganar"

      Kasa jurar kallon sa tayi ta maida kanta ƙasa ba tace komai ba yace "shikenan tashi jeki zanyi tunani akai" daga nan ɗaki ta wuce abunta bayan ta ɗauki wayar ta, shi kuwa yah Sheikh ya cigaba da aikin sa ɗaya bangaren kuma yana tunanin abinda Jiddarh ta faɗa murmushi kawai yayi.


Haka suka cigaba da zama ba abinda ya sauya duk friday a gida Jiddarh ke Yuni har dare a hankali kuma ta fara sanin makwabtan ta ɗan sukan ɗan leƙo mata.

Bayan wata biyu da sukayi suka fara shirin komawa Makka saboda hutu ya ƙare gashi har sun ƙara kwana huɗu, ranar laraba suka yi ma kowa sallama dan ranar dan a daren Alhamis jirgin su zai ɗaga da misalin ƙarfe 3am sosae Jiddarh tayi kukan rabuwa da yan gidansu har a ranar har gdan  su Aunty khadeeja taje sukayi ban kwana. Suna a parlour gaba ɗayan su har da su Abdul da zasu ajiye su su koma da mota gda hakan yasa suka zo nan gdan suka zauna, sai kusan 11pm suka fita gdan bayan sun kashe komai suka rufe ko ina daga nan airport suka wuce dan a can zasu zauna har lokacin tashin jirgin su yayi su Abdul kuma suka masu bankwana suka koma gda.
  A nan suka samu room suka zauna har lokaci yayi.  2:50 suka fito daga dakin sbd an fara kiran passengers har aka kawo kan su.
    
   Toh Jiddarh safe flight.......



Alhmdllh sun isa Makka Lpy a gajiye suka isa masaukin su kamar an masu duk ga bacci dan ba wani isasshen bacci suka samu a jirgi ba, wanka Jiddarh tayi shima haka ya Sheikh  bayan sun rama sallolin dake kansu suka kwanta baccu, basu farka ba sai da aka fara kiran sallar azahar ya Sheikh ne ya fara farkawa bayan yayi wanka ya saka jallabiya ya leƙa ɗakin Jiddarh ya samu tana bacci, karasa wa yayi bakin gadon ya tada ta ta buɗe ido ta lumshe yace "lokacin sallah yayi"

Kamar zatayi kuka tace "yaj wlh bacci nake ji zanyi idan na tashi"

Yace "lokaci na tafiya ki tashi idan kinyi sai ki kwanta"

Kamar zatayi kuka ta sakkowa daga kan gadon ta shiga toilet Shi kuma ya fice daga ɗalibai zuwa masallaci.

Koda ta fito dakyar ta iya saka doguwar riga tayi sallah tana idarwa ta faɗa gado tana hamma ba jimawa bacci ya kuma ɗaukar ta. Ya Sheikh kuma bai dawo ba sai dare sbd yaje gurin Nu'aym a nan ya jima sai da ya masu takeaway Kanan ya nufi gda.

A parlour ya same ta tana zaune hannun ta rike da cup tana Shan tea, zama yayi yana faɗin "washh Allah na na barki da yunwa ko?"

Tace "a'a sannu da zuwa" yace "yauwa ɗauki plate da cups" ta miƙe ta je kitchen ta ɗauko ta dawo ya juya masu kazar daya siyo yace ta sakko dama yunwa take  ji nan suka ci sukayi nake.


Washe gari tayi shirin skl tsaf ta fito a parlour ta tarar da ya Sheikh yana shan tea ta ƙara sa dining tana turo baki dan bata yi niyar zuwa Skl ba a cewar ta akwai gajiya a jikin ta har yanzu amma fir ya sheikh yace ta shirya shi yasa take ta kumbura baki shi dai bai ce mata komai ba ya ciro wayarsa ya kira mai aikin su ya gaya mata sun dawo tace toh zata zo nan ya kashe wayar ya kalli Jiddarh yace "mu tafi" tana turo baki suka fice daga gdan.
   A Skl ɗin ma sai da ya ɗan jima a office din wani malami kana ya samu komai ya daidaita ya ya wuce office ɗinsa.


*A gurguje*

Haka rayuwa ta cigaba da tafiya sosae Jiddarh ta dage a kan karatun ta alhmdllh yanzu kam ta fara jin larabci kuma ya Sheikh yana mata zaman gidan su ya ɗan sauya zaman ma'aurata suke yanzu alhmdllh Jiddarh na yarda da ya Sheikh sai dai wata rana sai tai ta masa shagwaɓa a haka zai lallaɓata. Maganar ciki kuma har yanzu shiru hakan bai ɗaga hankalin ya Sheikh ba sai addu'a kawai yake Allah ya bashi masu tarbiyya kawai.


.........      ..........    ..........    ...........     .........
 A hankali rayuwa ke shurawa tana tafiya cike da ƙalubale da kuma nasara ciki kuwa har da gama karatun Jiddarh  na matakin secondary ganin result dinta yayi kyau ne yasa makarantar ta ɗauki nauyin cigaban karatun Jiddarh kuma Alhmdllh abinda take so suka bata wato medicine. 

Yanzu kam kusan kullum sai tayi kukan gida shekara ɗaya kenan da wata uku da sati biyu da kwana ɗaya a lissafin ta bata ga yan gdan su ba gashi yah Sheikh ba yanzu zasu koma ba sai bayan shekara uku ko huɗu idan ta tuna hakan sai tayi ta kuka yana rarrashi.

Bayan sati biyu ta fara ciwo gashi dama ba Skl take zuwa ba Sai next month zasu Fara lectures, Koda ya Sheikh ya dawo a kwance ya ganta tana rawar sanyi da sauri ya ƙara sa yana tambayar Lpy jin jikinta da zafi kuma ta kasa masa magana yasa saka shi ɗaukar ta zuwa bedroom ɗin sa a kan bed ya ajiyeta ya rufa mata blanket ya kashe AC gaba ɗaya gaba ɗaya hankalin sa ya tashi bakinta har rawa yake haƙoran ta na dukan juna Dr ya kira a waya ya gaya masa ba jimawa sai gashi.

Tashin farko result ya nuna tana ɗauke da cikin wata ɗaya da sati uku ƙara maimaita wa Abdallah yayi "ciki akan Jiddarh" sai kuma wani murmushi ya suɓce masa nan da nan wani annuri ya rufe fuskarsa bayan yayi ma Dr godiya ya rakasa har bakin mota ya dawo kusa da Jiddarh ya zauna a hankali yakai bakin sa saman gashin ta ya mata kisa kana ya maida a bakinta cikin bacci taji alaman bakin sa cikin nata hakan yasa ta buɗe idon ta da suka mata nauyi ganin sa yasa ta lumshe idon ta shima ya ɗago yana smiling . Shafa kanta yayi yana saka mata albarka har dare yana gurin zaune sallah kawai ke tada sa.

      Ya kira yan gidansu ya sanar masu sosae suka yi farin ciki da jin wannan labari mamy harda kwallarta. Tun daga wannan ranar Jiddarh ke samun tattali daga gurin Abdallah har mamaki take dan har yanzu bai sanar mata ba dan bai san ya zata ɗauki abun ba tunda daga farko ta nuna bata so.
   Idan ya tuna wannan abun sai yaji wani iri haka dai ya cigaba da kuka da ita wani lokaci har drip ake saka mata alhmdllh ta fara samun sauki sai dai tana jin chanji a jikin ta sai dai bata kawo komai ba. 
   Fuskar ta tayi fayau idon ta su kara fitowa ta rame sosae sai wani fari data ƙara.

Bayan wani lokaci ta fara zuwa Skl sosae take jin daɗin yanda lectures ɗin ke tafiya kullum a gajiye yake dawowa gida ga kasala da rashin karfi da take ji amma haka take daurewa.

Suna zaune a parlour Bayan sallah isha Abdallah ya kalleta cike da ƙauna yace "Jiddarh"  a hankali ta amsa da "na'am" dan kwana biyun nan tana mamakin yanda take fama da jikinta haka wata biyu kenan tana jin wani iri.

Kama hannun ta yayi yace "do you love me?" Kallon sa take da mamaki sai kuma tace "haba ya Abdallah what kind of question is this" yace "just answer me do you?"

Tace " I do yah Abdallah my love for you is unmeasurable" 


Yace "ohh really?" Ta rufe fuskarta tace "Yes"
Yace "since when kanwata ta fara so na ban sani ba?"
Tace "kai yah mana Ai ka San da sonka aka haifeni"
Yace "hmmm AM afraid of loosing you Jiddarh"

Da sauri ta ɗago tana kallon sa idon ta cike da tashin hankali yace "Jiddarh bakya son kyautar da Allah ya maki ban san ya zakiyi reacting ba Idan na gaya maki"

Tace "kai yaya mana plsss ka gaya min"

Yace "promise me bazaki gujeni ba"

Tace "I promise"

Yace "Jiddarh you're pregnant"

Da sauri ta ɗago tare da zaro ido tana kallon sa ya rike hanunta yace "calm yourself plsss, dama nasan ba so na kike ba shi yasa bakya sun haɗa jini da Ni ba komai zan kai a cire maki kinji karki ɗaga hankalin ki plsss"

Da damuwa a fuskar ta tace "yah" ya kalleta tace "Ina son ka ya kuma ina son Abunda kake so sai dai kuma..."

Yace "sai dai me?"

"Yah karatu na fah"

Yace "Jiddarh ba cikin ki William not affect your studies I promise you that"

Tace "yah da gaske?"

Yace "ehh mana"
Ya kwantar da ita a ƙirjinsa yana rarrashi har ta saki.


Haka suka cigaba da kula da cikin jikin Jiddarh sosae take samun tattali har agun su ummee dake Nigeria suna kiran waya akai akai dan jin lpyr ta.

A har cikin ya shiga watan haihuwa  gashi exams suke yi sosae take wahala yanzu kullum cikin complain din ciwon baya dana ƙafa take a haka har suka gama exams din. Saboda kiran da ummee ke masa akan ya daure ya maida Jiddarh ta haihu gda idan da hali.
  Ganin yana da sarari ya saka shi fara shirya masu tafiya ranar talata suka isa garin Kano direct gdan ummee aka wuce da ita sosae ta wahala sbd gajiya hakan yasa cikin dare naƙuda taso mata dama ummee na tare da ita.

Da sauri ummee ta fita zuwa ɗakin Abdallah daya ki tafiya can gdan sa yace a nan zai kwana buga masa kofa tayi dama ba bacci yake ba hakan yasa taso da sauri jin Muryar ummee na kiran sa, bata tsaya masa bayani ba ta nufi cikin gda hakan yasaka shi bin bayanta da sauri suka shiga ɗakunan tare Jiddarh na nan kwance tana kwalla da sauri ya sunkuce ta ummee ta shiga ɗakik Abii ta taso shi a tare suka fito Abii ya buɗe motar ya Sheikh ya saka Jiddarh a ciki suka nufi asibiti.

Da sauri aka karɓe ta sai labour room nan aka shiga taimaka mata ya Sheikh sai kawo yake a harabar asibitin yama kasa zama guri ɗaya. Kusan awa ɗaya aka samu ta haifo yarta mace katuwa gaba ɗaya ta wahala ta galabaita Sai da aka kimtsa su ne aka fito da babu cikin wani towel Sai a lokacin ummee ta tuna ashe basu ɗauko komai ba Abii ya ƙarɓi jaririyar nurse din ta koma sai a lokacin Abdallah yaji wata mutuwa na shigar sa sai dai daya tuna Jiddarh na ciki hankalin sa ya tashi da sauri ya ƙara sa bakin ƙofar ɗakin sai ga Nurses din da Dr sun fito suna tura gadon da Jiddarh ke kwance tana baccin wahala sa a lokacin wani murmushi ya suɓce masa yana ma Alkah godiya ga wannan ni'imar tasa.

Jaririya na hannun ummee ya kasa karasa wa sbd kunya sai kawai yabi bayan Nurses dinzuwa room din da aka kwantar da ita. Zama yayi bakin gadon ya kama hannun ta ɗaya ya sumbata Yana saka mata albarka suna a haka ummee suka shigo ya miƙa daga gurin daya ke yana sosa kansa Abii yayi murmushi yace "Abdullahi an zama babban mutum Allah ya raya maka" a zuciyar sa ya amsa da Ameen yana murmushi. Ummee tace "toh ko zaku koma gida ne gashi asuba ma ya kusa idan yaso in gari yayi haske sai ku ɗakko abinda za'a buƙata.

Abdallah yay mitsi mitsi da ido yana kallon ummee ganin kamar zai kawo gardama yasa tace "kuje Abdallah karka damu"  badan yaso ba suka tafi gida shi da Abii sai dai bai kwanta ba yashi nuna ma Allah godiyar sa ta hanyar bauta masa.

Washe gari da karfe shida ya Sheikh ya isa asibiti bayan ya shiga ɗakunan ummee ya ɗauki duk abinda ta gaya masa, a lokacin Jiddarh ta farka da sauri ya karasa cikin ɗakin yana ajiye kayan hannun sa ya ƙara sa bakin gadon Jiddarh ta sakar masa lallausan murmushi a wahalce ya mayar mata tare da rungume ta a bankuna furta "Allah ya maki albarka" ta lumshe ido tana fadin "Ameen" gyaran Muryar da ummee tayi ne ya saki shi ɗagowa da sauri yana sinne kai Jiddarh kuma ta kwanta tare da juya masu baya tana murmushi.
  Dama ummee ta tara kayan babu tun ranar da aka faɗa mata Jiddarh ta samu ciki, kayan sanyi ta sakama jaririyar. Da misalin 11 akyi discharging din su suka haɗa kayan su sai gda.
Dakyar mamy ta iya ɗaukar jaririyar wai kunya abun dariya ma ya bama Abdallah.
       Jaririya da mahaifiyar ta sosae suke samun kulawa ta musamman ya Sheikh yayi iya kar ƙoƙarin sa gurin kayan haihuwa akwati set ɗaya ya haɗa masu.
  Ranar suna yarinya taci suna Nana Aisha. 
  
   Toh Allah ya raya mana Nana Shatou...🥰



Faɗa maku samun kulawar da suke samu ɓata lokaci ne har aka shafe wata uku nan suka fara shirin komawa Makka sbd makaranta da kuma aikin Abdallah nan suka naɗe suka koma cike da kewar gida.

Sosae Nana ke samun kulawa gurin iyayen ta duk da Jiddarh na zuwa Skl hakan bai hanata kula da gdan ta ba sai yanzu ne wani hankali ke kara shigar ta sai yanzu take sanin daɗin aure sai kuma yanzu take nadamar abinda tayi niyar aikatawa na son rabuwa da Abdallah Ashe shiɗin Alkhairi ne a gare ta.
  Inatee kamar yanda suke kiran Nna Aisha Nada sheraka daya da wata biyar aka yaye ta ana aka nema mata mai raino ta cigaba yayin da Jiddarh kuma ke zuwa makaranta.


   Bayan shekara 5


"Ummun intee kiyi sauri fa kar girnan na ya tashi mu tafi mu barki"

  Daga cikin ɗaki tace "sorry sweetheart wlh intee ce taƙi ta tsaya na saka mata takalmin nan" fitowa tayi hannun ta rike da na wata cute little girl fara mai gashi kallo ɗaya zaka mata kasan hutu ya zauna a tare da ita da gudu ta ƙara sa gurin ya Sheikh tace "Abba Ni fa bana don zuwa"

Yace "meyasa bakya son ganin Granny ne?"

Tace "noo Abba ai kace baza mu dawo nan ba"

Yace "Yes intee we're going back to our country"

Tace" Abba skl Dina fa"

Yace "don't.worry angel zan sama maki wata a Abuja tunda can zamu koma yanzu"

Tace "really"
Yace "Yes dear" 

Kama hannunta  yayi ya kalli Jiddarh dake tsaye yace "Madam muje ko"
Sai ga hawaye tace "Nikam Sai Naji ba daɗi kamar kar mu tafi"

Dariya yayi yace "kin tuna lokacin da muka zo kina kuka?"

Dariya tayi tace" toh ai yanzu na saba ba"

Yace "Hmm let go we're getting late"



Malam Aminu Kano international airport anan jirgin su yayi landing intee Sai kallo airport din take tana smiling Abdallah days ɗauke ta yace "how do you feel"

Shakar iska tayi tana lumshe ido tace "far better"
Yayi dariya suka ƙara so sai a lokacin ya kula da Abdul Malik daya zo ɗaukar sa dan Abdul majid kam yayi aure last year Basu samu sun zo ba. Kallon sa intee tayi kana ta kalli Abbanta tace "Abba wannan shine Uncle?"
Yace "ehh" sai ta rungume sa tana dariya ɗaukar ta yayi yace "my angel has grown up o"
Jiddarh tace "su ya Abdul Malik an kai ga ƴaƴa"
Dariya sukayi gaba ɗaya suka kwasa sai gida.
Bayan ya ajiye su ya wuce gida shima .


Wasje gari suka shirya sai gidan su ummee sosae sukayi farin cikin ganin su intee sai surutu take zubawa kamar Radio bayan Abii ya dawo Abdallah ya masa baya Ni akan komawar da zasu yi Abuja cikin satin nan dan an fara neman sa dama makarantar Nile University ne suka nema ya dawo nan ƙasar sa zasu ɗauke aiki ɗaya zauna ƙasar wasu yana masu bauta sosae  yaji daɗin hakan dama ya gani da zaman Makka ga Jiddarh ma ta samu aiki a general Hospital addu'a Abii ya masu suka shiga gidan mamy sai dare suka koma gida. 
   Gaba ɗaya abu ya haɗe masu ba yanda suka iya dole suka shirya komawa Abuja a satin.


Bayan wani lokaci



"Washhhhh Abban intee na gaji wlh"

Yace "sannu  ya patients din naki" 

Tace "alhmdllh ya Yan matan ka" ta faɗa tana cire labcaot din da ke jikinta yace "suna Lpy yau ma na samar miki kishiya"

Haɗe fuska tayi fuuuj zata wuce sai ga intee da kaninta sun fito.daga bedroom din su da gudu Ammar ya ƙara sa gurin Jiddarh yana "oyoyo Ummu " tace "how are you"
Yace "fine" tace "have you eaten?"
Yace "Ni we just came back from Skl"
Tace "ok then go and eat lemme fresh up and come back" ta kwalawa Mai aikin ta kira tazo ta tafi dasu intee yan mata ƴan primary.

Ganin yaran sun tafi ya saka ya Sheikh mike wa ya shiga ɗakin Jiddarh har ta cire kaya ta ɗauka towel ya rungume ta ta baya yace "Are You angry with me"

Turo baki tayi tace "why should I  am just jealous"

Dariya yayi ya kama hannun ta suka shiga toilet cike da farin ciki mara misaltawa a fuskar su daga cikin ɗaki kana jin yanda suke dariya suna wasa da ruwa dan a buɗe suka bar kofar sanin  cewa yaran baza su shigo ba amma dai sai naja masu ƙofar na rufe ina masu fatan gamawa da duniya Lpy..........✍🏻


Alhamdulillah😃

A nan na kawo karshen wannan littafin nawa kuskuren dake ciki Allah ya yafe min yasa ku amfani da abinda na rubuta ina mai godiya sosae ga ƙaunar da kuke nuna min Nima ina son ku saboda Allah ina godiya sosae da sosae.

Ayshatu M Musa (Neeshar.jay) ina matukar godiya ban san yanda zan kwatanta maki ba Allah ya saka da Alkhairi ya bar ƙauna son so fisabilillah❤️😍


Bye😢🤧



Khairaty✍🏻


