[9/29, 12:47 PM] Aysha Galadima: *'YAR SHUGABA👑* _page_ *1.* _Na_ *Rahma Kabir*✍🏾 Mototaci ne guda uku suke tafe bisa hanya aguje, dukansu gilas d'in motocin masu duhu ne, mota ta farko dake gaba bodyguard ne a ciki. Sai na tsakiya motar d'auke yake da tsadaddun 'yan mata su uku wanda ba zasu wuce shekaru Ashirin da biyu (22yrs) ba a duniya. *'Yar Shugaban k'asa ce* Queen Basma, ta hakimce a seat d'in baya ita kad'ai, sai Meena 'yar Governor Kaduna ce ita ke driving, sai Leema 'yar Sarkin Kano wacce take gefen Meena. K'aran wak'ar Music na Larabawa ke tashi a motan, dukkan su suna bin wak'ar tamkar sune suka rerata, sunayi suna rawa da jinsu da kad'a kai, kana ganin su kaga 'ya'yan gata, cike suke da farin ciki fal da nishad'i, domin ba suda wata damuwa ko matsala a rayuwansu. Motan baya itama na bodyguard ne, suke marawa motan Queen baya. Wani Matashin Saurayi wanda bai wuce shekara Talatin ba (30yrs), yake tafiya cikin sauri domin ya amso wa Ummansa nik'an masara da k'anwarsa Khadija ta kai ta aje, saboda zata wuce tallan kwai, hankalinsa yayi nisa sosai cikin tunani, baisan yahau kan titi ba. Meena ce taja mugun burki, ji kake k'iiiii kad'an ya rage ta buge shi, Aryan tsayawa yayi cak ya runtse ido yana fad'in *Innalillahi wa inna ilaihir rajuun* jira yake motan ta bigeshi domin ya riga ya sadak'ar motan zata kad'eshi, Cikin b'acin rai Queen Basma, Leema, Meena duk suka fito a motan, haka bodyguard suka yi parking akan hanya suka fito rik'e da bindigogi, cikin k'ank'anin lokaci suka had'a gosilo, mutane suka fara taruwa, ganin bindiga ne yasa kowa ya kama kansa, Queen Basma ta k'arasa kusa da Aryan bodyguard suka take mata baya, tsadadden k'amshin turarenta ne ya dawo da hankalin Aryan jikinsa, domin ji yayi wani k'amshi na ratsashi, bud'e ido yayi a hankali yayi tozali da kyakkyawar fuskan Queen wanda saida gabansa ya fad'i, nan take tsoro ya ziyarce shi, kallon k'asa da sama Queen Basma ta bisa dashi cike da jin haushinsa, kyamansa taji saboda wani irin warin zufa dake tashi a jikinsa, tattaro miyon bakinta tayi ta tofa masa a jikinsa tare da toshe hancinta da hankacif, juyawa tayi ta kalli d'aya daga cikin bodyguard d'inta, cikin sauri ya k'araso, Aryan baiyi aune ba bodyguard d'in ya kifa masa kyakkyawan mari guda biyu, Leema ce ta k'araso cikin isa tace "Hee, Marin ma kad'ai ya ishe shi" sai ta juya tana kallonsu Meena tana murmushi, ta kuma cewa "babies mu wuce kar mu b'atawa kanmu lokaci akan wannan mahaukacin, kunsan duk muna da abinyi a gabanmu". Dakyar Aryan yaja k'afansa zuwa gefen hanya, zuciyansa cike da k'unci, su kuma su Meena suka shiga mota suka wuce. Tsananin damuwa ne Aryan ya tsinci kansa a ciki, sai ya fara zancen zuci yace, "shi dai talaka kullun shi wulak'antacce ne a idon jama'a, Allah kai ka haliccemu kayimu ma banbantan jinsi, kaine mai girma, ka saka mini da kyakkyawan sakayya" wani guntun hawayen ya sauka a kuncin sa, ba abinda yake k'ara masa bak'in ciki sai irin yanda Queen Basma ta tofa masa miyau, murmushi yayi na k'arfin hali ya girgiza kai a fili ya furta "Rayuwa ce" sai ya wuce inda zashi. Sai gabda Magrib ya kaiwa Umma nik'an masaran, ya sameta ta rafka tagumi, sallaman da yayi shine ya dawo da ita daga duniyar tunani data fad'a, nisawa tayi ta amsa tace "Aryan ya akayi ka dad'e ga ruwan sanwan ya tausa harya fara k'onewa" zama yayi a tabarma dake tsakar gidan yace "Umma kiyi hakuri naje basu nik'a ba saida na jira suka nik'a shiyasa na dad'e" Umma tace "Allah sarki, ba damuwa tunda mun samu nik'an yanzu zan gama insha Allah" Nan ya zauna yana mata hira tana aikinta har aka kira sallan Magrib ya wuce masallaci. Ta b'angaren su Queen Basma kuwa gidan hutawanta suka wuce, musamma tasa aka gina mata shi dan hutuwa. K'aton gida ne babban flat wanda ya k'unci kayan alatu a ciki, ginin zamani aka yi shi a tsakiyar babban fili, filin gidan za a iya pakin mota goma, sai daga can gefe ruffa ne mai d'auke da kujeru da table a tsakiya, an tanaji wannan wurin dan hutuwa, wurin zagaye yake da shukokin furenni masu fidda k'amshi mai dad'i, sai kuma daga bayan gidan katon swimming pool ne wanda aka sanya masa ruwa mai kyau da tsafta, in ka kalli ruwan har kashe ido yake dan haske, lokaci-lokaci ake jenye ruwan ana sauya wani. Daga gaban swimming pool d'in akwai wata yar k'aramar k'ofa wanda sai sadaka da cikin garden(lanbu), ya k'unci bishiyoyi na kayan marmari (fruits) da kuma kujeru na hutu dan shawakatawa, wurin ya had'u matuk'a. Suna shiga cikin gidan suka shiga babban falo, basu zauna ba sai ko wacce ta nufi d'akinta kamar yanda suka saba, falo ne mai d'auke da d'akuna guda biyar ko wanne da ban d'aki a ciki (toilet), d'akin faro shine na Leema wanda aka k'awata shi da kayan Sarauta a matsayinta na gimbiyar 'yar Sarkin Kano. D'aki na biyu shine na Queen Basma wanda aka kawatashi da kayan more rayuwa, an kashe mak'udan kud'i sosai, a matsayinta na 'yar shugaban k'asa. Sai d'aki na uku na Meena ce, wanda shima aka k'awata shi da dukiya, amma bai kai na Queen ba, a matsayinta na 'yar gomna. D'aki na hud'u kuma an sanya masa kaya dai-dai misali, sun bar d'akin na masaukin bak'insu. Sai kuma d'aki na biyar, tsadaddun kayan motsa jiki ne a ciki, wanda ko wani lokaci sukan mota jikinsu a ciki. Sai katon kitchen dake gefe yaji kayan amfani. Wannan gidan musamnan Basma tasa mahaifinta president ya gina mata shi, bayan dawowarta daga k'asar England karatu, kasan tuwar sunyi karatu tare da Leema da Meena yasa ta sanya ko wacce aka shirya mata d'akinta dan soboda tsananin shak'uwar su kullun suna tare. Queen ce ta fito daga ita sai best da pant ta d'aura towel a k'ugunta, hanyar k'ofar baya tabi ta bud'e, direct wurin swimming pool ta wuce, tana isa ta cire towel d'in ta fad'a cikin ruwan ta soma iyo, suma su Meena haka suka fito cikin shigar da Basma tayi, cikin ruwan suka shiga suma suka fara wanka, ko wacce na abinda ya shafeta. Sun kai misalin Rabin awa a ciki kana Meena ta fita a ruwan, ta zauna a kujeran hutawa dake bakin swimming pool d'in, wani jaka naga ta d'auka ta zage zip d'insa, sigari ta ciro tare da leta, sai ta kunna mata wuta ta hure, kana ta kwanta a bayanta tana zuk'ar sigarin tare da fidda hayak'i sosai ta hanci da baki. Leema ma fita tayi ta zauna a kujeran hutuwa nesa da Meena kad'an, wayarta ta d'auka ta fara chart da abokin harkanta, murmushi take zubawa ita kad'ai da alama tana jin dad'in hiran. Queen Basma tana cikin ruwan ta tsaya da wankan cikin fad'a tace ma Meena "Malama kinsan na hanaki wannan shirman muddun ina wuri ko, ya zaki kunna sigari ya rik'a cutar damu, kuma kinsan bana son warinta" cike da d'aure fuska Meena tace "To maida damuwarki zan kashe shikenan?" sai ta kashe ta jefar, bud'e jakanta ta kuma yi ta d'auko kwalban syrup tace cikin gatsali, "in kin hanani shan sigarin to ba zaki hanani shan wannan ba, don ita ba hayak'i". Basma take ta fito cikin ruwan ta d'auki towel d'inta tare da gallawa Meena harara tace " kanki kike cutarwa" taja tsaki ta wuce cikin falo. Meena itama ta bita da harara bata ce komai ba, Leema ta kalleta ta kwashe da dariya tace "wow ina son fad'anki da Basma, domin kullun sai kinyi abinda bata so a wurin nan, ita kuma kullun sai ta tanka miki". Tsaki Meena taja tace "Ke kuma 'yar sa ido, to ya isheki, kije ki cigaba da iskancin ki, gwara ni bana bin maza" ran Leema ne ya sosu, ta d'aure fuska, nan take sarauta ya motsa mata, tashi tayi tabi bayan Basma. Meena ta bita da dariya tace "na dai rama". Leema ta samu Basma sanye cikin riga iya cinya ya kamata, ta sanya wakar music sai tikar rawa takeyi tana mota duk sassan jikinta, tsaki Leema tayi tace "zaki damu mutane da wannan wak'ok'in shirme" cikin fad'a Basma tace "ina ruwanki, naga kowa yanayin abinda ya dameshi ne, ki shiga d'akinki kiyi chart da samarinki ban takuraki ba, nima ki barni inyi rawata", hararanta Leema tayi bata tanka mata ba, Meena ce ta shigo falon idunanunta sunyi jawur saboda ta shawu, joining d'in Basma tayi suka cigaba da rawa ba tare da ta canza shigar dake jikinta ba. Saida aka kira sallan magrib kana Basma ta kashe wak'ar, duk suka wuce d'aki, wanka ta fara yi tare da d'auro alwala, jallabiya ta sanya wacce take sallah dashi ta sanya hijab ta tayar da sallah, bayan ta idar tayi duk azkar da ake karantawa da yamma, ta d'aura da Addu'a, Al'Qur'ani ta shiga karantawa cikin muryanta mai zak'i, tana zaune a haka har aka kira sallan Isha'i, sai ta rufe Al'Qur'ani ta gabatar da Sallan Isha'i. Bayan ta idar ta mik'e ta sauya shiga cikin doguwar riga har k'asa yar kanti, ta kamata sosai tun daga samanta har k'ugu, daga gwiwa ya bud'e kad'an har k'asa an masa tsagu. Ta busar da gashinta da hand dryer, ta sanya mai ta kamashi da ribon a tsakiyan kai, ta bar jelan gashin yana reto a bayanta, ta d'auko hular mulki na Queen ta aza a saman gashinta, turare ta fesa masu dad'in k'amshi, ta sanya siririn sark'an goal a wuyanta tare da d'an kunne, a gogon hannu ta sanya da zobe, tayi kyau sosai, sai ta sanya takalmi dogo mai igiya, haka ta d'aureshi har k'auri, saida ta k'arewa kanta kallo a madubi sosai kana tayi wani murmushi wanda yake k'ara fidda kyanta, sai ta nufi falo cike da takun k'asaita. Kallon-kallon su Meena da Leema suka yi saboda irin had'uwar da Basma tayi, sai suka ga tasu wankan ba komai bane saboda Queen ta lashe duka wankansu. D'aukarta photo suka farayi kala-kala, suna mata kirayi tare da kurantata, a kullun Basma in dai zasu fita zuwa club irin wannan shigan takeyi, amma fa ko wani shiga da kalarsa domin sai afi watanni bata maimaita wani shigan da tayi ba, ko wace rigan daban. Bayan sun gama d'aukarta photo, nan suka had'u suka yita selfee, suma su Meena sunyi kyau ba laifi, shigan dogayen riguna sukayi tare da barin sumarsu ya zuba a bayan su, kansu ba d'ankwali, dogayen cover shoe suka sanya sunyi kyau sosai amma fa basu kai Basma ba. Fita sukayi suka shiga mota dukansu a seat d'in baya suka zauna suka sanya Basma a tsakiya, driver ya jasu, tare da bodyguard suna gaba, da kuma masu rufa musu baya sai club. Aryan ya dawo daga sallan Isha'i, ya samu su Umma a tsakar gida kan tabarma suna cin abinci, shima zama yayi a shinfid'ar da yake mai girma ne, Khadija ta mik'e ta isa kitchen ta kawo masa abincinsa, bud'ewa yayi tare da cewa "nagode Dija", sun kammla cin abinci dukansu sai Aryan ya kai dubansa inda Dija ta zauna yace "Khadija meyasa in kika fita tallan kwai bakya dawowa gida da wuri" marai raicewa tayi tace "Yaya Aryan wallahi ba kasuwa ne shiyasa nace bari na k'ara lokaci ko zan saida duka, ka gafa tun shekaran jiya Umma ta dafa min amma har yau bai k'are ba" shuru yayi na 'yan dak'ik'a kana yace "ai Dija mutum baya wuce rabonsa, ni dai dan Allah ki rik'a dawowa da wuri kuma duk inda kike ki tuna matsayinki da rik'e mutuncinki" "tom Yaya Aryan insha Allah zan kiyaye" Umma na jinsu tace "Aryan gwara ka rik'a mata fad'a, d'azu ma sai bayan magriba ta dawo" yace "ai Umma wallahi ni da ina da hali da Dija ta daina tallan nan sam bana sonta" Umma tace "to Aryan ya zamuyi, haka Allah ya rubuta mana, ya zancen rumfanka an gyara kuwa?" gyara zama yayi yace "Umma ba kud'in gyara shiyasa na koma gefe ina aikina inna samu kud'in zan gyara, gashi yanzu cinikin sai Addu'a tunda Lawal ya dawo kusa dani ya kwashemin customers d'ina" Umma tace "karka damu insha Allah in kud'in kwai ya taru zan baka ka gyara runfar, batun kuma Lawal ka rabu dashi kowa rabonsa zai ci, muyi ta Addu'a Allah ya kawo mana karshen wannan hali da muke ciki". Duk suna amsa da Ameen kana suka cigaba da hiran duniya. *Muje zuwa...*🤔 *_Rahma Ce_* (Sirrin 'ya mace group) WhatsApp. [9/29, 12:47 PM] Aysha Galadima: *'YAR SHUGABA*👑 _page_ *2.* _Na_ _*Rahma Kabir*_✍🏾 Su Basma suna isa club, suka wuce cikin hol d'in, mutane ne sosai a ciki maza da mata, daka gansu kaga 'ya'yan manya, tsautsayi ne zai kai d'an talaka wurin, kid'a da sauti ke tashi kowa na zaune, kamar yanda suka saba zuwa suna da nasu wurin zama na musamman, duk suka zauna, aka cike musu wurin da kayan motsa baki, wani kyakkyawan Guy ne yazo kusa dasu suka gaisa Amma banda Basma domin bata shiga harkan Maza, Leema ce ta mik'e saurayin mai suna Jalal ya rik'ota ta kugunta suka wuce tare da hiransu na masoya, fita sukayi a wurin suka wuce cikin hotel da club d'in ke ciki. D'akinsa ya bud'e suka shiga, kamar suna jirace da juna suka fara kaiwa juna sak'onni, nan da nan suka rikice suka lula duniyar shashanci, Allah ya shirya Ameen, nan na fito na basu guri. Ita kuma Meena ta mik'e ta wuce group d'insu na mashaya, wurin mata ne da maza a had'e, suna ganinta suka fara ihu, wuri suka bata ta zauna ta fara aikawa da syrup. Queen itama Abokan rawanta suka matso kusa da ita nan suka d'unguma zuwa saman dandamali, nan fa kowa hankalinsa ya tashi ganin Basma ta hau, hayaniya ya k'aru suka fara ihu domin sunyi missing ganin rawan Basma, aka d'aura mata best wak'arta na music d'in labarawa, Queen Basma ta soma rawa mai ban mamaki tamkar ba jikinta take k'aryawa ba, sai wuri ya kuma hautsibewa da ihu, dama abinda Basma keso kenan, mutane suka fara mata yayyafin kud'i masu taya ta rawa suka k'ara dagewa farin ciki ne ya rufe su domin sunsan yau zasu kwashi kud'i. Dan in sun gama Basma cewa take a basu kud'in su raba. Sai da taci rawa mai isarta kana ta sauka ta samu guri ta zauna tana maida numfashi, sauran 'yan rawar suma suka sauka, aka kwashe kud'in su tas aka basu, farin ciki ya gama rufesu domin yau sun samu kud'i sosai, suna alfahari da Queen data zama star d'insu. Sai misalin k'arfe ukun dare suka dawo gida, ko wacce ta nufi d'aki ta kwanta, nima saina tayasu rufe k'ofa nace saida safe. *Washe gari* Da misalin k'arfe takwas na safe Aryan yayiwa Umma sallama ya wuce kasuwa kamar kullun, yana isa rumfansa hawaye ya ciko fal idonta, girgiza kai yayi saiya bud'e k'aton buhu da yake kasa kayan miya, haka ya karkasa tumatur, tarugu, sai tattasai, samun wuri yayi ya zauna daga inda rufin shagonsa ya kifa ya rab'e, sai ya rafka tagumi ya fara tuno rayuwansu. *ASALIN ARYAN? "* Sunan mahaifinsu Aliyu, Asalinsu fulanin Gombe ne, mahaifinsa ya rasa Iyayensa tun yana k'arami, a wurin k'anin Baffansa ya tashi Malam Mu'azu, ya had'ashi da yaransa su biyu Aisha da Ibrahim ya rik'e. Matarsa Inna Amina suna kiranta da Inna Lami ta rik'e Aliyu Amana tamkar ita ta haifeshi, duk inda Aliyu yake Khalil na wurin, sun tsaku sosai makaranta tare suke zuwa, ga k'anwarsu Aisha suna ji da ita. Wata rana Inna Lami ta aiki Khalil kasuwa shuru-shuru bai dawo ba har aka d'auki tsawon lokaci, abu kamar wasa Khalil ya b'ace anyi niman duniya amma ba amo ba labari, Malam Mu'azu da Inna Lami sun shiga tsananin damuwa, tun ana kwana d'aya da b'atan Khalil har ya d'auki tsawon wata ba'a ganshi ba balle aji labarinsa. Haka su Inna suka runguma Aliyu da Aisha suka barwa Allah lamarin sa da Addu'an Allah ya bayyana musu Khalil ko a mace ko a raye. Aliyu kuwa har rashin lafiya yayi saboda rashin d'an uwansa. *Bayan shekaru* Aliyu ya gama diploman sa a b'angaren kasuwanci, yana da shekaru 26. Aisha kuma tana da shekara sha takwas Malam Mu'az ya had'a Aliyu da Aisha auren zumunci, basu damu ba dama suna son junansu saboda akwai shakuwa mai k'arfi a tsakaninsu, Ana d'aura musu Aure sai suka tare a wani gefe daga cikin gidansu. Bayan wata biyar da aurensu wani abokin Malam Mu'azu yazo Gombe mai suna Alhaji Sani, Malam yayi masa kyakkyawan tarba, d'aya tashi tafiya ya rok'i Malam akan ya bashi Aliyu ya tafi dashi Abuja tunda yayi karatu, ya d'auke shi aiki a companyn sa, da farko Malam bai yarda ba, amma daga baya saiya amince bisa sharad'in sai dai Aliyu ya tafi da matarsa, Alhaji Sani ya amince, cikin kwana biyu suka shirya sai garin Abuja. Alhaji Sani mutum ne mai kirki, ya siyawa Aliyu k'aramin gida mai d'aki ciki uku da kicin da ban d'aki, sai kuma filin tsakar gida k'arami madaidaici a unguwar suleja, ya kuma siyan masa mashin da zai rik'a zuwa aiki. Farin cikin wurin Aisha da Aliyu baya misaltuwa, Aliyu ya fara aiki a company Alhaji Sani a matsayin Massinger. Sukan ziyarci Gombe duk bayan watanni biyu ko uku tare da alkhairai masu yawa. *Bayan wani lokaci* Aisha ta haifo d'anta Namiji suka sanya masa suna Aryan, Aryan ya tashi cikin kulawa da gata na iyaye, sun sanya shi makaranta mai kyau da tsada, Aryan yaro ne mai hazak'a b'angaren boko da islamiya, ga kuma natsuwa, gashi da kyau sosai, da ka ganshi gaka Asalin bafula tani, hakan yasa yayi farin jini sosai a makarantansu. Aryan yana da shekara takwas Aisha wanda Aryan yake kiranta da Umma ta haifo 'Yarta kyakkyawa khajida, tun tana k'arama Aryan yake matukar son k'anwarsa duk abinda ya samu tofa na Khadija ce daya sanya mata suna Deeja. Arya ya kammala secondary school Khadija na primary 5, mahaifinsa ya nima masa makaranta a kadpoly Kaduna ya tafi ya fara karatun computer science, cikin ikon Allah da mai da hankali ya kammala, shekarunsa uku a makaranta ya dawo da cirtificate d'insa na diploma, ya koma Abuja lokacin Deeja ta shiga jss3 a secondary. Wata rana Aliyu ya wayi gari da matsanancin ciwon ciki Abu kamar wasa, zuwa yamma yace ga garinku, wannan family sun shiga tashin hankali sosai da rashin Mahaifinsu, karma ace maka Aryan da yayi mugun sabo da mahaifinsa, mutanan Gombe suka zo saida akayi arba'in sannan Inna ta tafi, sun so su Umma su tattara su koma Gombe amma Alhaji Sani yace su barsu anan, yana so Aryan ya cigaba da aikin Mahaifinsa, haka suka amince badan ransu yaso ba. Aryan ya fara zuwa aiki a company Alhaji Sani, tunda ya fara zuwa ya fara samun matsaloli, wasu daga wurin aikin suka sanya masa ido saboda sunga yanda Alhaji sani ke nan-nan dashi. Daga karshe suka yi masa sharri bayan shekaransa guda da fara aiki Alhaji Sani ya koreshi. Aryan yayi kuka sosai rayuwa tayi musu k'unci abinda za suci wuya yake musu cikin k'ank'anin lokaci duk suka rame suka lalace, Khadija ta daina zuwa makaranta domin ba kud'in school fees, Allah yasa ba haya suke ba domin da gidan su kawai suka tsira. Dole yasa Aryan ya fara bige-bige, Umma kuma ta soma wankau a gida da haka ne suke samun abincin da zasuci, Aryan yayi yawon niman aiki Amma bai samu ba, wani wurin inya je sai suce mai Digree suke nima, ba suda kud'in da zai koma karatu dole yasa ya soma dako a kasuwa. Allah ya taimakeshi ya samu baro yana amfani dashi wajen dakon. Da wannan kud'in baron ne ya samu ya kafa runfa a cikin kasuwa yana biyan kud'in hayan wurin, ya fara saida kayan miya, abu kamar wasa sai sana'ar ya amshe shi, da haka Deeja ta koma makaranta ya cigaba da biya mata school fees, Umma kuma ta daina wankau saboda sanyi ya fara mata illa, sai ta samu jari ta fara dafawa Deeja kwai tana saidawa, in ta dawo makarantan boko saita fita tallan kwai, da yake duk sunyi saukar Al'Qur'ani, boko kawai take zuwa. A daddafe Khadija ta kammala secondary school, tunda ta gama Aryan yaso nima mata school of health ta cigaba amma ba kud'i, burin Khadija ta zama babban likitan mata amma ba hali. Samari sosai take da su amma Yaya Aryan ya hanata hira, saida Umma ta sanya baki ya fara barinta tana fitan ma wani malaminsu na ialamiyan da ta gama mai suna Musa. Soyayya sosai suke yi, sun fara zancen Aure Iyayen Musa suka hana shi aurenta saboda akwai yarinyar da suka zab'an masa, wannan dalilin ne ya kawo k'arshen soyayyan Dija da Musa. Tun daga nan Dija ta tsani soyayya burinta yanzu bai wuce ta samu ta cigaba da karatu. Aryan yazame mata uba duk abinda 'ya budurwa take buk'ata Aryan ya tsare mata shi, ta maida hankali sosai wajen tallan kwai. Aryan runfansa ya rufta tun daga wannan ranar komai ya dagule masa cinikinsa yaja baya, wata biyu kenan da rushewan rumfansa. Ana cikin hakane mak'ocinsu Malam Lawal yaje ya kafa tashi rumfan kusa dana Aryan da hakane Malam Lawal ya kwashewa Aryan customers, ya zamana Aryan saiya fita kasuwa ya dawo gida baiyi cinikin kirki ba. Aryan saurayi ne matashi mai cikar kamala, yanada tsayi amma dai-dai misali, yanada kauri, kuma fatarsa mai haske ne, yanada dogon hanci da dara-daran ido, bakinsa dai-dai da fuskansa, Namiji ne mai cike da kwarjini ga faffad'an k'irji, suman kansa luf-luf yake tamkar d'an India, in ya d'auki lokaci baiyi aski ba gashinta yana taruwa wanda zai iya kamawa da ribom, gashi da santsi sosai. Hakane kesa kullun Kansa da Hula baya son sumansa na fitowa, ba kowa yasan sumarsa haka yake ba saboda baya fita ba hula, sai dai in yaje masallaci wurin yin Alwala sai mutane su gani. 'yan Matan unguwansu Aryan sun rud'e sosai akansa, suna haukan sonsa, shi kuma bai san ma suna yi ba. Shekarunsa Talatin (30yrs) a duniya har yanzu baida budurwa, baima kallon mata balle ma su birgeshi, shiyasa ranar da sukayi ido hud'u da Basma gabansa ya fad'i domin shi Sam baya kallon mata, amma fuskan Basma ya kasa b'ace masa a ido saboda wulak'ancin da tayi masa. A yanzu kullun burinsa bai wuce ya samu kud'i ya farantawa Ummansa rai da k'anwarsa abin sonsa. *Cigaban Labari...* Malam lawal ne ya kwad'a ma Aryan sallama, firgigit ya farka daga dogon tunanin da ya shiga, cikin sark'ewan murya yace "Naam Malam Lawal ashe harka iso" cikin dariya Malam Lawal yace "tun d'azu nazo, nayi maka magana naga gaba d'aya hankalinka ya yi nisa ince dai lafiya?" murmushi yayi yace "lafiya lau Malam Lawal, ya kwanan iyalin?" "Lafiya lau, d'azun nan naga Deeja zata aiken Ummanku, sai na tambayeta ko ka wuce? sai tace aika fita da wuri" "eh wallahi na fito da wuri, da yake na biya wajen saro kayan miya" "Ok, Allah ya bamu sa'a da kasuwa mai Albarka" "Ameen Malam Lawal". Nan suka cigaba da tattaunawa akan maganar kasuwan. B'angaren su Queen Basma sai goma na safe suka farka, ko wacce ta fito cikin shigan mu ta Hausawa, Leema ta sanya leshi riga da zani rafa, Meena ta sanya shadda doguwar Riga, Basma kuma ta sanya atamfa super, d'inkin Riga da siket, ba k'aramin kyau sukayi ba, ko wacce da gyale a kanta, hakan da suka yi sai suka bani mamaki, gaba d'aya kamar ba sune jiya suka yi shigan dogayen riga sai kace ba 'ya'yan Musulmai ba, suka tafi zuwa club. Queen ce tace "Ni zan tafi gida domin a yanzu haka ana jirana domin yin breakfast, in kuma za kuje tom sai mu tafi tare" Leema ta yatsine fuska tace "Ni bazani ba saboda Momynki akwai takura gwara-gwara Ammi, dan haka hotel d'in da muka sauka ni da Meena zan wuce" Meena tace "kai Leema kiyi hak'uri muje kawai kinga fa sunsan muna garin nan bai kamata muje wani guri ba tunda duk Family ne mu ba bare ba" Queen ta yi hanyar fita tace "ban takurawa kowa ba, in kun so ku fito mu tafi in kuma kun k'i ko wacce ta kama hanyar inda zata, yau dai ba mai kwana min a wannan gidan, nima gidan Ubana zani na kwana" tana gama fad'an haka tasa kai ta fice, tsaki Meena tayi tace "In kina tak'ama da mulki muma fa gidanta muka fito, kinga Leema mu wuce gidan President d'in inya so in munyi two days sai ki koma Kano ni kuma na wuce Kaduna, domin wallahi ina missing Family na" Murmushi Leema tayi tace "hmmm wallahi nima hankalina ya koma gida fa, yanzu fa iyayenmu sun d'auka yau ne zamu dawo daga Dubai da muka tafi, bacin yau satinmu d'aya da dawowa, muna biyewa Queen bayan ita iyayenta sun ga dawowarta a ranar, muko munyi k'arya sai yawo muke bamu nan bamu can" Dariya Meena ta kwashe dashi tace "kefa saboda Jalal kika tsaya anan" hararan wasa Leema tayi mata tace "Ke kuma saboda mashayarku kika tsaya, saboda kinsan in kika koma gida Yaya Jamal zai takura miki ba shiga ba fita" duka Meena ta kaiwa Leema saita goce ta fice da sauri tana dariya. Haka su dukansu suka d'unguma zuwa babban gidan Shugaban k'asa. *WACECE QUEEN BASMA?...* _*Rahma Ce*_ (Sirrin 'ya mace group) WhatsApp. [9/29, 12:47 PM] Aysha Galadima: *'YAR SHUGABA*👑 _page_ *3.* _Na_ _*Rahma Kabir*_✍🏾 *WACECE QUEEN BASMA?* 'Yace a wurin Alhaji Mukhtar Bukar Bulama, wanda yake shugabancin k'asarmu Nigeria a yanzu. Asalin Mahaifinsa d'an Maiduguri ne Kanuri, mahaifiyarsa kuma mai suna Asma'u 'yar Gombe ce Fulani, Alhaji Bukar Bulama babban d'an kasuwa ne, yana fita k'asashen waje sosai, ya jima baiyi aure ba saboda yanayin kasuwancinsa, Mahaifin Asma'u Alhaji Salis, abokinsa ne k'ud da k'ud wanda a sanadin kasuwanci abotansu ya had'u, ganin Ahaji Bukar Bulam baiyi aure ba yasa Alhaji Salis ya bama Alhaji Bukar auren 'yar tilo d'aya Asma'u. Suna zama a cikin garin Kaduna a Unguwar Rimi, Alhaji Bukar an sanshi sosai, Mutum ne mai tausayi da taimakon talakawa, yaransa biyu a duniya Mukhtar da Halimatus Sadiya, sun taso cikin gata da kulawa kuma Asma'u tayi k'ok'ari sosai wajen basu tarbiyya mai kyau. Mukhtar yana gama primary mahaifinsa ya turashi karatu k'asar Germany a can ya fara secondary school d'insa. Tafiya ya kama su Alhaji Bukar zuwa Gombe sanafin rasuwan mahaifiyar Asma'u, bayan sunje basu dawo ba har akayi Addu'an bakwai kana suka kamo hanyar Kaduna, basu fita daga Gombe ba akan hanyarsu suka bige wani yaro, cike da tashin hankali suka nufi Asibiti dashi, aka karb'esu emergency, an samu yaron ya farfad'o, amma baya iya magana sai zaro idonsa yake waje, Likita ya basu tabbacin yaron ya samu Matsala a kwakwalwansa, hankalin Alhaji Bukar yayi masifar tashi, sunyi iya bincike ganin an gano iyayan yaron amma shuru ba a gano ba, da haka ya d'auki yaron ya wuce dashi Kaduna da nufin in ya samawa yaron lafiya ya maidashi wurin Iyayensa. Alhaji Bukar suna dawowa da kwana biyu ya shirya zuwa kasar Germany da iyalensa domin duba lafiyan Yaron daya bige, wanda baya iya magana. Da isarsu da kwana biyu cikin ikon Allah Yaron ya soma magana, sunan shi kad'ai ya iya tunawa Ibrahim, amma banda haka bai tuna komai ba, Likitoci suka tabbatar musu da Yaron ya samu mancewar kwakwalwa (loosing Memory). Abin ya damu Hajiya Asma'u sosai hakan yasa Alhaji Bukar ya bar Ibrahim a wajen Mukhtar ya fara karatu shima, sai suka tarkato suka dawo Nigeria. *Bayan shekaru mai tsawo* Su Muktar sun dawo Nigeria wanda dukkansu sun gama karatunsu sun samu aiki, har zuwa lokacin Ibrahim bai dawo cikin kwakwalwansa ba. Sadiya kuma tana karatu a KASU, tun dawowar su Mukhtar Allah ya daurawa Sadiya son Ibrahim, Abu kamar wasa har mahaifiyarsu ta ganeta saita kwab'eta, abinda basu Sani ba shima ta wurin Ibrahim d'in ya kamu da son Sadiya, daga bisani ya bayyana mata zuciyanshi suka fara soyayya. An sanya bikin su Ibrahim da Sadiya ba b'ata lokaci, wanda Alhaji Bukar yace ta cigaba da karatunta a d'akin mijinta, Mukhtar shima yana soyayya da k'anwar Sarkin kano mai suna Fatima, soyayya tayi k'arfi wanda hakan yasa aka had'a bikin su duka a kayi. Anyi biki sosai na manyan Attajirai, ko wacce ta tare a sabon gidanta da Alhaji Bukar ya siya musu a unguwar sunusi. Wata rana Alhaji Bukar ya shirya tafiya k'asar Dubai shida Mahaifin Asma'u, domin kula da kasuwancinsu dake can, a hanyar dawowarsu jirginsu yayi hatsari suka rasu. tashin hankali ba'a sanya masa rana, wannan Family sun shiga cikin damuwa da k'unci na rashin jigonsu, Hajiya Asma'u ta zama ba Uwa ba Uba ba Miji sai sauran danginta da yaranta. Hakan ya girgizata wanda haka yasa ta samu ciwon hawan jini. Su kuma su Mukhtar sun rasa Bango abin jingina watarsu. Ibrahim yayi kuka matuk'a domin da bazar Alhaji Bukar yake taka rawa, har yau baisan shi waye ba ko danginsa, yasan dai su Hajiya Asma'u basune iyayensa ba, ya kasa tuna komai na danginsa. Bayan Addu'an Arba'in duk dangi suka watse, an rab'e musu gadonsu, Muktar ya had'a duka dana k'anwarsa Sadiya dana Ummansu ya cigaba da kasuwanci dasu sannan yana aikinsa. Shi kuma Ibrahim sun bashi wani kaso mai tsoka daga dukiyar nasu kamar yanda mahaifinsu ya rubuta a cikin dairy d'insa, Ibrahim ya amsa yana godiya harda kukansa, daga nan shima ya cigaba da business. Hajiya Fatima matar Muktar ta haifi d'a Namiji mai suna Ahmad, bayan shekara guda ta kuma samun ciki, bata so ba amma dole ta hak'ura saboda Alhaji Mukhtar yana son abinsa, haka ya d'auki Ahamd ya bama Ummansu ta cigaba da rik'onsa. Bayan wata tara ta kuma haifo d'anta Namiji mai suna Abubakar suna kiransa da Naufal. Sati biyu da haihuwarta Allah ya azurta Alhaji Ibrahim samun k'aruwa da d'a Namiji wanda suke sanya masa suna Jamal. Sun raini 'ya'yansu cikin Kauna da soyayya, sun basu tarbiya sosai domin kud'insu bai hanasu tsayawa bisa tarbiyyan yaransu ba. *Bayan shekara biyu* Hajiya Fatima ta kuma haifo 'ya mace suka sanya mata Asma'u suna kiranta da Husnah. Ta b'angaren Hajiya Sadiya ita bata k'ara haihuwa ba tana rik'e da d'anta Jamal. Alhaji Mukhtar ya rik'e mukamin Commissioner har kujera uku, soyayyar da ya samu wurin Mutane yasa ya fito takaran gomna, cikin ikwan Allah ya samu. Ta b'angaren Ibrahim shima yana ta samun mukamai a wurin aikinsa dukiyarsu sai hab'aka take ta ko ina. Alhaji Mukhtar ya k'ara aure da 'yar wani hamshak'in mai kud'i a garin Kano 'yar Alhaji Buba mai Naira itace 'yarsa tilo guda d'aya mai suna Maryam, anyi Biki sosai na manyan Mutane, Alhaji Mukhtar ya tare da ita a gidansa na Gomnati, gida d'aya ya had'asu da Hajiya Fatima, suna zaune zaman lafiya ba tashin hankali. *Bayan shekara Hudu* yana kujeran Gomna, Hajiya Maryam ta Haifi 'yarta mace k'atuwa ga kyau, suka sanya mata suna Basma, Basma ta taso cikin gata da soyayyan iyayenta, Yaya Ahmad yana sonta sosai tun tana k'arama suka shak'u sosai, bata shiri da Yaya Naufal, Anty Husnah kuwa duk inda zata suna tare, tun tana k'arama ta koma hannun Hajiya Fatima, Nono kawai ke kaita gun Momynta. Itama Hajiya Sadiya ta k'ara haihuwar 'ya mace aka sanya mata Ameena suna kiranta da Meena, tserayen wata biyu ne tsakanin haihuwar Basma da Meena. Yaya Ahmad da Yaya Naufal kusan tare suka wuce k'asar Malesia karatu, Yaya Ahmad yana karanta Medicine Yaya Naufal yana karana Biochemistry. A lokacin Anty Husnah tana secondary school. Basma kuma tana primary. Hajiya Fatima wanda suke kira da Ammi ta gama sangartata duk wani rashin ji ta sani, ga tsokanar fad'a a makaranta, duk wani kiriniya tare suke yi da Meena da yake makarantar su d'aya. A daffafe suka kare primary saboda irin kai k'aransu da iyayen yara keyi, kasantuwar iyayensu manya ne shiyasa ba'a koresu ba. Hajiya Maryam ta k'ara haihuwar yara Maza 'yan biyu Anwar da Na'im, anyi shagali sosai da haihuwarsu, su Basma kuwa murna har kunne. So tari Hajiyar Maryam wanda suke kira da Momy bata ragawa Basma tayita mata fad'a hakan yasa Basma bata son kwana a b'angarenta sai wurin Ammi saboda Ammi na kula da ita bata son b'acin ranta. An d'aurawa Anty Husnah aure da Jabir d'an senator, sun had'u a makarantar Abu Zaria inda ta fara karatu, an d'aura auren tana cigaba da zuwa makaranta. A wannan shagalin bikin ne akayi taron da ba'a tab'a yiba, mutanan Gombe, Maiduguri, kano duk sun hallara, matar Sarkin Kano yayan Ammi, Hajiya Murja tazo bikin wanda ta taho da 'yarta mace sa'ar su Husnah mai suna Haleema suna ce mata Leema, tun daga nan su Basma aka samu kawa, da zasu tafi Leema ta kafe saita zauna wurin Ammi, haka mahaifiyarta ta barta mai martaba Sarki Abdallah ya amince Leema ta zauna wurin Ammi domin yasan gidan Gomna Muktar Bukar Bulama akwai tarbiyya. Abdullahi shine ya gaji sarautar gidansu bayan rasuwan Babansu, Yayane ga Hajiya Fatima, uwa d'aya uba d'aya suke, yana da mata biyu Hajiya Sa'a itace Uwar gida tana da yara biyu duk Maza Adam shine babba sai Shureym shine k'arami, sai Amaryansa Murja yarta guda d'aya ce itace Leema, sun d'aura son duniya sun azawa Leema kowa na dangi yana sonta, tun tana k'arama ta taso cikin sarauta, gimbiya Leema 'ya ga Sarki Abdallah. Hajiya Sa'a Mace ce yar k'arya da son duniya ta shigewa Hajiya Maryam Momyn Basma, amma Momy tak'i sake mata saboda halayyarsu bai zo d'aya ba, Hajiya Sa'a basa shiri Sam da Ammi wato k'anuwar mijinta, hakan yasa Momy tak'i sake jiki da ita. Hajiya Sa'a ta sangarta Shureym da gata, ta d'aura son duniya ta bashi saboda tana ganin shine zai gaji kujaran Babansu, shiyasa tun yana k'arami take kiranshi da Prince Shureym, hakan yana masa dad'i sosai. Adam shi kuma Mutum ne salihi ba yida hayaniya hakan yasa nasu yazo d'aya da Hajiya Murja, a wurinta yake komai. Shureym yana America yana karatun Engineering, shiko Adam Madina ya tafi karatunsa bangaren Islamic studies. Basma, Meena, Leema duk makarantar d'aya suke secondary, a part d'in Ammi suka tare domin Ammi ita bata kwab'a musu, Meena ta kwaso kayanta ta dawo gidansu Basma gaba d'aya. Alhaji Ibrahim Baban Meena ya samu cigaba sosai, wanda yaita samun K'arin girma a wurin aikinsa, ya tura Yaya Jamal karatu inda su Yaya Ahmad suke k'asar Malesia yana karanta Business admin. Gomna Muktar Bukar Bulama ya sauka a kan kujeran Gomna bayan shekara takwas daya shafe akai, ya k'ara samun kurajeran Sanator wanda ya wuce Abuja, sai weekend yake dawowa gida Kaduna. Dukiyarsu na gado sai hab'aka yake yi. Su Yaya Ahmad sun gama karatunsu gaba d'aya duk sun dawo, Yaya Ahmad ya fara aiki a babban Asibiti dake garin Abuja, Yaya Naufal kuma ya karb'i kasuwancin Abbansu ya cigaba da juyawa. Yaya Jamal ma dukiyar Dadynsa ya cigaba da rik'ewa. Ta b'angaren Mutanan Kano kuwa Yarima Adam ya dawo ya fara lecturing a BUK, shi kuma Shureym bai riga ya kammala masters d'inshi ba. Su Basma an zama 'yan Mata sun gama Secondary School yanzu suna England suna karatu. Basma na karanta Micro Biological, Leema tana karanta Pharmacy, Meena kuma tana karanta Low. Tunda suka koma England rayuwarsu ta k'ara sauyawa, sun had'u da 'ya'yan turawa da kuma 'yan k'asashe daban-daban, Basma tunda ta soma karatu saita natsu ta zama mara son magana, amma fa akwai tsiwa in aka tab'ota, Meena kuma akwai shegen surutu, Leema kuma akwai ji dakai da kuma k'asaita na Sarauta. Sunyi farin jini sosai saboda suna da k'ok'ari sosai. Meena ta had'u da wata yar ajinsu ta koya mata zuwa club, abu kamar wasa Meena in bata je club ba bata jin dad'i, tun su Leema na mata k'orafin ta daina zuwa har taja ra'ayin Leema ta fara zuwa. Abu na farko da suka koya shine Meena ta shiga group d'in 'yan shaye-shaye, tun bata iya ba harta kware sosai wajen zukar sigari da shan kwayoyi. Leema kuma Mace ce mai yawan sha'awa, in Meena ta jata cikin group d'insu saita kasa sakewa a haka harta had'u da Jalal suka fara soyayya tun bata sakewa harta sake dashi, Jalal ya fara fita da ita yawo kullun sai sun fita. A hankali yayi ta jan ra'ayinta gareshi, tun tanak'in amince masa harta bashi kai bori ya hau. Tun daga nan suka d'inke da Jalal, ya mai da ta tamkar Matarsa shine mutum na farko da yasa fara sanin ta a 'ya mace. A hankali Leema ta raba shi da duk 'yan matanshi, Basma kullun cikin musu nasiha take akan sun gurb'ata tarbiyyan da iyayensu suka yi musu dasu gyara halinsu. Meena tayi murmushi tace "ke bazaki gane ba, meye amfanin zuwanmu k'asar waje bamu waye ba, ai wannan itace wayewar, kinga ni shaye-shaye kawai nakeyi ita kuwa Leema da Jalal take harka, kinga ta samu abinda zuciyarta take so". Basma tayi tsaki tace "Allah ya kyauta" Murmushi Leema tayi tace "ki shirya yau muje club dake Allah za kiji dad'in wurin sosai" Basma tace "Kun dameni da zancen club d'in nan, yau dai zani inga abinda akeyi a gun shikenan kunyi farin ciki ko?" cikin farin ciki suka ce "wow munyi Murna kema zaki shigo sabon rayuwa ki huta da rayuwan duhun kai" Sunje club gaba d'ayansu, yanda Basma taga wurin sai ya sanyata farin ciki musamman data ga 'yan rawa sai hakan ya kwanta mata arai, dan a duniya Basma tana son rawa, kawai sai ta mik'e ta nufi wurin rawan ta hau, cike da mamakin mutane suka bita da kallo, ji tayi k'afarta ya k'asa d'aukarta, dan gani tayi ido ya mata yawa bazata iya ba, su Meena ne suka fara kiranta "common Besty ki fara" nan kowa ya fara ihu suna mata kirari dan ta fara, nan kanta yayi chargy taji wani k'arfi da dakewa saita fara rawa cikin salo naban namaki, sai wurin ya kaure da ihu, dan tayi matuk'ar burgesu, ba wanda yayi tsammanin ta iya rawa haka, hatta su Leema sunsha mamaki. Nan aka fara mata yayyafin kud'i kan basma ya k'ara kato saida tayi sosai kana ta sauko, koda ta samu guri ta zauna sai mai wurin ya kawo mata kud'in data samu bud'en bakinta tace ya barshi. Murna sosai yayi ya mata godiya. Tun daga wannan rana Basma ta fara zuwa club burinta bai wuce taje tayi rawa a yi mata kuwwa a fasa mata kai. Musamman ta shiga makarantar koyan rawa babu irin wanda ba a koya mata ba hatta na larabawa. *_Rahma Ce_* (Sirrin 'ya mace group) WhatsApp. [9/29, 12:47 PM] Aysha Galadima: *'YAR SHUGABA*👑 _page_ *4.* _Na_ _*Rahma Kabir*_✍🏾 An shirya gagarumin gasa na rawa a k'asar England, Basma na d'aya daga cikin masu fafatawa. In ta dawo daga school babu abinda take yi sai gwajin rawa, su Leema suke k'ara mata k'arfin gwiwa. Ranar taro, k'aton hol cike yake mak'il da mutane maza da mata, ko wanne yana mazauninsa, ga kuma masu tantance rawar daga gefe, zaune suke akan kujeru na alfarma, ga dogon table a gabansu an d'aura kayan motsa baki da kuma abin sha, masu fafata gasar su Hamsin ne, a ciki ake son a finda zakara guda d'aya wanda aka tanada mak'udan kud'i da key na mota sai kuma hular Queen na rawa ga wanda taci, sai na biyu dana uku kyautar kud'i. Gasar maza da mata ne, Ganin yawansu da Basma tayi sai zuciyarta ya tsinke ta karaya, gani take ba zata ci ba, jere suke akan layi wannan na bin wannan, sun sanya riga top mai dogon hannu sai kuma wando dogo pencil ya matse jikinsu, rigan ta kama su daga sama zuwa ciki, k'asan kuma ya bud'e, tsayinta ya kawo rabin cinya. Wasu sun sanya hula a kai wasu kuma sun baje gashin su a baya, shigar Basma tayi mata kyau, ta dunk'ule gashinta ta sanya hula, ba wani makeup a fuskanta amma tayi kyau sosai. Basma itace ta goma sha shida a cikin jerin layin. D'aya bayan d'aya suke fitowa suna gwada rawan su, alkalai suna dubawa tare da rubuta makin, 'yan kallo kuma suna ihu in rawar tayi musu kyau ga masu gwajin. A haka layi yazo kan Basma, cikin salo da kwarewa ta fara rawa mai ban sha'awa, a hankali take komai cikin nutsuwa, lauye duk sassan jikinta take yi tamkar roba, ta d'auki tsayin minti ashirin tana rawa, nan fa hol ya kaure da ihu da alama rawarta ya birge su. Alkalai suka dakatar da ita suka ce ta tafi, na gaba yazo ya nuna nashi. Da haka har aka gama tantance rawar su Hamsin. Daga cikin alkalai wani ya mik'e yace cikin harshen turanci, zasu cire mutane goma daga cikin su, domin fafatawa na k'arshe, washe gari zasu yi rawa a cikinsu za'a tantance Mutum na farko dana biyu har zuwa na uku da sauran numbers. Nan fa hol yayi tsit ana son aji su waye zasu shiga gasa ta k'arshe. An fara kiran Mutum na farko da haka har aka je kan Mutum na tara, Basma bata ji sunanta ba sai ta sadak'ar da ta rasa gasar, wanda basuji sunan su ba sai kuka wasu kuma damuwa ya bayyana a fuskokinsu, Basma bata an k'araba taji an kira sunanta Basima MB a ta goma, da yake da haka tayi regista da sunan ta basima MB, saboda basaja, kuma ita ba 'yar k'asan ba ce. Ai hol saiya kaure da ihun su Leema da Meena sauran Mutane ma suka tayasu ihun. Da haka aka tashi taro Maza hud'u mata shida sune zasu fafata a washe gari. *Washe gari* Hol ya cika mak'il da Mutane fiye dana jiya ma, nan kowa ya samu guri ya zauna, yau shigan dasu Basma sukayi kusan irin na jiya ne sai dai an sauya launin kalan kayan da suka sanya jiya. Alk'alai suka baza ido, na farko ya fito ya fara fafatawa, har aka kai na biyar, daga nan sai aka tafi hutun tak'aitaccen lokaci. Bayan an dawo aka d'aura har zuwa na k"arshe ta fito wato Basma, nan ta soma kafa tarihi domin rawar ta na yau yasha ban-ban dana jiya, Basma ta dage iya iyawanta, sai baza rawa take tamkar ba ita ba, inba ka mata kallon caf ba bazaka shaida Basma ce ba, domin tayi shiga na b'adda kama. Saida tayi rawa sosai sannan aka dakatar da ita, alk'alai sun fita a hol sunje had'a marking, sai da suka b'ata kimanin rabin awa kana suka dawo kan high table suka zauna, sun fara fad'an sakamako daga na goma ne, har suka zo kan na shida ya rage saura mutum Hud'u, Basma na ciki, a haka har suka fad'i na Hud'u dana uku, saura Basma dawata 'yar k'asar England d'in, sai aka tafi hutun rabin sa'a, nan fa kawayen su Basma suka rufe ta da Murna Addu'a suke Allah yasa itace mai nasara. Burin Basma ko na biyu tazo zatayi farin ciki tunda ta kafa Tarihi a fagen rawa. Koda aka dawo daga hutun takaitaccen lokaci, hol d'in yayi shuru ana jiran aji wacce tayi winning, mai fad'an sakamako saida yayi shurun minti biyar kafin ya furta first position Basima MB kece ki kai nasara, d'ayan kuma ta zama na biyu, hol d'in ya kaure da kuwwa, nan take aka d'aurawa Basma Hular Queen, wannan dalilin ne yasa Basma take amsa sunan Queen Basma. Sunyi hotuna kala-kala hatta gidan TV na k'asar sun nuna gasar a TV. Taro ya watse, su Meena cike da farin ciki suke, kana ganinsu kasan yau suna cikin murna, har gidan da suke zama aka kaiwa Basma motarta da kuma kud'in data samu. Tun daga wannan lokacin su Leema fankama da d'aga kai ya k'aru, Basma kuwa sunan ta sai da ya shiga cikin k'asar England sosai, kowa na sonta har wani respect d'inta ake. Ana saura shekara d'aya su gama karatunsu su dawo k'asarmu, Mahaifin Basma ya fito takaran shugaban k'asan Nigeria, Mahaifin Meena ma ya fito takaran Gomnan jahar Kaduna. Abu kamar wasa da lokacin zab'e yazo duk suka ci zab'en. Mahaifin Basma President Mukhtar Bukar Bulama sai kuma Gomna Ibrahim Abubakar, yana amsa sunan Alhaji Bukar wanda ya rik'eshi. Farin ciki wurinsu Basma ba a magana musamman suka dawo Nigeria akayi bikin rantsar da iyayensu, tun daga wannan lokacin sai suka chanza salo suka k'ara sauya rayuwansu ga mutane, suka keb'e kansu, musammam aka samu ascot suka bi su Basma England suna basu kariya, feeling da d'agawa ya k'aru a wajensu Leema. Su Basma sun kammala karatunsu sun dawo gida, ta matsawa president saiya gina mata gidan huta a Abuja, haka ya sanya aka mata k'erarren gini aka zuba kayan da ta buk'ata, koda suka dawo Abuja suka sauka, domin yanzu Alhaji Mukhtar yadawo Abuja da iyalensa suna gidan shugaban k'asa, su Meena da Leema suma nan suka sauka, sun k'i komawa gidansu saida suka shafe wata guda kan suka wuce gidajen iyayensu. Akwai wani lokaci da Basma ta tafi kano hutu, tunda Hajiya Sa'a ta ganta saita k'udurta wa ranta Prince Shureym ya samu mata, tayi alkhawari yana dawowa zata turashi yaje gun Basma su dai-daita koda baya sonta, burinta Shureym sai 'yar babban mutum zai aura. Saboda wannan k'udirin nata ne yasa ta k'ara shigewa Momy mahaifyar Basma, dole yasa ta shirya da Ammi, domin tasan tabbas sai tabi ta wajenta tunda Basma a hannunta take, Hajiya Sa'a bini-bini tana Abuja, kasan tuwar su Ammi basu san nufinta ba sai suka sake mata suka saba sosai, zumunci ya k'ara kulluwa mai k'arfi. Duk wannan abinda Hajiya Sa'a takeyi Shureym bai sani ba yana can America, shi a can ya had'u da wata 'yar Yola mai suna Safeena, soyayya sukeyi sosai, sunyi wa juna, Alkwari aure in sun dawo k'asarmu. Hajiya Sa'a tayi k'ok'arin had'a Basma da Shureym a waya suna gaisawa, da kyar ta shawo kan shureym bayan tayi masa bayani akan Basma, ya amince amma da sharad'in zata barshi ya auri Safeena, haka ta amince masa, ita dai burinta Shureym ya auri *'Yar Shugaba* a matsayinsa na D'an Sarki. Da dubara Hajiya Sa'a ta soma tusa maganar a wajen iyayen Basma, kuma su a zuciyarsu hakan yayi musu dad'i sosai. Basma kuma suka fara soyayya da Shureym kamar gaske. Leema kuma ta kamu da son Yaya Jamal amma shi ko kad'an baya sonta baya ma shiga hanyarta, Duk da haka bata daina harka da Jalal ba. Meena kuwa soyayya take da Yaya Naufal kamar zasu cinye juna. Su Basma koda suka dawo Abuja basu sauya rayuwar da suka fara ba a England, da zarar sun tafi gidan Hutu tofa bazasu dawo gida ba sai sunje wani babban club dake cikin garin Abuja, sunyi abinda ran su ke so, sannan su koma gidan Hutu su kwana ba tare da kowa ya san rayuwar da suke ai katawa ba. *Hmmm adai jure zuwa rafi...* Bayan sun dawo da shekara guda, Meena ta tafi Abuja, Leema ma ta bar kano ta tafi Abuja da nufin zasu Dubai siyayya. Duk suka had'u, suka shirya tsaf suka tafi Dubai, achan ma saida suka lalubo babban club can suka b'arje lokacin su, da zasu dawo su Meena da Leema basu gaya ma iyayensu zasu dawo ba, Queen ta kira aka zo a ka d'aukesu a airport, direct hotel suka je suka kama Leema da Meena domin so suke su wataya kan su koma gida, ita kuma Basma gida ta wuce sai ta cewa iyayenta su Meena suna gidan hutunta. A fitan da Basma tayi ta fita d'auko su Meena a hotel don suje gidan hutunta, bayan ta d'auko su ne a hanyar zuwa gidan Hutu ne suka had'u da Aryan har suka kusa bigeshi, Basma ta tofa masa miyau takuma sanya aka mareshi. *Cigaban labari...* Basma sun wuce gida gaba d'ayan su, bayan sun isa sai suka wuce part d'in Abbansu domin tasan breakfast d'insu yayi ready a can, suna shiga duka iyayan nasu suka bisu da kallon sha'awa a nutse suka k'arasa suka kwashi gaisuwa, President dake zaune a dining ya kalle su yace yarana kun girma fa sai aure tunda kun gama karatu, dariya duk suka yi, Basma a tsagwabe tace "Ni Abba ba yanzu zanyi Aure ba sai na kai 25yrs tukunna lokacin na kara wayo" duka mutanen falon suka sanya dariya amma banga Momy da take doka mata harara, koda suka had'a ido da juna sai tayi saurin kauda kai, dan tasan laifin da tayi. Nan suka zauna suka karya duka, bayan sun gama ne Abba yace "Basma ki sameni a falon sama" Cikin farin ciki tace "to" kana ta mik'e tabi yansa, Ammi ma bayansu ta bi, Momy kuma ta kalli su Meena tace "wai ku yaushe za kuyi hankali ne, kun dawo amma kunk'i zuwa ku kwana anan ko? sannan nayi waya da Hajiya Sa'a tace ai ke Leema baki samar musu kin dawo ba, ke kuma Meena Maminki ma bata san kin dawo ba, to wallahi ranku duk sai ya b'aci, inna sanya k'afar wando d'aya daku, ku tashi kuje sashi na ku jirani gani nan zuwa, in ba haka ba saina ci muntuncin ku" Sum-sum suka mik'e suka tafi part d'inta, su Na'im da Anwar suka mik'e suka ce "Momy mun tafi Makarantan hadda" Da murmushi a fuskanta tace "To sai kun dawo ku mai dankali sosai banda wasa" suka ce "to" sannan suka wuce. Momy ta danna k'araurawar kicin, da gudu ma'aikatan kicin d'in suka fito tare da risinawa, umarni tayi musu dasu kwashe kayan abincin su gyara wurin, cikin sauri suka mik'e dan cika umarninta. Momy ta mik'e tayi wurinsu Basma. Ta same su Ammi zaune suna jiran fitowar Abba, koda ya fito sai ya samu guri ya zauna yace "Basma nayi waya da Mai Martaba ya sanar dani dawowar Shureym gobe insha Allah, dan haka sai ki tsumayi zuwansa domin a nan zai fara sauka in yayi mana kwana biyu zai wuce Kano" sunkuyar da kai tayi k'asa tace cikin ladabi "To Abba" Ammi tace "sai ki d'auki su Meena a mota kuje kuyi siyayya dan had'a masa kayan tarba" Momy tayi tsaraf tace "su Meena yau d'in nan zan turasu su koma gida, domin duk iyayensu basu san sun dawo ba" ido bude Ammi tace "kaji min ja'iran yara, shiyasa suka k'i kwana anan, to Allah ya shirya mana su" duk suka amsa da "Amin" Abba ne ya ciro bandir d'in kud'i na 'yan dubu-dubu ya mik'awa Basma yace "Ga wannan kud'in ko kinada bukatar wani abu" cikin natsuwa tace "Abba akwai kud'i a account d'ina fa" "Eh nasan dasu wannan cash ne ai" Basma cikin farin ciki ta amsa tayi godiya, saita mik'e ta fito tabar iyayan nata anan ta nufi sashin Momy. Can ta samu su Meena sunyi jugum-jugum, kwashewa tayi da dariya tace "wow yau kun shiga hannu Momy mai fiddaku sai Allah" hararenta Leema tayi tace "ai duk ke kika ja mana, munce bazamu zo ma kika wani damemu, gashi yanzu ta tsaremu, dama ni ita nake ji, dan ta cika takurawa Mutane" ta k'arasa maganar dayin tsaki, kan basma ta basu amsa sai ga Momy ta shigo, zama tayi ta zuba musu ido tace "ku shirya yanzu nan driver zai kaiku airport, ke Leema ki wuce Kano a jirgin sama, Ke kuma Meena jirgin k'asa zaki bi ki sauka a Kaduna". Leema kamar zata yi kuka tace "Momy ki bari gobe in Allah ya kaimu sai mu tafi" Momy tace cikin fushi "rufemin baki yau d'in nan zaku tafi, maza ku tafi driver suna jiran ku" jiki na rawa suka mik'e suka fita saida suka biya gidan hutun Basma da kuma hotel d'in da suka sauka suka kwashi kayansu kana suka tafi Airport sai gida. Momy ta kai dubanta ga Basma tace "Wato ke Basma har yanzu ba kida hankali ko? bana hanaki kwana a wannan gidan hutun ba, shine kika kwana jiya baki sanar dani ba saboda Ammi ta d'aure miki kiyi yanda kika ga dama ko" cikin shagwab'a tace Momy "wallahi dare tayi ne shiyasa ban dawo ba" "dalla can yimin shuru, ni tunda kika tafi England kika dawo kedasu Leema kuka sauya hali, na rasa me kukeyi a wannan gidan" da sauri ta d'ago tace "babu abinda mukeyi fa, hutawa kawai muke sai wanka a swimming pool" "ok naji, yanzu dai na sanya abokan naki sun tafi, naga dalilin fitanki kullun, gobe in Allah ya kaimu zan aike ki gidan hajiya Aisha k'awata" cikin sauri ta katseta tace "Momy gobe ne fa Shureym zaizo kinga bai kamata na fita ba, ki aiki su Na'im mana pls" hararanta tayi tace "bazan aike su ba, ke nake so ki tafi, tashi ki bani wuri" cikin shagwab'a Basma ta mik'e tare da buka k'afafunta ta fita a sashin Momy harda kwalla, ta nufi part d'in Ammi. Momy ta girgiza kai tace "ohh ni Maryamu ka haifi d'a amma Baka haifi halinka ba, Allah ka shirya min Basma" tana gama fad'an haka sai ta mik'e ta shiga d'akinta. *Muje zuwa...* _*Rahma Ce*_ (Sirrin 'ya mace group) WhatsApp. [9/29, 12:47 PM] Aysha Galadima: *'YAR SHUGABA*👑 _page_ *5.* _Na_ _*Rahma Kabir*_✍🏾 *washe gari* Basma ta tafi aiken Momy da misalin ƙarfe sha biyu na rana, gidan hajiya Aisha ta tafi ta kaimata saƙon Momy. A hanyarta na dawowa ne saita wuce gidan hutu ta ɗauko wasu kayanta kana ta kama hanyar gida, escot na biye da ita a baya, ta hau kan babban hanya bata ankara ba ta bige wata Yarinya, cike da tashin hankali ta koma bakin hanya tayi parking, bodyguard suka fito a motansu suka nufa wacce ta bige, saboda tsoro Basma ta kasa fitowa, sun ganta kwance cikin jini a sume, cikin sauri ɗaya daga cikin ascot ɗin ya isa gun basma yace "Hajiya Yarinya ta suma fa" cikin sarƙewan murya tace "ku sata a motanku a seat na baya, sai kuzo ku biyu ku shiga tawa motan tunda ku huɗu ne" cikin sauri ya amsa "yes Madam" ya tafi tare da cika umarnin data basu. General hospital direct suka wuce, aka wuce da ita emergency room, cikin sauri Basma ta ɗauki wayarta ta kira Yaya Ahmad ta shaida masa suna cikin asibity ta bige wata yazo da sauri, baifi minti biyar da kiranshi ba saiga shi yazo yace "ina take?" cikin damuwa tace "tana emergency room" bata kaiga ƙarasawa ba ya wuce ciki. Zarya ta shiga yi hankali ta a tashe ganin ma ashe ba ƙaramar Yarinya ta bige ba budurwa ce, an ɗauki kusan minti talatin kafin duka likitocin suka fito, da sauri Basma ta tari Yaya Ahmad tace "Yaya ta farfaɗo kuwa?" ciki da tausayawa ƙanwar tashi ganin yanda ta burkice yace "ta farfaɗo yanzu dai ta samu barci kuma anyi mata dressing inda taji ciwo, nan da awa guda zata farka insha Allah". Da ƙarfi Basma tayi ajiyan zuciya tace "Alhamdulillah" sai Yaya ya jefo mata tambaya yace "in kika je ne har kika bigeta?" gefe ta koma ta samu wuri ta zauna, shima binta yayi ya zauna, nan ta bashi labarin yanda ya faru. Ya girgaza kai yace "Allah ya kyauta gaba, amma meyasa kikayi driving da kanki" murmushi tayi tace "Yaya Ahmad wlh kawai hakanan naji ina sha'awar tuka kaina" Dariya yayi yace "hmm su Basma rikici, kije gida kawai saiki turo Shugaban mai kula da sashin Ammi Baba kulu tazo ta zauna da ita, tunda ke yau nasan kinada baƙo ya kusa sauka ma", murmushi tayi tace "tom Yaya Ahmad bari naje anjima zan dawo insha Allah" "ok sai kin dawo, ki kula da kankifa" "insha Allah Yaya zan kula" suka rabu cikin farin ciki. Tana isa gida taje ta samu Baba Kulu ta sanar da ita saƙon Yaya Ahmad, driver zai kaita, cikin sauri Baba kulu ta tafi. Basma tasa masu aikin Kicin na ɓangaran Ammi ta sanar musu abincin da za suyi mata na tarban baƙonta. Sai ta nufi sashin Momy ta samesu zaune da Ammi suna magana ta gaishesu kana tace "Momy na kai mata saƙon tace za kuyi waya" Momy tace "ok, amma naga kin daɗe ko kin biya gidan hutun naki da kika saba?" murmushi tayi tace "a'a Momy wallahi a kan hanyar dawowa na gida, na bige wata, yanzu haka tana asibity, na tura Baba Kulu ta zauna da ita zuwa anjima zan koma" cikin tashin hankali Ammi da Momy suka hada baki "subhanallah da fatan dai abin da sauki" murmushi tayi tace "da sauki kamar yanda Yaya Ahmad ya sanar dani shiyasa na taho ma" Ammi tace "to Allah ya bata lafiya ya kuma tsare na gaba" duk suka amsa da "Amin". Saita shiga ɗakinta dake sashin Momy. Tana Shiga ta faɗa makeken gadonta wayarta ta jawo ta duba taga miss call ɗin su Meena, kiranta tayi bugu buyu ta ɗauka, Meena bata jira Basma ta yi magana tace "wlh Basma ba kida kirki, jiya ko ki kiramu kiji ya muka sauka" cikin natsuwa tace "Afwan ya habibty, nima Momy saida tamin faɗa, haushin haka yasa ban kiraku ba" Nan dai suka shirya, Basma ta bata labarin accident ɗin da tayi, Meena ta mata Allah ya kyauta na gaba kana suka kashe wayar. Basma ta kuma kiran Leema itama mita tayi mata ƙorafi kamar yanda Meena tayi nan ta bata haƙuri suka yi hira kana suka yi sallama. Bayan sallan asri Basma tayi wani wanka ta sanya baƙar jallabiya mai ɗauke da kwalliya pink color, tayi rolin da gyalen abayan, saita fito, abinci ta ɗauka a baske kamar yanda Momy tasa aka dafawa mara lafiyan, saita shiga mota driver ya jata zuwa asibity. Ta nufi ɗakin da aka sauyawa mara lafiyan, ta shiga ta sameta zaune jingine da pillow, idonta a lumshe da alama tana hutawa ne, Baba Kulu ta amshi kwandon abincin tace "sannu Basma" cikin fara'a Basma ta ce "yauwa Baba Kulu, ya mai jiki, "da sauki, ta farka tun ɗazu amma fa kuka take tayi min, wai ita zata tafi, da kyar na lallashe" cikin kulawa Basma ta kai dubanta ga mara lafiyan, wuri ta samu gefen gadon ta zauba ta kama hannun mara lafiyan tace cikin sanyin murya "baiwar Allah ya jikin da fatan dai babu wata damuwa" idonta cike da hawaye tace "lafiya lau ni naji sauƙi, ni dai ku taimaka ku kaini gida, wlh nasan hankalin Umma na da Yaya a tashe yake in basu ganni ba" cikin nutsuwa Basma ta kuma cewa "kiyi hakuri, ya sunanki?" cikin damuwa tace "Khadija" girgiza kai tayi a laman gamsuwa tace "kiyi haƙuri kici abinci zan kira likita yazo ya bamu sallama saina kaiki gida" cike da fara'a tace "nagode Hajiya" Basma tayi murmushi tace "sunana Basma ba Hajiya ba" itama Khadija murmushi tayi kawai batace komai ba. Baba Kulu ta sanya mata tuwon semo miyar agushi, ga wani plet ɗin ta sanya mata farfesun kayan ciki ta kuma zuba mata drink na 5alive a cup, a kan gadon ta jera mata, cikin kulawa Deeja tace "nagode Baba" dama da ɗan yunwanta ta fito zuwa wurin saro kwai, bata kaiga siyo bane Basma ta bigeta, saita buɗe ciki ta kwashi girki Basma sai kallonta take yi, a zuciyarta tana yaba kyawun khadijan sai dai a irin shigan da taganta dashi ya tabbatar mata masu ƙaramin ƙarfi ne, hakanan taji Kadijan ta kwanta mata a rai saboda ta lura tanada sauƙin hali, bayan ta gama cin abincin suka kawo mata wurin wanke hannu ta wanke kana ta kalli Basma tace, "Hajiya au, kince sunanki Basma ko" ta gyada mata kai alaman eh, ta cigaba dacewa "ke nake jira ki kira likita in tafi gida, wlh Ummata zata damu da Yaya Aryan, murmushi Basma tayi mata ba tace komai ba a zuciyarta tana maimaita sunan Aryan, hakanan taji sunan tayi mata daɗi. Wayarta da ɗauka ta kira Yaya Ahmad bai ɓata lokaci ba yazo, yace "Basma ashe kin dawo?" "eh Yaya Ahmad na dawo, dama Patient ɗinka ce tace a sallameta zata gida" dubansa ya kai wurin Khadija yayi mata murmushi yace "haba dai kiyi haƙuri ki kwana gobe zaina sallamaki" Deeja ta zaro ido waje tace cikin tsoro wlh Ummata nake ji da Yaya Aryan, kuyi hakuri Ku sallameni" shima Yaya Ahmad cikin zolaya ya zaro ido yace "tafɗi, ni bazan sallameki ba sai gobe in Allah ya kaimu" ai sai Deeja ta fara fidda kwalla, Basma tace "Yaya kaga kuka take yifa, ka sallameta kawai sai a bata magunguna, in yaso ni da kaina zan dawo maka da ita sai ka kara dubata" cikin fara'a yace "Basma rabu da ita wasa nake mata, dolena na sallameta kafin ta nima hanyar guduwa" dukansu sai suka sa dariya amma banda Deeja da ta sunkuyar da kai ƙasa tana murmushi. Yaya Ahmad ya rubuta mata sallama yace "Basma zaki dawo da ita nan da kwana biyu" "OK Yaya insha Allah zan dawo da ita". Nan Yaya Ahmad ya kira driver ya kwashi kayan su yasa a mota, ya kalli Baba Kulu yace "Baba kuje gida ni zan kaisu Basma", cikin kulawa Baba Kulu tayi godiya kana ta tafi. Ya kai dubansa ga Basma yace "muje ko, da fatan ta sanar miki da inda take" "Ok, Yaya ba damuwa zan tambayeta a mota". Sai suka kama hanya, Yaya Ahmad ya shiga dasu shopping complex ya siya mata kayan ciye-ciye, kana suka ɗauki hanyan gidansu Deeja. Aɓangaren su Umma kuwa Yaya Aryan zaune yake a gidan yayi jugum, Umma ma tayi tagumi tace "wlh hankali ya tashi har yanzu ace bata dawo ba? ban taɓa aiken Deeja ta dad.ɗe haka ba, gashi kaje har wajen masu kwai bata ba labarinta, sunce ma bata jeba, Allah yasa ba sace min 'ya akaya ba" ta ƙarasa maganar tana matsar kwalla, Yaya Aryan cikin damuwa yace "Umma kiyi haƙuri insha Allah za'a ganta, bari na ƙara fita in duba ko Allah zaisa muji wanda yaganta" ya miƙe tare da cewa "Umma saina dawo" ta amsa da "to Allah yasa a dace". Sun shigo Layin su Deeja saita tace "Ku saukeni a nan in ƙarasa, nagode Allah ya saka da alkhairi" Basma ce ta juyo da sauri, da yake tana kusa da Yaya Ahmad dake tuƙasu, tace "haba dai Khadija, ki bari mu kaiki har gida mana", cikin dishewar murya tace "a'a Ku bari kawai na tafi" cikin kulawa Basma tace "daga nan zuwa gidanku da nisa?" tace "a'a ba nisa nan sama ne kaɗan" Basma ta kai dubanta ga Yaya Ahmad tace "Yaya saukemu anan mu ƙarasa, ƙila bata so wasu suga an sauketa a mota ne" cike da kallon tuhuma yace "kinsan dai ba tare muke da escot ba" Basma ta gyaɗa kai "na sani Yaya Ahmad, insha babu abin da zai faru" "Ok, kuje bari na jira ki anan, amma karki daɗe, tace "Tom Yaya na tnx. Sun kama hanyar gidan su Deeja, suna zuwa ƙofar gidan Deeja tace "ga gidan mun kawo" Basma tace "Ok mu Shiga" Deeja tana shiga ta hango Umma zaune tasha kuka idonta yayi ja, da ganinta tana cikin damuwan rashinta ne, da gudu ta ƙarasa ta faɗa jikin Umma tace "Umma na dawo" cikin damuwa Umma tace "Khadija ina kika tsaya tun d.ɗazu kin asamu hankalinmu a tashe?" tace "Umma tafe nake da baƙuwa" da sauri Umma ta kai dubanta hanyar waje ta hango Basma tsaye tana kallonsu, da sauri ta miƙe tace "lale sannu da zuwa, ƙaraso ciki mana" da murmushi a fuskarta ta ƙarasa, wuri ta samu ta zauna kan tabarma cikin nutsuwa tace "Umma ina yini" nan suka gaisa kana ta yiwa Umma bayanin duk abin da ya faru, Umma tayi godiya da kulwanta sannan tace "sun yafe ba komai, nan dai Basma ta miƙe tayi musu sallama tare da aje musu bandir ɗin 'yan budu ɗai-ɗai har dubu Hamsin, ga kuma siyayyan da Yaya Ahmad yayi mata, Umma cike da tsoro tace " 'yar nan mun yafe ki d.ɗauki kuɗinki" cikin fara'a Basma tace "Umma nima 'yar kice, wannan kyauta nayi ma Ummata, kiyi haƙuri ki amsa" da farin ciki Umma tayi mata godiya, sai suka rakata har ƙofar gida, kana ta wuce su kuma suka shiga gida. Basma ta tafi cike da tausayinsu ganin irin gidan da suke ciki, hakanan taji a zuciyarta tana son ta taimaka musu, amma tana tunanin ta wace hanya zata taimakesu, da haka tayi nisa cikin tunani bata ankaraba taji tayi karo da mutum, da sauri ta ɗago ta kalle shi, ido Huɗu suka yi da juna, nan take zuciyarta ta buga, haka shima nashi ya buga, Aryan sarai ya gane ta, haka itama ta gane shi, cikin yanayi na ko in kula Aryan yace "Ke ba kida hankali ne zaki riƙa tafiya ba kya kallon hanya, ko makauniya ce ke da kike tafiya bakya kallon gabanki, ko har gefen hanya kina takama dashi ne?" cike da jin zafin abinda ya gaya mata, wato ma ya ganeta ta faɗa a zuciyarta, tace cikin tsiwa "Kaine ba kada hankali ƙazami kawai, kuma kaine makaho da baka ganin kan hanya" cike da ƙunan zuciya ya d'aga hannunsa ya kwashe ta da mari, abinda bai taɓa yiba kenan ya daki mace, nan fa mutane suka fara taruwa, Basma ta dafe kuncinta tace "ni ka mara? kasan ko wacece ni?" yace "Na mareki koke wacece, kiyi abinda za kiyi, kina tsammanin zan mance baƙar fuskarki ne? Mara tunani kawai, dalla ɓace min da gani" ya ƙarasa maganar cikin zare mata ido, nan take tsoranshi ya mamaye mata zuciya, cikin kuka gudu-dugu Basma ta bar wurin tana ƙoƙarin isa wurin motansu. Shi kuma yabi bayan ta da kallo yayi kwafa sannan ya cigaba da tafiya. Tunda take ba'a taɓa wulaƙanta ta irin na yau ba, tana isa ta faɗa mota, Yaya Ahmad cikin tashin hankali yace "lafiya Basma me aka miki? meya faru? haka ya jero mata tambaya babu amsa, illa a cikin kuka tace "Yaya Ahmad muje gida, muje gida". Cikin tashin hankali ya tada mota ya figeta a guje. Aryan yana tafiya ya fara tunani, a wani ɓangare na zuciyanshi yana farin cikin rama marin da yayi, wani ɓangare kuma yana gargaɗinsa, meyasa ya mareta, nan take wannan tunanin ya rinjayi wancen sai yaji zuciyansa yayi masa ba daɗi da haka ya ƙarasa gida. *Basmatyyy ansha mari ooo 😉 ko kunga laifin Aryan daya rama? muje zuwa...* *Rahma Ce* (Sirrin 'ya mace group) WhatsApp. [9/29, 12:47 PM] Aysha Galadima: *'YAR SHUGABA*👑 _page_ *6.* _Na_ _*Rahma Kabir*_✍🏾 Ya Ahmad saida ya bari sun kusa gida sai ya samu guri yayi parking, ya kalli Basma yace "Basma ki gaya min me ya faru? dan bazani gida dake a haka ba" share hawayenta tayi ta fara bashi labarin duk abinda ya faru, bata ɓoya masa komai ba tun farkon haɗuwanta da Aryan, saida ta gama tsaf kana ya gyara zamansa ya fuskanceta da kyau yace "Basma gaskiya baki kyauta ba, domin ke kika ja komai ya faru, meyasa idonki zai rufe saboda samun duniya ki wulakanta Mutum, Allah da kanshi ya karrama ɗan Adam ya fifitamu akan Aljanu, Basma yanzu halittan Allah ya cancanci wulakanci? haba Basma ban san yaushe kika sauya halinki ba, kina taƙama da mulki da kuɗi ko, to wallahi Allah zai iya amshesu daga hannun mu ya bama wasu, ki sani wannan duniyar ba matabbata bace munzo cin kasuwa ne, duk kuma abinda muka shuka shi zamu girba a makomarmu, Basma na lura tunda kuka tafi England ke dasu Meena duk kuka sauya hali" Jikin Basma ne yayi sanyi sosai, tabbas maganganun sa sun ratsata, cikin mutuwar jiki tace "Yaya Ahmad wallahi yanzu hankalina ya dawo jikina tabbas ban kyauta masa ba, nagode daka tunatar dani da kayi, lallai na shagala da ruɗin duniya, Yaya Ahmad bansan me ya shiga kaina ba" saita ƙarasa maganar tana kuka, murmushi yayi yace "Ai shi Allah mai gafara ne, inaso duk lokacin da kika ƙara haɗuwa dashi, to ki bashi haƙuri" tace "to Yaya Ahmad insha Allah zanyi yanda kace" wannan karan dariya yayi har haƙoransa na fitowa yace "yauwa ƙanwata farin cikina, yanzu bani labarin yanda kika ƙarasa a gidansu Khadija" murmushi tayi ta soma bashi labari, masha Allah yace, kana ya tada motan suka wuce gida suna hira cikin nishaɗi tamkar Basma batayi kuka ba. Yaya Aryan yana isa gida ya tadda Umma riƙe da kuɗi tana juyasu a hannunta, da sauri ya ƙarasa yace "Umma wannan kuɗin fa? Khadija ta dawo kuwa? dan na zaga sosai ban ga mai kamarta ba, na tambaya ba wanda ya ganta" murmushi Umma tayi tace "Khadija ta dawo yanzu ta shiga bayi, ashe wai wata Yarinya ce ta bigeta a mota suka kaita asibity" nan dai Umma ta labarta masa abinda ta sani, Yaya Aryan ya jinjina lamarin yace "to Allah ya kyauta nagaba, yanzu duk wannan kuɗin su suka bada?" "eh su suka bayar, harda siyayya ma suka yi mata na kayan ciye-ciye" kafin yayi magana Khadija ce ta fito daga wanka tace "sannu da zuwa Yaya Aryan" "yauwa Khadija" nan suka gaisa itama ta ƙara bashi labari, Umma ce ta miƙa masa kuɗin tace "ga kuɗin saika gyara runfarka daga nan ka biya kuɗin haya, sauran kuɗin ka siya mana kayan abinci" Amsa yayi cikin natsuwa yace "Allah ya saka da alkhairi, bari na fita in duba Muntari kafinta sai mu fara maganar gyaran" "to Aryan saika dawo, Allah ya muku albarka" duk suka amsa da "Ameen" kana ya fice. Bayan sallan Magrib jirginsu Prince Shureym ya iso, yana sauka a jirgi motoci na jiransa, ya ƙarasa su tafi gidan president. Bayan sun kai ya wuce falon shugaban ƙasa ya gaisheshi, kana ya wuce part ɗin Ammi ya gaisheta, ya shiga wurin Momy itama ya gaisheta, saiya wuce part ɗinsu Yaya Ahmad can ne masaukinsa, yana shiga falon sai ya faɗa wani ɗaki, wanka yayi ya kimtsa saiya gabatar da sallan Magrib, yana idarwa aka kira sallan isha'i, ya tashi ya gabatar, sai da ya kammala gaba ɗaya, kana ya tashi ya fita falon ya zauna, TV ya kunna sannan ya ɗauki wayarsa ya kira Safeena hira suka shiga yi na kewar junansu. Ɓangaren Basma kuwa, ta sanya aka kawo masa abinci aka jera a kan kafet dake tsakiyar falon, wanka tayi ta sanya doguwar riga na leshi, tayi ɗaurin Maryam Babangida, tayi kyau matuƙa sai ƙamshi takeyi. Basma doguwa ce kaɗan tanada ƙiba shima kaɗan, sai fatarta akwai ɗan duhu mai haɗe da haske, ita ba baka ba ita ba fara ba, tsaka tsaki, sai kuma tana da Boobs dai-dai da jikinta maca ce mai hips sosai, mazaunanta yayi dai-dai da jikinta, cikinta a ɗame yake tamkar bata cin abinci, Basma akwai shape mai kyau da diri. Fuskarta ɗauke yake da dara daran idanu, bakinta ɗan ƙarami ne pink color, sai dogon hanci da yayi tsini har baka, in tayi dariya dimple ɗinta sai ya lotsa, gashin giranta tamkar anyi mata kabin, Basma tanada yalwataccen gashi har gadon baya, mai silɓi da baƙi sosai, Basma ta haɗu domin ko ba makeup fuskarta a haɗe take, Allah ya gama halitta anan. A fili in ka ganta za kayi zaton za tayi nauyi amma ana ɗaukarta shagwal take, kyau dai ta haɗa na Barebari da kuma Fulani. Masu karatu ya kuka hango kyawun Basma, abin ba acewa komai lol😃. A hankali take taku, saboda dogon takalmin dake ƙafarta, a haka ta isa part ɗin su Yaya Ahmad, ta same shi yanata waya ganinta ne ya sashi saurin kashe wayar, galala yayi yana kallon halittar Allah, haɗiya miyau yayi a zuciyansa yace "gaskiya Basma kin haɗu, dole in fara lasar zumanki kan muyi aure, dan bazan jure ganinki haka ba" a fili kuma yace "walcome my Baby" ya buɗe hannu domin taje tayi hugging ɗinshi, rungume hannunta yayi ta gyara tsayuwa, domin ba zata iya abinda yake nufi ba, miƙewa yayi ya isa gab da ita kamshin turarensu ya gauraye gurin, kama hannunta yayi sai ta runtse ido, ƙoƙarin rungumeta ya shiga yi, da sauri ta janye tace "miye haka Yaya Shureym, ka bari kaci abinci mana" dariya yayi yace "afwan gimbiyata ganinki ne duk ya ruɗani, muje ki zuba min" suka je suka zauna, ta zuba masa abincin ya soma ci, yana santi duk a haukansa ya ɗauka ita tayi. Bayan ya kammala ci, saiya miƙe yaje ya wanke bakinsa ya dayo, ita kuma ta zauna akan kushum tana jiran dawowarsa, daya dawo saiya zauna kusa da ita, hannunta ya kama yace "Basma ina sonki sosai, gobe ina son zamu fita zaki rakani wani guri da yamma" tace "ok Allah ya kaimu". Wasa ya farayi da yatsun hanunta, yana mata magana rad'a-rad'a, janye hannun tayi tace "haba Prince ka bari mana" sosa k'eya yayi yace "haba my Basma ya kike yi kamar baki waye ba, ina ce a England kika yi karatu, ai nasan duk kin waye da irin wannan ai" gaban tane ya fad'i tana tambayar kanta "shin me wannan yake nufi?" a ranta, bata ankara ba taji ya rungumeta yana kokorin yi had'a bakinsu guri d'aya, ai da sauri ta fara kiciniyar kwatar kanta, shi kuma ya rik'eta gam, Sallaman da Yaya Ahmad yayi ne ya shigo, shine yasa yayi saurin sakinta, ita kuma ta mik'e da sauri tayi k'ok'arin barin d'akin da gudu, Shureym ne yake kiranta amma ina ta fece a guje, haka ta isa part d'in Ammi tana haki, Allah yasa bata tadda kowa a falon ba, saita wuce d'akinta ta fad'a kan gado, runtse idonta tayi tana mai ambaton Allah, tsanani damuwa ta shiga, yanda Yaya Ahmad yazo ya gansu shine matsalanta. Acan kuma Yaya Ahmad yace "haba Shureym wallahi ba girmanka bane yin haka, iskancin da kake yi a can America sai kace zaka gwada a kan k'anwarka, kuma akan matar da zaka aura?" shafa kansa yayi yace "to meye? ai aurenta zanyi, kuma ma kasan duk abinda zanyi bazan wuce gona da iri ba" tsaki Yaya Ahmad yayi yace "Allah ya shiryeka" bai jira Mai zaice ba ya fice a falon. Bayan Basma yabi, yasan tabbas tana part d'in Amminsa, can ya wuce ya sameta a d'akinta ta kwanta, jin an shigo mata d'aki ne yasa tayi saurin d'agowa ta zauna, Yaya Ahmad ya rufe d'akin, ya jawo wata kujera ya zauna ya fuskanceta, sunkuyar da kai tayi k'asa tana wasa da hannunta, kiran sunanta yayi yace "Basma, ban sanki da hali haka ba, ko da yake nasan shaidani ne shi, amma kuma duk da haka da laifinki Basma, kinje har d'akinmu a wannan shigar kuma ba mayafi, sannan kuma daga ke sai shi, kin san cikon na ukun ku shaidan ne, Basma mace da Namiji ba aso suna keb'ewa haka, in dai ba mata da miji bane, ki daina d'aukar Shureym a matsayinmu, domin mu jininki ne, shi kuma aure zai shiga tsakaninku, dole kiyi taka tsan-tsan dashi domin na fiki sanin waye Shureym". Dago jajayen idonta tayi tace "Yaya kayi hak'uri ba laifi bane, shine ya matsamin, ina k'ok'arin kwacewa ne kazo ka samemu a haka" "eh, Nagani ai, ina so in dai zaki sashinmu, tofa ki tafi da su Na'im da Anwar, karki yarda kina keb'ewa dashi ke kad'ai" tace "to Yaya Ahmad, insha Allah zan kiyaye" "yauwa k'anwata" nan yayi ta mata nasiha har ta saki jiki sukayi barkwanci, kana yayi mata saida safe ya wuce. Basma ji tayi duk Shureym d'inma ya sire mata a rai, bata zata haka yake ba, amma ta d'auki alkhawari za tayi maganinsa. *Washe gari* Da misalin k'arfe 4:30pm na yamma Basma ta shirya cikin riga da sket na kanti, ta sanya lafaya, ba k'aramin kyau tayi ba, yau ta fito a 'yar Maiduguri sosai, fitowa tayi su Anwar da Na'im suna biye a bayanta, suma sunyi shigan kananan kaya sunyi kyau, shekarunsu zai kai 16yrs, har motan Prince suka isa, sai ga shi ya tawo, tun daga nesa yake washe baki harya k'araso, ganinsu twins ne yasa yace "My Basma kin ga yanda kika yi kyau kuwa" murmushi tayi ba tace komai ba, yace "ba dai da su twins zamu tafi ba?" da murmushi a fuskanta tace "tare Zamu tafi, ko akwai Matsala ne?" bata rai yayi yace "amma ai kinsan ba haka mu kai dake ba ko?" kafin ta bashi amsa twins suka ce "Haba Yaya Shureym me mukayi da ba za'a damu ba, mu gaskiya sai munje" Basma ma tace "in ba zamu dasu ba sai dai a fasa tafiyan" k'ara tsare gira Shureym yayi, sai ya bud'e mota bai ce komai ba, haka su ka tafi tare badan ransa ya so ba, har suka dawo Prince bai saki fuska ba. Siyayyan kayan kwalama yayi musu suka dawo, Basma ko a zuciyarta sai dariya take yi. Bayan Sallan Isha'i, Yaya Ahmad ya shigo falon Ammi, bai sameta a falon ba, saiya wuce wurin Basma ya sameta tana danna system d'inta, rufewa tayi suka gaisa, ya samu guri ya zauna tace "Yaya Ahmad kasan yanda nayi yau da mutuminka kuwa?" cikin dariya yace "wa kenan?" tace "Yaya Shureym mana" nan ta kwashe yanda suka yi ta bashi labari, aiko sai ya kwashe da dariya yace "good k'anwata, yanzu ma ko yace kije side d'inmu karki je, kice yazo falon Ammi kuyi hiran, kinga ai ba zai yi shakiyanci anan ba" dariya itama tayi tace "sosai ma kuwa, ai ba zai yi ba, maganinsa zanyi ai tunda shi shaid'ani ne" dariya yayi yace "Mijinki ne dai ba ruwana, yauwa gobe ne fa zaki kawomin patient d'ina ko?" Tace "eh, insha Allah gobe ne zanje har gida na d'aukota, "to Allah ya kaimu" "Ameen". Nan suka yi sallama ya wuce. *Washe gari* Da misalin k'arfe goma na safe, Basma ta shirya ta fita cikin shigar doguwar riga na atamfa ya kamata daga sama k'asa ya bud'e, babu wani kwalliya a fuskanta, ta shiga motanta sai d'aya daga bodyguard d'inta yazo zai yi magana tace "yau ni ka d'ai nake jin fita ba dad'ewa zanyi ba" daga wannan bata sake magana ba ta tada mota tayi gaba. Yau ak'ofar gidan tayi parking ta shiga a nutse, ta samu Deeja tana wanke-wanke, da sallama ta shiga, Deeja ta mik'e da sauri tace "sannu da zuwa Anty Basma" Basma ta amsa cike da fara'a, tabarma ta d'auko ta shinfid'a mata ta zauna, tace "Deeja ina Umma" tace "Umma ta fita mak'ota dubiya yanzu zata dawo, bari na k'arasa wanke-wanke kan tazo" Basma ta mik'e tace "bari na tayaki" da sauri Deeja tace "a'a ki barshi nagode" ai sai ta b'ata rai tace "baki so na samu lada ne nima?" "a'a inaso ki samu, gani nayi daga nin ki baki saba da wahala ba" dariya tayi tace "haka dai kika gani" haka ta sanya mata hannu tana d'auraye kayan tana kifewa a kwando suna kuma hira. Yaya Aryan ne yayi sallama ya shiga, ai sai gaban Basma ya fad'i, da sauri ta waiga aiko tsaraf suka had'a ido nan take gabansu ya fad'i dukansu, mamaki ne ya kama Aryan, sai da suka yiwa juba kallon tsayin minti uku, kana ya je ya zauna kan wata kujera, Deeja ce tace "Yaya ba kaje kasuwan bane?" yace "naje, wani Abu nazo amsa gun Umma" "ok, aiko ta fita amma bazata dad'e ba" a sanyaye Basma ta k'arasa taya Deeja wanke-wanke, ta koma ta zauna, Deeja ta d'au kayan ta kai kicin ta dawo ta zauna gefen Basma, tace Basma ga Yayana Aryan" "ok" tace, Deeja ta kai dubanta ga Yaya Aryan tace "Yaya Aryan ga Basma nan, wanda na baka labari, yanzu ma tazo muje asibity ne a k'ara dubani" murmushi yayi na gefen baki yace "ok na ganta" sai Khadija taji abin yayi mata wani iri yanda Yaya Aryan yace, Basma tace "ina kwana" tayi maganar a sanyaye, amsawa yayi a dak'ile, sai ya mik'e yace "Deeja zan koma, anjima zan dawo, dan yau ba zan dad'e ba a kasuwan" "To adawo lafiya" Basma ta bi bayansa da kallo. Saita juya tace "dama wannan ne Yayan naki?" da murmushi Deeja tace "eh" Umma ce tayi sallama sai duk suka amsa, nan Basma ta gaishe ta, ta kuma bayanin komawansu asibity, Umma tayi godiya tace "to sai kun dawo" Deeja ta d'auko hijabi ta sanya suka wuce. Umma da mamaki tace "ikon Allah, Basma sam bata kyamarmu". *Rahma Ce* (Sirrin 'ya mace group) WhatsApp. [9/29, 12:47 PM] Aysha Galadima: *'YAR SHUGABA*👑 _page_ *8.* _Na_ _*Rahma Kabir*_✍🏾 *Bayan mako guda* Yaya Aryan yanata zuba ido yaga zuwan Basma amma shuru, wani lokacin har tashi yake a kasuwa da wuri domin yazo ko zasu had'u, cikin da bara yake tambayan su Umma akan Basma tazo? sai suce bata zoba, wasa-wasa har aka shafe sati d'aya, sai rashin zuwan nata ya fara sa shi damuwa, Addu'a yake Allah yasa lafiya. Ta b'angaren Basma kula kalau take, domin a cikin satin Yaya Shureym yazo, sun sha soyayya shiyasa bata samun lokaci sosai ba na zuwa gidansu Deeja, domin kullun yamma suna fita da Yaya Shureym dasu Na'im, sai Magrib suke dawowa. Hakan yasa bata samu damar zuwa ba, amma fa tana tunaninsu da kewar Umma sosai, ta d'auki aniyar siyan musu waya, in bata samu zuwa ba ta rik'a kirasu. Yau ya kama ranar Juma'a, bayan Sallan La'asar Basma da Yaya Ahmad suka shirya zuwa gidansu Deeja, Basma tayi shigan lafaya mai kalan fari da green, Yaya Ahmad kuma ya sanya sky blue na shadda hula bak'in dara da takalmi bak'i, sunyi kyau sosai. suka kama hanya suka tafi a mota ba tare da escot ba, hira suke cikin nishad'i tare da kwanciyar hankali, a haka suka isa gidan. Bayan sun isa Basma, ta fito tace "Yaya bari na gaya musu tukunna saika shigo" ya kalle ta da murmushi yace "ba damuwa ina jira". Cikin natsuwa ta Shiga gidan, duk kan su suka amsa, cike da fara'a Umma ta tarbeta, Deeja kuwa tasowa tayi ta amshi jakan hannunta tana mata sannu, Yaya Aryan kuwa basar da ita yayi tamkar bai ganeta ba, Amma fa a zuciyansa yana yaba kyawun da tayi, dauriya kawai yayi ya matse, zama tayi a kan tafarma sai da suka gaisa da Umma kana suka gaisa da Deeja, ta kai kallonta wajen Yaya Aryan tace "ina yini Yaya Aryan?" farin cikin ne ya mamaye zuciyansa jin yanda ta kira sunansa yayi masa matuk'ar dad'i, a fili kuma ya amsa fuska ba yabo ba fallasa a dak'ile, daga nan bata k'ara cewa komai ba domin jikinta yayi sanyi yanda taga ya amsa mata, sai duk ta jita a takure, Waigawa tayi wurin Umma tace "da Yaya Ahmad muke yana waje, nace bari na sanar muku kafin ya shigo" Umma ta fad'ad'a fara'an fuskanta tace "Allah Sarki ai da ya shigo tunda duk gida ne, Kai Aryan tashi ka shigo dashi" da sauri ya mik'e ya fita, cikin minti uku saiga su sun shigo, ya zauna a tabarman da Yaya Aryan ke zaune shima ya zauna gefensa, cikin natsuwa ya gaida Umma, ta amsa cike da farin ciki, Deeja ne ta fito daga d'aki sanye da gyale ta kawo masa ruwan pure water a cikin plet ta aje a gabansa, sannan ta gaishe shi, cikin kulawa ta amsa, Basma na satan kallonshi, taga sai wani kallon Deeja yake kamar zai had'iyeta, ita ko Deeja batasan yana yiba, nan ya shiga yiwa su Umma bayanin zuwansa, yace "Umma kan zancen makarantar Deeja ce, insha Allah ranar Monday zasuje tare da Basma tayi mata registration, saboda yanzu ana farkon fara d'aukan sabbin dalibai, sannan kuma na d'auki Aryan zai yi aiki a company Abbanmu, In ba damuwa" Aryan cikin natsuwa yace "Ayi haka kuwa? wannan dawai niya ai zata yi yawa, ga Deeja ga kuma ni" murmushi Yaya Ahmad yayi yace "d'an uwa karma damu duk yiwa kaine" Aryan yace mun gode Allah ya saka da Alkhairi" Umma ma godiya tayi harda yan kwallanta, Deeja ko murna ne kan murna, itama godiya tayi. Nan fa hira ya b'arke sunata zan tawa, Amma fa banda Basma data takure, saboda irin nuna ko in kula da Yaya Aryan yayi mata, bayan minti talatin da zuwansu, Yaya Ahmad yace zai je wani wuri inya dawo zaizo ya d'auki Basma, nan yayi musu sallama Yaya Aryan ya rakashi waje, Basma ne ta juyo wurin Deeja tace "saiki shirya ranar Monday da wuri zanzo domin mu tafi makarantan, ina so mu gama registration a ranar ne" cikin farin ciki tace "insha Allah tun Asuba zan tashi na shirya da wuri" Umma tace "da dai ya fi miki da wannan shegen barcin asaran da kike yi, to yanzu ga makaranta nan saiki cigaba da barcin mu gani" duk suka sanya dariya, Yaya Aryan ne ya shigo yace "Umma wai ina furan ne? wallahi yunwa nakeji" da sauri tace "af kaga na manta, da an dama Ahmad yasha kan ya tafi, ke Deeja d'auko min kwanan furan nan da kuma kindirmo had'e da sugar" taje ta d'auko, nan Umma ta dama fura da nono da yawa, ta fara zubawa Basma a cup ta aje a gabanta, sannan sauran ta zuba musu. Deeja ta mik'awa Yaya Aryan nashi yace "mik'o min sugar na k'ara" ta mik'a masa ya k'ara, ya juya da kyau ya fara sha, duk suka fara sha banda Basma, Umma tace "ya dai Basma yau na ganki wani iri ko lafiya?" dariya tayi tace "Umma lafiya lau zan sha" Yaya Aryan ya mik'e ya shiga d'aki d'auko wani abu ya bar furan a wurin, yana shiga Basma tayi sauri ta d'auko furansa ta fara sha, Umma da Deeja suka sanya dariya ba tare da sunce komai ba, sun zuba ido suga drama ya Aryan zaiyi, yana fitowa yaga wurin wayam ba cup d'in furansa. D'ago kan da zai yi, ya hango Basma tana sha hankalinta kwance, murmushi kawai yayi ya matsa kusa da ita yace, "bani furana ai ba naki bane wannan" ko d'agowa bata yi ba, ta cigaba da sha, Khadija ce ta kwashe da dariya tace "kai Yaya tunda ta d'auka naka sai kayi hak'uri ka d'auki nata kasha" d'aura fuska yayi ya harareta, sai ta gimtse dariyan da takeyi, Umma dai uffan ba tace ba, k'arshe ma tashi tayi ta shiga kicin dan ta duba tukunyarta, aiko tana shiga kicin ya saka hannu ya wafce kofin furansa, sai Basma ta sa kukan harda shagwab'a, ga hawaye na malala, mamaki ma ta bashi, Amma saiya dake ya koma ya zauna, murza gyad'a mai gishiri yayi, ya zuba a furan ya cigaba da sha, Umma ce ta fito daga abin mamaki, d'aure fuska tayi tace "Aryan ba dai amsa kayi ba?" da murmushi fuskansa yace "Umma ai ba nata bane nawa ne fa, shiyasa na amsa" d'aure fuska ta kuma yi tace "banson shirme ita ma ba k'anwarka bace, shine baka barmata ba" aiko Basma ta samu goyon baya, sai ta kuma narkewa cike da shagwab'a tace "Umma ni nashi zan sha ki ce masa ya bani" Umma taso tayi dariya Amma sai ta dake tace "Aryan bata naka kayi hak'uri kasha nata" shima cikin yana yi na shagwab'a yace "Umma nawa nake so na sha" Umma ganin zasu sa mata hauka sai ta shige d'aki ta basu guri, domin tasan da gan-gan Aryan yayi haka, zuciyarta ne ya fara mata zargin wani abu. Deeja ta dinga dariya a b'oye, haka Yaya Aryan ya shanye furan, harda lashe kofi, Basma na gefe sai kumbure-kumbure take yi. *Nace ohhh su Basma ko ina akaje sai an raba hali lol.*😉😄 Deeja ta mik'e ta shige bayi, Yaya Aryan ya mik'e ya matsa kusa da ita ya d'auki furanta yace a hankali yanda Umma ba zata ji ba, "Ga naki kisha kar kuda ya shanye miki, domin nima ban koshi ba, in baza ki shaba sai na shanye" hawaye cike a narkakkun idonta ta d'ago, sai suka had'a ido, ai gaba d'aya saita saukar masa da kasala, sun d'auki tsawon minti biyar suna kallon juna, ita tana masa kallon tuhuma "meyasa baka yafemin ba" shi kuma yana mata kallon "da sauranki ban hak'ura ba" Shine ya katse kallon ya limshe idonsa, kana ya bud'e ya sakar mata wani shu'umin murmushi, da sauri ta sunkuyar da kai domin tabbas duk gangar jikinta ya amsa, bai kuma cewa komai ba, ya aje cup d'in a gabanta, ya sanya takalmi yace da k'arfi "Umma na fita saina dawo" a cikin d'aki ta amsa masa "adawo lafiya". Yana fita Basma itama ta sanya takami ta bi bayan sa. Shi dai yaji ajikinsa Basma zata biyo shi, sai ya d'aure fuska ya cigaba da tafiya, sai da ya d'anyi nisa da gida kana ya juyo fuska d'aure, yace "lafiya kike bina?" Cike da damuwa tace "ba kaga sak'ona bane" yayi guntun murmushi yace "inna gani me zan miki" marai raice fuska tayi tamkar zatayi kuka tace "Yaya Aryan na baka hak'uri Amma kayi burus, kamar ma na k'ara zuga ka ne" ya kuma d'aure fuska yace "da yake kin raina min hankali ba, zaki wani rubuta min a takarda, to ki sani bai min ba, kaya kuma suna nan na aje, duk lokacin da kika ga dama zaki zo ki d'auka" Cikin rashin jin dad'in abin da ya ce mata tace cikin tsiwa, "dan ma na baka hak'uri, wlh banda kaci darajan su Umma ba abinda zaisa na baka hak'uri, tunda wancen bada hak'urin bai maka ba, yanzu nace Yaya Aryan kayi hak'uri komai ya wuce" dariya ya kwashe dashi yace a ransa "wannan Yarinya ba tad'a kunya zanyi maganinta" a fili kuma yace "a haka zaki bani hak'uri kina min masifa? malama banda lokacin ki yanzu, sai anjima" ya juya zai tafi da sauri ta sha gabansa tace cikin marai raice fuska "Yaya Aryan kaine kake hasalani, to naji zan baka hak'uri, Yaya Aryan kayi hak'uri bazan sake ba" sai tayi shuru, murmushi yayi yace "to naji na hak'ura Amma kad'an, ki wuce gida sai anjima" bai jira me zata ce ba ya wuce da sauri, ita kuma murmushi tayi, tace a fili "Aiko zan maganinka". Bayan sallan Magrib Yaya Ahmad ya dawo, kai tsaye ya shigo gidan, ya same su duka a tsakar gidan, ya kuma gaishe da Umma, ya kalli Basma yace "kin shirya mu wuce ko?" tace "na shirya" Umma tace "ka tsaya kaci tuwo mana, itama yanzu ta gama ci" da sauri ya dubi Basma yace "da gaske kinci?" dariya tayi tace "eh mana na ci" yace "tafd'i, aiko yau za ayi ruwa da k'ank'ara, keda bakya k'aunar tuwo" dariya duk suka yi tace "eh yau dai naci na Umma na mai dad'i" Yaya Ahmad ya mik'e yace "Umma wallahi a k'oshe nake, sai dai wani lokacin inna zo" Umma tace "Ba komai Allah ya kaimu" Basma ma mik'ewa tayi ta d'auki jakanta, suka yi wa Umma saida safe, Deeja tayi musu rakiya har mota. Basma ta ciro waya Android mai kyau ta bawa Deeja tace "ki rik'e a hannun ki, zan dinga kiranku da shi, ina jin lafiyanku" ta amsa tayi godiya sosai. Yaya Ahmad ne ya kalli Deeja yace "Hajiya ba magana ne" murmushi tayi tace "akwai, ai d'azu mun gaisa" yace "hakane Amma ai gaisuwa bata yawa" "eh hakane, to ina wuni Yaya Ahmad" yace "bazan amsa ba tunda saida na rok'a" d'ago kai tayi suka had'a ido sai ya kanne mata ido d'aya, da sauri ta sunkuyar da kai k'asa tana murmushi tace "ayi hak'uri Yaya Ahmad bazan sake ba" dariya yayi yace "karki damu, masu suna Deeja basa laifa dama, amma a wurina" murmushi kawai tayi bata ce komai ba, a yanzu dai ta fara gane ina Yaya Ahmad ya dosa, domin duk had'uwansu saiya tsokaneta. Nan suka yi sallama ya ciro kud'i bandir d'in dubu d'ai-d'ai ya mik'a mata yace "ga wannan ki sha sweet" sai tak'i karb'a, sai da Basma ta sa baki, kana ta amsa tayi godiya, sannan suka wuce. Yaya Aryan sai bayan sallan isha'i ya dawo, bai samu Basma ba, sai hakan bai masa dad'i ba, domin yana son fad'ansu dan yana masa dad'i. Bayan ya gama komai ya shiga d'aki da nufin kwanciya, sai ya ga d'akinsa a gyare, murmushi yayi domin yasan wacce ta gyasa masa, sauya kayan jikinsa yayi ya sanya na barci, ya kwanta akan katifansa, yayi d'ai-d'ai akan filo, ya d'aura kansa baifi minti goma ba yaji baburetin k'ark'ashin filo, da sauri ya mik'e cike da tsoro yana tunanin menene haka, Sam tunaninsa bai kawo masa waya bane, saboda shi baida ita, da sauri ya finciko filon yaga ko miye, waya ce android babba mai kyau a shinfid'e ya gani, mamaki ya cika shi, tace "wannan yarinyar ko mayya ce sai haka, kullun sai ta barni da mamaki, nasan ba kowa ba ne sai Basma" Wayan ne yaga yana haske da alama kira ne ya shigo, da sauri ya matsa kusa ya d'auka ganin Basma a zanen kan wayan ne, yasa shi murmushi yace "mayyar k'anwata" d'agawa yayi ya kara a kunne bai ce komai ba, itama bata ce komai ba har tsayin minti uku, ganin ba zaiyi magana ba yasa tace "Yaya Aryaaan" tsigan jikinsa yaji ya tashi, irin yanda ta kira sunansa taja k'arshe, a kasale yayi murmushi wanda sai da taji sautinsa, itama murmushi tayi tace "dama zance maka ne kayan d'akinka sunyi datti, zanin gadonka yana bukatar wanki da labule, kayi k'ok'ari ka bayar a wanke maka ko kai ka wanke, domin tsafta cikon addini ne, dan d'azun dakyar nake shak'ar numfashi, saboda yanda kayan ke tashi ya kuma had'e da k'amshin turare" Tsananin fushi Yaya Aryan yayi, cike da b'acin rai yace "wai ke ni sa'anki ne? wallahi inda kina kusa sai na miki marin dayafi na rannan, mara kunya kawai" kwashewa tayi da dariya tace "haba Yayana Aryannny, daga gyara kayanka ai ba zai zama sauke mu raba ba, Allah dan ni ban iya wanki bane, dana wanke maka, shiyasa nace bari na gaya maka a wanke" Murmushin takaici yayi yace "ko kin wanke saina sake wankewa" murmushi kawai tayi bata ce komai ba, yace "kuma wannan wayar ta miye zaki aje min a d'aki?" tace "dan na rik'a jin muryan Yayana, shiyasa na aje a gun" a wannan lokacin gyara kwanciyansa yayi gaba d'aya lamarin Basma ya daina bashi mamaki, tana da saurin hasala mutum, tanada saurin sakko da mutum in yayi fushi, Yarinya kamar mai Aljanu, a nushe yace "to Yayan naki yace bai so, ki zo ki d'auki kayanki" cike da shgwab'a tace "uhum ni ban yarda ba, ina son jin muryan Yayana ne, ba zan amsa ba" murmushi ne ya sub'uce masa yace "shi kuma Yayan naki baya buk'atar jin muryanki, dan haka ba zai yi amfani da wayan ki ba, ni saida safe barci nake ji" sai ya gimtse kiran. Saiya rungume wayar a k'irjinsa, haka nan ya tsinci kanshi cikin nishad'i. Basma sam bata ji dad'in gimtse kiran da yayi ba, hakanan ta tsinci kanta da k'ara son jin muryansa, sake kiransa tayi, baburetin d'in wayar ce ya dawo dashi daga duniyar tunanin da ya shiga, sai ya d'aga kiran, cikin kasalan murya yace "Basmaaa, ki barni nayi barci mana" sai taji wani yarrrr, tsigan jikinta ya tashi, gaba d'aya sai ta ji wani irin nutsuwa ya shigeta, tace cikin irin yanayin muryan da yayi magana tace "eh bazan bari ba sai munyi hira" cikin tsokana yace "ke wai mayya ce" tace cikin tsiwa "eh mayya ce Amma a gunka kai kad'ai" dariya yayi sosai yace "to nama na d'aci gareshi yarinya dan yafi k'arfin ki" itama dariya tayi tace "namanka dai zak'i zaiyi kanma a ce hancinka zai d'auki romo sosai" dariya duk suka kwashe dashi a tare, kana cikin dariya yace "kwalelen ki Yarinya" itama cikin yana yin farin cikin tace "ba wani kwalele Yaya Aryany" nan dai sukai ta hira cikin nishad'i- nishad'i da fad'a-fad'a. Sai misalin sha biyun dare suka yi sallama, sun rabu cike da kewar juna, da rashin jin dadin rabuwansu. Aryan da kyar barci ya d'auki shi, yanata tunani bar katai a kan Basma. itama ta b'angaranta da tunaninsa ta kwanta, cike farin cikin duk suka kwana. *Tofa anya kuwa? 🤔muje dai zuwaaa....* *Rahma Ce* (Sirrin 'ya mace group) WhatsApp. [9/29, 12:47 PM] Aysha Galadima: *'YAR SHUGABA*👑 _page_ *7.* _Na_ _*Rahma Kabir*_✍🏾 Basma da Deeja suna tafe a hankali a cikin mota, Basma ta kalli Deeja tace "Deeja dan Allah ina son ki bani tarihinku a tak'aice in ba damuwa" murmushi Deeja tayi tace "ba damuwa Anty Basma" nan ta fara bata labarinsu tas a takaice, har suka isa Asibiti zancen suke yi, Basma tana girgiza kai alaman tausayawa sosai. Bayan sun isa Asibiti, suka tadda Yaya Ahmad a office d'insa, ya duba Deeja ya k'ara bata wasu maganin kana ya sallamsu yace "an gama ba zata k'ara dawowa ba" Basma ce tace "ok Yaya godiya muke" murmushi yayi mata yace a cikin harshen yaran barebari, "Basma, Khadija tana da kyau, ko kin lura da haka kuwa?" da murmushi a fuskanta ta mayar masa cikin yare, "sosai ma kuwa, haka Yayanta yake kuma yama fita kyau, ita tafi kama da Ummansu" murmushi yayi yace cikin sigar wasa "to kina ganin inna zab'eta tayi?" zaro ido tayi waje tace "Yaya talakawa ne fa, amma kana ganin su Ammi zasu yarda?" dariya yayi sosai yace "mai zai hana suk'i yarda, damu dasu duk d'aya muke a gurin Allah, face wanda yafi wani imani, kawai ke zaki wayar da ita sosai ta zama kamar yanda kika waye, sannan zan sata a makaranta tayi karatu, kinga ai shikenan ba mai hanani aurenta" murmushi tayi tace "hakane Yaya Ahmad, ni ai wallahi ka sani farin ciki sosai, dama kuwa kasan abin da nake shiri kenan na maidata makaranta" dariya yayi yace "to na rigaki buk'atar samun Ladan" itama dariya tayi tace "yauwa Yaya Ahmad, ya za ayi ka samar ma Yayanta aiki a company Abbanmu, yana da diploma a computer science, kaga in an d'aukeshi sai ya koma karatunsa, yayi digree da masters, kuma yana aiki ana biyansa salary mai kyau" murmushi yayi yace "shawara mai kyau, kinga mun taimaka su, tunda suna cikin buk'atan haka, kuma dama amfanin Arzikin kenan, in ka samu ka bama na k'asa da kai, zansa ma a k'ara yiwa unguwarsu titi, zamu d'auki matasan unguwan marasa k'arfi mu sanya su a makaranta, dan naga unguwar akwai mabuk'ata sosai" tace "da kyau Yaya Ahmad, wannan shawaran yayi, Allah ya bamu ikon yi" yace "Ameen" duk wannan hiran cikin yaransu na barebari suke yi, Deeja tayi shuru tana saurarensu amma bata fahimtar me suke cewa, computer science d'in da Basma tace, shine ya bata damar fahimtar k'ila hiran da sukayi da ita ne, take gaya masa. Mik'ewa Basma tayi tace "Yaya bari mu tafi" murmushi yayi yace a cikin harshen labaraci "ki kulamin da Matata, karki sake ki gaya mata ba yanzu ba tukun, kuma ina so ki b'oye musu asalinmu, saboda su samu damar sake jiki damu" murmushi tayi tace itma cikin larabci, "ai Yaya bazan fad'a ba, zance musu Mom d'nmu da Dad basa k'asarnan suna Canada, muke Nigeria da sauran family d'inmu, kuma gidan hutuna shine gidan iyayenmu, kaga bazasu gane ba" Cikin harshen turanci yace "good girl" tana dariya suka fita, Deeja dai jinsu takeyi, tad'an so ta fahimci hiran amma bata gane ba saboda batajin labarci sai kalmomi kad'an take iya tsinta. Suna tafe a hanya suna hira a yanzu Deeja ta saki jiki sosai da Basma, koda suna kusan sa'a amma akwai girmamawa na musamman da Deeja kewa Basma, Basma tace "Deeja samu shiga kasuwa siyayya" tace "to Anty Allah ya kaimu lafiya". Sunje Babban shago na saida kayan kanti, side d'in maza suka fara shiga, riga da wando ta siya kala biyar k'ananun kaya, sai manyan kaya shadda da material na maza kala biyar d'inkakku, sai su singilet da gajeran wando guda biyar-biyar, sai takalmi kala hud'u, huda kala biyu, da kuma turare masu k'amshi har kala Hud'u, sai a gogo kala biyu. Aka sanya kowanne a jaka, ta bada kud'i aka sanya musu a mota. Suka shiga side d'in mata nanma kaya ta sanya Deeja ta zaba kananu da kuma lesshi da atamfa, hatta gyale, takalma da d'an kunne duk ta siya mata, sannan ta siyawa Umma nata kayan kala uku da mayafi, takalmi da d'an kunne da sarka, harda turare, Siyayya suka yi sosai kana suka wuce gida. Suna isa suka fara shiga da kaya, Umma ai bud'e baki tayi tana kallon kayan cike da mamaki, saida suka shigo dashi tas, Basma ta ware na Yaya Aryan tace "Deeja ina d'akin Yaya Aryan yake?" Deeja tace "shine can da yake kallonki" tace "d'akin abude yake?" "Eh a bud'e yake kullun" Umma kallonta take kawai ta kasa magana, Basma ta nufi d'akin ta bud'e, ba laifi d'akin ba wari yana k'amshin turaren wuta na tsinke, sai dai d'akin akwai datti da tarkacen kaya, aiko shiga tayi ta bud'e k'ofar, ta fara kauda kaya kana ta samu tsintsiya ta share d'akin, har wani gumi ta had'a abinda ba'a saba yiba, Deeja tazo zata tayata tace ta barshi itama zata iya, tana gama sharan ta kakkab'e zanin katifar ta gyara kana tazo ta kwashi kayan data siya masa ta aje gefe guda, ta fito tana sharce zufa, Umma ne tace "Sannu da k'ok'ari Basma Allah ya miki albarka, ya baki miji nagari, yasa ki gama da duniya lafiya" ta k'arasa maganar tana matsar kwalla, Murmushi Basma tayi ta k'arasa kusa da Umma, zama tayi gefenta a kan tabarma tace "Umma na d'aukeki Uwa a gareni, duk abin da na muku na yiwa kaina ne domin Uwata nayi mawa, kuma Umma meye amfanin kud'in da za'a tara a aje ba'a yi taimako dashi ba, ki d'auka tamkar ke kika haifeni Umma, domin Allah ya riga ya had'amu, iyayena basa nan suna k'asar waje dagani sai Yaya na Ahmad da kuma sauran danginmu, lokaci-lokaci suke zuwa nan domin mu munk'i zama dasu, munfi son zama a k'asarmu, Umma iyayenmu suna bamu kud'in wanda bamu san me zamu yi dashi ba saboda yawansu, kinga kuwa danna bayar wa Alumman Annabi bamu Fad'i ba" Da murmushi a fuskan Umma tace "kwarai kuwa Allah ya saka da alkhairi" "Ameen Umma, kuma nayi magana da Yaya na yace zai mai da Khadija makaranta, yace in gaya muku kafin yazo" Umma cike da farin ciki mara misaltuwa ta rungume Basma, Deeja kuwa tsalle tayi ta dawo kusa da Basma, godiya ta shiga zuba mata sosai tamkar ta biya mata saudiya. Haka sukaita murna suna zuba mata godiya, Basma ta d'auko takadda a jakarta ta shiga rubuta short note, ta bama Yaya Aryan hak'uri akan abinda tayi masa. Tana gama rubutawa ta mik'e ta je ta sanya letter a cikin d'aya daga cikin jakukunan kayan data siya masa, kana ta fito ta d'auki Jakarta tayiwa su Umma sallama, Umma har k'ofar gida ta rakota tana shi mata da albarka tare da addua, Deeja kuwa har mota taraka ta. Basma na isa gida wanka ta yi ta dad'e cikin ruwan zafi tana gasa jiki domin yau ta kwaso gajiya, tana fitowa ta shirya ta wuce part d'in Momynta, ta same ta zaune bisa dadduma ta idar da sallan La'asar, zuwa tayi ta kwanta ajikinta cike da shagwab'a tace "Momy kin jini shuru yau baki nime ni ba?" murmushi tayi tace "ai kwanakin nan naga kamar kinyi hankali ne, kodan basu Leema ne k'ila" dariya tayi tace "kai Momy, dama can ma haka nake, hala su Na'im suna islamiya?" "eh suna can, wai ke kuwa yaushe rabon naga kina karatun al'Qur'ani?" murmushi tayi tace "Momy ina karantawa bayan sallan Magrib da kuma in zan kwanta barci, a wata sau biyu nake saukewa fa" "Masha Allah haka nake so ki rik'a kula da ibadarki sosai" "tom Momy zan kula insha Allah, Momy dama ina son muyi magana akan yarinyar dana bige rannan, sunan ta Khadija" nan ta shiga bama Momy labarinsu kaf da kuma abubuwan da tayi musu, da ma taimakon da take shirin yi musu ita da Yaya Ahmad, Murmushi Momy tayi na farin ciki tace "Basma ban tab'a tunanin kinyi hankali irin haka ba sai yau, wannan abu da kike yi tunani ne mai kyau, nima zan bada tawa gudun mawar akai, sai muyi tarayya a cikin Ladan gaba d'aya, zanga Ahmad saimu tattauna akan gyaran unguwar da taimakon mutanan unguwar, Allah ya bamu ikon yi da iklasi" tace "Ameen Momy, kin amince in cigaba da taimaka musu kenan?" "sosai kuwa na amince, ai in dai wannan ne sai inda k'arfi na ya k'are wajen baki goyen baya, kuma mun taimaka wa Abbanku ne, tunda shike Mulkan k'asatar nan" "hakane Momy" kamar zata gayawa Momy k'udirin Yaya Ahmad akan Deeja saita fasa, saboda ta d'aukar masa alkhawari akan bazata gayawa kowa ba. Haka suka cigaba da hira na 'Ya da Uwa har barci ya d'auke Basma, Momy kuma ta cigaba da lazumi, sai gabda sallan Magrib ta tasheta, sannan duk suka nufi d'aki. Yaya Aryan ya dawo da yamma lis, ya samu Umma tana tuka tuwo, ya gaisheta kana ya nufi d'akinsa, yana tura k'ofa ya shiga yaga daki fes an gyara, bai k'ara tsinkewa ba saida ya hango jakukuna a gefe, da sauri ya juyo ya kalli Umma yace "Umma waya shigan min d'aki kuma jakukunar waye a ciki?" Murmushi tayi tace "ka shiga ka duba akwai sak'on bayani a ciki" Deeja ce tayi tsaraf tace "Yaya Aryan kayanka ne da" bata k'arasa ba Umma tayi mata dak'uwa tace "yi min shuru a wurin nan, ya shiga ya gani mana da kansa, ya tsaya yana tambaya" jikinsa a sanyaye ya koma d'akin, zama yayi dirshen a ledan d'akin, ya shiga fidda kayan dake jakukunan d'aya bayan d'aya, harya isa jakan da huluna da agogo ke ciki, yana ciro hula sai letter ya fad'o, da sauri ya aje hulan ya shiga bud'e letter, gyara zama yayi ya soma karantawa kamar haka *Assalamu Alaikum* *"Yaya Aryan nasan zaka yi mamakin ganin sak'o na, da farko ina mai baka hak'uri akan duk abin da na yi maka kwanaki, hak'ik'a nayi kuskure, kuma naji kunya d'azu sosai, saboda bansan kaine Yayan Deeja ba."* *"Yaya Aryan wannan kayan naka ne, a matsayina na k'anwarka na siya maka, karka d'aukesu a matsayin na raina maka ne, wallahi nayi maka dan Allah ne, domin a yanzu ka zama Yaya a gareni."* *"Dan Allah kar kace ba zaka sanya kayan ba, domin in kayi amfani dasu, hakan ne zai nuna min ka yafemin akan abinda ya faru tsakanin mu, kuma ka d'aukeni k'anwarka. Hakan zai sanya ni farin ciki sosai Yaya Aryan."* *Kanwarka Basma Bulama.* Nagode. Wani irin yanayi Yaya Aryan ya tsinci kansa a ciki, komawa yayi ya d'aura kansa bisa katifa, ya kuma karanta sak'on, yayi ta maimaitawa kusan sau biyar, mamaki ne ya cika shi, zuciyarsa yana harbawa a hankali, ji yayi duk kasala ya rufeshi, lumshe idonsa yayi ya shiga tariyo abinda ya faru a tsakaninsu, nan take yaji ta burgeshi yanda take nuna isa kamar wata *'YAR SHUGABA* salonta ya bashi mamaki yanda tayi saurin sakowa ta bashi hak'uri, sai yaji zuciyansa ya wanke babu sauran jin haushinta da yake yi, hakanan ya tsinci kanshi da k'ara son ganin ta, yana kissima ya salon zai sauya tunda yanzu sun shirya ba fad'a, murmushi yayi wanda ya k'ara bayyana kyawunsa, a bayyane yace "nima naso na baki hak'uri, saboda irin k'ok'arin da kika yi akan Deeja, baki cancanci mari a guna ba Basma, kawai dai munyi abun a cikin rashin sani ne, koda ke kika rafa tsokana ta, amma duk da haka zan ja aji, domin ki gane ni d'in Namijin gaske ne" Dariya yayi wanda ya bayyana fararen hak'oransa, ya tashi zaune ya k'ara duba kayan, duk sun kwanta masa arai, godiya yayi ma Allah, kana ya mai da kayan mazauninsu ya fita zuwa masallaci dan gabatar da sallan Magrib. *_Rahma Ce_* (Sirrin 'ya mace group) WhatsApp. [9/29, 12:47 PM] Aysha Galadima: *'YAR SHUGABA*👑 _page_ *9.* _Na_ _*Rahma Kabir*_✍🏾 *Washe gari* Da misalin k'arfe hud'u na yamma, ya Aryan yayi wanka, sai ya d'auki d'aya daga cikin kanyan da Basma ta siya masa ya sanya, yayi kyau sosai da yake k'ananun kaya ne, sai ya d'auki hulan sanyi ya sanya a kansa saboda gashin kansa. Ya fito yace wa Umma sai ya dawo, Deeja tace "Yaya Aryan kayan nan ya maka kyau, amma meyasa ka sanya hulan nan, ai daka cire zaka fi kyau" murmushi yayi yace "Deeja banyi aski bane, kinga sumana ya taru shiyasa na sanya" murmushi tayi tace "hakane, to sai ka dawo" kana yasa kai ya fita. Tafiya yake bai san ina zashi ba, ya mik'e hanya sanb'al saida ya kai k'arshen layin su kana ya karya kwana, tafe yanke yana tunanin Basma da irin hiran da suka yi jiya, bai ankara ba wata mota ta taho a guje, gadan-dagan tawo kansa, ai ba shiri yayi tsalle ya koma jikin bangon wani gini saura kiris ya fad'a kwata, ya razana sosai, Basma dake cikin motan me zata yi inba dariya ba, da yake motan mai bak'in glass ne, Aryan ya kafa wa motan ido yana jiran wanda yake ciki ya fito, saida ta gama cin dariya sosai, kana ta bud'e ta fito, ido Hud'u suka yi sai ta kwashe da dariya, iya kuluwa yayi sai ya tamke fuska, cikin fushi yace "dama kece kika son bigeni da gan-gan ko? anya Basma ba kida Matsala a kwakwalwa ba kuwa" yana fad'an haka saita tsaida dariyanta tace cikin tsiwa "haba Yaya Aryan ya zaka kamanta ni da hauka, nifa da wasa nayi maka, tun daga nesa na hango ka nace bari na dan tsokane ka, ashe Yaya Aryan haka kake da tsoro" saita k'ara kwashewa da dariya, a yanzu shima dariyan yayi domin Basma ta kai mak'ura wurin shak'iyanci, tace "Yaya Aryan dama fa wurinka zani, ka rakani wani wuri" kallonta yayi tare da tsare gira yace "ni sa'anki ne, kije ki samu Deeja tana gida ita saita raka ki, amma ba dai ni ba" ai nan da nan Basma tayi fuskan tausayi tace "Yaya Aryan ni kai nake so ka rakani" yayi murmushi yace "to bazani ba" b'ata rai tayi kamar zatayi kuka tace "haba Yaya Aryan kayi hak'uri muje ba zamu dad'e ba" ganin zata fara masa kuka yace "to muje". Nan suka shiga mota suka fara tafiya, ta sanya wak'ar larabawa yana yi a hankali, ta juyo tace "Yaya Aryan kayi kyau amma abu d'aya ya b'ata wankanka" murmushi yayi bai tanka mata ba, ai bai aune ba sai yaje ta janye hulan kansa ta b'oye a dayan gefenta, da sauri ya juyo yace "wai ina wasa dake ne?" tuni Basma ta shagaltu da kallon sumansa saura kad'an ta buga motan dake gabansu, da sauri ta gyara tuk'in ta mai da hankali kan hanya, Yaya Aryan ya kwashe da dariya yace "Yarinya taga suma ba irin nata ba ta rikice" dariya kawai tayi bata ce komai ba har suka isa wurin shak'atawa. Parking suka yi duk suka fito, suka jera ba tare da sunce ma juna komai ba, shi dai binta kawai yakeyi, sun isa wani wurin da aka zagayeshi da furanni masu k'amshi, wuri sanyi ga iska mai dad'i, kujerune a ciki da table a tsakiya duk suka zaune, weta ne ya zo da sauri ya tambayesu abinda za a kawo musu, Basma tace "ice cream da shawarma da kuma drink" ta kalli Yaya Aryan tace "Yaya me za'a kawo maka" yace "duk abinda zaki ci shi zanci" murmushi tayi ta gaya ma weta ya tafi kawo musu. Suna fuskantan juna Yaya Aryan yace "dama nan wurin zaki kawoni" dariya tayi tace "eh, saboda in dan saka ka waye, dan naga kamar baka waye ba" hararanta yayi yace "kece dai baki waye ba da kike sanya k'ananun kaya ki fito ko ajikinki wai irin kin had'u" da sauri ta kalli jikinta tace "Yaya kana nufin banyi kyau ba ne?" "eh baki kyau ba saboda shigan bata dace dake ba" tace "Yaya Aryan, na sanya ne saboda naga a mota nake" riga da wando ta sanya sun kamata sai dai rigan ya sakko har gwiwanta amma duk shape d'in jikinta ya fito sai ta yi rolling da gale a kanta ta rufe gashinta" yace "eh, ai ba shiga bane na musulunci mace tayi ta fita" jikinta ne yayi sanyi tace "To insha Allah bazan sake yin shigan na fito ba, amma zan rik'a sanyawa a gida" murmushi yayi yace "da dai yafi miki" tace "Yaya Aryan sumanka tayi maka kyau, meyasa kake rufewa?" ya kalleta suka had'a ido sai da suka kalli juna na tsayin minti uku, kana ya sauke ajiyan zuciya yace "Basmaaa" sai duk jikinta ya mutu ta sunkuyar da kai k'asa, sai taji ta cigaba da magana, "bana son barin suman, kuma yawan askewa yana k'ara yawansa, shiyasa nake yawo da hula, saboda in mutane suka gani suna yawan min magana akai" murmushi tayi tace "Yaya Aryan dan Allah karka aske, zan siyo maka mayuka na maza, da zaka rik'a gyarawa, wlh har sheki zai rik'ayi, ba kaga yanda mazan India suke yi bane" murmushi yayi yace "ni Basma bana son sumar dan a takure nake" marairaice fuska tayi tace "to ko zaka aske, karka aske duka ni ina son ganinka dashi" hararenta yayi, kan yayi magana an kawo musu shawarman. Sai wayar Basma ce ta d'auki k'ara, da sauri ta d'auka ta kara a kunne, tace "My Shureym" saita shagwab'e fuska ta fara shagwab'a, "bayan kasan ina missing d'inka, shine duk yau baka kirani ba ka manta dani" ta b'angaren Shureym kuwa ya shiga lallashinta. Aryan zuciyansa ne ke dukan uku-uku hankalinsa ya tashi, amma saiya dake, ya cigaba da cin shawarman, amma abin mamaki kamar yana cin magani sam baya jin dad'in sa, sunkuyar da kai yayi k'asa, zuciyansa nayi masa zugi, numfashinsa yana fita da k'arfi, dakiya kawai yayi. Basma sun d'auki tsawon minti sha Biyar suna wayan, daga bisani suka yi bankwana ta kashe wayar. Ta kalli Yaya Aryan tace "Yaya kayi hak'uri na d'auki waya ban nima izini ba" d'agowa yayi idonsa ya kad'a ya d'anyi ja, sai yayi mata murmushin yak'e yace "karki damu bakomai" murmushi ta mayar masa, ta mik'a hannu ta d'auko sauran shawarman da ya rage ta soma ci ko ajikinta. Sam bata lura da sauyawan yanayin sa ba, saida ta gama tace "Yaya Aryan" ya d'ago ya kalle, tace "bari muyi salfee mana?" murmushi gefen baki yayi yace "ni bana hoto" shagwab'e fuska tayi tace "ni dai dan Allah muyi" bata jira me zaice ba ta mik'e ta zo bayanta ta tsaya, shi kuma yana zaune, aiko ta kashe musu photo har uku, shi dai fuskansa ba yabo ba fallasa, gaba d'aya zuciyansa a takure yake, tace "gaka kuwa yanda mukayi kyau?" ta nuna masa, ya kalla shima kanshi hoton ya ma kyau yace "yayi kyau" tace "Yaya muje gida yamma yayi sosai". Bayan sun kama hanya, ta ciro hulansa ta bashi tace "Yaya Aryan, gobe in Allah ya kaimu zanzo mu k'ara fita" murmushi yayi yace "Allah ya kaimu" haka ta sanya wani wanka da music na soyayya, sai bin wakar take, shi ko kwantawa yayi a bayansa yana sauraren wak'ar da muryarta ,gaba d'aya ya shiga wani duniya wanda shi kanshi bai san wani irin duniya ya lula ba. Ta sauke shi suka yi sallama, kana ya wuce cike da damuwa a zuciyansa, itama ta wuce cike da farin cikin a zuciyarta mara misaltuwa. Da dare misalin k'arfe goma da rabi, Basma ta kira Yaya Aryan, yana kallon kiran yak'i d'auka, ta kira shi ya kai sau goma amma yak'i d'agawa, haka nan yaji ba zai d'auka ba, domin shak'uwar da zuciyansa yake da Basma, ya fara bashi tsoro kuma ga dukkan alamu ya soma shiga wani hurumi da ba nashi ba, dole ya d'auki matakan kaucewa damuwa. Basma kuka ta shiga yi hawaye wannan na bin wannan, iyaka damuwa ta shiga, da kyar barci da d'auketa. Haka ma ta b'angaren Yaya Aryan, k'arshe ma tashi yayi ya gabatar da sallan nafila yayi Addu'a akan, Allah ya k'are masa zuciyansa da irin abinda ya soma raya masa game da Basma. *Washe gari* Basma da ciwon kai ta tashi, ta samu ta karya tasha magani sannan ta koma barci. Ta wurin Yaya Aryan kuwa ya samu sassauci game da abinda yake ji, ya shirya ya tafi kasuwa kamar yanda ya saba kullun, amma a k'asan zuciyansa yana tuna masa hiran Basma da Shureym sai damuwa ya ziyarce shi. Da misalin k'arfe biyar ya dawo daga kasuwa, da sauri yayi wanka ya shirya ya fita, unguwar ya bari gaba d'aya saboda baya so su had'u da Basma. Ta b'angarenta kuwa ta zo tayi parking in da suka had'u jiya, tayi ta kiran wayan ba'a d'auka ba, kuma ta jira shi bai zo ba har kusan k'arfe shida na yamma, abinda bata sani ba Aryan yana hangen motanta ya b'oye a wani shagon aski, hakanan yaji tausayinta kamar ya fito sai kawai ya basar, haka ta hak'ura zuciyarta na mata zafi ta tuka motan a hankali, idonta na zubda hawaye, ta shiga damuwa na rashin zuwan Yaya Aryan, a haka ta isa gida kamar mara lafiya. Shima Aryan cikin damuwa ya wuce gida bayan tafiyarta, koda Umma ta ganshi ta tambaye shi ko lafiya? yace mata kansa ke ciwo, sai tayi masa sannu. Yau da wuri ya dawo gida ya kwanta, yau ma yak"i d'auka wayarta, a haka ko wanne ya kwana cikin damuwa. *Washe gari Monday* Basma da sassafe ta fito tazo gidansu Deeja, ta samu Deeja ta shirya suka gaisa da Umma, Aryan yana d'aki yana jinsu amma yak'i fitowa, dauriya Basma tayi tak'i tambayar ko yana nan, suka yiwa Umna sallama suka wuce University dake cikin Abuja, da yake ansan da zuwansu basu sha wani wahala ba wajen yin registration d'in, kuma dama president yasa hannu, Deeja an d'auke ta ba tare da zana wani exam ba, ta samu Medicine b'angaren mata (gynecology). Zuwa k'arfe biyu sun gama komai, sai suka kama hanyar gida. B'angaren Yaya Aryan, ya tafi company su Basma, ya had'u da Yaya Naufal kamar yanda Yaya Ahmad ya gaya ma Naufal d'in, Yaya Naufal yayi masa interview, ga mamakinsa duka Yaya Aryan ya amsa masa, gashi dai ba digree gareshi ba amma ya amsa masa duk tambayoyinsa. Ya duba takardunsa sosai, cikin k'asaita da mulki yace "sunana Naufal, a yanda na gwadaka kuma na duba takardunka gaskiya komai yayi yanda muke so, mun d'auke ka aiki, sannan bayan kamar watanni zamu turaka ka k'aro karatu kayi degree da masters, ga wannan kud'in kuma ka samu ka siya kaya na zuwa office, dole ne ka rik'a shiga mai kyau domin zaka rik'a ganawa da manyan mutane, office d'inka shine na b'angaren computer, kai ne mai shigar da komai in an fitar da kaya ko an shigo da su, da fatan ka fahimta" Yaya Aryan cike da farin ciki yace "na fahimta, nagode Allah ya saka da alkhairi" duk wannan bayanin cikin harshen turanci suke magana, kana Yaya Naufal ya rakashi katon office d'insa, mai d'auke da kujeru na alfarma da katon table, ga AC, ga fridge, kai har toilet akwai a ciki, komai dai normal, Yaya Naufal ya gama nuna masa komai ya fice, Yaya Aryan ya zauna kan kujeran table d'in ya juya yana kallon kud'in da aka zubama office d'in, sai hawaye ya soma zarya a kuncinsa, farin ciki da begen son ganin Basma ne ya bijiro masa, ba dan Allah yasa sanadin ta ba, da ba zai tsinci kansa a irin nan wurin ba. Suna isa Basma ta fad'a d'akin Yaya Aryan ta kwanta bisa katifansa, cikin kankanin lokacin barci ya d'auke ta. Deeja ce ta shigo taga tana barci, taso tashinta ta koma d'akin su, amma saita kyaleta ta cigaba da barcin, ta koma wurin Umma tace "Umma Basma fa barci takeyi, da zan tasheta ta koma d'akinmu saina barta" Umma tace "kyaleta ta kwanta ta gaji ne, kinsan yaran masu kud'i basu saba da wahala ba, kuma ma ai d'akin Aryan yafi namu gyaruwa zata fi jin dad'in barcin anan". Khadija tace "hakane kuma" sai suka cigaba da aikin su na girki, Umma na rangad'a musu, tuwon shinkafa miyar kub'ewa d'anya wanda yaji nama. Da misalin k'arfe uku da rabi, Yaya Aryan ya dawo gida daga company su Basma, ya zauna bisa tabarma a tsakar gida, ya gaisa da Umma, kana yace "Khadija kun gama registration d'in?" tace "eh, Yaya mun gama komai, Monday mai zuwa zan fara zuwa d'aukan lectures" yace "masha Allah, Allah ya taimaka" duk suka amsa da "Ameen", Umma tace ya kuka yi ne a wurin da kaje?" murmushi tayi yace "Umma komai Alhandulillah, an min interview, kuma na ci, musamman suka bani office nawa ni kad'ai, nine zan d'inka shigar da komai na company" kud'i ya ciro daga aljihunsa yace "wannan kud'in budi D'ari biyu ne, sun bani na siya kayan sawa kawai na zuwa office, saboda zan d'inga ganawa da mutane, masu amsan yakan company" baki Umma ta bud'e tace "ikon Allah, wannan Abu haka, gaskiya ba abinda za mucewa Basma da Yayanta sai Allah ya saka musu da gidan Aljanna" duk suka amsa da "Amin" Yaya Aryan yace 'gobe insha Allah zan fara zuwa aiki, albashi na kuma dubu d'ari biyu duk wata" ai Umma sai kabbara, ta yiwa annabi salati s.a.w, hawayen farin cikin ta soma fiddawa, Deeja tace "Umma ba kuka za kiyi ba, waraka Allah ya kawo mana dan haka saimu gode masa". Nan ya mik'e ya shiga d'akinsa, ai sai yaci karo da Basma tayi d'ai-d'ai bisa godonsa, gashin kanta ya baje a bayanta, da gani barcin gajiya take yi, murmushi kawai tayi yace a ransa "Basma rigima, wato ba tad'a wurin barci sai d'akina" Wasu kaya ya d'auka, ya fito ya shiga bayi, Basma da tun shigowarsa ta farka tabi bayansa da kallo tana murmushi. Bayan ya fito daga wankan ya wuce d'akin Umma ya sauya kaya, masallaci ya wuce dan yin sallan La'asar, suma su Umma suka gabatar da nasu sallan. Basma ta fito tayi alwala ta shiga d'akin Umma tayi sallah, anan Deeja ta kawo masu tuwo suka ci tare, bayan sun gama ta shirya zuwa gida ta yiwa su Umma sallama ta fito, Deeja ta rakata mota ta wuce. Tafiya take a hankali zuciyarta cike da son ganin Yaya Aryan, aiko tana yin kwana ta hangeshi tsaye inda ta d'auke shi rannan, farin ciki taji a zuciyarta kana ta d'aure fuska tamkar ba ita ba, ta k'arasa tayi parking mota, ba tare da ta ce masa uffan ba ya bud'e motan ya shiga, yana shiga ta tada motan suka wuce ba wanda wace wani Abu, ko wanne da abinda zuciyansa ke saka masa. Yaya Aryan ya katse shurun yace "Basma" juyiwa tayi ba tare ta tace komai ba, sai hawaye ya fara zuba a idonta, ta juga ta cigaba da tukasu.... *Hmmmm wannan abu ya fara bani tsooloooo😉😂 koya zasu kwashe...🤔* *Rahma Ce* (Sirrin 'ya mace group) WhatsApp. [9/29, 12:47 PM] Aysha Galadima: *'YAR SHUGABA*👑 _page_ *10.* _Na_ _*Rahma Kabir*_✍🏾 Wani wajen shak'atawa ta kaisu ba wancen na farko ba, sun samu k'asan wata bishiya suka zauna kan kujeru, ga table a tsakiya, an kawo musu drinks ne da ruwa, Basma ko kallon Yaya Aryan batayi ba kuma tak'i magana, jikin Yaya Aryan yayi sanyi sai ya kwantar da murya yace "Basma fushi kike dani?" kallo d'aya ta mishi a fak'aice sai ta kauda kai gefe, murmushi yayi yace "haba k'anwata ki daina fushi dani mana, bana son ganin b'acin ranki, burina in saki farin ciki har k'arshen rayuwana" d'agowa tayi suka had'a id, idonunta fal da hawaye suna gabda zubowa, da sauri Yaya Aryan ya tara hannunsa a fuskanta domin hawayen ya sauka bisa tafin hannunsa, cikin wani irin murya wanda shi kanshi baisan yanada ita ba, mai dad'i da zak'i yace "Basma karki min asaran hawayenki ya kai ga zuba a k'asa, ba tare da na sharesu ba, ki yafe ma Yayanki, ba zai zake b'ata miki raiba" murmushi tayi na jin dad'i, saita runtse idonta hawayen suka sauka bisa hannunsa, Yaya Aryan ya koma ya zauna, suna kallon juna ya d'aga hannunsa zuwa bakinsa ya lashe digon hawayen ya shanye, Basma saita tafa masa rap rap rap, cike da farin ciki tace "wow, Yaya Aryan yau kawai na tabbatar da cewa ka d'aunke ni jinin jikinka kuma 'yar uwanka" murmushi yayi yace "ke ce baki sani ba amma tun ranar da kika bani hak'uri na d'auke ki a haka, kawai dai na d'an nuna miki ni din Namiji ne" hararansa tayi na wasa tace "ohoo dama shiyasa ka ke basar dani domin kaga rauni na ko, amma ba komai tunda ka fahimci yanda na d'auke ka" dariya yayi yace "sosai na sani, Basma kin zama haske a rayuwana da Ahalina, sanadinki Umma da Deeja da Ni kaina muna farin ciki, kin mana abinda ban san dame zan biya ki ba face Allah ya baki miji nagari, ya kuma baki Aljannah" murmushi tayi najin dad'in abinda yace har cikin taranta, Abu d'aya ne taji ya mata wani iri lokacin da ta tuno da Yaya Shureym, tambayar kanta ta shiga yi, "yanzu inna yi aure shikenan Yaya Shureym ya rabani da Yaya Aryan kenan?" Nan danan taji zuciyarta ya mata wani iri, ganin ta lula duniyar tunani, sai Yaya Aryan ya matso da fuskansa ya hura mata iskan bakinsa, nan take ta dawo hayyacinta, sai duk suka zubawa juna ido, suna baiwa junansu wasu sak'onnin cikin kwayar idonsu, suna karantar wa juna sirrin zuciyansu, sun d'auki tsawon minti biyar kana Yaya Aryan ya kashe mata ido d'aya, da sauri ta sunne kai k'asa alaman jin kunya, a gaskiya duk wanda ya gansu a wannan yanayin, babu abinda mutum zaice illa Aryan da Basma masoya ne. Yaya Aryan ya d'auko kujeransa ya dawo kusa da ita, da muryansa mai dad'i yace "k'anwata meyasa ba kya jin kunyar kallon kwayar ido na? ke ce mace ta farko da take iya kallon ido na harta karanta wasu sirri dake ciki, domin ido naya d'aya daga cikin abinda kewa mutane kwarjini" murmushi tayi kawai ba tace komai ba, ya cigaba da cewa "Amma na fahimci idanunmu sun fara sanin sirrin dake cikin juna, kema haka idonki yake kamar nawa" Basma sunkuyar da kai tayi k'asa, bata tab'a jin nauyi ko kunyar wani namiji ba sai akan Yaya Aryan, wasa take da yatsun hannunta, ta kasa motsi mai k'arfi, gaba d'aya tanajin ta a cikin sabon yanayi da bata tab'a jiba game da wani d'a namiji sai akan Yaya Aryan, a yanzu kunya da kwarjininsa ke tasiri a jikinta, Yaya Aryan ya kira sunansa yace "Basma kinyi shuru ko yau ba kya jin tsokana ne, magana da kuma fad'a?" murmushi tayi tace "ai Kaine kake magana, tun d'azu kake wasu bayanai da ban fahimcesu ba" murmushi yayi yace "kina so ki sansu?" tace "eh ina so" yace "to d'ago fuskanki ki kalleni, zaki fahimci abinda nake nufi acikin ido na" ta d'auki minti d'aya kafin ta d'ago fuskanta, suka had'a ido ko wanne fuskansa da murmushi, sakonni suke zubawa zuciyoyinsu, ko wanne idonsa yayi tamkar mangyada aciki, bugun zuciyarsu yana buguwa a hankali, zan iya ce muku suna bugawa kusan a tare, idonun su yana k'eftawa a hankali tamkar ba zasu rufe ba, numfashinsu yana fita a hankali kamar basa cikin duniyarmu, sun d'auki tsawon minti bakwai, kana Basma ta yi ajiyar zuciya ta sun kuyar da kai, shima Yaya Aryan ajiyan zuciya yayi, cikin wani irin murya kamar yana rad'a yace, Basma kin fatimci abinda nake nufi yanzu?" murmushi tayi kawai ba tace komai ba. Wayar Basma ce tayi ringing, Yaya Shureym ne ya kirata, a wannan lokacin sai taji sam bataji dad'in kiran nasa ba, kamar ba zata d'aga ba, saita d'auka suka gaisa, yau hiran nasu sama-sama suka yi, hakanan taji bata son magana dashi, bayan ta gama ta kashe wayar juyowan da zatayi sai taga ba Yaya Aryan a gun, gabanta ne ya fad'i, ta fara tunanin ko ta b'ata masa raine akan d'aukar wayan, mik'ewa tayi ta hangoshi can yana wasa da ganyen wata bishiya, wurin ta k'arasa tace "Yaya Aryan" da sauri ya juyo idonsa ya kad'a ya d'anyi ja, kan ta kuma magana ya d'aura hannunsa bida leb'ensa yace "shiiii, kin gama wayan?" cikin yanayin rashin jin dad'i tace "eh Amma kayi hak'uri" murmushi yayi yace "hak'urin me zanyi, ai baki laifi ba, da mijinki kike waya fa to me zaisa raina ya b'aci" gabanta ne taji ya fad'i "dammm", hakanan taji maganar da yayi bai mata dad'i ba, tace "Yaya Aryan ba mijina bane fa kawai dai saurayina ne" murmushin yak'e yayi yace "Amma ai aure za kuyi" yana gama fad'an haka yayi gaba ya barta a tsaye, Basma ji tayi zuciyarta ya mata ba dad'i, hawaye ne ke son zubo mata, da sauri tabi bayansa tasha gabansa tace cikin shagwab'a. "Yaya hawayen zai zubo" dariya ta bashi Amma ya dake, yace me ya kawo hawaye, keda kika gama shan soyayya da mijinki" ai tuni hawayen ya soma zuba, sam bata k'aunar Aryan na fad'an haka, matsawa yayi gab da ita cikin salon muryansa mai kashe jiki yace "wlh karki kuskura hawayenki ya sauka k'asa, domin saina mugun sab'a miki, hawayan Basma mai daraja ne a gun yayanta Aryan." Da sauri ya tara hannunsa biyu yace "duk lokacin da kike jin kuka koda bama tare ki rik'e kukan, sai mun had'u kiyi shi akan hannnu na, domin in maida shi cikina". Murmushi tayi tace "tom na bari Amma saika daina cemin Yaya Shureym shine Mijina" dariya yayi sosai yace "dama a kan shi zaki min asaran hawayanki tom karki k'ara" yatsansa yasa ya lakuto hawayenta ya sanya a baki yasha, saida ya raba fuskan da hawaye kana yace "muje gida". Sun kama hanyan zuwa gida, Basma tace "Yaya Aryan wlh da za'a barni dana kwana a gidan ku" Murmushi yayi yace "saboda me zaki kwana mana a gida?" "saboda kawai in tashi inga Yaya Aryan, in nayi kuka ya shanye min hawayena" dariya yayi sosai yace "tom bazan k'ara sha ba, kuma mun b'ata" fuskar tausayi tayi yace "wlh bamu b'ata ba, muna nan a tare, Yayana ba fad'a" duk suka kwashe da dariya. Cikin farin ciki da nishad'i suka isa gida, a wannan rana kamar karsu rabu ko wanne yana jin kewar d'an Uwansa. Tun daga wannan rana Yaya Aryan da Basma suka d'inke, rana d'ai-d'ai ne basa fita wurin shak'atawa. Aryan ya kama aiki gadan-gadan wanda a sanadin zuwansa company ya k'ara hab'aka, Deeja kuma tana ta zuwa makaranta, a yanzu soyayya take sosai da Yaya Ahmad a waya, wani lokacin yakan zo hira, Basma ta rako shi, itama dan su sha hira da Yaya Aryan. Umma da Yaya Aryan sun san soyayyan Yaya Ahmad da Deeja, abinda ke basu tsoro shine, kar gaba iyayen su Basma suk'i yarda ya aureta, domin su talaka ne, Yaya Ahmad ya gyarawa su Deeja gida, anyi fenti an gyara gidan yayi kyau, an zuba musu sabon furniture's. Yaya Aryan ya siyan musu kaya da komai na abincin, da kud'in albashinsa na farko dana biyu, yanzu ko sun fita da Basma shi yake musu siyayya, ya sauya waya ya mai dama Basma nata. Shak'uwa mai k'arfi ya shiga tsakaninsu, Basma ba tada abokin hira sai Yaya Aryan, video call, charts da kuma zuwa wurin shak'atawa, duk tare suke komai, gaba d'aya ta sauyawa Yaya Shureym, wayansa da kyar take d'agawa, shima da yake yanada wacce yake so sai ya daina damuwa da ita, dama shi abinda yasa ya rik'e wuta, ko zai tusa mata son shi ya samu yana rage zafi da ita. Bayan wata uku Basma da Yaya Aryan lamarinsu ya wuce tunanin kowa, basu tab'a furtawa juna kalmar So ba, Amma kuma idanun su, sassan jikinsu, jini, b'argo, da tsoka sun gama zama d'aya, sun tabbatar da in ba d'aya ba rayuwa, amma duk da haka zuciyansu yak'i ya basu damar yarda da abida jikinsu ke fad'a musu. Yau ya kama Lahadi, Yaya Aryan da Basma suna zaune bisa dadduma a wurin shak'atawa, hira suke na nishad'i, wayar Basma ya d'auki k'ara, cikin rashin damuwa ba tare da ta duba mai kiran ba saita d'auka tare da sanya hands free, muryan Yaya Shureym taji yace "My Basma nazo yanzu ance kin fita kina ina ne? ni fa yau na zo muyita ta k'ara, gaba d'aya kin sauyamin kin shareni, kin barni da missing d'inki, Basma ina cike da shauk'inki mai yawa, dan Allah Basma ki bani had'in kai ko da sau d'aya ne muyi rayuwa, wlh bazan bari kowa ya sani ba, kuma kinga Aure za muyi, inma kina tsoro miyu a k'asar nan saimu fita England muje can mu huta" Tsoro, fargaba, damuwa ne suka ziyarci Basma, wani zafafan hawaye ke fita a idonta, jikinta ya d'auki rawa, sam bata zaci abinda zai ce mata ba kenan har tabar wayan a hands free, Yaya Aryan mik'ewa Yayi da sauri ya fizge wayan ya bugata da k'asa, komai na waya ya tarwatse, Basma toshe kunne tayi saboda k'aran fashewan wayan, Yaya Aryan sai huci yake kamar wani zaki, sanya takalmi yayi ya fara tafiya, ya rasa ina zai sanya ransa yaji sanyi, ya d'anyi nisa a tafiyan ya shiga cikin mutane, da gudu Basma ta ruga ta rungumeshi ta baya tana kuka, tace "Yaya Aryan wlh ban tab'a yin wani Abu ba, Yaya Shureym ya sha kawo min farmaki da irin wannan maganar amma nak'i amincewa da k'udurinsa, wlh tun lokacin ya fara fita a raina ni sam bana Sonsa" Aryan ya b'abb'are hannunta daga jikinsa, ya juyo da ita gabanshi ya tsinketa da kyakkyawan Mari guda biyu, nan da nan hankalin mutane ya dawo gunsu, Ya matsa gab da ita yace "Basma kalli ido na ki gayamin abinda kika gani a ciki yanzu" idonta na zubda hawaye ta dafe kumatunta tace "Yaya Aryan kayi hak'uri wlh ban aikata komai ba" cikin fushi da fad'a ya daka mata tsawa yace "Basma me kika gani a idona ki gayamin" tace "idonka yayi ja" yace "Basma kukan zuciyana ne ya bayyana a idona, kina son ki kasheni ko" ya k'arasa maganar muryanshi na rawa, ido ta zaro waje tace "Yaya Aryan ni bazan kasheka ba" lumshe ido yayi ya bud'e, cikin kasalalliyan murya da rauni yace "Basma ina sonki, ina k'aunarki" idonsa ne ya kawo kwalla yana gabda zubowa, sai Basma ta tara hannunta tace cikin kuka "Yaya Aryan nima ina sonka, ina k'aunarka, kaine rayuwata, karka min asaran hawayenka, wanda ban tab'a ganinsa ya fitaba sai yau, ka gau-gauta mayar min da sauran ka adana min su, sai lokacin farin ciki ka fiddamin su" sai hawayen ya d'iga a hannunta, bakinta takai ta shanye su, hannunsa ta kama tana jansa suna tafiya, Yaya Aryan binta yayi da kallon mamaki, gaba d'aya Basma ta bashi mamaki da maganarta. Mutunan dake gurin sai suka fara tafa musu, lallai sun bada salo da kowa yayi sha'awarsu, haka suka bar wurin su ko ajikinsu, kowa na fad'an albarkacin bakinsa. Bayan sun kama hanyan gida Yaya Aryan yace ta samu guri tayi parking za suyi magana, bata masa musu ba ta samu guri tayi parking, yace "Basma ina so ki sani tun ranar dana fara tozali dake da kika tofamin miyau, wani Abu ya d'arsu a zuciyana akanki, a da ina tsammanin k'iyayya ne, sai daga bata na gane ashe So ne, ban tab'a jin d'an d'anon So akan wata mace ba, sai akanki Basma, dan Allah Basma ki kulamin da kanki da rayuwanki, domin kece rayuwata" Farin ciki ne ya lullub'e Basma, yau ta gasgata abinda gan-gan jikinta yake gaya mata akan Yaya Aryan, tace cikin jin kunya "Yaya Aryan karka damu, insha Allah zan kula maka da kaina da kuma mutunci na, kai ne rayuwata nima, kai kad'ai nake gani a idona na kasance cikin farin ciki, dan Allah ka rik'e min Amanar zuciyata, domin kaine mutum na farko da ya bud'e shafukan So da K'auna a ciki, kuma har abada kai ne mutum na farko kuma na k'arshe ba na biyunka" Murmushi yayi yace "Kinsani farin ciki Murmushi na, amma fa ina da kishi, sai ki san yanda za kiyi da Shureym" murmushi tayi tace "my Aryan karka damu zan gayawa ya Ahmad komai". Cikin farin ciki suka k'arasa gida, yau Yaya Aryan ji yake ya sauke wani abu mai nauyi a zuciyansa, haka ma Basma yanzu ta tabbatar Aryan nata ne. *Da dare* Basma ta tafi wurin Yaya Ahmad ta sameshi yana aiki a system d'insa, sai ta gaishe shi, kana ta samu guri ta zauna tace "Yaya Ahmad nazo muyi magana ne" cikin kulawa yace "ina jinki Basma" gyara zama tayi ta soma gaya masa duk abinda Yaya Shureym ke gaya mata, hankalinsa yayi matuk'ar tashi, nan ya shiga niman number Shureym, amma bai shiga ba, cikin yanayi na damuwa ya shiga yi mata fad'a akan meyasa bata gaya da wuri ba, fad'a da nasiha yayi mata sosai kana yace "ina ganin zan gayawa su Momy a sanya bikin kawai ayi kowa ya huta" da sauri Basma ta kalli Yaya Ahmad bakinta har yana rawa tace "Yaya Ahmad wlh bana sonsa bazan aureshi ba na tsaneshi" ta k'arasa maganar cikin damuwa... _*Su Basma da Aryan an shiga lanbun masoya, gaskiya fa salon soyayyanku ya bada kala, koya kuka ce masu karatu...*_ *Rahma Ce* (Sirrin 'ya mace group) WhatsApp. [9/29, 12:47 PM] Aysha Galadima: *'YAR SHUGABA*👑 _page_ *11.* _Na_ _*Rahma Kabir*_✍🏾 Yaya Ahmad yace "Basma auren ki da Shureym dole za'ayi shi, tunda iyaye sun riga sunyi magana, kuma da an d'aura shikenan zai daina wannan iskancin nashi" hawaye ne ya sauka a kuncinta tace "Yaya Ahmad bana fatan auren Yaya Shureym ni ina da wanda nake so, kuma in ba a bani shima wlh Yaya zaku rasani, domin zan mutu" a razane ya kalleta yace "Basma kina da hankali kuwa? waye kike So haka? waye shi kuma d'an gidan waye?" Cikin kuka tace "ni Yaya Aryan nake so, kuma in ban aureshi ba zan iya mutuwa" a razane Yaya Ahmad ya mik'e tsaye yace cikin kad'uwa, "a'a Basma, a'a Basma, karki ce za kiyi sanadin rabuwar family d'inmu, kinsan yanda Shureym yake a wajenmu, yaron Yayan Ammi ne, karki ce za kiyiwa Ammi haka, plss ki d'auka mafarki kike da sanin Aryan, ki gaggauta cire Aryan a ranki" a razane ta d'ago ta mik'e tsaye tace "Yaya Ahmad bazan iya ba, wlh Yaya Aryan nake so" da gudu ta fita daga d'akin tana kuka, lanbun gidan ta nufa taje ta zauna, kuka take kamar ranta zai fita ba tare da sauti sosai ba, Yaya Ahmad cikin sauri ya isketa a gun, dan yasan tabbas ba zata koma part d'in Ammi ba a haka, zama yayi gefenta ya kama hannunta shima a zuciyarta yana gasgata lallai Basma da Aryan ta dace, domin Mutumin kirki ne ga Addini da sanin yakama, a d'an zaman da yayi dashi baiga wani aibu a gunsa ba, sai dai matsala d'aya ne, su Ammi ba zasu yarda Basma ta kawo wani Mijin ba, sai Shureym, sannan kuma Aryan ba d'an kowa bane shi, baya tunanin su Ammi zasu yarda ta auri talaka. Yace "Basma nima ina son ki auri Aryan, amma kin san hakan bazai yuwuba a wurin su Ammi" cikin kuka tace "Yaya zai wuyu tunda ina sonsa, kai zaka taimaka na aureshi kamar yanda zan taimaka maka ka auri Deeja" nisawa yayi yace "karki damu zanyi wani Abu a kai, ki bani lokaci" sassauta kukan tayi ta share hawayenta tace "Nagode Yaya Ahmad, Allah ya mana jagora" "Ameen" yace, kana ya rakata part d'in Ammi ya koma d'akinsu cike da tunani barkatai, da damuwa fal zuciyansa. Lallai yana tausayin Basma kuma yana sonta fiye da kansa. dole yayi k'ok'arin sama mata mafita, da wannan tunanin har barci ya kwashe shi. *Bayan kwana biyu* Basma sun cigaba da soyayyansu, wanda a yanzu basa b'oyeta ko a gaban waye, Umma ta kad'u sosai data fahimci haka, kiran Yaya Aryan tayi, ta masa fad'a akan yabi a hankali Basma ba tsaran aurensa bane, dole ya iya takunsa, hankalin Aryan ya tashi yace "Umma wlh ina son Basma ki mana addua, domin Addu'anki yana da matuk'ar tasiri a garemu" Umma tayi ajiyar zuciya, ta sanya musu Albarka, can kasan zuciyarta tana tausayawa yaranta, domin tasan iyayansu Basma ba zasu yarda da auren su Deeja ba, saboda su d'in ba kowa bane, talaka ne futuk. Haka Yaya Shureym ya k'araci zama a gidansu Basma bai samu fuska a gunta ba, ko ya kirata bata d'agawa, haka ya tattara ya koma Kano. *To bari na waiwayi wajensu Leema da Meena.* Leema tana kano a takure take, domin bata samun sakewa sosai kullun tana gida, in zata fita saida kuyangi da dogarai, hakan yasa taji duk zaman Kano ya gundureta, ta fata tunanin komawa Abuja, in sha'awarta ta motsa kamar za tayi hauka, wataran a sace take fita tayi b'adda kama taje su had'u da Jalal, su gama shek'e ayarsu ta dawo gida a gau-gauce. A daddafe ta iya kaiwa har wata hud'u a Kano, yanzu ta gama shirya kayanta da yawa domin komawa Abuja, in kuma ta koma bata tunanin dawowa, sai dai ta rik'a zuwa tana gaishe da iyayenta. Haka ma b'angaren Meena, Alhaji Ibrahim mahaifinta mutum ne mai sanya ido sosai kan yaransa, hakan ne yasa Meena bata fita saida dalili mai k'arfi, Yaya Jamal ya sanya mata ido shima domin yaga take-takenta akwai rawar kai, Meena in son shan syrup ya motsa mata, rufe kanta take yi a d'aki taita kuka tana buk'atar abinda zata sha, dakyar barci ke d'aukanta, in ta farka shikenan ta dawo dai-dai, hakan yasa ta samu wani shed'ani d'an unguwarsu, suka tsadance yana siyo mata syrup a sace ya kawo mata, sai ta bashi kud'i mai yawa, haka zatai ta maneji dashi harya k'are, gaba d'aya zaman Kaduna ya gundureta, saita soma had'a kaya dan komawa Abuja gaba d'aya, ita sam ba zata zauna a Kaduna ba, waya sukayi da Leema, suka gayawa juna matsalansu, nan take suka yanke shawaran barin gidan iyayensu a gobe in Allah ya kaimu, domin ci gaba da rayuwan freedom da suka fara a England. *Washe gari* Da safe Meena tayi sallama da iyayenta, dama ta riga ta sanar musu zata koma Abuja, jirgin k'asa tabi, daga gidan president aka aiko mota ya d'auke ta. Leema ma haka ta sauka a airport, mota daga gidan President yazo ya d'auketa. Dukansu suna zaune a falon Ammi suna shan farfesun kifi, Ammi ne ta fito tace "Leema wai ku baza ku zauna guri d'aya ba, baku nan baku can, ni dai naga alama aure kuke so, bari anjima zan samu president in sanar masa, sai a sanya rana mu fara shiri kowa ya huta" bata rufe baki ba Leema tace "taf wlh Ammi aure ba yanzu ba, munyi k'anana" Meena tace "gaskiya kuwa aure sai mun kai 30yrs" Basma dai murmushi tayi kawai domin ita a yanzu auren take so amma fa da Aryan d'inta, Momy ce tace "lallai yaran nan da sauranku, wlh baku isa mu zuba muku ido ba har kukai lokacin da kuke so, aure kam kuma fara shiri" tana gama fad'a ta mik'e ta wuce d'aki, turo baki su Meena sukayi, su a dole basa so, Basma ce ta kallesu tace "dama dai kun bar wannan shirman, domin dai aure shine riban ko wace mace" tana gama fad'a ta mik'e ta wuce d'aki tana murmushi, kallon mamaki suka bita dashi, daga bisa ni suka tafa Leema tace "nifa Basma ta sauya, ko ke baki ga a lama ba? Sam ba ji da kai, ba shan k'amshi, duk wani mulki ta aje, anya babu wani abu a k'asa kuwa?" Meena tace "ita ta sani dai, dan ni ba zanyi aure yanzu ba" haka suka mik'e tare, d'akin Basma suka Shiga sun sameta bisa gado tana chart, ba wanda ya kulata suka haye gadon suka fara hiran yanda suka yi missing zuwa clup, yau sunyi masa shiri na musamman, Basma na jinsu bata ce musu k'ala ba. Bayan sallan la'asar suka shirya sai gidan hutun Basma, Basma bata bisu ba, sun wuce tare da escot, ita kuma ta wuce wurin masoyinta, suka had'u a in da suka saba had'uwa, suka wuce wurin hutawa domin su samu yin hira mai dad'i. Sai misalin k'arfe shiga na yamma suka yi sallama da Yaya Aryan ta wuce gidan hutun da sauri, domin tana son yin wanka a swimming pool, dan ta kwana biyu bata yi ba. Tana isa ta samu su Meena a wajen, haka itama ta shiga ta soma wankanta, Leema ce tace "Besty wai yane naga duk kin sauya ne, ko akwai abinda ke damunki ne?" murumushi tayi a ranta tace "soyayyan Aryan ya sauya ni" a zahiri kuma tace "Me kika gani besty, ina nan a Queen Basma kamar yanda kuka sanni" Meena ce tayi caraf tace "ba wani nan, da akwai abinda ke going wanda bakya so ki gaya mana, sam ban gane sauya wanki akan zancen aure ba, ko kuma soyayyar Yaya Shureym ke fizgarki" nan take Basma ta b'ata rai, bata ce komai ba, ta cigaba da wankanta, Leema da Meena suka had'a ido sai suka kwashe da dariya, hiransu suke bata tanka musu ba, harta gama ta bar su ta nufi d'akinta. Magrib ya gabato ba halin yin rawa, shiyasa ta wuce d'aki dan gabatar da Sallah akan lokaci. Bayan k'arfe takwas na dare kamar yanda suka saba fita, yau ma cikin shirin doguwar riga masu fidda tsiraici su Leema suka sanya, Basma harta d'auko wata yalolon riga wanda duk rabin cinyarta a waje yake, sai zuciyarta ya karaya saboda da tunawa da tayi da Yaya Aryan, dole yasa ta maida ta d'auko wata doguwar riga mara tsagu, kuma mai kauri ta sanya, duk da haka tana jin wani iri, zuciyarta na gaya mata kamar taci amanar Yaya Aryan, haka dai ta shirya, ta taje sumanta ta sakeshi a bayanta, ta d'aura hular Queen, sai ta fito a Queen Basma tamkar yanda take a da, tayi kyau sosai, haka sukaita d'aukar photo kafin nan suka wuce. Kamar yanda suka saba, Leema dama Jalal yana Abuja, cikin k'ank'anin lokaci ya bayyana, yazo suka tafi cikin hotel, Leema kuwa cikin group d'in su na mashaya ta nufa, nan suka soma ihu da kalamai masu dad'i, da irin missing d'inta da suka yi, Basma dai yau a d'arare take ta kasa sakin jikinta, duk hankalinta yaki kwanciya gani take kamar Yaya Aryan zai bayyana a gurin, dakewa tayi ta mik'e ta nufi saman step da abokan rawarta, suka fara cashewa cikin salo mai ban sha'awa. A can gida kuma, Momy ta shiga part d'in Ammi domin ta kira su Meena, zata sanya su aiki a system d'inta, koda ta shiga wayam, da yake Ammi yau ita ke da girki tana part d'in president, mamaki ne ya cikata, sam bata san sun fita ba, kiran wayansu tayi amma duk a kwashe, girgiza kai tayi tace a fili "wato Basma bata tashi rashin da'a sai su Meena sunzo, yau kenan a gidan Hutu zasu kwana, anya yaran nan suka aikata Alkhairi kuwa? amma zan d'auki mataki" sai ta ja tsaki ta fice rai b'ace. Sai misalin k'arfe sha d'aya na dare Basma ta dawo hayyacinta, tunda ta soma rawa saita manta da duniyar da take ciki, Aryan ya fad'o mata a rai a zabure ta fita daga hol d'in ta shiga mota ta rufe, wayarta ta ciro ta kunna, sak'oninsa ne suka fara shigowa har kusan biyar, kan ta kaiga bud'ewa kiransa ya shigo, a tsora ce ta d'auka tamkar mara gaskiya tace "My Aryan lol, afwan wayana ta mutu ba chrgy ne" murmushi yayi tare da ajiyar zuciya yace "Alhamdulillah tunda lafiya kike, amma Basma baki tab'a min k'arya ba sai yau" damm gaban Basma ya buga, a tsorace tace "k'aryan me nayi baby lol?" yace "saboda tunda nake dake wayoyinki basu tab'a mutuwa babu chrgy ba sai yau, domin wayoyinki uku ne kuma layi daban-daban" jikinta ne ya d'auki rawa cikin rawar murya tace "am am dama" tsawa ya saka mata "yimin shuru karki b'atamin rai, ina kika je?" nan take fitsari ya kamata tace "naje gidan Hutuna ne ni da su Meena" murmushi yayi yace "good, to kinga abinda ya sa kika kashe waya, saboda yau su Meena sunzo har kin fara mantawa dani, haba Basma kinsan kuwa halin da kika sani dana ji wayarki a kashe" marairaice murya tayi ta shiga bashi hak'uri, ajiyar zuciya yayi yace "Basma babu komai banyi fushi ba, sai dai zan rubuta wannan ranar a cikin tarihin rayuwana, ranar da Basma ta fara min k'arya, amma ki kiyaye, kuma ki tabbatar kin ware min lokacina, domin na lura sai na dage miki akan su Meena, dan naga zasu rage soyayyar mu" murmushi tayi ta kuma bashi hak'uri da kalamai masu dad'i har ya sakko, sukayi hira mai dad'i, hakan ya d'auke su har kusan k'arfe d'aya, kana suka yiwa juna sallama. Sai misalin k'arfe uku na dare suka koma gida, ko wacce d'akinta ta nufa ba ko tub'e kaya duk suka fad'a gado sai barci. Yau kusan kwana biyar kenan su Basma basa kwana a gida, kullun sai sunje club, Basma tana k'ok'arin ki yayewa Yaya Aryan, domin time d'in wayansu na dare nayi take fita a hol, taje susha hira a waya. Ta b'angaren Momy kuwa abin yana matuk'ar damunta, in suka fita da yamma sai da safe suke dawowa gida, sam bata nuna musu ta sani ba, kuma bata gayawa kowa ba, yau tayi shirin bin diddiginsu, Yaya Ahmad ta kira yazo sameta a d'aki, suka gaisa, bayani ta shiga yi masa akan su Basma, mamaki k'arara ya bayyana a idonsa, domin bai tab'a tunanin hakan zai faru ba, duk yawan security dake gidan, Momy ta gama gaya masa tsaf, tace "ina so yau kaje gidan hutun Basma, ka gano min meke faruwa" ajiyar zuciya yayi yace "insha Allah Momy zanje, domin ni abin nasu ma mamaki ya bani, a ce wai harda Basma, duk yanda akayi su Meena ne suka sauya ta" murmushin takaici Momy tayi tace "ba ruwansu duk halinsu d'aya, ko da can ma haka suke yi" "To Allah ya shiryesu, bari mu gani zuwa dare in basu dawo ba, sai na d'auki Naufal muje tare dashi". *Rahma Ce* (Sirrin 'ya mace group) WhatsApp. [9/29, 12:47 PM] Aysha Galadima: *'YAR SHUGABA*👑 _page_ *12.* _Na_ _*Rahma Kabir*_✍🏾 *Da Dare* Bayan sallan Isha'i, Yaya Ahmad ya nufi d'akin Momy ya tambaya ko su Basma sun dawo, Momy ta shaida masa masu dawo ba, da mamakin hakan yabar part d'in Momy, ya kira Yaya Naufal a waya yace masa ya fito ya raka shi wani guri, cikin sauri ya fito suka kama hanya. Ta b'angaren Basma kuwa sun gama shiri tsaf sunyi hotunan da suka saba, sai suka fito haraban gidan suka shiga mota, mai gadi ya bud'e musu gate, d'aya bayan d'aya suka fice, wanda yayi dai-dai da shigowan Yaya Ahmad layin, ganin motocin su ne, sai Yaya Naufal yace "to ai gasu nan sun fito ina ga gida zasu" Yaya Ahmad yace "ai kuwa, amma bari mubi bayansu mu tabbatar da gidan zasu" da sauri ya juya akalan motansa yabi bayansu, tafiya suke da gudu kamar zasu bar gari, sun zo dai-dai kan kwanar da zai sadasu da gida, sai Yaya Ahmad yaga sun mik'e, da mamaki ya juya ya kalli Naufal yace "ka gani ko, ba gida zasu ba, duk yanda akayi akwai inda suke zuwa yaran nan, Amma dai bari muje" sun cigaba da bin bayansu har su Meena suka isa hotel d'in. Sun shiga ciki sunyi parking motocin, Yaya Ahmad yayi parking motonshi a waje, da sauri ya fito Naufal na biye dashi a baya, da shigansu sai suka hango su Basma cikin wani shegen shigan tamkar zasu gasar kyawawa, tafiya suke tamkar ba zasu taka ba, har suka shiga cikin club d'in, mamaki da tsoro ne ya lullub'e su Yaya Ahmad, binsu su kai a baya, escot na ganin su Naufal duk suka fara b'arin jiki, d'aya daga ciki bakinsa ya d'auki rawa yace, "sir sannu da zuwa" Yaya Ahmad ya masa wani mugun kallo ya wuce su, har cikin hol d'in suka bi su Basma, suna hangen inda suke zauna, Yaya Ahmad yace "Naufal ga key je gida da sauri ka d'auko Momy da Ammi, kace kawai suzo, dan bai kamata ace mu kad'ai muka gansu ba" cikin sauri Yaya Naufal ya amsa ya wuce, Yaya Ahmad ya samu wani kujera ya zauna daga baya duk yana hango su, bayan kamar minti ashirin saiga Jalal yazo ya kama hannun Leema suka bi ta wata k'araman k'ofa ta gefe suka fita, da sauri Yaya Ahmad ya bi bayansu, a hankali yake binsu tambayar b'arawo, har suka isa d'akin hotel d'in da Jalal ya kama, suna shiga ya dawo, jikinsa ne ya d'auki rawa saboda tsabar b'acin rai, yana dawowa hol d'in ya hangi Meena cikin wani group maza da mata suna d'aga kwalaben syrup, bai tsinke da lamarin ba saida ya hango Basma kan step tana kwasan rawa iya k'arfinta, da karairaya jiki, ai tuni wasu zafafan hawaye suka cika masa ido bai taba tsammanin haka ba, lamarin ya girgiza shi, wayansa ne ya soma ringing da sauri ya fita hol d'in, ya duba ashe Yaya Naufal ne sai ya d'aga, ya sanar masa sun zo, da sauri ya isa wurin motocin harda escot d'in su Momy, Ahmad ya kasa magana hannun Momy ya kama suka wuce cikin hotel d'in, haka su Ammi suketa binshi har suka isa d'akin da Leema ke ciki, kwankwa k'ofan yayi, daga ciki Jalal ya bud'e daga shi sai best da gajeran wando, Yaya Ahmad ya runtse ido ya bud'e, Jalal ya na musu kallon mamaki yace "lafiya wa kuke nima?" daga ciki ne Leema ke cewa cikin d'aga murya "baby waye ne? kazo mana wlh ina cike da buk'atarka fa" ai da k'arfin Yaya Ahmad ya bangaje Jalal ya kusa kai ciki, su Ammi ma suka rufa masa baya, a razane Leema ta mik'e tana ja da baya harta kai jikin bango, Allah yasa bata cire kayan jikinta ba, idonta ne kamar zasu yo waje saboda tsananin furgici, su Momy da Ammi sai suka hau salati, abin ya girgiza su, Yaya Naufal saboda fushi baisan sanda ya zaro bel d'insa ba ya shiga jibgar Leema, ai Jalal na ganin haka ya fice a sittin, Leema ta kasa ihu domin tashin hankalin da take ciki ya wuce na jin azabar dukan da Yaya Naufal ke mata, da kyar Ammi ta kwaceta tace su fita, haka suka fito cikin tashin hankali. Momy tace "ina su Basma suke" Yaya Ahmad yace "muje in kaiku" ya musu jagora har cikin hol d'in, saboda dan dazon mutane da kyar suka samu hanyar shiga, Yaya Ahmad ne yace "Momy ga Basma can" yayi mata nuni da inda take kwasan rawa, Ammi ne tace "innalillahi wa inna ilai hir rajiun, mun shiga uku ni Faitima" idon Momy ne ya kawo kwalla, sai tayi saurin shanyewa tace "ita kuma Meena tana ina?" cikin mutane Yaya Ahmad ya kusa dasu, ya kaisu hargun da take, suka tsaya ta bayanta, Momy ta dafata, Meena ta juya da niyyar kwararo ashar domin ta riga tayi tatil, ganin Momy a bayanta ne yasa ta mik'e zunbur tace cikin maye "Ke ya kike min kama da Momy ce" wani wawan mari Yaya Naufal ya sakar mata saida taga taurari, a gigice ta kalle shi, ai tuni hanjin cikinta suka hautsine sai taji cikin ta ya murda, nan da nan jikinta ya d'auki b'ari, ta kasa magana sai rufe baki tayi, idonta tamkar zasu fad'o k'asa saboda tsoro, Momy ce ta kama hannunta suka fita waje, a cikin mota suka sanya ta kusa da Leema, sannan suka k'ara komawa cikin hol d'in. Yaya Ahmad yabi ta baya ya hau kan step d'in, ya kutsa cikin masu rawan yaje ta bayan Basma ya ya jawota ta baya, ya rad'a mata magana a kunne "In kin gama rawan ga su Ammi can suna jiranki" sai yayi mata nuni da in da suka tsaya" ai a razane Basma ta juyo, ganin Yaya Ahmad ne yasa tayi luuu zata fad'i k'asa, da sauri ya tallabota ya kamo hannunta suka sauka akan step d'in, mutane suna ta ihu yau Basma ta kula Namiji, a tunaninsu saurayi ne ta samu, suna sauka suka fita a hop d'in, su Momy suka rufa musu baya, ba wanda yayi magana duk suka shiga mota suka wuce gida. Suna isa gida suka wuce part d'in su Yaya Ahmad, d'aki ya bud'e musu suka shiga, Yaya Naufal ya shiga dukansu saida ya musu lis sannan ya fito ya sanya key ya rufe su, Momy suka wuce part d'in president. Sun zauna dukansu a falon, sai gashi ya sauko ya zauna, Yaya Ahmad suka gaishe shi, sannan suka d'aura da bayanin abinda ya faru, mamaki ne ya ziyarci Abba mik'ewa yayi ya shiga safa da marwa a falon, sunan Basma yaketa ammabato yana girgiza kai, komawa yayi ya zauna, ya d'auki wayarsa ya kira number gomna Ibrahim mahaifin Meena, suka gaisa kana ya sanar masa da "gobe in Allah ya kai mu suzo akwai family meeting na gaggawa" cikin ladabi ya amsa masa da ""to suna nan zuwa" sai suka yi sallama ya kashe wayar, gomna Ibrahim ya kalli mahaifiyar su Meena ya labarta mata abinda president yace masa, duk suka cika da mamaki suna Allah-Allah gari ya waye su wuce Abuja d'an jin ko lafiya. Haka Abba ya kira sarkin kano yayi masa umarnin da suzo suma domin family meeting, cikin kulawa ya amsa da alkawarin suna tafe, Abba ya kalli su Ammi yace "kuna gidan nan ace yaran nan suke fita suna wannan iskancin" cikin damuwa Momy tace "yallabai kayi hak'uri, amma iyaka kulawa munayi, kuskuren da akayi shine yanda aka basu daman fita ko ina da mota ba mai kwab'a musu, an basu escot duk da haka ya zama aikin banza, Allah ya shirya mana su" duk suka amsa da "Ameen" Abba yace "lallai laifi nane dana nuna musu gata, kanma ace Basma na sakar mata komai, a gani na Yarinya ce mai hankali kuma mun bata tarbiyya ga kuma ilimi na addini, ashe shirme mukayi, amma insha Allah daga yau zan d'auki tsastsauran mataki" yana gama fad'an haka ya haye sama cike da b'acin rai, su Momy suka bishi da kallo yau ran maza ya b'aci, haka zuka watse a falon cike da damuwa. B'angaren Yaya Aryan yanata kiran wayan Basma, gata a kunne amma anki d'auka, ya kira ya kai sau ashirin amma ba a d'auka ba, hankalinsa yayi matuk'ar tashi, yana ji a jikinsa akwai abinda ya sameta, dak'ar barci ya d'aukeshi tare da yin mafarkai barkatai marasa tushe. Basma kuka suke ba k'auk'autawa, kanma ace maka Meena da Leema tamkar zasu had'iye ransu, yau dai dubunsu ya cika, suna tsoron gamuwansu da iyayensu. *Washe gari* Da misalin k'arfe goma na safe, gida ya cika da dangi, an cika babban falon bak'i, abinci kala-kala aka jera, duk suna zazzaune, mai martaba da iyalensa Hajiya Sa'a da Hajiya Murja, sai gomna Ibrahim shima da matarsa Hajiya Sadiya, sai kakansu Ahmad Kaka Ma'u, sai su Momy da Ammi, President yana gefe shima, nan suka bud'e taro da addua, president ya soma bayani akan had'uwansu yace "Mun had'u anan ne domin in sanar maku da cewa, na sanya aurensu Basma nan da wata d'aya, Basma da Shureym, Meena da Naufal, Leema da Jamal, bisa sadaki dubu D'ari, ina so duk sai ku fara shiri daga yau" Cike da mamaki iyayen suke kallon juna, gomna Ibrahim ne yace "Yallabai yaushe muka yi magana da kai akan batun aurensu, kace sai nan da shekara d'aya, amma me ya kawo sauyawan wannan lamarin" cike da fad'a Ammi tace "wannan hukunci shine dai-dai, domin yaranmu suna gab da lalacewa ko ince summa lalace" falon ne ya hautsine da magana ko wanne yana tambayan meya faru, nan Ammi ta kira Yaya Ahmad yazo ya labarta musu komai, ai mai Martaba yafi kowa shiga tashin hankali, cike da b'acin rai yace "a kira yaran dukansu" cikin k'ank'anin lokaci suka shigo sanye da kayan da suka fita jiya, salati iyayen nasu suka saki kowanne mamaki ya gama cika su, sai suka zauna, nan mai Martaba ya soma musu fad'a daga k'arshe ya shiga nasihi, ya kuma kafa musu doka. "Daga yau na yanke fitanku waje" ya kai dubanshi ga Momy yace "ke Maryam ina son yaran nan su zauna a part d'inki" ya cigaba da cewa "sannan kuma na haramta muku amfani da waya, kuma koda lanbun gidan nan na hana kuje gun, daga part d'in Mominku sai part d'in Ammi da president, Ku tashi Ku bani guri mutanen kawai" President ne ya dakatar dasu, suka koma suka zauna, yace ma Yaya Ahmad daya kira su Yaya Naufal, yaje ya kirasu. Nan duk suka shigo da yake duk sun zo da iyayensu, Anty Husnah Autan Ammi wacce take aure d'an senator, Yaya Naufal, Yaya Ahmad, Yaya Jamal. Yaya Shureym, Yaya Adam duk suka samu guri suka zauna, Gomna Ibrahim shine ya fara magana yace "Ku yaranmu ne, kuma ba zamu yanke muku hukuncin da zaisa muku damuwa ba, duk yanda kuka kai ga lalacewa baza mu k'iku ba, dan haka mun yanke aurenku nan da wata d'aya mai suwa za ayi insha Allah, kai Shureym an bada sadakin Basma, kai Jamal kai da Haleema, kai kuma Naufal kai da Ameena, dama tuntuni mun yanke haka domin mun fahimci kuna son junanku, sai dai yanzu saboda wasu dalilai mun dawo da zancen baya, za'a d'aura muku aure nan da wata d'aya mai zuwa, kai Ahmad da Adam kuyi k'ok'arin gabatar mana da wanda kuke so domin a had'a bikin gaba d'aya". Yaya Naufal a ransa sam baiji dad'i ba saboda Meena ta gama fita a ransa, Yaya Jamal ma ransa ne ya b'aci dan Gaskiya baya son Leema ya tsani halinta, biyayya kawai zaiwa iyayensa. Basma ita kuma kuka ta fashe dashi tace "Wallahi Abba bana son Yaya Shureym, karku had'a auren nan" wani mari Yaya Naufal ya sakar mata wanda ya k'ara gigitata, kuka ta shiga yi sosai tace "wlh zan mutu bana sonsa, dan Allah karku min haka, na tuba bazan sake ba" Lamarin ba k'aramin mamaki ya bama iyayen masu ba, domin sun san Basma soyayya suke yi da Shureym, ta b'angaren Shureym baiyi mamaki ba, domin k'ila tana k'inshi ne saboda abinda yake ce mata, tsoronsa karta tona masa asiri. Momy ce ta dakawa Basma tsawa, sai ta shiga natsuwanta, duk suka fito suka bar iyayen nasu, Basma tana fita tayi hanyar waje da gudu, ai da gudu su Naufal suka bita suna gargad'in masu gadi "karku barta ta fita". Kamata sukayi suka kaita d'akin Momy suka rufe, ihu take tana buga k'ofa "kun daina sona kuna so na mutu, Yaya Aryan kazo ka ceceni zasu rabamu wayyo na shiga uku, wai ba mai Sona ne a gidan nan" surutai take ta yi kamar mahaukaciya, Ammi ce ta shigo falon zata bud'e k'ofar, president na shigowa yace "karki kuskura ki bud'e ta, yau ina so ta nuna mana karshen hauka, kuma wlh na rantse aure tsakaninta da Shureym ba fashi" yana gama fad'a haka ya fice. Kaka Ma'u ce ta sanya aka bud'e d'akin ta shiga, Basma ta rungumeta tanata sambatu, Addu'a taketa tofa mata, a tunaninta ko akwai jinnu a lamarin, lallashinta ta shiga yi har ta samu tayi shuru, tana ajiyan zuciya, da haka barci mai nauyi ya d'auketa. Bayan komai ya lafa, su Meena da Leema an natsu, sun zama kamar kurame, farin cikin su ma za'a aura musu abinda suke so, sai dai zuciyansu na cike da damuwan waye Basma take so haka? sun tausaya mata sosai. Yaya Ahmad ya wuce d'akinsa, damuwa ne ya shigeshi, yasan dole dama za'ayi haka, kira a wayan Basma ne ya shigo, yana dubawa yaga an rubuta my lol Aryan, kamar bazai d'aga ba saiya d'auka, Yaya Aryan ya fara magana "Basma, Basma me ya sameki dan Allah kimin magana, ina cikin damuwa" hawaye ne ya kawo ma Yaya Ahmad na tausayinsu yace "ba Basma bace Ahmad ne" cikin sauri ya tari numfashinsa "me ya samu Basma dan Allah karka b'oye min" Yaya Ahmad yace "ka kwantar da hankalinka Basma tana lafiya barci take yi" cikin damuwa yace "Basma ba tada lafiya, karka b'oyemin akwai abinda ke damunta" kawai saita fashe masa da kuka.... *Rahma Ce* (Sirrin 'ya mace group) WhatsApp. [9/29, 12:47 PM] Aysha Galadima: *'YAR SHUGABA*👑 _page_ *13.* _Na_ _*Rahma Kabir*_✍🏾 Hankalin Yaya Ahmad yayi matuk'ar tashi, cikin kulawa yace "haba Aryan ya, kake abu kamar k'aramin yaro, nace maka Basma tana barci inna farka zansa ta kiraka" ajiyan zuciya Aryan yayi yace cikin damuwa, "to shikenan nagode" nan suka yi sallama ya kashe wayar. Basma ta farka da misalin k'arfe biyu na rana, Kaka Ma'u ta sanyata tayi wanka ta sauya kaya marasa nauyi, sallan Azahar ta gabatar kana aka kawo mata abinci, Kaka Ma'u ce ta matsa mata taci, loma uku tayi da kyar kana ta sha ruwa tace ta k'oshi, mik'ewa tayi kamar an tsikareta tace wa Kaka Ma'u tana zuwa sai ta fice, tayi sa'a falon ba kowa haka ta sanya takalmi ta fito haraban gidan, motocin gidan sun ragu da alama sun tafi raka su mai Martaba ne airport, hanyar k'ofar fita tayi tana waige-waige kamar mara gaskiya, masu gadi suka hanata fita, saita fara musu masifa akan su bata hanya ta wuce, ganin ta cije ne yasa suka bata hanya tawuce, tana fita, taga Yaya Ahmad zaune bisa wani dakali daga gefe ashe duk yana jin hayaniyansu, tsayawa tayi cak ta kasa tafiya, Yaya Ahmad ne ya mik'e yazo gabanta ya tsaya cike da tuhuma yace "Basma bakya jin magana, ina zaki bayan an hanaku fita, ya kike so ki zama mara biyayya ne" fashe masa da kuka tayi, girgiza kai yayi ya kama hannuta suka koma cikin gidan, part d'in su ya wuce da ita ya zaunar da ita a gefen sa ya kira sunanta a nutse "Basma kin ga abinda rashin ji ya haifar miki, naso ace haka bai faru ba, dana tsaya miki tsayin daka akan baki auri Shureym ba a baki wanda kike so, Basma meyasa kika aje tarbiyanki kika nima lalacewa haka, bayan kinyi saukar Al'Qur'ani har sau biyu, kina da sani akan littafai Addini sosai, a takaice in aka baki aji zaki iya rik'ewa a matsayin Malama, ya a kayi kika shagala da duniya haka Basma?" Jikinta ne yayi sanyi sosai ta kuma b'arkewa da kuka tace "Yaya wlh mun riga munyi kuskure, kuma wannan rayuwar a England muka koyoshi, insha Allah bazamu sake ba mun tuba, ni dai ka taimakeni karka bari a aura min Yaya Shureym wlh bana sonsa, kafi kowa sanin waye Shureym bai cancanta ya zama mijina ba" ajiyan zuciya yayi yace "na sani Basma amma Abba ya riga ya yanke hukunci, ni shawara a gareki shine ki masa biyayya sai Allah ya sauk'ak'a miki lamarin" "To Yaya kamin Addu'a, amma da son Aryan zan mutu" Tsaki yayi baice komai ba wayarta ya d'auka yayi dailing number Aryan, bugu d'aya ya d'aga, sai ya mik'a mata ta kara a kunne, a cikin damuwa Aryan yace "My Basma kina lafiya kuwa?" kuka ta saki wanda hakan yayi dai-dai da k'ara rikicewansa, cikin damuwa yace "meya faru gayamin mana ko so kike nima nayi kukan". Tuni Yaya Ahmad ya bata wurin domin ya gaji da jin kukan nata, Basma ta shiga bashi labarin komai bata b'oye ba, ai zubbur ya mik'e a tsorace yace "Basma shikenan kinyi sanadin rabuwanmu, shikanan kin jawo mana damuwa mara yankewa" ya k'arasa maganar cikin rawar murya, Basma sai tai k'ara tsinkewa da sabon kuka, Aryan kashe wayar yayi gaba d'aya, Basma taita dialing number akashe, a firgice ta mik'e ta fita da gudu, Yaya Ahmad yana waje, ganin ta a guje yasa ya bita a guje, wurin gate ta nufa, masu gadi suka tare ta, kuka take da magiya akan su barta ta fita, amma suka k'i har Yaya Ahmad ya cimmu su. Kama hannunta yayi gam yana janta, ihu sa saka tana tirjiya, ihun ta ne ya dawo da duk hankulan mutanan gidan duk suka fito a guje, da yake sun dawo daga rakiyan, kafin su k'arasa cikin gidan sosai Basma tayi wani ihu saita langwab'e, a razane Yaya Ahmad ya juyo yaga idanunta sun kafe ta suma, jikinsa na b'ari ya d'auketa tsak ya shiga cikin gida da gudu, a hanya yaci karo dasu momy, nan ya kewaye su ya wuce da ita part d'in president, a falon ya ajeta duk suka shigo ko wanne ya rufa a kanta, Ammi ne keta kiran sunanta amma shuru, da gudu Meena ta kawo ruwa aka yayyafa mata, lumshe ido tayi tare da sauke ajiyan zuciya mai k'arfi, President da kansa yazo ya d'auketa cak ya haye da ita sama, ya kuma yi gargad'in kar wanda ya biyoshi, a zata yayi akan gadonsa ya d'auki wayansa ya kira likitansu. Baifi rafin awa ba sai gashi, ya haura sama ya dubata, allurai yayi mata a ciki harda na barci, yayi wa Abba bayanin "damuwa ce ya haifar mata da suma, yanzu nayi mata alluran barci domin kwakwalwanta ya huta" nan Abba ya mishi kyauta ya fice yana godiya. Su Ammi duk suna falon sun kasa tafiya, Yaya Ahmad ne ya zauna jugum yace "Ammi dan Allah kusa baki a jenye maganar Auren nan, lamarin Basma ya fara bani tsoro" Ammi tace "nima abinda na gama tunani kenan, amma kasan Abbanku baya sauya magana in yayi" Momy ce tace "uhum nikam ina bayan Abbanku, aure kuma da Shureym ba fashi" tana gama fad'an haka ta mik'e tace "Husnah zo muje na had'a miki turarukanki kan ki tafi" Cikin sanyi jiki da damuwa Anty Husnah tabi bayanta cike da tauyawa 'yar uwanta. Sai bayan Sallan Isha'i ta farka, Abba da kansa ya kira Ammi tazo tayiwa Basma wanka ta shiryata, Abinci ta bata da kanta, da kyar take iya cin kad'an, bayan sun natsa Abba ya kira su Meena dasu Momy, dasu Yaya Ahmad duk suka had'u a falon sa, ya soma magana "na taraku a nan ne domin in kuma jaddada muka akan zancen Auden ku, saboda wasu dalilai mun k'ara kwanakin bikin zuwa bayan wata Uku, lokacin Basma ta samu lafiya sosai, Meena tasha maganin Islamic akan kwayoyin da tasha, ke kuma Leema ki samu yin istibra'i" Leema saita sunkuyar da kai k'asa, cike da dana sani, yanzu kowa yasan ita fasik'a ce wa'iyazu billah, maganar zuci takeyi hayawa na zuba a kuncinta. Abba yakai dubansa ga Basma data rakub'e gefe d'aya kusa da Ammi yace "ke kuma Basma ina so ki sani tun da muka haifeki, ban tab'a saki abu kin k'i yimin ba, to ina niman alfarma a gunki a matsayina na mahaifinki, kiyi hak'uri kiyi min biyayya insha Allah zaki nasara a rayuwanki, Basma ke mai biyayya ce a garemu, akwai abubuwa dana auna na tabbatar da yin aurenki ga Shureym shine dai-dai, zumunci ba abun wasa bane, dan haka ki sanyawa ranki salama ki tabbatar min da nine mahaifinki kuma na isa dana saki Abu kiyi min" Kuka ta soma yi amma mara sauti, tashin hakanli ta shiga, domin yau ta riga ta sadak'ar an rabata da Aryan, kwantawa tayi a jikin Ammi tace cikin kuka mai karya zuciya "Abba ina son Aryan ne wlh shi nake so, burina in muku biyayya, Abba kamin komai a rayuwata, k'arshe na sab'a muku, na aje tarbiyyan da kuka bani na soma yin wata rayuwa mara tushe, mai dinbin dana sani aciki, nagodewa Allah da kune kuka ganni da idonku, na tabbatar da labari aka baku baza ku yarda ba, saboda kun bani dukkar yardanku, Abba saboda haka na hak'ura da soyayyar Aryan, amma ku sani zan auri Shureym bisa ga biyayya a gareku ne, domin in cire muku rad'ad'in sab'a muku da nayi, Na amince zan auri Shureym, Aryan ka yafemin" Saita k'arasa maganar da wani matsanan cin kuka, da gudu ta mik'e tabar falon, ta nufi d'akin Abba, ta fad'a gado tana rera kuka mai tsuma zuciya. Gaba d'aya illahirin mutanan falon jikinsu yayi sanyi, hatta Abba ya tausayawa 'yarsa abin sonsa, sunyi shuru ko wanne da irin abin da yake sak'awa a ransa, sautin kukansu Meena da Leema ne ke tashi a falon, Kaka Ma'u ce tace "ni kam wannan lamari yana bani mamaki, waye wannan Aryan d'in da yake son raba zumunci" Yaya Ahmad ne yace cikin wasan kaka "ke kuma tsoguwa ina ruwanki, ana Abu na yara kin tsomo baki, sai ki mana shuru" Abba ne ya masa dak'uwa yace "kai ungo naka uwata kake cewa hakan" su Ammi duk suka yi murmushi, nan take fara'ansu ya dawo, damuwan da suke ciki ya ragu, Abba yace "Ahmad ina so gobe in Allah ya kaimu ka tattaro min dukkan takardu da makullan abubuwan da Basma ta mallaka" Cikin dalabi yace "to Abba insha Allah zanyi, Allah ya kaimu" Nan Abba ya sallami kowa, Momy ce mai girki Abba ya cewa Ammi, ta wuce da Basma d'akinta, ta bata kyakkyawan tsaro saboda karta fita cikin dare ba'a sani ba. Shureym bayan sun isa Kano, ya samu Maminsa ya matsa mata akan shifa lallai sai an aura masa Basma in ba haka ba akwai Matsala, Hajiya Sa'a tayi murmushi tace masa "Ka kwantar da hankalinka, aurenka da Basma kamar anyi an gama, ita d'in banza harta isa tace bazata aureka ba, zanje in samu Mai Martaba na k'ara hura masa wuta akan lamarin" dariya yayi na farin ciki yace "to Mami ya maganar aurena da Safeena? Kinsan fa so nake a fara d'aurawa da ita kan na Basma" tace "Karka damu cikin satin nan zan had'aka da sarkin gida da wasu, domin su jagoranci aurenka da Safeena, a cikin sirri ba tare da kowa ya sani ba, kaga sai a d'aura muku aure kafin bikin su Basma da wata guda, ka ajeta a gidan gonarka, da an d'aura aurenku da Basma ku tarkata ku wuce America, bazaku dawo ba sai ka kammala komai da shekara guda, kaga lokacin komai yayi dai-dai" dariya yayi harda tafawa yace "Gaskiya Mami kin gama min komai in kika min haka, zanyi murna sosai" tunowa da yanda Basma ta nuna masa tsantsar kiyayya yayi, yasa ya cije leb'e yayi wani shu'umin murmushi. *Bayan kwana biyu* Aryan ya lalace yayi duhu, hankalin Umma ya tashi sosai dan kwanan sa biyu ko k'ofar gida baya iya zuwa, sallah ma a gida yake yi, baya iya cin komai sai abu mai ruwa, sai yawan barci. Deeja ce take sanarwa Yaya Ahmad halinda suke ciki domin sam Yaya Aryan yak'i yarda suje asibity kuma yace shi lafiyansa kalau, Ahmad ya shirya yazo, ya samu Umma ya sanar mata abin da ke faruwa game fa Basma da Aryan, bai b'oye mata komai ba, hankalin Umma ya tashi sosai ta tausaya musu, dama tasan za ayi haka, Deeja d'aki ta shiga ta fara kuka, Yaya Ahmad ya sanar mata da zuwan iyayensa nan da ranar Juma'a akan maganar auren Deeja, Umma ta sanya albarka tayi murna koba komai hakan ya rage mata damuwa, nan ya shiga wurin Aryan da kyar ya shawo kanshi suka tafi asibity tare. Likita ya duba shi ya rubata masa magani da allurai, haka akai treatment d'insa, Yaya Ahmad yayi masa siyayyan kayan ciye-ciye, kana ya dawo dashi gida, ya yiwa Umma sallama ya tafi. *Bayan wata guda* Bikinsu Basma saura wata biyu, Yaya Aryan ya warware ya cigaba da zuwa aikinsa, sai dai yanzu miskilanci ya k'aru, baya magana saiya kama dole, baya cin abinci sosai duk ya rame yayi fari, Umma tayi mita da lallashi harta gaji ta kyaleshi, kullun dare baya iya barci sai yayi kuka sosai, kana yayi Nafila ya rok'i Allah kan ya sassauta masa akan lamarin. Abba ya wakilta Abokansa wajen nimawa Ahmad auren Deeja, da yake Ahmad ya sanar da Abba komai tun farkon had'uwansu, Abba ya jinjina lamarin kuma yayi farin ciki da 'ya'yansa, da suka kasance masu tausayi da taimakon na k'asa dasu, hakanne ya k'ara bashi k'arfin gwiwan ya amince da Auren Ahmad da Deeja, a ransa baiji dad'in raba Basma da Aryan ba, Amma yayi alkwarin zai d'aukaka darajan Aryan yanda duniya da 'yan uwansa zasu amfana dashi. Mak'otan su Deeja da mai anguwa sune suka amshi maganar Auren Deeja, iyayen Ahmad da suka zo sun boye asalin Ahmad, suka sanya biki dai-dai dana su Meena, a haka suka gama taron cikin mutunci, kowa ya koma gida. Deeja farin ciki ya lullub'eta, amma inta tuno da Yaya Aryan sai damuwa ya rufeta. A haka suka fara shirye-shieyen biki, Yaya Ahmad ya sanar musu da, shifa Deeja kawai yakeso a bashi, baya buk'atar komai, hatta abincin biki Abbansu ya d'auki nauyi, dan haka kar su takurawa kansu, Umma saboda murna har kuka tayi. B'angaren Basma kuwa, lamura sun dagule mata ta lalace tayi bak'i, duk ta rame inka ganta sai ka k'ara kallonta ka tambaya anya itace Basma 'yar kwalisa kuwa? domin duk ta fice a hayyacinta, kowa na gidan yana tausaya mata, hatta Momy tana jin tausayin 'yarta haka yasa take jawota a jiki, tana lallashinta da maganganu masu dad'i da nasiha, yanzu Basma ta saduda ta kuma hak'ura da lamarin, burinta bai wuce ta k'ara tozali da Aryan ba suyi magana na bankwana. Su Meena an natsu, ana ta bata magunguna na Islamic wanda zai wanke mata dattin kwayoyin data sha. Leema kuwa Momy musamman takwo mai gyara, domin a gyarata, yanda zata dawo kamar budurwa, koda dai ta riga ta rasa budurcinta. *Ni kam nace anbaro shiri tun rani* Shirye-shirye ake ta ko wani b'angare, Abuja, Kano, Kaduna, duk sunata shirye-shieye, biki ne na 'ya'yan manya. *Biki saura wata guda* President ya kira Ahmad suka gana dashi a d'akinsa. Yaya Ahmad ya fita da sauri domin aiwatar da ummarnin Abba. Abba ya kira Momy da Ammi, ya kira duk yaran gidan, kaka Ma'u ita ta koma Kaduna dan tafi jin dad'in zaman can. Yaya Ahmad ya nufi gidansu Aryan, ya samu duk suna gida da yake weekend ne, Yaya Ahmad ya shiga ya zauna a shinfid'an da Deeja ta masa, suka gaisa da Umma, ya kalli Aryan ya kalli Umma yace "Umma mahaifina ne yace inzo in tafi daku gidanmu, domin yana buk'atar ganinku, yace in baku hak'uri akan hakan, yasan shine ya kamata yazo amma bisa wasu dalilai yace da kuje ku same shi" Yaya Aryan ne yace "ok badamuwa yaushe yake son ganinmu?" "Yanzu yake son ganinku" Umma tace "to shikenan bari mu tafi" ta k'ara maganar tana mik'ewa, komawa d'aki suka yi duk suka canza shiga mai kyau, suka rufe gidan suka gida mota. Aryan na gaba Umma da Deeja suna kujeran baya, sun kama hanya suna tafiya, Aryan suna hira da Yaya Ahmad, tafiya sukai mai nisa, tun suna arean talakawa har suka gota arean masu hannu da shuni, Yaya Ahmad yana zullumi a zuciyansa yanda in suka san Abbansu ne Shugaba k'asa ya zasu d'auki lamarin , Yaya Aryan ne ya katse masa tunaninsa yace "Ahmad naga mun doshi hanyar gidan Shugaba k"asa ne, kasan fa ta arean akwai check point kuma ga yawan security" murmushi Yaya Ahmad yayi yace "eh gidanmu dole sai tanan zamu bi, karka damu" haka suka fara ratsa check point ba tare da an tare su ba, security suna d'agawa Yaya Ahmad hannu, mamaki ne ya fara cika su, basu tsinke ba saida suka ga security na bud'e musu hanya suna sarawa Yaya Ahmad, katon tangameman gate d'in fadar shugaban k'asa suka dosa, wanda kan su k'araso an bud'e musu gate, a tsorace Yaya Aryan ya kalli Ahmad bakinsa yana yawa yana nuna shi yace..... *Rahma ce* (Sirrin 'ya mace group) WhatsApp. [9/29, 12:47 PM] Aysha Galadima: *'YAR SHUGABA*👑 _page_ *14.* _Na_ _*Rahma Kabir*_✍🏾 Yace "Ahmad kasan inda ka kawo mu kuwa?" Ahmad murmushi kawai yayi, sai yayi parking mota, ya fito tare da cewa "Umma mun kawo Ku futo" a sanyaye suka fito suna k'arewa gidan kallo, cikin kulawa Yaya Ahmad yace "kumu je" Umma tace "Kai Ahmad wai ina ne nan, gaskiya a tsorace nake" murmushi yayi yace "Umma Ku kwantar da hankalinku bakomai fa" a tsorace suka bi bayansa, direct part d'in president ya kaisu, suna shiga duk mutanan falon suka zuba musu ido, jikin su Deeja sai ya d'au rawa, ido suka saki suna kallon kayan alatu da aka zuba a falon, har suka isa tsakiyan falon, Basma ne ta rugo da gudu ta rungume Umma, ai sai ta fashe da kuka, Umma ta rik'eta gam tana lallashinta, a haka suka k'arasa cikin falon suka zauna a kan kafet, Ahmad yace su zauna a kujera amma suka k'i hawa, Su Ammi da Momy suka bisu da kallo, su Meena ma dasu Yaya Naufal kallonsu suke yi da mamaki, sun gaisa gaba d'aya sai falon ya d'auki shuru, baifi minti goma da zuwansu ba President ya fito, cikin shiga na manya kaya, yana tafiya cike da izza tamkar Baba Buhari ya bayya a cikin bainar Jama'a, sai dai shi Abba bai yi tsufan Baba Buhari ba, lol. Su Aryan suna arba dashi sai cikinsu ya d'uru ruwa, kamma ace Umma da tayi mutuwar zaune, Deeja ko kamar ace mata ket ta ruga a guje dan tsoro. Zama yayi a kan kujeransa na alfarma, Ahmad ne yace "Abba gasunan nazo dasu" Abba ne ya kalli inda suka zauna yace "barkanku da zuwa" baki na rawa suka amsa gami da gaisheshi, Abba yace "Nine mahaifin su Basma, Ahmad shine Babban Yaro na, nasan za kuyi mamaki da haka, Ahmad ya sanar dani labarinku, sai dai Ku bakusan nine Mahaifinsu ba sai a yau" a razane Aryan yake kallon Abba yana magana, ya juya kallonsa ga Yaya Ahmad da Basma, murmushi Yaya Ahmad yayi masa ya gyad'a masa kai alaman eh, Basma Kuma ta sunkuyar da kai k'asa, tunda tayi tozali da Yaya Aryan hankalinta ya tashi, taga ya rame sosai tausayinsu ya kamata tasan lallai an yiwa rayuwansu gib'i. Nan Abba ya cigaba da bayani yace "Aryan nasan komai dake tsakanin ka da Basma, kayi hak'uri da abinda ya faru, ba zan iya hana Auren ta da Shureym ba, domin ina martaba zumunci, dan haka ne na amince da Auren Ahmad da 'yar Uwanka saboda in sanya muku farin ciki, ku tabbatar da bama kyamar talaka, sannan yanzu nayi maka alkhawarin ka kawo duk yarinyar da tayi maka, insha Allah zan zame maka Uba na jagoranci lamarin, sannan nasan a company na kake aiki, yanzu na baka MD na company, sannan zaka Zab'i k'asar da kake so domin kaje ka k'aro karatunka a can" Aryan kuka ya fara yi, yace cikin ladabi, "Yallabai nagode kwarai da karamci, ban tab'a kawowa a rayuwata zanga Shugaban k'asa da idona ba, sai gashi a sanadin soyayyan Basma na ganka, Basma ke haske ce a rayuwanmu, Yallab'ai nagode da duk abinda ka bani, amma ina so ku sani, ba zai iya siyan soyayyan Basma ba a zuciyana, domin an riga an halittamin shi a zuciya, na hak'ura da soyayanta dan nariga na sadak'ar Basma tafi k'arfi na, mun gode sosai da karamci" yana gama magana sai yayi shuru. Shasshek'an kukan Basma ke tashi a falon, kowanne yayi shuru suna zancen zuci. Umma itama tayi godiya tace "lallai Basma da Ahmad kunyi gadon halaye na kwarai wurin mahaifinku, nayi mamaki sosai da yanda kuka shigo cukinmu kuka zauna damu duk girman matsayinku, kun rungume mu tamkar jininku" saita k'arasa maganar da kuka, Deeja ma kuka ta soma yi, falon ne yayi shuru na 'yan dak'ik'a, sai Abba yace "Hajiya kuyi hak'uri ai wannan ba abin kuka bane, kai Aryan ba wai na maka wannan kyauta bane domin ka fansar min da soyayyarka ba, nayi maka ne saboda Allah a matsayin d'an cikina, taso ka amshi wannan takardun, na gidan Hutun Basma ce da kuma takardun motanta guda uku, ni na baka su halak malak, ina so kafin lokacin Biki Ku tare a gidan" Yaya Ahmad ne ya matsa danya Amsa takardun, sai Abba yace "shi nake so ya amsa da kansa, domin shima d'ana ne" jikin Aryan ne yayi sanyi, haka ya mik'e yaje ya amsa tare dayi masa godiya. Momy itama tayi masa Addu'a da Allah ya bashi mata tagari, har a zuciyarta taji tana son Aryan, taso ace ya zama sirikinta. Ammi kuwa ta gama k'ulewa kamar zata fashe dan haushi, Meena da Leema sun shaida Aryan kuma sun yaba da kyawunsa lallai sun dace da Basma, Yaya Naufal da yake yasan Aryan ya tayashi murna, amma har a azuciyansa baya son ya auri Basma domin tafi k'arfinsa. Nan Umma tayita godiya, Abba yace "Hajiya ya isa haka Allah ne ya baku, ina 'yata Khadija?" Kanta a sunkuye tace gani, Abba yace "Masha Allah, Allah ya muku Albarka yasa Albarka a aurenku" ya kai dubansa ga Momy yace "Hajiya Maryam gafa surukarku nan, matar Ahmad" ai sai Momy ta fad'ad'a murmushinta tace "Masha Allah, Allah ya sanya alkhairi, ai tunda tazo ma ba zasu tafi da ita ba, zata zauna anan domin ayi mata gyaran jini dasu Leema gaba d'aya" Abba yace "To shikenan, Abu yayi kyau, bari na fita ana jira na" nan yayi musu sallama ya fice, Ammi ce ya mik'e da sauri tace "Ahmad yanzu ka rasa matar aure sai wannan yarinyan, to ka sani ba da yawuna ba, dan bataimin ba" tana gama fad'an haka ta fice, da mamaki duk suka bita da kallon, Ahmad cike da tashin hankali yace ma Momy, "Momy kinji abinda Ammi tace ko, dan Allah ki shawomin kanta" Momy tayi murmushi tace "karkaji komai zata sakko ne" ta kai dubanta gasu Umma tace "Hajiya kuyi hak'uri rashin fahimta ne" Murmushin yak'e Umma tayi domin abin ya bata haushi tace "ba komai ai" nan Yaya Ahmad yace su tashi ya rakasu gidan da Abba ya basu, Basma ta mik'e tace "Yaya Ahmad zani" hararan wasa yayi mata yace "kinsan dai yanzu bakwa fita, kiyi hak'uri kiyi zamanki a gida" marairaice fuska tayi tace "tom zanyi magana da Yaya Aryan" da sauri Aryan ya juyo yace "a'a Basma magana a tsakani mu ya k'are" yana gama fad'an haka yayi waje da sauri, ai da gudu Basma ta bi bayansa tana kwala masa kira. Ya kusa kaiwa gate, sai ya tsaya tsak amma bai juyo ba, ta cimmasa ta tsaya a gabansa tana haki, kallonta yayi ya kauda kai, hawaye ke sauka bisa kuncinta tace cikin sark'ewan murya "Yaya Aryan guduna kakeyi na zama abin gudu ko, ko ka daina sona ne?" Runtse idonsa yayi ya bud'e su, sun rine sunyi ja yace "Basma dole na gujeki domin ke yanzu ba tawa bace, Basma kin haramta a gareni, magana a tsakaninmu bai dace ba, domin zai tado min da mikin dake zuciyana wanda mai gama warkewa ba, ina Sonki Basma baya musaltuwa, amma ki sani soyayyan da mukayi dake kisa aranki tamkar mafarki ne, ki cireni a zuciyarki kiyiwa iyayenki biyayya" yana gama fad'an haka ya matsa ya cigaba da tafiyan, Basma durkushewa tayi a gurin ta saki wani kuka mai tsuma zuciya, Aryan shima da kuka ya fita gidan, yana fita ya tsaya gefen wani dakali ya durkusa agun ya shiga rera kuka tamkar k'aramin Yaro. Leema, Meena da Deeja ne suka zo suka d'aga Basma, suka wuce da ita part d'in Momy. Umma suka fita itama tana kwalla, a haka suka cimma Yaya Aryan ita da Yaya Ahmad da kuma Yaya Naufal, dafashi Yaya Ahmad yayi, ya d'agoshi ya shiga share masa hawaye tare da gaya masa kalamai masu sanyaye rai. A haka ya sanyashi a mota ya wuce dasu gidan da Abba ya basu. B'angaren Shureym kuwa Mami ta aika Sarkin Gida da wasu mutane garin Yola, an basu auren Safeena, sun kai musu akwati da komai da Shureym ya siya, anyi shagulgulan Biki lafiya an d'auko Amarya. sun sauka a gidanta dake garin Kano wanda Shureym ya gyara shi sosai, komai na jin dad'i akwai a gidan. Sun gama bikin auren sirri, wanda daga Mami sai Shureym sai wanda suka je nema masa aure sune kawai suka sani. An bar Amarya da Ango suna cin Amarci. Momy ta samu Ammi akan batun Auren Yaya Ahmad da Deeja, tayi mata bayani mai gamsarwa, Ammi ta sauko, tace ta hak'uri amma tana son Ahmad ya zauna da matar anan cikin gidan President, ta da sanyawa Auren Albarka, Momy taji dad'in haka sosai, tace zata Sanar ma President domin a gyara part d'in da Ahmad zai zauna. *Biki saura mako guda* Anata shirin biki ta ko ina, mutanan Kano sun tattaro sun wuce Abuja, mutanan Kaduna ma haka, gidan president ya cika da dangi da abokan arziki, kowa kagan shi yana cikin farin ciki. Amare kuwa sunsha gyara sai kyalli suke, a zuwa yanzu su Yaya Naufal da Yaya Jamal sun sauko da k'in da sukewa su Meena, yanzu burinsu bai wuce a d'aura aure ba susha amarci, sai dai a Kasan zuciyan Yaya Jamal yayi alkawarin sake aure da sabuwar budurwa domin shima ya mori aure, dan yasan Leema saura zai samu agunta. Basma ta saduda sosai tayi sanyi, tana tsayawa tayi hira da Yaya Shureym amma a k'asar zuciyanta Aryan yana nan, kullun dare saita yi kuka na rashinsa, Shureym sai rawan jiki yake yi, yana nunawa Basma kuwala ta musamman, dan burinshi bai wuce yaga an d'aura Auren ba, domin yana cike da tsananin sha'awarta, yasan duk k'insa da take yi da an d'aura zata bada kai bori ya hau. B'angaren Safeena, Yaya Shureym ya sanar mata da komai na aurensa da Basma, ta nuna rashin damuwa akan haka, sun tawo Abuja a tare, ya kama mata d'aki a hotel har a gama bikin su wuce America, Safeena burinta bai wuce ana gama shagalin biki ba su wuce America, ta juya Basma yanda ranta keso, domin Shureym ta gama dashi a tafin hannunta yake, sannan tayi alkhawarin Shureym bazai tab'a tarawa da Basma ba in dai tana raye. Amarya Deeja tayi kyau tamkar ba ita ba, hatta Ammi da take k'inta ta yaba da yanda ta sauya, fatarta tayi kyau, kamannin ta da Meena ya fito sosai, a hankali taji ta kwanta mata arai saboda yanda Deeja take mata biyayya da kuma nuna kunya a gareta a matayinta na mahaifiyan mijinta, cikin k'ank'anin lokacin ta nima k'iyayyar da take mata ta rasa, har wautan kanta take gani akan meyasa ta nunawa Yarinya tsana haka. Deeja ta koma gida, ta samu su Ammi a sabon gidansu, domin a nan ne za'a d'aukota a kawota gidan president. *Ana gobe biki* Mutane sun gama hallara, ta wajen su Umma mutanan Gombe sunzo, sai dai mahaifinta Malam ba shida lafiya, dan haka Innarta basu samu zuwa ba sai danginsu, sunata shirye-shirye cikin kwanciyar hankali. Yaya Aryan ya bar K'asan ana saura kwana uku biki, ya wuce K'asar Manaco domin yaji ba zai iya tsayawa bikin ba, koda ya isa k'asar ya kashe duk wayoyinsa ya soma Harkan karatunsa, Basma tana ransa, shi kad'ai yasan irin k'unan da zuciyansa yake ciki, kullun saiya kalla hotunanta da wanda take ita kad'ai da wanda suka d'auka tare a cikin system d'inshi, wani yayi murmushi wani yayi kuka, ya saba da haka, harya zame masa jiki. *Ranar daurin aure* Angwaye sun fito sunyi fas sai shek'i suke yi, ta b'angaren amare kuwa tsayawa fad'an kyawunsu b'ata lokaci ne, Basma koda tana cikin damuwa tayi kyau, tasha kwalliya amma bai haka zuban hawaye a fuskanta ba, duk wanda ya ganta saiya tausaya mata, ta k'ara tsukewa ta rame, ko tayi dariya yake tayi, sam bata farin ciki da wannan auren, Addu'a take Allah ya bata hak'uri da juriya akan auren. Bayan sun idar da Sallah Juma'a limamin masallaci ya sanar da d'aurin Auren yaran President da Gomnan Kaduna, da kuma Sarkin Kano. Biki na 'yayan gata. An d'aura auren Yaya Ahmad da Khadija Yaya Shureym da Basma Yaya Jamal da Haleema Yaya Naufal da Ameena Yaya Adam da Munaya 'yar wazirin Sarkin Kano. Anyi addu'o'i kana aka wuce taron walima a babban hol dake fadar Shugaban k'asa, anci ansha kowa ya shaida wannan aure, na 'yayan manya ne kuma masu gata. Basma tana jin an d'aura ta shiga d'akinta ta kulle kanta, kwantawa tayi a gadonta ta fara kuka mara sauti, hoton Aryan a wayanta take kallo tace "shikenan an rabamu, Yaya Aryan ina sonka Allah ya rabamu, Allah kasamin juriya da hak'uri azuciyata, Aryan na je soyayyarka a zuciyata, zan yi kok'arin yin biyayyar aure ga mijina, Allah ya had'a fuskokinmu yasa na zama matarka a aljanna" saita b'alle da sabon kuka. A haka barci mai nauyi ya d'auketa, ba ita ta farka ba sai bayan sallan La'asar. Wanka ta tayi, ta canza wasu kayan zuwa leshi marun mai fulawa fari, tayi makeup tamkar ba Basma ba, ta b'ata lokaci sosai wajen kwalliya, kana ta aza gwagwaro Fari, ta sanya takalmi mai tsini, turaruka kuwa kamar wanka tayi dasu. Kallon kanta tayi a madubi, ita kanta ta yaba da Kyan da tayi. Ta fito a Queen Basma. A can kuwa cikin gidan hankalin kowa ya tashi ba'a ga Basma ba, an duba duk inda ya kama ta amma ba'a ganta ba, gaba d'aya gidan ya hautsine cikin tashin hankali, a cikin wannan yanayi ne Basma ta fito cikin taku na k'asaita, yau Queen Basma ta fito a sunanta, ai sai kallo ya koma gunta cike suke da mamakin ganinta a rinin wannan shiga, nan take suka fara murna, Basma tayi kyau sosai, masu d'aukan hoto suka fara d'aukanta, Ammi ce ta tawo da gudu ta rungemata tace "Basma ina kika shige ne haka?" dariya tayi tace ina d'akina, nayi bankwana da Yaya Aryan shine barci ya d'aukeni, yanzu na kimsha nace bari na fito a cigaba da shagalin Biki dani" ai baki bud'e Ammi ta bita da kallo tana mamakinta tare da tausayinta. *Rahma Ce* (Sirrin 'ya mace group) WhatsApp. [9/29, 12:47 PM] Aysha Galadima: *'YAR SHUGABA*👑 _page_ *15.* _Na_ _*Rahma Kabir*_✍🏾 *Da dare* An shirya kayataccen Dinner a katon hol mai d'aukan mutane dubu, manyan mutane sun halarci wannan Dinner, harda wasu yan k'asashen waje sun halarta, Amare da Angwaye sunsha kyau, ko wanne zaune yake da Amaryansa, Safeena na zaune cikin mutane ranta ya gama b'aci, zuciyarta yana mata zafi dan tsananin kishi, tunani ta shiga yi, ita fa Auren sirri aka mata sam ba'ayi irin wannan shagalin ba, haushi ya k'ara cikata, amma tasan matakin da zata d'auka akan Shureym, dan taga yana ta rawan jiki akan Basma. Kowa ka ganshi a wannan lokacin yana cikin farin ciki, amma banda Basma da take cikin damuwa na rashin ganin Aryan agun, dan batasan yayi tafiya ba, sai kuma Safeena da take jin haushi akan mijinta. Anyi taro lafiya an watse lafiya, cikin farin ciki da kwanciyar hankali. *Washe gari* An kai ko wace Amarya gidan Mijinta da misalin larfe hud'u na yamma, Deeja an kawota gidan president a side d'in mijinta, haka Meena ma an ajeta acikin gidan president, part d'insu na gefen nasu Yaya Ahmad, Leema kuma an wuce da ita Kaduna zuwa gidan Jamal da Dady ya siya masa, sai Yaya Adam an wuce da matarsa Munayah, an kaita part d'inta dake cikin gidan Sarki, Basma ita ce tayi saura a gida, itama part d'inta yana gidan Sarki kusa dana Yaya Adam, kasantuwar Yaya Shureym bai gama aikin da suka d'aukeshi ba na shekara biyu, yasa zasu wuce America, su cikasa sauran shekara d'ayan daya rage. Sauran baki kuma suna nan basu soma tafiya ba. Sai Washe gari ko wani Ango ya shiga d'akin matansa, suka fud'e faifan sabon rayuwa cike da So da K'auna. Da safe su Basma suka wuce airport, da kyar aka raba Basma da jikin Ammi, tasha kuka kaman ranta zai fita, Shureym kuwa sai wani kamata yake yana lallashi, sun shiga jirgi Basma na d'agawa iyayenta hannu, ji take kamar in ta tafi bazata dawo ba, haka suka zauna wuri guda, sannan aka rufe k'ofar jirgi, ana rufewa Shureym ya tashi kusa da ita ya kowa gefen hagunsa, kusa da Safeena ya zauna, ta cika ta batse dan haushi, Basma ta bishi da kallo ganin ya zauna kusa da wata mace cike da mamaki, bata iya cewa komai ba, Safeena ce da taga Basma na kallonsu, sai tayi saurin sakin fusha ta juyo fuskanta tana kallon Shureym, sai ta had'a bakinsu guri guda, ai da sauri Basma ta kauda kai, zuciyarta na dukan uku-uku, bakinta na fad'an "Inalillahi wa inna ilaihir raji'un" kwantar da bayanta tayi jikin kujera, ta runtse ido, tsananin radad'i zuciyarta yake mata, bawai kishin Yaya Shureym taji ba, tsabar bak'in ciki da irin tsanar hayayyansa take, a tunaninta k'aruwansa ce, Safeena tana ganin Basma ta kauda kai, sai ta janye jikinta ta fara magana k'asa-k'asa tace "Baby wlh ka b'ata min rai cikin kwanakin nan, naga sai wani rawar jiki kake akan wancen yar iskan Yarinya, to wlh ka sani bazan tab'a raba kwana da ita ba, alkwari ka d'aukan min cewa kai mijin mace d'aya ce, dan haka kai nawa ne ni kad'ai, tunda kace had'in zumunci ne shiyasa na yarda da auren, dan haka da kanta zata gaji da zaman gidanka, harta nima saki tayi gaba" Gaban Shureym ne ya fad'i, hankalinsa ya tashi, amma sai ya dake ya wayince yace "Love ke kad'ai ce a guna, me zanyi da Basma, had'in zumunci akai mana dan bana sonta" Cike da murmushi tace "yauwa Babyna, kamin alkwara ba raba kwana da ita" murmushi yayi wanda yafi kuka ciwo yace "na miki alkawari, ai bana son b'acin ran ki, ko me kike so zan miki domin in saki farin ciki" Safeena farin ciki ya rufeta, take nan ta manta da b'acin rai data shiga. Basma kuwa kuka ta shiga yi mara sauti, a haka har barci ya kwasheta. *America* Bayan sun kai, mota biyu ke jiransu, d'aya wanda zai d'auki kayan su, d'aya kuma wanda zasu shiga, Basma jikinta a mace ta bud'e k'ofan bayan mota zata shiga, sai Yaya Shureym ya daka mata tsawa yace "Karki kuskura ki shiga nan, ki shiga gaba ki zauna da driver, ko baki ga ina tare da matata bace?" cikin tsoro Basma ta bar jikin mota cike da tsiwa tace "Matarka ko Karuwa?" Ai bata rufe baki ba ya tawo da sauri ya wanketa da mari, a razane ta dafe kuncinta tace "Ni ka mara akan wannan yar iskan, to Allah ya isa mugu fasik'i kawai" tana gama fad'an haka tabar wurin da gudu, ta shige gaban motan daya d'auki kayansu ta zauna, driver ya tukasu suka wuce. Cike da k'unar rai Yaya Shureym ya girgiza kai yayi kwafa, iya ka k'uluwa Safeena tayi, amma ta share suka shiga mota tana sake-saken irin matakin da zata d'auka akan Basma, Lallai dole saita fahimtar da ita cewa ita matar Shureym ce. Suna isa gidan, ta shiga babban falon gidan Driver ya shigo musu da kayansu, d'akuna uku ne a cikin falon, ko wanne da kaya aciki wanda President yasa aka sanya musu komai na buk'ata aciki, Basma ta zauna akan kushim tana jiran su Shureym su shigo, koda suka shigo sai suka zauna suma, Yaya Shureym ya kira wani kuku, sai gashi da gudu yazo, da yake gidan ai'nahi anan Shureym yake zama, ya Umarcesa daya kawo musu ruwa, da sauri yaje ya kawo musu ya dire musu goran ruwa biyu da cup, yaje zai aje goran ruwa a gaban Basma, sai Safeena ta dakatar dashi cikin turanci tace "kai zonan" jikinsa na b'ari ya isa gurin ya risina, tace "daga yau Ni zaka rik'awa aiki amma banda wacen 'yar iskan, domin Mijina ni kad'ai yake aure" tana kaiwa nan tayi shuru, jiki na rawa Kuku ya amsa mata yabar gurin. Cikin ko in kula Basma ta mik'e tace "Yaya Shureym ina ne d'aki na?" Hararanta yayi yace "ban sani ba mara kunyar banza, wlh nan ba Nigeria bane da zaki min iskanci na d'auka, koda kika ga ina lallab'a ki, dama ina yi ne dan ayi auren, saboda kar in b'atawa Iyayena rai, kuma ki sani bana son ki, biyayya ga Iyayena yasa na aureki" Gaban Basma ne ya shiga bugawa da sauri, saboda tashin hankali, ya cigaba da cewa "kinga wannan sunanta Safeena, itace zab'ina, kuma munyi aure da ita wata guda daya wuce cikin sirri, ba tare da kowa ya sani ba, daga ni sai Mami na data goya min baya, dan haka in kina son zaman lafiya a gidan nan, to dole sai kin bita sauda k'afa, inba haka ba wlh na lahira saiya fiki jin dad'i" Basma durkushewa tayi a gurin, saboda k'afafunta bazai iya d'aukanta ba, ta shiga rera kuka wiwi, sai ya kwashe da dariya yace "wawuya nasan kin d'auka son ki nake ko, tashi dalla ki bani wuri, ki wuce d'akinki shine na gefen hagu, na tsakiya kuma nawa ne, na gefen dama na Safeena ce, kuma na haramta miki shiga d'akina" yana kaiwa nan ya mik'e ya kama hannun Safeena suka wuce d'aki. Basma cikin tashin hankali taja trolley kayanta, ta shiga d'akin daya gaya mata, katon d'akine mai d'auke da katon gado, sai daga gefe an jera kujeru set, sai bayi da kicin a ciki, kalan d'akin da kayan ciki purple da ash color ne, rufe d'akin tayi da key, ta shiga wanka, kanta ta sanyawa ruwa sosai, saboda zafin da yake mata, tayi kuka kamar zata shid'e, daga bisani tayi wanka ta d'auro alwala ta fito, kaya ta sanya mara nauyi, ta sanya hijab ta tada sallah, sai da ta rama duk Sallolin da ake binta kana tayi Addu'a, ta mik'e ta shiga cikin d'in d'akinta, komai data ke buk'ata akwai aciki, dan akwai k'aramin store a ciki, ruwan tea ta dafa, ta zo ta diba cin-cin d'in data tawo dashi a plet, ta zauna taci kana ta d'aura da danbun Namam kaza, bayan ta gama sai ta kwanta akan doguwar kujera, ta runtsa idonta ta shiga tunanin wani irin rayuwa zatayi yanzu, kuma wani mataki zata d'auka akan Yaya Shureym da Safeena wacce yake ik'ira rin matarsa ce, hawaye ne ya sauka a kuncinta, a fili tace cikin kuka "babu wanda ya jamin wannan rayuwa sai ku Abbana, dan haka ba wani matakin da zan d'auka ma, domin ko me ya sameni kune sila" Ta goge hawayenta, ta d'auko wayanta ta shiga kiran Momy, ta sanar da ita sun sauka lafiya, nan sukayi sallama, ta kira President ta sanar masa da sun sauka lafiya shima, haka kuma ta kiranl Ammi ta sanar mata da sun sauka lafiya itama, bayan ta gama wayan, sai ta tuna da Umma, sai tayi murmushi, itama ta kira ta suka gaisa, Umma tayi mata nasiha sosai akan biyayyan aure, kana suka yi sallama, saita kashe wayen gaba d'aya ta gyara kwanciya, bata dad'e ba barci ya d'auketa. *A Nigeria* Mutanan Biki duk sun watse sai dai-dai da suka rage, ta b'angaren Amare kuwa sunata cin Amarci hankalin su kwance, kowa yana cikin farin ciki. Ta b'angaren Yaya Jalal ya samu Leema ta yanda bai yi tsammani ba, domin gaskiya tasha gyara wajensu Momy, duk da dai bata isa ta maida mudurcinta ba, amma dai ya gamsu sosai da ita, Leema ta kasance cikin murna da yanda Jalal ya saki jiki da ita, tamkar babu wani abin da ya faru a baya. *A K'asar Monaco* Yaya Aryan ya cigaba da rayuwa shi kad'ai, da Umma kawai yake waya su gaida, da sun gama saiya kashe wayan. Kullun soyayyan Basma k'aruwa yake a zuciyansa, yanzu da baya ganinta yafi shiga tashin hankali da damuwa, ya k'ara ramewa sosai, burinsa yanzu bai wuce Basma ta kwantar da hankalinta ba, tayi rayuwan Aure cikin farin ciki da annatsuwa. Ya duk'ufa sosai wajen karatunsa, yana k'ok'arin kafa sabon rayuwa. *Bayan mako guda* *A America* Basma tunda ta kulle kanta a d'aki, bata kuma bud'ewa ba har tsawon mako guda, komai a cikin d'akinta take yi, hatta girki da kanta take yi, taci ta wanke kayan data b'ata, tun yin aikin na bata wuya kasantuwar bata saba yi ba, har ta fara sabawa, Allah yasa ta iya girki, domin Momy ta koyawa Basma girki dan gaba zai mata amfani, kamar yanda yanzu ya soma mata amfani. Yaya Shureym suna falo suna hira, Safeena tayi pillow da cinyansa, hankalinsa na kan k'ofar d'akin Basma, hira take mishi amma sam baya tare da ita, sha'awan Basma na d'awainiya dashi, sannan ya fara damuwa da rashin ganinta da baiyi ba, tun ran da suka zo, bai sake tozali da ita ba, Safeena ganin baya tare da ita ya barta tana ta surutu, sai ta d'ago kai tana kallon direction d'in da yake kallo, gabanta ne ya fad'i cikin jin haushi tace "Baby tunanin me kake yi haka? Ko ka fara sonta ne?" Firgigit ya farka, cikin inda-inda yace "ba komai, me zanyi da Basma, Allah ya kyauta" cikin fushi tace "k'arya kake yi, d'akinta fa kake kallo, kana ce min ba komai" murmushin ta kaici yayi domin ya soma gajiya da yawan k'orafinta, kawai ba yanda zaiyi da ita saboda yana sonta, kuma baya son b'acin ranta yace "kedai kin cika kishi, kawai ina tunanin yarinyar nan ne, akan tunda muka zo ban ganta ba, ina tsoron kar wani abu ya sameta, domin in wani abu ya sameta wlh zamu shiga cikin matsala, kinsan *YAR SHUGABA* ce, gwara na rika duba lafiyan ta domin president ya bani amanarta, ko ba komai kuma 'Yar Uwata ce" Safeena cikin nuna ko in kula tace "wannan kaita shafa" tana gama fad'an haka ta mik'e ta shiga d'aki tana jan tsaki, binta yayi da kallo yace a fili "Safeena sarkin kishi" sai ya mik'e ya nufa d'akin Basma... *Rahma Ce* (Sirrin 'ya mace group) WhatsApp. [9/29, 12:47 PM] Aysha Galadima: *'YAR SHUGABA*👑 _page_ *16.* _Na_ _*Rahma Kabir*_ Yana isa d'akin ya shiga bugawa, kwance take bisa gadonta tana kallon tv, koda taji bugun k'ofan, ta d'auki kusan minti uku kafin ta mik'e ta nufi k'ofar ta bud'e, tsaye ta ganshi yana k'are mata kallo, miyau ya had'iye da k'arfi, gaba d'aya hankalinsa ya tashi da ganin Basma cikin k'ananun kaya, hararansa tayi cikin tsiwa tace "Malam lafiya ko da matsala ne" guntun murmushi yayi bai ce komai ba, sai yabi gefenta ya kutsa kai cikin d'akin, zama yayi kan kujeran zaman Mutum d'aya, ya shiga k'arewa d'akin kallo yana shakar kamshin d'akin, wanda ya saukar masa da kasala had'e da tsananin sha'awar Basma, ita kuma tura k'ofan tayi ta koma cikin d'akin ta zauna gefen gadonta ta cigaba da kallon tv, sun kai minti biyar a haka ba tare da wani yace wani abu ba, Yaya Shureym ne ya katse shurun yace "Basma meyasa bakya fitowa falo ki zauna?" Cikin nuna ko in kula tayi banza dashi, yace "magana nake kinyi banza dani" Cikin yatsina fuska tace "naga cewa wannan ba matsalan ka bane, ka je ka cigaba da zama da karuwanka, don ni ban yarda aure ku kai ba, kyamarka nake ma, da zaka taimaka ka tashi ka fita da ka kyauta min" "Iya b'acin rai ransa ya baci, mik'ewa yayi da sauri zai isa inda ta zauna, ai da sauri itama ta mik'e tana ja da baya harta isa jikin bango, kankame jikinta tayi ta runtse ido domin yanda taga ransa ya b'aci ta sadakar zai duketa, gabda ita ya tsaya wanda hartana jin hucinsa, hannunta ya shiga b'amb'arewa a jikinta, a razane ta bud'e ido tana kallonsa, ba tayi aune ba ya rungumeta da k'arfi ya matseta a jikinshi, tirjiya ta shiga yi tana k'ok'arin kwatar kanta, ganin ya rik'eta gam yak'i sakinta, saita gantsara masa cizo a damtsan hannusa, da sauri ya saketa yana yarfe hannu, saita maza ta matsa a gun, yana jiyowa ya nima k'ara kamota, da sauri ta ruga, guje-guje suka fara a cikin d'akin, yana k'ok'arin kamata tana kaucewa. Safeena shiganta d'aki da tayi, tana tsammanin Shureym zai biyo bayan ta, sai taji shuru, ganin haka yasa ta lek'a falo sai taga wayam baya gun data barshi, cike da masifa ta fito ta nufi d'akin Basma, tana bud'e k'ofa sai ta cimmusu suna wannan wasan guje-guje, ai sakin baki tayi tana kallonsu, shiga ciki tayi rai b'ace, Shureym yana ganinta yayi sauri ya tsaya yana sosa k'eya, mugun kallo Safeena tabi shi dashi bata ce masa uffan ba, sai nuna masa hanyar waje tayi alaman ya fita, sum-sum ya fita yana murmushi k'asa-k'asa, yana fita ta gyara tsayuwa tana kallon Basma tace "A hir d'inki da Mijina domin ba sa'anki bane, in kuma ke mayya ce to Mijina yafin k'arfinki, ki shiga taitayinki domin wlh inna kuma ganin haka zan d'auki tsastsauran mataki mafi muni a gareki" tsaki Basma tayi tace cikin fad'a "ai ko wlh da kinga yanda zanyi k'asa-k'asa dake, ke d'in banza ke wacece da zaki zo ki nima shiga tsakanina da Mijina kuma d'an Uwana, kefa ba kowa bace face karuwa mara lasisi mara mutunci, ki gaugauta fita sabgata domin had'uwata dake bazai yi kyauta, kibar ganin ina miki shuru-shuru, jaka kawai" Ai tuni Safeena ta cika ta b'atse, magananun Basma sun tunzurata, bata san lokacin da tayi kukan kura ba ta nufi Basma gadan-dagan, Basma na ganin tayo kanta sai ta shige bayi da gudu tare da sanya key, tana maida numfashi, iya tsoro ta tsorata da Safeena, dan ta girmeta kuma ta fita girman jiki, tace a fili "ko banza nasha dakyar muguwa kawai" Safeena tana ganin ta shige bayi sai tayi kwafa, ta fita da sauri. Ta tada Shureym a d'akinsa, ta shiga surfa masa masifa shi dai uffan bai ce ba, da ya gaji da jin haya niyarta sai ya shige baya danyin wanka ya barta tsaye baki na kumfa, a ransa yace "Safeena akwai masifa, ta dage ta hakikance akan abin da yake halal d'ina, gaskiya bazan d'auki wannan sakarcin ba, domin ko ban son Basma ai ina feeling d'inta, balle ma ina sonta kawai kauda kai nake ina miki biyayya, saboda ina tsananin sonki, amma nasan hukuncin da zan d"auka" Basma sai da ta tabbatar ta fita a d'akin saita fito da sauri ta rufe k'ofarta, ta haye gado tana kwasar dariya, ko ba komai ranta ya mata dad'i tunda ta bak'anta ran Safeena, Jakarta ta jawo na kayan gurinta, lollypop ta d'auko, ta bud'e sweet ta sanya a baki tare da lumshe ido dan dad'in ya fara ratsa ta, nan take ta tuna da sunanta Queen Basma 'yar rawa, tashi tayi ta kunna radio tare da sakin sauti, ta shiga cashewa son ranta tare da tuno rayuwanta na makaranta cike da nishad'i. Yaya Shureym ya fito zai fita, jin wakar da Basma ta sanya yasa shi girgiza kai, a fili ya furta "Basma dangin k'uruciya" sai ya fice, Safeena ma fitowa tayi cikin shirin fita tabi bayansa da sauri ta taddashi harya kunna mota zai wuce, da sauri ta cimmasa ta bud'e gaba kusa dashi ta zauna, tana mai kallonsa cike da shagwab'a tace "haba baby shine zaka tafi ka barni" murmushi yayi yace "ai naga fushi kike dani shiyasa nayi shirin fita in je in wayata kona sarara" kamo hannunsa tayi tace "sorry Baby, d'azu raina ne ya b'aci bazan sake ba" gyad'a kai kawai yayi alaman ya gamsu, sai suka fice daga gidan. *Washe gari* Shureym ya tashi da sassafe yayi shirin office, haka ma Safeena tayi shirin fita, nan suka had'u suka fice a gidan. Basma tana jin k'aran fitan motansu, saita bud'e k'ofa ta fito, d'akin Shureym ta shiga ta gama kallon komai, yanda akayi decoration d'akin yayi mata kyau, kalan fentin coffee brown da milk color, haka ma kalan furniture d'in, d'akinsa ba kitchen sai dai akwai toilet babba wanda yafi nasu Basma. D'akin Safeena ma yanayin d'akin Basma ne, sai dai itama ba Kitchen sai toilet kamar na Basma, kalan fentin d'akin ash da pink ne hakama furniture d'inta, fitowa tayi ta shiga cikin babban kitchen na falo, nan ma ya tsaru sosai, kuku guda biyu ta gani a ciki, cikin ladabi suka gaisheta tare ta tambayan abinda take buk'ata, da murmushi tace "bata buk'atar komai" shiga tayi store d'in ta shiga diban abinda ba tada shi ta kai kitchen d'akinta, kana ta fice farfajiyan gidan, baya ta nufa inda shukoki na furanni suke, ta tsak'i iskan wurin sai taji dad'i a ranta, nan take ta tuno da wurin shak'atawan da suke zuwa ita da Yaya Aryan, idonta ya ciko da kwalla, zama tayi kan wani kujera na katako mai lilo, runtse idonta tayi ta shiga duniyan tunanin Aryan, ta kai kusan rabin awa agun kana ta bud'e ido, ta shiga rera kuka, istigfari tayi ta nima yafiyan Allah akan tunanin da tayi na Aryan Alhalin tanada auren wani akanta, tashi tayi ta nufi d'akinta ta fad'a bayi dan watsa ruwa, ko jikinta zai mata dad'i. Yaya Shureym yana office amma ya kasa aiwatar da komai, gaba d'aya tunanin Basma ya cika masa kai, burinsa bai wuce ya samu Basma ba, agogan hannunsa ya duba yaga k'arfe 11am na safe, mik'ewa yayi da sauri ya d'auki wayansa, jakansa da key d'in mota ya wuce gida. Basma ta fito wanka d'aure da towel a k'irjinta, tana zaune gefen gado cike da damuwa a ranta, tunanin iyayenta da family d'inta takeyi, tunawa tayi da tun ranar da suka sauka ta kashe wayarta bata kuma waiwayan sa ba, murmushi ne ya sub'uce mata data tuna dasu Meena, tunanin ya sukaci amarci ne ya fad'o mata, tace a fili "guys nayi missing d'inku sosai, anjima zan bud'e waya muyi chart" Tana gama fad'an haka taje kusa da dressing mirror ta soma Shafa mai, jin motsin k'ofa tayi sai ta juya da sauri, dan shaf ta manta bata rufe ba d'azun, Yaya Shureym ne tsaye yana jefo mata mayen kallo, gabanta ne ya shiga fad'uwa sam bataji k'ugin motansa ba, takowa ya fara yi yana mata wani shu'umin murmushi, Jada baya ta shiga yi, k'ok'arin isa Waldrop d'inta tayi da nufin d'auko hijabi dan ta sanya, da sassarfa ya cimmata a gurin, jikinta ne ya soma b'ari, hannu ya kai saman k'irjinta inda ta d'aura towel d'in, ta rik'e gam ta shiga kuka tana cewa "meye haka Yaya Shureym dan Allan ka fita" Murmushi kawai yayi ya sanya k'arfinsa ya fisge towel d'in, da sauri ta zukunna k'asa ta shiga kuka da k'arfi, d'aukarta yayi ya jefata kan gado, zanin gadon ta jawo ta rufe jikinta dashi, cire kayansa ya shiga yi, vest da gajeran wandon kawai ya rage a jikinsa, sai ya hau kan gadon, Basma ganin haka ta kuma rushewa da kuka, bai hanashi fasa k'udirinsa ba, zanin gadon ya shiga yayewa amma Basma ta cukukuye jikinta da shi, wani wawan mari ya sakar mata, sai ta tsandara uban ihu, duk da haka baisa ta saki ba, cikin fushi yace "wlh ko ki so ko kar kiso yau saina karb'i hakk'i na" Wani marin ya kuma sakar mata, duk da haka tak'i saki, da k'arfi ya finciko zanin gadon, sai ta k'ank'ame hannunta a k'irjinta, kuka take kamar ranta zai fita, magiya ta shiga yi masa cikin kuka "Yaya Shureym dan Allah ka kyaleni karka kasheni, me nayi maka ne da zaka yi min mugunta" Bige mata baki yayi, bakin ya fashe sai jini, abinda yake son aiwatarwa bai fasa ba, Basma kuwa gunjin kuka take yi, a wannan lokacin tariga ta sadak'ar, cizo ta ganna masa a kunne sai ya saketa ya kai mata naushi a baki, ya shiga dukanta ta ko ina Basma wani wahalanlan ihu ta saki wanda yayi dai-dai da shugawar Safeena falon, dama ta shigo falon da mamaki, saboda ganin motan Shureym da tayi a gida, da sauri ta nufi inda take jin kukan, harta isa d'akin Basma, ta tsaya a bakin k'ofar, dai-dai lokacin Shureym yana k'ok'arin kai ga cika k'udurinsa Basma ta saki wani wawan k'ara, ai da k'arfi Safeena ta tura k'ofan ta buga garam, ta fad'a d'akin ta tuna huci.... *Rahma Ce* (Sirrin 'ya mace group) WhatsApp. [9/29, 12:47 PM] Aysha Galadima: *'YAR SHUGABA*👑 _page_ *17.* _Na_ _*Rahma Kabir*_✍🏾 K'aran bugun k'ofar shine yayi dai-dai da Shureym ya dawo hayyacinsa, da sauri ya sauka akan gadon, cikin jin haushi da borin kunya ya kwaci kayanshi a hannu ya fita a d'akin, da gudu-dugu ya fad'a d'akinsa tare da sanya key. Basma kuka take tana cewa "Allah ya isa bazan yafe maka ba, mugu azzazulumi insha Allah harka mutu baza ka cimma burinka a kaina ba" furucin Basma na k'arshe shine ya sanya Safeena ajiyan zuciya, dama fargabanta shine ace ya samu Basma, tasan lallai kashinta ya bushe, gashi Basma ta fita komai na kyawun sura, sannan ta tabbatar Basma bata bin maza lallai zai sameta a budurwa, kallo Basma tayi cikin tausayawa, da sanyin murya tace cikin tsoratarwa "Kad'an kika gani in dai Shureym ne, mugune shi sosai haka yakemin nima, karki k'ara yanda haka ta faru in ba haka ba wataran zai kashe ki, maza tashi ki gasa jiki a toilet, kuma karki sake barin k'ofarki a bud'e, dan Shureym ya wuce yanda kike tunani" tana gama fad'an haka ta fice a d'akin. Basma wani sabon kuka ta saki, da kyar ta iya sakowa daga gadon, tana bin bango harta shiga bayi, ruwa ta had'a mai zafi ta shiga ciki, ta kai kusan rabin awa tana ciki, kana tayi wanka ta fito, mirror taje ta tsaya tana kallon yanda fuskanta ya kummbura, hawaye ne ya sauka a kuncinta mai zafi, fuskan ta tayi ja sosai, gashi kumatunta ya kunbura da leb'enta, idonta yayi k'anana gaba d'aya ya sauya mata kamanni, hawaye ta share tace a fili "Abba Ku kuka jamin" kaya ta sanya marasa nauyi ta cire zanin gadon ta ta sanya wani, taje ta kulle d'akinta ta koma gadon ta kwanta cikin k'ankanin lokaci barcin wahala ya d'auketa. Shureym saida ya samu yayi wanka kafin ya samu nutsuwa, nadama ne ya lullub'eshi akan abinda yayi wa Basma, ga kuma kunyar Safeena da yakeji, wannan dalilin ne ya hanashi fitowa sai kawai ya kwanta har barci ya d'aukeshi. Safeena kuwa ta kasa ta tsare a falo tana jiran fitowan Shureym, jin yayi shuru bai fito ba saita gyara zama ta kunna tv tana kallo, sai bayan k'arfe biyu Shureym ya fito daga d'akinsa, ya had'e giran sama dana k'asa yana hura hanci duk na borin kunya, Safeena tana ganin shi sai ta kwashe da dariya, dan gaba d'aya ya bata dariya sai wani basarwa yake yi, zama yayi gefenta yace cikin fishi "meye kika gani na dariya a jikina?" ya mutse fuska tayi tace cikin tsiwa "wlh Shureym kaji kunya, banda Allah yasa nazo na ritsaka, da ka kashe musu Yarinya, kanata cika min baki akanta, ashe duk burga ce na d'a Namiji, Allah ya kyauta maka, kuma ka sani Basma Yarinya ce imma zaka amshi hakk'inka, to ba da k'arfi zaka amsa ba saika bita a hankali" Tana gama fad'a ta mik'e ta shige kicin, abinci ta zubo masa ta mik'a masa, murmushi yayi ya amsa tare da cewa "Tnx my Baby, banyi tunanin zaki saurin saukowa haka ba" hararenshi tayi ta koma ta zauna tare da d'aura k'afa d'aya kan d'aya, ya soma cin abincin tace "Shureym ina Sonka sosai, bazan iyi dogon fishi da kai ba, da ace d'azun baka rufe d'akinka ba, har na sameka a ciki, da saina sauke maka kwandon rashin mutunci, amma na sauko, sai dai yanzu na daina yarda da alk'awarinka domin nasan watara saika karya shi" zai yi magana ta d'aga masa hannu tace "kai dai ci abinci kawai". Bayan la'asar Basma tayi shigar doguwar riga abaya brown, tayi rolin da gyalen, jaka ta d'auka bak'i ta sanya takalmi bak'i, ta same su a falo bata kalli inda suke ba tayi hanyar fita, da sauri cikin tsawa Shureym yace "ke ina zaki?" tsayawa tayi cak bata juyo ba kuma bata ba shi amsa ba, saida ya kuma maimaita tambayan, amma shuru ta masa, k'arshema tasa kai ta fice, a zuciye ya mik'e zaibi bayanta, Safeena na rik'e hannunsa tace "haba Shureym wani irin abune wannan, ka duketa d'azun ka kumbura mata fuska, ka sani ko asibiti zata je, ka rabu da ita taji da kanta mana" cike da mamaki ya juyo ya kalleta yace "Safeena yaushe kika zama haka? da har zaki tausayawa wannan shaid'aniyar yarinyan' murmushi tayi tace "Shureym ni mace ce mai rauni, dole ne inyi saurin tausaya mata akan irin lahanin da kaso yi mata, tana gama fad'an haka ta d'aure fuska, kana ta wuce d'aki. Basma tana fita ta tari taxi asibiti ta fara zuwa, likita ya dubata ya bata Magani da kuma alluran zazzabin da take ji, daga nan saita wuce wurin wani gidan abinci, zama tayi ta sanya aka kawota drink da snacks, nan taci tana nazarin wani mataki ya kamata da d'auka, a haka ta gama komai saita wuce wani studio na kusa da gidansu, ta shiga ta sanya aka d'auki hoton fuskanta kana aka wanke aka bata ta dawo gida. Bata samu kowa a falon ba saita wuce d'akinta ta bud'e ta shiga tare da sanya key, wani jaka ta ciro ta bud'e da wani k'aramin key, ta ciro diary d'inta ta shiga rubuta abin da ya faru da ita na wannan ranar, sannan ta maida cikin jakan tare da sanya wannan hoton aciki, sai ta maida ta rufe ta ajeshi cikin wani dirowa, ta dawo kan gado ta zauna tare da rafka tagumi. Wannan diary d'inta ne tun ranar da suka sauka a k'asar America, ta fara rubuta duk abinda Yaya Shureym yake mata na muzgunawa a ciki, dan ya zame mata tarihi da zata rik'a tunawa. Wayarta ta ciro a jaka ta kunna, sak'onnin text suka fara shigowa, gaba d'aya text d'in yan uwanta ne, d'aya bayan d'aya ta rik'a karantawa, wani tayi kuka wani tayi dariya, nan take kewar family d'inta ya taso mata, WhatsApp d'inta ta bud'e, sakonni suka fara shigowa, ta mance rabonta da hawa online, group ta shiga na family d'insu, nan fa tayi sallama suka fara amsawa cike da murnan sake ganinta, duk suka gaisa na yaushe gamo, Meena ce tace "ke Besty akwai labari muje group d'inmu" nan suka koma group d'in su mai sunan *Manyan Mata, One family* Leema ma ta shigo can sai ga Deeja ta shigo, yanzu su had'u ne a group d'in, sunata murnan ganin Basma, nan suka shiga hira, Meena tace "kinsan kuwa Leema da Deeja ciki ne dasu" Basma cikin farin ciki tace "Dagaske? kice mun kusa samun yara" "Eh wallahi, two month yanzu" "ikwan Allah, yanzu fa mun kai 3month da aure, lallai abin ba wuya, to Allah ya musu albarka ya rabasu lafiya, to Meena kefa?" Meena tace "Ni nawa 1month ne yanzu" "lallai kuce kun girma, Allah ya inganta" Deeja tace "waya sani ko kema kina da naki a k'unshe bamu sani ba" dariya tayi sosai tace "wace ni, ai in gaya muku banda komai, ina planning tukunna" Leema tace "Malama ki fad'a mana gaskiya kawai" "Hmmm Allah kuwa gaskiyar kenan" nan dai suka cigaba da hira, sun shafe lokaci sosai suna hira, sallama su kayi saboda dare yayi sosai a Nigeria, su kuma Basma yamma ne a nan. Cike da kewar family d'inta ta mik'e ta shiga kicin, abinshi ta shiga girkawa. *Bayan Mako biyu* Basma ta shirya da yamma k'arfe hud'u, tayi shigar riga da wando na Pakistan, tayi rolin da gyalen shi, jaka ta d'auka da takalmi ta ficewarta, yau tayi sa'a ba kowa a falon, taxi ta tare ta nufi wurin cin abinci, yau drink kawai ta sha, saita ciro wayarta ta hau online tana chart dasu Meena, wani saurayi ne mai tsayi kyakkyawa, ya tako a hankali har wurin da Basma ta zauna, ya tsaya tare da yi mata sallama, cike da kulawa ta amsa tare da d'ago kanta, cikin harshen labarabci yayi mata magana yace "In zauna?" murmushi tayi tace "eh" sai ya zauna ya cigaba da magana "Ni sunana Bilal dan k'asar Sudan, nazo nan karatun masters d'ina ne" murmushi tayi cikin larabcin tace "sunana Basma Bulama ni 'yar Nigeria ce" cike da mamaki ya kalleta yace "kina nufin ke 'yar Nigeria ce?" Tace "kwarai kuwa" murmushi yayi yace "nayi miki kallon ke 'yar k'asar labarawa ce, shiyasa ma nazo nayi miki magana, ashe 'yan Nigeria sunajin labarci sosai haka" dariya tayi tace "sosai kuwa munaji, domin muna da makarantu acan na larabci" yace "good, yanzu meya kawo ki America?" murmushi tayi tace "Hutu muka zo tare da family na" yace "masha Allah, in ba damuwa zan iya zama abokinki?" murmushi tayi tare da yin tunani kad'an tace "eh ba damuwa" nan su kayi exchanging contact d'insu, tare da alkawarin zasu had'u washe gari in Allah ya kaimu, nan ya taka mata ta shiga taxi kana ya wuce shima yana farin cikin had'uwa da Basma, cikin k'ank'aninin lokaci ya kamu da Sonta, Basma irin tsarin matar da yake burin aura ce, dama ashe a Nigeria suna da kyawawan mata haka? Tambayan da yayiwa zuciyansa kenan, harya k'osa dare yayi gari ya waye su k'ara had'uwa. Basma tana isa gida ta same su zaune a falon, kallon arziki bata yi musu ba ta wuce su, Yaya Shureym yace "Basma wai ina kike zuwa ne?" cikin b'acin rai tace "inda ka aikeni, kuma ka fita cikin rayuwata in ba haka ba zan maka abinda baka tsammani daga gareni" tana fad'an haka tayi gaba, bud'e murya yayi yace "wlh in kika kaini mak'ura zaki sha wuya, mara kunyar banza" tsaki tayi ta bud'e d'aki ta rufa da k'arfi ya buga gam, kana ta sanya key, tayi wanka tare da d'auro alwalan Magrib. *Washe gari* Ya kama week end, yau Shureym yana gida yana hutawa tare da matarshi Safeena, da misalin k'arfe biyun rana Safeena ta fito, tazo d'akin Basma, bugawa tayi amma kusan minti biyu shuru Basma bata bud'e ba, saida ta kuma bugawa tare da bud'e murya tace "Basma ki bud'e Safeena ce" murmushi Basma tayi ta sauko a kan gadon ta bud'e mata, da murmushi a fuskan Safeena tace "Basma dan Allah kin iya wainar fulawa?" Basma tayi murmushi tace "eh na iya" "to dan Allah kiyi hak'uri ki d'an yi min mana, saboda Kuku basu iya ba, kuma wlh marmarinsa nake, in kuma ni nayi bazan iya ci ba" murmushi Basma tayi tace a ranta "shegiya yanzu haka ciki ne dake, kuma in dai wainar fulawa ce za kici kuwa" tace a fili "OK muje nayi miki" "yauwa sis nagode bari na jiraki a falo" murmushi kawai Basma tayi bata ce komai ba, tace aranta "wato yau kinzo da fuskan arziki kenan, saboda zaki more ni, dole a fake da cemin sis" kicin ta shiga, cikin minti talatin ta had'a mata wainar fulawa, taji kayan had'i kuwa, saita kawo mata harda ruwan sha, ta aje bisa table na falon, Safeena na gani ta Shiga lashe baki, jiki na b'ari ta jawo table ta shiga cin wainar, ai had'iyan farko ya tsaya mata a wuya, da sauri ta tashi da gudu ta fad'a bayin dake falo, ta shiga kwara amai kamar zata amayar da hanjin cikinta, Basma zama tayi a falon tana zuba dariyan mugunta, Safeena a galabaice ta fito ta zauna tana maida numfashi, Shureym ne ya shigo falon yana fad'in "Safeena lafiya har yanzu aman bai tsaya ba, ko zamuje asibiti ne?" cikin kasalan murya Safeena ta nuna Basma tace "kaga wacce ta sani amai, nace ta min wainar fulawa saita zabga masa yaji da gishi, loma d'aya nayi na kasa had'iyiwa saida na amayar dashi" cikin b'acin rai ya kalli Basma yace "dan Ubanki kashemin mata zaki ko, saboda kina bak'in ciki da abinda ke cikinta ko, to wlh maza tashi kije ki dafa mata wani wainar, kuma in kika yi kuskure jikinki zai gaya miki" Jikin Basma a sanyaye ta koma kicin ta kuma b'ata lokaci ta had'o wani wainar ta kawo mata, Safeena ta saki ciki ta soma ci harda lumshe ido dan dad'insa saida ta cinye tas kana ta kora da ruwa. Shureym ya kalli Basma yace "D'auko wancen da kika b'ata ki cinye, dan wlh baza kimin asanar abinci ba" cikin k'unk'unai tace "wlh ni na k'oshi" belt d'in wandonsa ya zaro ya rik'e, yaje ya d'auko plet d'in wainar fulawan ya dire a gabanta yace "wlh sai kinci, in kuwa baki cinye ba jikinki zai gaya miki" ai da sauri ta sanya hannu ta d'ibo, tana kaiwa bakinta, zafin yaji da gishiri ya d'arsu a kan harshenta, ai da sauri ta furzar tare da goge harshen, Shureym ya zuba mata belt d'in a gadon bayanta, ai saita tsandara ihu ta shiga sosa bayan, bai hanashi sake zabga mata belt d'in jikinta ba, ya shiga jibgarta tare da cewa saita cinye shi, Safeena dariya ta shiga yi tare da d'aura k'afa kan table, saida yayi mata lilis kafin ya dena dukanta, kuka take tace "Allah ya isa Shureym, haka kawai ka maidani baiwarka, wlh sai kayi nadaman abinda ka aikatamin, azzalumi fasiki, maci amana" wani wawan naushi ya kai mata a baki, nan take bakinta ya fashe ya shiga zubda jini, da sauri Basma ta dafe bakinta tana kuka, tashi tayi dakyar ta isa d'akinta... *Rahma Ce* (Sirrin 'ya mace group) WhatsApp. [9/29, 12:47 PM] Aysha Galadima: *'YAR SHUGABA*👑 _page_ *18.* _Na_ _*Rahma Kabir*_✍🏾 Bayi ta shiga ta gasa jikinta da ruwan zafi, domin duk jikin yayi mata tsami, bayan ta fito ta samu ta sanya kaya ta fice zuwa studio, photo ta d'auka aka wanke mata, fuskanta ta fito da kyau bakinta a kubbure, ta dawo gida. Rubutawa tayi a diary d'inta kamar yanda ta saba, kana ta koma ta ajiye shi a mazau ninsa, ta had'a tea tasha kana ta d'aura da pain relief tasha, saita bi lafiyan gado. *Nigeria* Gudu take tana ihu, Abba kawai take kira tana cewa "wayyo Abba zai kasheni kazo ka taimake Ni, Momy na wai bakwa sona ne kuka bari zai kashe ni" a razane Abba ya farka daga barcin tare dayin Addu'a *"A'uzu bi kalimatil lahit taammat min sharri ma kalak'a"* gumi ne ke tsatsowa a jikinsa, gaba d'aya hankalinsa ya tashi, jingina yayi jikin gado, Momy ta farka a barci saita ganshi zaune, tashi ta yi ta zauna, cikin muryan barci tace "yallab'ai lafiya ka zauna cikin wannan Daren?" agogan dake manne a d'akin ta kalla, k'arfe biyu da rabi na dare, sharce zufa yayi ya dafe kansa cikin damuwa yace "Hajiya Maryam wlh mugun mafarki nayi da Basma, hakan ya nuna kamar tana cikin Matsala" Momy ta gyara zamanta tace cikin natsuwa "Abba wannan aikin shaid'an ne kawai, amma Basma bata cikin matsala, saboda munsan wa muka bama 'yar mu fa, kawai dai kila ka sanya ta a ranka ne saboda rashinta na tsayin lokaci da bata tare damu" ajiyar zuciya yayi yace "a gaskiya jiki na ya bani Basma tana cikin damuwa, insha Allah gobe in Allah ya kaimu da sassafe zanje America dan ganin lafiyar ta" ajiyar zuciya Momy tayi tace "Allah ya kaimu goben nima saina maka rakiya" murmushi kawai yayi ya tashi ya shiga bayi, alwala ya d'auro ya shiga jero sallan Nafila, itama Momy bata kwanta ba, tashi tayi itama tayi alwala tare da gabatar da nata Nafilan. *Washe gari* Da misalin k'arfe Bakwai na safe su Abba sun gama shirin tafiya, Abba ya hana Momy tafiya yace tayi zamansa ba zai kwana ba shima, Yaya Naufal tare da muk'arrbansa suka wuce airport ba tare da b'ata lokaci ba, dama jirgin President na jiran zuwansu, shiga suka yi suka kama hanya sai America. *America* Basma na kwance a d'aki sai nishi take fitarwa da k'arfi, numfashinta na fita da kyar, ta rufa da bargo amma duk da haka bai hanata jin sanyi ba, sai kerma jikinta yake yi, zufa ne ya lullb'eta hawaye na fita a idonta, a wannan lokacin tana buk'atar tai mako. President suna isa, aka turo motoci daga gidan shugaban k'asar America ya kwashe su, sun gaisa dashi kana suka ci abincin, shi Abba ya kasa cin komai drink kawai yasha, burinsa bai wuce yaga Basma ba, wayarsa ya ciro ya kira Shureym, bugu biyu ya d'auka cikin ladabi yace "Abba ina kwana?" Abba ya amsa fuska sake yace "Shureym gani nazo k'asarku, ina gidan shugaban k'asa, kana ina kazo ka kaini gidanka, domin mu gaisa da Basma" Ai bai k'arasa maganan ba jikinsa ya d'auki rawa, muryansa har tana sirk'ewa dan fargaba yace "Abba naje wurin aiki gani bisa hanya zanzo" "OK saika zo karka b'ata lokaci fa domin yau zan koma" "to Abba, insha Allah gani bisa hanya". Sai suka kashe wayar. Ai jikin Shureym na rawa ya tafi gidanshi, ya kira Safeena ya shaida mata zuwan President, itama hankalinta ya tashi, yana isa ya shiga gidan a sukwane, ya samu Safeena a falo tana kai kawo, da sauri ya kama hannunta yace "kije gidan k'awarki, anjima in sun tafi zan kiraki ki dawo" jiki na rawa ta fice a gidan, d'akin Basma ya nufa ya bubbuga k'ofar amma shuru, hankalinsa a tashe yace "Basma dan Allah ki bud'e, Abba ne ya zo zani na d'auko shi, dan Allah ki rufa min asiri zan gyara mistake d'in dana miki pls Basma, bari naje da sauri kinga ma kirana yakeyi" bai jira amsarta ba ya fice da sauri. Hawaye Basma ta cigaba da fitarwa tace "Bana son ganin kowa, gwara na mutu ma" tsaki taja ta mik'e da kyar ta shiga bayi wanka tayi ta sanya atamfa, riga da sket, bud'e k'ofar d'akin ta tayi, kana ta koma kan gado ta kwanta saboda zazzab'in bai saketa ba. Sun iso gidan Shureym sai rawan jiki yake yi, yana fargaban Basma karta tona masa asiri, koda suka shiga falon sun zazzauna, sai Shureym yace "Abba bari na kirata" murmushi yayi yace "Basma fushi take dani, dan tasan da zuwana, ya kamata ace mun sameta a tsakar gida dan tarbanmu, barni da ita bari naje na lallasheta" Gaban Shureym ne ya buga damm, amma sai yayi na maza yace "OK Abba ga d'akinta chan" ya nuna masa d'akin da hannunsa, Abba mik'ewa yayi da sassarfa ya wuce d'akin, turawa yayi a hankali tare da sallama, Basma na kwance ta runtsa idonta hawaye me zafi ya fito a idonta, kanta ta santa cikin bargo ta share hawayenta, ta amsa sallaman a zuciyarta, Abba matsawa yayi gaban gadon cikin lallashi ya fara magana "haba shalelen Abbanta fushi kike dani, kiyi hak'uri kinji Basma na, aiki ne ya hanani zuwa, wannan tafiyan musamman dan ke nayishi" Kukanta ne ya fito fili, da sauri ya yaye bargon, sai yaga tana rawan sanyi, da sauri ya isa gareta ya dagota, jikinta ne yaji yayi zafi kamar wuta, yace "ya salam Basma ba kida lafiya ne?" Langwab'ewa tayi a jikinsa, da sauri Abba ya d'auketa yayi falo da ita, ai Shureym yana ganinsu, gabansa yayi mummunar fad'uwa, rai bace Abba yace "yanzu Shureym har zaka iya tafiya aiki ka barmin Basma kwance ba tada lafiya?" cikin in ina yace "em em Abba ayi hak'uri, nima na fita nabarta tana barci, ban zata zazzabi take ba" Abba yayi tsaki yace "shirman banza, Amanar dana baka kenan nace ka kula min da ita shine zanzo na ganta haka, Yarinya duk ta lalace ta fita hayyacinta" zama yayi da ita akan kujera ya kalli fuskanta, ai gabansa ne ya dad'i, da k'arfi ya furta "Basma me ya sameki a fuska? ya bakinki ya kumbura haka, me yake faruwa ne wai?" Basma banda kuka babu abin da yake yi. Jikin Shureym ya d'auki rawa cikin sark'ewan murya yace "Abba fad'uwa tayi, santsin tyles ne ya kwashe ta ta fad'i, ina ga fad'uwan da tayi shine ya saukar mata da zazzab'i" Basma mamaki ne ya cikata da irin k'aryan da Shureym yake fad'a, Abba ya kalli Basma yace "wai hakane Basma?" cikin kuka tace "eh" wani nannauyen ajiyar zuciya Shureym ya saki ba tare da kowa ya gane ba, Abba yace "to Shureym zan tafi da ita Nigeria, inta samu sauk'i sosai sai na dawo da ita" da sauri Shureym yace "haba Abba kayi hak'uri, ka barta anan, zan kaita asibiti a dubata da kyau, ko jiyan ma na bata pain relief tasha, bansan jikin nata yayi zafi haka da tun safe munje asibiti" Ajiyar zuciya Abba yayi yace "to shikenan bari mu tafi, sai ka d'auketa yanzu ka kaita asibiti mu zamu wuce kawai, Allah ya sauke" ya kalli Basma yace "Basma su Amminki da Momy suna gaidaki, Yayanki Ahmad ya so zuwa, aiki ya rik'eshi" murmushi tayi tace a hankali "ina amsawa" ta kalli Yaya Naufal ta gaisheshi, ya mata sannu da jiki, duk ta gaisa da wanda suka rako Abba, bandir d'in kud'i mai yawa Abba ya bama Basma yace "ga wannan kud'in in kina buk'atar wani Abu" cikin murmushi tace "Abba akwai kud'i a guna fa" "eh na sani ki k'ara da wannan d'in" godiya tayi masa da kuma Addu'an Allah ya sauke su lafiya, ta bada sakon gaisuwa wurin su Ammi da duk family d'in ta. Shureym ya kamata kamar gaske sai wani lallab'ata yake, haka suka yi musu rakiya har mota, Basma tana d'aga musu hannu tare da zubda hawaye, Abba tausayinta ya kamashi kwalla ne ya faru a idonsa, shanyewa yayi tare da d'auke kansa, har suka bar haraban gidan. Shureym mota ya sanya Basma ya wuce da ita asibiti, likita ya bata Magani da kuma allurai nan akayi treatment d'inta, sannan ya biya da ita wurin siyayyan kayan ciye-ciye, ya siya mata su ice cream, kana suka dawo gida, d'aukanta yayi cak ya kaita d'akinta, bisa kan gadonta ya direta, ya zauna a bakin gadon, yace cikin sanyin murya "Nagode Basma da kika rufa min asiri a yau, nayi nadaman duk abin da na ai kata miki, Basma wlh ina sonki sosai, ke kike ja nake dukanki, pls ki amince mu fara zaman aure kamar kowa" Hararansa tayi tace "Shureym ina so ka sani, a duniya kaine mutumin dana fi tsana, kuma kar kaga na rufa maka asiri, kawai na kyaleka ne saboda Iyayena su suka jamin duk wulak'ancin da kake min, ka mai dani baiwarka mara gata da galihu, wlh ka sani na baka talala ne kayi duk iskancin daka ga dama, wlh nasan akwai limit, wataran ko ance ka min wlh bazaka yi ba, dan haka ka tashi ka fita min a d'aki mayaudari kawai azzalumi" Iyaka fushi ya zuciya, amma dakewa yayi bai furta komai ba, ya fice ad'akin tare da jawo mata k'ofa. Kuka ta saki mai tsuma zuciya tace "Abba kun cuceni, da gatana na zama baiwa, Ina *'YAR SHUGABA* na zama mara galihu" saida tayi kuka mai isarta, kana ta mik'e ta fita falo, kud'in da Abba ya bata ta d'auko su a inda ta bari, d'aki ta koma ta rufe, ta aje kud'in a inda take adana kud'inta, murmushi kawai tayi ita kad'ai tasan matakin da zata d'auka akan Shureym. Safeena bata dawo ba sai cikin dare, ta shiga d'akinta, wanka tayi ta fito tana tsaki, zama yai tace "gaskiya Shureym na gaji da wannan auren boyen, ya kamata a fito da zancen nan kowa ya sani, Ni da Mijina auren halal, amma ina guje-guje sai kace auren tsiya mukayi, to wlh da sake, ka kira Maminka ka sanar mata na gaji da wannan wasan kuran da nake da danginka" Sassauta murya Shureym yayi cikin lallashi yace "Haba my baby love, meye na damuwa? da zaran kin haihu magana zai bayyana a dangi, ran nan nayi magana da Mami ita tace haka, dan haka ki kwantar da hankalinki, yanzu cikinki ba wata hud'u ba, nan da 5month in kin haihu komai zaiyi dai-dai" Ajiyar zuciya tayi tace "to shikenan baby wlh d'azun naji haushi sosai, kawai an sani yini a gidan mutane" murmushi yayi ya kamota, nan ya shiga jefa mata zazzafar soyayyansa, tuni ya mantar da ita damuwa. *Rahma Ce* (Sirrin 'ya mace group) WhatsApp. [9/29, 8:48 PM] Aysha Galadima: *'YAR SHUGABA*👑 _page_ *19.* _Na_ _*Rahma Kabir*_✍🏾 *Nigeria* Abba sun sauka lafiya cikin dare, ya shaida ma su Momy Basma na gaishesu ba wata Matsala. Yaya Naufal ya labaratawa Yaya Ahmad duk abinda ya faru, damuwa ne ya ziyarceshi yace "anya kuwa Shureym na kula da Basma?" Yaya Naufal yace "yana kula da ita a yanda muka gani, kuma ai in da da matsala zata gayawa Abba" murmushi kawai Yaya Ahmad yayi a ransa yace "ban yarda ba dole zanyi bincike akai, dan Basma tana da zurfin ciki, ni kad'ai take gayawa damuwanta ko Momy" a fili kuma yace "hakane, to Allah ya bata lafiya ya k'ara musu zaman lafiya" "Ameen" Yaya Naufal yace, kana ya wuce part d'inshi. *Kasar Monaco* Aryan yayi nisa cikin karatunsa, a yanzu hankalinsa ya kwanta, sai dai har yanzu bai maida jikinsa ba, yana waya dasu Umma da Khadija sai Yaya Ahmad, yanzu ya daina kashe wayansa kullun tana kunne, har yanzu bai dawo cikin walwala ba, baya dariya sai dai yak'e kuma shima saiya d'auro, murmushi ne kawai ya kanyi time to time. Wata rana yana makaranta ya fito daga aji yana tafiya, karo yaci da wata ta tawo a guje bata lura dashi ba, d'agowa tayi cike da tsoro, cikin harshen turanci tace "yi hak'uri wlh ban kula bane" gyad'a mata kai kawai yayi sai ya rab'eta ya wuce, binsa tayi da kallo cike da tunani barkatai, "iya had'uwa wannan guy d'in ya had'u, ko dan wani kasa ne oho? Gaskiya bazan bari ya kub'ucemin ba, dan na kamu da sonsa, kuma shine dai-dai tsarina" Abinda take fad'a a ranta kenan, da gudu ta bi bayanshi, bata san sunanshi ba gashi ya tsere mata, duk da haka bata hak'uri ba, ta cigaba da bin bayansa da gudu ta cimmasa, gabansa ta sha, sai ta tsaya cike da yin nishi tace "Yi hak'uri na tsaidaka, sunana Jidda Bukar, ni 'yar Nigeria ce katsina state, muna zama a Abuja, nazo nan karatu ne, in ba zaka damu ba ko zan san daga ina kake? dan kayi min zubin d'an k'asar India" Murmushi yayi a takaice yace cikin harshen turanci "sunana Aryan Aliyu, Dan k'asar Nigeria" ido ta zaro tace "wow ashe k'asarmu d'aya, wlh gani nayi ba kayi kama da 'yan Nigeria ba, amma nayi murna sosai, cewa nayi bari na biyo ka saboda naga Kana da sauk'in kai, in ba damuwa ko zamu kulla abota" ransa ne ya b'aci, amma saiya dake cikin rashin sakin fuska yace "nagode, amma ba zai yuwu ba kawai, in dai mun had'u sai mu rik'a gaisawa" yana gama fad'an haka ya wuce, binsa ta cigaba da yi tare da yi masa magayi akan suyi exchangen number, tsayawa yayi zuciyansa na tafasa cikin masifa yace "ya isa dan Allah, kiyi hak'uri ina da mata, pls ki fita a harkata, sai wani bina kike kamar naci miki bashi" jikinta ne yayi sanyi bata k'ara furta komai ba sai ta juya ta fara tafiya, tausayi ta bashi sai ya dakatar da ita yace "Jidda kiyi hak'uri ban cika son ana takura min ba" juyowa tayi idonta ya cika da kwalla tace "ba komai na fahimceka" Numbern shi ya karanta mata, kana suka yi sallama. Ta wuce cike da murna shi kuma ya tafi cike da tunanin Basma, ji yake kamar yaci amananta, wani b'angare na zuciyansa yace "bakaci amana ba, itama ai tanacan tare da mijinta" runtse idonsa yayi hawaye mai zafi ya fito masa, ji yayi komai ya dawo mishi sabo, zazzab'i ne ya rufeshi, sai ya tafi gida cike da matsananciyar damuwa. Tun daga wannan ranar Jidda ta mak'alewa Aryan, Sam baya son abinda take masa, yana k'ok'arin janye mata amma sai k'ara shige masa take, ita burinta bai wuce ta samu zuciyar Aryan, ko bazai aureta ba tunda yace yana da mata, zata amince masa su tab'a rayuwa ko kad'an ne, domin tana fama da sha'awansa. Aryan yana gida a kwance da yamma, sai yaji anyi masa knocking, tashi yayi ya tafi ya bud'e, mamaki me ya rufe shi ganin Jidda ce, murmushi tayi masa sai tabi gefensa ta shige d'akin, binta yayi da kallon yana mamakin yanda akayi tasan gidansa, cikin nuna ko rashin damuwa Jidda ta cire mayafinta ta zauna a kan kujera mai mazaunin mutum d'aya, komawa yayi ya zauna kujeran dayake fuskantarta tace "Nasan kayi mamakin yanda akayi na gano gidanka, kasan ance mai son d'an tsuntsun shike binsa da jifa, Aryan wlh ina sonka amma kak'i bani gurbi a zuciyanta" Aryan d'aure fuska yayi yace "Jidda nafiso ki bar alak'anmu da abota kawai, domin bana tunanin zaki samu gurbi a raina, dan na riga na bada soyayyata ga wata" Hawaye ne ya cika mata ido tace "pls Aryan, ni wlh ko kaina kace in baka a shirye nake" mik'ewa tayi ta juya a gabansa ta cigaba da cewa "Kalli surata da kyau, ina da duk abinda mace take dashi a jikinta wanda namiji zai mora, dan Allah ka yarda dani in zama mai d'ebe maka kewa, koda baka sona in har ka yarda min da haka zanyi murna" Aryan cikin b'acin rai ya mik'e nuna mata hanyar waje yace "Jidda natsaki na tsani mata masu irin halinki, ki sani har ki mutu ba zaka samu yanda kike so ba domin nafi k'arfin iskancinki, kuma ki sani Ni ba kalar ki bane, ki gaugauta cireni a cikin jinsin mutanan da kikasani" jiki na rawa ta mik'e zata bashi hak'uri, cikin tsawa ya dakatar da ita "Na ce ki fita" da sauri ta kwashi kayanta ta fita tana mai jin haushin kanta, rufe k'ofarsa yayi tare da sauke ajiyan zuciya, Addua yayi da k'ara niman tsari ga irin wannan matan. Tunanin Basma ya shiga yi, "Yarinya ce mai natsuwa, duk wayewarta a kame take, ga kud'i da jin dad'i na rayuwa amma akwai tarbiyya mai kyau, har abada yanajin ba zai samu mace kamarta ba" hawaye ne ya zubo mashi yace a fili "Basma har abada ina sonki, babun macen da zan aura ta kai matsayinki, nasan haduwata dake wani jarabawa ne a rayuwana, Allah ya rabamu ina tsananin sonki, Allah ka bani wacce zata share min hawaye na". *_Aryan nima na tayaka da cewa "Ameen". Masu karatun bari mu koma k'asar America mu ga wainar da Suke toyawa._* *Bayan wata guda* Basma ta warware, zamansu kuma yana nan zaman doya da manja, da dad'i ba dad'i, kadaran kadahan, Basma yau tasha Riga da wando English wears, saita d'auko gyale tayi rolin iya kyau tayi, jaka ta d'auka ta fito falo, Safeena ta tarar tana shan fruit, Safeena tace cikin tsokanar fad'a "Ayawo yau kuma shigan yan iska kike ji?" Basma bata tanka mata ba, illa tsaki taja ta fice, Safeena ta ce " 'yar rainin wayo, zaki had'u da Shureym shine dai dai da iskamcin ki". Basma na fita taxi ta shiga ta wuce inda suke had'uwa da Bilal, ta sameshi yana jiranta, kallonta yake cike da soyayya yace "Basma kinyi kyau sosai" murmushi tayi tace "nagode muje ko" wurin shak'atawa suka wuce, suna tafe suna hira, Bilal yace "Basma yaushe zaki kaini gidan ku na gaida da Iyayenki, nifa da gaske sonki nake kuma aurenki zanyi, dan har na fara magana da Ammi na" Murmushi tayi tace "ni iyaye na suna Nigeria, yanzu da Yaya na muke a nan k'asar, kuma ina so ka sani gaskiya ina da aure" ai bata k'arasa maganar ba ya juyo a zabure yace "pls my Basma ki daina fad'an wannan maganar imma wasa kike" murmushi tayi tace "Bilal da gaske nake, Mijina dai baya tare dani yana k'asarmu" tab'oye masa hakan saboda bata son yasan komai nata, cike da damuwa ya samu guri yayi parking yace "meyasa kike wasa da aure, Basma na tabbata ke mace ce mai ilimin addini, meyasa bakya amfani dashi, yanzu kusan 1month da had'uwarmu, sauk'in abin ma tun farko kink'i Amincewa dani muyi soyayya, kin ce ke kin d'ukeni brother d'inki ne, dama nike kid'ana da rawa, da tun farko kin gaya min kina da aure da alak'anmu batayi nisa ba, ko kuma dana nasan yanda zan fuskance ki, amma ba damuwa naji dad'i da kika gayamin gaskiya, zan koyawa kaina hak'uri da soyayanki, sai mu cigaba da zumunci" Murmushi tayi tace "nagode da tunatarwa, insha Allah zan gyara muje ko" "yanzu ina muka nifa?" murmushi tayi tace "muje wurin wasa da mota ko?" dariya yayi yace "OK my Friend" dariya tayi tace "abotan harya fara aiki kenan" murmushi kawai yayi ya tada mota suka cigaba da tafiya. Sai k'arfe bakwai na dare Basma ta dawo daga wurin kallonta wasan mota, Bilal ya sauketa a k'ofar gida, hakan yayi dai-dai da cillowar motan Yaya Shureym, ita kuma tana d'aga ma Bilal hannu harya wuce, sannan ta shiga gida. Ta samu Safeena zaune sai d'irkan abinci take, tsaki Basma taja tace "Mutum baida aikin yi sai ya zauna yaita d'irkan abinci kamar jaka, wai dole ita mai ciki" Murmushi Safeena tayi bata ce komai ba domin ta riga ta had'a mata bomb mai kwacenta yau a gun shureym sai Allah. Safeena ta gayawa Shureym daya dawo, k'arya da gaskiya akan fitan da Basma take yawan yi da kuma mummunar shiga, ransa yayi matuk'ar b'aci, fita yayi nimanta wuraren shak'atawa ko zai ganta a can, amma haka ya karad'e yawan nimanta bai ganta ba, dawowansa kenan yanzu daya hangota tana d'agawa wani hannu, ransa ya k'ara b'aci sosai kishi ya rufe masa ido, da sauri ya shiga gidan yayi parking. Falo ya shiga da sauri ya soma kwalawa Basma kira, da sauri ta fito tana fad'in "dan Allah karka fasa min kunne, sai wani kwala min kira kake, sai kace tsohon makawo" a zuciye ya bud'e baki zaiyi magana, sai ga Bilal ya kwad'a sallama ya shigo falon, Basma saida gabanta ya tad'i, amma saita dake tace cikin Fara'a "Friend hala nayi mantuwa ko?" murmushi yayi yace "kin manta da ice cream d'inki kina sauri" "ayya wlh ban kula ba, nagode kuwa sosai" Shureym ai sakin bakin yayi yana kallon ikwan Allah, cikin harshen turanci Bilal yace masa "ina yini big brother" Shureym ya amsa a tak'aice, sai ya fice da sauri. Yaya Shureym zama yayi akan kushim yana cizon leb'ensa, gaba d'aya kishi ya rufe masa ido. Har wani d'aci bakinsa yake masa saboda b'acin rai, Basma tana ganin ya zauna bai ce mata komai ba, sai kawai ta shige d'aki. Shureym ya d'aga wayarsa ya kira Dadyn Kaduna, Gobna Ibrahim, suka gaisa Dady yace "Shureym ya Basma da fatan kuna lafiya?" cikin k'unan rai yace "Dady Basma tana cin Amanta, fita take yi tana hurd'a da wasu maza a waje, yau tun rana ta fita sai yanzu ta dawo, kuma Dady wani saurayinta ne ya kawota gida, yanzu yabar falon mu" a razane Dady ya mik'e yana fad'in "Inalillahi wa inna ilai hir raji'un, Basman ce ta zama haka, to maza ku shirya gobe-goben nan ku tawo Nigeria, zan kira family meeting gaba d'aya zamu had'u a Abuja duka, kayi hak'uri kaji Shureym karka ce mata komai" sai suka yi sallama. Dady ya fara kai koma a falo sai salati yake, Ummin Meena dake zaune itama ta mik'e a tsorace tana tambayarsa "Alhaji lafiya?" kallonta yayi bai ce komai ba, ya shiga niman number Mai Martarba Sarkin Kano, suka gaisa, sai ya shaida masa akwai family meeting a Abuja gobe in Allah ya kaimu, nan suka yi sallama. ya d'aga waya ya kira President, shima haka ya shaida masa kamar yanda suka yi da Mai Martaba, President cikin mamaki yace "Ibrahim lafiya dai ko?" cikin murmushi yak'e yace "Lafiya Kalau sai in munzo zaka ji komai insha Allah" da haka suka yi sallama. Dady ya koma ya zauna, itama Ummi ta zauna, ya shiga gaya mata Abinda Shureym yace masa, cikin salati Ummi tace "wlh k'arya yake yi, ba dai Basman mu ba, sai dai in sharri zai mata, dan ba haka muka tarbiyyantar da ita ba" Cikin b'acin rai Dady yace "karki shaideta domin d'an yau ba a iya masa, kuma ai ba tare dasu muke zama ba, hasali ma ba gari d'aya muke ba, Basma zata iya komai tunda dama bason Shureym take ba" sai jikin Ummi yayi sanyi ta shiga nazarin maganar Dady... *Rahma Ce* (Sirrin 'ya mace group) WhatsApp. [9/30, 7:55 PM] Aysha Galadima: *'YAR SHUGABA*👑 _page_ *20.* _Na_ _*Rahma Kabir*_✍🏾 Safeena cike da damuwa tace "amma Shureym anya baka jawo tonuwar asirinmu ba, domin in dai Basma taji cewa ka kai karanta ne, tofa zata gaya duk abinda ya faruwa, da kuma dukanta da kake yi" Runtse idonsa yayi ya bud'e, cike da damuwa yace "wlh Safeena raina ne ya b'aci, idona ya rufe sam ban kawo haka ba, sai yanzu da kika tunatar da ni, yanzu ya kike ganin za'ayi" cikin damuwa ta rafka tagumi tace "ina ganin karka gaya mata, kace kawai ana nimanku ne, inya so inta je can taji komai, kuma na fison dama kowa yasan dani a family d'inku dan nagaji da b'oye-b'oye" cike da damuwa Shureym yace "haba safeena bai kamata ace abinnan ya fasu yanzu ba, kawai ki tayani da Addu'a kar asirinmu ya tonu" yana gama fad'an haka sai ya mik'e ya shige d'aki, Safeena ta bi bayansa da kallo, ta yatsine baki tace "ba Addu'an da zanyi, in maganar ta fito karshe dai ace an raba aurenka da Basma, kuma abinda nake so kenan". Shureym yana shiga d'aki ya kira Maminsa ya sanar mata duk abinda ke faruwa, hankalinta ya tsahi ta shiga yi masa fad'a, tace "yanzu kazo kaja asirina zai tonu, a gaskiya ba yanzu naso ace maganar nan ya fito ba, domin hakan zai iyi barazana ga aure na, kuma kaima za ka fuskanci fushin Mahaifinka, gaskiya zan San abinyi" tana gama fad'a ta kashe wayar. Kai komo ta shiga yi a d'akinta tana tunanin hanyar da zata bullowa lamarin, zama tayi tayi dogon nazari, murmushi naga tayi sai ta ce "Allah ya kaimu goben, na samo mafita". Da dare Shureym ya kira Basma a waya, yasan in yaje d'akinta ba zata bud'e ba, yace "ki shirya gobe in Allah ya kaimu zamu tafi Nigeria, Dady ya kirani yace muje akwai Family miteeng, dan haka ki shirya da wuri da sassafe mamu tafi" cike da murna tace "Allah ya kaimu" saita kashe wayar. Mikewa tayi, tayi rawa da tsalle, tana murnan zata ga family d'inta, kaya ta shiga had'awa kamar wacce zata bar garin duka ba dawowa. Zan iyace cewa barci b'arawo shine ya saceta, amma sam ta kasa sukuni, kosawa tayi gari ya waye. *Washe gari* Yau Basma harda yiwa Safeena sallama sai fara'a take mata, Safeena tace "hoo su Basma za'a tafi min da miji sai dariya kike, to Allah yasa in kin tafi karki dawo" harara Yaya Shureym ya galla mata, saita gimtse sauran maganarta tana dariya k'asa-k'asa, Basma kuwa cike da dariya tace "Ameen ya rabb, nima bana fata na dawo, kuma mijinki gaki ga shi, babu abinda zan miki dashi, ni dai na barki lafiya" saita fice tare da jan trolley kayanta. Safeena ta bisu har mota tare da musu Addu'a, haka suka wuce airport, Shureym yana cike da damuwa, Basma kuma cike take da murmushi. *Nigeria* Gidan President ya cika da dangi, sunzo sunata zumunci, da yake ya kama yau rana ce ta Juma'a, mazan gidan duka suka taru suka tafi babban masallacin Juma'a na Abuja. Bayan sun dawo gida, iyayen maza da mata suka had'u a babban falon bak'i na shugaban k'asa, anan aka shirya musu abinci a tsakiyar falon kan babban dadduma daya mamaye falon, yara kuma suka baje nasu liyafar a part d'in Ammi, can suke hidimarsu. Bayan sun gama cin abinci suka shiga hiran zumunci, Abba (President) ya kalli Dady (Gobno Ibrahim) yace "Ibrahim yanzu gamu duk mun had'u gaba d'ayanmu, ina so ka sanar mana musabbabin had'uwarmu anan daka buk'aci muyi" Dady ya nisa ya d'ago ya kalli Abba yace "naso ace Shureym da Basma sun zo tukunna sai kuji bayani a bakinsu, dan dama mun had'u anan ne domin su, na tabbatar suna gab da shigowa" Mai martaba yace "A'a Ibrahim ka fara sanar mana da komai kafin zuwansu" Mami (Hajiya sa'a) tace "kwarai kuwa, ya kamata mu ji komai, domin ni hankali na ya ya shi" Hajiya Fatima (Ammi) tace "gwara ka fad'a kawai domin mu fara tattaunawa akai" ita dai Momyn Basma bata iya furta komai ba saboda nuna kawaici, Hajiya Murja Mahaifiyar Leema ita ma bata furta komai ba, Ummin Meena kuwa shuru tayi cike da damuwa a fuskanta. Dady yayi gyaran murya ya gaya musu duk abinda Shureym ya fad'a masa jiya, ai duka falon sai suka d'auki salati, Momy kuwa wani irin fad'uwa gabanta yayi, idonta ne ya kawo kwalla zuciyarta na mata suya, Abba sun kuyar da kai yayi ya kasa yin magana, duk falon ya d'auki shuru sai k'aran fanka da kukan AC ke tashi, Mami ce tace "hmmm nasan za'a rina saboda Shureym ya sanar min cewa tsawan watannin bikinsu da suka yi, Basma tak'i bashi had'in kai suyi rayuwar aure, akwai ranar da har fad'a suka yi nice na sasanta lamarin, har nayi masa fad'a, akan cewa yarinya ce ya bita a hankali, Shureym tunda yaji su Meena duk suna d'auke da ciki abin ya dameshi, nice nake lallashinsa" Mai Martaba ya katseta da cewa "meyasa kinsan da wannan matsalan yanzu tsawon wata 7 da aurensu, sai yanzu za ki fad'a da kika ji matsala ta kunno kai?" "Mai martaba gani nayi Basma ba son aure tayi ba tun farko, shiyasa nace bari mu lalkab'ata harta hak'ura ta yarda da shi". Ba wanda ya tanka mata sai duk suka yi shuru. Sallaman shigiwar su Basma falon, shine ya k'atse shurun domin kusan yaran nasu duka shun shigo falon suna murnan ganinsu Basma, Yaya Ahmad na rik'e da hannun Basma sai suka samu guri suka zauna a gefe, duk yaran suka zauna, Yaya Naufal, Yaya Shureym, Yaya Adam, Yaya Jamal, Anty Husnah, Meena, Leema, Deeja, twins din Momy k'annan Basma. Falo yayi Albarka, kowa ya zauna duk suka gaishe da iyayensu, sai dai fuskokinsu babu walwala, Basma ta tashi ta isa gaban Abba ta zauna tare da sanya kanta akan cinyansa, cike da b'acin rai ya tureta tare da cewa "tashi ki bani wuri" da sauri ta d'ago ta kalleshi, cikin shagwab'a tace "Abba me nayi kake fushi dani" shuru yayi mata, sai duk jikinta yayi sanyi, takai kallonta ga Momy, saita kauda kai a ranta tana tausayawa d'iyarta, duk tabi fuskokin iyayan nasu babu wanda yayi mata dariya ko murmushi, duk ransu na b'ace, cikin tashin hankali tace "Wai me yake faruwa ne?" Dady ne yace "Ku su Meena Ku tashi Ku fita Ku bamu wuri, Anwar da Na'im kuma kuje d'akinku kiyi karatu, ku kuma mazan ku zauna ayi maganar daku" jikinsu duk a sanyaye su Leema suka fita, Basma ta mik'e zata bi bayanzu Dady ya daka mata tsawa yace "zauna karki sake ki fita, dama zaman danke a kayi shi" kuka ta fara yi ta koma kusa da Yaya Ahmad ta zauna, hannunta ya kama ya shiga lallashinta. Falon yayi shuru na tsawon minti biyar, Dady ya kalli Shureym yace "Shureym ina so ka sanar mana da abinda ka gayamin jiya a waya" "Shureym cike da fargaba da damuwa ya shiga zayyana magana k'arya da gaskiya, bayan ya gama gaya musu abinda ya gayawa Dady sai ya d'ora da cewa "Basma bata jin maganata, ban isa in sata ba ko in hanata ba, zagi iri-iri na cin mutunci babu wanda bata yi min, zata fita da banzan shiga na fidda tsiraici, ban isa inyi magana ba" ai bai k'arasa ba Basma tayi magana cikin d'aga murya da tashin hankali tace "karya kake Yaya Shureym, wlh sharri kake min" takalli iyayenta ta cigaba da cewa "wlh Aba sharri yake min, Ammi yanzu ku kun yarda da bayaninsa, Mai martaba wlh Yaya Shureym sharri yake min, karku yarda da maganar shi" ta rarrafa ta isa gaban Mominta tace "Momy in kowa bai yarda dani ba nasan ke zaki yarda dani" Momy sun kuyar da kai tayi k'asa hawaye mai zafi ya sauka a kuncinta, Abba ne ya mik'e da sauri ya wanke Basma da mari guda biyu, tare da hamb'arinta da k'afansa yace "tir da halinki Basma, acikin zuri'ata kin fita zakka sam baki halinmu ba, kuma in kika kuma yin magana anan wlh jikinki zai gaya miki, mituniyar banza kawai" Dady ne ya mik'e ya kama Abba yace "haba Yallab'ai, bai kamata ka duketa ba" komawa duk suka yi suka zauna. Momy cikin fushi tace "Tunda nake ban tab'a sanya baki a cikin lamarin Basma ba saboda ina nuna kawaici, amma yau zanyi magana, a irin tarbiyyan dana bawa 'yata bana tunanin zata aikata abinda Shureym ya gaya, in kuma ku kun yarda toni wlh Ni bazan tab'a yarda da magan ganunsa ba, dan haka Basma 'yata ce, nice nayi nak'udarta babu wanda zai d'aura mata k'azafin zina in d'auka" Saita mik'e taje ta kama hannun Basma suka yi hanyar fita daga Falon, yaya Ahmad shima mik'ewa yayi cikin b'acin rai ya kalli Shureym yace "D'an iska banza baka isa ka yiwa 'yar Uwata sharri ba, domin nafi kowa sanin mugun halinka, dama mazinaci kamar ka ai dole kaga kowa ma haka yake, Basma nasan abinda zata aika nasan wanda ba zata yi ba, mak'arya cin banza dana hofi" shima sai ya bi bayan su Momy. suna gabda zasu fita Abba ya bud'e murya yace "Maryam wlh muddun kika sanya k'afa kika fita a falon nan to a bakin aurenki, Kai kuma Ahmad wlh in ka fita saina sassab'a maka mutumin b'anza kawai, har zaka zo ka goyi bayan shaid'ayar yarinya nan, tun farko dama ta nuna bata Son shi, dan haka kome aka ce tayi to zata iya aika shi" A gigice Momy ta tsaya ta juyo tana mamakin furucin Abba, mai martaba yace "Subhanallah Yallab'ai wani irin furuci ne haka?" Ammi da Ummi da sauri suka mik'e suka isa wurinta, Momy tana kukan bak'in ciki amma sam bata karaya ba dan tana bayan Basma, gabanta su Ammi suka sha, tare da rik'o mata hannu suka jata har zuwa mazauninta, Yaya Ahmad ya kama Basma ya had'ata da jikinsa yana lallashinta, haka suka isa cikin falon suka zauna. Mai Martaba yayi gyaran murya yace "Dan Allah kuyi hak'uri kar b'acin rai yasa a yanke hukunci cikin fushi, ba tare da bincike ba, ke Basma gaya mana gaskiyar abinda ke faruwa" kuka ne yaci k'arfin Basma tace "Wlh ban tab'a zina ba ban tab'a ba, kune iyayena ku zaku shaideni akan haka, wlh ban tab'a ai'kata abinda yace muku ba ko d'aya daga ciki" kuka ne yaci k'arfinta saita d'aura kanta a cinyar Yaya Ahmad, jikinta ne ya soma kad'uwar jin sanyi nan take zazzab'i ya rufeta... *Rahma Ce* (Sirrin 'ya mace group) WhatsApp.