﻿Compiled by Umar Dalha Funtua.

💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
       💖💖💖
 💗💗💗💗💗



  Bismillahirahmanurrahim


Aysha A bagudo



Page 1-2


Lekki  Unguwace  mai dauke da karancin mutane da suke rayuwa acikinta   ,a silent place, saboda bata cika   hayaniya mutane ba  , dauke da tarin sanyin ni'ima mai dadi  sakamakon kusancinsu da ruwan teku" unguwace da tattara kan manya ma'aikata da kusoshin gwanati, hade da manyan masu kudi ,ga tarin  yan yahoo boy'z  domin mafi yawancisu   sunfi sha'awar  zama acikinta. rayuwar mutane  unguwar abin sha'awa  bbu ruwan wani da wani  domin suna rayuwasu ne tamkar a kasar waje   .


PLASNUW ROWS FAMILY ESTATE 

Estate ne mai dauke da tarin dangi acikinta , hadin kai tattare da zaman lfy,  Sam bbu hayaniya acikin wannan family kowa kagani cikin nishadi da farinciki zaka gansa ,ga tsantsar fahimtar juna dake tsakanin wannan family. kwakkywan family ne masu matukar kaunar junansu .


Let alh Muhammed bello khaliyal ,haifafen garin Lagos ne ,Amman asalinsa fulanin khaliyal ne dake jahar kebbi. sananne  mai kudi ne yayi tashe tun alokacin da duniya ke kwance. sannan kuma take zaman lfy, marigayi Muhammed bello  soldier ne daya taka rawar Gani a kasar nan .
 ya rike mukamai da dama a wancan lokacin. ya rasu yabar tarin dukiya da da ya'ya da jikoki  bila adade.
    gabadaya family Muhammed bello bbu talaka aciki  domin sun gaji dukiya mai tarin yawa daga mahaifinsu  .

 kafin rasuwarsa    dake shine babba a dakinsu kuma Allah yabashi tarin dukiya da en'uwan , dan ganin ya inganta rayuwar kannensa kafin daga baya ya Gina wannan katanfarin estate din  mai mazan kanta.
 ya tattara  kan yan'uwasa suna zaune a ciki ,yana da mata hudu  hjy  shema'u  wacce aka musu aure tun saurayi da budurwa tana da ya'ya  goma   Sha biyu, mata takwas maza hudu  sai hjy  hauwa mai dauke da ya'ya goma maza biyar mata biyar ,sai hajiya rabi mai ya'ya takwas maza biyar mata uku   sai hajiya Fatima wacce suke kira da hjy  shuwa  itama tana   da yaya takwas mata bakwai namiji daya .
 bbu abinda bbu acikin wannan estate din kama daga makarantar islamiyya wajen wasa buga kwallo wajajen exercise wajen swimming pool library Sannan ga wani katanfarin Holl dake gefe wanda aka shiryashi da kayan kyale kyale zagaye da kujerun zama . an ginashine  saboda  taron sada zumunci , wanda zasu dinga yi a duk karshen wata  .

 haka suka taso har zuwa girmansu cike da son junansu .
 anan cikin  dangi mazan suka zabi matan suma  matan suka zaba akayi  bikinsu anan cikin estate din suka zauna  tare da iyalinsu  har zuwa  sanda tsufa yacima marigayi Muhammed bello yayi retire.
 yayinda ya'yansa da ya'yan en uwa suka cigaba da kula da estate din .
  a lokacin  aliyu  da  habib ne kadai suka rage da basuyi aure ba saboda  karatu . 

Byn rasuwar marigayi bello ne aka raba gado aliyu  ya dukufa  gurin juya dukiyarsa ,ba abinda  yasaka a gaba sai neman kudi wanda acikin kankani lokaci ya gawurta yayi fice yayi suna a duniya,  yayiwa sauran yan'uwansa zarra  aliyu ya mallaki tarin dukiya da shi kansa bai san iyakarta ba. hade da tarin compenis  a Lagos da kudancin Nigeria yana da gidajen saida man petir Bila adadi shine mallakin aliyu airlines yana da hannu jari da dama a compenis na kasashen duniya yana da  gidaje a abuja da sauran garuruwa .
tsananin neman kudinsa ne yasa  bai ajiye iyali da wuri ba ,burinsa bai wuce  ya auri mace mai matukar kyau da tarin illimi ba .

Garin neman kudinsa ne ya hadu da fadila  a india tun daga lokacin da aliyu ya daura  idanunshi akanta "ya dauki son duniya ya daura mata kasancewarta kyakkywa gaske ga tarin illimi . fadila itace Diya ta biyu a gurin iyayenta su uku ne , ahmed  ne babba sai ita sai farida ,  kin amincewa iyayenta sukayi da auren shi a cewarsu bako ne sannan kuma bakin fata. sai da aka kai ruwa rana dasu sannan suka amince  da auren .
 koda yazo daita Nigeria ma bata wani sha wuyan zama cikin family dinsa ba .
kasancewarta mace mai tsananin  son jama'a da son yara cikin lokaci kadan tashaku da sulaiman da  mahamud ya'ya ne ga yayyen aliyu sun shaku matuka da yaran ta daukesu tamkar ya'yan data haifa  acikinta .
suma  kuma suna maseefar kaunarta dan haka suke   kiranta da ummi ,duk abinda suke so itace take musu bata ragesu da komai ba saboda bata da rowa  hakan ne yasa ta sake janyo mata soyayya ta daban a gurin iyayensu.

 shekarata biyar da aure mutuwar mahaifiyar ta risketa ,zuwan datayi indiya ne dazata dawo tazo da kanwarta fadila  ta hada dasu Mahmoud tacigaba da rikonsu .
 sai da fadila ta dauki sama da  shekara takwas  da aure  sannan tasamu cikin murna a wajen wannan family bai faduwa .
    cikinta na da wata tara cif ta haifi NASURUDEEN  daga ita har aliyu suna matukar son DEENI tamkar numfashinsu DEENI yataso cikin gata da kulawar iyayensa, da dangi gabadaya suna nuna masa tsansar  gata da soyayya fiyye da tunanin mai karatu .
shiyasa yataso a shagwabe a sangartacce saboda kaf estate din  kowa yasan da zaman DEENI babbar matsalar da suka fara fuskanta da deeni  , shine rashin magana da bai yi ,da farko fadila  ta dauka ko kurma ne sai daga baya tagane tsabar miskilanci ne kawai yayi masa yawa .
duk tarin ya'yan dake cikin wannan estate din DEENI yafita dabam acikinsu,   bashida aboki  ,.
 gabadaya baya yarda da kowa  koda yaushe  yana tare da umminsa ko farida ko su  Mahmoud tun tasowarsa yake da burin son zama soldier yayinda ummi take bashi goyon baya wajen kiransa soja .
Domin  wani lokacin zai je yatasa hotonta marigayi kakansa dake manne a falonsu gaba yayi ta kallo yana shafa fuskar tsohon yana murmushin ,Sam shi  bashi da fara'a ballanantana sakin fuska   koda yaushe fuska nan tashi a hade take tamkar hadari , .DEENI Nada shekara takwas byn yakare primary school aka sai mishi form din  shiga makarantar sojoji ba'awani samu wata matsala ba yasamu  sakamakon matsayin mahaifinsa da kakansa. sabanin wayanda  basu da gata.
 domin a wanan lokacin idan dai kai bawani  bane  ko dan wani  ba  ko bakada  hanya a military school  ,sunanka sorry.
Domin kuwa  kana ji kana Gani  military school zai gareka shiga  .

    byn wani lokacin farida ta samu miji anan cikin estate din  wanda shima    yakasance "Da"ne ga marigayi  Muhammad bello wato  habibu ubansu daya da aliyu mahaifin ga DEENI   .
duk da fadila ta nuna rashin amincewarta matuka , da nuna wa er'uwartata illar aurenta da Habib   Amman sai taga yarinya ta nuna tana so abunta  ,dan haka ta kyaleta kuma da kunya dai ta fito fili tace batason jinin aliyu ,wanda itama kanta tasan hakan ba mai yiwu bane . itama ba wai shi din ne bataso ba ,halinsa ta tsana , 
Amman shi babban  ma'aikace  gwanati ne,   director of land  and housing & same   na Lagos state gabadaya. yana da mata biyu da yaya bakwai farida ce ta uku . 
Ko alokaci daya auri   farida   takasance mace ce mai tsananin hakuri .
duk da mijin nata Vai kasance mutun  mai adalci ga iyalansa ba. Amman bata taba kawo kararshi ga ummi ba domin tasan halin ummi Sam bata son raini .

Shekarar da aka yiwa sulaiman da mahamud aure shekarace Allah yayiwa mijin ummi rasuwa wato alh aliyu Muhammad bello sunji matuwar farar daya  , mutuwar tayi matukar gigita ummi dan byn ya dawo  daga sallah asuba ne yayi irin kishingide nan yana lazimi  koda ummi taji shiru shiru bai sake fitowa ba Sannan bai nemeta ba  kmr yadda ya saba , wanda aldarsa ce  da zarar gari yayi sha ...yake fitowa ko yakirata a waya    Amman taji shr .
 tashiga dakin nasa  ta tarar dashi kishingide da carbi a hannunsa .
 da fari ta dauka ko bacci yakeyi sai tayi nufin ta tasheshi yakoma kan gado.
  Ammai sai taga alamun rashin motse atare dashi takai hannuta wajen hancinsa da karjinsa a lokacin daya taji baya numfashi.
   take ta zube anan ta sume.
 har a kashare zaman makoki ummi  batasan a wani hali take ba ,dan   bata  cikin haiyacinta' koda ta farfado ma sai da akayi ta hadawa da addu'a Sannan aka samu kanta ta dawo daidai , dan mutuwar ta girgiza har ta kusan zarar daita  .

Byn wani lokacin  su sulaiman suka cigaba da tallafawa ummi da DEENI a lokacin farida na dauke da tsohon ciki  duk da itama ta dan jima bata haihuwa ba, kuma har lokacin ummi bata san er'uwarta tana cikin matsala ba ,sai byn data haihu" lokacin ne ummi taga komai bbu alhalin ga tarin dukiya kmr zai kashe habibu , gashi yasake kara wani sabon  auren matansa sun cike hudu cif .
ummi tayi kuka kmr may  gashi tana cikin danginsu da suke tamkar tsiya madauri daya.
 ba daman tace zata dauki wani mataki akan  haka  .
dan tasan yadda kansu yake a hade .
    dan haka taci kukanta  takoshi ita da er uwarta ahankali take furta kalmar shiyasa tun farko naki amincewa da auren nan naki da habibu ,ba dan komai ba sai dan irin haka  Amman kika nace ,ga  irin abinda nake gudar miki kennan Amman kika kiji , sai kuma ta tsagaita da kukanta ahankali  tace  ba yadda zamuyi da ikon Allah ,sannan ga rabo a tsakani.
 Amman duk da haka sai da ummi tayi masa tatas saboda daman ita bawani sakar masa fuska take ba kuma  yana shakkata.
 kullum ummi acan take wuni har ranar suna    yarinya tace sunan mahaifiyarsu ummi wato muzeenat ,  shima habibu yayi hakan ne saboda ya wanke kansa a wajen ummi,kuma yayi nasara domin  hakan da yayi  yasa ummi taji dadi Sosai aranta har ta dan rage jin zafinsa .
 sannan bakaramin kudi ummi takashewa bby ba. haka ma   ranar suna ummi Tayi rawar Gani sosai .
byn anyi suna ne ummi  tasamu habibu akan dan Allah  ya dinga kula da farida dan ita kadai gareta bata da kowa duk fadin Nigeria sai ita,  idan ma bazai damu ba,  zata bashi Rabin dukiyarta yakara akan nashi  da duk wani  abinda yake so, ita dai burinta kawai ya kular mata da er,uwa ,yayi murmushi kawai hade da ce mata yaji  .

Byn wani lokacin farida ta kuma samun wani ciki wanda tun yana karami take fama da laulayi tun lokacin ummi tadawo da zeenat wajenta ,
a kwana a tashi bbu wuya a gurin Allah har cikin farida ya isa haihuwa gurin haihuwar ne taji jiki sosai .
koda     ta haifi yaron ma  bbu rai sannan itama tace ga garinku .
mutuwar ta shigi habibu matuka yayi kuka tamkar ransa zai fita ,dan shi kansa yasan yayi babbar rashin  da ba zai taba maida irinsa ba.
  yayi rashin mata  mai tsananin kirki da hakuri da sanin darajar miji . Allah sarki ummi   kusan har  tafi habibu jin mutuwar tilon er'uwarta ta ,.
a  wannan Lokacin ne  rikon zeenat ya dawo dindindin  gurin ummi ta dauki soyayyar duniya ta daurawa zeenat tana mugun ji da Yarinyar   tamkar ranta kwata kwata bata son abinda zai rabata da zeenat Sannan kuma   tana debe mata kewar er'uwarta .
lokacin shi  DEENI   na ss1  a NMS, Nigeria military school dake zariya.
   yayinda DEENI Sam ba halinsu daya da ummi ba koda yaushe kagansa fuskar nan tasa  a daure a cunkushi  bbu wani fara'a ga shegen miskilanci tsiya  sai dai mugun kyakkyawa ne na karshe . ajin farko, wato first class ,gashi  da  maseefar  iya sa kaya kallo daya zaka masa ya gigitaka kaji yashiga   ranka farar daya saboda tsabar kyawunsa sai shegen shiga ran mutane domin kusan yan'mata cikin  estate din suna maseefar son sa yayinda yake  girma kyawunsa na sake bayyana hade da miskilancinsa     .

Tunda zeenat ta dawo gidan magana bata taba hadasu ba ko gaisheshi Tayi baya amsawa in dai bayaga idanun ummi ba yana da matsanancin tsafta wanda kusan a wajen ummi yagada .
Cikin haka ya kammala karatunsa na secondary school ya wuce NDA burinsa kennan nason zama cikakken soja itama  ummi kuwa  nasake karfafamasa gwiwa da bashi goyon baya   yana karantar science ne ,wato likitan soja .
bansan yadda zan kwatanta muka  halinsa ba Amman yakasance mutun ne shi mai bambanci ra,ayi.
 byn yakare karatunsa ya fito da mukami second lieutenant star biyu  kennan   .

Zaune zeenat take a falo tana kallon wani serisfilm  a zeeword my let home Tayi zurfi cikin kallon film din gabadaya attention dinta naga kallon ita kadai ce ummi tashiga cikin estate din yin barka taji karar Bell wanda shine kusan karo na hudu da taji ana dannawa. cikin jin haushi ta mike dan bata son abinda zai dagata daga kallon datakeyi , tana bude door din bata tsaya ganin kowaye ba ta juya abinta takoma mazauninta  sallama taji  hade da shigowa ta dago kanta  kennan   da niyar amsa sallama sai taga mutun tsaye kikam  sanye da sabon  kayansu na  sojoji gabadaya zeenat ta gigice hade da rikicewa tsabar tsoro dan ita Allah yayita  da maseefar jin  tsoron soja   take cikinta ya dauki kugi Amman still  idanunta  na kansa ta tsaresa da  kallo .
  in ina tasoma yi wa..wa.. waalai....ya dakatar daita da hannushi, yana zabga mata wata uwar  harara muryasa a kwasashe yace yau ne kika fara ganina  da har zaki wani  tsareni da idanu Kona canza miki ne ?da sauri tasoma girgiza masa kai. Kai tsaye dakin ummi ya nufa tunda bai ganta a parlour ba yasan tana dakinta  tana kallonsa ta kasa dauke idanunta daga garesa har sanda ya dawo fuskar nan tasa a hade yace ke.....dan iskanci kina kallon mutune bazaki iya cewa  ummi bata nan ba   kin wani tsare mutun da idanuwa tamkar na maciji ,dayake bawani manyan idanu gareta , da sauri bakinta na rawa tace dan Allah kayi hakuri mantawa nayi  ko kallonta bai sake yi  ba yaja tsarki yayi hanyar dakinsa  ta tabe baki hade dacewa   jarababbe kawai ai  yadawo kennan, itama taja tsaki ta juya tacigaba da kallonta ..


MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



Aysha A bagudo



Page 3-4

 Sai da tagama kallonta tsab Sannan ta canza Chennal hade da   tashige kitchen dan daura abinci  abincin dare 
 bakin kofar kitchen din ta dawo  Tayi tsaye abunta  tana cigaba da kallonta Chennal data canza,  ajima ajima    tana zuwa tana  duba abinda ta daura.
 Karar bell taji ba kaukautawa shiyasa  da sauri   taje ta bude gudun maseefar DEENi  dan tasan muddin yana    gida baya son yawan hayaniya , yanzu ne zai gama daita,   Maryam   tagani tsaye  da wasu en school dinsu su biyu    tuni murna yakama  zeenat ,ta rungume su  daya bayan daya tana musu sannu da zuwa  hade da basu hanya "suka shigo har cikin main parlour din  hade da  Sallamar su  .
waje ta nuna musu da hunnu kuzauna mana  suka zauna  ita kuma takoma kitchen ta duba abinda ta daura taga yayi ta kashe gas din sannan ta  dawo inda tabarsu hade da kawo musu drunks mai tsanyi da snacks ta ajiye agabasun  .
 gabadaya hayaniyya ce ta barke a  atsakaninsu da murna ganin juna ,zeenat ta kalli su Sumy hade dayin  kasa kasa da muryata tace  kuyi magana ahankali fa   sannan tace  kun kyauta sai yau kuka ga damar zuwar mana , Sumy tace ba gara mu ba muna zuwa time to time.
 kufa sai aikin sa rana   kullum,  hira suka shiga .
a inda   Maryam ta dube zeenat  tace wai nan fa IV suka kawo mana na birth din rukky, zeenat ta zaro idanu waje I ....me Maryam tace  IV .
zeenat Tayi dariya hade da cewa uhmm badani ba" kema kinsa sarai baza'a taba  barinmu zuwa wani birthday party ba " Sumy Tayi murmushi sannan tace ai sai da nagaya rukky Amman tace ga zance ga magana " gashi nan, ni ai nasan bazakuyi attending birthday party dinta ba ,da day itace sarkin shishigi da neman suna , zeenat tace kmr kinsani  ,duk abinda ya wuce cikin gidan nan namu "ta girgiza kanta baza'a taba  barinmu ba ,ki bata hakuri  kawai  Amman wlh har ga Allah naso zuwa ko dan rukky   Sumy tace to why nut ku sace hanya kuje a boye batare da kowa yasani ba ... zeenat ta  kalli Sumy fuskarta a hade tace kefa kin cika matsala fa wlh.
 kmr bada hausa nake miki  magana ba.
 ta bude bakinta kennan da niyar sake balbale summy.
 sai ga DEENi ya sake fitowa   parlour  jikinsa  sanye da jallabiya marun colour may maseefar kyau sai kyalli take zuwa ga kamshin turarensa mai mugun sanyi dadi wanda tun tasowar zeenat ta sanshi da auren Hamilton  har yanzu fuskarsa  a daure take tam ..  kmr koda yaushe "  take ta hadiye maganarta batare da tasan Tayi hakan  ba  ,ta zuba masa idanu tana  kallon kwayar idanunshi, sai data ya  hararata, sannan   ta dauke idanunta ,ta maida kallonta da hankalinta kacukam a kansu Sumy dake zaune surusuru. Yayinda    gabadaya Maryam duk ta fisu tsurewa ko dan ita Yar gidan ce oho.. 
  cikin wata irin murya mai  sanyi dadi  tamkar  ba soja ba yace ke......ta juyo ta ahankali ta sake  zuba masa  idanunta dan tasan dai daita yake dan haka tabada duk  attention dinta  garesa.
     bakisan kibawa mutun abinci bane ? Dan iskanci sai an roka ,zatayi magana ya katseta a fusace , ai ba  tun yanzu nasan ke muguwar  rowa ce dake ba Tayi surusuru  da idanu ,da   sauri tace  kayi hakuri dan Allah nayi zaton ko kana azumi ne "naga kullum kana  yi "
yace "oh "dama kinsa min ido ne har kinsa cewa azumi nake kullum ?
Jikin Maryam har rawa yake ,a hankali tace wayoo Allah ashe ya dawo ,bari in gudu tun bai gama daita ya da kanmu ba , zeenat tayi shr har sanda   ya sake maimaita tambayarsa hade da cewa dan ubanki bada ke nake ba kike bina da idanu kmr zaki cinyeni" ta sake     girgiza masa  kai,. Tana bashi hakuri
  marowaciyace banza kawai mai mugun gado.  shiru  yayi na dan wani  lokaci hade da sauke numfashi .
Sannan can kuma yace ai idan bakiyi rowa ba sai Allah ya tambayeki" km baza'asan ke...Yar uncle Habib bace .
kin taba ganin barewa Tayi gudu danta yakasa rarrafe" zeenat ta sake  girgiza kai da sauri ,yace  OK ashe dai kema kinsa gaskiya dole kiyi gadon rowa.
Ganin haka yasa su sumy suka nemi sulalewa duk yana kallonsu sai daya ga Maryam na shirin gudu  itama dan  har summy ta  daura hannuta kan handle din kofar ,ya dakatar dasu da hannusa , sannan yacigaba duban zeenat yace  barikiji da kyau  yana mai  nuna da  yatsansa" nan ba gidan marowata bane gidan masu bayarwa ne aci . yace menace ? Da sauri tace  gidan masu bayarwa ne.
 yace gud daga yau  bama ni ba ,ko wani ki kaga yazo gidan nan  ki  bashi ruwa da abinci yaci dan ba naki bane.
 ya sake jiho mata wata  tambayar yace ko abincin naki ne?, da sauri ta girgiza masa kai    dan gabadaya ta sure  ta kasa kwakwaran motsi sai ajiye zuciya kawai take yi , yace" baki da baki ne kike kadawa mutane kai , tace naji kayi hakuri dan Allah. Sannan  ya juya kan  Maryam da kadan ya rage ta fashe da kuka , ya zuba musu ritattun idanunsa da suka fi kama da mage masu saurin raunana mutun kai tsaye , yace   ku kuma en iskanci banza kun wani cikawa mutane kunne   da hayaniya tamkar kuna club  ,kallo daya yayi musu kowace tabawa kafarta iska  yaja tsaki  ya juya   ya nufi dakinsa.

 ahankali zeenat take  sauke ajiyar zuciya hade da dafe kirjinta , batasan meyasa ba ,idan har Yaya DEENI  yana guri Sam  bata samun cikakkiyar natsuwa  "sai tarinka ganin duk yacika guri ga tsananin tsoransa da take ji yana mamaye zuciyarta  . Maryam har da kuka tayi byn sun fita dan daman can ita haka take ,shegen tsoro gareta   aiko, su sumy suka ce mezasu ba dariya ba dariya suka dinga yi har da rike ciki suna nuna ta aiko tace yau sai da suyi ta zama a estate din dan bazata rakasu gun securities ba sai da sukayi ta bata hakuri sannan suka jera suna hirar abunda ya faru. 

Ko lokacin da ummi tadawo tuni murna da farinciki Ganin tilon "dan " nata  yamamayeta zuciyarta nan suka zauna a parlour suna hira cikin hirar ne ummi take masa maganar aure  in da tace masa yakamata yanemi mata yayi aure   kasan shekararka nawa kuwa  yanzu ?yayi  murmushi ai dole nasan shekaruna ,muke nan  kullum cikin rubuta date of birth ,talatin da biyu ne kawai fa ummi Tayi dariya 32 din ne kawai   kusan duk sa'annin haihuwar ka duk sunyi aure acikin estate din nan  gasu yasir nan ma duk ansa musu rana  dan haka kaima  ka fidda mata kafin azumi DEENI yazaro idannu yana bin ummi da kallo a shagwabe yace haba first love dan sunan da yake kiranta dashi kennan tun tasowarsa  .... ni din guda nawa nake da zakice inyi wani aure yanzu. Dan Allah kiyi hakuri my  first lov zuwa wani lokaci  ,duk hirar da suke zeenat  na zaune tana jinsu haka kawai taji gabanta na faduwa lokacin da taji abinda ummi tace ,Amma jin amsar da yaya DEENI yabata yasa taji  wani irin  sanyi na ratsa  zuciyarta .
  kmr ance ya dago idanunsa suka sauka cikin nata harararta yayi  yace kallon fa kin wani tsare mutun da idanu, ummi tace uhmm kafa dawo kennan karka takuramin yarinya ,
 ya langwabar da kansa  yana maida idanunsa kan ummi cikin sanyi murya yace  haba first lov baki ga irin kallon da take bin mutune dashi bane, kmr bata san mutun ba , ummi tace kai da wani idanu ka kalleta har kasan tana kallonka. kuma ma  ni  banga komai ba kai dai ta kurace kawai dakai indai kana gida  baka barin yarinya nan ta huta  ta sarara ,  ya dubi ummi ya tabe baki , Sannan yace ke....kawo min  coffee ,ta mike  taje ta hado  coffee din takawo masa gabanta na wani irin faduwa ta durkusa har kasa ta ajiye masa .

Adaidai wannan  lokacin ne zeenat  ta kammala karatunta na secondary school , ta fito da sakamakon mai kyau domin tasamu almost 7 credit masu kyau .
shi kansa DEENI yaji dadi Sosai sanda ummi ta nuna masa Amman dayake miskili ne, sai cewa yayi Sam shi bai ga wani kokari da Tayi ba tunda bata cinye duka ba .
 ummi Tayi murmushin tace kai ne dai bakaga kokarin ta ba. Amman ni nagani km  nasan Tayi kokarin Sosai .
 Ina laifi duk cikin wayanda suka rubuta jarabawa tare bbu wanda  yakaita marks ,.
yace  ok inda ta cinye duka ne zan iya cewa Tayi kokarin  ai wayanda suke cinye 9 credit ba finta brain sukayi ba.
 Ita dai  wasa da kallace kallacen banza  tasa a gaba.
 ummi ta hade fuska tana harararsa yacigaba da zagin zeenat  ganin yadda ummi Ta canza fuska ne ,yasa yabar maganar  ,  ummi ta sake  duba result din tana shafawa hade da kwallawa zeenat data tashi tun sanda taji DEENi yasoma  zaginta  kira ,takaraso  tazo ta tsaya kusa da ummi  DEENi ya dauki wayarsa yana daddannawa ba ko kalli inda take ba  ummi ta mika mata  slip din tana murmushin tace kinyi kokari sosai , zeenat ta karba ta juya ta bar gurin dan bazata iya zama a duk inda yake ba .
 ummi ta dubi DEENI tace yanzu kuma sai aure zanwa zanwa yarinyata .
 DEENI  ya juyo a sukwane  yace wani irin aure kuma first lov  da rana tsaka , kudai Bari yarinya tacigaba da karatu kawai"  dan yanzu  kai yawaye , an daina irin wannan auren,  ballanantana mata marasa illimi  "ummi ta dubesa da kyau  ta numfasa Sannan tace ni tawa iya secondary zan  aurar daita dan ma taki sauraran masu sonta . itama shegen iyayi ne daita kuma dai   kasan matan wannan family din basa wuce secondary ake musu aure .
 kuma kasan baza'a fara karatun jami'a daga kanta ba, uhm  nima nafi son na  aurar da  abita. DEENI ya tabe baki Sannan yace Allah ya kyauta  ni ko zanyi aure bazan    auren Yar secondary   ba wlh  sai wacce tagama jami'a mai tarin illimi ,kuma ba auren family zanyi ba dan baya birgeni. yakarasa maganar yana dan murmushi ,ummi tace to Allah yabaka sa'a. amman ni tawa aure zan mata da wuri .
kai kasan halin  big dady bazai taba barinka kayi aure a waje ba .
Wlh nasoma a hada aurenka dana su  yasir yace uhmmmm su dai yi nasu ni sai nan gaba .

A wata yammacin DEENI zaune akan dadduma   awajen shakatawa   shi da abokansa wayanda duk kusan  , family ne zagaye dashi gefe guda kuma flasks ne cike  da ruwan zafi da kananan cups  ,  hira suke sosai atsakaninsu Amman banda DEENI dan gabadaya daukar hirar tasu yake shirme dan duk zance nasu akan maganar aurene wanda shi kuma  Sam baya kaunar ji , dan haka ya sharesu  yacigaba da lasalasar wayarsa ya yinda ya kai  hannunsa daya  ya dauki cup din coffee wanda orready fk ya tsiyaya masa ya kai bakinsa  yasha hade da rufe rikitattun idanunshi wanda yazame masa jiki  fk ya kalli yasir da faysal dake tawowa inda suke, ya kwashe da dariya har suka karaso bai bar musu dariya ba fk yace sannuku da karasowa Mayan angwane kunsha kamshin kunsha kamshin ,faysal yace kai dai anyi dan iskan yaro ,  kai baka tsaya ruwan ido ba kana biyewa wannan ya nuna DEENI da yatsa fk yayi murmushi yace yayi   an gwanen bana wannan karon gabadaya suka dara hannu suka bawa juna suka gaigaisa  har DEENI.
 yasir ya dube fk yace ai gara muyi aurenmu tunda muna son juna kai ka zauna kar kayi har mahdi ya bayyana  ,fk yace   A'a nifa bance saboda   me zakuyi aurenku ba . Amman gaskiya zaku takura kanku ne kawai yanzu  da wani aure wayannan kananan bbys din.
   DEENI ya tabe baki Sannan ya dube fk yace shiyasa rawar kan yaran ke kara yawa ba . dukkansu suka sa dariya  suna cikin dariyar ne  fk har da rike ciki sai gasu zeenat da suka taso daga islamiyya su biyar suka jero kowace sanye da hijab dinta  raudat da  shemah  da samiha da Maryam  sai zeenat dake tsakiyar su dukkansu kyawawane .
 da hannut fk   yake nuna musu inda  suke Sannan ya dakata dariyarsa    ya kalli inda DEENi ke zaune tamkar bai san abinda ake ciki ba , ko kallon inda  suke  bai yi ba, yacigaba   daddannawa da sarrafa wayarsa .
fk yace kai gaskiya bbys din nan fa su hadu  dayawa fa , nima ko zan dan shiga daga ciki ne.
 yasir yace dako ka huta , kabar wannan ya nuna DEENi fk ya  cigaba A'a ina ai  bazan barsa ba tare zamuyi namu auren , ko yakace mutumina kaga  Shikenan mun huta da surutu jama'a   DEENi ya kallesa a kaikaice   yace A'a ku dai da kuka ji zaku iya kuje kuyi Tayi .
Amman ni ya nuna kansa da yatsansa hade da tabe baki, ba yanzu ba"    har  sanda su zeenat suka zo suka wuce . Suna hirarsu suna  dariya  Maryam ce ke basu labarin abinda ya faru jiya bbu wanda bai dara ba har ita zeenat din raudat tacewa zeenat  ai ke kika daukar masa wlh kuma yarinka yi miki kennan ina ma nice daya gane kuresan  suka sake yin dariya .

Tun lokacin daya dawo zance sa da ummi bai wuce  DEENI kayi aure  fito da mata cikin yan,uwanka kayi aure hirar kennan sai dai idan basu zauna ba  .

Yau takama walimarsu  zeenat  ta saukar alqur'ani mai girma wanda aka  shirya musu  anan islamiyyarsu dake cikin estate din ,su kusan goma   anyi taro  walima lfy  yayinda zeenat ta karbi kyaututtuka da dama saboda kokarinta har kuka ummi Tayi sakamakon tunowa datayi da er'uwarta taro ya watse lfy  kowa yakama gabansa  ,byn sun gama hirarsu da ya zame musu jiki  suka fara hada kujerun da akayi walimar dasu   .     sun fito kennan suka ga Yaya DEENI da wani abokinsa zaune   akan  kujera biyu  suna hira ,take suka ja birki samiha tacewa zeenat jeki amso wadan can kujerun, cikin zolaya tayi mata maganar dan tasan yadda take jin tsoronsa zeenat tace uhmmmm ku dai kuje "suka sa mata dariya ke wlh muguwar matsoraciyace  wlh ki rage tsoransa shiyasa yabi duk  ya renaki ,Tayi    sororo tana kallonsu , Sannan tace to bari naje amso Tayi tafiya kmr zata isa gurinsa sai kuna ta juyo da sauri" aiko suka sake  kwashe mata da dariya .
muryashi ce ta katse musu dariyar tasu lokacin daya suke kallonsa a frigice" yayinda gaban zeenat   yasoma faduwa yace ke....da hannu ya nuna musu alamun suzo 's  suka nufo  inda 
Yake cike da tsoro ya zuba musu rikitattun idanunsa  yana kallonsu daya byn daya  yana nazarinsu  Sannan yace da ganinku akwai alamun rashin gaskiya atare daku ? ya nuna su da dan yatsansa zeenat Tayi saurin cewa A'a cikin inda inda   uhm bbu komai fa Tayi gudun Kar wata cikinsu tafada masa shiyasa Tayi saurin yin magana ,to menene na inda inda wama ya tambayeki  ?Tayi shiru tamkar ruwa yacinyeta. Sannan ya juya ya kalli abokin nasa da ya zubawa zeenat   idanu yana kallonta   kafarsa  yasa ya take kafar manir  dashi ,sannan ya dawo natsuwarsa ya  mai da hankalinsa kan DEENi , DEENi ya  nuna su  zeenat da samiha hade da shemah da Maryam yace gasu nan    bansa inda sauran suka nufa ba,  manir  yace ina tayaku murna walima saukar alqur'ani mai girma, Allah yasa na tsoron Allah ne  ,suka hada baki wajen cewa Ameen , kallonsu kawai DEENi yayi jikinsu har  rawa yake suka bar wajen.
  manir yabi bayansu da kallo yace  kai sisters din nan naka  fa akwai kyau DEENi ya kallesa yana watsa masa harara ok iskancin naka kuma yau agidanmu zai Kare.
 manir yayi murmushi yace Allah barin ma wace ta tsakiyarsu gaskiya duk tafiso haduwa DEENi ya kalli inda ya nuna sai yaga zeenat yake nufi take yaja tsaki  manir yace dama ita ka zaba wlh  dan nasan karshe ma  auren zumunci za'a maka DEENi ya sake jan tsaki dan Allah malam karka dameni da wannan shirme bazan ,manir bai daddara ba ya  sake cewa Allah dama tsayawa kayi akayi Yar gida tunda duk tarin  matan dake sonka baka kallonsu , a fusace  DEENi yayi magana dan me zan kallesu alhalin  banda abinyi dasu.
 manir yayi murmushi  ina ma ni ne kai wlh tsayawa zanyi na kwashi gara son raina  har sai nagaji in more kuriciyata  , DEENi yace ai kai dan iskanci ne lamba daya , wlh  ka guji abinda kakewa ya'yan mutane "ko dan gaba .
   ka dauki neman mata tamkar wani abinci, manir ya dan  daki kafadar DEENi yace  ai sun fi abinci dadi ,.
Amman Allah koni ina son na daina bin matan bazan ,wlh  abun ne da kmr wuya Amma kacigaba da yimin addu'a . DEENi ya nuna sa  kai zanwa addu'a saboda banda abinda zan roka   Allah , manir ya dage masa gira daya yes meye dan kamin addu'a kaga idan Allah ya shiryani sai kabani wacce Yar dimadimar  sister din taka na aura , bai kulasa ba sai canza zance da yayi nan dai suka cigaba da hirarsu har zuwa sanda  sukayi  sallama da juna   .

Abinda zai daure maka kai   bai wuce yadda  ummi ke sake  bawa zeenat kulawa ta musamman ba ,ta kowani part tana iya kokarin ganin  ta fito da diyarta ta  tsab,  zeenat bata rasa komai ba tun daga  dangin sutura da  mayuka shafe masu tsada zuwa kayan kwalliya  ana cikin haka tafiya takama ummi zuwa India dan haka ta tasa diyarta gaba suka tafi   zeenat taji dadin  zuwansu India tamkar karta  dawo ,watan su daya suka tattaro suka diro Nigeria saboda bikin family dinsu yakusa koda ta dawo ma su Maryam sun dinka mata duk anco din da aka fidda tunda damar suna da telarsu ce da yake zuwa har gida ya karba dinki,.
 biki akayi sosai bakama hannu yaro an kashe kudi tamkar ba'asan  ciwonsu ba  bidia iri kuma a duk anan cikin estate din akayi komai, daga karshe akayi walima washegari ranar  Sunday aka daura auren  en mata biyar haka ma samarin aka dan kowace gidan mijinta, ya saura  mutun  uku ne cal suka rage da basu aure ba, Maryam da shemah sai zeena amaza  kuma fk da DEENi sai  kamil  .



MMN SUDAIS CE

💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗




Aysha A bagudo



Page 5-6



Zeenat na da kyau  sai dai ba can ba" fara ce Sol Amman batada dagon hanci wannan bai sa fuskarta muni ba" haka idanunta matsakaita ne ita mutun ce mai tsananin son kwalliya wanda ko alwala Tayi sai ta sake yin  wata sabuwar kwalliya, haka  nan ummi bata gajiya da siya mata kayan kwalliya iri iri  sannan bata ganin aibunta a duk lokacin da zata bata a gurin yin kwalliyar .
abinda kawai bata so kuma bata yarda dashi ba, shine a yimata dinkin da zai bayyana surar jikinta ,nan nefa tace bazata bada goyon baya gurin  bata kamasho yada zina ba , dan a cewarta shigar da yawancin ena'mata keyi a wannan zamani itace ke sake haifar da fashadi a doron kasa.
  zeenat akwaita  da saurin sabo da mutane sannan km tana da son kawaye ita da Maryam dan ko yanzu suka san mutun   ko km kuka  hadu dasu sanadin wata kawar, Shikenan sun zama kawaye  , shiyasa suka fi dukkan sauran en'uwansu   jama'a dan daga  waje ma zuwa ake gurinsu  sabanin sauran" kullum kaga ana rikinci a bakin get da sune , gurin shigo da baki   most especially ma na school dinsu. abinda ummi tafi tsana kennan daga gareta yawan tara kawaye gata da matukar son gayu ,da son kallace kallacen film muddin tana gida kuwa bata da aikin yi sai na kallo ,daga wannan Chennal zuwa wata ,sai dai duk da wannan halin nata Allah yabata illimi sosai both arabic & school.

Daidai misali   Allah yayi mata farin jinin samari masu sonta daga waje ma biyota akeyi, sai dai bata fita dan ma ummi taki yarda tafara zance da wuri sai data kai ss2 kuma duk masu zuwa gurinta da aure suke sonta "amman matsalar dai daya ce family dinsu basa yarda da macce Tayi  auren  wajen Amman sukan bar namiji.
  kana duk masu son nata bataji son su har cikin  ranta 'har wani lokacin ummi kesata gaba da fada "tace maza ki tsaya ruwan ido daga karshe kirasa kowa kizo kina nema yawan yi mata fadan da ummi keyi ne yasa ta tsaida kamil dan gwaggonta"  yayar mahaifinta  da suke uwa guda uba guda .
  shima bakowa yasan suna tare dashi ba , dan bata gama tantancewa aurensa ba" kuma shi bai fiyye  zama a garin  ba  yana aiki ne a abuja  ". haka kawai taji idan bata samu  wanda yafi ba  , zata iya aurensa dan shima ba laifi .

Jiki da jini wata safiya  ummi ta tashi da ciwon ciki , wasa wasa  tun tana daurewa har abun yafi karfinta gabadaya tafita haiyacinta'  hankalin zeenat yayi mugun tashi dan bazata manta yawan labarin da ummi ke yawan bata na mahaifiyarta  da irin wahalar da batasha  kafin mutuwarta ,ciki har da  cewa mata Tayi ta bude ido ta zabi miji wanda zai san mutuncinta kar taje gurin ruwan idonta ta kwashi gaibu ,shiyasa take massefar jin tsoron haihuwa da mutuwa dan ta kudircewa ranta, ta amince da mutuwa tunda tasan muddin kwanakinta suka Kare Shikenan "amman ita kam bazata yarda da haihuwa ba ganinta garata tasha wahala daya .
wunin ranar da ciwo ummi ta wuni can kuma tasamu sauki    dare nayi ciwo ya sake dawo zeenat taso zuwa ta sanar da DEENi Amman ummi taki .
 washegari DEENi yashigo da shirin fita aiki  dan bai san bata da lafiya ba koda yashigo dakin yayi matukar girgiza da ganinta kwance cikin bargo da kyar take iya magana a rude yakaraso inda take  ya  tambayar ba lafiya ne ? Ummi tace eh tun jiya  yace meyasa  baki sa an tashe ni ba ,ya kalli inda zeenat ke rukube kusa da ummi duk tazama wata  kalar tausayi.
 ke....Wace irin" sakariyace da baza ki iya zuwa kisanar min ba da kyar ummi ta iya bude baki ,tace ni na hanata  ya furzar da huci ta bakinsa hade da cire hular kansa yayi wurgi dashi gefe ,take ya Ciro waya cikin aljihun bayan wandonsa yakira family doctor dinsu wanda side dinsu kawai yake dubawa.
 mintina kadan sai gashi likinta dayake bai da Nisa dasu cikin sauri yashiga duba ummi sosai har drip aka sawa ummi a ranar DEENi kasa fita yayi koina byn likinta ya wuce ne, ya kirasu ya Mahmoud ya sanar masu da ummi fa ba lfy , idanunta ta zuba mashi tana kallon bakinsa yadda yake maganar ne  tamkar wata mace shi yafi daukar hankalinta, 
ba taba jin DEENi ya birgeta  ba irin na yau.
 duk wunin  ranar  kusan shi yayiwa ummi komai  hatta magani da abinci a baki yabata sai gurin la'asar su Yaya Mahmood sukazo tare da matansu    sai zuwansu ne ma yasa mutane cikin estate din suka sani   dan DEENi bai sanar da kowa ba, shi dai ta mahaifiyarsa kawai yake.
Ai kafin kace me tuni side din ummi yacika da jama'a, haka  suka dinga shigowa duba ummi har dare DEENi na tare da ummi yana bata kulawa. duk yayi wani iri cikin lokaci kadan yafita haiyacinsa zeenat na zaune a gefe guda tana jiyo hirarsu rokonsa ummi take akan yayi aure ahankali takira sunansa NASURULDEEN ....abinda  yasake tada ma DEENi hankali kennan yaushe rabon dayaji ummi  takira complete name dinsa , tacigaba ban rasa  komai  na rayuwar duniya ba inada tarin dukiya da kadaroro  wanda ni kaina basan iyakarsu ba ,burina da muradina ahalin  yanzu bai wuce inga aurenka ba,  Amman na fuskanci kafi son sai na mutu sannan zakayi aure . Jikin DEENi ya dauki rawa hankalinsa ya sake tashi matuka ta sake kiransa cikin tattausar  muryar hade da rarrashi DEENi banida kowa daga kai sai zeenat sai kuma dan uwana wanda yake wata uwa duniya ,idan bakayi aure ka taramin jikoki masu albarka ba mezakayi min naji dadi , ina ji ajikina sai na mutu zakayi aure a rude yace first lov ki daina cewa haka  zanyi inshallahu kina raye Tayi murmushin karfin hali tace kullun haka kake cewa, ni tuni na fidda raina ka tashi katafi Allah ya maka albarka ... Amman yarinyar nan zeenat na rokeka dan Allah ko ban tashi ba kada kabari ta koma hannun mahaifinta, na damka  amanarta a hannunka ,bata da kowa duk duniyar nan daga ni sai kai ,karikemin ita a hannunka har zuwa lokacin da zata samu miji . DEENi yakamo tafin hannun ummi cikin nasa ahankali yasoma magana muryasa cike da rauni da fargaba, yace haba  first lov ki daina maganar mutuwa nan kece zaki aurar daita  da hannuki kuma kina raye inshallahu ta girgiza kai ita kadai tasan abinda take ji cikin muryarta irinta marasa lfy tace Shikenan tashi kaje ka kwanta , hankalinsa a tashe ya fice daga dakin..
 zeenat ta mike daga inda take idanunta na zubda hawaye  ta taimaka mata suka kwanta tana kuka kasa kasa ummi tace lfy zeenat  ummi . .... ummi..... cikin sheshekar kuka tace banason naji kina cewa zaki mutu kibarni dan Allah ,ummi   tace nafa da kar na fada mutuwa ta zamemin dole  sai dai idan ajalina bai zo ba . zeenat ta saki kuka hade da  kamkameta ummi a jikinta , tacigaba  da  kuka mai cin rai hade  da cewa ummi bazaki mutu ba inshallahu da kanki zaki aurar dani ni ga duk wanda kike so  da kyar bacci ya dauketa yayinda ummi Tayi nisa a bacci .

Shi kuwa DEENi tunda ya koma dakinsa ya kasa zaune ya kasa tsaye  sai zariya yake daga farkon dakin zuwa karshe kafin daga baya ya nemi gurin ya zauna.
  yayi tagumi da duka hannuwansa yayi zurfi cikin tunanin yadda zai yi lallai ya zama dole ya nemo mata  domin cikawa umminsa burinta. sai dai shi matsalar sa bai san ta ina zai fara ba ? Bai taba yin buduwar ba ballanantana wata aba soyayya,  shi duk a tunaninsa raini hakan zai jawo masa idan  yaje yace yana son budurwar .
ya kamo gefen lips dinsa ya dan cizawa a hankali har daga karshe ya yanke shawara zai nemi fk da zance anan ya sulale ya kwanta rigingine idanunsa na kallon celling  dakin .
yayinda ya rungume hannushi a saman kirjinsa  yana aiyana irin type din maccen dayake son  ta mallakesa,kuma  wacce ya dace ya aura cikin sanyi ya runtse idanunsa gam  take yasoma zaiyano irin type dinsa kyakkyawa dogowa mai dirin jiki , choculate colour, mai dara daran idanu sannan educated mai wushiryar haka dai ya rinka yi har dare ya sula  bai samu wani  ishashen bacci ba. koda asuba kafin ya tafi masallaci sai  da ya fara shiga Bedroom din ummi ya sameta tana sallah ya sauke ajiyar zuciya sannan ya wuce ganinta tsaye tana sallah yasan Allah yakawo mata sauki .

A masallaci DEENi suka hadu da fk byn an idar da sallah "yajashi gefe guda da idanu fk yake binsa da kallo "abinda bai taba faruwa ba saboda DEENi  daya idar da sallah yayi yan addu'oinsa yake wuce wa  gida .
  fk ya dube sa da kyau yana nazarinsa  kafin daga baya yace lfy kuwa  naganka haka ? Gabadaya fk yagama tsurewa da ganin yanayinsa sai da ya sake maimaita tambayarsa sannan DEENi yace ina fa lfy jiya  ummi kwana Tayi  ba lfy har tana barmin wasiya burinta da muradinta yanzu bai wuce nayi aure ba.
 fk yayi shr yana jin DEENi har sanda yagama bayaninsa sannan yace baita kadai ba har big dady ma burinsa kennan  dan ko jiya sai daya min maganar nida kai  Amman tunda kai ummi ta damu  ta tsananta gara kayi  kawai kurabu lfy .
DEENi yace ai bakasan inda zan nemi matar ba nifa gabadaya en,mata family din nan basu min ba  sannan kuma sun min kankanta da aure  ,fk yace A'a bawani kankanta" mace na kankanta  da aure ne ?  kaine dai kawai  kake ganin haka ,ni   yanzu na yanke  shawarar  zan tsaida shemah kawai  tunda na dade ina sonta nida zakaji shawarata ma  da  zeenat ka aura  DEENi ya mishi wani irin kallon bakada hankali sannan yaja tsaki yace haba dai  zeenat , fk yacigaba yarinyar akwai hankali wlh ,ba kmr  wancan banzar ubannata ba, dayake duk sun tsani  halinsa.
    kaga kawai sai a hada bikinka  da nawa kawai  kaga zeenat batada matsalar, km ko bakomai ummi zata ji dadin Sosai da wannan hadin.
 DEENi yace Amma ban taba jin koda alamar digon sonta ba, kuma ni gaskiya ina ganin tamin yarinta dayawa duk fa shekarunta sha tara  zuwa sha ashirin ne  fa. nafison mutual girl wace ta mallaki hankalin kanta tasan yadda zata kula dani akan bed ,amman wannan Yar bbyn maimakon ta kula dani ,ni ne zan koma renonta.
 fk ya dubesa a kaikaice yace lallai yaran zamanin da   kasani Amman banda na yanzu, sai su maka abinda manyan matan baza su iya ba,  kana rai nata ne kawai , sai kaga mararta ta daukeka tsab, DEENi yaja tsarki kai ban son iskanci shawara nake so, ba wani shirme ka  can na bazan    ba .
fk ya kada kafada yace well tunda kaga bata maka ba kana iya duba wasu acikin gari .
DEENi ya kalleshi  yana watsamasa harara "kaifa dan iskane dan kaga nazo maka da maganata shine zaka rainawa kanka hankali " sai kuma yayi kasa kasa da murya  yace kasan Allah ni fa ko a waje ba wai ina kallon mata bane, fk yace to katsaya akan zeenat din kawai, duk inda ake neman macce mai natsuwa yarinyar nan takai ,DEENi ya sake jan tsaki yace ai inda takaicin yake kennan sai kuma nakirata ince ina sonta ...ya fada yana tabe baki "hade  jin takaici da  haushin shawarar da fk yakawo masa " fk yace inda bazaka iya ba kabi ta sama , ma'ana kasamu big dady da maganar kawai, kasanar dashi kana sonta  nasan zai ji dadi Sosai .
DEENi  ya sake watsamasa wata harara yace dan Allah malam ka dameni , ina ganin fa kmr kafara samun tabin hankali , wa yace dakai   ina sonta "zan dai yi aure badan ina so ba ,ya juya yabar fk nan  tsaye   yana binsa da kallon mamaki sannan kuma yace ai kaine babban  mahaukacin   dan iskan kawai , sai iskanci fall ciki ,shi bai ga laifinsa da yace bazata ya saukarsa a bed sai nawa sai kuma ya kwashe da dariya .



MMN SUDAIS CE

💗💗💗💗💗
 AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO


Page  7-8


Har DEENi yazo gida tunanin yake akan shawarar da fk ya bashi" anya kuwa zai iya amince da auren zeenat ? 
Lokacin da yashigo yayi daidai da zeenat ta tabare magani tana mikawa ummi ,ta amsa ta apa zeenat ta Mika mata ruwa  ,yayinda shi km yake tsaye jingine da jikin kofa rungume da hannuwansa duka a kirjinsa yana kallonsu, take zuciyarsa ta dinga ingizashi akan lallai bbu wace ta dace ya aura sama da zeenat bisa ga hujarsa tacewa ,bazai taba samun matsala daita gurin kula da mahaifinsa saboda irin soyayyar dake tsakaninsu "
yasan ko yana nan ko baya nan zata   kula daita, umminsa zata zamo a karkashin kukawarta tunda zeenat bata da wata uwar da wuce ummi tunaninsa ya katse lokacin da ummi takira sunansa' tace son karaso mana yayi frigigit ya dawo natsuwarsa ahankali yashiga takowa har inda ummi take ,ya zauna zeenat ta gaidashi ta mike zata fice daga dakin bai amsa mata gaisuwar data masa sai dai yabi bayanta da kallo" ummi ta kalleshi  ta kauda kanta,  yace first lov yajikin naki ummi ta danyi murmushi hade daura hannuta kan sumar kansa  tace naji sauki sosai , ahankali sauke ajiyar zuciya ko bai ce komai ummi ta fahimci yaji dadin yadda yaganta ,yana nan zaune , Sam yakasa  yiwa ummi zance yana ya   auren zeenat din  ,daga  karshe ma tunani yayi kawai gara yasamu ya mahamud  da zance dan gaskiya kunya yake ji yayiwa ummi maganar da kansa .

Da yammacin ranar byn ya dawo daga office yaje har gida yasamu ya mahamud da maganar ya ji dadi kwarai da gaske, har yarasa inda zai sa DEENi dan farinciki dan shima da kansa  ya matsu yaga DEENi  ya ajiye iyali kmr kowani magidanci , yace Shikenan sai kasamu yarinyar da zance, ku daidaita kanku DEENi yace A'a ina ganin  basai na sameta ba in dai first lov ta amince ai Shikenan .
yaya mahamud  yace ummi bazata taki ba Amman dai kasan kaidar auren gidanmu kennan  bbu dole a ciki "muddin kuka daidaita kanku na iyayenmu may sauki ne idan Kuma ita ummi ta amince ita yarinyar  tace bata sonka fa? DEENi yaji haushi da takaici  sunkamasa alokaci guda yace ai nima ba wai ina sonta bane kawai dai zan aureta ne.
 Yaya mahamud yace  shirme bazan kennan kai yanzu idan anzo meeting cewa zakayi basonta kake yi ba ,zadai ka aureta ne ?DEENi yayi murmushin gefen baki har dimple dinsa ya lotsa sannan yace  cewa kurum zanyi ina son zan aure zeenat ne ' Yaya mahamud yace to Allah ya mana zabi na alkhari kabari zanje gurin ummi tukun  duk yadda mukayi daita  zakaji   DEENi yace Shikenan ya mike fice ,a office ma koda yaje  aikinsa kawai yasa gaba  .
 dan shi gabadaya ya manta da wani zance aure can .


Mahamud yasamu ummi cike da karfin gwiwa" ganinsa ba wanda zai kai ummi murna tunda daman burinta kennan  naganin auren DEENi, Amman ga mamakinsa yana gama labarta mata abinda yakawo shi, sai yaga ummi tayi kicin kicni da ranta tamkar bata taba sanin wani abu  farinciki ba "sai da gaban Yaya mahamud ya fadi dan  ganin yadda ummi tayi da fuska tamkar yazo mata da zance mugun abu " tace kai ne kaga sun dace kaba shi shawara  ya nemi aurenta ko Kuma shi da kansa ya sameka da zance ?
 Da sauri yaya mahamud yace A'a shine dai yazo min da zance ummi ta sake daure fuska, sannan tace ka koma ka fada masa ban amince ba ,kace masa akwai sauran mata  a gidan nan  yana da damar zabar duk wacce tayi masa, idan ma ya canza ra,ayinsa nakin auren family'  to yaje waje ya nemi matarsa can itama Allah zai bata nata mijin, Amman Sam ni ban yarda da wannan hadin ba " tayi shiru  na wani lokacin kana zubawa Mahmud idanunta tana kallon yanayin daya shiga ,ahankali ta numfasa sannan tace kana iya  wucewa idan kana da abinyi ka manta da wannan shirme na DEENi .
 Yaya mahamud yayi kasa da kansa Sosai cikin muryasa can kasa kasa  da alamun km  rarrashi yace dan Allah ummi ki amince da auren nan bazan iya tunkarar DEENi da maganar ba.
  duk da bansa dalilinki nakin amincewa ba" ummi ta dan saki fuskanta ba kmr dazu ba tana mugun son mahamud tamkar dan da ta haifa acikinta tana jinsa har cikin zuciyarta .

 tace bawai ina kin hadin bane duk duniya idan akwai wanda zai so auren DEENi da zeenat a bayana yake ,na farko dai kaima kasan halin DEENi  da dan bazar zuciya , ga saurin fushi ga maseefar miskilanci tsiya ga jin kai sannan da bakinsa yasha gayamin cewar shi bazai taba yin auren family ba sannan shi mai digiri yake so ya aura ,shine km yanzu  zai zowa mutane  da wani salo.
 ni da tawa iya secondary kadai ta tsaya" ai kai da jin zancensa ma kasan akwai wani makirci daya shirya "dan nace yayi aure ai bance lallai sai ya aure tawa yarinyar ba , Muhamud yace ummi ki duba  lamarin abun  tunda shi da kansa ya furta cewa ita ta masa ba za'a samu wata  matsala ba ,.
  ummi tace Sam bata yarda da wannan tsarin ba " ita dai yaje gaba ya nema hakurin duniya nan  bbu wanda yaya Muhamud bai bawa ummi ba amman taki amincewa ,duk ta inda ya bullo mata sai itama tabiyo masa ta wata hanyar, har ran  yaya mahamud yasoma baci ,yaji haushin abinda ummi tayi dan haka ya hakura ya fice ransa abace .


DEENi zaune a office dinsa  ya dukufa wajen tura sakwanni a yanar gizo ,hankalinsa kwance yake bin komai daki daki , yaji daya daga cikin wayoyinsa ,daya ta dauki karar sauti mai dadi ,ya dauke idanunsa  daga kallon system din yasa hannu ya dauki wayar yana dubawa ganin sunan dake yawo akan screen din ne" yasa yayi sauri dagawa yakara a kunnenshi hade da yin sallama"  kana ina muryar Yaya mahamud yaji ta daki dodon kunnenshi cikin sanyi murya DEENi yace ina office yace ok idan katashi kabiyo  inason ganinka sannan ya kashe wayar .

DEENi zaune a gaban Yaya mahamud kansa sunkuye a kasa yayinda  idanunshi ke  kallon zarazaran yatsun kafafunsa yana sauraron sakonshi da ummi tabayar a sanar dashi.
 a gurin Yaya mahamud sam bai tsammaci jin haka daga umminsa ba ,ga mamakin Yaya mahamud sai yaji deeni yace Shikenan babu komai Allah yasa haka shine mafi alkhari .
ya mahamud yace ka hakura kennan? Nashi ganin bazai damu dan ummi ta hanashi auren zeenat , dan haka Yace  eh "tunda daman ba wai yana sonta bane" nan dai suka bar zance  aure suka shiga wata hirar daban a inda Yaya mahamud ya tashi yaje  ya kwaso wasu takardu da file files ya zubesu nan  a gaban DEENi yace yasa masa hannu ciki " kai tsaye DEENi  ya zaro wani hadadden Biro daga gaban aljihun  rigarsa yasoma cike  gurraren da akeso yayi sign, dan gabadaya dukiyar DEENi , sulaiman da Muhamud ne akai su suke kula daita  kuma komai na tafiya daidai " domin dukkannisu abu guda ne a gurin ummi  dan ma idan ba'agaya maka ba…
 zaka dauka duk ummi ce ta haife su . 

Sai da DEENi yagama sign din ,sannan yaya mahamud hada da mishi bayanin companies din da suke son budewa a  kasar  American, sun turo musu da sako akan suna da bukatar mutun daya daga cikin masu company din " yazo interview dan haka shi ya wakilta sulaiman yaje , DEENi yayi murmushin yace Shikenan bbu komai duk yadda kukayi ,daidai ne  Allah ya taimaka .


To byn DEENi yakoma gida ya dingawa ummi wani irin kallon, wanda shi kansa yakasa gane dalilin yin haka, yana son yi mata magana Amman yayi shr    ,yayinda  zuciyarsa ke kwabarsa akan ya share kawai ai baita kadai bace mace a duniya" daman ai dan ita yake son ya aure zeenat din ,da yaje waje ya aure wata wacce bai san halinta na boye ba ai gara zeenat din Amman tunda  bata so shima ya hakura .


Da misalin karfe goma na dare DEENi sanye da rigar wanka dan fitawarsa kennan daga bathroom ,ya tsaya gaban dress mirrow yana karewa jikinsa hade da  zare rigar wanka dake jikinsa" ya saura  daga shi sai boxer   , yabi koina a jikinsa da turaren Hamilton 27, sai daya kammala da  komai na al'adarsa da yasaba yi kafin ya kwanta   sannan ya hau kan royal bed din ya lumshe rikitattun idanunshi, alamun yana son yayi bacci' sai dai baccin yaki zuwa  kawai ya tsinci kansa da tunanin zeenat.ya rinka jinta ajikinsa , yadda yake jinta a halin yanzu bai tsammaci abin har ya zai  haka ba ,,
Sosai ya tsinci kansa cikin damuwa ko baya son yarinyar hakika ya tsananta da son aurenta yayi shr yana tambayar kansa abinda ummi take nufi da kin amincewa datayi,shi  ya guji big dady da  maganar a tunaninsa sai umminsa tafi kowa murna da jin dadi 'ya dauki tsawon lokacin kwance kafin bacci barawo yayi gaba dashi .

Byn kwanaki , DEENi yakasa hakuri da maganar zeenat din kmr yadda yaso shima ta share da zance kawai  ya manta dasu "
 Amman yakasa, ya samu ummi da kansa a wata safiya dayazo gaisheta byn yayi shirinsa na zuwa aiki cikin kakinsa dake kara masa kyau tamkar dan shi kadai akayi" sai kamshin yake zubawa ta koina "gashin kan nan nasa kwance luf luf luf dasu , duk da bacika yawa sukayi ba ,saboda yanayin aiki "Amman dayake Allah yayi mishi suma  takoina ajikinsa ko yayi askin ma baya wani dadewa" gashin zai sake fitowa" sosai yayi  kyau  matuka ,ita kanta ummi satar kallonsa take har ya tagota ya sakar mata murmushi tace son kayi kyau sosai fa, uniform din nan  nakara maka kyau ,ya dage mata girarsa daya yace Allah first lov  yace ai daman can nj  may kyau ne   sannan duk maccen datayi dacen samuna , ta gama samun duniyarta  sai dai ta nemi lahirarta kawai " ummi tayi dariya sosai ya kamo hannun umminsa cikin nasa muryasa a shagwabe hade da dan karyar da wuyansa, yace first lov  da kanki ma kin yaba dani "tace uhmm  yabon gwani yazama dole "yace to meyasa bazaki bani auren zeenat ba ? 
Ta lissafomasa dalilinta kmr yadda ta sanarwa Muhammad ta Kuma sake jaddada masa yaje gaba ya nemi mata Amman banda diyarta ranshi ya baci Amman ya share take Yar fara'a dake fuskarsa  ta dauke "  sai dai bai nuna ba , cikin sanyi murya yace to Shikenan ummi na hakura" Amman bazan taba zuwa koina neman aure ba" saboda banida nagartar  daza'a soni Kuma  bani aure"  ummi tace ba fa haka nake nufi ba yace haka ne mana first lov" ina da munanan halayen da ban cancanci abani mata aure  ba. ummi tayi murmushi tace nifa bance haka ba yace haba first lov kince mana  gashin nan kema da kanki kin hanani taki Yar , to waye zai amince yabani yana kaiwa nan ya cire hannun umminsa cikin nasa ya mike cikin sanyi jiki tamkar bai damu ba ,.
gabadaya jikin ummi yayi tsanyi ita bawai auren ne bata so ba halinsa take gudu ta yaya zata yarda ta aura masa marainiyar Allah yazo yana cutar mata da yarinya .

Abin mamaki duk a tunanin DEENi na bazai shiga damuwa ba akan kin amincewar ummi ,
sai gashi dumu dumu cikin tashin hankali kullun sai yayiwa umminsa naci da magiya akan tabashi auren zeenat ,ita kuwa ummi duk lokacin dataga ya dauko mata zance sai share hade da bata fuska  .



Please kumin uziri , may be zaku dan jini shiri sakamakon matsalar rashin wuta naso narinka muku type akai akai batare da westing time ba Amman kuyi hakuri ana kyawun tare🤝🏻🤝🏻



MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO



Page 9-10


Zeenat kwance a  bedroom din ummi hannuta rike da  wani English novel   face to face tayi zurfi cikin karatun novel din saboda yadda  take enjoy din novel din ya .

Yaya DEENI ne yashigo gaishe da ummi    kafin yafita aiki  ,byn sun gaisa ne ummi  tace har ka shirya   fita kennan ? Yace mata eh sannan yaja ya tsaya yayi  shr ya zubawa ummi idanunshi .
ummi ta dubeshi tace da magana ne ?   Tunda tarigada tasan muddin yayi shr irin haka to da magana a bakinsa.

 koda yake tasan dai zance nasa bai wuce maganar zeenat bane " Kuma daman tana son zeenat din tajima kunneta idan ta amince ruwanta "
dan haka ummi kalleshi da kyau tana nazarinsa ta numfasa sannan tace masa kayi shr alhalin nasan da magana abakinka   .
, muryasa a shagwabe yace first lov kan dai maganar zeenat ne ,dan Allah first lov, ba yabon kai ba  "ina da qualities  din da za'a bani auren  kowace irin mata nake so" Kuma ko Yar gidan waye ,.
Yar taki ma daba wani kyau ne daita ba" dan ma zan taimaka mata "ya fadi haka fuskarsa a hade ,.

ummi tace duk da haka day bazan bada diyata ba kaje waje ka gwada sa'a r ka" wai ma in tambayeka DEENi yamaida hankalinsa sosai  ga umminsa" tace   kai da kake ta damun kanka da zance nan  kullum. kasamu ita yarinya da maganar ,kun daidaita kanku  ne ? 
DEENI yace uhmm kece dai zaki sanar mata, ummi ta nuna kanta  da dan yatsanta,  nice ma zan tayaka  yakin nemar maka soyayyarta" lallai ma bason auren nata kakeyi ba"  kashare zance kawai tunda baka shiriya neman aure ba. yace to ni first lov in na fada   sai  naga tamkar Raina ne zatayi, ummi tace kunji girman kan ba  a hassale ummi tace dan Allah kayi hakuri kabar zance nan. haba duk kabi katadda hankalinka da nawa. yarda ne dai bazanyi .
dan haka   kayi hakuri kabar zancen nan kwata kwata dan ba yarda zanyi ba .

DEENI daya gaji  dayiwa ummi magiya ya hakura ya ficewarsa ,yana jin takaici kansa, tunda daga lokacin da zeenat taji DEENi ya ambaci sunanta ta mike zubur zaune daga kwanciyar datayi, hankalinta a tashe jikinta har rawa yake tsabar rudewa"   ita zeenat din yaya DEENi  yake nufi ko wata daban.
 ahankali ta furta in ko ita yake nufi dakuwa ta more a rayuwarta, dan gaskiya  yaya DEENi ba irin namijin da mace zatace bataso bane , ahankali ta sake furta A'a dan Allah ummi kada kimin bakinciki mana.

 tana jin fitarsa ta fito da sauri daga dakin tana kallon ummi dake zaune tana jan carbi,  zatonta ko ummi zata mata maganar ne. Amman sai taga sabanin haka .
  dan kuwa ummi  ko kallon inda zeena take tsaye batayi ba.
 dan tarigada tasan taji komai" to Kuma bayanin me zata tsaya yi mata. Ta dai yi shr ne  taga yadda zata dauki lamarin .
Can kuma, ummi ta dago tana duban zeenat din tana nazarinta" yayinda zeenat din itama ummi take kallo" har zuwa lokacin  ummi batace komai ba .
sai ma  kau da kanta gefe datayi  , ganin ummi bada niyyar ce mata komai  ,yasa zeenat kira sunan ummi"  ta juyo tana duban zeenat din da kyau".
 ahankali cikin sanyi murya tace ummi wai wata zeenat din yaya DEENi keso ?
Ummi ta dan tabe baki sannan tace dan Allah rabu dashi  wai ke yake nufi "da sauri zeenat tasa hannuwanta duka ta dafe kirjinta dasu tana zaro idanu waje "tace  da gaske  ni yake so ?
ummi tace zan miki karya ne"  zeenat ta marairaice murya tace shine Kuma ummi zakice  masa baki yarda ba.

 ummi tace to may kike nufi ,kina son kice min kina son DEENi kennan ? Zeenat Tayi shr dan bata da amsar bawa ummi dan  gabadaya ilahirin jikinta bbu inda bai dauki rawa ba.
 ummi ta sake yin magana daman kina son DEENi ne naga duk kin tada hankalinki  haka ?zeenat tace nifa bance ina son shi ba Amman ke meyasa zakice A'a Kuma ma mayye dalilin dayasa kika ki amincewa ,ummi tace ok tutseni zakiyi" kan naki yarda ko yaya , zeenat tace ba haka bane" ummi tace tsaya ma kiji  abinda yasa naki yarda, DEENi "da" nane' ni haife shi da cikina sannan ke ma kinsa halinsa sarai da shege miskilanci da saurin jin haushi  mutun ,abu kankani ke hassalashi ga tarin  girman kan tsiya, zeenat ta tsugunna nan gaban ummi  hade kamo hannuwan ummi  duka cikin nata muryarta sanyaye tace  haba  ummi dan day kawai saboda wannan halin nasa ne "zai sa kike amincewa  , in dai dan haka ne' ni na amince da aurensa  kinji .
ummi tace duk kinbi kin koma kalar tausayi wai ma  meyye birgeki   da DEENi  ne naga duk jikinki ya dauki  rawa haka ?.
 Zeenat tace ai gaskiya yaya ba irin mutunmin da za'a tsaya cewa ba,aso bane ni dai na amince ,ummi tace ko kin amince, ni nace A'a ban yarda ba ,.

Zeenat ta mike  cikin fushi tayi bedroom din ummi .
da kallo ummi tabi bayanta dashi ummi taji matukar mamakin ganin reaction dinta musamman da tasan zeenat din ,bata fiyye nuna fushinta akan abu ba .

Koda tashiga dakin ma waje tasamu ta zauna abunta tayi tagumi batayi aune ba, kawai taji  hawaye na silalowa mata.
 ita kanta tasha mamakin ganin hawayen  na zuba a idanunta "ta tambayi kanta  to  daman can tana son DEENI ko yaya? domin abun itama yayi maseefar  daure mata kai ".
kuka takeyi " iya karfinta hade da ganin laifin ummi din ,to meyyesa ummi zatace batason aurenta da ya'ya DEENi  byn ita tasha kisma haka a ranta .
taci  kukanta sosai har sai da taji alamun kanta ya fara mata ciwo ta runtse idanunta  sannan ta kwanta "nan a gefen   bed din ummi tacigaba rera kukanta kasa kasa .

Yinin  ranar tayi shi ne cikin daki hade da  tunanin  DEENi  da kitsima kalar    rayuwar da zatayi a gidan DEENi.
 Da zarar taga  ummi kuwa  take hade fuskarta saboda jin haushin abinda tayi " .
kusan zuwa Maryam uku gidan "Amman zeenat taki saukowa kasa" dan gabadaya takasa samun  sukuni  gabadaya haushin kowa take ji.
,ita kuwa ummi sai binta take da idanu dan ma kasa magana tayi ,  gashi  ranar Sam DEENi ma kin dawowa yayi da wuri sai wajen shabiyu , .


haka ma washegari tun asubar fari yabar gida  ya dai shigo ya gaida umminsa a tsaitsaye.

 ,byn ummi ta idar da sallah ne kafin ta soma lazimi ,  yayinda zeenat ke kwance akan bed , idanunta a runtse tamkar  may  bacci Amman Kuma ba  baccin take ba .
ummi takira sunanta kusan sau uku Amman tayi mata shr alhalin tana jinta.
 ummi ta sake kiran sunanta  tace zeenat nasan kina jina Kuma idanunki biyu Amman kika min banza , hade da ganin laifina .
bakomai yasa kika ga naki yarda da maganarki da DEENi  ba" nasan halin DEENi ciki da bai bashida dadin sha'ani kwata kwata gashi da bakar zuciya tsiya azo ayi auren nan yazo yana  gana miki azaba, .

ni.. nasan abinda nake gudar miki Amman inda kinkiji  ke kika sani , kije Allah yabada sa'a .
Amman ki sani idan akwai wanda zai ji dadin aurenki da DEENi a bayana yake, Amman duk da hakan bazai hanani fadar gaskiya ba idan tazo.
 Kuma shawarata gareki ki rage rawar kai dan idan ya  fahimci haka  zaki sha wulakancin, da karshe  km mutuncinki ya zube a gurinsa.

 ga zaton ummi  zata ji zeenat din tace ta hakura da auren DEENi din ne  Amman sai ganinta tayi ta duro daga kan gado ta zube gabanta  durkushe.
 , taji tace idan dai har kin amince ummi  inshallahu bbu abinda zai faru .

Ummi tayi shr ta tsura mata idanu tana kallonta  ummi tace kina nufin kin amince zaki auri DEENi kennan ? Zeenat tayi shi shr  takasa cewa komai ba sai karyar da wuya datayi , ummi ta sake duban  tace ke..bafa zan yarda da auren nan ba  . take zeenat ta fashe da wani irin  kuka tana bawa ummi hakuri ta amince dan Allah abin ma ya daina bawa ummi mamaki , yadawo bata  tsoro ,.
Cikin kuka  zeenat ,tace ai shi yace yana sona " to ta yaya ke zakice A'a ummi tabita da wani irin kallo tausayi , aranta kuma  tace ya'yan yanzu sam basu da kunya   . wani irin son zeenat din ne taji yana  ratsa ko wani part  na jikinta.
 ga tarin tausayin yarinyar dake matukar damunta ,Amman hakan ba zai sa taji zata iya amincewa da muradinsu ba .
 ta kau da tausayin yarinyar a ranta ta hade fuskarta tamau ,sannan  tace ke dan ubanki akan na hana aurenki DEENi ne zaki ,ta sani gaba da kuka "dan bakisan ciwon kakin ba  ,danma ke shashace ko shi dayace yana son naki" bawai damuwa yayi dake ba.
 tunda har  zuwa yanzu bai kawo kansa gareki ba.
   sai kece zaki wani damu mutane  da kuka akanshi ,cikin wani irin sabon kukan zeenat tace bagashi ke yayi miki maganar ba .
Ummi tace  OK dan yayi min maganar shine may . ni zai aura ko ke  ,da kyar ta iya sausauta kukanta sannan tace ummi  dan Allah  ki amince mana  tunda day har shi ya furta da kanshi".
 ummi taja tsaki ta mike  tsaye tace ni masa, ban waje tun banyi ball dake ba shashar bazan kawai.ta wuce parlour 
tavarta zeenat nan durkushe.
 aiko zeenat naganin haka ta fashe da wani kukan har da shesheka .

Da daddare misalin karfe tara ,DEENi zaune a parlour shida ummi  suna kallo Amman jifa jifa take sako masa  hirar duniya "    shi dai  jinta kawai yake , yayi tamkar bbu abinda ke damunsa Amman shi kadai yasan abinda yake ji aransa' zeenat ta hado masa coffee   tazo har inda yake zaune ta ajiye masa nan kusa dashi ta juya zata bar gurin  ko kallo bata ishe shi ba ballanantana yasan ko ita wacce, hakan da yayi  ne yasa  ummi  taji ba'adadi  aranta . muryasa a kwasashe yace ke.....ta juyo ahankali hade da zuba masa idanunta  shima ita yake kallo da ritattun idanunsa ,yace dawo ki dauki abinki  konace miki  ina bukatane" da sauri  ta zeenat ta girgiza kai, ya kau fuskarsa kmr bashi yayi maganar ba .
 bai sake cewa komai ba ,km  bai  kalli inda ummi ke zaune ba, ya mike kan three site yayi kwanciyarsa " aransa yace akanki zan dinga huci  takaici abinda ummi tamin" tunda tace bazata auramin ke ba.
 nima na hakura da auren naki" sai ta jikaki tay tasha .
kunya ne  hade da tsoro suka taru sukama zeenat rubdugu , taji gabadaya kakafunta sun Gaza daukarta "  ana cikin haka shemah tashigo da sallamarta "kai tsaye wajen ummi ta nufa ta zauna tana gaishe da ummi "ta amsata cikin sakin fuska , .
,sai sannan ta juyo tana kallon  inda zeenat ke tsaye kikam  tamkar an dasata' km sai a lokacin idanun shemah yaKai ga DEENi,dake kwance idanunshi a lumshe.  itama idanu ta zuba masa tana kallonsa  , tana jin wani irin ajikinta  yayinda  gefe daya zuciyarta ke wani irin dokawa da sau da sauri "  shi  km kwata kwata   bai  ma san Allah yayi ruwan mutun  a gurinba " ahankali ya mike  tsaye yana wa ummi sai da safe "a ciki ta amsa masa  dan takaici abinda yayiwa zeenat  " suna hada ido da ummi yasakar mata murmushin gefen baki hade da yakashe mata idanunsa daya  wanda ita kadai tagani   "  da sauri ya haye step  ,.
 yana barin wajen atare suka sauke ajiyar zuciya daga zeenat din har shemah " .
dan har gara shemah ma akan  zeenat din dan ita gabadaya a frigice take "idanunta ta dan juya da niyar satar kallon inda  ummi take  , ai ko take suka hada ido daita ummi kalli zeenat din tana watsa mata harara dan gabadaya tagama  bata haushi .

yana shiga  dakinsa ya fada kan bed dinsa ya jawo system dinsa kennan idanunsa yaKai ga phone dinshi  dayaga almost 12 miss cul da sauri  yasa hannu ya dauki wayar yayi dealing number  daya Gani bugu daya biyu "fk ya dauka   yace ka kyauta angon zeenat"  bukatarka ,ta biya ai dole  kashare mutane. DEENi yaja tsaki mtssss sannan  yace dan Allah  ni rabani da wannan zancen naka na banza" haka kurum kasa mutun a one chance,.
gashi   kaja wa mutun  wulakancin kawai ,fk yace wulakancin Kuma a gurinwa DEENi ya tabe baki tamkar fk din na ganinsa sannan yace a gurin ummi mana.
 to meyya faru inji cewar fk.
 sai da DEENi ya jima  bai yi magana ba kafin daga baya ,yaja wani irin  numfashi  yace ummi fa taki amincewa da shawarka ,sai ma  wani yawo ake min da hankali kmr za'a bani gold.
 fk ya kwashe da dariya yace mutumina kodai ka zurma ne, irin wannan jin haushi haka.
  DEENi yace kai nifa na hakura da yarinyar nan wlh  ,dan gaskiya bazan jura wannan wulakancin ba  .
ga mata nan dayawa a waje suna bina kmr su lashe ne "  fk yace tsaya ranka ya dade ba haka za'a yi ba, bari zamu samu big dady da zance nasan komai zaizo da sauki .
ko Kuma kai me zai hana kasa zeenat din da kanka.
   DEENi ya sake jan tsaki yace maganar bazan  kennan ai inda takaicin yake kennan haba ai kauyancine a wajena    na tsaya  ina gayawa wannan yar karamar yarinyar kalmar  so .
fk yace kaji irin ta ko kana son yarinya Amman girman kanka na neman cutar dakai "DEENi ya katseshi " hade da cewa kai fa dan matsala ne , nasha gaya maka ka daina cewa ina son yarinyar nan, zan dai aureta ne kawai  fk yace Shikenan ajiye wannan zance.
 bari gobe  inshaallahu zanzo muje gurin big dady DEENi baice komai ba ya katse wayarsa .



MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO


Page 11-12


Washegari bai tashi da wuri ba sai wajejen shabiyu na safe yatashi. yashiga, bathroom byn ya fito ne yayi tsaye gaban mirrow yana kallon every part of him ,tsawon lokacin yana tsaye yana kallon kansa ta mirrow kafin daga baya ya janyo wata karamar   stood dake gefe  ya zauna . 
hannushi ya dora a saman fadaden kirjinsa yana shafa kwantaccen gashin kirjinsa  hade da lumshe idanunsa "shi kansa yasan duk matar data mallakesa  matsayin mijinta bakaramin Lucky Tayi ba .

cikin sanyi jiki tamkar macce yasoma    shafe jikinsa da body lotion "  DEENi na kashewa kanshi kudi fiyye da tunanin may karatu , 
 mikewa yayi cikin tafiyarsa ta kasaita ya nufi cikin bedroom din shi dan saka kayan " har  ya nufi kofar dazata kaishi parlour" sai ya tuna ana jiransa dan haka yaja  tsaki  mtssss sannan ya nufe kofar bedroom dinshi  byn yashige tare da cewa koma waye zai tafi idan yagaji da zama dan yanzu baida lokacin kowa  .


Shiryawa yayi cikin wasu hadadun kananan kaya wando blue jeans da  riga longslive" wani irin kyau Allah yayi masa na daukar hankali"  ya isa kan durowa ya kwashi wayoyinsa ya zuba cikin aljihun wandonsa "ya sanya takalmansa mai sawun ciki  ya zura hannushi daya  cikin dayan aljihun .


Shemah ce zaune  a parlour DEENi  take  zaman jiransa "wacce     tun karfe  tara na safiyar ranar   ta dako samamko son ganin DEENI din.

  da farko bedroom din ummi ta nufa , sanin datayi dole zai shigo gurin ummi ,ganin har ummi tagama abinda take  tadawo main  parlour dinta yasa itama tabiyo bayanta , .
Ganin tagaji da zama   kusan 1 hour tana  zaune  zaman jiransa  Amman bata ga alamun. fitowarsa ba  yasa tacewa ummi dan Allah takira mata shi .

 Ummi takirasa  tasanar dashi bai ce  da ummi  komai ba dan kusan  da haushi yatashi . Ita Kuma ganin yayi shr yasa tace mata taje part dinsa .


Koda ya yafito falonsa yaga mutun zaune shi duk tunaninsa FK ne ko cikin abokan aikinsa kallo daya Yayi mata ya dauke idanunsa daga kanta "yi yayi tamkar bai ganta  ya nufi hanyar fita. ta taso da sauri tana kiran sunanshi " cigaba yayi da tafiyarsa danshi a ganinsa bai ga abinda zai sa ya tsaya ba ,.
 ganin saurin bazai mata ba , dan  haka ta kara da dan  gudu da sassarfa har ta cimmasa  ,a  daidai cona da zata kai mutun main parlour din gidan tasha gabansa da sauri  tana sauke ajiyar zuciya hade da cewa dan Allah yaya katsaya magana nake son yi dakai .
 dubanta yayi tamkar bazaiyi magana  sai Kuma yace  meyye matsalarki dani ? Dan ji Yayi kmr ya dauketa da maruka " Kalmar daya fada ne yasa taji zuciyarta ta tsinke "  Tayi wani irin tsalle kmr zata tafasa kirjinta ,.
Tayi shiru tana tattaro kalmar dazatayi amfani  wajen fahimtar dashi abinda ke ranta . 
  cikin sanyi murya yace ina zaton kin manta ko ni wanene shiyasa kika tareni , sai da  ta saita kanta sosai, ta'aro jarumta takara akan wanda take da"  sannan tasamu kwarin gwiwa. cikin marairaicewa murya irin ta masu neman taimako tace dan Allah yaya" kadan bani aron  lokacin uziri ne dani.
 yamata wani irin duban dayasa yanhanji cikinta kadawa sannan yace uhmm ina jinki kuma ki tabbatar da uzirinnaki mai ma'ana ne .
"da idanunta ta amsa masa dan gabadaya  ilahirin jikinta  kirma yake tsabar rudewa datayi har wani gumi take fitarwa na wahala.
 tun ba yau  ba DEENi  yasan shemah nason furta wani abu gareshi Amman rashin ganin fuskarsa yasa taki tunkarsa shi bema san dalilinsa na tsayawa ba  .
 Shi kansa yasan  dole wannan ranar zata zo komai daren dadewa  ".

 ahankali take sauke ajiyar zuciya saboda fargaban da tashin hankali , abinda  zai biyo baya " numfashi taja hade dayin   kasa da kanta dan sam bazata iya kallon kwayar idanunshi a wannan lokacin .
Ahankali    tasoma magana muryata  kasa kasa  cikin in...inna ,tace  daman ..daman..ina son sanar dakai   " ina..ina so.....da hannushi ya dakatar  daita" tun bata kai ga karasa maganarta ba  tare da buga mata wata irin razananniyar  tsawa  wanda yasa ba shemah ba ,har zeenat dake kokarin  fitowa daga dakin ummi zuwa parlour "ta   koma cikin daki da sauri " ta manne da jikin kofar  hade da cewa wayyo... Allahna me Kuma yasame sa  haka cikin tashin hankali ta sake mannewa da jikin kofar .   , hatta ummi dake zaune a falo  say da taji amon muryasa  ,wani irin kallo yake jifarta dashi   yace kina.... me uhmm repeat what u say   ,  lip's dinshi  cikin bakinsa yana cizawa sannna yace  what ar u try to  say ,ya sake jiho mata wata  tambaya, still shr kake jin shemah  ba bakin magana Amman gabadaya ilahirin jikinta ya dauki kirma .
 Cikin isa da takama yace u better keep what'ever you won't say before I sikater you now  jikin  shemah yacigaba   rawa kafafuwanta suka Gaza daukarta dana sani kuwa tayishi yafi cikin buhu ,  ya tsareta da mayatattun idanunsa " murya a kwasashe yace     na sake jin kin Kuma furtamin  wannan bazar kalmar wlh azim  zakiga yadda zanyi da namanki stupid girl kawai.
 ya ja tsaki  ya wuce abinsa ta tsaya nan tana bin bayansa da kallo  ranta a bace  batasan lokacin da Hawaye yasoma zubo mata   tana tunanin yaushe ne zata daina kuka akan son DEENi mutumin da take matukar so tamkar ranta  mutumin da mata ke rububin son shi  mutumin dayake jama mata aji ga shegen kyau da kwarjini " nan ta zube kasa  ta risgar kuka  ahankali hade da sa hunnta duka ta toshe bakinta dasu .

Zeenat dake tsaye jikin byn kofar  dakin ,banda kirma  bbu abinda jikinta keyi , tsabar frigice jin abinda shemah ke kokarin yi' domin taji  duk abinda ya faru tsakanin yaya DEENi da shemah tsabar  tsoro ne ya hanata fitowa ,wani irin kishi ne taji yana taso mata tun daga kan tsintsiyar kafarta  yana bin ilahirin jikinta hade da kashe mata duk wani  gabobin dake jikinta ,  taji a ranta  da tana iya fitowa,. tabbas  da ita kadai tasan  yadda zatayi da shemah, tsinuwa kuwa iri iri  bbu wanda zeenat bata aikawa shemah ba .

 , ahankali zeenat ta sulale   kasa ta dora hannuwanta duka bisa kanta.cikin kuka take cewa  Shikenan ummi tacuce ni  zata kai ni  tabaro "gashi taki yarda da aurena ,da yaya DEENi ga wasu can suna neman   farautarsa .
,ba tasan tana shirin jefa diyarta cikin halaka bane akan tilon danta.
  dan ita yanzu ji take zata iya yin komai akan DEENI  .
Ahankali  Tace ita yanzu yazatayi da ranta , idan Kuma  yace hakura daita fa ?  Taji gabanta fadi 
Da sauri tasoma girgiza kanta tace hakan ma  bazai taba faruwa  ba inshallahu sai ta aure yaya DEENi  mijinta ne ita kadai , .
dan ita yanzu wani irin son DEENi din ne yashigeta na  farat daya ,kmr kar taji ya furta yana sonta ...itama  taji tana maseefar kaunarsa ,  Ita taji ta Gani zata iya rayuwa dashi  akowani irin  hali.
 kawai,a hankali ta sake  ta saki  wani irin  marayar kuka mai ban tausayi  tana furta ummi karkimin haka dan Allah  ..kar min haka ummi ke uwace gareni har da rabi .
dan Allah karki rabani yaya DEENi  wlh zan iya zama dashi a haka , duk munin halinsa ina son shi  " tunda harshi  ne ya furta yana sona ...
 gabadaya  ta rikece da wani sabon  kuka tana sambatu .
 kuka tayi sosai har da shesheka ahankali ta sauko da hannuta bisa kirjinta" ta dafe kirjinta dataji yana mata  wani irin ciwo zuciyarta na  dokowa da sauri da sauri  zeenat ta runtse idanunta dan ita kadai tasan yadda take ji.....

  ta ciki  dakin zeenat ke rizgar  nata kukan ,yayinda shemah da ke  waje durkushe ta nata   .


 Taku yake cikin izza da jin kai da jin shi wani ne yake takunsa har yakaraso ya zauna kujerar da umminsa ke zaune ya dora kansa kan cinyarta "ita Kuma ta'ajiye jaridar dake hannuta tun  soma jin amon muryasa ta daina karatu  datake "ya sakar mata murmushi  gafen baki tamkar bbu abinda ke damunsa ,yace gud morning my first lov ....
ta daura hannuta bisa sumar kansa tare da fadin morning my son yakatashi lfy , ya dan tabe baki sannan yace nut bad  ....
 tace ya'akayi ne son  me kakeson cine akwai dinshi iri iri akan darning wanda   orready zeenat tashirya komai  .
 turo baki yayi cike shagwaba har zaiyi magana " kome ya tuna sai Kuma ya fasa cewa komai " ummi ta tsurawa fusharshi idanu tace kayi shr ya lumshe idanunsa  muje kayi breakfast din ina lura da kai tunda kasoma zancen yarinyar nan bakason zama  ma a gidan  ballanantana Kaci abinci  ahankali ya ware idanunshi akan umminsa sannan yace first lov  na koshi fita ma zanyi yanzu ....



MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO


Page 13-14



Bangane fita zakayi  ba byn ko breakfast bakayi  ba ina fa hankalce dakai fa  duk kwanakin nan bakason  cin abinci,  
ina  zaka ma tukun danaji kace fita zakayi   naga week end ce  yau .ta hade fuska ta mau hade da zuba masa idanunta.
Ya dan yi murmushi gefen baki har  dimple dinsa ya lotsa" kyaunsa ya sake bayyana" ya mike daga kan cinyarta ya zauna sosai shima  yana kallon yanayin  umminsa"  yana jin yadda soyayyar Ummi nasa  fiyye da komai nasa  "yana sonta baya son damuwarta itace duniyarsa sannan itace ke  tattare da duk wani farincikinsa  tana tsantsar " son  shi da nuna masa duk wata kulawar da uwa kadai zata iya yin haka  .

Hannuta yakamo duka cikin nasa ganin yadda ta damu muryasa a sanyaye  kmr koda yaushe  yace am so sorry my first lov muje zanci tayi murmushi tace kai ko hade da  dan dungure masa kai "dan bazata iya fushi dashi "shi kadai Allah yabata " batada. Kmr sa  duk duniya  . Cikin dan daga murya  Ummi   tayi kiran  zeenat .
 DEENi ya  yamutsa fuskar sannan ya langwabar da kai   yace kibarta kawai  "first lov .
ki zuba min da kanki nafi son naci dagareki dan ma banson wahalar dake ne ma  da sabon girki zaki min yakarasa fadar  maganar cike da shagwaba " ummi ta dubesa ta sake yin dariya tace  Allah yashirya min kai  yace Ameen  yana kashe mata idansa .

byn yagama cin abinci duk da bawani abin kirki yaci ba "Amman hakan yatiwa ummi dadi ko bakomai ya dan saki ranshi ba kmr  kwanaki ba"  wayarsa ce ta sake  karade parlour da  kara wanda tun soma cin abincinsa  yake jin kukanta  "Amma ya" share.
 ahankali yasa hannu ya  dauki wayar  yana kallon screen din " sunan FK yagani rubuce yana wayo "tabe baki  Yayi kana ya  manna wayar da kunnenshi , , FK najin alamun an daga wayar yace Yayi angon zeenat da girma "kujerarka . DEENi yaja tsaki yace ya'akayi  ne" sarkin matsala.

  bangaren  FK kuwa shekewa Yayi da  dariya    sannan yace ina waje ina jiranka fa dan  banson nashigo muyi westing time dan nasan halinka da son jikin tsiya " shima DEENi  bay wani damu da shigorwasa ba  dan baya son ummi  tasan inda zashi  ,

  'Umminsa yake kallo har sanda yagama" waya sannan yace mata shi zai fita sai ya dawo  tayi masa a dawo lfy  " mikewa  Yayi tsam cikin tafiyarsa ta kaisata ya nufi hanyar kofar fita ya daura hannushi kan handle ummi takira sunansa ya juyo yana dubanta tace kar kade fa  yayi murmushi yace love you mum ya  murda kofar  ya fice  .

Tsaye ya iske FK shi kadai jingine da jikin motar DEENI hannuwansa rungumeta da kirjinsa DEENi  ya Mika masa suka gaisa sannan suka  wuce kai tsaye gidan big dady.

  FK na gaba DEENi na biye dashi a baya har suka karasa cikin gidan  suka nufin  inda suka san zasu  tarar da  big dady .

 zaune suka hango  tsohon mai tarin shekaru da dattako,sai dai" ya dan manyanta kadan  domin shine "dan"  Muhammad bello khaliyal na farko  Kuma shi ke yanke  hukunci ga duk abinda yataso dangane da   komai" na cikin family  .

Zaune yake  idanunshi manner da  medical glass "da Gani kasan nakara lafiyar ido ne.
 suka karaso inda yake da sallarmasu ,da  fararsa yake dubansu.
 ya ajiye   jaridar daily trust  din dake hannushi gefe cikin sakin"  fuskarsa dauke da murmushi ya amsa sallamar sannan suka gaidashi ya amsa yana tambaye aikinsu" suka ce alhmd .
shr yabiyo baya tsawon lokacin kafin da tsohon ya dago ya sake dubansu.
 da  fk, suka hada ido dan DEENi tun byn gaisuwar da Yayi masa Yayi kasa da kansa yana kallon yatsun kafarsa" tsai Yayi yana nazarinsu duka sannan   yace lfy  dai naganku haka duk da yana ganinsu koda yaushe "amman wannan zuwan nasu  da dan banbanci "sai daya sake maimaitawa, tambayarsa sannan fk Yayi gyaran murya yasoma yi masa bayanin abinda ke tafi dasu.
Sannan  yakara danashi maganar tsakaninsa shemah .
  big dady yaji dadi Sosai matuka da jin haka  duk da yasan kusan irin aure da akeyi kennan a family din .
Amman duk da haka yaji dadi fiyye da kowani aure da'akeyi family din.
Yana murmushi  yace har kun daidaita junan ku kennan ?
fk Yayi tsuru tsuru yana kallon big dady" yayinda   shi  DEENi har zuwa yanzu kansa na soke a kasa" yana jin  duk abinda big dady ke cewa. take  yaji karfin gwiwarsa tayi kasa big dady yace    uhmm kun gama daidaita kanku  ?
still fk ne ya sake bashi amsa  yace A'a sai dai shi DEENi ya sanarwa umminsa" amman bata amince da abun ba.
 big dady ya kira sunansu daya byn daya, a tare suka dago, suka zubawa masa ido.
 big dady yace kuje ku nemi amincewarsu ku daidaita tsakaninku  inyaso sai asan abin yi

 DEENi zaune tamkar an dasa shi ji yayi kmr  kasa ya tsage  ya shige  ciki haka yaji " dan wani irin kunya yaji tamasa rubdugu dan haka  da kyar yasamu ya iya Mikewa  tsaye    suka bar part din  jikisu duk  a sanyaye barin ma fk da bai taba tunanin haka ba .

Suna fitowa daga part din big dady" DEENi yasoma zagin fk yana bude masa wuta , yace daman ka kawo ne a sake nuna min iyakata ?
 ,fk yace haba DEENi ka natsu mana musan abinyi  "wlh ko ni kaina bansa haka zata faru ba dan Allah kayi hakuri ka sausauta  wlh na dauka  komai zai zo da sauki shiya gaji nace muje . wani irin duba DEENi ke jifansa dashi " DEENI yace  ok wani sabon  rainin wayon  zaka sake kawo min .
gabadaya fk yakasa cigaba da magana illa idanu daya zubawa DEENi yanzu yace son zeenat  yake" yace masa sam ba haka ba .
 DEENi ya tsaya sosai suna kallon juna shi  da kf  .
a fusace yace kasan Allah kasan yadda zakayi da haukar, damuwar da kaman nami   dan ban ai keka kabani irin wannan gurbataccen shawar ba.
Gabada ka rusa min komai ,  fk dayaga hassala shima  jin zantuttukan da DEENi ke furtawa .
A harzuke yace  ai bani  nace kazo min da shawarar taka ba " iya abinda naga  zan iyayi  ne" na sanar maka.
Kai tsaye ka fito  kace  daman can kana son yarinyar" bancin haka daga baka shawarar , meye naka na damuwa daita .
 DEENi bai san sanda ya  dunkule hannushi" zai kaiwa fk naushi a baki  ba.
Take   fk ya goce yana kallonsa gabadaya  yanayinsa yagama canzawa sai huci yake kmr mayuncin zaki .
Fk  yace wai meke samunka ne ?
 kodai  kasha wani abu  ne yau , a fusace DEENi yace wuta nasha ba wani abu .
Sai daya furzar da huci mai zafi  sannan yace  kasan Allah sai dai kasan yadda zakayi da tashin hankali daka jefani ciki .

fk yace idan ba  haka ba Kuma fa "DEENi Yayi kyacci yace I will finish you....  ya wuce fuuuuuu kmr wani zaki .fk yabi bayansa da sauri yana kiran sunanshi  yayi banza dashi yacigaba da tafiyarsa da sassarfa har yacimasa ya ruko hannushi "da sauri DEENi ya juyo, ya bige masa  hannu " fk yace haba DEENi meyasa kake daukar komai da zafi ? DEENi yace da fetir ne kasan Allah idan har kana son zaman lafiyarka  dani " wlh ka nemo solution ya wuce nan yabashi . 


Cikin tsanyi jiki zeenat ta mike tsaye  byn taci kukanta ta koshi . bathroom tashiga ta wanke fuskarta tukun  sannan  ta fito' ta murda handle din kofar ' daidai lokacin da shemah ta mike tsaye itama " tasa byn hannuta tana  goge fuskarta " yayinda  wasu ke sake silalowa" wani irin kallon zeenat  ke binta dashi  ,kmr takasheta haka take ji wanda kallo daya shemah tayi mata "tarasa dalilin dayasa zeenat ke mata irin wannan kallon  haka  .

Zeenat  tace munafuka ashe zuwan dakike mana gidan" ba dan Allah kikeyi ba.
Shemah tace lfyr kuwa , bangane nufinki ba.

 zeenat tace zaki gane manufakar banza kawai daga karki sake shigo mana gida tunda kinada manufarki ta zuwa .

 jin haka yayi mugun  hassala shemah, gashi daman tana  tare da  haushin abinda DEENi Yayi mata , hannuta  tacire ta dauke zeenat da wani  mari wanda ya frigita zeenat  .
ai kafin ta sauke hannun  zeenat bata tsaya wata wata ba" ta damki makonshi shemah tace ni kika mara.. kika mareni daga bazaki sake marin wata ba ,wani irin nishi shemah ke fitarwa tana mutsu mutsun kwatar kanta har hawayen wahala take fitarwa ,zeenat tace   ba kukan soyayya kikeyi  ba zan aikaki   abarzahu inyaso kya ji dadi yin kukan da tushe .
Km still tana damke da makoshinta  " tace nufinki kice kina  son yaya DEENi ko .

  Wlh yarinya  karyar tasha karya " da kyar shemah tasamu tasa iya karfinta ta kwace kanta  daga rikon da zeenat ta mata .
 Take suka suma kwokuwa da juna gabadaya  hayaniryasu  ta cika gidan ,a tsorace ummi takaraso gurinsu ta shiga tsakanin" zeenat da shemah wacce har shedewa take saboda kukan dayaci karfinta gabadayansu  fuskarsu  tayi jazir,.
 zeenat na kuka shemah na kuka cikin fushi da bacin rai ummi ke tambayar su abinda ya hadasu fada amman cikin bbu wanda yabata amsa har sanda   " DEENi yashigo gidan ya samesu  tsaye cirko cirko , yaja ya tsaya  yana jan tsaki dan tun shigowarsa yake jin hayaniryasu yanzu ma  ganin ummi ne yasa ya tsaya ,  da kallo yabisu dashi " ummi  na  ganinsa tace yauwa gara ma  daka shigo , ta sanar masa abinda faru ummi nagama fada masa takama gabanta  .

   ai yana gama jin abinda umminsa tace ya fara dauke zeenat da wani mahaukacin ,mari dayasa taji dan guntun fitsarin dake makale da mararta zubowa ,  itama shemah bata nata sannan ya gwara  kansu gabadaya  waje daya jikake gum.......  Bbu wacce tayi kokarin yin kuka cikinsu dan sunan halinsa sarai  bakaramin aikinsa bane ya hada musu da punishment.

 tsawa ya daka musu   yace kowace ta takama gabanta  tun bai sabauta musu jiki  ba , hade da cewa yan iskan yaran kawai  .

Dakinsa ya  wuce yasoma  zariya daga farkon daki zuwa karshe  hannuwansa duka yasa yana balbale botura rigarsa" wani irin zafi yake ji  a zuciyarsa tamkar ana zuba masa barkono , gumi ke tsatsafo masa takoina kmr ba dazu yayi wanka ba " sai daya balle botura rigar ya cire yayi jifa daita ya  fada   kan bed   idanunshi na kallon sama  celling dakin ahankali .
Ahankali yasoma runtse idanunshi  har ya rufesu ruf  gabadaya tunani mafuta kawai yake tabbas indai sai ya tunkari yarinyar nan da sunan yana sonta to wlh ya hakura daita har abada kai auran ma yafasa gabadaya  .


MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO



Page  15-16


Tare zeenat suka jero da shemah" suna kuka saboda  marin da yaya DEENi yayi musu  yashigi    kowannesu" amman hakan bai hana zeenat aikawa shemah da zagi iri iri  ba" har suka karaso  parlour"  inda ummi ke zaune  tayi xuru ...hade da zubawa sarautar Allah ido abin ya faru Yayi maseefar girgiza zuciyarta .  kirasu ummi tayi tana sake tambayar su"  abinda ya hada su fada  haka" alhalin da can ba haka sukeyi ba,.
   shemah ce  tasoma magana cikin kuka   Allah ummi ni bansan nayi mata wanj abu  ba"  kawai ganinta  nayi tafito daga daki" tana wasu abubuwa   ,daga nan Kuma sai ta hau ni da zagi ,.
zeenat zatayi magana ummi "ta katseta  tace  ya isa   banson jin komai daga bakinki  .
 dan ta fara zargin wani abu dangane da abinda ya faru yanzu " ummi tayi musu fada sosai da nasiha mai ratsa jiki .
     tace karta sake ganin sunyi fada da juna  ,  shemah ce kawai ta iya amsawa  tayi wa Ummi sallama ta wuce Amman it's zeenat kishi tattare da kunar zuci suka taru suka tsaya mata a kirjinta hakan yasa takasa cewa komai  .

Ko byn fitar shemah ma  "zeenat  tsaye tayi tacigaba da kukanta tana jin haushin ummi data hanata yin  magana ,alhalin gaskiya tana Gani  .
   yatsun DEENI ne  kwance a gefen  fuskarta wanda ya haddasa wajen dan tasawa , dan gabadaya fuskarta ta canza kala tayi jazir ".
  tun  Ummi  naji haushin kukanta nata  har ta dawo tausaya mata dan tasan , ta daukar kanta wahala ne  in dai akan DEENi  ne . 
  Ummi na kallon yatsun DEENi  kwance a fuskarta take taji wani abu ya tsarga mata " har cikin zuciyarta taji kmr ta zubda hawayen takaici  kiran sunanta tayi  hade da  nuna mata guri zama kusa daita.
    cikin sanyi jiki zeenat ke daga kafafunta inda take tsaye  har ta isa inda Ummi ke zaune ta zauna "kmr yadda ummi ta umarceta  ,

Ummi ta zuba mata idanu  kawai tana kallonta dan abun nata na neman fin karfinta  "tsawon lokacin zeenat tana risgar  kukanta ,batare da  ummi tace mata komai ba ,
  sai da ummi ta gama nazarinta tsab sannan tace duk wannan kukan   na meye haka  ?   

    Kar kice min duk akan son  DEENI kike neman yin fada da er'uwarki . Saboda Allah Ke ko kunya  abinda kika aikata baki ji ba .
"  zeenat tayi shr takasa  cewa komai dan ita kadai tasan yadda take jin zuciyarta, .
Ummi tace meyasa  zeenat , meyasa bakya jin maganata ne ,irin abinda zaki min kennan ko wannan shine kalar tarbiyar dana baki uhmm ?
    kina ganin haka kawai zanki amincewa da auranki da DEENI " kiyi tunanin mana .
koda yake  baki san ciwon kanki ba shiyasa.
' ballanantana" kisan gata neke miki  .

  mutumin da bai san da zamanki ba, bai damu dake ba" ko kallon  arziki baki isheshi ba" shine zaki  zauna  kina westing din  hawayenki akansa takarasa fadar maganar tana takaicin zeenat,.
"    Ummi ta sake maida dubanta sosai gareta tana mamakin yadda zeenat din  ta canza cikin lokacin kadan . Alhalin ita duk iya lokacin ta dauka tare da yarinyar bata taba ganin irin haka atattare daita ba 
 cikin kuka    zeenat tace   ummi  kinki  amincewa da aurenmu  yaya DEENi .
  ai gashi nan ai ...... sai km tayi shr" dan jin kunyar abinda take kokarin son fadi "dan haka tacigaba da  sheshekar kukanta,.

" Ummi tace uhm Ina jinki kikarasa mana ,   tace wlh  wlh idan kika kuskura" kika bari  yasan kina wannan"  haukar akansa " kin shiga uku  da wulakanciinsa " .

 zeenat  ta zube nan  kasa  tana kuka hade da  kamo kafafun Ummi .
tace  dan Allah  Ummi ki Amince da maganar yaya kinji "wlh ni Ina sonshi a haka " kiyi mana addu'a kawai"  bbu abinda zai faru  inshallahu .
  Ummi ta sake  zuba mata idanun tana kallon  sarautar Allah, da rashin kunya irin ta Zeenat , su fa daman  yayan zamanin nan ba wata  kunyace ta ishe su ba .

 ,ummi tace" da bai ce yana sonki ba fa ? 
Ta jeho mata tmyr " data girgiza zuciyar  Zeenat " din" tayi kasa da kanta tana zubda kwalla ita fa ganinta bbu abinda tayi  .
 a ranta ko cewa tayi  ai shima yana sona tunda ya iya furtawa .

 Ummi  ta sake kiran sunanta tace zeenat idan bakiji kunyata" ta matsayina  ta  mahaifiyarki ba " ,
Ai kya ji kunyata ta ummin DEENI .
amman tunda kin nacewa auren DEENi  km kinji" kin Gani  to wlh duk abinda kika Gani  Shikenan , .
da ma  sharadi kozan  amince da auranki dashi .
   Banda zuwa kawo kara  kum  duk abinda yabiyo baya babu ruwana ciki sai dai ki haye abinki tunda shi kika zaba .
   da sauri zeenat tace to....ummin indai kin amince bbu ma abinda zai faru sai alkhari .
Wani irin    kallo Ummi tabita dashi wanda da Gani kasan na tausayi ne. 
  Dan yanzu ta daina  mamakin duk abinda zatayi  .
da murna ta tashi ta koma bedroom  tayi kwanciyarta tana jin dadi Ummi ta amince da aurenta da yaya DEENi . idanunta ta lumshe"  tana jin Yadda soyayyar   DEENi ke sake huda zuciyarta .

Yinin ranar da murna zeenat tayi shi cike  da tsantsar  farinciki ga tarin  tunanin DEENi dake sake mamaye kowane part na jikinta yau tazo mata da abubuwa masu yawa bacin rai da farinciki  .
duk abinda takeyi Ummi na hankalce daita . kallonta kawai take   tana   binta da idanu   .

 Washegari zeenat" ta zaci ummi zata sanarwa yaya DEENi  cewa ta amince"  sai  kurum taji ummi ta share da zance gabadaya , koda dai  da wuri yake fita ,.

 wasa wasa ummin ta share da maganar kwata kwata garakar gabanta kawai take , .
tana jin lokacin da dama idan yaya DEENi ya dauko mata maganar zata katse shi  tace kar ya dameta ya rabu daita .

sai dai abun yana damun zeenat matuka  yadda kullum yaya DEENi ke sake daure mata fuska da wulakanci iri iri. Amman takan masa uziri ganinta killa sai lokacin da ummi ta amince masa ' sannan zai daina nuna ko in kula dayake ,mata.

 shi kansa yaya DEENi baisan  cewar zeenat din tasan da zance ba. kullum dai ya shigo wajen ummi sai yayi mata nacin ,shifa yana nan yana Jirata.
 ita km tace kar ya dameta bayace yafi son Yar jami'a  ba .
"to yaje ya nema  Amman ita sam bazata bashi diyarta ba , .

yana  fita   zeenat ta  matso sosai kusa da ummi  tace ummi dan Allah bakince ,kin hakura  ki amince  tunda na yarda ba .

sai ummi ta dube tana watsa mata harara tace                  sakariya bazan kawai".
       kalli fa ko kallo arziki baki isheshi ba .Amman duk kinbi jin  tsamgwami kanki .dan fitina tsiya  da jaraba , .
  ni duk abinda nake Ina yi ne "dan Kare matuncinki , ba dan Ina kin   aurenki da DEENi   bane .


 tunda yashiga dakinsa bai sake  fitowa ba" sai dai yatashi" yayi sallah kawai  yakoma gado .
 yasawa ranshi, cewa ya hakura daita kwata kwata dan baiga dalilin  da zai sa shi ya dinga batawa kansa lokaci ba .



Kwance yake akan makeken royal bed dinshi ya rufe kanshi cikin alky  blanket mai matukar taushi ,.
bacci yake Sosai hankalinsa kwance ya rufe  koina na jikinsa banda fuskarsa  saboda yanayin unguwar su mai dauke da sanyin ni'ima ,.

 ahankali ta bude Kofar dakin" kwance ta ganshi, yana sharar  baccinsa ,sai yanzu hankalinta ya kwanta gangar jikinta yasamu natsuwa , kusan kwana biyu kennnn rabon data sashi a idanunta,.

 ahankali take daga kafafunta har ta isa inda yake,. kwance
   idanunta ta   zuba masa" tana kare ma kwakkywan fuskasa  kallo yadda tayi kyau tana fidda annuri na musamman .
Ahankali   ta lumshe idanunta " tana jin wani irin tsanyi nabi jijiyoyon jikinta.
Ahankali ta bude idannuta suka sake sauka akan beautiful face dinshi ,.
  fuskarsa ta kurawa ido  har wani kyalli kyallin  kyauwu take fitarwa  , cikin rawar hannu takai hannuta  gefen fuskasa ta dan  tashafo .  wani irin taushi taji wanda ya  sake dulmiyar daita a duniyar kaunarsa .
Take taji koina na jikinta ya mutu sai wani yammmmuu take ji.
 ita kanta tarasa dalilin dayasa take jin  haka ajikinta .
   ganin bacci yake sosai  yasa ta juya ahankali tabar dakin cike da shaukin soyayyar DEENi  dama Ummi ce "tace ta dubashi    dan har lokacin fitarsa aiki na neman   wuce .

 Koda ta sanar da Ummi cewar  bacci yake har yanzu, yasa ummi ta nufi dakin" dakanta kusa dashi taje" kai DEENI sai data kira sunanshi" kusan sau biyu" sannan  ya dan bude gengerous eyes dinshi ya kalleta dashi "tace  lafiyarka da har yanzu   dabaka tashi ba , .
 tacikin blanket din ya dan yi Mika hade da salati sannna ya dan gyara kwanciyarsa yace lfy first lov ,natashi har nayi sallah " to bazaka aiki bane yace zani.

 Ummi tace Ina jiranka idan kagama.
 ya amsa mata da kai kawai .
a hankali  ya zame jikinsa daga cikin blanket din ,  daga sai dan gareni wando Mika ya sake yi yasa hannunsa ya gyara jijiyarsa dake mike .
Sannan ya shiga bathroom,.
duk da yamakara hakan bai sashin yin sauri ba, wanda normally haka yake da sanyi jiki .
 wanka   yayi, ya fito. ya shirya cikin kakinsa da suka dace da surar jikinsa,  har ya murda handle din  kofar "dazata Kai shi parlour ya tuna Yayi mantuwar wasu files  a dakin baccins" dan haka yakoma ciki daukowa      . 

Tsaye take a bakin kofar dakinsa tafi kusan minti biyar a wajen tana saka dawarwara yadda zata sake  shiga  Bedroom din sa.
 ummi ce tasake aikota .
Ta dubashi dan taji shr  har yanzu .
 tana son tayi nocking Amman tsoro da fargabane  suka hanata .
 daidai wannan lokacin DEENI ke shirin fitowa daga part dinsa . ta daura hannuta kan handle din kofar.
 ai agigice cikin matsanancin tsoro tasaki  wani irin kara  da tasa DEENI , tushe kunnuwanshi " da duka  hannushi "ai batasan sanda  ta fada saman fadaden kirjinsa ba .
hade da runtse idanunta  gam dan tsabar jin  tsoro , batasa abinda zai mata ba Jira kawai take taji saukar mari dan gabadaya tagama frigicewa.
 Amman abin mamaki sai taji sabanin haka.s shiyasa  tasaki jiki ta sake narkewa a fadadden kirjinsa tana shakar dadeden kamshin turarenn jikinsa mai birkita mata tunani "a duk sanda ta Shaka  .

 wani irin ya dinga  ji ajikinsa,  yrrrrrrrrrrrrr.... yrrrrrrrrrrrrr  abinda bai taba faruwa dashi ba  kennan" jikinsa ya hadu da wata macce" shi tunda yake ma  ko hannun macce bai ta ba rikewa ba ballanantana yakai ga hada jiki .
Ya  dinga jin wani irin wani irin  a gangar ajikinsa.
   gabadaya tsigar jikinsa suka mike tsaye , yaji da zai iya " rungume zai yi kawai zaiyi .
 ko zai ragewa zuciyarsa radadi da ciwon dayake ji.
  Amman Ina... Sam bazai  taba iya aikata hakan ba .
ganin yadda tayi lamo ajikinsa ne yasa, cikin takaici  ya bambareta daga kirjinsa cikin tsanyi jiki,
 tsayuwa ce ta gareta , zuciyarta ke neman tarwatse tsabar tsoro da rikincin data tsinci kanta ciki.
,ko ta kanta bai bi ba ya tsuke fuska yana kallonta  ,itama idannuta ta zuba masa  ko kiftawa batayi.
 ga wani irin tsoransa dake lugudar  zuciyarta.

 ahankali muryasa a sanyaye yace malama ki daina min "irin wannan kallon na munafurci .
in ba haka na kwakule idanun rashin kunya tsaki yaja hade da bin   gefenta yazagayeta ya wuce kai tsaye part din umminsa yashiga" sai dai bai ganta ba,.
 dan haka ya wuce main parlour 'dan yasan tunda bata dakinta, tana can .

 zaune yasameta tana yin breakfast fuskarsa a dan sake yakarasa har kusa daita ya zauna   yace gud morning my first lov, ta dubeshi fuskarta dauke da murmushi tace morning dear ,kata tashi lfy girarsa ya dage mata.

 cikin tsnayin jiki  zeenat  takaraso wajen, kallo daya DEENi Yayi mata yasa  ta canza hanya batare da ta sake kallonsa  , kan wasu kujeru dake ajiye a gefe  ummi tabishi da kallo batare da tace masa komai ba  " da kanta tayi savice , din shi ,shi km sai wani zuba mata  shawaba yake , .
  coffee kawai ya iya  yasha, ya mike tsaye  cikin hanzari sakamakon wayarsa data dauki kara yana dubawa yaga  ogansa ne daga wajen  aiki  .
 dan haka yayiwa umminsa sallama  da hannushi ya fice    wayar manne da kunnenshi  .

 Zeenat data  zuba tagumi ,Da hannu biyu  tabi bayansa da kallo har yabar   gurin idanunta na kansa , itama ummi  data dauke idanunta daga kan DEENI "zuru tayi tana kallon Zeenat din , tana girgiza kanta .
 waskewa zeenat tayi hade da sakarwa ummi murmushin dole ummi tayi mata dakuwa da hannu .


Byn DEENi ya gama amsa wayar oganshi ne yana zaune  cikin mota wayar  fk yashigo  " yasa hannu ya dauki wayar ya duba ganin fk ne yasa ya maida wayar ,mazauninta .
Yakirasa yafi sau gomasha daya Amman yaki pic sai  a karo na shabiyu ne  ya danna wani abu "sai ga muryar fk radau  yakarade koina a motar , hello.... hello DEENi kana jina   .... 
Yayi shr  yaki yin magana,sai ma  cigaba da yayi " da direving dinshi .
fk yace haba DEENi ya kana jin zaka min shr. "duk  fa" maganar bata kai haka.
 afusace DEENi ya katse shi  yace maganar tafi haka har ta zarce haka  a waje na.
 km wlh wlh karka kuskura, ka tako inda nake  da sunan kasan ni ai bansa cewar da kungurumin ,dan iska nake zaune ba.
 fk yayi murmushi yace Allah dai ya huci zuciyarka ,dan shi.
 bai fiyye fushi ba" kwata kwata ma bayason duk wani abinda zai kawo masa tashin hankali .
dan haka yayi tabawa DEENi hakuri hade da bashi baki .
 DEENi yaja numfashi  ya sauke ajiyar zuciya . hakan yasa fk ya gane cewar ya sauko kennan fk  yace to yanzu yazamuyi da maganar da  big dady yace.
 DEENi ya tabe baki yace ya dai zakayi dan ni tuni na hakura da wannan yarinyar , karma ka km yimin wannan bazar zance.
 daidai da yakaraso wajen aiki ,ya katse wayar fk batare daya tsaya  ji mai fk din zai km ce masa ba .



MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
   AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO



Page 17-18


 Wata daya kennan  fk yaji "shiru DEENi bai km yimasa zance maganarsa da Zeenat ba musamman" yazo gurinsa  dan zance daman Kuma sun dade basu ga juna ba" sai dai sukan yi waya lokaci zuwa , lokaci  dama ya kirashi a waya cewa yana nan zuwa .


Byn sun gaisa fk yace friend har yanzu ban sake jin  batunka da yarinyar nan ba .
 deeni ya gyara zama ,hade da  yaja tsaki sannan ya lumshe idanunsa dan takaici da Haushi  maganar .
 ya zubawa fk ido yana kallonsa kawai domin  rasa me zaice masa Yayi   ,tsawon lokacin suna zaune a haka sannan fk yace friend hakuri zakayi dan Allah  ba wai Ina son dawo maka da hannun agogo baya bane .

 Amman idan maganar danayi  akan Zeenat ya bata maka rai, kayi hakuri.

 ahankali deeni ya furzar da iska mai dumi ya miko hannushi ya dafa gwiwar fk , Friend   ban tasamun abinda ya bani matsala kmr maganar yarinyar nan"  abin haushi duk lokacin da nayi kudirin hakura daita sai nakasa .

Kullum addu'a ta Allah yaye min ita daga raina Amman abin ya faskara ko son yarinyar ne yakamani "oho " fk yayi murmushi yace  lallai sonta kakeyi Allah yasa itama ta soka haka .

DEENi ya gintse fuska yace Ina ruwana daita first lov ce kawai damuwata ,data amince da yanzu an wuce gurin Amman tsohuwar nan sai cewa take zan cuci Yar mutane ita bazata bani  Yarinyar karama ba inzo Ina bata wahala fk yace sanin halin ka tayi dan kai din bana wasa bane  kana raina yarinyar ne dayawa shiyasa ummi batason aura maka ita wani lokacin sai inga kmr da gaskiya ummi DEENI yayi masa wani kallo dan ni bason iskanci idan abinda yakawo kennan kana iya tafiya .

Fk yace zanje in sameta da kaina kar damu .
deeni yace dama kabar ta kawai dan ko kaje ba amincewa zatayi ba.
 nasan halin first lov , da zata yarda da tunin ta amince .
na dai fada mata cewar ni na hakura dayin auren gabadaya" inda tagaji da zamana haka tasan abinyi .

Fk yayi ta dariya tare da xolayar DEENI" friend ka dai shiga da yawa da ka'ajiye duk wani girman kai ,ka dinga kiran yarinyar  kana janta ajiki ,idan ummi taga haka zatafi yarda da gaske kakeyi "Amman kai kullum fuskarka a hade  kmr hadari .


DEENi ya tabe baki, kasan Allah bazan taba iya kiran ko wace irin  yarinyar bace, da sunnan zance koba Zeenat ba. kai ma abinda kariga kasani ne "bansa ta Ina zan soma ba   ,nifa bana kawo Zeenat a raina ,in dai  first lov ta yarda " to tayi hakuri ta aureni kawai   dan ni banda wani lokacin ya mace . dan ma taji dadi ta samu miji irina  ,yakarasa fadar  maganar yana jan tsaki fk yayi dariya yace friend banda yabon kai fa , DEENI ya dan yi murmushi gefen baki har dimple dinsa ya lotsa  kai ma  kasan gaskiya fada ne dai kawai  bazakayi cikin  "nida ita wazai taimaka wani ? 

 Bbu abinda zata nuna min " fari ne kawaiya ceceta  "  wanda kai kasan ko man bleaching takara bazata taba kamo nawa ba "fk yace ai shiyasa ka daurawa kanka girman kai al'amarin mata" km duk da kafita kyau ita zuciyarka ta zaba  ,ta zama abokiyar rayuwarka "  zanyi  maka iya bakin kokarina ,.

DEENi yabishi da kallo yace sannan ya maida bayansa ya jingina  da kujera , dama kabar, damun kanka akan zance yarinyar nan , wai dole ne  sai na aureta   ,fk yace tunda nace zanyi kabarni mana ,na gwada sa'a ta ko ummi zata yarda . DEENi  ya daga kafadarsa alamun shi yasani ,sannan yace tunda ka nace  kaje din Amman idan  labarin ba may dadi bane ,karka zomin dashi ba  ,.

 

Kmr yadda fk yayi alkawari   haka ce takasance    yasamu ummi da zance  byn sun gaisa ne   yace daman akan zance deeni ne  da Zeenat" ummi najin haka ta canza fuska " har tasa karfin gwiwar da fk yazo dashi " yayi kasa.

Ahankali yacigaba" dan girman Allah ummi kiyi hakuri ki amince da auren nan "saboda dukkansu naki ne a ganina wannan abin farin ciki ne  .
Ummi ta sake tamke fuskarta Sosai tace  faruk Ina matukar ganin kimarka da mutuncinka  zai fi kyau kabar zance nan" bana jin cewar zan iya amincewa .
  fk yayi shr yana tunanin yadda zai bullo mata  can dabara tazo masa yace to Shikenan Amman naso ki Amince domin deeni yana cikin wani hali  nason yarinyar  nan. daidai lokacin da Zeenat ta dawo daga gidansu Maryam tanac kokarin shigowa  parlour ummi  .
   ,karaf zance ya fada cikin kunneta cak taja ta tsaya jikinta ya dauki kirma .
Fk yace ummi  kin san halinshi baya daga cikin mutane masu magana biyu  ,ya min ransuwa  ba zai tabayin  aure ba ,in ba Zeenat ba ,km duk duniya ita ya Gani yake so.

 zamanshi haka nasan yana damunki ummi tace in duk duniya Zeenat yagani  yake so ita  Zeenat din ya sameta yaji ko tana son shi ? Ko haka kawai dan shi yana sonta" zan dauke  diyata ta nabashi batare da ya nemi amincewarta ba.

Nifa bazanyiwa diyata auren dole ba dan kawai Ina son na faranta masa rai ba .

Daga inda Zeenat ke tsaye tana jin komai" take jikinta ya dauki  yacigaba wara  har wani zazzabi zazzabi taji yana neman rufeta , kafafunta suka Gaza daukarta sakamakon kirmar da suke , nan ta sulale kasa tana jin yadda gabanta yashiga faduwa da sauri da sauri ,  tarasa dalilin ummin nakin aurenta da yaya DEENi .
alhalin tasan yana sonta har haka .
 ,to hakan na nufin ummi tafison yaya yaje waje ya aure wata ,  sabanin ita kennan . 
kawai batayi aune ba taji saukar    hawaye nabin kuncinta .
   Da sauri tasa Hannuta  ta dangwalo hawayen dake bin fuskarta, tana kallo ta girgiza kai  kawai tana jin tamkar an diga mata dalma ne zuciya ,.
Ta runtse idanunta  ahankali muryarta cike da rauni tace meyasa ...
Meyasa ummi kike son ki ruguzamin rayuwa  please ummi ki amince na auri yaya DEENi  , Ina sonshi har bansan iya kar kaunarsa a zuciyata ba " bazan iya rayuwa in bashi ba 

Fk ya fahimci abinda ummi take nufi  shiyasa yace ma DEENi ya dinga kiran yarinyar suna hira. ko km yajata ajikinsa . Ta hakan ne komai zai zo da sauki , fuskasa dauke da murmushi yace ummi idan dan wannan ne ,karki damu , duk wannan me sauki ne zamu tuntubi yarinyar muji , idan bata amince ba Shikenan .


Ummi tace da dai yafiye muku" ba ku tsaya girman kai ba, fk ya sake yin dariya yana girgiza kai  yayi mata godiya ya mike  .

Jin  da Zeenat tayi fk  yayiwa ummi sallama ne  yasa tayi hanzari  mikewa da sauri tashige bathroom din parlour din dake manne da falon nan ta fashe da wani irin kuka ita kam zuwa yanzu tafara jin haushin ummu  .


Fk na fita yakira deeni bugu  biyu ya dauki wayar , fk yace friend kafara da bani goron albishir ,cikin yanayi na ko in kula deeni yace kada kace min first lov ta saurareka ? 

Fk yace ta saurareni km  inshallahu zamuyi nasara da alamun ummi ta amince  ,.
 duk yayi masa bayanin   yadda suka yi da ummi ,
 yakarasa zance  da ummu   ta nuna tanason asamu yarinyar a nemi amincewarta .....
  DEENi yayi shr sannan yace to ai wannan  shine mai wahalar dan bazan taba iyawa ba , fk yace wai kai tsorota kake jine ko yaya ?
 ,ai take deeni ya hassala a fusace ya aiko masa da wata irin uwar ashariya " wanda yasa fk yayi  sauri  cire wayar daga kunnenshi ,ya dan duba  sai daya tabbatar daya yana kan layi. sannan ya mayar yacigaba magana" haba friend meyasa kake saurin daukar zafi akan abinda bai yakawo ba .

 bance dole sai kasameta da kankaba ,ni dakaina zanyi komai.
  sai Kuma ya sausauta yana jan numfashi yace ai kai ne da wani zancen baza.
 naji tsorota akan me ,raini ne kawai banaso , yanzun dai kai kaje kasameta  kuyi magana  da in ni nakirata bafa ra'ayinta zanjira ba. umarni kawai zan bata   fk yace Shikenan sai na nemeka  .

 Zeenat  zaune gaban TV dake manne a parlour su ta hada uban   tagumi ,hade da  zubawa   TV idanun . Kallo daya zaka mata , kasan kwata kwata hankalinta bai kan shirin da'ake gabatarwa .
gabadaya tunaninta ya kashi gida biyu .

ga tashin hankali ummi taki amince wa da aurenta da yaya DEENi. ga kamil  da yasako, gaba da zance yanason kai  maganarsu gurin big dady, .
hankalinta a  matukar tashe yake  .
har ummi   takaraso inda take zaune  taba tasani ba".
 ummi  ta  zuba mata idanu kawai tana nazarinta sannan ta numfasa  sai data kira sunanta tukun ,  Zeenat tayi saurin juyo a frigice tayi firgigib tana duban ummi .
idanunta ta  zubawa ummi kmr wata mara gaskiya " ummi tace wai ke wace irin  sakarriyar yarinyar ce" da kwata kwata baki san ciwon kanki ba "kalli ummi ta nuna jikin Zeenat da dan yatsanta , dube yadda kika dawo ,duk kinbi kin sakama kanki tunanin banza ji yadda kika koma  duk kin tsotse kin rame dan jarabar tsiya ,anason a karemiki mutuncinki ,kinki natsuwa, kisan haka  .
sai kiyi tayi ai.

 cikin haka fk yayi sallama yashigo ya zauna akan kujerar one site  yana   gaida ummi 
Ta amsa masa  fuskarta a gimtse da tasan kwanan zance "  Zeenat ma ta gaisheshi tsam mike taje takawo masa abin sha  .

,ummi ta tabe baki tana hararata dan takaici  sannan ta sake kai dubanta ga fk  din" tace   DEENI fa yana dakinsa .
   Fk yayi murmushi yace ai  ba gurinsa nazo ba ,jin haka yasa  ummi tashare   , ta cigaba da kallonta , gabadaya  parlour ya dauki shr tamkar babu mutane a cikinsa  baka jin motsen  komai sai karar TV .
Zeenat kam kamewa tayi tashiga hankalita dan motsi kadan  , ummi zatace tafiye   rawar kai .
 ganin shr yayi yawa     yasa ummi ta mike tabar gurin ta nufi dakinta . Parlour  ya saura daga Zeenat sai fk .

 yana Ganin  ummi tashiga dakinta yasa ya  juyo  yana fuskantar Zeenat yace sister wajenki nazo fa  .   tace to Allah yasa dai  lfy yace lafiya  nasan zakiyi mamakin zuwa na ?

Tace bawani mamaki killa akwai abinda kake son nayi maka ne .
yace ba wannan bane nazo ne dan nasanar miki da wani abun alkhari koda yake bansan yadda zaki dauki abun ba.
  tsab Zeenat tagane abinda yakawo shi gabanta taji ya tsananta faduwa ,.

fk yace deeni ya duba duk cikin en'mata dake cikin  family din nan.
 yaga bbu wacce tayi masa km tadace dashi sai ke .
Zeenat ta zaro idanu waje kmr da gaske  ta nuna kanta    tace ni fa kace yana so...


Fk yace bawani abin mamaki bane , Dami kika tsinta a kala ,a ranta tace maganar ka gaskiya.
  fk yace yanzu me kika gani idan kin amince , magana zata wuce gurin big dady kai tsaye  batare da bata lokacin ba .
ta tabe bakinta kmr batayi murna dajin zance ba  ,  sannan tace gaskiya kagaya masa kawai yayi hakuri  dan ni  narigada na tsaida wanda zan aura ,.

fk yace waye shi km a ina yake   km kin kai maganar wajen big dady ne ? Duk alokaci yajero mata tambayar ,tace Ko daya muna dai shirin yin haka fk yace yace shi din wanene tace wani ne acikin family dinmu yake humm yace  inbaki shawara ta daga masa kanta" zan so ki dakatar da koma waye.
 dan kowa zaki aura ina tabbatar miki ba zai taba kai kmr DEENI ba .

ke kanki kinsa samun irin su DEENi sai an tona. zakiyi alfahari samun  mijin kmr sa "mata dayawa suna ,sonshi ban sani ba kodan  sun fahimci qualities dinsa ne .
sai km yace amman bazan takura miki ba in kinga bakison shi Shikenan  .
ta kalleshi  a shashance hade da wani irin salo sannan tace nifa bance maka bana son shi ba  na dai kawai kace masa na  tsaida wanda zan aura .
Kaga  yanzu idan na canza raayina da sauri haka shi saurayin nawa  bazai  dadi ba .
ka dai bashi hakuri Allah ya hada kowa da rabonsa na alkhari .

fk yayi shiru yana cizan yatsa hankalinsa yasoma tashi  "karfa yarinyar nan ta kwafsa masa yazaci yana mata zance zata amsa da murna  ya fadi haka a kasan ranshi.
can km yace to ni yanzu mekike son nace masa ? 

 Ta sake tabe baki yace Kafada masa gaskiya kawai , yace ba za kiyi tunani akai ba kafin ki yanke hukunci ,ko km kuje kisamu wanda kika san kin amince mata km tasan deeni  din sosai tabaki shawara akai, Zeenat  tace naji zanyi tunanin  .

Fk Yace Shikenan zan sake  nemeki zuwa  gobe naji abinda kika yanke akai , tace badamuwa .

Byn ya tafi, ne tashiga dakin ummi  tana murna cike da farincikin burinta yakusan cika ,fitowar ummi kennan daga bathroom aiko tana ganin yanayinta da alamun tace musu ta amince  ,take ta sake daure fuskarta , ta  rufeta  ta fada, ai gashi nan saboda baisan darajarki ,da kimarki ba sannan  bai dauke ki da mahimmanci ba ,yakasa zuwa da kansa sai  abokinsa ya turo miki nasan  jikinki na rawa kika   amincewa ko ?.

 Zeenat taaba fuska tamkar zata saki kuka tace nifa ba wani rawar jikin danayi   .
  ummi tace wlh kiyiwa kanki fada, akan sakarcin da kikeyi ke kmr ba macce ba .
 sam bawani  jan aji irin na sauran mata .
 Zeenat ta sake bata rai sosai .
 ummi tace gaki nan ga deeni ,inda shine nabarki dashi ya isheki wando da riga .


A waya DEENi yaji duk yadda sukayi ya dinga mamaki wai wannan yar yarinyar ce zata ce sai tayi shawara to dawa zatayi ?  Km ita ce wa ?

Fk yace itace mace deeni yace dan Allah  malam imin shiru shiya sa fa kaga bazan iya kai kaina gareta da sunan Ina sonta ba bare tamin salo . Nan km yau zazzagawa fk maseefa yana Ai shi  yaja masa duk wulakancin da'aka masa fk yace kwanta da hankalinka kavarni daita kawai nasan zata yarda ma kawai dai itama so take ta nuna mana itama macce .
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO


Page 19-20



 Shiyasa kaga bazan iya kai" kaina gareta ba  da sunan Ina sonta , bare tamin salo .

Nan km yayi ta zazzagawa Fk maseefa hade da  cewa ai  shi yaja masa duk  wulakancin da'aka masa .

Fk yace kwantar da hankalinka   kabarni daita kawai ,nasan zata yarda ma ,.
kawai dai itama so take ta nuna mana ,itama macece , nasan jan aji ne kawai na mata Amman ita din wa dazatace bata sonka ,Ina rai inshallahu  zamuyi nasara.

Cikin fushi da jin haushi deeni Yace in taki yarda ka kyaleta kawai , yarinya sai kace wata  gold sai wani yawo akamin da hankali akanta, yaja tsaki hade da kashe wayar batare daya sake jin abinda fk zai ce ba .


Kwana deeni yayi da tunanin hade  da zullumi halin da zai tsinci kansa idan  yarinyar nan taki yarda dashi, duk shi Gani yake ba sonta yake ba. zai dai yi aure ne kawai saboda umarnin umminsa, bugu da Kari ma, bazai iya kaskantar da kansa wajen mace ba ballanantana har ya kai shi ga furta kalmar so.

Har zuwa wayewar garin ya cigaban mamakinta  ganinta yake , tamkar yau aka haifeta, sannan har zuwa yanzu kallon karamar yarinya yake mata,  ashe tasan abinda take yi ,uhmmmm  uhmmmm ahankali ya dinga sauke ajiyar zuciya, wai zatayi tunani akai ya sake tunawa da kalmar data fadawa fk to da ko da uban wa zatayi tunani ya furta hakan a kasan rashi .


kwance take akan bed din ummi  Amman ba bacci takeyi ba ,hannuta rike da wani  English novel  mai suna ,mumy why sanye take cikin kananan kaya, pencil  jeans da riga iya gwiwa a natse take karatunta dan tana jin dadi labarin yarinyar ciki litattafin ta birgeta kwaira ,ta yadda take kokarin kwatarwa kanta enci saboda mahaifiyarta ta hanata auren saurayin da take son ..
Cikin isa da kasaita  yashigo dakin , tana jin motsen bude kofa Amman tashare dan batason abinda zai  katse mata karatunta .

Jin kamshin turarensa yasa ta dan dago idanunta suka sauka akansa , ganinsa yasa  ta dan mike daga kwanciyar datayi, tasha jinin jikinta   bata san meke sata jin yawan  faduwar gaba ba, a duk sanda taga yaya DEENi .
 ta gaidashi batare daya kalli inda take ba , ya amsa mata a ciki ,km  cikin isa da takama sannan  a takaice , tamkar dai yadda yasaba dan baya son duk abinda zai  sa magana tayi tsawo atsakaninsu . 
sai dai ita kam tsintar kanta  tayi da  zuba masa idanunta, tana binsa da  wani irin mayyen kallo , cikakken namiji ne sosai mai ji da kansa , ko a tafiyarsa zaka shida haka.  gabadaya bbu wata  alamun ragwanta atare dashi .kana ganinsa zakaji ya birgeka ,daman aikin da yakace shi kennan wato  jami'in tsaro .

Har suka gaisa da ummi dake tsaye fitowarta kennan daga bathroom  ya juya da niyar barin dakin,  idanun Zeenat na kansa tamkar zata ya dawo ya zauna kada ya fita saboda tsoron masu farautarsa ,takasa dauke idanunta daga kallonsa take taji wani irin masefaffen kishinsa ya diram mata zuciyarta ta dinga rawa bata idanunta a kansa ba sai data daina ganinsa  .

Ummi tabita da kallo tausayi  tace inkin gama kallon nashi sai   ki tashi ki hado masa abinsa ko kawai soyayya aka iya ba'asan tattali ba , Zeenat ta dan turo baki tace ni dai ummi kwanan bansa abinda na miki ba  komai nayi sai kin min fada, ki dinga ganin laifina , nifa bashi nake kallo ba , ummi tace eh ai nasan bashi kike kallo ba kuruwarsa kike kallo jairar yarinya kawai ni tashi ban guri  .

 Washegari 

Zeenat tarasa dawa zatayi    zance yaya DEENi taji dadi kuma yaba shawara tamkar yadda zuciyarta ta aminta dashi  ,ganinta duk wanda ta nufa da maganar baza tasamu goyon baya ba ,kmr dai yadda ummi tayi ,
Maryam ce ta fado mata a rai ,dan haka tashirya taje har part din su.

Tana shiga part din idanunta  sukaci karo da fuskar data tsana a halin yanzun arayuwarta  ,kmr ta juya ta koma haka taji , shemah ta hango zaune akan three site  suna hira da Maryam  take taji wani iri abu ya caki zuciyarta .


 ganinta yasa taji tamkar an soka mata kibiya ne a kahon  zuciya taja ta tsaya takasa karasawa inda suke dan baza juri zama a duk inda take ba , ganin haka yasa itama  shemah ta mike ta fice Tama bar part din gabadaya . Da kallo Maryam tabi kowanne su 
Ahankali Zeenat takaraso tasamu waje kusa da Maryam din ta zauna zuciyarta a cunkushe , tsawon lokacin takasa cewa komai  , Maryam tace wai yana ganki haka ne ? Cikin nishadi Maryam ta soma janta hira  har  Zeenat ta sake Sosai    
 Daga nan ta labarta mata duk halin da'ake ciki ,.

Maryam ta zaro idanu waje  tana mamaki tace kai da gaske kike ,to Ina girman kan nasa km?
 Zeenat tace yana nan bai je koina ba" sai ma abinda yakaru ,

 Maryam tace in fada miki gaskiya,zeenat ta daga mata kai  alamun eh "ki amince kawai" karkiyi wasa da damarki domin mata dayawa suna can suna  neman miji irin yaya DEENi 
basu samu ba.  

amman idan kin yi saken da kika  tsaya  yauki ,wai ke jan aji   ,kya zo daga baya kina nadama  dan irinsu tsada ne dasu   ,.
kin dai san halinsa da maseefar zuciyar tsiya.
maryam takarasa zance da 
Uhmmmm .. Ina ma ni Yace yana so ......

jin haka yasa take  Zeenat ta hade fuskarta tamau , hade da zabgawa  Maryam din wata uwar harara tace kefa Yar wulakanci ce  bangane dama ke yace yana so ba Maryam tace ke nifa da wasa nake dan baga kmr kin fara hassala Zeenat tace  ,wani irin wasa wannan, nifa  banson shirme bazan.
 Ko kema zaki shiga layin  shemah  ne?

 Maryam tayi murmushi  tace bada dai Ai tsakaninmu bbu haka   yauwa naji ance ma  kunyi fada da shemah Kwanaki ?

    wai may ya hadaku fada  ne , Zeenat ta tabe baki tana sauke ajiyar zuciya sannan tace shirme tamin irin naki .
nan dai ta zaiyanewa Maryam komai ,suka tafa suna kyalkyale dariya Maryam tace kai tawan kina wuta   , Zeenat tace Ai ni bata wasa bace  ban daukar raini tuni nagama daita duk da batasan abinda tamin ba har yanzu.

Maryam ta sake bata hannu suka taba, tace   baki da  kyau fa" sai dai  idan ba'a tabo ki ba.
 Maryam tacigaba tawan  ki Amince kawai da auren nan  musha biki amman fa zakisha fama da wannan miskililin   ,Zeenat ta sake yin murmushi tace indai zai cigaba da sona kmr yadda yake yi yanzu Ina ruwana da wani miskilancinsa can yakarata  , ai abinda yafi ma birgeni dashi kennan.
Amman nasan  wuyarta dai ayi auren da sannu zai rage duk wannan jin kan nasa  .


    Zeena ta kagu dare yayi  saboda cewar da yaya faruk yayi zai dawo .
 ,tun tana  Jiran zuwansa har ta fida tsammani  dan  tara  tayi   gabadaya hankalinta a matukar tashe yake,t unaninta  kar dai ya deeni ya hakura daita kmr yadda tace abashi hakuri.

 zuciyar tashiga rawa tamkar zata  tsinke ta mike tsaye  cikin sanyi jiki tasoma zariya duk dai ummi biye daita da kallo can Ganin goma   tayi yasa ta nufi  dakin ummi tana shiga  ta fada kan gadon   tana zubda kwalla,.
 ahankali tace Allah  Allah kasa ba hakura yaya DEENi yayi ba ,.
dako na cuci kaina da kaina tashiga zubda hawaye baji ba Gani tana jin zuciyarta na neman taewatsewa tace Allah ka tausayin ka jin kai na ka mallakamin abin kaunarta deeni ina sonka deeni tunda ka furta kana sona nakasa samun sukuni dan karkace ka fasa kuka take sosai hade da sambatu ,,.

  Shadaya daidai  ummi tashigo ta dubi inda Zeenat take kwance taga alamun kmr bata jin dadi karasowa yayi tace ke lafiyarki kuwa  da kyar Zeenat ta iya bude bakinta,t ace  kaina ke min  ciwo ummi tace shine zaki zauna kina kuka ,tayi mata sannu taje takawo mata magani .

Wasa wasa sai da Zeenat tayi kwana biyar cur  batare da taga zuwan yaya faruk  ba.h hakan yasa  hankalinta  sake tashi fiyye da koda yaushe .
cikin lokacin kadan ta zabge ta sake ragewa   zazzabi may zafi  ya rufeta, jikinta ya dauki zafi gwau ,  hankalin ummi yatashi , da Ganin halin  da Zeenat take ciki  kmr zatayi kuka.
   Ummi ta kira likitan dake duba su, wato family doctor dinsu , byn yazo ne yasoma aikinsa  cikin sauri ganin yadda Zeenat din takeyi  taki magana sai zubda hawaye kawai take  ga zuciyarta na buguwa da sauri da sauri  Ganin haka yasa doctor din ya dauko abin awo ,ya  auna BP dinta ,cikin mintina da basu wace ashirin ba ya gano abinda yake damunta sannan ya daura ma drip  hade da sanya allurar bacci ciki take ko bacci yayi awon gaba daita .

 Gabadaya hankalin Ummi ya sake tashi wani irin tsoro ne yashigeta lokacin daya ,da sauri tace doctor meke damunta ?
doctor yayi shiru yana nazarin abinda zai cewa Ummi kafin daga bisani ya  numfasa ,sannan Yace  akwai abinda tasa aranta wanda shine yayi dalilin  haddasa mata damuwa har takai jinita ya hau sosai , Ummi ta sake maimaita abinda doctor yace  , doctor yace  Amman inshallahu bbu da damuwa zata samu lfy da zarar ta tashi komai zai yi dade, ummi tace to doctor na gode yayi mata sallama tare da gayamata yadda zata bata magani.duk wannan drama da akeyi deeni bai sani ba dan ko yashiga gaida Ummi baya damuwa daita ballantana yasan ko bata da lfy ne ,ita Kuma da haushi taki sanar masa Ai shi ba makaho bane 

Kwata kwata Fk bai samu damar zuwa ba sai acikon  kwana na bakwai tukun yazo ,yasamu Zeenat din bayadda take yayi mamakin , yadda DEENi bai sanar masa ba gashi kusan kullum sai sun hadu .
byn sun gaisa da ummi ne ,ya fita Yace Zeenat din  ta same shi a  parlour .

Cikin tsanyi jiki ta mike tasoma daga karta da kyar, cikin gimtsewar  fuska ummi tace Ina km  zaki  kefa bakida lfy ?
 Zeenat tabata fuska dan kada ummi ta hanata zuwa tace ummi sako zan karbo gurin Yaya faruk ,yanzu zan dawo , Ummi ta bita da idanu kawai  Zeenat tace ummi sai nadawo  cikin jin haushi  da akaici Ummi  tace  kada ma ki dawo ki kwana a can  .


 Da sallamarta  tashigo parlour "Zaune ta same yaya faruk din suka gaisa ya sake yi mata ya jiki sannan  Yace  sister kiyi hakuri dan girman  da rashin zuwana kmr yadda nace, wasu abubuwa ne suka sha kaina wlh,  dan haka yanzun naxo naji abinda kika yanke,zeenat   ta danyi shr kmr mai nazari Yace kada ki damu idan  har baki son shi , kisanar dani ,danshi yace idan baki amince ba, kada atakura miki  shi ya hakura, a dan frigice tace Ai yaya kaima kasan  bazan iya cewa banason shi ba, ko dan ummi dan haka kace masa kawai  na amince .


Fk ya saki murmushi  murna yayi hamdala a zuciyarsa hade da godiyar cin nasara  yace Shikenan  ni zan wuce sai kin jimu .

 A ranar  ummi ta nemi ciwon Zeenat ,tarasa  duk tana zargin ciwan nata bazai wuce akan DEENi bane ,da daddare har nafila Zeenat tayi dan Mika godiyar ga Allah. ummi tayi murmushi tace yau km ibadar ce ta motsa  har da sallar dare ?

Zeenat tayi mata banza kmr bataji ba  tacigaba da sallarta, Ummi  ta sake cewa Allah yasa a dore in km nasamun NASURULDEENI ne nasan daga yau Shikenan .

Abinda ke sake bawa Zeenat mamaki bai wuce Ganin  yadda kullum yaya DEENi ke nuna ko in kula akanta ba gabadaya ma Gani take kmr  baisan da zamanta ba .
 ko magana ta fatar baki bata hadu su, idan ma yana guri kennan ita kanta batason zama in da yake yanzu ,Allah Allah take tabar wanje dan juriyarta takusan karewa .


Fk bai samu ganin deeni ba, sakamakon wani aiki daya taso masa ,Amman Yace masa yabari zuwa weekend ,ya same shi a gida .sai da fk yakirasa a waya ya tabbatar masa da yana gida sannan yazo  .
 zaune suke cikin parlour  deeni  byn sun gaisa fk yayi masa bayani duk yadda suka yi  da Zeenat a boye DEENi ya sauke ajiyar zuciya ,sannan   Yace  ta taimaki kanta da kanta , kennan , fk yabishi da wani irin  kallo sannan yace kai fa dan rainin wayo ne abinda yakamata kace kennan, deeni Yace nifa bawai na matsu dole sai ta amince da aurena bane .
 asalima ita din ba irin kalar  type dina bace zan dai aureta  ne  kawai ,a rashi  samun choice dina fk ya saki baki yana kallon deeni ,Yace Amman friend kasan itama tana kyawunta daidaina , sai da ya dauki lokacin sannan yace  ni nace maka  dan kyawunta zan aureta?
 Ai bata da kyawun da zai rudeni ,km wlh har ga Allah da bata amince ba na hakura , har zuwa sanda zansamu type dina.

MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO



Page 21-22



Wani irin kallon mamaki fk yake masa , ,gabadaya ya zamo  tamkar mutun mutimi a zaune a gurin ,

Yarasa meke damun brain din DEENi , mutun Sai girman kan tsiya da nuna isa " wai shi  DEENi wani irin bahagon mutun ne ?
Shi sam  bbu ruwan shi  da fadar duk magana da tazo bakinsa  .

In a low voice   fk yace yanzu duk wahalar danayi akan yarinyar nan yatashi a banza kennan?

A'a bakayi a banza ba tunda gashi "zan aureta gaskiya ce dai na gaya maka,dan kasan  ita din ba ra'ayina bace .
Amman narasa dalilin da yasa zuciyata ke muradin kasancewa tare daita " fk ya sake dubanshi  sannan yace  dan rainin wayo kawai kar  mai dani  kmr wanda bai san komai ba mana .
 ,tunda har zuciyarka ta iya amincewa daita, har kaji zaka iya aurenta  definitely kana sonta" ko yaya ne" ,.
deeni yaja tsaki hade da furzar da iska ta bakinsa" matsala dakai kennan rashin saurin fahimta fk yace idan son da kake mata ne ,na fahimta ,Amman kace wai kai baka sonta km kake kokarin aurenta , wannan ne fa bazan taba fahimta ba , DEENI ya sake first da huci may zafi ranshi tasoma baci muryasa a sarke" yace da alamun kana son musamu matsala dakai fa" muddin  baka daina cewa Ina son yarinyar nan ba .

 Idan km kafin son haka ya daga kafadarsa alamun Shikenan , parlour ya dauki shr na wani "dan lokaci yayinda  deeni ya jingina bayansa da kujera da yake zaune, hade da runtse idanunshi ya dan jin daci maganar fk 'ta yaya ma " zai nace akan yana son yarinyar byn shi yasan  aure kawai yake da bukatar yi bawata ,aba soyayya ba ...
   maganar fk ce ta daki dodon kunnenshi" to yanzu meyye solution tunda yarinya ta rigada ta amince ?


Ahankali ya bude rikitattun idanunshi ya sauke su ,akan fuskar fk sannan  yayi magana cikin sanyi tamkar wanda aka takura masa. Yace karkadamu zan samu yaya mahamud ,Ai kagama may wuyar "ya maida idanunshi ya sake lumshe su tamkar dai yadda yayi dazu  .
 girgiza kai kawai fk yayi uhmm shi wannan  bazai taba canzawa zai ba .
halinsa, na nan kmr dai yadda yasan shi" haka km yataso "  shi komai baya so matsawar ba ra'ayin sa bane" duk yayi magana ne akasan ransa,,.
 Ganin ya bawa banza ajiyarsa yasa shima ya mike yayi masa sallama .

 
Daga gurin DEENi kai tsaye fk part dinsu shemah yayi  yaja ya tsaya byn ya tura ayi masa kiranta fk  tafito sanye da doguwar rigar  material  puppy colour mai shegen kyau hade yane kanta da karamin mayafe baki ahankali take isowa gareshi duk step daya Sai kirjinta ya motsa tun fitowarta ya zubawa kirjinta ido kyam yana kallon yadda kirjinta ke motsawa lumshe idanunsa shi yayi na wani lokacin sannan ya sake budesu ahankali mutuwar tsaye a gurin har takaraso inda yake ta gaisheshi cikin sanyi jiki bai dauke idanunshi akanta ba yacigaba da da binta mayataccen kallo da sallamarta iso inda yake  ta gaisheshi ya amsa yana sake bin koina na jikinta da kallo cikin sanyi tace  yaya faruk Gani Yace Ai naganki ,daman nazo ne na fayace miki abinda na dade Ina boyewa akanki ,nan dai yasanar mata koma , tunda yasoma magana tayi shr  kawai hade da sunkuyar da kanta badan tana jin dadin abinda yake kokarin fahimtar dai ba ahankali ta dago ta zuba masa idanunta  Sai data tabbatar ya gama fadar abinda yakawoshi sannan tace ,dan Allah yaya kayi hakuri wlh akwai wanda zuciyata ta dade da kamuwa da soyayyarsa , Amman kayi hakuri idan maganata ta bata maka rai ,yace Ina Gaza bata min rai Ai iya gaskiyar ki kika fada Sai dai ki sani zuciyata bazata iya hakura dake ba Amman zan baki lokaci yi tunani akai tace nifa bawani tunanin dazanyi akai ka dai yi hakuri ka nemi wata ,ta juya ta wuce tabar sa nan tsaye ,da mamaki yabi bayanta da kallo ya dauki lokacin tsaye a gurin batare yasan abinda zaiyi ba , Ganin tsayuwa nasa bata da wani amfani yasa yasoma kokarin daga kafafunta  ahankali  tafe yake yana saka da warwara da tunanin malomasarsa a gurinsa ,a fusace  shemah tashiga part dinsu tana zuba tsaki da zage zage har mmnta ta tambayeta abinda yasameta tace matabakomai.

Byn kwana biyu 

Da misalin karfe takwas na dare  fk  ya km samu shemah da zance shi fa ba zai iya wani hakura daita ba kawai tayi hakuri ta amincewa da bukatar domin shi   yana matukar  son ta  km aurenta yake son yi ,tace dan Allah yaya  kayi hakuri   wlh da bbu wanda nake so ne ,zan iya soka dan kaima baka rasa komai da zankika ba ,  kadai yi  hakuri kawai .
al'amarin dayayi matukar dagawa fk hankali kennan ,yayi shr kawai yana kallon yanayinta tare da nazarin kalamanta masu kokarin tarwatsa masa zuciyar rasa yadda zanyi daita yayi can dabara tazo masa,ya tsareta da idanunshi  Yace ke banso iskanci da rainin hankali fa  ni zaki cewa kina da wanda zaki kike so  byn  Banga uban da  kike  saurara  ba ,lafazinsa yayi mugun bata mata rai dan haka a ranta abace  tace to dole ne Sai na aurenka kaje Kanemi wata mana ko ana soyayya dole ? ta juya a fusace  zata bar guri ,ya fizgota hannuta , gabadayanta ta fado jikinsa , idanun ta zaro a tsorace, ,take taji  wani irin faduwar gaba , .
Hannuwansa dukka  yasa  rungumeta tsam ajikinsa yana sauke ajiyar zuciya daidai kunneta ya kai bakinsa Yace  maimaita abinda kikace Ina jinki cikin tsiwa tace wannan wani irin iskanci dazaka wani  rungume mutun ?  Ok nine ma nake miki iskanci ?
Uhmmmm fa shemah karkibari muyi haka dake zaki amince ta girma da  arziki ne ko km na jawo soyayyata ta karfin tsiya ,.batare da na wahalar da kaina ba muryarta na rawa tace anki a amince da soyayyarka .
ko ana so dole ne ?
, dan Allah ni kasake ni ,ya zuba mata manyan idanunshi  kawai ,yasoma yawo da hannushi a jikinta  gabadaya jikinta ya  dauki kirma abinda bai taba faruwa daita ba kennan tunda take arayuwar ta ,wai namiji ya rabi jikinta har  takaita ga runguma ,dan takaici ma batasan sanda , kwalla ta cicciko a idanunta ba , hawaye yaga yana silalowa daga idanunta ahankali ya sauke ajiyar zuciya, ya dan sausauta rungumar da yayi mata  yasa yatsansa ya dangwalo hawayen dake bin fuskarta yana kallo Yace duk wannan kukan akan nace Ina sonki ne kike zubda hawayen ki?
  ,tayi shr taki cewa komai dan haushi ji tayi kmr ta daura hannuta akanta ta kurma ihu  , ahankali ya sake maida ita jikinsa ya rungumeta yana shinshina wuyanta  daidai nan Sai ga big  dady dake dawo daga masallaci , a tsorace yake binsu da kallo cike da mamaki da alajabi abinda yagani , meke shirin faruwa km yau acikin zuri'arsu ,fk yacigaba manneta da jikinsa yana rarrashi ta amincewa aurensa , dagowar nan da zai  lyi  karaf idanunsa suka sauka kan big dady dake tsaye duk da duhu ne hakan bai hana gareshi ba  gabansa yaji yayi muguwar faduwa jikinsa ya dauki kirma duk da ya tsorata Amman yaji dadi Ganin da big dady yayi musu ,yasan hakan zai sa a aura masa shemah  batare da bata lokaci ba tsabar frigice yasa yakasa rabata da jikinsa gabadaya jikinsu rawa yake shemah da batasan wainar da'ake tuyawa ba sake   lafewa tayi ajikinsa saboda irin rungumar dayayi mata ba wacce zata iya kwacewa bace har big dady ya wuce su a gurin shemah batasa big dady yagansu , ahankali fk  yasoma rabata da jikinsa  har zuwa yanzu hawaye bai daina bin fuskarta ba hannuta yakamo yasoma tafiya ita kum tana biye dashi bbu wanda ya iya cewa dan'uwansa komai har yakawo part dinsu yaja ya tsaya ahankali Yace shemah kiyi hakuri dan Allah kibar kuka ba nufi na kuraki ba Ina matukar kaunarki bansan lokacin dana fara sonki ba Amman zan baki lokacin kiyi tunani akai ,zan dawo zuwa jibi yana gama fadar haka ya juya da kyar yake iya daga kafafunsa tsabar frigice da nauyin da suka masa zuciyarsa tamkar zata buga , dan fargaba haduwarsu da big dady shi yasan ba makuwa tunda har big dady yagansu aure kmr anyi an gama Amman kunya fa ,har ya iso part dinsu wanda kusan nan samari suke zaune  wayanda basuyi aure ,
     

Itama tana shiga dakisu ta wuce kai tsaye tana kuka , mamanta dake zaune a parlour tace ke lafiyarki Amman ko juyo batayi ba fadawa tayi kan gado tana risgar kuka to meye yaya faruk yake nufi daya sonta  alhalin ita DEENi take mutuwar so ..... Dan haka bata taba aurensa ba ,tunawa datayi ba'a musu auren dole a family dinsu sai sun amince da juna yasa taji hankalinta ya kwanta Amman gabadaya jikinta yayi bala'in sanyi haka ta wuni a daki batare data sake fita ko parlour ba ,fk bai dawo ba kmr yadda Yace mata kusan sati tsakani shiyasa tayi tunanin ko yayi wa kansa fada ne ya hakura daita dan haka ta sake abinta kwasam Sai gashi a wani daren lahadi byn tagaishi a dage ,yayi murmushi yace yazo ne akan maganar su ,a fusace tace wata magana kennan i tough mun gama da wannan zance tunda nace ban sonka , Yace haka kika ce ,tace eh ko dole soyyaya dakai ,Yace uhmm Amman dolenki ki aureni ya wuce batare da damuwa ,



DEENi yasamu yaya mahamud yayi masa bayanin shi kuma ya samu big dady da zance  tsohon yaji dadi Sosai jin sun hada kansu yace Shikenan bbu damu zai tuntubi yarinyan tukun asan abinyi .



Nan dai aka saka ranar aure   tare da yanka sadaki yaya mahamud ne yayi komai ko sisin Kobo bata fita daga aljihun ogo deeni ba ko mahaifin zeenat yayi murna sosai da jin DEENi ne zai aure diyarsa 

Anyaka sadaki da dukiyar aure  naira duba  dari biyar wanda duk a aljihun yaya mahamud suka fita  .


Da kyar big dady yashawo kan Ummi dan tuburewa tayi ita sam bata yarda da wannan aure ba big dady yace Ai tunda dai yara sun hada kansu km suna juna Ai Ina Gani  magana takare fatanmu Allah ya zaunar dasu lfy .

 Lokacin da aka sanar da DEENi ansa ranar wata biyar deeni Yace  wa yaya mahamud lokacin nan bai yi yawa ba kuwa ?

Dan akwai aiki da zai kaini  akwaibon Ina Ganin zaifi kyau a takaita lokacin koma ba dan haka anawa raayin nafi son ayi nan da wata uku   yaya mahamud yace Shikenan kabari dai zan samu Ummi da maganar  .


  Zaune take a cikin extra room dinsu wanda kusan yanzu can tafi zama tunda aka sa musu rana da yaya DEENi ta zabga uban tagumi tana mamakin hali irin na yaya DEENi yau kusan wata biyu Keenan dasamusu rana Amman ko sau daya bai taba kiranta da sunan zance ba  haka nan ko cikin part din Ummi yashigo bata ishe shi kallo ba   takan ji tsoro da frigice sun shigeta a duk sanda taga yaya DEENi nuna rashin damuwarsa akanta ,a kasan ranta tace, anya kuwa banyi kuskure da wautaba wajen  saurin amincewa aurensa ba  domin fa zuwa yanzu tasoma sarewa anya kuwa yaya DEENi yana sonta ?
kullum miskilancinsa sake gaba yake har  zuwa yanzu dabatason cikakken matsayin ta a gurinsa ba ,son auren yasoma fice mata arai   domin ita kadai tasan fargaban da take cikin zuciyarta ga ,gorin da Ummi kebinta dashi kullun garin Allah ya waye , dan haka ta yanke hukunci samun yaya faruk dan ta inda aka hau tanan ake sauka .ta shirya taje har part dinsu tace daman tazo ne akan maganar mu da yaya DEENi idan fa abin nan bazai yiwu ba gara tun yanzu   abarshi  .

Fk ya gyara tsayuwa sannan yace wani abu ne ya faru ? Tace to yaya faruk a haka ne zamu fahimci juna in San abinda yake so shima yasan wanda banaso shi fa aure ba banza bane kmr yadda ya dauki komai tacigaba bai taba kirana ba km ko gida yashigo ban ishe shi kallo ba  shi bashi da lokacin kowa sai na kansa fk yace kiyi hakuri bawai zangoyi bayansa ba aikine yayimasa yawa kiyi nasa uziri Amman kina ranshi zeenat ta tabe baki dan tasan karya ne yace wai tana ran yaya DEENi Ai abinda kake son baka sakaci dashi  fk yacigaba  komai yakusan zuwa karshe da zarar kin zama a gidansa nasan dole ya baki dukkan lokacin sa ,zeenat tayi shr ne kawai ba wai dan maganar tashigeta ba  ,  fk yace tayi hakuri zai masa magana da sauri ,zeenat ta dago tace dan Allah yaya kar kace ni nayi maka maganar ya sake dubanta sosai yaga duk ta wani frigice yace karki damu ni nasan abinda zanyi     .


Fk yakira deeni a waya Amman ba'a daga ba

Da misalin karfe goma na dare fk ya amsa kiran DEENi tare da yin sallama byn sun gaisa yace friend dazo inata kira baka daga ba DEENi ya runtse ritattun idanunshi tamkar na may  jin bacci sannan yace wlh aiki ne yasha kaina lafiya dai ko ya fadi cikin kasala dan duk a gajiye yake fk yace lfy dama akan maganar yarinyar nan ne yakama mushirya muje zance gurinta , ,anhakali DEENi ya bude idanunshi  jin abinda fk yace muryasa a sarke yace  wacce yarinyar km?

Fk yace sai karinka yin kmr baka san da zance ba ,byn nasan tana ranka DEENi yace dan malam karkadameni go to the point dan bangane wacce yarinyar kake nufi ba fk yace Ai dole ka manta da ko wacce yarinya ce tunda kaga kasameta  cikin kwanciyar hankali  km Ummi ta amince ,tsaki yaja kana yace wai zeenat kake nufi ?
Yasake jan wani tsakin mtssss wani irin hira kum kmr muna kauye byn angama magana sai jiran lokacin  fk yace kai mugun dan iska ne Ai duk da haka yakamata muje dan ita yarinyar tasan  raayinka kai ma haka ku samu fahimtar juna DEENi ya katse shi da itace Keenan ta aiko ka fk yace ko daya ni dai naga dacewar haka DEENi yace to baza'aje ba ...  Kar Allah yasa  mu fahimci juna, ita tun tasowarta, bata san abinda nake so da wanda  ba,fk yace idan ita tasan abinda kake so da wanda baka so kai kasan nata ?

DEENi ya sake jan tsaki hade da kamo lip's dinshi na kasa yana dan ciccizawa sannan ahankali yace to sarkin yakinta ni ba haka taarina da raayina yake ba  Ina tunanin in har zanje zance gurin budurwar ,zanje ne dan tallar kaina in samu gindin zama to ni narigada na samu shigar ,bbu dalilin da zai sa na takurawa kaina me kadauki ni ,nafa san irin son da yarinyar nan  take min ,kawai dai ni banda lokacin wannan shirme dakace  km nasan ita ta aiko ka fitowa ne kawai bazakayi kafada ba .


Fk yaja tsaki shima yace kai ,dan Allah wani irin bahagon mutun ne?

To wlh ka canza wannan budadden halin naka, to ko waya ce ka tsiya mata  ,DEENi yace shima din baza'a tsiya ba  ,duk abinda zai faru ya faru ciki har da fasa aurena ,fk yace kai fa kafiyye kafiya ,da maida karamar magana tazama babba ,. yace sake cewa  yanzu dai kayi hakuri dan girman Allah ka Sai mata ko karamar  waya ce.

   DEENi yace kasan Allah ko game  bazan  Sai mata ba ,  ballanantana waya ,  tunda har taiya zuwa ta sameka da maganar bana kiranta   fk yace kadaina cewa tasameni ni kawai Gani nayi ya dace muje DEENi ya tabe baki tamkar fk din  na ganinsa Shikenan kai ka sani ni km kar ka sake damuna da maganar wata yarinya ya kashe wayarsa batare da ya tsaya jin abinda fk zai ce ba  .

Wasa wasa lokacin bikin ya dinga karatowa da kwanaki ya wattani har zuwa yanzu dayayi sauran wata cif cif ayi daurin aure  to Ganin kurewar lokaci yasa DEENi yasamu Ummi da maganar shifa baya son zamansa cikin estate din  taje Ummi tayi kicin kicin da ranta sannan ta dago tana dubansa tace bangane abinda kake nufi  ?
Sai da  ya sake maimaita mata tukun Ummi tace sam ita bata yarda ba salon yaje yana dinga cin amanar Yar marainiyar Allah ga babbin gurin bid dady yasa an Gina musu shida sauran enuwansa shine kai dan iyayi zaka ce bazaka zauna ba ,to wlh kaji na rantse anan zaku zauna Sai naga yana yin zaman naku  cikin yin kasa da murya yace Shikenan first lov na hakura duk abinda kika ce shi za'a yi tace da dai yafiye ma a yi mutun Sai girman tsiya da iyayi yace to kiyi hakuri .

Zeenat dake sauransu ta lumshe idanunta jin Ummi bata amince ba dan tana matukar jin tsoro zaman daga ita Sai shi ahankali cikin sanyi jiki ya mike idanunshi suka sauka akan inda zeenat ke kwance  suka hada ido da sauri ta gaidashi  hade da  dauke idanunta ,bai sake kallonta ba bare ya amsa gaisuwar ta  .


Shirye shiryen biki ya tashi gadan gadan  enmata duka   a tare suke shirinsu dan yanzu zeenat ta saki da shemah sun koma kmr da ganin da tayi wanda ma take haukar akansa bai san da zamanta ba wata safiya suka shirya zuwa siyayar su irinta amare mutun biyu ne abayanta mota Maryam da shemah yayinda zeenat ke gaba kai tsaye kasuwar Lagos  suka nufa sukace derive yayi parking a idimota su kum suka shiga cikin market din   


Derive yaja ya tsaya suna fitowa da yaya kamil suka soma cin karo  tun shigowar motar dayaga hango zeenat zaune ya zubawa motar ido har sanda ta fito ahankali suka jiro suna hira Amman banda zeenat dataji gabanta ya yanke ya fadi dan tun lokacin da aka mata rana ,rabonta dashi dai dai sun kusan geftashi yakira sunnanta zeenat..... tacigaba da tafiyarta dan batason abinda zai km hada ta dashi cikin sassarfa ya biyo bayanta yasha gabanta cak taja ta tsaya suna kallon junansu,yayinda su Maryam suka cigaba da tafiyarsu suna tsaye batare da dukkansu suyi yunkurin yin magana ba kamil ya gyara tsayuwa ya tura  hannuwansa duka cikin aljihun wandonsa  ya kafeta da  idanunshi ta sunkuyar da kanta kasa sannan tace lfy yaya ka tsayar dani muryasa a dashi yace lfyr ce takowa haka yanzu zeenat kin kyauta kennan ki zabi wani kibarni byn duk lokacin dana dauka Ina fama da soyayyarki ,a she kinsa bakya sona kibarni inata faman hauka akanki  tace Allah yaya ba haka bane Amman kayi hakuri dan Allah, ya sake gyara tsayursa , yayinda idanunshi ke kanta har  yanzu   yace iya hakuri ne kawai zai wadatar da zuciyar da tayi sama shekara biyu tana mata da miki so.... yace Shikenan bbu komai  Nagode Kwarai da abinda kika saka min tace ka dauka haka Allah yaso ni din ba matar ka bace yayi murmushin karfin hali sannan yace haka ne fa al'amarin ubgj  Amman agaskiya DEENi ya cuceni ,tace kabar cewa ,tayi ta dago suna kallon juna fuskarta dauke da murmushi  ta bude baki kennan Sai ga motar DEENI ta kuno kai cikin compound din km shi suke facin Ai take maganar ta ta tsaya sakamakon  DEENi data Gani zaune a mota yana kallonsu duk kasancewar akwai dan duhun magariba hakan ba zai sa takasa gane bscin ransa ba  , gabanta ya yanke ya fadi  ,  ,shima kamil din shr yayi bai sake yin magana va kusan minti goma yayi yana kallonsu koda bata ga fuskasa sosai ba tasan  a daure take  ,har sanda  DEENi ya fito yayi matarsa key  idanunshi na kansu ,cikin tsoro da frigice zeenat tace ni zanshiga ciki ,kamil  yace Shikenan Allah yabaki zaman lfy ta gefensu yazo yazo ya gifta hade da  jan  tsaki sannan ya wuce .   a filli ta furta wayo Allahna nashi uku kamil ya sake yin murmushi dole sannan yace da'aka me,da kika shiga uku,  nifa Banga abinda ya birgeki a DEENi ba,har da kika iya zabarsa , kalli fa yadda jikinki ke rawa saboda Allah tamkar kinga wani malaika tsaki taja hade da zabga masa harara dan Allah kabarni naji da damuwa Ai duk kai kaja min matsala Ina zaman zamana da yanzu Ina cikin gida💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO



Page 21-22



Wani irin kallon mamaki fk yake masa , ,gabadaya ya zamo  tamkar mutun mutumi ,a zaune a gurin ,

Yarasa meke damun brain din DEENi , mutun Sai girman kan tsiya da nuna isa ,fk ya dinga masa kallon bahagon   mutun wanda 
Shi sam  bbu ruwan shi  da fadar duk magana da tazo bakinsa  .

In a low voice   fk yace yanzu duk wahalar danayi akan yarinyar nan yatashi a banza kennan?

 DEENi ya tabe bakinsa hade da cewa  A'a bakayi a banza ba tunda gashi "zan aureta gaskiya ce dai na gaya maka,dan kasan  ita din ba ra'ayina bace .
Amman narasa dalilin da yasa zuciyata ke muradin kasancewa tare daita "alhalin bata sonta nake yi ba .
 fk ya sake  dubanshi  sannan yace   dan rainin wayo kawai "kar ka  mai dani  tamkar wanda bai san komai ba mana .
 ,tunda har ita zuciyartaka ta iya amincewa daita, har kaji zaka iya aurenta  definitely kana sonta" ko yaya ne" ,. Amman maganar kace  baka sonta,wannan ma ba gaskiya bane .

deeni yaja tsaki hade da furzar da iska ta bakinsa" sannan yace matsalata dakai kennan rashin saurin fahimta .

fk yace ta yaya kake so na fahimta ?
 Alhalin ga zahirin gaskiya nan"  idan son da kake mata ne ,na fahimta wannan.
,Amman kace wai kai baka sonta km kake kokarin aurenta , wannan ne fa bazan taba fahimta ba.sai dai kayi hakuri ,

 DEENI ya sake furzar da huci may zafi ranshi yasoma baci muryasa a sarke" yace da alamun kana son mu samu matsala dakai fa" muddin  baka daina cewa Ina son yarinyar nan ba .

 Idan km kafin son haka  ya daga kafadarsa alamun Shikenan ,.
    parlour ya dauki shr na wani "dan lokaci, yayinda  deeni ya jingina bayansa da kujera da yake zaune, hade da soma jijiga kafarsa daya a tile's dakin " runtse idanunshi Yayi dan jin daci abinda  fk din yace"
 'ta yaya ma " zai nace akan lallai yana son yarinyar byn shi yasan  auren kawai yake da bukatar yi" bawata ,aba soyayya ba ...

   maganar fk ce ta daki dodon kunnenshi" to yanzu meyye solution akan maganar, tunda yarinya ta rigada ta amince ?


Ahankali ya bude rikitattun idanunshi ya sauke su ,akan fuskar fk sannan  yayi magana cikin sanyi tamkar wanda aka takura masa dole. Yace karkadamu zan samu yaya mahamud ,Ai kagama may wuyar " tare da maida idanunshi ya sake lumshe su tamkar dai yadda yayi dazu  .

 girgiza kai kawai fk yayi. uhmm shi wannan  bazai taba canzawa ba .
halinsa, na nan kmr dai yadda yasan shi" haka km yataso da murdanden raayi "  shi komai baya so matsawar ba ra'ayin sa bane"fk  yayi magana ne akasan ransa,,.
 Ganin da yayi DEENi ya bawa banza ajiyarsa yasa shima ya mike yayi masa sallama yayi ficewarsa .

 
Daga gurin DEENi kai tsaye fk part dinsu shemah yayi  ,ba bata lokaci yasamu yaro ya tura ayi masa kiranta dan ya kudirtawa ransa ,yau ce, ranar da zai isar da sakon zuciyarsa  gareta domin yagaji da cutar da kansa .

  tafito sanye cikin   doguwar rigar  material  puppy colour mai shegen kyau hade da yane kanta da karamin mayafe baki, 

ahankali take isowa gareshi duk step daya datayi Sai kirjinta ya motsa sakamakon dukiyar fulani dake gareta.
tun fitowarta ya zubawa kirjinta idanunshi kyam ko kyafta ido bai yi  yana kallon yadda albarkatun kirjinta ke motsawa, lumshe idanunsa shi yayi na wani lokacin ,sannan ya sake budesu ahankali. mutuwar tsaye yayi a gurin "  har takaraso inda yake tayi sallama.
  bai dauke idanunshi "akanta ba .Sai ma  cigaba da yayi" da binta da wani irin   mayataccen kallo wanda yasa shemah tasha jinin jikinta.
Ganin irin duban da take masa ne yayi saurin ,sauke idanunshi,tare da sakin ajiyar zuciya,   ta gaisheshi ya amsa cikin sakin fuska, yana sake bin koina na jikinta da kallo dan tayi masa kyau matuka ,rigar jikinta irin mai flay akasa ce Sai dai taka mata a sama sosai.  cikin sanyi murya tace  yaya faruk Gani , Yace Ai naganki .

,yayi shr yana tunanin ta inda zai soma ,itama shr tayi Sai dai,haka kawai ta tsinci kanta da jin ,faduwar gaba.   haka nan kallon da yaya faruk din kema ,yasa taji wani iri ajikinta ,dan haka ,ta sunkuyar da kanta kasa tana Jira daga gareshi.
 ,can  numfasa,hade da jin kwarin gwiwa yazo masa ,ya danyi gyaran murya" yace daman nazo ne na fayace miki abinda na dade Ina boyewa akanki ,  taji gabanta yashiga faduwa ,ta dan dago kadan ,taga ita yake kallo , ahankali tace na mefa? Sannan ta km maida kanta kasa tana jin yadda gabanta ke lugude faduwa.
Yayi murmushi yana cigaba da kallonta, cikin natsuwa  da jarumta.
 yasanar mata koma .

tun da yasoma magana tayi shr  kawai hade da sake sunkuyar da kanta kasa, sosai badan tana jin dadin sauraron abinda yake kokarin fahimtar din bane ,taji hankalinta ya yayi matukar tashi dan haka ,  ahankali ta dago kanta , ta zuba masa idanunta ,  Sai data tabbatar daya gama fadar abinda yakawoshi a dan frigice tace ,dan Allah yaya kayi hakuri wlh akwai wanda zuciyata ta dade da kamuwa da soyayyarsa , Amman kayi hakuri idan maganata ta bata maka rai ,yace Ina fa za bata min rai Ai iya gaskiyar ki kika fada Sai dai ki sani zuciyata bazata iya wannan  hakura dake bani ba Sai d zan baki lokaci kiyi tunani akai , tace  tunanin me km zanyi? nifa bawani tunanin dazanyi  ka dai yi hakuri kawai ka  nemi wata ,ta juya ta wuce tabar sa nan tsaye .
,da mamaki yabi bayanta da kallo ya dauki lokacin tsaye a gurin batare da yasan abinda zaiyi ba , Ganin tsayuwa nasa bata da wani amfani yasa yasoma kokarin daga kafafunsa da suka masa nauyi, ahankali yake daga kafafunsa   yana saka da warwara" da tunanin makomasarsa a gurinta .
 ,a fusace  shemah tashiga part dinsu tana zuba tsaki da zage zage har mmnta ta tambayeta abinda yasameta tace mata bakomai.

Byn kwana biyu 

Da misalin karfe takwas na dare  fk  ya km samu shemah da zance ,shi fa bai ji zai iya wani hakura daita ka " kawai tayi hakuri ta amincewa da aurensa , domin shi   yana matukar  sonta ,tace ni dai  dan Allah yaya  kayi hakuri   wlh da bbu wanda nake so ne ,zan iya aurenka dan kaima baka rasa komai da zankika ba . kadai yi  hakuri kawai .

al'amarin dayayi matukar dagawa fk hankali kennan ,yayi shr kawai yana kallon yanayinta tare da nazarin kalamanta masu kokarin tarwatsa masa zuciyar rasa " yatasa yadda zaiyi daita,  can dabara tazo masa, dan haka ya tsareta da idanunshi  Yace ke banso iskanci da rainin hankali fa"  ni zaki cewa kina da wanda zaki kike so  byn  Banga uban da  kike  saurara  ba.
   ,lafazinsa yayi,  matukar bata haushi da mugun bata mata rai" dan haka  ranta a bace  tace to dole ne Sai na aurenka kaje Kanemi wata mana ko ana soyayya dole ? ta juya a fusace  zata bar guri ,ba zato ba tsammani taji ya fizgo  hannuta , gabadayanta ta fado jikinsa , idanunta "zaro a tsorace, ,take taji  wani irin faduwar gaba fiyye da wanda taji dazu  , .
Hannuwansa dukka  yasa ,ya rungumeta tsam ajikinsa yana sauke ajiyar zuciya "daidai kunneta ya kai bakinsa Yace uhmmm  maimaita abinda kikace Ina jinki?
 cikin tsiwa tace wannan wani irin iskanci ne dazaka wani  rungume mutun ? 
 Ok nine ma nake miki iskanci ?
Uhmmmm fa shemah karkibari muyi haka dake ,tace muyima mana ,dan Allah ni malam kasake ni ,yayi murmushin karfin hali sannan yace zaki amince ta girma da  arziki ne.
 ko km na" jawo soyayyartawa " ta karfin tsiya ,.batare da na wahalar da kaina ba. muryarta na rawa ta sake cewa  anki a amince da soyayyarka .
ko ana so dole ne ?
, dan Allah ni kasake ni , tun ban saka maka ihu ba ,ya zuba mata manyan idanunshi  kawai yana kallonta. ahankali ,yasoma yawo da hannushi a sansar  jikinta " gabadaya jikinta ya  dauki kirma " abinda bai taba faruwa daita ba kennan" tunda take arayuwarta ,wai namiji ya rabi jikinta har  takaita ga runguma ,dan takaici ma batasan sanda ta saki kara ba , kwalla ce cicciko a idanunta . Ya dan sausauta
Rungumar da ,  yayi mata ya zubawa fuskarta ido hawaye yaga yana silalowa daga idanunta ahankali ya sauke ajiyar zuciya,yasa  yatsansa ya dangwalo hawayen dake bin fuskarta yana kallo Yace duk wannan kukan akan nace Ina sonki ne kike zubda hawayen ki?
  ,tayi shr taki cewa komai dan haushi , ji tayi kmr ta daura hannuta akanta ta sake , kurma ihu  , ahankali ya sake maida ita jikinsa ya rungumeta yana shinshina wuyanta Yace please  kidaina zubda hawayenki, Akan nace Ina sonki wlh duk ma wanda kike tunanin zaki aura nafi shi sonki , yasoma shafa bayanta da hannushi daya , daidai nan Sai ga big  dady dake dawo daga masallaci take yaja birki , a tsorace yake binsu da kallo cike da mamaki da alajabi abinda yagani , meke shirin faruwa km yau acikin zuri'arsu ,fk yacigaba shafa bayanta tare da sake manneta da jikinsa yana rarrashita tayi hakuri ta amincewa aurensa .
dagowar nan da zai yi da niyar rabata da jikinsa karaf idanunsa suka sauka cikin na  big dady dake tsaye ,gurin da Yar sandarsa yana kallonsu. "duk da duhu ne hakan bai hana ganeshi ba  gabansa yaji yayi muguwar faduwa"take  jikinsa ya dauki kirma duk da ya tsorata ,hakan bai sa ya saketa ba Sai dai   yaji dadi Ganin da big dady din yayi musu .

yasan hakan zai sa a aura masa shemah  batare da wani bata lokaci ba "tsabar frigice da yake ciki Ne yasa yakasa rabata da jikinsa gabadaya jikinsu rawa yake shemah da batasan wainar da'ake tuyawa ba .
 sake   lafewa tayi ajikinsa saboda irin rungumar dayayi mata ba wacce zata iya kwacewa bace" har big sanda big  dady ya wuce su  a gurin shemah batasa big dady yagansu ba , ahankali fk  yasoma rabata daga jikinsa " har zuwa yanzu " hawaye bai daina bin fuskarta ba. Bai tsaya Ganin yanayin datake ciki ba  hannuta ya damko yasoma tafiya.
      ita kum tana biye dashi a baya , bbu wanda ya iya cewa dan'uwansa komai ,har yakawo part dinsu yaja ya tsaya , sannan ahankali Yace please... shemah kiyi hakuri dan girman Allah kibar kuka nan haka ba nufi na ta kuraki ba .
Ina matukar kaunarki" Ina miki son da ko ni kaina  bansan lokacin dana fara  ba Amman zan baki lokacin ki sake yi tunani ,zan dawo zuwa jibi yana gama fadar haka ya juya ,da kyar yake iya daga kafafunsa tsabar frigice da nauyin da suka masa zuciyarsa tamkar zata buga , dan fargaba haduwarsu da big dady "shi yasan ba makawa" tunda har big dady yagansu" aure kmr anyi an gama Amman kunya fa? Tana nan  har  abada .
 ,har ya iso part dinsu wanda kusan nan samari suke zaune  wayanda basuyi aure gumi ke tsatsafo masa,
     

Itama shemah da kuka ta shiga part dinsu , mamanta dake zaune a parlour tace ke lafiyarki kike kuka  ?
 ko juyo batayi ba daki ta wuce ,ta fada kan gado ta cigaba da risgar kuka to yaya faruk yake nufi da yana sonta  alhalin ita DEENi take mutuwar so ..... Dan haka tace wlh  bazata taba aurensa ba ,tunawa datayi ba'a musu auren dole a family dinsu sai sun amince da juna yasa taji hankalinta ya kwanta Amman gabadaya jikinta yayi bala'in yi sanyi, haka ta kwanta da tunanin abinda fk yayi mata Ta dinga jinsa ajikinta tsagar jikinta suka mike ga kamshi turarensa daya fureera ,ko ta juya kamshinsa da hannushi ke yawo a koina na jikinta,.

Washegari ma kin fitowa tayi daga   daki  ,gabadaya 
Yinin ranar a kwance tayi shi  batare data fita ko parlour ba .

,fk bai dawo gurinta  ba kmr yadda Yace mata kusan sati kennan tsakani ,shiyasa hankalinta ya kwanta Sosai tayi tunanin ko ya janye ne Tare  da yiwa kansa fada  ya hakura daita ,dan haka ta sake abinta.
 kwatsam Sai gashi a wani daren lahadi byn ta gaisheshi, a dage ,yayi murmushi yace shifa  yazo ne akan maganar su ,a fusace tace wata magana kennan?
 i tough mun gama da wannan zance tunda nace ban sonka , Yace haka kika ce ,tace eh ko dole sai anyi soyyaya dakai?
 ,Yace  ba dole kiyi soyayya dani ba ,Amman Ina son in tabbatar miki da   aurena  yazame miki dole ,yakamo hannuta ya sumbaci  tafin hannuta sannan  wuce ya yabar nan   tare da damuwa ,



DEENi yasamu yaya mahamud yayi masa bayanin shi kuma ya samu big dady da zance  tsohon yaji dadi Sosai jin sun hada kansu yace Shikenan bbu damuwa zai tuntubi yarinyan tukun yaji kafin yaasan abinyi .




Bayan wata  daya 

A wata lahadi da takasance ta karshen wata wanda sukeyi taronsu na family.
Holl din cike da yaya da jikoki  tare da iyaye kowa kagani cike yake da tsantsar murna sabanin shemah da jikinta ke a tsanyaye sakamakon jin rade radin datayi na DEENi ne zai aure zeenat km Sai lokacin tasan dalilin dayasa zeenat ta mata wulakanci kwanaki 
Byn wani lokacin gaishe gaishe ne yasoma biyu baya.
 Takan shemah big dady yasoma, bai tsaya  jin tabakinta ba yace  akwai wanda taKe so ne ? Tace   A'a  yace shikennan  yabawa faruk aurenta Take hawaye wanke mata fuska baita ba ko fk dake kokarin kiran DEENi wanda shi kadai bai iso ba , duk da hukunci big dady yayi masa dadi hakan bai    hana  jin  gabansa faduwa ba daidai lokacin DEENI ya dau waya yaakayi ne mlm zaka dameni da kira fk yace angama dani fa sauran kai DEENI yace mezanzo yi km ?  Fk yace kai fa dan rainin hankali ne zaka ce  bakasan abinda akayi ba yau , uhmmmm tare da katse kiran Yama kashe  wayar gabadaya  dan bai son damuwa  ,.

Kuka sosai shemah takeyi ta dinga datasanin cewa bata kowa gashi an kasaba mata auren fk  nan Aka kira zeenat itama big dady yayi mata Mata tmbyrta ta Amince  Sai sanda akazo neman su fk aka nemi DEENI akarasa  kiran duniya akayiwa wayarsa taki shiga ,daga karshe big dady yace tunda yaji raayin zeenat din Ai  aishikenan.
Nan dai aka saka ranar auren DEENi da fk    tare da yanka sadaki, yaya mahamud ne yayi komai na DEENi  ko sisin Kobo bata bai  fita daga aljihun ogo deeni ba, ko mahaifin zeenat ma yayi murna sosai da jin DEENi ne zai aure diyarsa. 

Anyaka sadakin zeenat tare da dukiyar aure  naira duba  dari biyar wanda duk a aljihun yaya mahamud suka fita  .


Da kyar big dady yashawo kan Ummi dan tuburewa tayi ita fa  sam bata yarda da wannan aure ba , big dady ne  yace Ai tunda dai yara sun hada kansu km suna so junansu  Ai Ina Gani  magana takare fatanmu Allah ya zaunar dasu lfy .
Tace Ameen.


 Lokacin da aka sanar da DEENi ansa ranar auren  wata biyar , Yace  wa yaya mahamud anya kuwa lokacin nan bai yi yawa ba kuwa ? 
   ,Dan akwai aiki da zai kaini  akwaibon Ina Ganin zaifi kyau a takaita lokacin koma ba dan haka ba ,anawa ra'ayin nafi son ayi komai nan da wata uku   yaya mahamud yace Shikenan kabari dai zan samu Ummi da maganar  .


  Zaune take a cikin extra room dinsu wanda kusan yanzu can tafi zama tunda aka sa musu rana da yaya DEENi ta zabga uban tagumi tana mamakin hali irin na yaya DEENi yau kusan wata biyu Keenan dasamusu rana Amman ko sau daya bai taba kiranta da sunan zance ba  haka nan ko cikin part din Ummi yashigo, bata ishe shi kallo ba   takan ji tsoro da frigice sun shigeta a duk sanda taga yaya DEENi nuna rashin damuwarsa akanta ,a kasan ranta tace, anya kuwa banyi kuskure da wautaba wajen  saurin amincewa aurensa ba  domin fa zuwa yanzu tasoma sarewa anya kuwa yaya DEENi yana sonta ?
kullum miskilancinsa sake gaba yake har  zuwa yanzu dabatason cikakken matsayin ta a gurinsa ba ,son auren yasoma fice mata arai   domin ita kadai tasan fargaban da take cikin zuciyarta ga ,gorin da Ummi kebinta dashi kullun garin Allah ya waye , dan haka ta yanke hukunci samun yaya faruk dan ta inda aka hau tanan ake sauka .ta shirya taje har part dinsu tace daman tazo ne akan maganar mu da yaya DEENi idan fa abin nan bazai yiwu ba gara tun yanzu   abarshi  .

Fk ya gyara tsayuwa sannan yace wani abu ne ya faru ? Tace to yaya faruk a haka ne zamu fahimci juna in San abinda yake so shima yasan wanda banaso shi fa aure ba banza bane kmr yadda ya dauki komai tacigaba bai taba kirana ba km ko gida yashigo ban ishe shi kallo ba  shi bashi da lokacin kowa sai na kansa fk yace kiyi hakuri bawai zangoyi bayansa ba aikine yayimasa yawa kiyi nasa uziri Amman kina ranshi zeenat ta tabe baki dan tasan karya ne yace wai tana ran yaya DEENi Ai abinda kake son baka sakaci dashi  fk yacigaba  komai yakusan zuwa karshe da zarar kin zama a gidansa nasan dole ya baki dukkan lokacin sa ,zeenat tayi shr ne kawai ba wai dan maganar tashigeta ba  ,  fk yace tayi hakuri zai masa magana da sauri ,zeenat ta dago tace dan Allah yaya kar kace ni nayi maka maganar ya sake dubanta sosai yaga duk ta wani frigice yace karki damu ni nasan abinda zanyi     .


Fk yakira deeni a waya Amman ba'a daga ba

Da misalin karfe goma na dare fk ya amsa kiran DEENi tare da yin sallama byn sun gaisa yace friend dazo inata kira baka daga ba DEENi ya runtse ritattun idanunshi tamkar na may  jin bacci sannan yace wlh aiki ne yasha kaina lafiya dai ko ya fadi cikin kasala dan duk a gajiye yake fk yace lfy dama akan maganar yarinyar nan ne yakama mushirya muje zance gurinta , ,anhakali DEENi ya bude idanunshi  jin abinda fk yace muryasa a sarke yace  wacce yarinyar km?

Fk yace sai karinka yin kmr baka san da zance ba ,byn nasan tana ranka DEENi yace dan malam karkadameni go to the point dan bangane wacce yarinyar kake nufi ba fk yace Ai dole ka manta da ko wacce yarinya ce tunda kaga kasameta  cikin kwanciyar hankali  km Ummi ta amince ,tsaki yaja kana yace wai zeenat kake nufi ?
Yasake jan wani tsakin mtssss wani irin hira kum kmr muna kauye byn angama magana sai jiran lokacin  fk yace kai mugun dan iska ne Ai duk da haka yakamata muje dan ita yarinyar tasan  raayinka kai ma haka ku samu fahimtar juna DEENi ya katse shi da itace Keenan ta aiko ka fk yace ko daya ni dai naga dacewar haka DEENi yace to baza'aje ba ...  Kar Allah yasa  mu fahimci juna, ita tun tasowarta, bata san abinda nake so da wanda  ba,fk yace idan ita tasan abinda kake so da wanda baka so kai kasan nata ?

DEENi ya sake jan tsaki hade da kamo lip's dinshi na kasa yana dan ciccizawa sannan ahankali yace to sarkin yakinta ni ba haka taarina da raayina yake ba  Ina tunanin in har zanje zance gurin budurwar ,zanje ne dan tallar kaina in samu gindin zama to ni narigada na samu shigar ,bbu dalilin da zai sa na takurawa kaina me kadauki ni ,nafa san irin son da yarinyar nan  take min ,kawai dai ni banda lokacin wannan shirme dakace  km nasan ita ta aiko ka fitowa ne kawai bazakayi kafada ba .


Fk yaja tsaki shima yace kai ,dan Allah wani irin bahagon mutun ne?

To wlh ka canza wannan budadden halin naka, to ko waya ce ka tsiya mata  ,DEENi yace shima din baza'a tsiya ba  ,duk abinda zai faru ya faru ciki har da fasa aurena ,fk yace kai fa kafiyye kafiya ,da maida karamar magana tazama babba ,. yace sake cewa  yanzu dai kayi hakuri dan girman Allah ka Sai mata ko karamar  waya ce.

   DEENi yace kasan Allah ko game  bazan  Sai mata ba ,  ballanantana waya ,  tunda har taiya zuwa ta sameka da maganar bana kiranta   fk yace kadaina cewa tasameni ni kawai Gani nayi ya dace muje DEENi ya tabe baki tamkar fk din  na ganinsa Shikenan kai ka sani ni km kar ka sake damuna da maganar wata yarinya ya kashe wayarsa batare da ya tsaya jin abinda fk zai ce ba  .

Wasa wasa lokacin bikin ya dinga karatowa da kwanaki ya wattani har zuwa yanzu dayayi sauran wata cif cif ayi daurin aure  to Ganin kurewar lokaci yasa DEENi yasamu Ummi da maganar shifa baya son zamansa cikin estate din  taje Ummi tayi kicin kicin da ranta sannan ta dago tana dubansa tace bangane abinda kake nufi  ?
Sai da  ya sake maimaita mata tukun Ummi tace sam ita bata yarda ba salon yaje yana dinga cin amanar Yar marainiyar Allah ga babbin gurin bid dady yasa an Gina musu shida sauran enuwansa shine kai dan iyayi zaka ce bazaka zauna ba ,to wlh kaji na rantse anan zaku zauna Sai naga yana yin zaman naku  cikin yin kasa da murya yace Shikenan first lov na hakura duk abinda kika ce shi za'a yi tace da dai yafiye ma a yi mutun Sai girman tsiya da iyayi yace to kiyi hakuri .

Zeenat dake sauransu ta lumshe idanunta jin Ummi bata amince ba dan tana matukar jin tsoro zaman daga ita Sai shi ahankali cikin sanyi jiki ya mike idanunshi suka sauka akan inda zeenat ke kwance  suka hada ido da sauri ta gaidashi  hade da  dauke idanunta ,bai sake kallonta ba bare ya amsa gaisuwar ta  .


Shirye shiryen biki ya tashi gadan gadan  enmata duka   a tare suke shirinsu dan yanzu zeenat ta saki da shemah sun koma kmr da ganin da tayi wanda ma take haukar akansa bai san da zamanta ba wata safiya suka shirya zuwa siyayar su irinta amare mutun biyu ne abayanta mota Maryam da shemah yayinda zeenat ke gaba kai tsaye kasuwar Lagos  suka nufa sukace derive yayi parking a idimota su kum suka shiga cikin market din   


Derive yaja ya tsaya suna fitowa da yaya kamil suka soma cin karo  tun shigowar motar dayaga hango zeenat zaune ya zubawa motar ido har sanda ta fito ahankali suka jiro suna hira Amman banda zeenat dataji gabanta ya yanke ya fadi dan tun lokacin da aka mata rana ,rabonta dashi dai dai sun kusan geftashi yakira sunnanta zeenat..... tacigaba da tafiyarta dan batason abinda zai km hada ta dashi cikin sassarfa ya biyo bayanta yasha gabanta cak taja ta tsaya suna kallon junansu,yayinda su Maryam suka cigaba da tafiyarsu suna tsaye batare da dukkansu suyi yunkurin yin magana ba kamil ya gyara tsayuwa ya tura  hannuwansa duka cikin aljihun wandonsa  ya kafeta da  idanunshi ta sunkuyar da kanta kasa sannan tace lfy yaya ka tsayar dani muryasa a dashi yace lfyr ce takowa haka yanzu zeenat kin kyauta kennan ki zabi wani kibarni byn duk lokacin dana dauka Ina fama da soyayyarki ,a she kinsa bakya sona kibarni inata faman hauka akanki  tace Allah yaya ba haka bane Amman kayi hakuri dan Allah, ya sake gyara tsayursa , yayinda idanunshi ke kanta har  yanzu   yace iya hakuri ne kawai zai wadatar da zuciyar da tayi sama shekara biyu tana mata da miki so.... yace Shikenan bbu komai  Nagode Kwarai da abinda kika saka min tace ka dauka haka Allah yaso ni din ba matar ka bace yayi murmushin karfin hali sannan yace haka ne fa al'amarin ubgj  Amman agaskiya DEENi ya cuceni ,tace kabar cewa ,tayi ta dago suna kallon juna fuskarta dauke da murmushi  ta bude baki kennan Sai ga motar DEENI ta kuno kai cikin compound din km shi suke facin Ai take maganar ta ta tsaya sakamakon  DEENi data Gani zaune a mota yana kallonsu duk kasancewar akwai dan duhun magariba hakan ba zai sa takasa gane bscin ransa ba  , gabanta ya yanke ya fadi  ,  ,shima kamil din shr yayi bai sake yin magana va kusan minti goma yayi yana kallonsu koda bata ga fuskasa sosai ba tasan  a daure take  ,har sanda  DEENi ya fito yayi matarsa key  idanunshi na kansu ,cikin tsoro da frigice zeenat tace ni zanshiga ciki ,kamil  yace Shikenan Allah yabaki zaman lfy ta gefensu yazo yazo ya gifta hade da  jan  tsaki sannan ya wuce .   a filli ta furta wayo Allahna nashi uku kamil ya sake yin murmushi dole sannan yace da'aka me,da kika shiga uku,  nifa Banga abinda ya birgeki a DEENi ba,har da kika iya zabarsa , kalli fa yadda jikinki ke rawa saboda Allah tamkar kinga wani malaika tsaki taja hade da zabga masa harara dan Allah kabarni naji da damuwa Ai duk kai kaja min matsala Ina zaman zamana da yanzu Ina cikin gida


MMN SUDAIS CE💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO



Page 21-22



Wani irin kallon mamaki fk yake masa , ,gabadaya ya zamo  tamkar mutun mutimi a zaune a gurin ,

Yarasa meke damun brain din DEENi , mutun Sai girman kan tsiya da nuna isa " wai shi  DEENi wani irin bahagon mutun ne ?
Shi sam  bbu ruwan shi  da fadar duk magana da tazo bakinsa  .

In a low voice   fk yace yanzu duk wahalar danayi akan yarinyar nan yatashi a banza kennan?

A'a bakayi a banza ba tunda gashi "zan aureta gaskiya ce dai na gaya maka,dan kasan  ita din ba ra'ayina bace .
Amman narasa dalilin da yasa zuciyata ke muradin kasancewa tare daita " fk ya sake dubanshi  sannan yace  dan rainin wayo kawai kar  mai dani  kmr wanda bai san komai ba mana .
 ,tunda har zuciyarka ta iya amincewa daita, har kaji zaka iya aurenta  definitely kana sonta" ko yaya ne" ,.
deeni yaja tsaki hade da furzar da iska ta bakinsa" matsala dakai kennan rashin saurin fahimta fk yace idan son da kake mata ne ,na fahimta ,Amman kace wai kai baka sonta km kake kokarin aurenta , wannan ne fa bazan taba fahimta ba , DEENI ya sake first da huci may zafi ranshi tasoma baci muryasa a sarke" yace da alamun kana son musamu matsala dakai fa" muddin  baka daina cewa Ina son yarinyar nan ba .

 Idan km kafin son haka ya daga kafadarsa alamun Shikenan , parlour ya dauki shr na wani "dan lokaci yayinda  deeni ya jingina bayansa da kujera da yake zaune, hade da runtse idanunshi ya dan jin daci maganar fk 'ta yaya ma " zai nace akan yana son yarinyar byn shi yasan  aure kawai yake da bukatar yi bawata ,aba soyayya ba ...
   maganar fk ce ta daki dodon kunnenshi" to yanzu meyye solution tunda yarinya ta rigada ta amince ?


Ahankali ya bude rikitattun idanunshi ya sauke su ,akan fuskar fk sannan  yayi magana cikin sanyi tamkar wanda aka takura masa. Yace karkadamu zan samu yaya mahamud ,Ai kagama may wuyar "ya maida idanunshi ya sake lumshe su tamkar dai yadda yayi dazu  .
 girgiza kai kawai fk yayi uhmm shi wannan  bazai taba canzawa zai ba .
halinsa, na nan kmr dai yadda yasan shi" haka km yataso "  shi komai baya so matsawar ba ra'ayin sa bane" duk yayi magana ne akasan ransa,,.
 Ganin ya bawa banza ajiyarsa yasa shima ya mike yayi masa sallama .

 
Daga gurin DEENi kai tsaye fk part dinsu shemah yayi  yaja ya tsaya byn ya tura ayi masa kiranta fk  tafito sanye da doguwar rigar  material  puppy colour mai shegen kyau hade yane kanta da karamin mayafe baki ahankali take isowa gareshi duk step daya Sai kirjinta ya motsa tun fitowarta ya zubawa kirjinta ido kyam yana kallon yadda kirjinta ke motsawa lumshe idanunsa shi yayi na wani lokacin sannan ya sake budesu ahankali mutuwar tsaye a gurin har takaraso inda yake ta gaisheshi cikin sanyi jiki bai dauke idanunshi akanta ba yacigaba da da binta mayataccen kallo da sallamarta iso inda yake  ta gaisheshi ya amsa yana sake bin koina na jikinta da kallo cikin sanyi tace  yaya faruk Gani Yace Ai naganki ,daman nazo ne na fayace miki abinda na dade Ina boyewa akanki ,nan dai yasanar mata koma , tunda yasoma magana tayi shr  kawai hade da sunkuyar da kanta badan tana jin dadin abinda yake kokarin fahimtar dai ba ahankali ta dago ta zuba masa idanunta  Sai data tabbatar ya gama fadar abinda yakawoshi sannan tace ,dan Allah yaya kayi hakuri wlh akwai wanda zuciyata ta dade da kamuwa da soyayyarsa , Amman kayi hakuri idan maganata ta bata maka rai ,yace Ina Gaza bata min rai Ai iya gaskiyar ki kika fada Sai dai ki sani zuciyata bazata iya hakura dake ba Amman zan baki lokaci yi tunani akai tace nifa bawani tunanin dazanyi akai ka dai yi hakuri ka nemi wata ,ta juya ta wuce tabar sa nan tsaye ,da mamaki yabi bayanta da kallo ya dauki lokacin tsaye a gurin batare yasan abinda zaiyi ba , Ganin tsayuwa nasa bata da wani amfani yasa yasoma kokarin daga kafafunta  ahankali  tafe yake yana saka da warwara da tunanin malomasarsa a gurinsa ,a fusace  shemah tashiga part dinsu tana zuba tsaki da zage zage har mmnta ta tambayeta abinda yasameta tace matabakomai.

Byn kwana biyu 

Da misalin karfe takwas na dare  fk  ya km samu shemah da zance shi fa ba zai iya wani hakura daita ba kawai tayi hakuri ta amincewa da bukatar domin shi   yana matukar  son ta  km aurenta yake son yi ,tace dan Allah yaya  kayi hakuri   wlh da bbu wanda nake so ne ,zan iya soka dan kaima baka rasa komai da zankika ba ,  kadai yi  hakuri kawai .
al'amarin dayayi matukar dagawa fk hankali kennan ,yayi shr kawai yana kallon yanayinta tare da nazarin kalamanta masu kokarin tarwatsa masa zuciyar rasa yadda zanyi daita yayi can dabara tazo masa,ya tsareta da idanunshi  Yace ke banso iskanci da rainin hankali fa  ni zaki cewa kina da wanda zaki kike so  byn  Banga uban da  kike  saurara  ba ,lafazinsa yayi mugun bata mata rai dan haka a ranta abace  tace to dole ne Sai na aurenka kaje Kanemi wata mana ko ana soyayya dole ? ta juya a fusace  zata bar guri ,ya fizgota hannuta , gabadayanta ta fado jikinsa , idanun ta zaro a tsorace, ,take taji  wani irin faduwar gaba , .
Hannuwansa dukka  yasa  rungumeta tsam ajikinsa yana sauke ajiyar zuciya daidai kunneta ya kai bakinsa Yace  maimaita abinda kikace Ina jinki cikin tsiwa tace wannan wani irin iskanci dazaka wani  rungume mutun ?  Ok nine ma nake miki iskanci ?
Uhmmmm fa shemah karkibari muyi haka dake zaki amince ta girma da  arziki ne ko km na jawo soyayyata ta karfin tsiya ,.batare da na wahalar da kaina ba muryarta na rawa tace anki a amince da soyayyarka .
ko ana so dole ne ?
, dan Allah ni kasake ni ,ya zuba mata manyan idanunshi  kawai ,yasoma yawo da hannushi a jikinta  gabadaya jikinta ya  dauki kirma abinda bai taba faruwa daita ba kennan tunda take arayuwar ta ,wai namiji ya rabi jikinta har  takaita ga runguma ,dan takaici ma batasan sanda , kwalla ta cicciko a idanunta ba , hawaye yaga yana silalowa daga idanunta ahankali ya sauke ajiyar zuciya, ya dan sausauta rungumar da yayi mata  yasa yatsansa ya dangwalo hawayen dake bin fuskarta yana kallo Yace duk wannan kukan akan nace Ina sonki ne kike zubda hawayen ki?
  ,tayi shr taki cewa komai dan haushi ji tayi kmr ta daura hannuta akanta ta kurma ihu  , ahankali ya sake maida ita jikinsa ya rungumeta yana shinshina wuyanta  daidai nan Sai ga big  dady dake dawo daga masallaci , a tsorace yake binsu da kallo cike da mamaki da alajabi abinda yagani , meke shirin faruwa km yau acikin zuri'arsu ,fk yacigaba manneta da jikinsa yana rarrashi ta amincewa aurensa , dagowar nan da zai  lyi  karaf idanunsa suka sauka kan big dady dake tsaye duk da duhu ne hakan bai hana gareshi ba  gabansa yaji yayi muguwar faduwa jikinsa ya dauki kirma duk da ya tsorata Amman yaji dadi Ganin da big dady yayi musu ,yasan hakan zai sa a aura masa shemah  batare da bata lokaci ba tsabar frigice yasa yakasa rabata da jikinsa gabadaya jikinsu rawa yake shemah da batasan wainar da'ake tuyawa ba sake   lafewa tayi ajikinsa saboda irin rungumar dayayi mata ba wacce zata iya kwacewa bace har big dady ya wuce su a gurin shemah batasa big dady yagansu , ahankali fk  yasoma rabata da jikinsa  har zuwa yanzu hawaye bai daina bin fuskarta ba hannuta yakamo yasoma tafiya ita kum tana biye dashi bbu wanda ya iya cewa dan'uwansa komai har yakawo part dinsu yaja ya tsaya ahankali Yace shemah kiyi hakuri dan Allah kibar kuka ba nufi na kuraki ba Ina matukar kaunarki bansan lokacin dana fara sonki ba Amman zan baki lokacin kiyi tunani akai ,zan dawo zuwa jibi yana gama fadar haka ya juya da kyar yake iya daga kafafunsa tsabar frigice da nauyin da suka masa zuciyarsa tamkar zata buga , dan fargaba haduwarsu da big dady shi yasan ba makuwa tunda har big dady yagansu aure kmr anyi an gama Amman kunya fa ,har ya iso part dinsu wanda kusan nan samari suke zaune  wayanda basuyi aure ,
     

Itama tana shiga dakisu ta wuce kai tsaye tana kuka , mamanta dake zaune a parlour tace ke lafiyarki Amman ko juyo batayi ba fadawa tayi kan gado tana risgar kuka to meye yaya faruk yake nufi daya sonta  alhalin ita DEENi take mutuwar so ..... Dan haka bata taba aurensa ba ,tunawa datayi ba'a musu auren dole a family dinsu sai sun amince da juna yasa taji hankalinta ya kwanta Amman gabadaya jikinta yayi bala'in sanyi haka ta wuni a daki batare data sake fita ko parlour ba ,fk bai dawo ba kmr yadda Yace mata kusan sati tsakani shiyasa tayi tunanin ko yayi wa kansa fada ne ya hakura daita dan haka ta sake abinta kwasam Sai gashi a wani daren lahadi byn tagaishi a dage ,yayi murmushi yace yazo ne akan maganar su ,a fusace tace wata magana kennan i tough mun gama da wannan zance tunda nace ban sonka , Yace haka kika ce ,tace eh ko dole soyyaya dakai ,Yace uhmm Amman dolenki ki aureni ya wuce batare da damuwa ,



DEENi yasamu yaya mahamud yayi masa bayanin shi kuma ya samu big dady da zance  tsohon yaji dadi Sosai jin sun hada kansu yace Shikenan bbu damu zai tuntubi yarinyan tukun asan abinyi .



Nan dai aka saka ranar aure   tare da yanka sadaki yaya mahamud ne yayi komai ko sisin Kobo bata fita daga aljihun ogo deeni ba ko mahaifin zeenat yayi murna sosai da jin DEENi ne zai aure diyarsa 

Anyaka sadaki da dukiyar aure  naira duba  dari biyar wanda duk a aljihun yaya mahamud suka fita  .


Da kyar big dady yashawo kan Ummi dan tuburewa tayi ita sam bata yarda da wannan aure ba big dady yace Ai tunda dai yara sun hada kansu km suna juna Ai Ina Gani  magana takare fatanmu Allah ya zaunar dasu lfy .

 Lokacin da aka sanar da DEENi ansa ranar wata biyar deeni Yace  wa yaya mahamud lokacin nan bai yi yawa ba kuwa ?

Dan akwai aiki da zai kaini  akwaibon Ina Ganin zaifi kyau a takaita lokacin koma ba dan haka anawa raayin nafi son ayi nan da wata uku   yaya mahamud yace Shikenan kabari dai zan samu Ummi da maganar  .


  Zaune take a cikin extra room dinsu wanda kusan yanzu can tafi zama tunda aka sa musu rana da yaya DEENi ta zabga uban tagumi tana mamakin hali irin na yaya DEENi yau kusan wata biyu Keenan dasamusu rana Amman ko sau daya bai taba kiranta da sunan zance ba  haka nan ko cikin part din Ummi yashigo bata ishe shi kallo ba   takan ji tsoro da frigice sun shigeta a duk sanda taga yaya DEENi nuna rashin damuwarsa akanta ,a kasan ranta tace, anya kuwa banyi kuskure da wautaba wajen  saurin amincewa aurensa ba  domin fa zuwa yanzu tasoma sarewa anya kuwa yaya DEENi yana sonta ?
kullum miskilancinsa sake gaba yake har  zuwa yanzu dabatason cikakken matsayin ta a gurinsa ba ,son auren yasoma fice mata arai   domin ita kadai tasan fargaban da take cikin zuciyarta ga ,gorin da Ummi kebinta dashi kullun garin Allah ya waye , dan haka ta yanke hukunci samun yaya faruk dan ta inda aka hau tanan ake sauka .ta shirya taje har part dinsu tace daman tazo ne akan maganar mu da yaya DEENi idan fa abin nan bazai yiwu ba gara tun yanzu   abarshi  .

Fk ya gyara tsayuwa sannan yace wani abu ne ya faru ? Tace to yaya faruk a haka ne zamu fahimci juna in San abinda yake so shima yasan wanda banaso shi fa aure ba banza bane kmr yadda ya dauki komai tacigaba bai taba kirana ba km ko gida yashigo ban ishe shi kallo ba  shi bashi da lokacin kowa sai na kansa fk yace kiyi hakuri bawai zangoyi bayansa ba aikine yayimasa yawa kiyi nasa uziri Amman kina ranshi zeenat ta tabe baki dan tasan karya ne yace wai tana ran yaya DEENi Ai abinda kake son baka sakaci dashi  fk yacigaba  komai yakusan zuwa karshe da zarar kin zama a gidansa nasan dole ya baki dukkan lokacin sa ,zeenat tayi shr ne kawai ba wai dan maganar tashigeta ba  ,  fk yace tayi hakuri zai masa magana da sauri ,zeenat ta dago tace dan Allah yaya kar kace ni nayi maka maganar ya sake dubanta sosai yaga duk ta wani frigice yace karki damu ni nasan abinda zanyi     .


Fk yakira deeni a waya Amman ba'a daga ba

Da misalin karfe goma na dare fk ya amsa kiran DEENi tare da yin sallama byn sun gaisa yace friend dazo inata kira baka daga ba DEENi ya runtse ritattun idanunshi tamkar na may  jin bacci sannan yace wlh aiki ne yasha kaina lafiya dai ko ya fadi cikin kasala dan duk a gajiye yake fk yace lfy dama akan maganar yarinyar nan ne yakama mushirya muje zance gurinta , ,anhakali DEENi ya bude idanunshi  jin abinda fk yace muryasa a sarke yace  wacce yarinyar km?

Fk yace sai karinka yin kmr baka san da zance ba ,byn nasan tana ranka DEENi yace dan malam karkadameni go to the point dan bangane wacce yarinyar kake nufi ba fk yace Ai dole ka manta da ko wacce yarinya ce tunda kaga kasameta  cikin kwanciyar hankali  km Ummi ta amince ,tsaki yaja kana yace wai zeenat kake nufi ?
Yasake jan wani tsakin mtssss wani irin hira kum kmr muna kauye byn angama magana sai jiran lokacin  fk yace kai mugun dan iska ne Ai duk da haka yakamata muje dan ita yarinyar tasan  raayinka kai ma haka ku samu fahimtar juna DEENi ya katse shi da itace Keenan ta aiko ka fk yace ko daya ni dai naga dacewar haka DEENi yace to baza'aje ba ...  Kar Allah yasa  mu fahimci juna, ita tun tasowarta, bata san abinda nake so da wanda  ba,fk yace idan ita tasan abinda kake so da wanda baka so kai kasan nata ?

DEENi ya sake jan tsaki hade da kamo lip's dinshi na kasa yana dan ciccizawa sannan ahankali yace to sarkin yakinta ni ba haka taarina da raayina yake ba  Ina tunanin in har zanje zance gurin budurwar ,zanje ne dan tallar kaina in samu gindin zama to ni narigada na samu shigar ,bbu dalilin da zai sa na takurawa kaina me kadauki ni ,nafa san irin son da yarinyar nan  take min ,kawai dai ni banda lokacin wannan shirme dakace  km nasan ita ta aiko ka fitowa ne kawai bazakayi kafada ba .


Fk yaja tsaki shima yace kai ,dan Allah wani irin bahagon mutun ne?

To wlh ka canza wannan budadden halin naka, to ko waya ce ka tsiya mata  ,DEENi yace shima din baza'a tsiya ba  ,duk abinda zai faru ya faru ciki har da fasa aurena ,fk yace kai fa kafiyye kafiya ,da maida karamar magana tazama babba ,. yace sake cewa  yanzu dai kayi hakuri dan girman Allah ka Sai mata ko karamar  waya ce.

   DEENi yace kasan Allah ko game  bazan  Sai mata ba ,  ballanantana waya ,  tunda har taiya zuwa ta sameka da maganar bana kiranta   fk yace kadaina cewa tasameni ni kawai Gani nayi ya dace muje DEENi ya tabe baki tamkar fk din  na ganinsa Shikenan kai ka sani ni km kar ka sake damuna da maganar wata yarinya ya kashe wayarsa batare da ya tsaya jin abinda fk zai ce ba  .

Wasa wasa lokacin bikin ya dinga karatowa da kwanaki ya wattani har zuwa yanzu dayayi sauran wata cif cif ayi daurin aure  to Ganin kurewar lokaci yasa DEENi yasamu Ummi da maganar shifa baya son zamansa cikin estate din  taje Ummi tayi kicin kicin da ranta sannan ta dago tana dubansa tace bangane abinda kake nufi  ?
Sai da  ya sake maimaita mata tukun Ummi tace sam ita bata yarda ba salon yaje yana dinga cin amanar Yar marainiyar Allah ga babbin gurin bid dady yasa an Gina musu shida sauran enuwansa shine kai dan iyayi zaka ce bazaka zauna ba ,to wlh kaji na rantse anan zaku zauna Sai naga yana yin zaman naku  cikin yin kasa da murya yace Shikenan first lov na hakura duk abinda kika ce shi za'a yi tace da dai yafiye ma a yi mutun Sai girman tsiya da iyayi yace to kiyi hakuri .

Zeenat dake sauransu ta lumshe idanunta jin Ummi bata amince ba dan tana matukar jin tsoro zaman daga ita Sai shi ahankali cikin sanyi jiki ya mike idanunshi suka sauka akan inda zeenat ke kwance  suka hada ido da sauri ta gaidashi  hade da  dauke idanunta ,bai sake kallonta ba bare ya amsa gaisuwar ta  .


Shirye shiryen biki ya tashi gadan gadan  enmata duka   a tare suke shirinsu dan yanzu zeenat ta saki da shemah sun koma kmr da ganin da tayi wanda ma take haukar akansa bai san da zamanta ba wata safiya suka shirya zuwa siyayar su irinta amare mutun biyu ne abayanta mota Maryam da shemah yayinda zeenat ke gaba kai tsaye kasuwar Lagos  suka nufa sukace derive yayi parking a idimota su kum suka shiga cikin market din   


Derive yaja ya tsaya suna fitowa da yaya kamil suka soma cin karo  tun shigowar motar dayaga hango zeenat zaune ya zubawa motar ido har sanda ta fito ahankali suka jiro suna hira Amman banda zeenat dataji gabanta ya yanke ya fadi dan tun lokacin da aka mata rana ,rabonta dashi dai dai sun kusan geftashi yakira sunnanta zeenat..... tacigaba da tafiyarta dan batason abinda zai km hada ta dashi cikin sassarfa ya biyo bayanta yasha gabanta cak taja ta tsaya suna kallon junansu,yayinda su Maryam suka cigaba da tafiyarsu suna tsaye batare da dukkansu suyi yunkurin yin magana ba kamil ya gyara tsayuwa ya tura  hannuwansa duka cikin aljihun wandonsa  ya kafeta da  idanunshi ta sunkuyar da kanta kasa sannan tace lfy yaya ka tsayar dani muryasa a dashi yace lfyr ce takowa haka yanzu zeenat kin kyauta kennan ki zabi wani kibarni byn duk lokacin dana dauka Ina fama da soyayyarki ,a she kinsa bakya sona kibarni inata faman hauka akanki  tace Allah yaya ba haka bane Amman kayi hakuri dan Allah, ya sake gyara tsayursa , yayinda idanunshi ke kanta har  yanzu   yace iya hakuri ne kawai zai wadatar da zuciyar da tayi sama shekara biyu tana mata da miki so.... yace Shikenan bbu komai  Nagode Kwarai da abinda kika saka min tace ka dauka haka Allah yaso ni din ba matar ka bace yayi murmushin karfin hali sannan yace haka ne fa al'amarin ubgj  Amman agaskiya DEENi ya cuceni ,tace kabar cewa ,tayi ta dago suna kallon juna fuskarta dauke da murmushi  ta bude baki kennan Sai ga motar DEENI ta kuno kai cikin compound din km shi suke facin Ai take maganar ta ta tsaya sakamakon  DEENi data Gani zaune a mota yana kallonsu duk kasancewar akwai dan duhun magariba hakan ba zai sa takasa gane bscin ransa ba  , gabanta ya yanke ya fadi  ,  ,shima kamil din shr yayi bai sake yin magana va kusan minti goma yayi yana kallonsu koda bata ga fuskasa sosai ba tasan  a daure take  ,har sanda  DEENi ya fito yayi matarsa key  idanunshi na kansu ,cikin tsoro da frigice zeenat tace ni zanshiga ciki ,kamil  yace Shikenan Allah yabaki zaman lfy ta gefensu yazo yazo ya gifta hade da  jan  tsaki sannan ya wuce .   a filli ta furta wayo Allahna nashi uku kamil ya sake yin murmushi dole sannan yace da'aka me,da kika shiga uku,  nifa Banga abinda ya birgeki a DEENi ba,har da kika iya zabarsa , kalli fa yadda jikinki ke rawa saboda Allah tamkar kinga wani malaika tsaki taja hade da zabga masa harara dan Allah kabarni naji da damuwa Ai duk kai kaja min matsala Ina zaman zamana da yanzu Ina cikin gida💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO



Page 21-22



Wani irin kallon mamaki fk yake binsa dashi , ,gabadaya ya zamo  tamkar mutun mutumi ,a zaune a gurin ,

Yarasa meke damun brain din DEENi , mutun Sai girman kan tsiya da nuna isa ,fk ya dinga masa kallon bahagon   mutun wanda 
Shi sam  bbu ruwan shi  da fadar duk magana da tazo bakinsa  .

In a low voice   fk yace yanzu duk wahalar danayi akan yarinyar nan yatashi a banza kennan?

 DEENi ya tabe bakinsa hade da cewa  A'a bakayi a banza ba tunda gashi "zan aureta gaskiya ce dai na gaya maka,dan kasan  ita din ba ra'ayina bace .
Amman narasa dalilin da yasa zuciyata ke muradin kasancewa tare daita ba "alhalin bata sonta nake yi ba .

 fk ya sake  dubanshi  sannan yace   dan rainin wayo kawai "kar ka  mai dani  tamkar wanda bai san komai ba mana .
 ,tunda har ita zuciyartaka ta iya amincewa daita, har kaji zaka iya aurenta  definitely kana sonta" ko yaya ne" .
,. Amman maganar kace  baka sonta,wanna ma ba gaskiya bane .

deeni yaja tsaki hade da furzar da iska ta bakinsa" sannan yace matsalata dakai kennan rashin saurin fahimta .

fk yace ta yaya kake so na fahimci wannan shime ?
 Alhalin ga zahirin gaskiya nan Ina Gani.

"  idan son da kake mata ne ,na fahimta wannan.
,Amman kace wai kai baka sonta km kake kokarin aurenta , wannan ne fa bazan taba fahimta ba.sai dai kayi hakuri ,

 DEENI ya sake furzar da huci may zafi ranshi yasoma baci muryasa a sarke" yace da alamun kana son mu samu matsala dakai fa" muddin  baka daina cewa Ina son yarinyar nan ba .

 Idan km kafin son haka  ya daga kafadarsa alamun Shikenan ,.
    parlour ya dauki shr na wani "dan lokaci, yayinda  deeni ya jingina bayansa da kujera da yake zaune, hade da soma jijiga kafarsa daya a tile's din dakin .
" runtse idanunshi Yayi dan jin daci abinda  fk din yace"
 'ta yaya ma " zai nace akan lallai yana son yarinyar byn shi yasan  auren kawai yake da bukatar yi" bawata ,aba soyayya ba ...

   maganar fk ce ta daki dodon kunnenshi" to yanzu meyye solution akan maganar, tunda yarinya ta rigada ta amince ?


Ahankali ya bude rikitattun idanunshi ya sauke su ,akan fuskar fk sannan  yayi magana cikin sanyi tamkar wanda aka takura masa dole. Yace karkadamu zan samu yaya mahamud ,Ai ka gama may wuyar " tare da maida idanunshi ya sake lumshe su tamkar dai yadda yayi dazu  .

 girgiza kai kawai fk yayi. shi wannan fa  bazai taba canzawa ba .

halinsa, na nan kmr dai yadda yasan shi" haka km yataso da murdanden ra'ayi "  shi komai baya so ,matsawar ba ra'ayin bane fk ya fadi haka haka kasan ransa,,.

 Ganin da fk yayi DEENi ya bawa banza ajiyarsa yasa shima ya mike yayi masa sallama yayi ficewarsa .

 
Daga gurin DEENi kai tsaye fk part dinsu shemah yayi  ,ba bata lokaci yasamu yaro ya tura ayi masa kiranta.
 dan ya kudirtawa ransa ,yau ce, ranar da zai isar da sakon zuciyarsa  gareta .
domin yagaji da cutar da kansa .

  tafito sanye cikin   doguwar rigar  material  puppy colour mai shegen kyau hade da yane kanta da karamin mayafe baki, 

ahankali take isowa gareshi duk step daya da tayi Sai kirjinta ya motsa sakamakon dukiyar fulani dake gareta.
tun fitowarta , ya zubawa kirjinta idanunshi kyam ko kyafta ido bai yi  .
yana kallon yadda albarkatun kirjinta ke motsawa, a duk takun datayi  lumshe idanunsa shi yayi na wani lokacin ,sannan ya sake budesu ahankali. mutuwar tsaye yayi a gurin "  har takaraso inda yake tayi sallama.
  bai dauke idanunshi "akanta ba .Sai ma  cigaba da yayi" da binta da wani irin   mayataccen kallo wanda yasa shemah tasha jinin jikinta.
Ganin irin duban da take masa ne yasa yayi saurin ,sauke idanunshi,tare da sakin ajiyar zuciya,   ta gaisheshi ya amsa cikin sakin fuska, yana sake bin koina na jikinta da kallo dan tayi masa kyau matuka ,rigar jikinta irin mai flay din nan ce daga kasa, Sai dai taka mata a samata sosai.
  cikin sanyi murya tace  yaya faruk Gani , Yace Ai naganki .

,yayi shr yana tunanin ta inda zai soma ,itama shr tayi Sai dai,haka kawai ta tsinci kanta da jin ,faduwar gaba.   haka nan kallon da yaya faruk din kema ,yasa taji wani iri ajikinta ,dan haka ,ta sunkuyar da kanta kasa kawai tana Jira daga gareshi.
 ,can ya  numfasa,hade da jin kwarin gwiwa yazo masa ,ya danyi gyaran murya" tukun yace daman nazo ne na fayace miki abinda na dade Ina boyewa akanki , .
Take taji gabanta yashiga faduwa ,ta dan dago kadan ,taga ita yake kallo , ahankali tace akan  mefa? 
Sannan ta km maida kanta kasa tana jin yadda gabanta ke lugude faduwa.
Yayi murmushi yana cigaba da kallonta, cikin natsuwa  da jarumta.
 yasanar mata da komai .

tun da yasoma maganar sa tayi shr  kawai hade da sake sunkuyar da kanta kasa, sosai badan tana jin dadin sauraron abinda yake kokarin fahimtar daita bane ,taji hankalinta ya yayi matukar tashi dan haka ,  ahankali ta dago kanta , ta zuba masa idanunta ,  Sai data tabbatar daya gama fadar abinda yakawoshi, a dan frigice tace ,dan Allah yaya kayi hakuri wlh akwai wanda zuciyata ta dade da kamuwa da soyayyarsa , Amman kayi hakuri idan maganata ta bata maka rai ,yace Ina fa za bata min rai Ai iya gaskiyar ki kika fada Sai dai ki sani zuciyata bazata iya wannan  hakuri dake bani ba, Sai dai zan baki lokaci kiyi tunani akai , tace  tunanin me km zanyi?byn na fada gsky nifa bawani tunanin dazanyi  ka dai yi hakuri kawai ka  nemi wata.
 ,ta juya ta wuce tabar sa nan tsaye .
,da mamaki yabi bayanta da kallo ya dauki lokacin tsaye a gurin batare da yasan abinda zaiyi ba , Ganin tsayuwa nasa bata da wani amfani yasa yasoma kokarin daga kafafunsa da suka masa mugun nauyi.
, ahankali yake daga kafafunsa   yana saka da warwara" da tunanin makomasarsa a gurinta .
 ,a fusace  shemah tashiga part dinsu tana zuba tsaki da zage zage iri iri har mmnta ta tambayeta abinda yasameta tace mata bakomai.

Byn kwana biyu 

Da misalin karfe takwas na dare  fk  ya km samu shemah da zance ,shi fa bai ji zai iya wani hakura daita ka " kawai tayi hakuri ta amincewa  aurensa .
   ,tace ni dai  dan Allah yaya  kayi hakuri karabudani,  wlh da bbu wanda nake so ne ,zan iya aurenka dan kaima baka rasa komai da zankika ba .
 kadai yi  hakuri kawai .

al'amarin dayayi matukar dagawa fk hankali kennan ,yayi shr kawai yana kallon yanayinta tare da nazarin kalamanta masu kokarin tarwatsa masa zuciyar rasa "
 yarasa yadda zaiyi daita,  can dabara tazo masa, dan haka ya tsareta da idanunshi  Yace ke banso iskanci da rainin hankali fa"  ni zaki cewa kina da wanda kike so  byn  Banga uban da  kike  saurara  ba.
   ,lafazinsa yayi,
💗💗💗💗💗
   AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO



Page 23-24





 Ni dan girman Allah kabarni na wuce tun kafin  laifina ya  Karu.

,Murmushi karfin hali kawai yayi ,tare da nuna mata hanya da hannushi alamun ta wuce din. 

 , kasa tafiya tayi " sakamakon idanushi da taji  yana mata yawo a gangar ajikinta  . Gabadaya taji tamkar ya daureta ne  .
takasa kwakwaran  motsi" jikinta yayi bala'in yin  sanyi.
 ,taji ina ma  zuciyarta na da yanci  da bata kamu da soyayyayar deeni ba. 

 Da bbu shakka zata  iya   hakura da kamil tunda shima yana da nashi kyawun daidai gwargwado . 

Yayi shr kawai yana kallonta" kaunarta ce ke tasomasa tare da  nukurkusan zuciyarsa.
 ,ya dinga jin  tamkar ya halaka kanshi     lokacin daya tsinci idanun deeni akan su.
 ya dinga kallonta "yana  jin yadda zuciyarsa ke tafarfasa " da gske dai yana shirin  yarasata kennan ,rashima na har abada.
 km ta haramta ta zama matarsa  wani irin zugi zuciyarsa keyi ahankali 
 Yakira sunanta..Zeenat   kina son deeni sosai ko ? Cikin sanyi 
 ta dago kanunun idanunta  ta kalleshi dasu  "sannan tace , wannan wace irin tmby ce ?  Yace amsa kawai nake bukata ,tace to bana son shi shikennan.
Karkimin karya mana Kina son shi kalli...kalli yadda yanayinki ya canza jikinki har rawa yake saboda  kin ganshi .
ya tabbata kennan baki sona ,rainamin hankali kawai kika dinyi  .

 
  A fusace Zeenat tace Nifa karka zageni da laifi da bansan na aikata ba. mgnr ina sonshi ko bana sonshi ma duk  bata taso ba .

 kai kanka kasan bantaba amsa  maka da  Ina sonka ba.
 ballanantana kace yaudararka nayi ka dai yi hakuri Allah ya hada  kowa da rabonsa  , yace ok yanzun  duk  tarin son da na miki yazama tarihi kennan ? 
Ta zuba mishi ido kawai dan tasan duk abinda zata gaya masa ahalin yanzu ba fahinmta zai yi ba shiyasa tayi shr taki cewa komai
 Ahankali Ya girgiza kanshi  kawai batare da  sake cewa mata komai ba  ya juya  yasoma tafiya.

 , Tayi jim  jikinta ya mata tsanyi ,bata ji dadin yadda taga reaction dinsa ba .
tasan kwata kwata bata kyautawa masa  ba. Amman ba yadda taiya da zuciyarta " DEENi shine muradin ranta .
   raba zuciyarta dashi tamkar barazana ce ga rayuwarta. 
Duk da taji ba dadi ba  hakan bai sa taji  tausayinsa yashigeta har taji zata iya hakura da auren DEENi . Dan haka ko ajikinta ta   wuce.
 
Jikinta a sanyaye yashigo part dinsu hankalinta a tashe 
 Tana shiga daki Ta daure fuskarta "ganin ya shigo dan a zatonta yana shigowa zai zabgamata mari.
 sanye yake  da t shirt din su na sojoji da wando.

 Tana jinshi yacewa Ummi shi ya wuce sai da safe "Ummi tace can zaka kwana  ne yau ?
yace eh "akwai abinda zai maidani  tace  to Allah ya tsare min kai ya km bada sa'a  ,ka yawaita  addu'a dan Allah yace Ina yi  sai dai zan kara kulawa .
ya sake wuce zeenat  zaune  ko kallon inda take baiyi ba .

 bayansa tabi da kallo tana jin wata irin masefaffiyar  kaunarsa nabin jininta,   hade da ratsa kowani part na jikinta.
, aranta tace attajirina kennan ,miskilili zaki maza .
nan ya fita yabarta da dadeden kamshinsa tare da  fargaba.
 sai dai, da ganin yanayinsa yana cikin tsananin  fushi .

 da misalin karfe tara dare  tana kwance akan gado" juyi kawai take, yayinda  zuciyarta ke   nazari akan irin  kallon da yaya deeni yayi mata, dazu  sakamakon  ganin  da yayi mata  tare da kamil .

ta ji tamkar takirashi tabashi hakuri amman tsananin tsoransa ya hanata aikata hakan , zuciyarta ce ta bata shawara kan tura masa text  ba sai takirashi ba .
dan haka ahankali ta mirgina ta janyo  wayar Ummi dake kan bedside .
 ta soma rubuta masa text da niyar turawa masa "  sai km  taji  zuciyata  na gargadinta akan kar ta sake ta tura masa text din  . Tayi tana tunanin ,ta tura ne ko ta share 
Tayi haka  ya   yafi sau goma kafin daga karshe tayi  jahadi ta tura masa  .

    Yaya dan Allah kayi hakuri idan na bata maka rai dazu wlh bazan sake ba ... daga zeenat 
 

 Byn ta tura sakon ne  ta goge "sannan takoma ta kwanta lamo tana jin yadda kirjinta ke tsarkewa ,ahankali  ta lumshe" idanunta ,xuciyarta ke beating tare da yi mata fadar abinda ta aikata .
ita kanta tasan tayi babban  kuskure sosai wajen tura masa  text ,dan tasha jin yadda yake yawan yi  complain akan tura masa sako  ko kiran wayarsa yayinda yake  kan  aiki , 
Sai dashi duk lokacin daya gadama zai kiraka   idan km baka dauka ba yazama matsala .
dan haka tayi shr kawai tana fidda numfashi sama sama .

Tsawon lokaci tana kwance "tana tunanin abinda zai biyo baya idan yaga sakonta , addu'a take Allah yasa ba karawa kanta laifi tayi ba agurinsa .

 take  tsoro da fargaba suka taru suka   dira  mata " alokaci daya.
   Idanunta a lumshe har lokacin tana saka da warwara  deeni dan ra'ayi baka masa dole ballanantana ta tursashi .

 can taji alamun shigowar  sako a zaburi ta mike" ta  rarumi wayar jikinta har rawa yake .
 idanunta ne suka ci karo da reply dinsa .
hankalinta a tashe  tasoma karanta text din .


   Ke ... Banida lokacin karanta wannan shirmen naki na baza , aikina yana da mahimmanci a wajena  banida  lokacin hada aikina da zantuttukan marasa ma'ana  dan haka ki kiyaye gaba   ..


Tana gama karantawa ta sauke ajiyar zuciya sannan ta  sulale takoma ta kwanta tare da  lumshe idanunta.
Tabbas tasan ta  daukarwa kanta abinda yafi karfinta .
 tayi shr  ,tana son tayi nazari akan kalamansa tasan dai yakaranta sakonta sarai  . 

tsabar rainin wayo ne  da miskilanci  irin nasa .
yasa ya nuna kmr bai da lokacinta  . 
tayi juyi tana mai    tausayawa kanta na nacewa  auren DEENi.
 yanzu Gabadaya son  aurensa ya sire mata ya fita akanta.
,  tsoro aurensa take  km sai yanzu maganganun Ummi ke sake  shigarta .
Inda tace  zeenat ,kin fahimtata ne kawai    deeni  dana ne dana haifa a cikina.
baki fini sonshi ba sanin halin miskilancinsa da girman kai irin nasa  yasa kikaga naki amincewa da aurenku  wahala kawai zakisha a hannushi    .
 , gara yaje waje  can ya nemo matarsa.

 batayi aune ba taji saukar hawaye nabin kuncinta" bata hana su zubowa  ba  ,domin ita kanta zata fi so   ta zubar dasu  ,kodan samun natsuwarta.
Km  ko ba komai hakan  zaisa taji  sanyi da ragewa kanta radadin  abinda ke nukurkusan ruhinta.

Jikinta yayi matukar yin tsanyi ahankali  tasoma sambatu ..
  Wayo Allahna... ni zeenat yaya zanyi da zuciyata data  ta makance akan kaunarka. 

Ina sonka yaya deeni har bansan yadda zan misalta tarin soyayyata  gareka ba.
 kaunarka ajinina da ruhina yake .
daita Allah ya hallice . bazan iya daina sonka ba muddin rai  .
koda baka sona ni Ina sonka km zan iya jurar komai akanka  ,raba zuciyata da soyayyarka tamkar rasa numfashina ne .
 Haka tayi surutai har sanda Tajiyo  motsen shigowar Ummi .
tayi shr tare da  saurin  juya mata  baya.
 tana cigaba  kukanta, kasa kasa  batare Ummi ta Gane halin da take ciki ba .
Zuciyarta ke mata wani irin ciwo da radadi mai zafi . 


Washegari ma  sukusuku ta tashi tamkar wace batada lfy ta rame sosai  " idanunta a kumbure   kallo daya Ummi tayi mata ,ta Gane kuka tayi .
km daman tana lura daita jiya bawani baccin kirki tayi ba .
 taji wani irin tausayinta ya tsarga mata har cikin zuciyarta "dan tasan tunda ta kwallafawa ranta auren DEENi , ta hadu da babban  aiki .
km sai ta hadu da abinda yafi haka.a addu'a dai zata cigaba  dayi musu Allah ya kauda fitana atsakaninsu.

Ahankali  Ummi takira sunanta ...ta dago  da kumburarun idanunta tana kallon Ummi dasu batare da tace mata  komai ba byn gaisuwar datayi mata .
 ,Ummi tace meke damunki ne  zeenat naga duk idanunki duk sun kunbura"  sai naga  ma kmr kuka kikayi .

Zeenat ta danyi murmushi dole sannan  tace kai Ummi bbu komai fa, idanuna kemin ciwo ,km jiya  da ciwon kai na kwana .
ta fadi hakan da hankalin Ummi ya kwanta .

Ummi  tayi shr kusan minti goma  tana kallonta sai da  tagama nazarinta tsab sannan ta numfasa tace shikennan Allah ya sawake kinsha magani ?
Zeenat ta girgiza kai kawai.
  Ummi tace maza ki tashi kije daki  ki dauko magani kisha.
 a sanyaye ta mike jikinta babu  kwari tace to ...
 tare da shigewa kitchen dan bataji zata iya shan wani magani a halin datake ciki  yanzu  ,dan tasan  ko tasha  bazai taba yi mata maganin damuwarta.

   kusan duk dare sai bacci ya katse mata  sakamakon tunanin DEENI da  hali ko in kula da yake nuna mata .
, shi sam mutun ne da  babu ruwanshi da wani damuwa harakar gabansa kawai yakeyi hankalinsa kwance  .


tayi shr cikin zullumi irin  zaman da zatayi da DEENi,a zahirin ce  tagama  duk wani tunani da zatayi akansa ,amman sam  bata hango wani jin dadi ko kulawa  da za samu aurenta  dashi ba .


Sai yanzun take gane manufar Ummi" tana guje mata wahala ne yayinda ita km ta kasa fahimtar hska . gashi yanzu lokaci ya kure mata bata da daman tace ta fasa  .


Misalin karfe takwas na dare .
 kwance take   a parlour kan doguwar kujerar three site .
hannuta rike da wayar Ummi ta juyata idanunta kuru akan   TV .zaka dauka ko  kallo take .
   amman a hakikanin gaskiya  kallo daya  zaka mata ka  gane  Gabadaya hankali bai gurin TV .
 tana can ta lula cikin  duniyar tunani tunani .

 , kamshin turarensa ne ya ankarar daita ,take tayi firgigib  da  dawo  duniyar kasa dan tasan tunda Tajiyo kamshinsa yana kusa kennan dan haka  ahankali ta dan juyo tsaitin datake jiyo kamshin nasa  , ahankali idanunta  suka  cin karo da kyakkyawan fuskarsa ko kallonta inda take baiyi ba  , yakarasa shigowa parlour  fuskar nan tashi a daure tamkar zaki  .

  ,take taji zuciyarta ta tsinke tasoma rawa   wata irin  zazzafar kaunarshi ce ta dinga taso mata tamkar ta tarwatsa mata zuciya  , lokacin data daura idanunta kansa.

 kamshin turarensa ya addabi hancinta ji take kmr  tajita a kusa dashi .
  sallama  Yayi aciki.
 ta amsa tare da sunkuyar da kanta kasa har ya wuceta yasoma taka step bata dago da kanta ba, sai da tabbatar da  tadaina jin motsen takunsa" sannan ta dago tana sauke ajiyar zuciya tare dafe kirjinta tace wayoooo Allah kirjina .
 dan ita kadai tasan yadda ta dinga ji  .
can taji sautin shigowar sako a wayar Ummi " ,sharewa tayi tunaninta ko yan  network ne.
   Dan haka ta maida hankalinta kan shirin da'ake gabatarwa a TV.
    minti biyar tsakani taji wayar ta dauki kara ta dauki wayar tana dubawa .
 Wata bakuwar number tagani" yana yawo akan screen din .
  Dan haka ta manna wayar a kunneta tare yin sallama .
 muryar   da tafi so da tsoro ne "ta daki dodon  kunneta hakan yasa  jikinta ya sake  daukar rawa gabanta yashiga faduwa  da sauri .

,yace   ke dan iskanci da rainin wayo  bakiga sako na bane ? 
Muryarta A sanyaye tace ban gani ba Amman kayi hakuri dan Allah tsaki yaja tare da   kashe wayarsa .
Da sauri tashiga in box din  tasoma  duba sakon 

      Kisame ni a dakina yanzu " abinda tagani kennan .


 ,take gabanta yacigaba da faduwa   , duk da tana cikin fargaba hakan bai hanata ,mutunta kanta 
 da son  janyowa kanta  martabarta ta Diya mace . 
 Sai da ta dauki mintina tukun ta mike cikin sanyin jiki ta nufi  dakin shi .
tsaye take akan kafafunta a  bakin kofar dakinsa zuciyarta na dokawa  .
tsoro taji yana shigarta  sai ta daura hannuta kan handle din kofar .
 sai tacire hannuta da sauri .
,da kyar tasamu  tattaro duk wani  kuzarin dake jikinta  .
,karfin hali tayi wanje murda handle din kofar da iya karfinta tashiga parlour'n da sallamarta .

shr parlour bakajin komai  sai karar TV  tsayawa tayi  tana jirashi kusan 5 minti  bata ga alamunsa ba ko jin  motsensa  batayi ba  . dan haka  ta yanke shawarar shiga Bedroom dinsa. 
tana shiga dakin gabanta ya tsananta faduwa , cikin sanyin murya ta sake yin sallama .ya amsa da kyar km a ciki .

 Zaune  taganshi   yana operating  system sanye cikon  wando  three counter da  pure whit singlet ,  ahankali take  takowa har  inda yake yayinda kanta ke  sunkuye  .
 tsugunnawa tayi a gabansa muryata na rawa tace Gani Yaya .


GA TSARABARKU TA KANO BA YAWA KUYI MANAGE 😃😃😃



MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
   AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO


Page 25- 26

Bai ko kalli inda take ba hasali ma operating  din system dinsa yacigaba dayi.
"  tayi kusan minti goma tsugunne a gabansa batare daya dago idanunshi ya kalleta ba .

 Shr Tayi tare da" sunkuyar da kanta kasa  .
Yayinda zuciyarta ke tsananta bugawa .

 cikin daddaden muryarsa may cike da dadin   sauraro "fiyye da komai  datafi kauna  .

Yace tun yaushe kike tare da wance sakaran   Dana ganku shekaranjiya ?

 Batasan sanda ta zauna  ba ,dan tsabar frigice da  tsoron   daya shigeta na lokaci guda  .

,zuciyarta ce tasoma rawa...rawa  tare dokawa .tarasa yadda me za tace.
 cikin  ya'n sakanni nan hankalinta  yayi matukar mugun tashi. kwakwaluwarta "tashiga tariyo mata abinda ya faru  a shekaranjiya  din .

 gabadaya tagama 
 frigita  da tmbyr daya jiho mata, tunaninta  ya ta'alaka ne akan ya  manta da abinda yagani din .
dan ganin ya share  Bai  nuna koda a fuskarsa ba .
  da kyar ta iya bude bakita tare da son  nuna  masa , itama batasan inda  zancesa ya nufa ba.
 ,   muryarta cike da rudani  tace wa kenan ?

Sai Lokacin ne ya  dago rikitattun  idanunshi ya dubeta dasu .
,tare da zabgamata wata uwar  harara .
cikin  sanyayyayiyar muryarsa, ta isa ya sake yin magana  Yace wawa ..... .ni zaki waskewa ya nuna kirjinsa da yatsansa
 bakaramin laifi zaki karawa kanki   wajen nuna min bakisan abinda nake nufi  ba .

Domin bana bukatar
 rainin hankali ko  karyata min  abinda idanuna suka gane me .

Amsa  tmbyta kawai nake da bukata . 

take  muryarta tasoma  rawa alamun kuka keson kufce mata.
   ,ahankali ya daura yatsan  hannunshi akan lip's dinshi " shiiiiiiiiiii....... karki kuskura naga Tear's dinki ko rawar murya .
dan  banida  bukatar su .
I said tun yaushe kuke tare ,  that's ol .... 
  A boye ya dinga sauke ajiyar zuciya sannan ya"
 yacigaba  ko duk dadewarku bakisan tun lokacin da kuke tare ba ?

 Lokacin daya taji maganarsa na neman birkita mata Brain dinta. to up side down" wani irin rudewa  da gigicewa  ta sake  yi .  

 Ba bakinta kadai ke rawa ba ,yanzu kam har gangar jikinta rawa yake .

 Ta dawo tamkar wata zautacciya Da kyar tasamu ta iya hadeye abinda taji ya tsaya mata a makoshi .
tare da zubda hawayen  da suka  taru a idanunta, cikin rawar murya  tace shekara biyu kennan.
Tana gama fadar haka 
 ,  tayi saurin sunkuyar da kanta kasa dan gudun jin saukar mari .

yayinda hawayen tausayin kanta suka cigaba da bin kuncinta.

 a hankali ya dinga girgiza kanshi shekara biyu kennan ya sake  maimaitawa kansa.
Cikin sanyi   ya  maida jikinsa" ya kwanta rigingine  ya Kuma cigaba da operating din system dinsa batare da ya sake ce mata  komai ba .
 ,Take yaji    zuciyarsa ya dauki  beating ,wanda yarasa dalilin jin haka  .

Kusan minti shabiyar kennan idanunshi  na kan system  dinshi yana cigaba da aikinsa  .
, wanda mutun zai iya    dauka aikin ne kawai a gabansa" 
 amman a zahirin gaskiya hankalinsa ya rabu gida biyu ne . kan aikinsa da nazarinta yanayinta " maganarta ba iya kunnenshi kadai ta tsaya ba " har gangar jikinsa takaiwa farmaki . ahankali ya dinga furzar da iskar mai zafi  daga bakinsa . gashi dai  magana yake son yi amman taki fitowa sakamakon zuciyarsa dake bugawa .
    ,da kyar yasamu  iya bude bakinsa  .
  yace kina nufin shima sonki yake yi kennan  ?

 Tsoro da faduwar gaba ne suka taru suka mamaye zuciyarta.
 cikin in..inna ..tace wai wai  haka yace "amman ,  dan Allah kayi  hakuri  .
  
 da sauri DEENi dake rigingine  ya mike zaune cikin daga murya  yace mene ? Nayi hakuri ubanki "
Da sadakin nawa akanki idan da kuna kula juna ,I don't care .
Amman yanzu iskanci ne yasa  kika, cigaba sauraran wancen sakaran dan tsabar kin raina min hankali.

Bakinta na rawa  tace Ai shima yasani" shiyasa ma  yace ya hakura dani .
, ok da shi m...
  sai km yayi shr yakoma ya kwanta . hade da runtse idanunshi . Lips dinshi na kasa yakamo yana  cizawa a hankali ahankali " cikin zafin rai  da kunar zuciya   ya nuna mata kofa da yatsansa alamun ta bar masa  dakin  .

 ,kasa Mikewa tayi tsabar tsoro gabanta yacigaba da faduwa ,muryarta na rawa" ta sake yunkurin bashi hakuri  dan Allah yaya kayi hakuri wlh mun rabu dashi tun ba ya...

Wata irin  tsawa ya daka mata take maganar ta makale "tun batakai ga karasa yin ta ba   .
 wanda hakan yasa ta mike tsaye da sauri  batare da tashirya   yin hakan ba.
  jikinta yacigaba da kirma . 
   Ahankali ya bude rikitattun idanunshi "kasa kasa yake kallonta ji yake tamkar ya tashi ya shakota" tare da  yaryarfa mata maruka" ko zai dan samu ya ragewa kansa  tension din daya addabe shi tun shekaranjiya.
 amman ina baya ji zai iyayi haka.
 kodan   "
,sanin halin Umminsa.
   yasa  muddin yayi haka ranta zai baci ,hakan kadai ne yasashi kasa aiwatar da komai akanta.

 idanunshi ya watsa mata yana mai  sake  kafeta dasu wani irin kwarjini ya sake  yi mata wanda hakan shi ya kawo katsewar duk wani kuzarin dake tattare daita  . 
Muryasa a sarke yace    live dis room now  before I skater  you .Ai Bai kai ga rufe bakinshi ta kwasa  "
 da sauri   ta soma kokarin barin  dakin.
  Hade da  tabe baki a ranta  Tace matsefafe banza kawai  "anya zan iya daukar wulakancin nan  naka  kuwa ? 
ta fice tana goge gumi  duk da ba lokacin zafi bane jikinta sharkaf yake da  gumi .
Tana fita ta dinga fidda numfashi  sama sama tamkar mai cutar asma.
    sai data goge gumin  daya cigaba tsatsafo  mata  sannan ta shiga daki . 
Zaune ta samu Ummi. Tana balle magani zata sha .
Ummi tabita  da wani irin kallo tace ke km daga ina haka ?  Tace yaya DEENi ne yakirani" Ummi tace yashigo ne ta girgiza mata kai" kawai " alamun Eh " to yana ganki duk a frigice  kmr wacce tayi  gudun  tsire ,ko wani abun yayi miki.
 zeenat tayi narainarai da idanuwa  tace A'a  Ba abinda ya  min   .
  Ummi ta sake dubanta hade da  tabe baki tace ke kika sani ma idan wani abun yayi miki .

,ba kinki tsayawa waje daya ba, sai  wani rawar jiki  kike yi  akansa dan tsabar sakarci irin naki .

Zeenat  dake tsaye tana duban Ummi   taji  tamkar ta  zubda kwalla   dan jin takaicin abinda Ummi tace mata  .
  ,  Tace to ni   yanzu Ummi  wani rawar kai nayi km ? tmbyta  abu kawai  yayi fa.
 Tace to  me Yace miki ko abinci zai ci  zeenat ta sake girgizawa Ummi  kai.
 , baki da bakin ne da zaki dinga  amsa minb da ka.   cikin rawar murya zeenat tace Allah Ummi   tmbyta kawai yayi. 
tmby ce kawai zai saki kiyi hujiga hujiga haka  kmr an kwatoki a bakin kura .
 Ki sanar dani idan wani abu  yayi miki.
Tukun na ma   , how many hours  dana dawo parlour na iske baki nan . Km nasan tun lokacin Kina dakinsa dubi yadda kike fidda gumi  dan Allah .
a sanyaye zeenat din  Tace to ni Ummi me kike so nace byn  .....
 sai km  hawaye ya balle mata   shar shar.
  yasoma bin fuskarta . Tayi saurin tare da
 sanya  byn hannuta tana goge hawayen   wasu na sake silalo mata.
  Ummi ta zuba mata idanu kawai tana kallonta tare da nazarinta tabbas tasan duk yadda akayi akwai abinda deeni ,yayi mata .
Amman dan sakarci da kafiya irin tata  gashi tski fadar gaskiya.
 sai da ummi ta numfasa sannan  ,tace meyye km na kuka ke da kika ce ba abinda aka miki  .
 ,bakiyi kuka a can inda aka ritsa ki ba sai a nan ,dan kin rai nani ko..

 kasa cewa komai zeenat din  tayi illa sanya    kai datayi cikin  bathroom, tashige abunta  tana  kuka kasa kasa , abubuwan sun taru sun cakude   mata .
 goma da ashirin ga rashin samun kulawar  DEENi gareta .
ga damuwar Ummi akan ta nacewa DEENI .

 cikin dare ma  sam kasa bacci tayi   .
Sai  faman  juyi kawai take akan gado  tare da tunanin iri iri ta jima kwance batare da bacci yayi nasarar dauketa ba  .
Wani   tunanin ne yazo  gara ta tashi  takai kukanta gurin mai duka.
 dan haka ta mike cikin sanyi jiki " taje tayo alwala .


 sallah nafila ta   dingayi ba kaukautawa  tare da neman zabbi Allah akan aureta da DEENi.

 dan ita kanta  tasan zuwa yanzu  tabbas tayi kuskuren  saurin amincewa da aurensa datayi .

Domin shine musababbabin abinda   yasa  wulakancinsa ya sake nunkuwa  gareta.  wanda   ita kanta tasan  hukuncita abinda yafi dacewa daita  kennan .
 na saurin  amincewa datayi da  auren DEENi  cikin gaggawa  batare da ta neman zabin Allah ba . 

hankalinta kan tashi.
 a duk sanda ta tuna da maganganu ummi. A  Ranta tace  anya kuwa bazan hakura da auren  nan na DEENi  na hutawa rayuwata ba .
 wai ace mijin da zaka aura  ne" ya zame maka  tamkar wani ma'alaikan daukar rai ko wani dodo . 
Kuka take sosai tana  , addu'a   neman Zabin   Allah a  game da auranta dashi .


 darajar nafilar data kwana tana yi ne  .
yasa washegari ta tashi  sakayau  daita cikin nishadi  da farinciki "
 ba  kmr ko wace  safiya  ba .
duk da bata da wani kuzari da walwala.  Amman hakan bai hana  jin dadi ba.

 kitchen ta nufa kai tsaye  dan   hada masa breakfast kasancewa weekend ce .


 " byn  wasu yan mintina ta kamla da komai na break tashirya dining . Cikin haka ummi ta iso parlour ta zauna kan dinning table   tana yi mata sannu , murmushi tayi  tare da  koma kusa   ummi  ta zauna" ta sheida mata ta gama komai .
 tana jinsa yashigo  yana  gaida ummi fuskasa a daure   kmr kullum.
Sanye yake  cikin dark blue t shirt da wando jeans . ummi ta amsa  masa cike da fara'a ka tashi lfy ya dan saki fuska kadan Yace lfy lau na tashi  first lov kujera ya zauna . a tsorace itama zeenat din  ta gaishe shi ,ya amsa mata a ciki batare daya kalli inda take ba.

 ,ummi Tace ya..ya .ayi serve  din ka ne ? Ya hade rai yaki yin magana .
da kai fa nake a zubo maka abinci  ne ta sake maimaita wa ?
  Ya dan dubi ummi a shagwabe Yace bana ci.

 ummi ta Gane tmbyrta  da tayi masa ce  ta hassala shi .
dan haka sake bi takansa ba  da kanta ,ta zuba mishi komai da'aka girka ta turo plate din gabansa ,tare da  dungure masa kai " gashi nan miskilili sarkin zuciya Yace  to ni ta yaya za'a  tmbye ni ko zanci abinci  " byn ansa zanci din " 
ummi tayi murmushinsu irin na manya Tace uhmmmm DEENi kennan halinka sai kai "Allah ya canza maka wannan budadden halin naka " Ameen yace tare da kai spoon bakinsa .

 parlour ya dauki  shr  baka jin motsin komai   baya ga karar spoon din zeenat .
 juyawa spoon din kawai take  takasa  kai ko loma daya bakinta sakamakon cika wajen da DEENi yayi"  duk  da tasan hankalinsa da idanunshi ba'akanta  suke ba .
  tayi shr ta fada cikin  duniyar tunanin abinda ya shafeta km  yafi damunta.
Wanda  a halin yanzun Bai wuce aurenta da DEENi ba .
domin kuwa   tana matukar jin tsoron zama dashi ba dan komai ba sai dan tsoron azabar da zai dinga gana mata a gidansa.
 hankalinta kan tashi a duk sanda ta tuna da hakan.
 Ahankali   Ummi ta ajiye  spoon din hannuta tare da zuba mata ido kawai  tana  binta da  kallo tarasa meke damun Brain dinta  a cikin kwanakin  nan .
 kusan  minti goma ta dauka tana kallonta batare da ita zeenat din tasani ba .

Zeenat .....ummi takira sunanta a frigice ta juyo tana kallon ummi  ,ci abinci abinda ummi ta iya cewa kennan .
 DEENi dake zaune haushi kmr ya kashe shi tsaki ya dan ja ,ummi ta juyo bangaren sa Tace lfy kai km ?  
Fuskarsa a dakune Yace babu   ,   Sai da taga  Ummi ta sake     dubeta   sannan tasoma cin abincin , shima bawani sosai .




Byn sati biyu 

Shirye shiryen bikinsu zeenat  aka soma  sosai ba kama hannu yaro.

 ,anshirya komai na  al'adar  hausa kmr   sabbabin dinkuna da gyaran jiki   komai  km tare akeyi musu ita   da shemah km iri daya.
   musamman ummi ta dauko kwararriyar  mai gyaran jikin  daga india domin ta gyara mata tilor diyarta da kyau.
 duk wani gata  da uwa zata yiwa diyarta "ummi tayiwa zeenat shi .
 shima mahaifin zeenat din yayi iya bakin kokarin Sosai .

a nyi kamu amare  idan aka feshe su da turare masu dadin kamshi na  mutune India wanda duk wacce  ummi ta dauko ta gyara zeenat din ce tazo dashi. 
Anyi musu murzar  lalle da kitso .
amman ansha fama da zeenat gurinyin kitso dan cewa tayi ita sam na attachment ,zatayi .
sai da ummi ta bude mata wuta sosai tare da cewa ,zata sanarwa DEENi tukun ta natsu .

Sau ran kwana biyu daurin aure mutane India suka iso , kusan mutum ashirin maza da mata sosai aka shiga hidimar da ,baki.ummi  taji dadi Sosai dan kusan duk  shakikanta ne suka zo wanda km shine zuwansu na farko Nigeria idan .

 ,gabadaya gidan nasu  cike yake  da baki dan haka ba kasafai  zeenat din take  zama a part dinsu ba ,tana can  gidansu shemah   .
 
 Zeenat Tace dan Maryam muje kirani part dinmu ina son naga ummi yau duk banganta ba  .
 , Maryam Tace gaskiya na gaji da yawa wlh kije kawai . zeenat ta ja saki Tace dan Allah muje kiraki ni  yanzu zamudawo.
 shemah dake kwance ta mike zaune tace muje na rakaki kinsa halin  Maryam da maseefar  son jikin tsiya.
 , Mikewa sukayi har sun fito sai ga  Maryam  Tace wlh baza kubarni ni kadai ba , zeenat tace ke km kika sani " idan zaki muje .
Tare ,  suka nufo part dinsu zeenat.
 tafe suke suna hira irin tasu ta amare  daga nisa zeenat ta hango motar DEENI parke  a kofar part dinsu "daga gefe .
" can baya km motar fk ce sai wata motar daban wanda batasan ko ta waye ba . 

Jingine  yake jikin motar shi yana amsa waya sanye cikin English wear's   black jeans da rigar ashi colour "mai gajeren hannu wanda ta fidda ainihin kyaunsa   da gargasan gashin jikinsa dake kwance kan Gabar  hannushi .
 idanunta fes akanshi  tana binshi da wani irin kallo saboda yadda taga yakara yi mata kyau. fuskasa har wani shekin annuri  take fitarwa kmr ance ya dago idanunshi  suka hada idanu.
 da sauri ta dauke idanunta wani abu ta dinga ji yana tsirga mata  ajikita. sai taga ya fita daban cikinsu fk duk da bawani kallonsa tayi sosai ba .
ta sake dago idanunta  da niyar sata kallonsa suka sake hada ido  harara ya sakar mata  ,  kallo daya ya sake yi mata ya kau da fuskarsa gefe yacigaba da wayarsa   a kallo dayan da Yayi mata yane yadda jikinta ya tsanyi .

 kai tsaye zeenat taja hannun Maryam wacce tafi kusa daita ta juya da sauri  ta karya cona itama shemah ganin haka yasa tabiyo bayansu da sauri tana jin fk na kiranta . shemah Tace  yazaki biyo damu tana km.
 zeenat Tace bbu komai mu bi nan di yafi sauki .


 ta bayan part dinmsu suka shiga , da ummi tasoma cin karo ta rungume tana sakin ajiyar ,ummi tace meyye haka ?muryata kmr mai shirin yin kuka take  Haba ummi  yau fa duk banganki ba ,baki ga har wata  rama nayi ba  " tayi murmushi tace lallai kam kin rame dan ga natsuwa nan suna bikin dariya mutane dake tare da ummi suka shiga yi .
Ummi tayi gaba zeenat nabiye daita tana  zuba mata shagwaba.
 shape shape tayi abinda zatayi  suka bar gidan . 


Ranar daurin auren da safe  ta nufo gidansu dan dauka kayanta dazata saka .
wanda ta manta bata hadu dashi ba cikin kaya .
,tafe take tana sauri . yayinda su ya faruk da abonkan DEENi  ke tsaye duk cikin  shirinsu na zuwa daurin aure .
amman banda  DEENi wanda dagani  shi suke Jira . 
Wani irin kunya ce taji takamata dan haka ta dan janyo gefen mayafinta ta rufe fuskarta ,tana jin yaya faruk nacewa amaryamu ki bude idanunta kada ki fadi mana .
amman ina ko waiwayo batayi ba tacigaba da tafiyarta ta kofar baya tabi yauma.
 tashigo dogon parlour'nsu ta baya kennan tasoma jiyo kamshin turarensa kafin tayi kokarin bude fuskarta  taji sunyi karo da mutun .
da sauri takarasa bude fuskarta  "yaya DEENi ne wanda zai fito har wayar dake hannushi ta fadi .
,gabanta ne  yayi wani irin faduwa dan har wani juya juya ta dinga ji   da sauri ta tsugunna dan miko masa shima ya tsugunna da zai dauka a tare hannunsu yakai kan wayar  ,wani irin shock ne  yajata " wanda  baita kadai ba har shi   DEENi yaji abinda taji.

 Wani iri shima yaji ajikinsa  tamkar an jona masa  lantarkin .
 . Shine yasoma kokarin janye hannushi daga kan nata ,ahankali ta  Miko masa wayar batare da ta mike ba  hade da cewa kayi hakuri  dan Allah .

komai Bai iya cewa ba baya ga amsar wayar  da Yayi ya barta nan  tsugunne.

Bayansa tabi da kallo yayi matukar yi mata kyau har batasan yadda zata misalta ba sanye yake  cikin shadda fara kal sai  kamshin yake zubawa .
  gabadaya kamshin turarensa  ya gyaraye dogon parlour'n .
Ahankali zuciyarta tasoma bugawa tamkar zata basa kirjinta ..
girgiza kai kawai tayi dan  batasan wani irin aure take shirin yi ba haka ta juya cikin sanyi jiki tabar gurin tana shiga ciki.m mutane  akama kiranta da  amarya amarya kinsha kamshi ita dai bata iya cewa komai ba dan gabadaya jikinta a sanyaye yake .


  



MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO



Page  27-28

Part din cike yake da  abonkan arzikin  da  en'uwa ,Ummi 
 Jikinta a sanyaye ta dinga ratsa mutane dake ,zaune a parlour ' har ta iso dakin ummi , da  idanun  take bin en  dakin da kallo .
kozata  ga  ummi  ganin bata  alamunta bane , yasa  tmbye  matar uncle din Inda ummi take.
 tace yanzu tashiga bathroom  .  
Ahankali ta fidda  numfashi tare sauke ajiyar zuciya   .
  cikin haka ummi ta fito tana ganin zeenat  din.
 ta bata  fuskarta "ta zauna tana dubanta"

 gefen ummi zeenat tasamu ta zauna fuskarta dauke da murmushi wanda da Gani na karfin hali ne .

 Cikin kasa da murya ummi tace yana ganki haka  ina kayanki ? 

Cikin sanyi jiki zeenat tace  shi nazo dauka .

,ummi tace ke dai kin cika   shiririta wlh "
   komai baza kiyi shi cikin sauri da kazar kazar ba kin dinga jan jiki kennan ,kmr wata mage .

Alhalin  kin   san halin wanda zaki aura " dan oya oya ne  . 

jin haka yasa jikin  zeenat din sake  yin  sanye, tare jin wata irin  faduwar gaba  " zuciyar ta dinga dokawa da sauri tamkar baso kirjinta.
  ahankali tasa hannuta ta kamo na   ummi 
 cikin nata jikinta har rawa yake  hade da rage    murya  tamkar mai shirin zubda kwalla  tace dan Allah ummi   kiyi hakuri kinji karkiyi fushi dani  ,zan canza inshallahu Amman  " kimin addu'a .
 wlh tun sanda aka samo shirin bikin nan nake  jin faduwar gaba wanda narasa dalili . 
ummi ta tayi shr tare da  zuba mata idanu kawai tana kallonta  .
 tausayinta  ne ya sake kamata  , ,duk sai   taga takara ramewa ba kmr kwanaki ba hakan yasa taji ba dadi aranta.
, ahankali ummi ta mike tare da riko hannuta tayi cikin  , bedroom  daita. En dakin suka bisu da kallon sha'awa duk da basu ji maganarsu ba Amman sun birgesu .

 ,Har suka shigo bedroom din Ummi na rike da hannuta Ta  zauna daita tana rarrashita kan ta kwantar da hankalinta fargaban aurene kawai ke sata jin faduwar gaba Amman   bbu abinda zai faru inshallahu "
 Ummi da kanta ta shirya diyatata   cikin wata arniyarta geziner  ligth blue sai daukar ido take da kamshi  tare da  fesheta  da turaruka kala kala masu sanyi kamshin take zeenat   ta fito  amarya sak  .tayi kyau sosai 
Ummi   ,ta dauki waya tayi mata hotuna sannan  takira Maryam tace tazo ta tafi daita din .  



Kwanciyar tayi flat  a kan gadon su shemah  tana kallo da sauraran  duk abinda ke faruwa  .
a cikin dakin dake cike da en mata da kawaye 

 abinka  ga  mai yawan  kawaye "  da  mutane kala  daban daban " yasa dayawa wayan dake cikin dakin kawayen zeenat din ne    .
gyara kwanciyarta tayi idanunta na kallon celling dakin hannuwanta duk rungume da kirjinta yayainda zuciyarta ke cigaba tsalle tamkar zata fasa kirjinta ta fito waje.

 ahankali ta runtse idanunta sanyi taji yana ratsa koina a jikinta  duk da tarin fargaban dake tattare daita hakan bai hanata jin jikinta yayi mata nauyi ba .
Tana ji ajikinta  burinta da dokin  son auren DEENi .
   duk   babu shi ahalin yanzu sakamakon fargaba da tsoron kasancewa tare dashi a muhalli daya .
 Ta dauki lokacin mai tsawo kwance yayinda ta dinga jin wani iri ajikinta .
Bugun zuciyata na sake karuwa.
 ta dinga kokarin ganinta ta cire damuwar dake damunta wanda a zahirance ita ta daurawa kanta  .
  har yanzu da take kwance  jikinta a sanyaye yake takasa tabuka komai.
 idanunta ta  runtse tana cigaba da sauraron hirar dasuke sama sama .     



10:30


Karfe goma da rabi daidai  na ranar lahadi  Allah ya cika alkawarinsa   domin    dimbin, jama'a sun shaida daurin auren NASURULDEENI ALIYU BELLO da MUZEENAT HABIB BELLO" daurin auren daya tara manya  attajirai da kusoshin gwanati hade da maikata 
 bakaramin farinciki  family din muhd bello  suka yi ba  ganin sun kara karfafa  zumunci a atsakaninsu, .
 dan haka farincikisu  ya sake karuwa takoina ka juya , family din murna ne cunkushe  a fuskokinsu 



Zeenat dake kwance har lokacin tana saka da warwara still jikinta a sanyaye yake takasa kwakwaran motse  .
 zuciyarta fall  da fargaba musamman lokacin da taji  hayaniyar mutane  ta cika gidan  alamun an daura aure, en'uwa nata  shigowa ana gaisawa , ajiyar zuciya dumin  hawaye taji yana bin kuncinta shikennan ta faru takare  tana matukar son  deeni Amman  tana jin tsoron zama dashi  hayaniyar mutane  take sake jiyowa hakan yasa  jikinta ya dauki kirma,kirrrrrr... sam ko kadan bbu wanda ya lura da yanayinta.
 Sai ma tashi sukayi suka fita waje km  har sanda suka fito tsakar gidan suna ta daukar  hotuna bbu wanda ya lura da yanayin da suka barta  .
"  Maryam ce data  karaso wajensu taga suna ta hotuna  bbu ita yasa tashiga dakin dan dubota dan kusan tana lura daita tun jiya tamkar mara lfy .

 kwance ta tadda ita tana  fidda numfashi sama sama .
 Da sauri ta karasa inda take  bbu abinda jikinta keyi sai fidda hucin zafi,  a rude ta dinga takiran sunanta zeenat ... zeenat  daman bakida lfy ne? 

Kai kawai ta iya girgiza  mata  alamun eh da sauri Maryam ta mike  ta nufi part din ummi tasanar mata  .
tare suka dawo gurinta da wasu en'uwa ummi guda biyu .
 zuwa yanzu jikinta ya tsananta zafi  tare da karkarwa   .
 ban da  salati bbu abinda ummi keyi  da sauri takarasa kusa da zeenat din ta zauna tare da riko hannuta" may zan Gani  , haka ni   fadeela ? 
, zeenat kina son ki kashe min kanki ne ?
Ko yaya ,
Alhalin kinsa ke kadai gareni  duk duniyan nan  km ke kadai debimin kewar er'uwarta dana rasa , bazan iya jurar rashinki ba dan Allah ki tausayi min  mamana.
 sai km  hawaye  shar shar daga idanun ummi  sosai Ummi ke zubda kwallar tausayi diyarta  ganin yadda  ta fita haiyacinta cikin lokaci daya   .
Ummi tace zahra kamama min ita dan Allah .
  su  aunty suka mata zeenat    sukayi  part din  Ummi daita .


  kai tsaye dakin DEENi  ummi tabada umarnin  a wuce daita.batare da bata lokaci ba ummi 
 takira family doctor dinsu .
 sannan takira DEENi tace yasameta a dakinshi yanzu yanzu  .


Doctor     bai dauki wani lokacin ba" sai gashi yana zuwa yasoma duddubata tare  dabata taimakon gaggawa  .

 ummi  ta dubi doctor  hankalinta a tashe tace  doctor meke damunta ?

doctor yace bawani abu bane   damuwace kawai tayi mata yawa  "amman inshallahu  zata. dawo daidai .

A gaugauce DEENi yashigo byn amsa kiran Ummi .
yana shigowa dakin  mutane  suka dan ragu  .

ahankali yakaraso kusa da Ummi ya tsaya yana tmbyrta abinda ke faru  sai data ja numfashi sannan ta nuna masa inda zeenat din  ke kwance tace zeenat ce ba lfy sai lokacin idanunshi suka kai gareta kwance take akan bed dinshi an lullubeta da bangon rufarsa.
 shr yayi tare da zuba mata rikitattun idanunshi. 

Daddaden kamshin turarensa tasoma juyowa may matukar sanyi ahankali ta dan lumshe idanunta .

Taku daya zuwa  biyu yayi yaja ya sake  ya  tsaya" sannan ya dubi inda ummi  ke tsaye  yace me doctor din yace yana damunta?
 , doctor din still ya sake mashi bayani kmr dai yadda yayiwa ummi  . ahankali ya sake mai idanushin kanta yana cigaba da kallonta wannan shine karo na farko daya tsaya ya Kare mata ,
  ,   sosai kamshin turarensa  ke sake kaiwa hancinta farmaki tare da susuta mata duk wata gaba dake  jikinta .
.
 jikinta da zuciyata suka dauki  rawa wani zazzabi  mai zafi yayi nasarar sake rufeta sakamakon idanushi dake yawo a gangar jikinta . 

Da sauri doctor ya  nufo inda take" deeni yasa hannu ya dakatar dashi   alamun kada yakarasa gareta" dan wani abu  yaji yana taso masa  sanda doctor ke masa bayanin abinda ke damunta , tamkar ya auna doctor waje  dan takaicin abinda ke cin zuciyarsa. 
ganin haka yasa  doctor  din yace a samo ruwa da towel a goge mata jiki dashi  dan tazo daya dubata yaji yadda jikinta ya dau zafi  yace zai je   ya dauko magani ya dawo  cikin sauri ya fice dakin  . 

  A ranta tace doctor dama kayi zamanka   dan   maganinka  kadai  ba  zai taba min  maganin damuwarta ba .

 dan ita kadai tasan abinda ke cin ranta .
Wanda   tun daga cikin zuciyarta take jin yake taso mata .
tare da haddasa mata  tsoro da faduwar gaba.


 Tsaye yake har yanzu sai  suke  hanuwanshi duka da Yayi  cikin aljihun wandonsa.

 ahankali yasoma takowa  zuwa bakin gadon km idanushi akanta.
cikin sanyi ya yaye bargon da aka lullube mata  jiki dashi. idanunshi fes akan fuskarta dake lumshe tayi fayu sannan km takara rame sosai  ahankali  ya daura  hannushi saman goshinta .
 jin yadda  goshinta  ya dau zafi da yadda take  fidda numfashi sama sama  yasanyashi kai  hannushi  da sauri jikinta.
 take yaji abinda ya sake frigitashi .
zafin dake jikinta ya ratsa tafin hannushi" wanda bai san sanda tausayinta ya lullubet shi  ba  ya dinga jin wani abu na tsigar wa ajikinsa ,  ya juyo tsaitin  Maryam yana harararta yace tsayuwar me kike anan da sauri ta fice daga dakin bata fi minti uku ba Sai gata ta dawo  da  ruwan ahanunta jikinta na rawa.
 azaton zeenat ummi ce ko auntyta  zasu goge mata jiki ,amman sai taga DEENi yakarbi robar ruwan a hannu maryam  .
Gabadaya suka fita daga dakin har ummi "tare da kulle masu dakin .

Cikin sanyi jiki ya tashi ya dawo gabanta har yanzu sanye yake cikin  shadda fara  tas sai kamshin turarensa ke  tashi a dakin .

ahankali ya cire farar hular shi ya ajiye gefe sannan yasa  hannushi duka  ya tattarota jikinsa yaja zip din rigar kasa ya zare rigar jikinta ya ajiye gefe ,take jikinta ya sake daukar kirma   gabanta  yacigaba da faduwa .
tsoro da mamaki suka taru  cika zuciyarta. aranta tace wayyo nashiga uku  me  yaya ke nufi  da cire min riga ? yana nufin shi ,zai goge min jiki  .
tana ji tana Gani ya cire mata kayan jikinta tsab   har bra dinta .
ta rage daga ita sai zani iya cibiya ,sannan ya zauna tare  daurata a saman  cinyarsa"  ya juyo daita suna facing juna  taso tasa hannu ta Kare kirjinta amman kasancewar  jikinta bbu kwari yasa takasa aiwatar da komai "dan haka  ta runtse idanunta gam.
 tana jiran taji    ruwa ajikinta Amman sai taji shr ahankali ta dan  bude idanunta ,DEENi zaune  idanunshi kyam akan kirjinta .
 da sauri ta maida idanunta ta rufe dan frigice da tsoro    ya dauko towel din ya matse sannan   yasoma goge  mata saman  jikinta   zuwa kirjinta da fuskarta , ya dimauce da ganin halitatta kirjinta    ,hakan  yasa yafi goge mata gurin a tare suka dinga sauke ajiyar zuciya .

 can yaji ana nouking din dakin  yayi sauri ya mayar mata da rigarta sannan yabada izinin  shigowa.
 doctor ne yashigo da ledar  magunguna ahannushi Yace abata abinci taci  tukun sannan tasha maganin.
 byn tafiyar doctor DEENI  yakira ummi Yace akawo  tea, en'uwa    dayawa suka shigo dakin "ummi da matar uncle din zeenat  ,Maryam har ma da shemah  . suka dinga jero mata sannu.

byn  sun  fita ne   taji tamkar kar su fita dan  bata son abarta daga ita Sai shi.
 hakan na sake frigita zuciyarta   . 
kadan tasha tea din tace takoshi bai wani takurata ba  ,ya ballo  magani ya Mike mata  ba musu tasa hannu ta karba tasha ,dan tasan halinsa  ciwonta bazai hana ya jibgeta ba .
Shiya  gabadaya a tsorace take dashi.


MMN SUDAIS
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
     💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO



Page 29-30


 Byn tasha magani . komawa tayi ta  kwanta  lomo ajikinsa' tana sakin numfashi sama sama wani iri taji ajikinta lokacin data tsinci kanta kwance kan tattausan jikinsa .
ga kamshin turaren jikinsa gyaraye dana dakin sun buwayi hancinta .
ji take tamkar sukasance haka har abada.
 ,  ahankali tasoma lumshe idanunta  har ta rufe su rufff..
   bacci ne may nauyi  Yayi nasarar daukarta  acikin mintina da basu wuce  goma ba .


Kyawawan idanushi masu matukar haske da daukar hankali ya zuba mata.
 Tare da  Kare mata kallo wani zirrrrrrrr   ya dinga ji ajikinsa" lokacin daya jita lefe a saman  kirjinsa   . 
da kyar yake jawo numfashin yana fesarwa.
hannushi ya sake kaiwa wuyanta har lokacin jikinta da sauran hucin zafi.
 janyota jikinsa ya sake yi .
Tare da  ,yasanya hannuwansa duka ya rungume tsam tsam   ajikinsa "yana fidda numfashi .
tare da  fatan samun saukin zugin da zuciyarsa ke masa wanda shi kansa yarasa dalilin haka.
   " Har lokacin bacci take  rungume ajikinsa suna musayar numfashin juna  mutuwar da jikinsa yayi ne  yasashi  sake zuba mata  rikitattun idanunshi tsawon lokaci yana kallonta 
  Da kyar yasamu yayo control din kansa cikin sanyi jiki  ya  zareta daga jikinsa ya kwantar daita ya sake lullube ta da blanket ,sannan ya Mike tsaye  yana karkabe  jikinsa.

 ,rigar jikinsa yasoma  cirewa  ya saura daga shi Sai  farar single da wanda shadda.

 Wordrob dinsa ya bude ya dauke  wasu kayan da zai canza  "  tare da yashigewa  bathroom .

 
Dakin ya sake dawo byn yagama shirya kansa  , cikin farin  yadin voyal  may matukar taushi da daukar hankali.
Agabanta ya tsaya  yana makale links din gaban  rigarsa  yayinda  idanushi ke kanta yana    cigaba da kallon fuskarta.

  Ahankali ya dinga jin reaction din jikinsa na sauyawa  ,yayinda zuciyarsa ke beating tana tsalle tamkar zata bafa masa kirji . wanda shi kansa yarasa dalilin dayasa shi  jin haka.
Ahankali ya dauke idanushi a kanta sakamakon 
 , ji yayi "ana nouking din dakin "yabada umarnin ashigo batare daya tmbyi kowaye ba . 
 Maryam ce tashigo da sallmarta .
 ta gaidashi ya amsa mata a dake .
 Cikin sanyi nan nasa 
Yakarasa gaban mirrow      ya dauki agogon  ya daura a tsintsiyar hannushi  tare daukar kwalbar turaren ya feshe ilahirin jikinsa ta cikin mirrow din  yake wa Maryam magana cikin dakakiyyar  "  muryasa ki kula daita idan ta farka .idan  kika ji zazzabi bai sauka ba ki sanar da first lov ,a tsorace tace ta amsa masa da to...
yana fita  ta bi bayansa da kallo cikin ranta tace wayyo zeenat na tausaya miki auren wannan maseefaffe .
 ,Sai kinyi   hakuri da wannan budadden  halin na shi .
 gefen gadon takoma ta zauna tana sake jin tausayin zeenat din a ranta .

Sosai zeenat tayi bacci baita ta tashi ba.
 Sai gaf da magariba.
 ji da Maryam tayi jikin zeenat din  bbu zafi ko daya .
yasa  ta sanarwa da  aunty zahra    .
 Su Aunty zahra   suka sata tayi  wanka da sallah .
 tana zaune akan prayer mat "duk jikinta a mace  taji sunce tunda jinkinta da sauki tashiyar  akaita tayi sallama da Ummi.

   fuskarta cike da tsoro  ta dubi aunty zahra tace dan Allah aunty  karku kai ni wani guri wlh bani da lfy  ..
 aunty zahra tace  A'a kiyi hakuri yanzu  za'a kai ki gidanki kya ji sauki a can.
 tana kuka tana komai aka shiryata cikin wata geziner mai ruwan kasa ,Sai kamshi ke tashi ajikinta kai tsaye  gurin ummi aka kaita ta mata nasiha mai ratsa jiki ,sannan takara da ce mata takasance may tsananin  tsafta da girki domin sune  manyan makamai dake  kara karfin aure .

Sai km hakuri ,kiyi hakuri  kiyi hakuri mamana da duk abinda zaki  Gani.gidan aure bbu komai acikknsa Sai   hakuri .
Km hakuri  shine jigon zaman  aure .
duk wata mata da kika ganta zaune gidan mijinta ,hakuri take yi 
  dan  haka ki kula da  kyau kinji mamana .
Zuciyar ummi ta tsinke tayi rauni  Sai km hawaye shar shar......suka soma zuba , en'uwa ummi da suka zo daga india sukai taba hakuri  suma sunyi mata tasu nasiha Sosai .

,  ita dai zeenat bbu abinda ummi ta fada wanda bai shiga kunneta ba .
tare  da kukan tausayin kanta .
duk sanda ta tuna yau  , za'a kaita gidan deeni hankalinta  ne  ke sake tashi .kuka sosai take har da majina .
  ganin irin kukan da zeenat din  ke yi yasa ummi kiran deeni a waya . 

Byn yan wasu yan mintina Sai gashi yashigo da sallama ,mutane dake zaune a dakin .
suka fita gabadayansu dan basu waje . 
Ahankali yakaraso cikin dakin sosai, ya  durkusawa gaban ummi yayi zaman dirshan har da tankwashe kafafunsa. ganin haka yasa itama  zeenat tazamo " tayi irin zaman da yayi  a gaban ummi" Sai dai ita zuciyarta da gangar jikinta  cike suke  da rauni.
 badan namijin kokarin datakeyi ba da tune zuciyarta ta buga tsabar frigici.
Ummi tayi shr  tare da zuba musu idanunta da suka gama canza kala saboda kukan datayi.
Tsawon lokaci tana zaune ta tasa su gaba tana kallonsu kafin daga baya tasoma magana 
 cikin sanyi muryata ta Kira " sunansa NASURUDEEN......  ahankali ya dago  idanunshi yana duban umminsa dasu  batare daya amsa ba .
Sai dai yadda takira sunanshi din ya girgiza zuciyarsa domin ya manta when last da yaji takira complete name dinshi haka   .
Dan haka ya tattara dukkan hankalinsa da natsuwarsa gareta .
Cikin sanyi murya data sha kuka tace DEENi ga zeenat nan ta sake dawo gareka" a karo na biyu . Sai dai wannan karon yasha bamban da sauran  lokuta .
'wanna karon ta dawo gareka ne da matsayi guda biyu ,kawarka km matarka .
zan ji matukar farinciki da kwanciyar hankali  idan kuka hada kanku ,kuka zauna lfy.
 , zeenat yarinya karama kayi hakuri daita"  duk wani  abinda ta maka  wanda bai yi maka ba , ka sanar min .
Ni Zan fahimtar daita ta hanyar da zata gane .
Ban yarda da duka ko zagi da cin fuska ba .
Kuka zeenat din keyi har lokacin shi kansa ya  tsausaya mata matuka 
Ga mamakin DEENI  Sai ya ga ummi itama ta sauko gabansu hawaye ne ke bin fuskarta wani nabin wani ,a rude deeni yasa hannushi yana share mata hawayen .
Cikin tsananin tashin hankali Yace dan Allah first lov ki daina zubda hawayenki  haka ,   kiyi hakuri "zubda hawayenki  bakaramin maseefa bane atattare dani "  idan har yanzu bakya son aurena da zeenat ne wlh  ashirye nake dana bar miki ita har abada .
Cikin kuka  ummi ta girgiza masa  kanta ba kukan komai nake ba DEENI facce na  tsantsar farinciki .
Farinciki ne yamin yawa har  yasani zubda su.
 ,ta janye garesu byn ta dauke hawayen idanunta.
kama hannun deeni dana zeenat tayi "ta hade su waje guda tare da daura nata hannu saman nasu .

Nagodewa Allah daya nuna min wannan rana may cike tarin farinciki mara misaltuwa , zeenat ga deeni nan nabaki shi amana har abada banida kowa Sai shi.
 ki zauna lfy dashi cikin amana "deeni kaima ga amanar zeenat nan naba  matukar ka cuceta "ban bazaka ji dadina ba. Dan Allah Ku kula   da junanku .
Ku rike min amanar junanku " ku kadai gareni byn Allah banida kowa Sai ku.
abinda tata fada kennan tana sake hade" hannuwansu waje daya .

Duk yadda yaso daurewa zuciyar kasawa yayi sakamakon  ,kaunar zeenat din da yake hangowa karara a cikin idanun umminsa.
 bai so zeenat din taga kasawarsa "  dan haka ya kife kansa kan hannun umminsa ya sumbata cikin dabara ya goge kwallar idanunshi. zuciyarsa ke kwabarsa akan alkawarin da umminsa ke so ya daukar mata " shi kadai yasan abinda ke damun zuciyarsa , aranshi ya dinga  ayyana abubuwa masu tarin yawa"anya  kuwa zai iya daukar alkawarin nan ....

jikinsa yayi masa nauyi tausayin ummin ya sake mamaye zuciyarsa. muryasa a sanyaye yace ummi ki kwantar da hankalinki  inshallahu bbu abinda zai faru  zan riketa amana yayinda a cikin zuciyarsa yake sauya kudirin ,ma,anar na karba dan kada Allah ya tuhumeshi gobe kiyama. 
 Yayinda ta kasa km hannuta dake cikin nashi  yake ta murzawa ahankali  cikin wani irin salo da yake sa tsagar jikinta tashi .
saboda nata hannu na kife ne cikin nashi tafin hannun. 
gabadaya jikinta yayi tsanyi  yasoma rawa rawa "dan samun  saukin hanyar tsira da son cire hannuta cikin nashi" yasa tayi saurin cewa na karba alkwarin ummi inshallahu ni dai addu'arki kawai nafi bukata "
.cikin sanyi ya sakar mata hannu .. 
Allah sarki ummi wani irin farinciki ne gyaraye da tsantsar kaunar ya mamaye zuciyarta . murmushin jin dadi ta dinga yi .sannan  ta mikar da zeenat din  tsaye ta rungume ajikinta . Tace Mamana ina miki addu'ar km bazan gushe wajen yi muku addu'a ba Allah ya muku albarka ,ya azurtaku da ya'ya masu albarka.

Da kyar su aunty zahra suka rikota sakamakon rukunkume ummi da zeenat din tayi  .

 sun fito  tsakar gidan dake  cike da  mutane .
Wanda ,Yawancin duk en'uwa ummi ne da kawayenta.

   Kai tsaye gidan  mahaifinta aka  kaita shima nasiha may tsara jiki yayi mata sosai  da nuna mata tayi  hakuri ta kula da mijinta , tamkar yadda mahaifiyarta tayi.  yace naji dadi kwarai da  deeni yakasance miji agareki,ina muku fatan alkhari .
Ina da   yakini deeni zai rike min ke da  amana .'
da baki duk wata kulawar da ta dace.
Ahankali  take cigaba da kukanta.. aranta kuwa cewa tayi  uhmmmm.
 abba  bakasan asalin halin deeni  bane .
shiya ka fadi haka.
 ,halinshi na zahiri kawai kasani bakasan na baniba.
 yace ta daina kuka  duk abinda take  da bukata karta zamo may  rokon miji  ta tmbye shi zai mata   .

,har gidan big dady Sai da aka kaita agurguje suka dawo gidan  kafin motar daukar amarya tazo.
 may gyaran amarya ce ta sake mata sabon gyara  na musamman zeenat din ta sake fitowa  fes abinta .
Sai sheki take zubawa ga wani irin kamshi na musamman dake tashi ajikinta .

Duk da cikin estate din zata zauna hakan bai hana motocin abokan deeni dana fk  cika kofar gidan  ummi ba  .
Dan  daukar amare .

Shemah aka soma saukewa , sannan zeenat aunty zahra ,ke rike da hannuta fuskarta rufe cikin  mayafi" har cikin gidan ta umarceta da tashiga da kafar" dama tare da yin Bismillah " tayi kmr yadda aunty'n tace.
 sannu ahankali har suka iso  dakinta ta zaunar daita akan gado.
 nan da nan mutane suka cika gidan  dan ganin dakin  amarya .

ahankali zeenat ta dan bude idanunta da suke rufe " tana kallon irin dukiyar da Ummi ta narka mata  a daki wanda take jin  ko mahaifiyarta ce a  raye .
bazata iya mata kwatankwacin haka ba , dan ma tsayawa bada labarin irin kayan da Ummi  ta zuba mata a dakin    ma bata lokaci ne ..


  Zaune dake a gefen laulausar zanin gadonta  ta cure  waje daya sakamakon tsaron daya cika . Ahankali ta kai idanunta kan agogon dake manne da bangon dakin" Karfe goma shada ta buga daidai"atsorace ta saki ajiyar zuciya saboda wani sabon tsoro dataji yana kawo mata ziyara.
A ranta tace  kar dai deeni barinni  zaiyi in kwana ni kadai.
 aiko idan haka ta kasance  da nashiga uku dan a gaskiya bazan  iya kwanta ni  daya acikin gidan ba .


Yan kawota basu minti goma da tafiya ba.
 taji saukar yayyafi sama sama wanda ya hadasawa yanayin garin yin tsanyi hade da kamshin kasa.
  " ruwa bai yi yawa ba haka nan  yayyenfin  bai tsaya ba.
Kusan tun lokacin da suka tafi suka barta anan take zaune bata ko motsa ba  Sai yanzu datayi tunanin deeni na iya barinta ta kwana ita kada . Hakan yasa ta Mike cikin tsoro ta kulle kofarta ta dawo ta zauna ,zamanta ke da wuya .

 Tasoma jiyo Hayaniyar   muryoyin  maza daban daban"  a cika gidan  hakan  yasa taji  tsinkewar zuciya  .Tare da faduwar gaba da .
 hankali  ta runtse idanunta tana jin yadda zuciyarta ke dukan uku uku kmr zatayi tsalle ta fito waje .

Deeni tsaye a parlour'n yayi  babbake  tare da dakatar da abonkansa .
 yace to to....Nagode sosai da kulawarku. 
rakiyar ta tsaya iya nan..
 ba Sai kunshiga ba.

 fahad ne yayi murmushi sannan  Yace ko baka fada ba ma anan zamu tsaya.
 ,muma bashiga zamuyi ba .
,dan an dade da daina wannan .
 Shr tayi tare da kamkame jikinta waje daya tsoro ne ke sake kawo mata ziyara .
tun tana jiyo hayaniryasu sama sama har tadaina taji dif...alamun basa cikin gidan sun fice .
 
Juyawa suka sake yi tare ya raka su , fahad na ta mishi tsiya iri iri 
Cikin sauri sauri "gudu gudu yashigo parlour sbd ruwan daya sake yin karfi duk ya jike masa farin yadin dake jikinsa . 
Ya tsaya kulle koina .

Ahankali ya murda handle din kofar dakinta yajita a kulle .
Ganin alaum murda kofa yasa ta sake mikewa tayi  taje ta bude masa .
Tana may   sunkuyar da kanta kasa . 
.cikin sanyi jiki ya shigo  dakin  tare da rungumeta tsam tsam ajikinsa da hannushi daya "sannan ya ajiye tarin ledodin dake hannushi kamshin dake dakin kawai ya isa yasa kagane rana ce ta musamman....



MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO




Page 31-32




Wani irin shock taji ajikinta " lokacin da shaki mayataccen kamshi turarensa , take jikinta ya dauki kirma.
Zuciyarta  ta tsaya cak ta daina aiki wani lokacin kafin daga baya tacigaba da bugawa da sauri da sauri "mamaki da fargaba ne  suka taru suka lullube ta ,wai itace yau  rungume akirjin Yaya DEENI" abinda ta dade tana mafarkin samu kennan.
 dan haka ta sake lafewa ajikinsa' tare da kai hancinta tsaitin dayafi kamshi ajikinsa .  muryata a sanyaye tayi masa sannu da zuwa tare da lumshe idanunta.
 , sake rungumeta yayi ajikinsa tsam tamkar wacce za'a kwace masa ita, sannan ya amsa da yauwa tana makale a jikinsa ya kulle dakin.
Taba zaci zai amsa mata ba dan ta sake narke masa .

 Ahankali yasoma takowa zuwa kan lullausar center rough   dinsu . 
ya zauna daita yana sauke ajiyar zuciya sosai take mamakin hali irin nashi 
"tamkar ba shi ne wannan maseefaffen  mutumin da kallo daya idan  yayi maka" ya isa ya tarwatsa zuciyar duk wanda akawa shi. 
,hannushi  duka yasa ya cire mayafin dake lullube da jikinta "tare da zuba mata sexy eyez dinshi.
 ,kamshin jikinta da wanda ke gyaraye da   dakin ke sake tsuma zuciyarsa.
,duk da bai tsananin sonta , Amman hakan bai hana shi jin mutuwar da ilahirin jikinsa yayi ba .
 gabadaya jikinsa bbu inda bai dauki sauyi na musamman ba .

A baki ya dinga bata kazar daya shigo daita tare da madarar holandia.

 cike take da fargaba da tsoro Amman haka  tayi ta sha  har Sai da yaga kmr zatayi amai ,sannan ya dakata .
Yace kinkoshi ? A tsorace tace eh ...

sallah sukayi byn yagama ciyar daita ,inda ya dafa kanta yayi mata addu'a ,bai bata lokaci ba gurin aiwatar da ibadar aure .
Narke mata yayi ajiki" wasu abubuwa yasoma yi mata  tare da   cire mata kayan jikinta, gabadaya  wasanninsa sunyi mata nauyi .

Atsorace tasoma rokonsa akan  yayi hakuri ya barta "maimakon ya barta kmr yadda take rokonsa  Amman ina  ji yayi tamkar wata sarewa take busa masa .

Cikin sanyi ya dauki hanyarsa ,shi kansa bai yi mamakin jin kofarta a kulle ba" sakamakon  sanin da yayi  ita din  tarbiyar umminsa ce , sosai yake bi daita ta yadda yake so .

Bakaramin wahala tasha a daren farkonta  ba. domin duk wata wahala da haushin abubuwa da Ummi Ta dinga  masa akanta lokacin ,dayace ita zai aura .
Say ,daya fanshe abinsa sannan ya dawo yana tausaya mata.

Dan shi kansa yasan bai saisaita kansa ba.
 shi da kanshi  ya taimaka mata ta gyara jikinta basu jima da kwanciya ba, suka ji kiran sallah a masallaci dake cikin gidan .
 , ya Mike sanye da jallabiya ya tafi masallaci ita km tayi tata sallar anan .

Taso ta kwanta kwarai  tayi bacci Amman sanin halinsa yasa  tashiga kitchen dan hada masa breakfast .
Koda daya dawo ma   tsammaninsa zai sameta kwance dan yasan ta ji jiki sosai ahannunshi.
 Amman Sai yaganta a kitchen .

" tsaye yake a bakin kofar kitchen din    hannuwanshi duka rungume a saman kirjinsa kallonta hade da ganin jarumtarta dan bako wace macee zata iya aiwatar da wani abu a yadda yabi daita  .


zeenat taji motsin  shigowar mutun ,hakan ya tabbatar mata da mijinta ne ya dawo. gabadaya kamshinnsa ne  ya gyaraye kitchen din .
 karamin murmushi tayi wanda ita kanta batasan dalilin fitowarsa ba.
 ,jin shr shr bai karaso ba har lokacin  yasa taji kmr ta juyo dan tabbatar da yana tsaye ne  ko wuce daki  .
say day tana tsoro ta dago su hada ido.
 dolenta ta hakura sbd yadda taji bugun zuciyar ya canza.
 ,  har lokacin bayanta yake kallo  ,ya tattara  hankalinsa da idanunshi a kanta tsaye tana kokarin hada musu breakfast .
lip's dinshi na kasa yakamo yana cizawa sannu sannu .
 ajiyar zuciya yasaki sannan ahankali yafara takowa zuwa  inda take yayinda still idanunshi ke yawo akanta  har yakaraso gareta .


  Tana cikin tunanin  taji ya rungumeta" ta bayanta  tsam   yana shinshina wuyanta .wani irin faduwar gaba taji zuciyarta tasoma rawa hannunta yakamo cikin ya hade danashi ahankali yasoma  murzawa shi kansa bai san sanda ya dinga lumlumshe idanuwansa ba" dan jin lallausan hannun dayake rike dashi.
   ,da sauri ya bude rikitattun idanunsa dan tabbatar da hannun yake rike  dashi .
ganin da ya yi  tabbas  dat  hannuta matarsa ne yasa yakai bakinsa cikin  tsakiyar hannuta ya   sumbata .wani irin kamshin jikinta ne  ya dinga  kawowa  hannninsa farmaki ya kasa dauke bakinsa daga tsakiyar hannuta  sbd yadda yake jin taushin hannu.
 yayinda gabadaya jikin zeenat ke amsar sakon da Denni ke aiko mata domin kowace gaba ta jikinta a mace take murus .
jikinta na rawa ta gaishe shi . 
ya amsa kawai batare da Yace komai ba .
   , tswon lokacin yana rike da hannuta yana cigaba da murzawa ,jin baida niyyar sakar mata hannu ga wani shauki dake seculating din jikinta.
 cikin sanyi tasoma kokarin zame hannunta daga  cikin nasa.
 haka ne yayi sanadiyar   juyo daita gareshi da yayi   suna facing juna.,
tare dazagaye kugunta da hannushi duka.
cikin wata irin kasalliyar muryarsa may maseefar sanyi da dadin sauraron.
" Yace bacci yakamata ace kina yi. 
"buy dis time ,ba wai  abinci ba.
 , hakan da yayi ne yasa ta zuba masa idanunta.sosai take    kallon  bahagon mijin  nata" dan ra,ayin .
  wani irin kyau na musamman taga ya sake yi mata.
 ,azuciyarta ta dinga furta kalmar alhamdulilllahi alhamdulilllahi..
shima ita din yake kallo kwayar idanunsu cikin na juna suke kallon junansu .
Ahankali ta  ,  lumshe idanunta tare da marairaice murya  tace bbu komai" Ai  zan iya.  idan ka fita say na  kwanta  .

Murmushin gefen baki yayi wanda dashi da bbu duk daya. Km hakan na sake fidda ainihin kyaunsa , Hannushi ke yawo a kugunta yana mammatsa mata tsantsar jiki sannan "Yace waya ce miki fita zanyi yau ?
ahankali ta girgiza masa kai " 
Yace  ko so kike mamanki tace tun yanzu nasoma sakaci da diyarta , girgiza kai ta sakeyi can km tayi sauri tace A'a Yace ok  muje  ki kwanta ki huta " first lov zata aiko  mana da breakfast .
ita kanta tasan Ummi zata aiko musu ,gudun  maseefarsa yasa tashiga kitchen din badan taso ba .daman km dauriya ce kawai irin nata .

Tunanita sakinta  zai yi ,ya wuce, Amman Sai taga ya juyar daita tsaitin kofa ,hannushi still na kan kugunta yana cigaba da mammatsa mata gurin  ,a haka suka shigo bedroom dinsa .
   ,wani irin shock zuciyarta tayi kamshi ne ke tashi Tako ina.
Bin koina take da kallo .komai na cikin dakin green ne hatta setin gado da su mirrow duk green ne.
 bata taba gin dakin da yayi mata kyau ba kmr nashi  .
Ahankali ya cire hannushi a kugunta ya maida su kan dukiyar fulaninta take zuciyar ta buga , bbu inda bai dauki  rawa ajikinta ba . Sakamakon tuno wahalar datashi a hannushi daren jiya .
 shi kansa yaji duk yadda jikinta ya dauki kirma .dan haka ahankali ya kwantar daita a kan bed dinshi .
sannan  ya cire jallabiyar jikinsa ya hawo gadon   ya rungume tsam ajikinsa yana saki numfashi .
hannushi duka ya daura akan Brest dinta yana jin tudunsu lumshe idanushi yayi tare da sake manneta.
Tun tana daurewa  taji yana neman canza salo dan haka ta fashe da wani irin kuka tana bashi hakuri
 daidai kunneta yakai bakinshi shiiiiiiii.......iya abinda ya iya cewa kennan yacigaba da abinda yake ,kuka take sosai  har shesheka Amman hakan baisa deeni  ya fasa abinda yake yi ba ,say ma wani karfe da ya dinga ji yana taso masa .
tana ji tana Gani deeni yarabata da rigar baccin  jikinta.
Cikin sanyi yasoma romancing yana murza dukiyar fulanin.kafi daga baya yasoma   sexy daita  gabadaya kukanta yakaru km hakan datake yi  ke sake tuzirashi bugu da Kari gwara ya soma nuna mata true colour dinsa tasan yanayinsa domin , tasaba  da wuri. da kyar take iya  fidda numfashi gabadaya jikinta ya sake ashe jiya ba wahala tasha ba .
 dan ko dan  yatsanta kasa dagawa tayi.
Ahankali Ta dinga sakin kuka ,kusan 3 hours ya dauka yana abu daya  ,say da komai ya lafa deeni mirgina gefe tare da rungumota jikinsa ,yana sakin numfashi .
Kasa  cewa komai yayi ballanantana ya rarrashita .ita km say kuka take tana jan numfashi idanunshi ya zuba mata take kukanta ya tsaya cak ya koma shesheka ....


Wooooooo deeni kaji kunya lol😃😃😃




MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
   AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO


This pages is for you my special khadeey pinky ina mugun yinka cos ke ta dabance a zuciyar bagudo ,Allah ya bar kaunar dake tsakaninmu muddin rai  you are soooo special to me dear💗💗💗💗💗💗




Page 33-34 


Idanunshi ya zuba mata  take kukanta ya tsaya cak ya koma shesheka ...


Wayarsa ce ta dauki  kara ,sauti may dadi ya karade dakin ,ya mika hannushi daya ya dauko wayar   yana dubawa ganin sunan dake yawo kan screen  din wayar  yasashi jan tsaki a fili ya furta dan matsala kawai .


Sake rungumeta  yayi tsam ajikinsa .
" sannan ya dauki wayar ya mannata a kunnenshi tare da yin shr .
,dumin jikinta ke ratsa nashi runtse idanunshi yayi tare sausauta rungumar da yayi mata . bangaren fk kuwa yana jin DEENI ya dauki wayar ya fashe da wata irin  dariya.
 ,ango  yarinya kasha kamshi irin wannan silent  haka . 
"deeni ya furzar da iska tare da  sake jan tsaki sannan Yace  kai fa mugun dan matsala ne wlh .
 yanzu meyye damuwarka  dazaka Kira mutun  da sanyi asuba .


,fk Yace lallai kace haka man byn kagama cika baki ,kai bazaka auri yarinya ba ,yanzu km an jika shr.
 ,kama duba agogo kuwa  dazakace akiraka da sanyi asuba .

Deeni yace yanzu dai mayye dalilin kiran dakayi ?
Nakira ne naji ko  kashiga daga ciki dan da jin muryarka ,nasan kagama may  gabadaya .

deeni ya waske Yace koma may gaba goma nashiga ina ruwanka .

Yace ok hadanni da zeenat din shemah ke  son magana daita .
, deeni  ya dan dubi fuskarta  yace batada lokacin yin waya da kowa.
Fk Yace   , dan Allah kabawa yarinya waya suyi mgn , kasan Allah wlh bazatayi magana da wata shemah ba.
 ,matar tawa ce wata ,deeni ya daga kafada tamkar fk din na kallonsa  nan day suka shiga yin hira  sama sama .
Km duk lokacin   Zeenat din na lefe ajikinsa. daman km abinda tafi so kennan tajita akan fadadden kirjinsa may cike da yalwar gashi sallama sukayi ,yayainda fk yayi tsokanarsa .da angon yarinya. 

Ahankali ya maida idanunshi kanta gabadaya ya jikinta ya sake  rikide ya dauki  wani irin zafi.
" wanda  hatta hucinta zafi yake fitarwa.
 suna hada idanu tayi saurin runtse idanunta gam dan tsoron kallon kyawar idanunshi take.


 bazato ba tsammani taji ya dauke cak sai cikin bathroom dinsa ahankali  ya direta cikin bathtub .

 dan kansa yayi mata wanka tare   nadeta cikin towel dinsa .
  sake daukota yayi ya dawo daita daki .
"    magunguna ya hada mata ta sha sbd yadda jikin nata ya karayin zafi ga rashin isashin baccin da bata samu ba .


Doguwar rigar jallabiyar sa ya zira mata tare da rungume ta yana shafa sumar kanta  ,tana gama shan magani tayi bacci rungume ajikin deeni say  faman yawo yake  da hannunsa a gashinta zuwa bayanta .


Kusan awa 3 ta dauka tana sharar baccin dan  har sanda  Ummi Ta aiko musu da breakfast bacci take  bata tashi ba .

Ummi takira wayar deeni byn ta tmby maryam ya zeenat din take .
 tace ita sam  bata ganta ba.
 Kira biyu tayi cikin na uku deeni  ya dauka da sallamarsa ,tare gaishe ta fisrt lov antashi lfy tace lfy ya kuka tashi .
Yace lfy lau ina zeenat din take?
 dip deeni ya dauke wuta kmr wutar NEPA dan bai zaci zata bmyeshi ita ba . say da ta sake maimaita tmbyrta ,muryasa a sanyaye ,yace lfy lau take first  lov , wani abu ne ?

a zafafe tace bangane lfy  lau take ba , dan Allah ni hadani da yarinyata naji muryarta .
yace bacci take ,wani irin bacci ne har  buy this Tim  take yinsa ,cikin haka Zeenat din  ta farka ta Mike zaune  da sauri ya hawo gadon tare  cewa yauwa gashin nan nan ma  ta tashi .
,ya Mikewa zeenat din waya ,shi km ya zauna kan stood din dakin ya zuba mata rikitattun idanunsa.

 ,hello  Ummi ,Ummi ta sauke ajiye zuciya sakamakon jin muryar diyar garau .
Hello ummina  ina kwana , Ummi tace kwana yanzu kin duba lokaci kuwa zeenat wani irin bacci kike yi haka ,kafin tace wani abu tacigaba .
 kina day lfy ko ?
,cikin sanyi murya tamkar ta may shirin zubda kwalla tace lfy lau nake ..... Sai lokacin deeni ya sauke numfashi bbu wani damuwa ko inji cewar Ummi ?
Zeenat ,tace bbu komai.
 to  ayi ta hakuri kinji tace to Ummi.
 ,tayi mata sallama.
 tare da mikawa Yaya DEENI wayarsa .
ta sunkuyar da kanta kasa kawai .
 amsa wayar yayi tare da hadawa da hannuta ,ya janyota jikinsa ,ina ke miki ciwo yanzu ta girgiza masa kanta kawai ,yace kinsa fa bana son kyaliya ,ki bude baki kimin magana tace bbu inda kamin ciwo yace gud  ,zaki iya tafiya yanzu tace eh ok to  muje dakinki ki canza kaya .



Tare suka shiga dakin tana manne  ajikinsa ita sam abin nasa ya daina bata tsoro yadawo bata  mamaki kwata kwata tamkar ba Yaya DEENI din data sani ba gabadaya ya canza mata . 
Ya sauya hali say wani jiji daita yake .


Wajen wordrob dinta yakaita sannan ya dawo ya zauna zaman jiranta .

 atamfa ta dauko dinkin Riga da sike ta sanyawa jikinta ,dinkin yayi matukar karbar jikinta gabadaya ya fito da ainihin dirin jikinta ,tayi kyau sosai.
Farinta har daukar ido yake .
 sai day bai ji kyawun nata ya ratsa shi ba ballanantana ta tsaya masa arai.
 tabbas yasan yana jinta  ajikinsa Amman ba zuciyarsa ba .

, Hannushi ya miko mata tasanya nata cikin nashi yamatse hannu gam tare zaunar daita kan cinyarsa a zabura ,zata  Mike ya maida ita.
 yace  zauna mana kmr ba cinyar mijikin ba.
Sai  naga kmr   wani dari dari kike.
Yace kinyi kyau fa  da wannan kayan.
 ta makale kanta cikin cinyoyinta sake  mannota yayi da jikinsa sosai suke ji. Numfashi juna .
 ,yace fada min gaskiya mayye ra,ayinki akai na tayi shr taki cewa komai yacigaba  Ina tunani kmr  daman can kina sona ?

 Duk da  halin da take ciki na faduwar gaba sbd yadda ya makaleta ajikinsa.
 hakan bai sa ta fada masa gskyr daya ke son ji daga gareta .
  aranta km cewa tayi wannan mutumin wayo kawai yake son yi min.
Ahankali  ,ya dago fuskarta ya kalli cikin idanunta ki fada min, dan zan iya gane in kiyi karya 
Kwayar idanuki kadai.
 zasu nuna min .

Jin haka yasa batasani  lokacin data furta daman can ina sonka ,kai fa kana sona..? 
Cikin wata mayaudariyar murya tayi maganar.
 ,kawai sai jin lip's dinshi tayi kan nata yana  tsotsa.
 ,yafi karfin  minti goma ya tsotsa bakinta tsoronta daya kada ya gota daga hakan dan gabadaya jikinta ciwo yake mata  hatta cinyoyinta ciwo suke mata .

Cikin sanyi ya zare bakinsa daga nata sannan Yace kinsan wani abu har zata girgiza masa kanta, sai km tayi saurin cewa  tace A'a  ,yace ina son mu fahimci juna .

 A ranta tace abinda yakamata yazama farko shine ya zama karshe.

 tamkar yashiga ranta yace zaki ga abun kmr bbu tsari ko ?
 Kafin tayi magana yacigaba 
Ni irin nawa raayin kennan.
 tace to.cikin sanyi muryrsa Yace kinsan da sanin bana son kazanta ,km har yanzu haka nake ban canza ba.

 Km bana son duk inda zan shiga a gidana na shaki wari km banason inganki bbu tsafta ko in shaki wari daga jikinki ko na  iske ki bbu kaya ajikinki "matsawar ba wanka zakiyi ba .

Nasan kin fi kowa   sanin   dokokina ciki har kuzarin jikinki saboda kin san  ni dan oya oya ne komai Ina son aminshi cikin hanzari . 
To ta sake cewa.

 yace ok ina sauraro naji naki cikin sanyi murya har da in inna ...tace ni ni duka da zagi ne kawai  bana so say km tayi shr takasa cigaba .

Yace uhmmmm ina jinki tace uhm shikennan bbu komai  yace A'a da komai da  alamun akwai sauran  magana a bakinki .
tace uhmmmm barshi kawai yace Aa ki sanar dani kar na aikata  miki cikin rashin sani , fada min duk abinda ke zuciyarki .

Tace umm... amm... Dama har da kishiya  bana so .
shi kansa shr yayi tare da zuba mata rikitattun idanunsa, lokacin daya ji karshen maganar.
Ita kanta  tasan  mamaki jin abinda tace ne.
Yasa shi yin shr .
 itama shr tayi jikinta yasoma rawa dan a tunaninta ko ta bata masa rai ne .

Can km yace bazan miki alkwarin haka ba .ni mutun ne kmr kowa km basan may zai faru dani a gaba ba .
Wata killa  kara aure yana cikin kaddarata. duba da komai rubutaccen tun daga lauhin mahafuz.
 ,ki fahimce ni da kyau bazan miki karya dan kiji dadi ba .
shawara daya da zan iya  baki kiyi kokarin ki tsare min duk wasu , hakokina da suka rataya  akanki.

 killa idan kika kiyaye kika yi  haka, bazaki rage gurbin wata diya macce ba. Km ba mamaki bazan yi shaawar kara aure ba .
shr tayi taki cewa komai zuciyar ce ke tsalle tamkar zata fasa kirjinta. hakan yasa ta runtse idanunta gam tare dafe cikinta  ganin haka ya dauka ko yunwa take ji dan haka yajata suka yi Denning area.


Tare suka karya lokacin biyu saura daidai agogon dake parlour ya buga.

 dakinsa ya sake janta har cikin bathroom dinsa ya kwabe zigidir dashi da sauri tasa  tafin hannuta Ta rufe idanunta.
 ya dan tabe baki ,sannan Yace dama kin cire kunyar nan' dan mun rigada muzama daya yanzu.
  sannan yace tazo ta cuda masa jikinsa tun tana jin kunyasa har ta ware .

Tunda daga ranar komai zamo  tare suke yi  matsawar yana gida .

wata irin kulawa yake bata na musamman wanda har mamaki take idan yana wasu abubuwa.

 sai day tana gane kurenta gurin kwanciyar aure .

dan yi yake tamkar baisan daga inda tafito ba ballanantana ya tausaya mata .

 domin kwana yake yana abu daya da asuba ma  sai yayi sexy daita yake fita masjid.
 abun duniya fa yasoma isarta abu kmr abinci  safe rana dare ,  duk abu daya .
har daga office ma  dawowa yake .
,iya juriya tanayi dashi shi .
km yana ji daita kmr ya lasheta .


zuwa yanzu al'amarin deeni  ya fara damunta dan gabadaya bata da wani  hutu , ko motsi taji sai gabanta ya yanke ya fadi .
Cikin kankanin lokaci ta zabge  tasoma rama.
 sai day ta kara haske tayi kyau jikinta ya goge .


Ummi tana ta dinga jin muryar  diyar  akai akai gashi bbu waya ahannu zeenat din .
dan haka takira deeni tace idan yataso aiki yazo tana son ganinshi .


Zaune yake a gaban umminsa ya tankwashe kafafunsa waje daya  yana dubanta byn ya gaisheta ta amsa.
 itama idanu ta zuba masa ,tana kallon yadda Ta  sake fari fiyye da da.  yayi kyau sosai fatar jikinsa ya sake gogewa.

 , ahankali tace deeni kayi kyau sosai da fatar tawa Yar tayi fiyye da haka?
 

, murmushi yayi tare  da dan soso keyarsa da key din motarsa , muryasa a shagwabe Yace  Ummi tayi kyau sosai har tafi ni. murmushi sukayi a tare say naganta zan tabbatar .
Shikennan nan  tace sai km mgnr waya ko say an roka dan naga  har yanzu kaki say mata waya.
 ko ma dinga  gaisawa da ita  akai akai, Tunda ka kulle min ita a gida  .
Amman kai kullun kana kan hanyar zuwa .

 murmushi ya sake yi Yace kmr kin shiga zuciyata wlh Ina da niyar sai mata Ai .
 ,tace a hanzarta dan  day yakamata.

 ,hira suka dan taba da umminsa sannan yayi mata sallama ya fice  .
 cikin sauri sauri gudu gudu ya fito daga part din Ummi .





MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗





AYSHA  A  BAGUDO



Page  35-36


Key din motarsa ya danna tun kafin yakaraso gareta ,budewa yayi yashiga yatada motar. dayake gidansu "
 da dan tazara kadan dan ummi .



Tana tsaye  byn tayi sallar isha'i  ,da shafa'i da wutiri .
Tasan duk inda akayi may gidanta na kan hanyar dawowa.
, Dan haka tashige bathroom  ta sake yin wani wanka.

 kwalliya tayi sosai duk da cewa tana cike da fargaba  dawowar mijin nata amman hakan bai hanata cakarewa cikin wasu matsatsun kananan kaya iya cinyarta   .

 Tana jin karar bell din tayi sauri  ta dauki turare kan mirrow  ta feshi ilahirin jikinta dashi.
kafin takaraso har an fara  nouking din kofar gidansu.
 da sauri karasa taje ta bude .

Tsaye taganshi cikin kakinsa na solider hannushi rike da jaka .

 fuskarta dauke da murmushin karfin hali ta amshi jaka da lailon din hannunsa tare da yi masa sannu da zuwa ,

Ya amsa tare rungumota  ajikinsa.
  ,fargabanta ta sake nukuwa fiye da wace take ciki.
  tana rungume ajikinsa ya rufe kofar.
  bakinsa ya hada da nata yana mata wani irin hot kiss datake jinsa  har cikin brain dinta har ta nemin fargabanta tarasa .


Har suka iso cikin bedroom dinsa bay barta tayi nisa dashi ba .
 Ya manneta a jikinsa tsam .
" say nanukarta jikinta yake ,tare da taba duk inda hannushi yaci karo dashi  a jikinta. musamman ma dukiyar fulaninta . Ahankali ta zame jikinta daga nashi .

Kwantawa  yayi flat tare fizgota , Ta fado saman kirjinsa " tana sakin numfashi .
Amman fa duk tsorace take dashi .
 Cikin sanyi jiki  tasoma balle masa Maballin rigar  white single dinsa fara qal ta bayyana.
 ta  zubawa kirjinsa ido tana kallonsa duk da bata hango kwantaccen gashin kirjinsa ba.
  taga hango kan nipplys dinsa. 
Shima ita yake kallo.shr kusan minti biyar batayi magana ba "say  shi .

muryasa a raunane Yace  kinyi kyau fa matars kwalliyarki  tamin kyau  sosai .
tayi murmushi tare dacewa Nagode .
 har mamaki yake bata wani lokaci idan yana wani abu . Ta dinga tunanin 
Ina girman kai ?
Ina nuna isa da ji da kai ?
Ashe dai mace itace rayuwar namiji .
Idan ba mace a rayuwar namiji ' jin dadinsu ragagine .

Ahankali taji yasoma kokarin zare mata   rigar jikinta,kafin ta ankare har  ya cire tare yin flinging daita 'sannan ya damki dauki fulaninta.
 'Gabanta taji ya tsananta faduwa  da sauri.
 ,tana jin yadda hannushi  ke yawo a kirjinta ,tasan  yanzu labari zai canza salo .
 ,kmr an sinkureta ta zabura zata Mike hakan yasa  ya sake maidaita jikinsa ya sake kai hannushi kan kirjinta dayake cike bam yasoma murzasu wani irin tsanyi da faduwar gaba ta dinga ji yana bin jikinta.
 ,tana matukar kaunar son kasancewa tare  da mijinta Amman tarasa dalilin dayasa duk sanda zai zo mata da bukatarsa gabanta ya dinga faduwa kennan dan gaskiya takasa sabawa da  jarabarsa .

 Haka kawai taji hawaye na shirin zubo mata dan haka  ta fashe da wani irin kuka " yayainda kirjinta ke bugawa sosai kmr zai tsage , gabadaya hucin numfashinta da kamshi turarenta yacika masa hanci.
 jin kukanta yasa ya hade bakinsu waje daya tare da kefe  hannushi daya kan nipply dinta yana murzawa ahankali.
, tsoro da fargaba suka hannata kasa maida masa martani kmr yadda ta tasaba ,

Jin taki yin shr ,da bashi hadin kai yasa ya tunzura  a zafafe ya bude rikitattun idanunsa ya zuba mata batare da Yace mata komai ba .
Sakinta yayi tare da ware hannuwansa akan bed ,still ita din yake kallo mamakinsa yake karewa akanta .
"  cikin tawa irin rikitatacciyar murya .
wani irin iskanci ne haka ?
 wani abu na miki ,kikewa mutane  kuka ?
jikinta na rawa tasoma girgiza tana bashi hakuri .
Wani kallo ya watsa mata alamun bar jikinsa .
a hankali tayi karfin zame jikinta daga gareshi.

Tsaki yaja tare da mikewa iskanci banza kawai ,sannan yashige bathroom ya barta nan tsaye da dan guntun kukanta .
 ,ita km daman abinda take so kennan yayi zuciya  yabar yau daya dai  ta samu  huta .
 kullu abu daya babu hutu 
dan haka bata tsaya  wani jiran fitowarsa ba takara gaba tayi dakinta har da sawa kofarta key .



Washegari da safe tashigo dakinsa da sallamarta.
 ciki ciki ya amsa mata  fuskarsa murtuk dan ko amsa gaisuwar data yi masa baiyi ba.
Ganinta da cup a hannu ya tuzirashi ,dan haka ,ya sake daure fuska tamau Yace lfy ?
cikin wani irin sautinsa na sali wanda tasan shi dashi.


Jikinta na rawa tace dama..dama.... coffee ne ...tun kafin takarasa Yace fita dashi ina  azumi .
tsoronta da fargabanta suka Karu tace dan Allah Yaya kayi hakuri wlh jiya banida l....

Ke ya katseta fita nace kafin na takaki .
da sauri Ta fita tana goge kwallar data zubo mata .

Wunin ranar a sukwane tayi shi ,tana mamakin yadda lokaci daya yake canza launi tamkar hawainiya.


Kimanin kwanaki uku  kennan yayi mata dip .
ko gaishe shi tayi baya amsawa say yagadama  haka ma ko abinci takawo mishi Sai Yace yana azumi .

Abin duniya fa yasoma damun zeenat hankalinta ya tashi matuka .
ita ba waya a hannu ba ballanantana ta Kira Ummi ko tadan rage jimami abinda ke damunta .
komai ya taru ya tsaya mata .


Gashi dai kullun sai sun hadu kafin ya fice haka ma idan ya dawo  Amman kwata kwata ya daina shiga harkarta.
Ya shareta ,shaanin gabansa kawai yake .


Misalin karfe hudu taji karar bell ,taje ta bude da sauri dan tasan shine sai day tayi mamakin  dawowar sa  gida da wuri .
Gefenta yabi ya wuce batare daya kalleta ballanantana ya amsa sannu da zuwan datayi masa .
Kai  tsaye kitchen Yashiga  ya bude Frij ya dauko ruwa may tsanyi.
,ya balle murfen bottle din tare kafa bakinsa .Bai dauke ba ,
Say daya sha rabi tukun   ko minti biyar bai yi ba .
Ya fito tare da  riko sauran ruwan  ahannunshi  ya sake wuce ta a parlour ya tana sake  mishi sannu da zuwa.
Harara ya watsa mata take ta dauke idanunta akansa kau dansa yayi ya shige bedroom .

 Yana shiga ya fada   akan makeken royal bed dinshi batare da ya cire kakinsa ba idanushi a runtse gam .yana jin yadda zuciyarsa ke tafasa wato ita tafi karfin tayi masa laifi tabashi hakuri ko .
Kyacci yayi .

 Ahankali tashigo dakin .
Yana kwance ta iso gurinsa gabanta na dokawa da sauri .
Amman bata fasa abinda tayi Niyya ba.
  ,duk da tana  zaton da zarar takaraso gareshi  zai daka mata tsawa tare da korarta .

Har Gabansa taje ta tsugunna tasoma kwance mishi takalmi kafarsa .
,ta ajiye a gefe sannan ta kwashe kafafunsa ta maidasu kan bed  har lokacin idanunshi biyu amman suna lumshe km yaji shigowar sarai da duk abinda take.


Kusan minti goma tana tsugunne ahankali taga ya Mike zaune , batare da  kalli idanunta ba.
 yasoma kici kicin cire rigarsa ta Mike da sauri tasoma balle masa boturan gaban rigarsa sannan ya cire rigar ya saura daga shi say  farar singlet ita Yakama ya cire .
Ta zubawa surar jikinsa ido , kwantaccen gashim kirjinsa yasoma tsumata dan itama zuwa yanzu tasoma jin bukatar mijinta .
 ahankali ta dauke idanunta ya cire wandonsa Sai gajeren wando boxe ,ta tattara takai ma,ajinsu ,ta dawo kusa dashi Ta zauna cike da fargaba.
 ,Shr dataji yayi mata ya nuna  alamun  ya sauko ba kmr shekaranjiya daya dau zafi daita ba.
Koma yayi ya kwanta ya runtse idanunshi tare dayin pillow da hannuwanshi .

 hannuta na rawa  Ta daura  saman kirjinsa tasoma shshafa  kwantaccen gashim kirjinsa .
shr yayi mata yana jinta ya shareta hakan yasa taji karfin cigaba har da kai hannuta kan nipply dinsa.
  ganin  hankalinsa yasoma tashi  yasa ya rike  hannuta cak  , atsorace take kallosa ,yayainda jikinta ya dauki kirma , ahankali ya bude rikitattun idanunsa ya zuba mata , tsawon lokaci yana kallonta sannan ya Mike tare da nuna mata kofa da yatsansa out .... before I finishe you now  zatayi magana ya katseta bason jin komai daga wannan stupid mouth dinki .
 ki fita kawai deeni bai da bukatar ki.

 ke har kin isa kimin wulakancin akan halalina .
, Allah Yaya ba haka bane kaki ka fahimce ni ne.
 , a zafafe Yace  baza'a fahimceki ba.
 kifita tun raina bai gama baci ba.
 badai ,takama zakimin akan  abinda yazama nawa ba ya nuna kirjinsa ya yatsansa.
Kinsa Allah ni km wlh bazan taba  baki hakuri ba akan hakina ba  .
 ,gashi nan na bar miki abinki kije  kijika ki sha.


  , tasoma kuka tana rokonsa yayiwa Allah yayi hakuri wlh bazata sake ba ,kima sake say kinga an damu da jikinki naki  ba tukun zaki kawo wa mutune rainin wayo.

  ,Kuka take sosai tana bashi hakuri ok ba zaki fita ba kennan.
 ,ganin yana shirin saukowa daga kan gado.

 yasa tabawa kafarta iska tun bay sabauta mata jiki ba ..


Haka tayi ta kuka tana datasanin abinda tayi ta sake zabgewa ta rame tamkar ba sabon aure ba .


Anyi haka da kwana biyu  ya isketa  zaune akan Denning tana yin breakfast .
Shi km yana sanye cikin kakinsa    ,ta gaishe shi  yana ciccin magani   ya amsa mata  ba yabo ba fallasa .
,sannan Yace ni zanyi tafiya ki duba abinda bbu a gidan .
Ta sauke ajiye zuciya tare da zuba masa ido tace  akwai komai ya ajiye mata kudi masu yawa ya wuce batare da sanar mata inda zashi ba .


Byn tafiyarsa da kwana biyu Maryam takawo mata ziyara cike da  farincikin ta tarbeta suka rungume juna.
 suna murnar famin junansu .
 ,taje takawo mata snacks da drinks suka zauna anan parlour suna ta hirar yaushe gamo , Maryam ta dubeta da kyau tace zeenat Sai naga kmr kin rame.
 , Zeenat  tayi murmushi Yace  Allah kawa Maryam tace wlh kin rame sosai ko ciki ne dake  
Zeenat tace wlh bbu ko daya zazzabi nayi kwana biyu shiyasa kika ganni haka.
 amman na samu sauki yanzu ,Maryam tace Allah ya sauwake .
 su Sumy da rukky ma  sun so zuwa gurinki wlh  amman suna tsoro wannan budadden mijin naki ,nima dan nasan yana aiki shiyasa nace bari lallabo nazo naganki  Sai da Ga numbers dinsu  sunce na baki.
Zeenat ta karba numbers din dake rubuce a Yar karamar white paper tana murmushi haba Ai da kinsani  kinbari kunzo  tare.
 dan baya ma nan yayi tafiya.
 , Maryam tayi tsalle ta dire kan kujera tace kice nasha shaani yau .
 Allah  na dauka yanan ne shiyasa kikaga na natsu kar bafa bansani ba  ,suka  kwashewa dariya .,


Kusan nan maryam ta wuni har yamma  suka shiga kitchen suka yi girki tare .
byn sun ci ta zubawa Ummi itama tace dan idan zata  wuce ta Mika mata say datayi sallar magrib sannan ta wuce .

Sai yakasance kusan kullun Sai Maryam tazo mata hira hakan ya dan sa hankalin zeenat din ya kwanta .


Wata sakaliyar rana sai gashi ya dawo fuskasa a sake sosai ba kmr lokacin da zaiyi tafiya ba .
,ta amshi jakar hannushi bai hanata ba , takai masa dakinsa ta ajiye takama gabanta,


washagari gidansu ya cika da mutune makil wai ashe Karin girma yasoma agurin aiki .
,amman  yakasa sanar mata .
,taji ciwon abun aranta sosai.
 amman hakan bai hanata zuwa har dakinsa tayi masa murna.

   ,yawancin yan estate din sunzo yayi shi murnar karin girman dauasamu .
 Amman banda Ummi .

 gabadaya yanzu dokin ganin Ummi take .
kusan wata hudu kennan rabanta daita duk dare say tayi kuka tare datasanin auren deeni Allah Ummi kin gargade ni amman ,nayi patali da maganarki ,


Wani dare ne tayi tunanin gara taje ta nemi sulhu dashi ,da zaman kuramen ya isheta zata   sake gwada kai masa  kanta gareshi .
,bai kamata dan shi yayi fushi daita.
 ,itama tayi dan haka tashirya tsab  cikin wata yololuwur rigar bacci  wacce bata wuce iya  gwiwarta ba rigar bacci may sharasharace sosai da wandonta  wanda kasanta  kawai ya rufe amman bayanta ana hango bombom dinta .
 bbu abinda rigar bacci takare ajikinta ana ganin komai miraransa Sai kamshi ne  ke tashi ajikinta.
 ,zuciyarta a dake ta nufi dakinsa ,

A kwance ta iske shi daga shi Sai towel daure a kungunsa ,wanda ya nuna alamun daga wanka ya fito.
 kallo daya yayi mata dauke kansa tare runtse idanunshi gam . sakamakon wani shock daya ji ajikinsa tamkar an jona masa wutar lantarki . 

Tana karasawa kusa dashi bata tsaya wata wata baTa fada saman fadadden  jikinsa tare da hade bakinsu waje daya tana mishi irin sumba dayake jinsa har cikin kwallwarsa .
 ahankali ya bude rikitattun idanunsa ya zuba mata idanunta a runtse take cigaba da tsotsan bakinsa.
 kasa yunkurin hanata yayi dan shima a bukace yake daita, dauriyace kawai da girman  irin nasa  yanashi nemanta.

 hannunshi dukka yasa ya zagaye kugunta dashi  tare birkitota ta koma kasa ,shi km yakoma samanta still bakinsu na hade taki sakar masa .
,hannushi yakai kan kirjinta yasoma  murzasu brest dinta yana lumshe ido .
 ,wani irin dadi tadinga ji yana bin jijiyoyon jikinta tare da bata wani irin murza take brest din tare da bata  romantic kiss .
  gabadayansu sun fita haiyacinsu basa ji basa Gani .
Sai daukin juna suke dan ita kam harda sambatu take zubawa ,dan Allah Yaya ..kayi hakuri kar kara irin wannan fushin dani .mutuwa zanyi uhmmmm wayo dadi  haka tayi tayi ,yasa hannunshi ya toshe mata baki yacigaba da aiki  km yasamu baza Sai hakarta yake  bashi yabarta ba Sai wuraren karfe uku  na dare tukun ya saura da mata shima bawai dan yagaji ba Sai dayaga numfashinta na neman tsaya dan har kuka ta dinga yi ahankali ya cire hannushi daya rufe mata baki dashj ya kalli cikinkwayar idanunta da suke a lumshe tabbas yasan taji jiki dan haka ya Mike tare da shigewa bathroom . 
Byn ya fito ne Yace ta tashi taje tayi wanka 

ta watsa masa kanunun idanunta tace  nagaji Yaya  say anjima zanyi bai sake cewa daita komai .
ganin haka yasa ta Mike taje tayo wanka ta dawo tashige jikinsa ,tana sake yamutsa shi ,  bai hanata ba say ,ma kara  manneta dayayi .

Sun koma sun shirya kmr  tamkar babu abinda yataba  shiga tsakaninsu duk abinda tasan zata masa yaji dadi shi takeyi shima yana ji daita yadda Yakama.
 har waya ya say mata kirar aitel may  finger print .
km har yau bai barta taje ganin Ummi ba.


Ranar da tacika wata shida daidai Sai ga Ummi tazo .
 , Ummi nason ganin diyarta , kwaici kawai  take yi.
 amman ganin deeni bai san tanayi ba yasa tazo kai gara tazo  .

 Duk inda zeenat tayi idanun Ummi na kanta ta kawo mata ruwa da abin ,tabawa ,tazo ta zauna kusa daita tarasa inda zata sakata taji dadi  har kuka tayi dan murna  tace Ummina nayi kewarki ,Ummi tace mamana kewa Ai ba'a magana .
,shine km zakiyi kuka ,kuna dai zaune lfy.
Zeenat tace lfy Ummi ina samun kulawa sosai a gurin Yaya.
 amman shine naga duk kin rame kina cin abinci ma kuwa ,ina ci Ummi zazzabi dare nakeyi shiyasa ,duk dare Sai nayi zazzabi.
 kunje hospital ?
,tana shirin bawa Ummi amsa taji karar bell ,Ummi ina zuwa ga ma Yaya nan ya dawo da sauri taje ta bude ya rungumota ajikinsa yana kis din wuyanta tare da sakin ajiye zuciya ahankali tace Ummi fa tazo ,tana ina ?

Tana parlour a zatonta zai saketa ne Sai ma taga ya sake manneta da barin jikinsa har parlon suka shiga ahaka.
 ya zauna tana jikinsa ahankali ta zame jikinta ta koma kusa da Ummi dan su gaisa sosai.

Takawo masa abinci Yace shi a koshe yake nazo na duba ki ne kawai dan nakira wayarki batashiga .
tace km a kunne take fa  Killa dai  matsalar network ne .
Ummi ta zuba mishi  ido da  kyau yayi kiba sosai .
, ahankali takira sunanshi  taredace ,yana  naga kai kayi kima sosai ,ita ko diyartawa duk ta zuke ta  rame .
,ya dube inda zeenat din take ashe bani kadai nake ganin haka ba.

 ,Ummi tace to kunje hospital ne ?
Yace A'a to kuje a dubata  karkabarni magani tukun asan abinda ke damunta   dan ramarta tayi yawa.
 .a tunanin Ummi ko ciki ne da zeenat din shiyasa tace kar,abata magani.
 
Zeenat tace Ummi ni fa bbu inda kemin ciwo lfy lau Ummi tace duk da haka gara  kuje aduba lafiyar ki .
,tare da sake maimaita kuna dai zaune lfy ko..Yace haba dai Ai diyartaki tana da biyayya sosai Ummi tayi murmushi tare godewa Allah sannan Tace Allah yayi muku albarka yabaku Yaya na gari.
 deeni ya amsa yana may kashewa zeenat din ido .
 ,Ummi ta sake yin murmushi to bari na wuce zeenat tace haba Ummi daga zuwanki har zaki wuce na dauka wuni zakimin.
 ina kika taba ganin uwar dake kawo diyarta wuni gidanta ?
 , zeenat ta shagwabe fuska tare cewa to a fara a kaina ,Ummi tace uhm tafiya zanyi , to kibari zuwa  anjima Sai ki wuce a fakaice deeni ya zabga mata harara ke zaki mata aikinta ?
  Zeenat Ta sake shagwabe  fuska dan Ummi ki zauna banason ki tafi yanzu.
 deeni ya kawo hannushi ya mintsine gefen cikinta har yasa ta danyi tsalle.
 ,Ummi ta nufi hanyar fita tana fadin mamana kina in zauna shi km deeni korata ma yake da sauri km cikin murmushi Yace haba first lov ni na isa  taya ma  zan koreki byn nima yanzu zan koma nazo dubata ne kawai.
Dawo  kuyi zamanku.
  ,duk suka sa dariya ita , zeenat tagane sarai abinda ya maidoshi gida .. shiyasa batason tafiyar  Ummi.

Ummi ta bude kofar ta fita ,deeni ya bita yayi mata rakiya ..

Byn ya dawo daga yiwa Ummi rakiya ne  ya sameta tana dan gaggyara waje.
 ya dauke cak Sai  bedroom dinsa ya direta akan gadonsa .

Ya jawota jikinsa tare da dago fuskarta kinsa sarai abinda ya kawoni shine dan iyayi  kike rokon first lov ta zauna ko ?

Gabanta yashiga faduwa amman Sai ta daure tayi murmushin yake .
tare da cewa Allah ba haka bane nayi missing dinta dayawa  ne  shiyasa banason ta tafi .

 gabanta yacigaba da dokawa ko shi kesata rama batasani ba  ,duk wanda yaganta Sai yayi maganar ramarta .


Cikin wani irin salo deeni  yasoma romancing dinta haka ta dinga  daurewa tana bashi hadin kai banda ranta taso ba.



MMN SUDAIS CE
[5/7, 4:04 PM] ‪+234 818 621 2985‬: 💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO



Page 37-38



Iya dauriya zeenat tana yi da jarabar deeni Amman shi sam baya Ganin kokarinta .
saboda tana nuna  gajiyawarta akan bukatarsa dan haka kullun yake aikin  kiranta da raguwa . 

Ummi tasake yi musu zance zuwa asibiti Amman zeenat ta fitittike taki zuwa ta maida zance shiririta.

 , idan ma  akaci sa'a DEENI  yayi mata  zance zuwa asibitin  Sai tasa masa  kuka tace ita akalleta fa bbu abinda ke damunta km bbu inda ke mata ciwo.dan haka deeni  ya tattarata ya watsar .

Abu daya zuwa biyu ke damunta km yake ci mata tuwo akwarya bai wuce yadda deeni yakanainayeta a gidansa ba , sam baya kaunar abinda zai fitar daita yau tsawon watanta bakwai kennan  da  kawota gidansa .
Amman ko sau daya deeni bai taba kuskuren barinta ta fita daidai kofar gidansu  ba.
 ,say dai kullun tana gida yana faman aikin  susukarta ,ba dare ba rana .


Three month later




 kwance take akan gadonta yayinda  tayi zurfi cikin tunanin budadden halin irin na mijin ta.
  Wanda shi  sam tamkar hawainiya yake may yawon  canza yanayi a duk sanda taso.
  idan har bashi yake son abu ba bata isa tasashi yin abu  dole ba .
Km muddin  tana son zaman lfyrta dashi Sai day  duk abinda yake so shi zatayi km duk  lokacin dayazo da bukatarsa ,a saurareshi km abashi hadin kai .
,hakan kadai zaisa taga walwalatsa  da fara'arsa Amman sabanin haka ,tashin hankali ne gareta .

 Ya dawo daga aiki ya iske kwance yake gaya mata shemah ta haihu.mikewa zaune tayi tana  murna tare da tmyrshi yaushe ta haihu yana murna shima tamkar shi aka haifawa   Yace  dazu ne da rana nima  Allah ka nuna min nawa haka dan yanzu bbu abinda nake da buri kmr naganni da dan cikina ,ya fada yana kallon fuskarta .
batace komai ba say ma tabe baki datayi  ,dan ganinta baida buri may ma,ana . 
Jikinta a sanyaye tace tana gida ne ko asibiti tana asibiti  ance ma tasha wahala sosai dan har yanzu bata farfado ba tukun  take gabanta yashiga  dukan uku uku a ranta tace  kunji irinta ko ba daukar cikin ba . wahalar dake ciki.  haihuwar .
 yana dan  murmushi har dimple dinsa ya lotsa  sannan yacigaba fk Yace a gasheki tace gidan kaje a zafafe Yace  A'a a bakin get muka hadu, dazaki min wata irin bmy.
 tace  Allah sarki to Allah yabaka hakuri .
tace gobe kuwa  inshaallahu zani na dubota .


Washegari gari dazai fita byn sun gama  karyawa  taji bai ce mata komai ba har tarakasa parking lot yana niyyar shiga motarsa .
 tace Yaya bakamin magana ba  ,batare daya juyo ba Yace ta me fa ?
Game da zuwa barkan   shemah.
 Yace eh naso kije yau din say day sauri nakeyi ana jirana a office.
Amman idan  na samu lokaci maje tare 

take tasakar masa kuka shagwaba tana, didira karfata kasa tare da cewa   shemah ta haihuwa shine zaka hanani zuwa ga baki ga hanci .
gashi Ina son naje naga  Ummi ,ya hade rai tamkar baita dariya ba ,yakoma mata   asalin deeni din datasani .
Ai kinsa sakarai ne ni da zanbarki kifita  ke kadai.

 ke.... naga jiya ne akayi haihuwar shine kike rawar jikin zuwa ,banason nasake jin komai daga bakinki byn a dawo lfy tarigada tasan halinsa Tunda Yace bazata ba to kuwa bazai barta ba.
 ,dan haka tace masa a dawo lfy Allah ya tsare ya dan saki fuska tare da kamo hannuta yana   murzawa acikin  nashi jin zai sata taji wani yanayi yasa tayi saurin zamewa tayi cikin gida .

Washegari tana zaune da misalin karfe uku rana  hannuta rike da waya tana  yin what's app
yakirata  byn ta dauka yakece mata takira number shemah ance ta farfado tun jiya  .
cike da murna tace to....layin shemah din tashiga nema byn sun gaisa ta tmbyi bby tace da wa yake  kama tace da Yaya faruk mana.
Zeenat tace da wahala ko ?
Shemah tace idan ma da wahalar nan gaskiya zuwa yanzu na kusan  mantawa ,Tunda ina ganin  yarona yana  cikin koshin lafiya .
to masu ya'ya mara kunya ga bakin nan radau kmr bakisha ruwan zafi ba , shemah tace tuni Ummi tamin zeenat tace shiyasa naji bakinki radau Tunda kika ce Ummi ai nasan bazata matsa miki ba.
 say yadda kikayi to bamu yarda ba wlh  zanyiwa aunty waya da kaina akawo miki umma ta zauna dake ta gasa mana ke da kyau.

 shemah tace muguwa kawai so kike umma takassarani bbu damuwa zan miki tanadin naki  Tunda ance kema kin kusa, haka dai kuke cewa amman ni banwani kusa ba, har yanzu  kuna shakawatawa kennan?
 kinga ni ko yanzu na mutu Ina da may mun addu'a km baza a yi saurin mantawa dani ba saboda nabar baya.
Zeenat  tace muma inshallahu zamu haifi namu amman ba yanzu ba tukun say nungama shanawa .
suka kwashe da dariya shemah tace kai zeenat baki da kyau ,ki dai tsaya  shanawa ,kiji ayiririiiiii an shigo   miki da wata .
,take zeenat tayi mata dip zuciyarta ta aushine ,gavanta yashiga faduwa ,hello hello.. zeenat kina jina kuwa  uhm injiki inji cewar zeenat .
 , bangane uhmmm ba daga maganar za'a karo miki wata har kin canza murya , Allah yarabaki da wannan maseefaffen kishin naki ,kar wata rana yakaiki yabaro ,ni da wasa nake fa.
Ajiya zuciya ta sauke tare da cewa  Ai ke ce kike son hawan jini ya kamani.
 shemah tasa dariya har kinsa na tuna da shakar dakika min  Sai daga baya fa nagane ashe  akan Yaya DEENI kika so kai lahira ,banshirya ba  dariya suka sake yi hira suka yi sosai sannan sukayi sallama .


Da zai wuce akwaibon  yaso tabishi amman taki ,dan dai yavarta taje gida gurin Ummi . haka ya tafi tamkar ,zai lasheta yayinda ita km ke matukar jin dadin yadda yake kula daita say day matsalar shi daya jarabar son   jima'i .
,kwata kwata baya gajiya dayin sexy  ,gashi ita km bata kaunar kishiya.ballantana 
 tace yaje yakara aure ko itama ta huta da jarabarsa.
 ,amman ita sam bata kaunar kishiya dan bazata iya zama daita ba . 

Suna zaune lfy da mijinta   km duk sanda yazo da bukatar sa tana iya kokarinta wajen gamsar dashi ,wata irin soyayya yake nuna mata da tsantsar kulawa duk awa Sai yakirata a waya yaji lafiyarta .


Kwance take akan thrre site tana tunanin mijinta wanda ya zame mata jiki .
 taji karar bell ta bada izinin shigowa dan oready bata sawa kofar key ba .
 su sumy da rukky ne suka rungume juna dan farinciki wuni sukayi suna shewa gashi km Allah ya taimaketa deeni bai dawo gidan ba, kmr yadda yasaba .

rukky tace Amman zeenat kema ciki ne dake ko?
 jifa yadda kirjinki ya cicciko tace ke ni rabani da wani ciki ,ni ko cikin gareni Ai Sai day nayi flashing dinshi Ina zan iya wani wahalar haihuwa.
 sumy tace Allah zeenat ciki ne dake.
 dan Allah kai ki dameni ke kika min cikin zaki ce cikine dani rukky tace kin canza dayawa shiyasa kinga kuwa yadda kika sauya kin kara wani kyau kmr bake ba.
Wai  me ma sojan nan naki yake baki ne ?
Rukky tace Ai ni bakiga Sai kallonta nake ba. murmushi tayi baza ku taba  gane abinda yake bani ba ko sanar muku.

 ,ku dai kuyi aure kawai  suka sa ihu bbu damuwa lokaci ne.
 ,da zasu tafi bataji dadi ba tace su tsaya zuwa anjima suka zaro idanun waje ki rufamana  asiri da wannan zakin mijin naki,may frigita mutane.
 ,ta tabe baki to yanzu  say yaushe km .
Say  munzo sunnan shemah .sukayiwa juna sallama .


Kwanan shemah hudu da haihuwa Amman sam deeni ya hanata zuwa ta zuba masa idanu kawai dan  tarasa yadda ,zatayi.

 tanason ta botsare masa Amman tasan halinsa sarai zai iya haikace mata.
 dan haka ta make Sai dai ta dan canza masa .
to shima haka yaga canjin a idanunta.
Dan  daya dawo aiki sannu da zuwa kawai tayi mishi takarbi jakar hannushi takai dakinsa . ta wuce bata  tsaya tayashi wanka ba haka daya zauna cin abinci ma bata kulashi ba asalima Sai tashigewarta daki ta kwanta .

koda yashigo ma rufe idanunta tayi tare da juya masa baya kwanciya yayi akan gadon tare janyota jikinsa abinda yafi so shi yashiga sarrafawa yana mammatsa mata jiki janye jikinta tayi anashi.

amman shi  say dada manneta yake da jikinsa ya manne bakinshi  danata Yace badai fushi kikayi ba ?

Tayi masa banza kinsa fa banason kyaliya.
 ko kiyi fushi idan  kika bani haushi say nace bazaki ba gabadaya naga abinda zai faru .

tace Amman dai ka aureni bawai katsiye ni bane ,asalima bbu ko sisin aljihunka acikin kudin aurena.
 Gani na kawai kayi .


Yes yes alamun ni din dan gata ne" ko kin taba ganin wanda ba dan gata ba amishi haka ?

Tasa kukan shagwaba ni dai bbu wani nan kawai shiyasa kake min wulakanci da duk  yadda kagadama .
 ,ya kai bakinsa ya sumbaci wuyanta ok zo ki gaya min may na miki na wulakanci .
Bakisan dan nasan darajarki da yadda nake kishinki yasa banason ana gane min ke ba .
Banason  kina yawo cikin estate din nan Amman dayake ke sakaryace shine kike fushi dan na hanaki fita .
km dan ni sauna ne Sai navari anata kalle min mata ni kadai nake son nayi ta kallonki ya fadi haka tare da  shafo fuskarta .

 lip's dinta  ya kamo yana dan tsotsa .
matseta yayi yana ta kokarin balle maballi gaban  rigarta kin yarda da maganata?

 ta tabe baki Amman kasan ko Ummi yaushe rabon dana ganta ban taba tunanin zan dau lokaci may tsawo haka banje gida  ba.
 kana dai son ganin bacin rai nane to kishirya gobe inshaallahu  da kaina zan kaiki ya rungumeta tsam tsam ajikinsa tare da cewa Ina bukatar natsuwa a tare da ke hannuta takai saman fadadden kirjinsa tana shashafawa tare da zubawa gashin kirjinsa ido masu tsananin taushi da tsantsi ta dinga may tafiyar tsutsa bata dire hannuta ba say akan jijiyarsa ta kamo tasoma shashafawa ahankali ahankali.
 tare da lailaya  kan jijiyar sannu sannu.
 nishi kawai yake  fitarwa yana sake   ware mata kafafunsa .

wani irin dadi ya dinga ji tundaga tsintsiyar kafafunsa yana ratsa gangar jikinsa sake kamota jikinsa yake hannushi yasa ya damko dukiyar fulaninta yana musu wani irin murza ahankali yana zagaye hannushi akan brest dinta.
 duk yadda taso yayi sambatu kiyawa yayi Sai itace ma ta dinga yi wayo uhm.... shiiiii.....yana jin tana kiran sunanshi ya de..e...ni...
 hakan yasa ya dinga jin tsigar jikinsa na mikewa gabadaya sun gama fita haiyacinsu Sai wajen uku saura ya barta shima badan yagaji ba.
 Sai dan ganin yadda Ta narke .
jawota yayi jikinsa ya rungume yana kai mata kiss a wuyanta raguwa banza kawai , tana ajikinsa tana jin wani iri kasala da bacci bacci  iska bskinsa yake hura mata a fuska har ta dan bude idanunta ta zuba cikin nasa sun dau lokaci suna kallon juna har bata sanda kalmar a I love you ta subuce daga bakinta ba .
 Ya hade  bakinsu  batare da ya maida mata martani ba.
 kiss dinta yacigaba dayi . Ahankali ya saki bakinta sakamakon wani testing din dayaji yayi ,yatsun hannuta yakamo farcenta ya zuba musu ido sosai tsawon lokaci dauka yana  kallons.cikin sanyi murya Yace zeenat kmr kina da ciki..?
A frigice ta wastsake Sosai tace uhmmmm ni bani da wani ciki ,kina da ciki man tace Allah ni Banda ciki ya girgiza kai kawai ya sakar mata hannu ya Mike yashige bathroom.



Washegari Sai kusan sha biyu suka tashi kasancewar weekend ce , zeenat ce ta fara  shiryawa ,ta hada  musu breakfast  deeni baici komai ba Sai coffee.

 doguwar riga baka ta saka har kasa   mai ratsin dowatsu green  ajikinta.
 tayi kyau sosai, rigar tabi da surar jikinta.
 tafiya take sannu ahankali har ta iso dakinsa ganin shr bai fito ba ,yasa tabiyo shi.

kallo daya tayi masa ta gane daga wanka ya fito ,yana goge jikinsa da wani karamin towel ta dan kwanta akan bed dinshi .
tana kallon yadda yake shiryawa cikin yadi fari qal may taushi da sharashara ,wanda har farar singlet din jikinsa ana hangowa .
".  kana ganin yadi basai angaya maka ba kasan yasa kudi ,Sai wani kamsh na maseefa ke tashi ajikinsa.
 ga gashin kan nan nasa kwance  wanda yake samu gyara akai akai  .
,duk da gashin bawani jima yake akansa ba  sbd yanayin aiki .
amman hakan bai hana shi samu gyara ba kafin aske .


Zeenat ta zubawa kyakkyawan mijinta ido tamkar  ta cinyeshi  ta sbd wani irin kyawun da yayi mata .
tabarakallah kawai take iya  fada a ranta.

 duk kyawunta da ake fada idan ta tsaya kusa dashi Sai ta raina kanta deeni first class ne km quality man ,kwararren dan gayu ne daya iya tsara kwalliya .
da iya sa kaya may tsari komai nashi a tsare yake dole ne idan kaganshi kaji ya birgeka tare da shiga rai.

Tana can tana tunaninsa ashe har yagama yazo kusa daita ya busa mata iska ya kamo, hannuwanta yana wasa dasu Yace banson tunanin nan fa.
 ki fada min idan kina da damuwa zan miki maganinta muddin bata fi karfina ba .
dan kinsa tunanin yana jawo matsala.

 mema yasaki tunani ,na roke kada ki boye min damuwarki kisanar dani kinsa  amanarki Ummi tabani .

Tayi murmushi tana sake jin kaunar mijin nata har  cikin zuciyarta 

ta sumbuci hannushi tana cewa karka damu Allah bbu abinda ke damuna.
kawai Ina tunaninka ne yayi murmushi kin tabbatar?
 ta daga masa girarta daya .
 to ya tsaya iya tunanina kadai yana jan hancinta.

ya  mikar daita tsaye tashi mutafi Yar umminta yau zaki kiga umminki shikennan hankali Sai ya kwanta ,can km yayi shr yana kallonta amman fa kmr kwalliyarki tayi yawa fa .
Gsky kayan ma kmr  sunyi shara shara dayawa .

Ta dan bata fuska dan tasan halinsa .
Yace,muje ki canza wasu kayan.
 taja ta tsaya tana dubansa dan Allah ni  kabar min kayana 

ya hade fuska Ina wasa dake ne  dazaki tsaya kina min  mutsu  ?

Yaja hannuta kawai  ta sake turjewa Yace wallahil azim bada wasa nake ba say kin canza kayan .
 haka ya tasata gaba har gaban wardrobe dinta   .

Ya dauko mata  riga tasa say yaga tafi ta farko yi mata kyau.
 ya km dauko mata wani shima the  same Duk wanda tasa say Yace yayi shara shara ta canza haka ya dinga sata canza kaya daga karshe da  kyar yasamu wata mai kwari ya zira mata ,.
bata mata ba amman ba yadda Ta iya da maseefar sa.
 dan Allah Allah take tabar gidan kar Yace anfasa zuwa  dan zai aika  .

Kwaliyar fuskarka yasoma goge tare da kai, bakinsa   kan lip's dinta ya tsotse lip's din tas ..say dayaga bbu komai .
 tukun hankalinsa ya kwanta .
ya sake zuba  mata ido say ma yaga kmr ma kyau takara Yace anya kuwa tafiyar nan bazamu fasa ba kuwa.




MMN SUDAIS CE
.
[5/7, 4:04 PM] ‪+234 818 621 2985‬: 💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
     💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO



Page 39-40


Mubari da daddare maje yana jawota cikin jikinsa bakinsa yakai saitin kunneta Ina da tsananin kishi zeenat bazan iya barinki kiyi  yadda so ba ....


Tayi narai narai da idanu zatayi kuka Yace kinsa Allah muddin kika kuskura kika bari hawayen nan  suka zubo daga idanuki  ki tabbatar bake ba fita koina .
,da sauri tasoma kokarin mayar da kwallar tana sakin numfashi .

Yace yauwa Yar umminta zo muta tafi .
"ko a mota ma hirarsu suke tayi irin ta masoya .

,can km duk suka yi shr hannushi ya daura a saman nata yana  ,dumin hannuta dayaji ne yasa shi saurin juyowa ya kalleta .
Ahankali ya riko hannun sosai cikin nashi yana murza tafin hannuta.
 ahankali ta dubeshi tare da cewa  ya'akayi ?
 ,ya dan yi murmushi nifa Ina son naganni da bby .

 dip tayi shr.........na wani lokacin takasa cewa komai kafin daga   tace zan haihu Amman ba yanzu ba ,da saura.
 , lip's dinshi na kasa yake cizawa da karfi dan jin dacin  abinda tace .

Wani irin radadi yake ji aranshi.
" wani irin magana ce haka ,zan haihu Amman ba yanzu ba da saura ,ya sake maimaita abinda tace .
 to me hakan yake nufi maganar ta tsaya masa a rai .
Dan haka ,yana tsayawa harabar gidan yashige yabarta a nan sbd takaicinta  .


,tayi sallama shiga cikin dakin mai jego yayinda DEENI ke zaune a parlour gidan .
  zainab tace   koma muyi fushi wlh  kiyi bby guda Amman Kiki zuwa Sai yau ana gobe suna zaki kwaso kafafunki kizo .
Zeenat tayi murmushi dan Allah ayi min afuwa wlh ba laifina bane Allah yasani laifin babanta ne .


Deeni da Yaya faruk ne suka shigo dakin zeenat ta gaisa da Yaya faruk ta dauki yaron "kai shemah  gsky kin iya" haihuwa ,Amman kiyin kokarin irin  wannan jibgegen bbyn ,kallon da deeni ya watsa mata yasa tayi saurin cewa  Mashaallah.

, shemah dan Allah kibarmuna shi ,say ki sake haifo wani .
Yaya faruk Yace anki abarmuku ,kuje kuma ku  haifi naku idan kuna so.
 "ayya ya faruk saurin me kake yi ,idan nataashi yan hudu zan haifa ma gabadaya ba kmr matarka data haifi daya ba .
mikawa DEENI yaron tayi ya amsa fuskarsa dauke da murmushi ba kmr shigowarsa ba.
 ,wani dadi yake ji tamkar ace dan sa ne na cikinsa yau yake rike dashi .
 ya zubawa bbyn ido kawai yana kallonsa tabbas yaron kama yake da ubansa.
 , addu'a ya dinga yi akasan ranshi shima Allah ya azurta tashi da samun bby irin haka .
 , ahankali yaron yasoma mutsmutsun kuka alamun yana son nono zeenat ta karbo shi ta mikawa uwarsa.
  Zeena ta zubawa  shemah ido ,yadda take kokarin rarrashin ,domin kunya take tabashi nono agaban deeni .
Zeenat tace uhmmmm  Sai fa kinyi hakuri da kukan bby .
to yazanyi ,da haka kowa ya saba .
Amman daganin alamun yana kukan dare ne ko ?

Shemah  tace Yana dan tabawa ba yawa.
 zeenat ta tabe baki tana girgiza kai kmr ance ta juyo inda deeni ke zaune hararata yayi alamun tayi shr ta damu mutane ,

Ya faruk ya dubi gefen da  deeni ke zaune  yace zeenat fa kmr ciki ne daita ko?

Deeni ya dago kansa yana kallonta itama shi take kallo ,dan jin me zaice , DEENI yace nima kallon dana ke mata kennan.
 Amman ita Sai  karyatawa take .
Faruk yace To kuje hospital mana ,can  za'afi tabbatar maka da gasky .
,eh shirin da nake yi kennan Monday inshallahu daita zan wuce.
Zeenat ta dubi  ya faruk  da kyau " tace ni ba ni da komai fa ,kawai  ku kuje min kallon haka .
 ,deeni ya sake zabga mata harara kiwa mutane shr duk kin damun mutane da surutun banza .

Da zasu tafi deeni Yace faruk kmr nafi da bby nan wlh to ka tsaya a hado masa  kayasa .
suka dariya .


Gidan Ummi suka nufa .
a guje  zeenat tashiga part din Ummi tayi sa'a tana parlour .
 ta  fada jikinta tare da murna    tayi matashi da cinyarta. Wayo Ummi  Nayi kewarki  ....

Ummi tana murmushi tace Ai ba'a maganar kewa , irin wannan jajur  din da kikayi .
kmr baza'a mutu ba ? 
Ai dole ki manta dani ,gashi ni kullun cikin kewarki nake. 

 ,deeni Yace haba dai first lov taya zata manta dake byn  kullun Sai tayi kewarki ,.

Ummi tayi murmushi tace ok tare mata ma kakeyi kennan ?  Ummi ta sake duban diyarta tace kinyi kyau sai kin rame ,da dago idanunta tana kallon inda  deeni yake zaune , wai wannan ramartata ta mecece data kici taki karewa ?

 DEENI ya tabe baki sannan yace  wayasan abinda ke Cinta take ramewa ,ayi maganar zuwa  asibiti ,tace ga zance ga magana . 

Su samiha    da sukake shigowa  suka gaishe da ya deeni ya amsa yana kokarin mikewa.
Tare da cewa To  madam ni zan dan fita say na dawo  .

Zeenat dake kwance kan cinyar Ummi  tace  ok Yaya  ni dai say zuwa jibi zan dawo.
   uhm kiyi   zamanki ,inkin iya ma karki dawo.

 ,Ummi ta harareshi tace wani irin magana ce haka ?
 , first lov  baki ji abinda tace min bane  tsabar ta rainani.

 ,to yi hakuri sarkin zuciya jeka say kadawo Allah ya tsare .

 ita dai zeenat tsit tayi da  bakin ganin yadda ya dau zafi , kyacci yayi tare da jan tsaki sannan Yasa kai ya   fice abinsa  .

Hirar yaushe gamo ta barke tsakaninsu.
 ,Ummi ta dubi zeenat me zaki ci a dafa miki ta dan langwabar da kanta tana tunanin abinda zatace Amin soyayyiyar doya ,Ummi ta sake kallonta da kyau dan sanin data mata bata cin doya ,shr kawai tayi ta nufi kitchen .

Har dare suna tare dasu shemah sunki tafiya .
,to oga da kanta ce yau tazo gida, dan zeenat ce lidarsau gabadaya komai za'a yi sai tabada Command sannan za'a yi .
  " dan  haka gabadayasu suka taro anan part din Ummi suna ta hira  har sanda Ummi tagama soya doyar tace Maryam tazo ta daukar musu.
 tare suka ci suka sha ,sai zeena bata wani ci may yawa ba .
 say faman murna take ganinta cikin yan'uwanta .

  ta gefe daya km ga Ummi murna tamkar ta kasheta dan dadi .
 ,har mantawa tayi da wani deeni ,dama wayarta gabadaya.
 , deeni yayita kiranta a waya  yaji shr taba dauka ba.
 ,har say data  kaishi ga kiran Ummi ta miko mata  wayar .
ta karba tare da bmyr Ummi da hannuta waye ,mijinki abinda Ummi ta fada kennan.


Ai da sauri Ta manne wayar a kunneta tare da sallama ,ko amsa sallamar bai yi ba .

Yana jin muryarta yace ke.... dan iskan Ina kika shiga kika bar wayarki ,tun daxo Ina faman kira?
 ,mikewa tayi tsam tayi ciki dakin Ummi tare da marairaice murya wayyo dan Allah Yaya kayi hakuri wlh abinci nake ci .
km wayar tana cikin hand bag dina.
Cin abinci ne har tsawon   awa hudu ?
Kifa kiyaye zeenat .
 naga kmr kanki na rawa rawa fa.

Say hakuri take faman bashi ,shi km yana sake  botsarewa ,ki cigaba zan gyara miki ,zama ne bar ganin kina kusa da Ummi ,km kishirya ganin nan  zuwa ,mu wuce ,gida .

Batasan sanda ta sakar masa kuka ba.
tana sake  bashi hakuri ok kuka ma zaki yi wa mutane tsabar kin raina min hankali ko .

, , ita dai batace masa  komai ba say ma hakuri data tacigaba bashi .
 , dan Allah Yaya kar kamin haka  kabarni zuwa  byn suna na koma .
 ,gobe ne  sunan fa.
    ,anki abar ki' idan ma kika sa wasa ,sunan ma ba zakizo ba gabadaya naga abinda zai faru.

 ,kawai ya kashe wayarsa batare da tsaya jin abinda zatace ba  .


Sosai take kuka har takaraso ta mikawa Ummi wayar duk da ta dan goge hawayen fuskarta hakan bai hana Ummi ganewa ba .
,ta tambayeta tace bbu komai ,haka dai zakice bbu komai kiyi ta zama da abu acikin har yazo yamiki illa.

 ,ta zauna tare dayin shr sure Maryam ma sudan ga sauyi a tare daita Amman bbu wanda ya damu da tmbyrta ,suka cigaba da hirar su sama sama  .

Shr kawai tayi zaune a gurin  yayinda ta dinga jin wani abu nataso mata a kahon zuciya, tasa hannu ta dafe kirjinta tare da  runtse idanunta gam cigaba abin yayi da taso mata .
 gabadaya cikinta ya aushine ,bakinta yacika da miya ,wani irin amai taji yana taso mata ,da gudu tayi bathroom din dake manne a main parlour .
Ako ta dinga Kwara amai ba kaukautawa tare da rike cikinta .
Aman ta dinga kwarawa tamkar zata amayo da kayan cikinta . gabadayansu suka gigice sukayo kanta sunata  mata sannu.
 Maryam ce tayi dakin Ummi dan ta sanar mata.
Wani yunkurin amai ta sake yi  ,dai dai lokacin da deeni ya sawo kanshi cikin gidan
 ,da sauri ya karasa shigowa duk da bai san takamaiman wakeyin amain ba.
 ,suna ganinsa suka dare gabadaya ,ga mamakinsa zeenat ya hangota durkushe Sai amai take Kwara gabadaya ta galaibaita jikinta yayi week ,atare suka yo kanta shi da Ummi kusan ma yariga Ummi karasowa bakin kofar bayin yana kallonta har lokacin amai  take 
 say dai ga , dukkanin ,alamun bbu wani wadataccen abinci acikinta .


Ahankali ya durkusa a gabanta ya  dafa kafadarta yana mata sannu.
  ,zaman dirshan tayi a bakin kofar tana mayar da  numfashi .
Ta fashe da kuka  da  ,tare da  jingina jikin bangon .ruwa ya dibo ya wanke mata bakinta da fuskarta .

 ganin haka yasa Ummi juyawa takoma dakinta tare yin  addu'ar Allah ya inganta musu , daman ita tun wancen zuwan nata  datayi gidan nasu ,take ma zeenat din  kallon may ciki.

Zeenat duk tarasa inda zatasa kanta taji dadi.
 km har lokacin su samiha na sunki  tafiya , ahankali deeni ya juyo inda suke tsaye cirko cirko suna kallon shi da zeenat din .
,muryarsa zafafe Yace tsayuwar uban me kukewa mutane ,yan iskan banza kawai yarinya tana  mai anrasa wanda zai taimaka mata ,duk kunzo kun rufeta kuna kokarin kasheta.
 ,Ai tunin suka gigice suka soma tattara inasu Ina su ,subar gidan . 
Yaja tsaki ya km maida kansa kan matarsa .

Juye juye kaiwa take tana kuka tare da kiran sunan Ummi .
 ya fizgota  tare da daka mata tsawa kina hauka ne ?

ko kallonsa batayi batayi ahankali tasoma rarrafawa tafito daga bathroom din ta zauna kan kujera ta jingina kanta  tacigaba da kuka tana mayar da numfashi.

 ya Mike ya dawo kusa daita yana kallonta yasa hannushi zai dafata ta Mike da sauri Ta km shige bathroom ta durkusa tashiga kwara wani  amai ,jikinta har wani rawa yake.
 lokaci daya jikinta ya dauki zafi ya riketa yana mata sannu ta langwabe masa tasoma kokarin mikewa ya rikota.
  Yace Ina zaki? gurin Ummi zani .
,say km ta fada kansa wayyo kwanciya zanyi na gaji yaya ..
 Ya dagota ya wanke mata baki da jikinta ,ya dauke cak  yayi dakin Ummi ,daita.
 
 Ummi ,ta dinga jero mata sannu .....
 , mikowa Ummi hannuta take alamun tazo gareta.

 ,Ummi takarasa ta zauna kusa daita  ta kamo hannuta cikin nata.
 ,sannu zeenat .ya jiki 
Ahankali zeenat ta lumshe idanunta ,cikin sanyi murya yadda deeni bazai ji abinda zata fadawa ummin  ba.


 Tace ,ummin dan Allah karki bari Yaya deeni ya tafi dani gida ,take gaban Ummi yashiga dukan uku uku.
 ,itama  ummi cikin muryata kasa kasa tace wani abun yake miki agidan ta girgiza kai.
 wlh baya min komai sbd sunan shemah ne.
 ,say lokacin gaban Ummi yabar faduwa dayake .
 tace shikennan  ta Mike tabar dakin ,shi km deeni ya dawo inda Ummi ta tashi.
 ,daukarta yayi  ya zaunar daita akan cinyarsa ,ya hada fuskarshi da tata waje daya ido cikin ido suke kallon juna , zeenat ....yakira sunan da wata irin murya ta wacce tayi nasarar  kashe mata jiki ,ta amsa da Na'...am ....my hrt.

 sunan data kirashi dashi yayi mishi dadi Sosai har yasa shi  yi  murmushi wanda har dimple dinsa ya lotsa .
Idanunsa ya zuba mata  yana sake kallon kwayar idanunta . 
Yace Me kika sanarwa first lov wanda ni kika kasa sanar min after ol ma 
 meke  damunki kika dinga kwara irin wannan amai ? 
Ta girgiza masa kai kawai  alamun bbu komai .
Yace  yanzu yakike jin jikin  naki.
 da kyar ta iya bude bakinta tace daidai nake jina.
 say abunda ba'a rasa ba .
,yace kinci abinci ma kuwa?
 ,tayi murmushin karfin hali ,tareda cewa naci doya dazu itace ma  ta dinga tasomin .
Amman Tunda na amayar daita naji ,daidai.

, Yace ok ki shirya mu wuce gidanmu ko ..
 ba mutsu tace masa to tasoma kokarin mikewa yace bi ahankali fa .


Tsab ta shirya abunta kmr bbu abinda ta shuka .
 , parlour'n kasa , Suka tadda Ummi a zaune tana kallon labarai a CNN. 
'ahankali Ummi  ta dago tana kallonsu ,Ina zuwa haka km .
,sukayi suru suru  dukkansu suna duban Ummi dake zaune.
 say ma deeni ne yayi karfin hali cewa gida zamu .
gidan lfy zaku byn kana kallon  yarinta badata da lfy shine ,zaka wani ce gida. 

Ba gida ba tukun runbu zaku  dan Allah ni kyalle min yarinta takara  samun natsuwa .
,Yaya da naci  haka idan zaka iya kadawo jibi ka tafi daita.
DEENI yaji tamkar kasa ta tsage yashige cikin Dan tsabar kunya da takaici abinda Ummi tamasa ,.

Take 'ya Gane setup , ne kawai aka masa dan kar zeenat din tabishi .
 dan haka ya dinga kallon zeenat din tare da hararar ta .


Da sauri tace Allah Yaya ni bbu ruwa acikin  ,mu wuce kawai abunmu .
da hannushi ya katseta ,karki dama kiyi zamanki kawai basai kin bini ba ya juya.
 ,tabi bayansa da hanzari zata bishi.
 Ummi takira sunnanta ke zeenat dawo nan ahankali tasoma girgizawa Ummi kai tamkar wata kadangaruwa.

Wai ,bada ke nake ba inji cewar Ummi ,jikinta a sabule ta dawo kusa da Ummi .
ta zauna ,duk jikinta yayi mata sanyi .
Ummi tace kima saki jikinki ki manta dashi ,ki daina wani dar dar .

 ,ke wai  har yanzu baki bar jin tsoransa ? Zeenat Ta zubawa Ummi ido kawai tana kallonta ,Ummi tace kin tsareni  da idanu .
 , zeenat  tace Ai kece Ummi da wani abu.
  Aa ba haka yakama kiyi masa ba.
 .ni dana so ki lallabaminshi ya Amince da kanshi Shi kika tunzarashi . 
Ummi ta saki baki Aa ba tunzarashi nayi ba kashe shi nayi .

 ,wawiya kawai kicigaba da jin tsoronsa  say ya kwashe miki hanjin ciki tare da manna miki hauka . 

Dan haka Zeenat din tayi shr ,dan gsky bataji dadin abinda tayi masa ba .

ahankali ummi ta dinga janta da hira har dai zeenat din ta saki jikinta sosai suka shiga hirarsu . 
Har shadayan dare , zeenat tasoma gyangyadi Ummi tace suje su kwanta .



Kwance take akan gadon Ummi .hankalinta kwance take sharar bacci ba matsi ba takurar oga deeni ,yau daya taji salama , har taso ta makara tashin asuba sai da Ummi tayi da gaske tukun ta mkie .



Washegari ranar suna yaro yaci sunan mahaifin deeni ,wato aliyu .

Deeni yaji dadin sosai da karar da faruk yayi masa .dan haka takardar  gida sukutun deeni yabawa bby  kusan shi yayi komai na suna  har raguna sunan yaron da kaya akwati goma sha biyu ,  ,hatta Holl din da,akayi taron suna shi yakama Amman  ita kwata kwata batasani ba dan ko kiranta baiyi ba . 

Har Washegari suna deeni bai nemeta ba irin shariyar dayayi mata , ya dameta, yaushe rabon ,daya shareta irin haka .datasani tasoma yi gashi angama suna mijinta na fushi daita.
Tayi zugun har Ummi taso ta harbo jirginta .
Dan sai data tmbyrta alahan tunanin wannan mijin naki kike ? zeenat tayi murmushi tare da wauancewa haba dai Ummi,tunani km . 
Tap jikina ne    kwata na
 ke jin yana  min nauyi .
Ummi tace ya day kamata kuga likita .


Daren ranar  sam takasa runtsawa zeenat tayi abin mamaki gabadaya ,kewar mijinta ce ta addabi ruhi da gangar jikinta .
ta dinga jin alamun hannushi yana yawo   aka dukiyar fulaninta , hatta kashim turarensa tana jinshi  tsam ajikinta .
,takoina ta juya ,mijinta take Gani ,idan ta runtse idanunta km  shi take Gani yana  make love daita .

A zubara ta Mike zaune ,tana kankame da jikinta . 
tamkar may jin rawar sanyi.
  Ummi data ji motsenta yaki karewa ,ta dan  juya tana dubanta tare da cewa  tace lfyrki kuwa  .
,a sanyaye zeenat Yace   lfy lau Ummi ? Ummi tace to me ya hanaki bacci?

Tace  mafarki nayi ummi ,.
Ummi ta tabe baki to kiyi addu'a ki komai.

 tace  to tayi addu'ar kmr yadda Ummi tace ahalin ita tasan ba wani  marfarki tayi ba.
 ,tsabar jarabar DEENI ya saba mata daita kedamunta .

haka ta koma ta kwanta ta dinga juyi da mutsmutsun , Amman bacci sam ya gagara daukarta har asuba bata samu ta runsa ba.
 km bata  daina jin hannushi  na kai kawo. jikinta ba .




 ,
[5/7, 4:05 PM] ‪+234 818 621 2985‬: 💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO


Page 41





Da kyar zeenat tasamu ta tashi  tayi sallah takoma ta kwanta   cike da kewar mijinta.

 ta kudindine jikinta cikin bargo sakamakon sanyi sanyi  data keji .
kamkame jikinta tayi waje daya,tana jin dama sukasance tare  ,wani irin feeling dinsa  take jin yana tasoma mata.
' har wani rawa rawa jikinta yake .

Ummi dake zaune akan pray mat tana lazimi tana  hankalce da duk wani motsinta Amman tashareta .

 Fargaba cike tsoro suka cika zuciyar  zeenat.
  kardai fushi Yaya deeni yayi daita ,wanda yasa yakasa zuwa gareta .

 dako duniya tayi mata warbar kunu.

  kwanki biyu din dabasa tare jinsu  tamkar shekara biyu ne .

 hawaye masu dumi taji suna  silalo mata a kuncinta tasa tafin hannuta tana dauke su ahankali.
 tana jin  zafi da radadin abinda Ummi tayi mashi dan tasan , haushin haka yasa ya hanashi zuwa gidan gabadaya .

Ahankali Ummi ta Mike tana  nade abin sallarta byn tayi addu'a.

Ahankali  takaraso inda zeenat din ke kwance lomo tamkar may baccin gaske.
, ta zuba mata ido kawai duk cikin bargo take hakan bai hanawa ummi  na nazarinta ba .

Ta dan dade tsaye akanta kafin daga baya takira sunanta  Cikin sanyi murya  mamana 2 shr ....... Kina jina fa dan nasan idonki biyu .

Say lokacin zeenat ta yaye bargon da dake luluba  ajikinta tasoma  murmurza idannuta tamkar wace ta dade tana  sharar  bacci .

Make damunki mamana  ko gidanki  kike da bukatar komawa inji Ummi?

 ,da sauri zeenat ta girgizawa ummi kanta .alamun A'a 

Tace To naga duk kinki sakin  jikinki kinyi wani  laushi dake ko wani abu ke damunki  na lura jiya bawani bacci kikayi ba?

da kyar zeenat din ta Mike zaune  tare da  bude bakinta tace bbu komai, to mezaki ci yanzu ? Ummi ta sake tmbyrta .

muryata a sanyaye tare da yatsuna fuskarta tace komai mayye .
 ta fadi hakan ne darasa abinda kema dadi .....

Ummi ta juya ta fice daga dakin , tabar zeenat da juyayin rashin jin duriyar  mijinta .



Some minti back


Ummi ta dawo dakin hannuta rike plate da jug ta jawo  karami stood dake gefen  gado ta daura plate din indomi data dafo mata akai .

,sannan tace  ki  tashi  ga indomi  nan na dafa miki .

, zeenat ta sake komawa ta kwanta ta Mike ahankali  ta ziro kafafuwanta kasa.
 kmr kar  Ummi ta ambaci sunan  indomi .

 shikennan taji kirjinta ya rike gam  ,aiko ummi na bude plate din take taji kanta yasoma jujjuyawa zuciyarta ta ausine a guje tayi hanyar bathroom din dake dakin Ummi ta dinga kwara amai ba kaukautawa .

Da sauri Ummi takaraso gareta tana yima mata sannu , sai kakarin  amai take amman bbu abinda yacigaba da fitowa sbd rashin abincin da bbu acikinta.

 ta galabaita matuka gurin yin Aman .
 Ummi ta dinga ji tsautsayi na ratsata tana girgiza hakan ya dinga tunowa ummi da yar,uwarta farida .

 hakika laulayin farida kika dauko zeenat , Allah ya day inganta ya bada masu albarka .
 ummi na tsaye har say dataga tadaina yunkurin amai sannan tashiga cikin bathroom din sosai ta dibo ruwa ta wanke mata baki da fuskarta sannan tace tayi wanka .


Koda tafito ma kwanciya ta sake koma .wunin ranar xurrrrrr akwance zeenat tayi shi .

Amman duk da wannan halin datake ciki hakan bai sa ta daina jin mijinta agangar  ajikinta .



 Jin shr shr ba deeni ba kiransa a waya yasa hankalin Ummi tashi danhaka  ta yanke shawarar ta  name shi a waya .

Byn ya  dauki waya  ,tun kafin yace wani abu Ummi ta rufeshi da fada rashin zuwansa ta inda take shiga bata nan take fita ba .
, tace ga matakar nan kwance bbu lfy amman dan tsabar  wulakanci yau kwananka biyu rabonka da gidan nan .

Shr yayi sai daya bari umminsa ta sauka. sannan yasoma bata hakuri.
 Dan girman Allah first lov kiyi hakuri wlh nima yarinyar nan tana cikin  raina wasu abubuwa ne suka sha kaina shiyasa kwata-kwata baki ganni  Amman inshallahu da zarar na dawo aiki  zanzo . Karma kazoTayi hanging din wayar .


Misalin karfe takwas na dare daidai deeni yashigo gidan . 

sanye yake cikin wasu hadaddun  kanan kaya blueblack din wandon jeans da black top anyi  rubutu white MM sport a gaba da baya rigar.
, kamshi turaren Hamilton ke tashi ajikinsa , ahankali cikin wata irin murya may ciki da kwarjini da haiba  yayi  sallama tare da  murda handle din kofar umminsa ya sanyo kanshi cikin dakin ido suka hada da umminsa ya sakar mata murmushi.

 ita km ta watsa masa hararar wasa . Kamshi turarensa ya sake  baibaiye dakin ummi .
tun bai kai ga karasa shigowa ba.


Ita kanta zeenat lefe tamkar bacci gaske . Batashirya kallon kofar ba  amman kamshin turaremsa ya hankaltar da ita mamallakin zuciyarta ne yaiso.
Dan haka  ahankali ta ta da saci kallonsa sannan ta maida   idanunta ta runtse  tsabar murna may gwaraye farinciki dan tasan yau bbu makawa gidanta  ,zata kwana .

Cikin muryasa mafi soyuwa a gurinta taji yace  First lov nashigo ko na koma ?

 ummi tayi murmushi wanda ya kawatar da fuskarta  .
taya zance ka koma nida nake cike da daukin ganinka .
Bismillah  attajirina . Tabashi amsa tana kallon kofar .

Ahankali ya tura kofar ya rufe ya sako farar kafarsa may dauke da Zara zaran yatsu masu kunshe da gashi a saman kowanne su  fuskarsa gunshe  da murmushi yakarasa har  inda umminsa ke zaune ,ya gaisheta tare cewa  Allah  nayi zaton kina fushi dani ne har yanzu . 


Uhmmmm Ai fushina baya wani tasiri akanka  ahankali ya juya ya dan kalli inda zeenat ke kwance .

,sannan ya juyo yana fuskantar umminsa yace ita wannan har yanzu jikin nata ne ?


,ummi tace eh jikin  da sauki Aman ne dai yaki tsayawa har yanzu komai taci say ta dawo dashi.
ni km Ina jin tsoron bata magani .

Gatan nan dai ka dauke kawuce daita.
 hannushi yakai ya taba saman  wunya ,yaji jikin nata da dan zafi kadan . 
Hira suka shiga shida umminsa .


zeenat dake kwance idanunta biyu.
 tamkar ta suma jin lafiyayen hanunshi ajikinta .
 Take tsigar jikinta suka shiga mimikewa ta dinga jin wani zirrrrrrrr ajikinta Ga wani  tsanyi  dake zariya a kasanta .
Ahankali ta sake lumshe idanunta .


Ummi tace katasheta ku wuce  tun dare bai yi ba .
 , DEENI ya dan langwabar da kai haba ummi korar mu kike ,kmr mun gundirekuli.

Ina zan koreko ,kaima kasan duk duniya nan Banda kmr ku .
Km inda akwai abinda nafi so da kauna a duniya yana bayan kai da mamana .
  ,ku kadai gareni ko cikin bacin rai nake da zarar na ganinku shikennan zuciyata zatayi min tsanyi.

Deeni  yayi murmushi yana tashin zeenat ,ke.....ke.. .ke .

ta dan motsa yace  tashi mana tasoma mutsutsuke idanun karya  sannan  ta Mike tana Mika hade dayin sallati .

 yace tashi  wuce zamuyi .
,ta narke kmr batason zuwa ya daka mata tsawa dan Allah malama ki Mike karki bata min lokaci.
,ummi tace haba kabita  ahankali kasan baita kadai ba .


Ahankali takarasa mikewa tsaye .
 daman jikinta da kaya dan haka mayafi kawai tayafa sukawa ummi sallama suka fice har waje ummi tarakasu .


Tun a mota deeni jin jarabarsa natasomasa sakamakon jin hannun zee cikin nashi.

Ita kuwa , zeenat sai wani   narkewa take ajikin ogo DEENI  hannuta sarkafe cikin nashi tana yamutsawa a dadafe suka kawo gida .


Yana parking din motar sa  ya sunkuceta  cak sai tsakiyar bed  dinsu .

 ahargitse yasoma cicire mata kayan jikinta.
 say daya rabata da komai na jikinta ,a zabure yake kallon bobbs dinta yana jin wani irin feeling na sake kawowa jikinsa farmaki.

 ahankali yakai hannushi yana mamatsa dukiyar fulaninta.
 atare suka dinga jin wani yrrrrrrrrrrrrr.

cikin sanyi yakai hannushi kasan mararta ya dan yaji yayi karfi ya kara matsawa yaji  tasa kara har tana kokarin mikewa zaune ya maidaita tare  zuba mata rikitattun idanunsa.

 muryasa a sanyaye  tamkar ta mashaya yace kika ce baki da komai ta girgiza masa kai  alamun haka .
Yace wannan kullin  dake kwance a mararki fa ?

Tace nima bansan komeye ba .
 
,zaki sani ne  yarinyar gobe goben nan zan kaiki inda za'a tabbatar min da ajiyar dana yi.

 ahankali yasoma shashafata yana aika mata da sakwanninsa masu wuyar mantawa.
  mimikewa yasoma yi yayinda taji  yakamo boob dinta yana murzawa tare da kife hannushi akan nipply dinta yana musu wani irin murza 

yakai dayan  nipply cikin bakinsa yashiga tsotsa  daya km yana murza mata tuni ta fita haiyacinnta  saboda  wani irin  salo yake mata wanda yake sake siye zuciyarta .
' Sosai ya dinga murzata yadda yake so kusan daren basu samu rintsawa ba ,suna jiyar dakansu dadi .



Washegari ma yana dawo daga masjid daita yayi breakfast ya daura daga inda ya tsaya.

 to ba laifi zeenat  tayi matukar taka rawar Gani a gurin deeni dan sam bata nuna masa kasawarta ballanantana gajiyawarta  hakan bukatarsa km hakan bakaramin dadi  yayi masa  ya dinga kwasar gara yadda ranshi keso.



Wani private hospital yakaita may zankasa ,nan kusa dasu bakaita nasu na sojoji ba .

Zaune suke a gaban doctor saira jack deeni ke mata bayanin abinda ke tafe dasu.

Doctor ta hada zeenat da wata nurse zuwa lap inda ake awon jinin aka dibi jinta ,nurse din tace tana iya wuce .

Jikinta a sanyaye ta dawo inda deeni ke jiranta . 


Some minti back 


Nurse din data kai zeenat wajen gwajin jinin ce tayi nocking aka bata izinin shigowa .


Tashigo ta ajiye wasu file envelop a sama  doctor saira  ta dau envelop din tare da  manna medical glass dinta tana duba sakamako.

 tashin farko ta Gane zeenat na dauke da cikin har na tswon wata uku da wasu yan kwanaki  atakaice dai yashiga wata hudu .

haka kawai zeenat ta tsincin kanta da jin wata irin mumunar faduwar gaba innalillahi wa inna  ilaihi rajiun kawai take maimaitawa a zuciyarta.addua taje  Allah yasa ba abinda ake mata zato bane ajikinta . zuciyarta  har rawa take dan fargaba  .


Doctor  ta cire medical din tare da  nike farar takarda ta tura cikin envelop ,tana mikawa deeni hannu fuskarta dauke da murmushi congrat your wife  is now 4 Month preg...... 

ai DEENI bai tsaya jin karashen zance  ba yasan kwallon yasamu fadawa raga .
Ya  mikowa doctor hannushi yana amsar result.
 ,ya salam abinda zeenat take iya furtawa kennan akasan zuciyarta  hankalinta ya sake  mugun tashi ganin irin murnar deeni keyi  yasa ta dan kalato murmushin dole .

Amman gabadaya bata km jin komai byn pregnant din data ji na farko duk wani kuzari da karfin jiki bbu shi a tare da ita .
 

Deeni yayiwa doctor saira bayaninin game da  yawan Aman datake.

 tace wannan normal thing ne wanda kusan kowace mace tanayi km kowace da irin laulayin cikinta , zuwa wani lokacin komai zai daidaita yayi mata godiya tare damko hannnu zeenat .



Kai tsaye gida suka nufa wani irin murna yake mai kunshe da farincikin dan gabadaya yasaka tsaye yakasa zaune .

Da  kansa yaje ya sanarwa ummi zeenat ciki gareta .

sannan  ya dinga bugawa en,uwa zeenat ciki ne daita .Ta dinga kallonsa tamkar wani tababbe tana mamaki irin murna dayake akan cikin da bai gama fita daga jinin ba .


Ahankali ta dinga bakinciki da bacin rai ,ita fa gaskiya ,taba shirya yin wani haihuwa yanzu ba.
Asalima haihuwa baya cikin budget dinta .

 ,haka kawai taje ta mutu gurin haihuwa kmr yadda tasamu labarin sanadiyar mutuwar mahafiyarta kennan dan haka ita da haihuwa say nan da shekara goma koma zatayi  .




Bayan wasu kwanaki tana zaune a parlour ta janyo wayarta dake kusa daita number sumy tashiga nema.

 byn ta dauka sumy tace mara zumunci kwata kwata ba Kya neman mutane wannan sojan ya hanaki zumunci da jama'a .

Zeenat kiyi hakuri Gani zuwa   gidan ku yau .

kina gida summy tayi shewa tace yes.ooo.... Ina nan  yanzu inzaki zo.

 dan amjima kadan  ,zani agege kamun khadeey , zeenat tace aure khadeey zatayi amman shine say yanzu zaki sanar min ok ganin nan dai zuwa .




Cikin sauri Ta shirya dan tana son tayi sauri taje ta dawo kafin  yamma tayi duk DEENI bai gari amman atsorace take.


Cikin minti da bai wuce 20 sai gata a one thousand four cike da tsantsar murna suka rungume juna da sumy  .


Sumy ta sake kiran rukky byn kiran datayi mata ta sanar mata da zuwan zeenat din
 Atare suka zaune a dakin sumy  din yaushe rabonsu da haduwa irin haka .


Zeenat Tayi shr ta zuba musu idanu tace  kunsa wani abu ?

Atare suka  girgiza mata taja numfashi ta sauke sannan tace ciki ne dani 


Suka hada baki wajen fadi.

   Meyyyyyyyyyy.....
Tace ciki ne dani  har na tsawon wata 4 ni kaina bansani ba , say shekaranjiya .

Keko mayye kaiki wannan sakacin da kuruciyarki da komai zaki fara tara ya'ya  inji cewar sumy .

Uhmmmm abinda nima ke damuna kennan shiyasa nace bari naxo gurin ku kawayena kubani shawara.



Rukky ta kwashe da dariya wani shawara  km zamu baki ,Ai is too late yarinya lokacin dayake open legs yake  sexy dake kina jin dadi ke bakinsa zai zama ciki ba .Sai yanzu zaki kina marairaice murya.


Sumy tace uhmmmm  rukky ba abinda ke gaban mu ba kennan yanzu solution yaka mata anemo .Tunda cikin ma bai wani girma ba ai da sauki .


Ke yanzu zeenat yaki keson ayi da cikin tace  ni kawai so nake a zubar batare da sanin kowa ,gud idea inji sumy .

Akwai wata doctor dana sani zan hada ki daita.

 aikinta kennan zubda ciki yanzu akwai enough Money a gurinki zeenat ta girgiza kmr nawa sumy tace kmr 50k zeenat tace gaskiya kudin hannu bazasu kai haka ba .


Rukky datayi shr tana sauraronsu tun dazu  bata ce dasu  uffan ba say yanzu da taji zance zubda ciki  tayi saurin kallo inda zeenat din ke zaune a raunane takira sunan zeenat...amsa mata tare maida hankankalinta kan rukky.

 tace ni day gaskiya shawarar da zan baki bai wuce  kiyi  hakuri kibar cikin nan ba.
baki sani ba ko shikennan kwanki  a duniya .

Na rokeki Karki biyewa sumy wlh zata kai ki tabaro ne kawai .

Sumy ta katseta tace kinji jakanci nata  ba.
 A haka kmr wayis .
Kina ganinta muguwar  cukus ce .

karki wani saurareta keday kije jibi kizo da enough money muyi abinda zamuyi .


Rukky tace Duk abinda zakuyi kuje kuyi amman duk abinda tabiyo baya bbu hannu ciki ta Mike ta fice a binta .


Summy data bi banyan rukky da kallo tana zaginta ta  juyo tana kallon zeenat da jikinta gabadaya yasoma tsanyi.
Tace  tashi muje naraki tun yamma batayi miki  ba ,ke day kizo jibi kawai  da shrinki .......

 


MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
 AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗


AYSHA A BAGUDO


Page 42


A galabaice ta karaso gidan  hankalinta a tashi sbd wani irin azababen kinshin  ruwa da ke tasoma mata . gabadaya jikinta rawa yake.bata damu da yunwar dake Cinta ba ita dai tasamu ruwa.

Da kyar tasamu ta rarrafa ta isa gurin Fridge ta bude Ta dauki ruwan faro mai maseefar sanyi takai bakinta tasoma kwankwada .bata ajiye robar ba "Sai data sha Rabin ruwan sannan ajiye tana sakin numfashi.

'Ahankali  taja jikinta tayi side dinta  daidai bakin kofarta dakinta taji amai from no where .Ta zube gurin ta dinga kwara amai kmr ranta zai fita .

Numfashi kawai take fitarwa idanuna gabadaya sun gama juyewa.
" Sai narainarai take da idanu.

cikin haka Allah yataimaketa ya jiho mata Maryam .

Dauri Maryam  takaraso gurin ganin halin datake ciki ya sake frigittata ta dinga jero mata sannu.

 takamata  tashigarta daita daki ta gyara mata jiki ta kwantar daita sannan ta dawo ta gyra inda ta bata .


Tare dasa hannu ta janyo karamar jakar zeenat din da take sautin karar waya ,daga cikinta tana dubawa taga sunan my hrt na yawo akan screen din wayar hakan yasa  tasan kowaye .

Batare da bata lokaci ba ta dauka da sallamarta jin ba murya matarsa bane yasa shi yin jinmmmm kafin yayi wani hanzari yaji ance yaya Ina wuni ya amsa muryasa a dake .
Sannan yace Ina zeenat din take?
 
Tace Ga  kwance Ina ganin kmr bata da lfy nima yanzu nashigo nasame shame shame cikin amai 
  "ya Allah !!!abinda ya iya furtawa kennan akasan zuciyarta hankalinsa atashe yace ok bani ita .

Ta Mikawa zeenat din wayar daga inda take zaune ta karba .

cikin wani irin salon shagwaba tace  My hrt ya'akayi zeenat ya jikin naki ?
tace da sauki yace Sosai ta runtse idanunta tace uhm yace  ok bari nakira Fk yanzu akira miki doctor tasa miki drip ta sake  lumshe idanunta kmr yana kusa daita .yayi hanging din kiran .

Gabadaya Sai ta dinga Haushi da takaicinsa shi yana can wata uwa duniya ya kakaba mata tayama zata iya jurar wannan maseefar.ahankali ta zame wayar daga kunneta .
 Bacci bacci take ji dan haka taki bude idanunta .


Maryam ta Mike tashiga bayi ta dauro alwala dan bata bata gabatar da  sallar la'asar ba .

Tana idar da sallar " taga alamun  zeenat tasoma bacci tashiga tashinta tana ke kasa sarkin bacci tashi , zeenat ta bude idanunta  tashiga  juye juye  kokarin  Mike zaune  Maryam ta zuba mata ido  .

Tace uhmmmm nazo miki da balabri may dadi fa .
zeenat ta bude baki  zatayi magana taji miyau yacika mata baki.
 ta Mike da kyar tashiga bayi ta zubar da miyau ta wanke bakinta Ta dawo.


Maryam ya dinga binta da kallo kafin tace komai  meyye haka km kmr mai ciki , kar dai abinda ake fada da gaske ne .

Zeenat tace Me kennan ?

Ciki mana wlh naji ance mukusan samun bby fa .

, zeenat ta tabe baki  ke dan Allah bawani bby malaria ce ke damuna Maryam tace wannan kyawin da kika yi  yafi karfin ace materia ce  damunki.idan tayi wari maje.


Zeenat tace ki rabani da maganar cikin  wani labari kika zo min dashi?
" Maryam tace wlh  daman  Yaya kamil ne Yace yana sona km oready har mun daita kanmu shine nace bari naxo insanar da aminiyarta  kafin maganar taje gaba.

 zeenat ta dan yatsuna fuskarta sannan  tace kice kema kin kusan shiga daga ciki .

Dadin dake ciwonki  bai hanaki yin motsi .

Byn  kmr minti 30.
Sai Ga Yaya faruk da wata doctor yana shigowa parlour gidan ya hau kiran sunan Maryam ta sauko kasa da sauri  tana gaishe da shi .
Tare suka haura upstairs din .yana tmbyrta jikin zeenat ,

Doctor tashiga dudduba zeenat din da kyar tasamu tasha tea sannan tayi mata  alurai acikin drip ta daura mata.



Washegari zeenat ta dan samu saukin jikinta  dan har  ta samu tasanyawa cikinta wani ,ummi ma tazo dubata da wasu daga cikin dangi kowa yazo sai yace irin laulayin mahaifiyarta ta dauko .
Ko mahaifinta dayasa labarin halin da take ciki Sai daya tausayawa diyartasa.

 Gabadaya zeenat takosa jibi takai " Allah Allah ta dinga yi  jibi tayi kmr yadda Sumy tace taje a cire cikin a wuce gurin .


Dan haka ranar Monday tun safe take shirin ta duk da bawani karfin jikinta take jiba hakan bai hanata shiryawa da wuri ba dan har addu'a taje kar Allah ya aiko mata da wani bakon da zai rusa mata shiri .

Aiko kmr Jira ciwa yake tagama addu'ar ta .
Tasoma jin ciwon kai can km cikinta yasoma kafin kace me "  laulayi ya dawo sabo ,dan  har wani irin juwa juya take ganin datayi yunkurin tashi juya ke maidaita .
Gabadaya  komai ya sake da gule mata tarasa yadda zatayi da ranta kuka zatayi komai tasoma rawar tsanyi .kusan hour 3 tana kwance .


Da kyar tasamu ta daina jin jirin, dan haka Mike tasoma  bin bango  . 
ta sauka parlour'n kasa  f da niyar zuwa gidansu sumy har tazo kafar fito ta tuna bata dauko jakar  kudin ,duk da tasan batada wasu kudi  masu yawa  kmr yadda Sumy tace.

Dan haka ta sake juyawa ta koma dakinta adaddafe.
Sai dai  tana shiga dakin ta sake  jin wani sabon irin jiri ya kwasheta" ta tafi luuuuuuuu ta zube kan bed dinta tana fidda numfashi.

'Ahankali tasoma runtse idanunta da suke cike da bacci da rauni  . Kwanciya tayi Sosai dan gabadaya jikinta yayi week .

Cikin bacci ta dinga jiyo kamshin turare sama sama wanda ajikin mutun daya tasaba jin irin wannan kalar kamshin.
km  tun ba yau ba ajikinsa kawai take kamshin.
 'ahankali take furta sunanshi ya DEENI....ya DEENI.....

Shi km deeni dake kokarin shigawa dakinta ,Jin sautin kiran sunanshi datake yi .
 yasa yakarasa shigowa dakin hanzarinsa .

  kwance zeenat take idanunta a runtse Amman still sunanshi take sake  maimaitawa ya DEENI Sai km yaga tayi murmushi ta juyar da kanta 'ahankali ya  ajiye jakar hannushi yayi kanta da sauri ya dawo kusa daita ya zauna tare da kura mata idanushi 'ahankali ya kai yatsansa  shafa lip's dinta .
  yakira sunanta da wata irin  murya may matukar sanyi da dadin sauraro. zeenat.......Ta amsa da Na'am my hrt . 
Yayi murmushi  tare daura mata light kis a lip's dinta murmushi yaga tayi itama amman  still idanunshi nakanta  yace sannu ya jikin naki  . Shr tayi taki amsawa ganin wani ya jiki zai mata ,byn shi ya hada da tashin hankali dake hanata tsukuni .

 Ganin yanayinta yasan ba karamar wahala take sha ba  tana jin jiki matuka . wani irin maseefaffen laulayi take  mai wahala da gangar jiki .
Sannu a hankali ya dinga jin tausayinta yana bin jikinsa  tare da  ratsa kowani gaba na gangar jikinsa.
   ,yaji takara samun wani matsayi na musamman a zuciyarsa.

  ,ya runtse idanushi yana sake tausaya mata  yayinda hannuta ke cikin nashi yana yamutsawa hakika yana son bby ,km yana son yaga kyakkyawan bbyn da zata haifar masa ,idan ma Allah yataimakeshi  bbyn ya dauko  facing dinsa bai san ma irin murna da zaiyi ba . Shi kadai yasan kyautar dazai mata daga ita har bbyn .

 dan murmushi gefen baki yasaki yana jin wani irin farinciki gyaraye da tsantsar kaunar bby,n dazata haifa masa  .


Yana rike da hannuta yaga ta Mike tsaye da sauri ya kamota ya zaunar daita kan cinyarsa yaga tafara tutturesa  zatayi hanyar bayi yaki sakinta yana faman  tmbyrta menene zeenat?
Ko  wani abu kike so,? Ta bude baki kennan da niyar fada masa yabata 
Aiko tashiga kwara masa amai ajiki yana rike daita har tayi ta tagama.
 Sai lokacin taji  tsoron yima sama amai ajiki

Muryata a sanyaye taso kokarin bashi hakuri ya dakarta daita da hannushi tare da cewa kingama ta daga masa kai ya dauketa yashiga bathroom daita.
" wanka yayi mata ya nadeta a towel ya fito daita ya zaunar daita akan stood tana rawar sanyi ya canza wani bedsheet din ya kwantar daita .

 Sannan ya kwashe bedsheet din databata  da kayan jikinta ya watsa su cikin washing machine sannan  shima yaje ya gyara jikinsa dan duk ta bata  masa jiki .

ya fito kungunshi daure da towel, duk wata siffa ta karfi  sun  a bayyane ajikinsa.
 , gabadaya koina ajikinsa cike suke da yalwar gashim wanda har  nipply dinsa dake  tsaye zagaye suke da gashi .
 hatta yatsun hannushi kowanne kwance suke da gashi . kallo daya tayi masa ta dauke idanunta  dan bazata iya cigaba da kallonsa ba .

Wordrob dinta ya bude ya Ciro doguwar rigar  jallabiya ya ziramata tare bata light kiss a goshinta  .



'Ahankali ya dauki wayarsa dake ajiye akan mirrow dinta yayi dealing number fk.
" byn  fk ya dauki wayar da sallama suka gaisa ,yace dan Allah ka turomin likitar nan data duba zeenat shekaranjiya.

 Fk yace ka dawo ne ?
yace uhmmmm  ok kaban 3 minti  .

Bai sake cewa komai ya dauki jakarsa ya nufi hanyar dakinsa .



Ba'a minti shabiyar Sai Ga doctor din ta iso.

 Ta gaida DEENI cikin girmamawa yayi   gaba  tana biye dashi har dakin zeenat.

 kwance take har lokacin 'ahankali yakarasa kusa daita ya zauna ya kamo hannuta cikin nashi yana murzawa .
, doctor ta ajiye jakarta aikinta  agefe tashiga fidda kayan aiki .

'Ahankali deeni ya dube doctor din da muryasa mai cike haiba yace akwai aluran da za'ki  iya mata wanda zai tsayar  da Aman doctor tace eh.
Yace  ok kiyi mata tace ok sir .

Doctor tayi mata duk abinda deeni ya umarce dayi " byn deeni ya tilastawa zeenat din dole  ta shan tea sannan tayi musu sallama ta wuce .


Anyi mata injection din tsaida  amai amman say  da zeenat ta gwammaci daman bai bari ayi mata ba dan gabadaya rasa inda zata sa kanta tayi Sai runtse ido kawai  take tana juye juye ya rungumota jikinsa  cike da tausayinta,a hankali ya dinga  yana lallabata dabata baki   har tayi bacci .


Ya lullube da bargo ganin ta kamkame jikinta guri sannan ya nufi gidan umminsa ,byn sun gaisa ta tmbye shi mai kiji yace da sauki na barota tana bacci . Ummi tace dan Allah deeni kakara hakuri da zeenat kaji .ni dan tafiya ta kamaka ka dinga kawo min ita nan inyaso idan kadawo ka dauketa ku koma ,yace to kawai .
Bai wani dadi ba sosai yayi mata sallama  tabashi sobon data hada may dan tsami tsami  tace gashi yakai mata  ya karba ya wuce .
Gurin  fk ya nufa shima bai wani dade ba  koma gida .

Kamshin  turarensa ya sa tagane yana hanyar shigowa dakinta ta Mike tun kafin yashigo tayi hanyar  bayi jiri ya debeta da sauri yakaraso gareta yakamota ta fada kansa suka zube kan bed yayi gefe ganin yadda take fidda numfashi ya dagota ya rungumrta tsam  ajinsa yana mata sannu.
 ,kukan wahala  ta fashe masa  dashi tana aiyana yadda zata raba kanta da wannan jararlbabben cikin nasa .
 , a zabure ya Mike ya zaune kmr yasan abinda take aiyanawa a ranta.

 yace please zeenat ki dinga bi 'ahankali km dan Allah kiyi hakuri da cikin nasan yadda yake wahalar dake ,idan wani abu yasamu bbyn basan yadda zan ji dan  wlh baki san yadda nake jin cikin nan naki a zuciyata ba .

Yasa hannu yana dauke mata hawayen dake bin kuncinta , tare da sake rungumeta tsam tsam ajikinsa .
kuka  tashiga rera masa shi km Sai rarrashita yake yana bata  hakuri ta jure ta haifa masa bbyn .

Kokarin raba jikinta take da nashi dan bataji zata iya wani hakurin haihuwa ba . wannan cikin nasa dake neman kaita lahira ,shine yake wani bata hakurin cuta  hannuta 'ya rike  gam yana tmbyrta Ina zaki tace amai nake ji .


 Ya Mike tare daita ajinsa har bathroom yaja ya tsaya yana jiranta .
Haka ta tsugunna  tayi ta yunkurin amai amman bbu abinda ya fito ackinta byn miyo .
haka ta hakura ta Mike ya sake rikota ta kwanta tana fidda numfashi sama sama. 
idanunsa ya zuba mata yana kallonta duk ta rame Sai dan wuya idanunta suka sake shigewa ciki .

Yasa hannushi ya sake jawota jikinsa  yana shafa kasan mararta  . Yace me zaki ci?
 ta girgiza masa kai bana son komai .


Yace ki taimakmin kici ,wani abu mana  .
kalli duk yadda kika rame jin haka yasa  ta fashe da kuka tana kiran sunan ummi .....

Ya dan  zuba mata rankwashi akai ,ki daina min kukan kmr wata bby. kema kina kuka   haka Ina Ga bby'n mu .

Kuka tacigaba dayi .
ita kadai tasan abinda take ji ajikinta .
Km tasan abinda  kesata kuka gabadaya dawowarsa ya rusa mata budget dinta kuka take sosai, ya ware idanushi kawai yana kallonta da mamaki . Ta dan ja baya kadan dan ta tsorata da irin kallon dayake mata.

Kyacci yayi tare da jan kunneta yace kinci sa'ar bbyna dake jikinki wlh.. ajiyar zuciya ta sauke jin ba wani abu zai mata ba . 'Ahankali ya sake maida jikinsa 'ahankali yasoma cire mata doguwar rigar jikinta ya hade jikinshi dana nata yana goga mata gashin kirjinsa . wani irin feeling yake ji yana taso masa cikin sanyi ya kai hannushi saman mararta yana shafa 'ahankali 'ahankali. Sakwanninsa masu frigitawa yashiga aika mata yakamo Brest dinta yana mammatsawa ,'ahankali itama tasoma maida masa da martani , cike da kwarewa ya dinga romancing dinta , sosai ta sakar masa jikinta kmr ba jin jiki ba ,sai da komai lafa ,km zazzabi ya rufe ta .



Washegari yana fita aiki .
Ta lallaba tashige dakinsa 'ahankali ta jawo  dorowa tajita akulle 'ahankali tace wayyo nashiga uku ta Mike tafara kwalle kwalle a dakin cikin dakin kmr zata zubda hawaye to ita zata samun kudin zuwa asibitin gashi kudin hannuta basu kai sun kawo ba dorowa din dakin ta dinga bubbudewa gabadaya ko zata ga kudi amman bbu .duk ta gaji sai haki take ga tsoron kar tsautsayi yasa deeni dawo gidan ya isketa tana masa bincike .

tuni hawaye ya balle mata tana addu'ar Allah ya taimaketa taga kudi ta bude waya dorowa taga tarin takardu da file files .taja tsaki ta mayar ta rufe da karfi ,kmr an tsinkireta ta Mike cikin sauri Ta nufi wordrob din kayansa ta bude batasan sanda ta lumshe idanunta ba sakamakon cinkaro da tayi da kudi bandir bandir jere da juna .wani irin  sanyi taji yana  nabin jinin jikinta hamdala ta shiga yi aranta .cikin sauri Ta dauki bandir daya ,dan tasan zai isheta har ya rage ta zuba cikin hand bag dinta tsabar murna samun kudin datayi ta nemi ciwon dake tattare daita tarasa .




MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
 AUREN SIRRI
     💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO



Page 43



Cikin sauri  sauri Ta fito daga dakinsh ta nufi nata  ta dauki  mayafinta ta yafa ,biyu biyu ta dinga saukowa daga step jikinta gabadaya Banda rawa bbu abinda yake .Ta nufi kofar fita.


Har zata fita taji makoshinta ya bushe ta dan dawo da baya da baya ta  bude fridge ta dauki sobon da ummi ta bayar akawo mata ta kafa kai  tasha sosai tana sauke ajiye zuciya .


Cikin haka taji wayar ta dauki kara 'ahankali ta zira hannuta cikin jakar dake makale da kafadarta ,tasoma kokarin Ciro wayar  ta duba tana sauke ajiyar zuciya .
Sunan wacce tagani yasa ta dauki wayar , da sauri .

Hello ....Zeenat ya' akayi najiki shr km?
  jiya haka nayi  ta zaman jiranki gashi yau ma haka ko kin fasane inji cewar sumy ?

"tayazan "fasa,  irin wannan bakar wahalar danake sha.
 wlh bbu abinda zan fasa  jiya ma  Sai dana gama shirina  say Ga my hrt ya dawo ya rusa min budget Amman karki damu Gani nan a kan hanya .

ok kiyi sauri  Ina jiranki kifa zo da enough money , zeenat tace karki damu kawas ganin nan day zuwa ok Sai kin karaso .
Ta yi hanging din kiran tare da km jefa wayarta ta cikin jaka ta ajiye robar sobon hannuta tun kafin da dago .

 Assalamu alaikum taji anyo sallamar ,take ta Mike ta sankame a guri daya jikinta ya dauki rawa waye ....waye ...km zai sake shiga cikin lokacinta ? 
Dafe kirjinta tayi wani frigice ya sake zuwa mata.
" bazata taba manta wannan muryar ba ko acikin mutane dubu ne ,cikin sanyi jiki takarasa bakin kofar jin sallamar taki karewa .

Assalamu alaikum wai Ina masu gidan ne? Tabbas 
 inda ba gizo murya ke mata , wannan murya shemah ce. hannuta na rawa Ta daura akan handle din kofar ta bude 
 ,shemah tagani tsaye tana sarka mata dariya.

Ya haka kin bar mutun yana ta faman rafka sallama km  kin kasa amsawa  dan Allah ni ban hanya na shiga ciki na kwaso gajiya.
  kinbarni  tsaye  .

Sai lokacin zeenat ta farga tasan abinda yakamata tayi  , ajiye zuciya ta sake saukewa tare da sakin murmushin karfin hali uhmmmm Ina shirin amsawa kennan wlh  sobon da nake sha ne yasa kikaji banyi  sauri amsawa  ba.
 ,sannu da zuwa tabata hanya tana cewa  daga Ina haka?

 daga gida  , shemah data karasa shigowa  tasoma kokarin kwanto danta dake goye abayanta  ta mikawa zeenat shi  .

jiya mukayi ar'bain shine nace yau dai sai  nazo na duba jikin guzuma .
dan naji ance bakida lfy sosai laulayin ciki yasaki gaba .
  abu fa ya hade da son jiki .
jikin zeenat duk a sanyaye tace duk son jikina  ban kai ki ba .

,Aa wlh bazama a hada ni dake ba wlh.


Lokacin danake laulayina waya sani .
Amman ke bbu wanda baisani ba .
Shemah ta maida hankankalinta  kan zeenat din sosai tana dubanta  say naga kmr fita ,zakiyi .

, zeenat ta sake yin murmushin fitar lfy    uhmmmm bbu inda zani  "
ok wuni fa muka kawo miki dan say yamma  zamu wuce gidan .



'Ahankali zeenat tasamu gurin ta zauna kan kujera tana furta kalmar inna lillahi wa inna ilaihi rajiun akasan zuciyarta .

Shemah tace yana Ga duk kinyi wani iri ko bakiji dadin zuwanmu bane?

 , zeenat tayi saurin wayencewa tare ware idanunta tana murmushin karfin hali may kike Gani.

 naga  jikinki duk yayi sanyi dana say yamma kmr baki so zuwanmu ba .

Zeenat ta girgiza kai uhm  bbu komai wlh yanayin jikina ne yasa kika Ga haka  kin san yanzu say 'ahankali .


Shema tace Kuma kunkusan shiga samun manya .

 suka sa dariya atare zeenat tace  shemah dan  dauko hollondia a store kisa a fridge ya dan sanyi kafin ki tashi sha   .
 ,shemah ta Mike .

Zeenat naganin  shigar shemah  store tayi saurin Ciro wayarta tayi dealing number sumy.

Sumy na dauka  zeenat tace  ,kawas yau ma fa damata ta km subuce min Sai day km gode .

me ya faru km yau  inji sumy wlh shemah ce  takawo min wunin.

 sumy tace shikennan kima kwantar da hankalinki karkisama kanki  damuwa.
 daga gidan  nurse din dazamu gurinta  nake yanzu   .

naje ban isketa ba   wai tayi tafiya Sai zuwa Thursday zata dawo.

 , zeenat dake zaune  rike da bby bbu abinda jikinta keyi  Sai rawa  jin abinda sumy tace.
'Ahankali ta furta shikennan ,nashiga uku ni zeenat yanzu yaza,ayi kennan ?

hakura zamuyi yanzu  say ta dawo , zeenat tace ke bakin wata  dazata iya cire min.

 uhmmmm  gaskiya bansan kowa dake irin wannan aikin  ba say ita.

 kinsa fa bakowa ke  irin wannan risking din ba  .
itama a boye takeyi a wani small  office dinta.

 keday kiyi hakuri kawai mubari  har ta dawo . Zeenat tace oh Sumy  Ina cikin one chance .
 
Kede ki natsu fa dakyau ki rufamin asiri kar shemah ta dagoki fa.
Komai ya kwabe mana  .

zata sake yin magana taji motsin shemah tana fitowa daga store zata shiga kitchen da  sauri tace shikennan Allah yakaimu Thursday din say muyi waya tayi saurin  hanging din kiran .


Tana kokarin dawo da natsuwarta dan kar shemah ta dago logonta .
 , amman sam hakan yagagara samuwa domin gabadaya hankalinta a tashe yake .



Sannu 'ahankali yanayinta ya fara canzawa daga shaukin  farincikin da take ciki zuwa bakin ciki da faduwar gaba .
Takasa fahimtar abinda ke shirin  faruwa daita.
Farinciki ko akasin haka  kullun da matsalar dake rusa mata budget .
 
 'Ahankali Nadama tasoma zuwa mata   tana jin laifin da zata aikata shine mafi  girman  zunubin dazata daukawar kanta.

 ita kanta tana son  ta haifawa deeni abinda ke cikinta  ko dan samun cigaban farincikinsa.

 amman tun kafin akai Ga  haihuwa tasoma renan kanta .


Wata zuciyarta na kwabarta akan tabar cikinta kmr yadda rukky taba shawara .

yayinda wani bangare na zuciyarta ke ingizata akan lallai ta cire kawai karta kuskura ta yarda ta haihuwa .

Bbu komai a Haihuwa facce   wahala.
 sosai tayi zurfi  acikin tunani   har shemah ta karaso gareta ta zauna kusa daita  zeenat na can Ga duniyar tunanin  yadda zatayi da cikin jikinta .

 Ta hakura ta jure wahalar dake cikin rainon ciki da haihuwa ko km ta zubar ta hutawa ranta .

Shemah  ta dan tabata  byn tayi ta kiran sunan taji shr.
 a frigice zeenat ta kallo barayin  da shemah ke zaune  tana  dan murmushi yake.

Shemah  ta zuba mata ido  kawai  tana kallonta .

'Ahankali ta sauke numfashi tace  ,make damunki haka Zeenat?

Wannan wani irin tunanin ne haka kika jefa kan ciki?
 tun dazu nake faman  magana da kiran sunanki Amma duk bakisan inayi ba .
 
 koma meke damunki , yakamata ki sausaitawa kanki kodan sbd yanayin da kike ciki.
 , wannan tunanin da kikeyi zai iya shafar dan dake  cikinki.
dan Allah kiyi hakuri  kibar tunani irin haka kinji komai na duniya dan hakuri ne  .

Zeenat da jikinta yagamayin sanyi  tace bbu komai fa  , shemah tace Allah yasa nan suka bar zance suka shiga hirar duniya .



Deeni dake zaune  office  yana saka da aikinsa  ya dinga jin faduwar gaba ba kaukautawa .
,'ahankali ya dinga karantu  duk  addu'ar da yasan zata kawo masa natsuwa da rage masa jin abinda yake ji .


' wani tunani yazo masa yasa hannu ya janyo wayar dake charge daga gefe  yashiga neman layin zeenat amman shr bata dauka ba.

 hankalisa ya sake tashi ,dan haka yashiga neman layin   umminsa  Kira daya cikin na biyu ummi ta dauka da sallamarta .
ya amsa yana  gaishe da  umminsa .
 tace ya aiki yace alhmd  tare da cewa first lov dan Allah Ina son asamo min   housrlegirl kmr guda biyu .

ummi tayi shr har sai dayagama maganar sa tukun ta numfasa ,sannan tace kai ko mezakayi da house girl har biyu ?

Ina ma laifin daya ,first lov saboda zeenat ne wlh  kinsa yadda ciwon nan  yasata gaba .
 gabadaya idan bana nan hankali baya kwanciya ,amman idan akasamu masu kular min  daita zanfi samun natsuwa .

Jin haka yasa  ummi tace shikennan za'a nemo" ita km Allah raba da cikin  lfy .
  yace  Ameen ,tare da cewa dan Allah first lov kisa a bincika daga yanzu zuwa anjima .

Ummi tayi murmushi tace to dan  oya oya zan kira momy fervor yanzu naji ko za'a samu .
sukayi sallama .

 still number zeenat din ya sake nema wannan karon tashiga  shr yayi tare da  kamo lip's dinshi kasa  yana dan cizawa sannu sannu yana  jiran ta dauka  .


'Ahankali ya sauke ajiyar zuciya jin muryata.

Hello my hrt yace ya'akayi zeenat?

 Ina kika shiga tun dazu  Ina faman nemanki har Kinsa hankalina tashi ?
  
Tayi murmushin jin dadi ta  marairaice murya sannan tace  wayyo my hrt wlh na dan yi busy  ne  shemah ce tazo  .

yace ok kina day lfy ko tace uhmmmm yanzu ya jikin naki  ta gyara zama  tare da cewa da sauki day .
ki kara mana hakuri da bby'na  nasan yana  wahalar dake sorry .

ta sake yin  murmushi  bbynka ka kadai kennan ban dani ko?
Yace sorry  I mean bby'nmu .
nasa ummi tasamo miki house girls dazadu dinga taimaka miki.
 idan an samu zaki Ga an kawo .

ok Nagode my hrt yayi murmushi karki damu wai meyasa kika zabi kice min zuciyarki ?

Sbd ina maka wani irin son da ni kaina ban iyakarsa ba " idan bbu kai  acikin duniyata  zuciyata zata iya yin damage.
 , Allah my zeenat ta girgiza masa kai tamkar yana kallonta . 

nouking din office dinsa dayaji  yasa shi cewa ki kularmin da kamki  please zankiraki zuwa anjima.

Eyyyye .... eyyyye..
agabana yarinya kike irin wannan narkewar tamkar yana kusa dake ko kunyata ba kyau 

,inji kunyarki tsoron ki ma nake inji cewar zeenat


Wunin ranar suna tare da shemah har karfe biyar sannan shemah tayi mata sallama ta wuce.

 byn tafiyarta shemah   momy fervor takawo mata  masu aiki guda .

Zeenat ta nuna nawa momy fervor wajen zama .
,tana murmushi ta zauna  tace Nagode madam  Ga masu aikin nan" hjy tace akawo zeenat ta dubi gurin da masu aikin ke tsaye  " ta yatsuna fuska  tace ok ,jikinsu na rawa  suka dan durkusa suna gaisheta ta amsa  tana  nuna musa wani daki dake manne da parlour'nsu    tace su shiga su ajiye kayansu suzo.
 ,byn sun je sun ajiye jakar kayansu suka dawo suka sake  tsayawa , zeenat ta dubi inda momy fervor take zaune tace meyye sunansu ?


Momy fervor ta kallli Yar gajeruwar ciki tace moris sannan wannan km rahma ,amman dukkansu ba muslin bane christen .

, zeenat ta kada kai kawai tana duban su moris sannan ta sake maida gurin momy fervor tace ayi komai a gabanki Tunda wuri ,idan aikin su zai yiwu  agidana .
Bana bukatar asakamin   Kanan kaya agida   wandon jeans  ko minti siket , anything rofdress I don't wont .

Momy fervor ta dube su da kyau tace kunday ji abinda madam tace ,suka sunji zasu kiyaye .

Zeenat ta   bude jakarta ta Ciro en  dubu dubu guda biyar ta mikowa momy fervor

Momy fervor  tace Aa ai hjy tabani zeenat tace kar ki damu ki karba kawai ta amsa tana risinawa da godiya . saannan ta sake  cewa su   moris dan Allah su maida hankali suyi duk abinda yakawosu da duk abinda yakamata  ta Mike tana yi musu sallah .


Say Washegari da safe deeni yaga masu aikin duk bawani kwanta masa sukayi ba ,dan haka ya kira doctor din dake kula da lfyr zeenat.
 yace tazo ta kai su moris a musu gwajin jinin sbd sanin cikakkiyar lfyrsu.
 ,hakance ta kasance anmusu gwajin komai normal zeenat tayi musu bayanin duk aikin daza su dinga yi mata  .

 Ke moris  girki zaki dinga yi ke km rahma  gyaran sama da kasa ,suka amsa mata  da to.



Zeenat  makale da  kudinrin tana  Allah Allah taji kiran sumy  dan sam bata zata  iya  hakura da zaman cikin ba  .


Thursday kmr yadda Sumy ta shida mata  dawowar nurse  .

Ta shirya suka je  km sun sameta a gida ,byn Sumy tayiwa nurse  titi  bayanin abinda ke tafe dasu .

Nurse titi   tace badamuwa su sameta a office hakance takasance .


byn sun sameta nurse titia office dibta   ta dubi Sumy tace  how many month cikin ,Sumy tace going to 4 month   .

Nurse titi ta dubi zeenat tace ke meyasa zaki zubar da ciki? Sumy tayi saurin cewa wlh wani saurayinta ne yayi mata cikin ...so km karatu suke shiyasa take son zubawa  . zeenat na tana jin yadda sumy ke zuba karya ,wel ita dai ba wannan ne matsalar ta .

 ,Nurse titi tace   ok yanzu abinda za'a yi   duk cikin wata daya muna cireshi dubu goma   .

Kinga  kudinta yakama 40k  kennan.
  kudi badamuwarmu bane mudai ayi komai agama  lfy.
zeenat ta kirga 40k ta ajiyesu nan  kan tablet din nurse .

Nurse titi ta Mike yasoma harhada aluran kala kala taja su a  sirinji tare da   nuna zeenat wani guri dake kewaye da labule .

Zeenat ta Mike cikin sanyi jiki tashiga gurin nurse titi   tayiwa mata injection   guda biyu "tare da bata  tablet shima guda  biyu tace idan taje gida tasha daya ta tura daya a gabanta da kyau .
"Ta kwanta sbd maganin zaifi aiki sosai ajikinta .
Sannan km idan taga jini karta kuskura tasha ruwan sanyi sai hot water . 


Da sauri suka Mike suka bar office din nurse titi saboda lokaci yasoma wucewa kai tsaye inda sumy tayi parking din motarta suka nufa .
suka bude kowanne su yashiga ya zauna .
  "sumy tayiwa motar key  ta fige motar da  gudu ta fita.
 ,ko acikin motar ma sumy sake jaddawa zeenat take dan Allah kartayi kuskure da wani abu zai faru ,dan duk abinda yaje ya dawo say a nemenita .
 kinga Kinsani cikin bala'i.


Zeenat taja numfashi karki damu kawas bbu abinda zai faru say alkhari , addu'a ta a yanzu naganni agida .


Daidai jakonde first get sumy ta sauketa tace to Allah yakiyaye say muyi waya takarasa barin jection din da sauri dan gudun  kar mugun ido yaganta .



Da kyar zeenat ke daga kafafunta har ta iso bakin get dinsu securities nata masa sannu da zuwa ,bata tsaya tabi takansu ba .
Burinta bai wuce ta ganta a cikin part dinta ba.



Tana shiga part dinta ta dan tsaya a parlour'n kasa tana sanarwa moris abinda zata daura dan kusan dowarta suke Jira .

Tana shiga dakinta bayi tashiga ta dauro alwala tazo tagabatar da sallar la'asar ta balli table din da nurse titi Tasha sannan ta tura dayan akasanta kmr yadda Ta umarceta.sai da tabbatar da ta tura tablet din akasanta da kyau sannan ta nemi guri ta Mike akan bed dinta tana Jiran abinda zai faru.




Kusan 2 hours ta dauka kwance Amman bata ji wani alamu ya canza ajikinta .dan haka ta Mike tashiga bayi ta duba sam bbu wani abu datagani wanda ya danganci jini sai ainihin ruwan jikinta .

Hankalinka ya tashi ta dauki waya ta Kira nurse titi tasanar mata .itafa bata Ga komai ba .
Tace kibari zuwa can dare mugani dan alluran dana miki duk masu karfi ne da wannan table din nasan kafin safiya cikin zai yi kasa .


Deeni yana shigowa estate din ya dinga Gabansa na cigaba da faduwa da sauri , addu'a yasoma karantowa .da haka ya dan samu natsuwa ,dan kwata kwata yarasa dalilin dayasa yake jin haka da farko ya danganta hakan da rashin lafiyar zeenat byn yakira zeenat din ya tabbatar da lfyrta km still yana jin gabansa na dokawa sam bay taba tsintar kanshi cikin wannan yanayin masallaci cikin gidan ya nufa byn yayi magrib da isha'i  yayi addu'a Sosai akan duk ma abinda zai sameshi yazo masa da sauki .

Bai tsaya wani bata time ba ya fito shida fk suna gaisawa sama sama fk na kokarin kowa masa wani zance yace sauri yake kasan madam dina sai a slow . Yayi gaba ya bar fk.

Fk ya dinga masa tsiya wai yanzu  yazama mijin hjy   sai rawa kai kake  akanta ko juyowa DEENI bai yi ba yacigaba da tafiyarsa tare da cewa kai ka sani dan sa ido kawai.




Kwance take akan gadonta ta bude idanunta byn taji shigowarsa ta Mike zaune tare da yaye bargon data lullube jikinta dashi.

Idanunta tsaye akansa tana kallon fine man dinta , tamkar wanda ake sake canza masa halitta da kara masa kyawu .
Kokarin tashi take  amman ya dakatar daita da hannushi .yana may karasowa gareta.


'Ahankali ya janyota jikinsa ya rungumeta tsam tsam yana shinshina wuyanta bby ya jiki ta narke masa ajiki.da sauki say day  bb'ynka na  ban wahala .
Sorry karki damu duk randa ya fito. zan zane miki shi I promise .tayi murmushi tana sake shigewa jikinsa .
Cikinta ta dan ya murda mata ,tasa hannu ta dafe mararta tare yatsuna fuska ,ya kalleta yace lfy ta girgiza masa kai kawai alamun bbu komai.

Yace bari naje showerl daman nazo naga lfyr bby'na ya kwantar daita tare da tmbyrta ko tayi sallar isha'i tace eh sannan ya wuce dakinsa .


Wanka yayi ya dawo dakinta byn ya hadawa kanshi coffee yasha dan kwata kwata bazai iya cin abinci masu aiki ba .

Zuwa lokacin ta kokarta ta Mike tayo wanka tare da sanya kayan bacci tayiwa kanta wanka da turare dan tasan mijinta mayye kamshi ne.


A gaban mirrow ya isketa  tsaye yakaraso gareta yazagaye hannushi a kungunta yana kaiwa wuyanta sumba ya amshi kwalbar turaren ya ajiye.

Ya janyota hannuta muje kiji wani labari mai dadi duk ta dago abinda yake so tana rungume ajikinsa har dakinsa.yajata suka zube kan bed yasoma aika mata da wasannisa masu saurin dagulamata lisafi da birkita mata Brain.gabanta say faduwa yake 'ahankali yayi kololuwar tashi dan alokaci bbu abinda ta tsana kmr yace zai yi sex daita.
Romancing dinta yasha yi amman sam taki yarda ta mayar masa martani cikin sanyi yadakata da abinda yake ya zuba mata idanushi,cikin kwayar idanunta yake hango wasu abubuwa wanda yakasa fassara su ,tsawon lokaci ya dauka yana kallonta ganin haka yasa ta wayance ta shige jikinsa tare kamo hannushi ta daura daidai kasan mararta my hrt cikina ke ciwo.
A take 'ya frigice cikinki ke ciwo shine baki sanar min ba say yanzu tashi tashi muje hospital ta zaro idanu waje tana datasanin cewa haka.
Ta sake narke masa Ai naji sauki uhm ke dai kibari muje kawai banason sakaci fa shine first hope dina idan wani abu ya sameshi zanji ba dadi I will blame my self  tasa hannu ta dago fuskarsa karka damu bbu abinda zai samu bbynmu ya lumshe idanushi tare da cewa Ameen a zuciyata km tana canza mafar addurta datayi.


Kwantar daita yayi ya rungumeta tsam ya fasa yin abinda ke rashin dan gudun kar wani abu ya samu bby'n.

Basu wani dade ba bacci yayi awon gaba dasu .

Cikin bacci ta dinga ji tamkar ana mintsininta can km taji wani azababen ciwon ciki hannuta dafe da mararta tana murkususu taki tayardashi dan kar Yace suje hospital say cizan lip's dinta take tana yarfe hannu duk sanyi AC dakin hakan bai hana gumi tsatsafo mata ba .

Ta Mike tana layi tayi cikin bathroom din dakinsa tasoma kokarin cire pent dinta abinda tagani ne ya frigita..




MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
    💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO



Page 44



Jini tagani har da gudaji gudaji  a pent dinta. Wanda hakan yayi sanadin tsugunwarta kasa da sauri .

 tsugunwarta keda wuya taji tamkar ankara mata wani ciwon ne akan wanda take ji.

 kmr Jira jini yake ta tsugunna yashiga zubowa " Ga wani  irin azababen ciwon  data ke  ji a kasan mararta kmr zata mutu.

 murkususu take sosai tana yarfe hannu.
 ta dinga nishi sama sama duk iya duriyar da take  dan kar DEENI ya farka ,bai hana Hawaye silalowa daga idanunta ba .

Da  azaba tayi azaba kawai say tasa kuka.

 Cikin bacci deeni ya dinga jin sautin kukanta  'ahankali 'yashiga lalubar inda take kwance da hannushi .yayinda idanunshi ke rufe ,yaji bai ji alamunta ba ya sake motsowa gaba still bbu ita da sauri ya mike zaune yana bin takin da kallo" km har zuwa lokacin baidana  jin gujin kukanta ba.
 
Hankalinsa ya tashe  ya zabura ya mike tsaye   yayi hanyar bathroom din dan tanan kunnenshi ke jiyomishi  sautin  kukanta  .

say day  yana daura hannushi akan handle din kofar yaji kofar gam  a garkame .
 ga km alamun  Tana cikin bathroom din  dan lokacin yana jiyo  sautin kukanta Sosai.


A razane  deeni ya hau buga fakor da karfi yana kiran sunanta zeenat...... Zeenat.. amman  shr taki amsawa sai kuka take .


 meke damunki zeenat ki taimaka bude min kofar  please ... Duk yabi ya rude ya gigice yacigaba da buga fakor yana kokarin ballata .


Ganin irin azabar da take sha wacce ita tajanyowa kanta gashi  idanunta har sun soma rufewa shi km yana cigaba da jijiga kofar hade da kiran sunanta yasa ta rarrafa da kyar ta bude masa yana ganinta haka ya gigice ya shiga  tmbyrta
  
Ita km tana murkususu dafe da mararta 'ahankali ta dinga nuna masa kasa inda jinin ke kwance dan gabadaya idanushin akanta  suke  shiyasa sam bai yi saurin gane abinda ke wakana ba .


Kallan yadda jinin ke tsiyaya akasa ya kara tayar masa da hankali .

Sai murkususu take tana wayyo Allahna Yaya mutuwa zanyi dan Allah kayafe min abinda nayi ....na...
Na ...say km tayi shr sakamakon wani yunkurin ciwo  daya tasomata  say Ga wani jini ya sake ballewa ..Ta Miko masa hannuta, kafin yakaraso gareta har ta suma .


A gigice yakaraso  ya rungumota jikinsa.
Tare da  kunnan popping yashiga shafa  mata ruwa ajiki da fuskarta.
  , ahankali yaga ta  sauke ajiyar zuciya.
 
A rude yake cewa "
Kingani ko zeenat.

 kinga abinda kika jawo min ko .

shiya nace muje hospital duk yabi ya kidime ya gigice  har yarasa me yakamata  yayi ,bbu komai kina sane kike kokarin jawo min   asarar bby'na ko.
 Amman 
, bbu komai .

Say kalmar bbu komai yake faman" maimaitawa .Bai yi aune ba yaji saukar hawaye a fuskarsa.

Ganin jinin  ma kmr sake  zubowa yake, yasa ya mike da  sauri  bbu inda baya kirma  jikinsa yakoma daki.


Jikinsa na rawa ya zira jallabiya ajikinsa ya dawo ya dauketa ya fita daita yasata abayan mota ya zagaya yashiga yatada motar  da gudun bala'i.

tun daga nisa yake dannan  hon kafin ya kawo get din estate din  hon dinsa hon ya karade koina . wanda hakan  yasa gabadaya securities din wajen suka zabura suka Mike tsaye  hankalinsu a tashe .
 ganin motar oga deeni ce yasa mutun uku sukayi  hanzarta bude get din a guje ya figi motar ya fice daga gidan.

 say addu'a wasu daga cikin  securities din suke Allah yasa day lfy.

Dan basu taba ganin oga deeni ya fita haka, km acikin wannan lokacin ba .

Kai tsaye hospital dinsu doctor saira Jack ya nufa daita wanda tun kan yakaraso yayi mata waya  .
"dan haka Komai yayi ready kafin  isowarsu .

Yana shigowa hospital din gadon marasa lfy na ajiye agefe  da sauri nurses suka kamota suka daurata akan gadon marasa lfy " cikin sauri sauri gudu gudu sukashiga turata deeni nabiye dasu  rike da hannuta har suka kawo kafar wani daki .

Dakatar dashi likitocin  sukayi sannan  suka shige daita .

Ciwo kmr Jira yake azo inda magani yake  yace Bismillah cikin lokaci kadan zeenat tayi mugun fita haiyacinta, dan kwata kwata batasan wanda ke  kanta ba  say aikin sunan ummi da ta dinga Kira .
,har zuwa wayewar gari ranar bbu wani sauki .

Likitoci akanta suka kwana aiki.
Yayinda deeni yakasa tsaye yakasa zaune sai patrol yake yana safa da Marwa tare da  addu'a Allah yasan bbu abinda yasamu bby .

 Iya dakiya deeni yayi amman hakan bai hana Hawaye bin kuncinsa ba  tamkar yaro . Tunda yake bai taba kasa abu aranshi haka ba tamkar yadda yasa cikin zeenat.


Duk abinda ya dace likitoci sunyi gurin tsaida cikin amman Ina hakan batasamu ba dan    cikin day  ya rigada ya  zube.

 jinin day ne day suke kokarin suga  tsaya Duk wannan wahalar da zeenat ke sha sunan ummi bai fita abakinta .

 deeni yaki kiran ummi ne  dan sanin say  hankalinta  yafi nashi tashi idan taga halin da zeenat din ke ciki .
,'"gashi itama kusan  tafi shi kwallafa rai da dokin  zuwan bby'n.

Kana kallon deeni zaka gane irin kalar tashin hankali dayake ciki .
dan gabadaya ciwon tamkar ajinkinshi yake .



Zeenat bata farka ba sai wuraren karfe goma da rabi na ranar    ta bude idanunta ne fes    akan mutane masu mahimmanci a rayuwarta  deeni dake zaune  rike da hannuta  ummi  da mahafinta say wasu daga cikin  cikin en,uwa  zagaye daita suna mata sannu.
 kallon su take 'ahankali tana mamakin ganin yanayin su , kwata kwata fuskarsu bata nuna mata alamun  sun san abinda ta aikata ba .

Dan haka ta lumshe idanunta  tana jin daci daradadi hade da  munin abinda ta aikawa DEENI.

 hakika tacika azaluma may cutar da yayan mutane wanda basu ji ba basu Gani ba ,domin  ta cutar da zuciyar da bata cancanci haka daga gareta ba .

 ,kara lumshe ido tayi Hawaye suka zubo mata zuciyarta sai bugawa take tamkar zata fasa kirjinta ,


Sannu zeenat Ummi ta fada hade da dafa goshinta tace mayye na kuka km?
 "Allah daya baki wannan ya karba tun bai kai koina ba" shi zai sake baki wani inshallahu.
 ,kiyi hakuri kukan yaisa haka kinji . 
Deeni da mahaifin zeenat suka  mike suka bar dakin sakamakon wata nurse datashigo ta mikawa deeni  wata white paper .shi km mahaifin zeenat amsa waya ya fita .

Zuciyar zeenat ta tsinke tashiga harbawa da sauri bbu abinda take ji da ganewa, tun fitar deeni daga dakin .

 Hakuri Sauran en,uwa  suka dinga bata akan abinda tasan ita tayi sanadin fitarsa.

Ya ya deeni zaiji idan yasamu wannan  labarin na zubar masa da ciki datayi ?

,tasan kasheta ne kawai bazai yi ba dan takaicin abinda ta aika masa.

 ,ita dai yanzu Duk  jinsu  kawai take honestly batasan ko a wani yanayi deeni yake ba .


It's alright zeenat kukan yaisa haka inji Ummi .
 ,jinjina kai kawai tayi yayinda Hawaye ke cigaba da bin  kuncinta dan tasan kuka kam yanzu ta farashi muddin DEENI yasan abinda tayi , gabadaya en'uwa hakuri suke bata tare da rarrashita.

Kokarin tashi take Ummi takamata suka shiga toilet tayi brush suka fito Ummi ta hada mata tea mai kwari ta bata.
 rike take da cup din tea amman kwata kwata takasa kaiwa bakinta .


Doctor saira Jack ce tashigo dakin ta umarce mutane dakin da suyi excuse dinsu .

Byn dakin ya rage bbu kowa daga doctor say zeenat  likitar ta  dan duddubata.

Sannan tace  ta  sha tea ,sbd zata mata injection ne.

 ,take gaban  zeenat yashiga faduwa ganin irin kallon da likitar ke binta dashi.
 hakika tana jin mutuwarta ce ta kusanto ,tun kwananta bai kai ba .

,murya likitar ce ta doki dodon kunneta madam drik ur tea.

 jikinta na rawa takai cup din bakinta Ta dan sha kadan ta,ajiye .

Duk doctor saira na hankalce da yanayinta gabadaya atsorace take .

 byn kmr 2 minti likitar na dubanta da wani yanayi. sannan ahankali tasoma magana cikin harshen turanci madam meyasa kika aikata  abinda kikayi ?



A frigice zeenat ta dago ta zubawa likitar ido tamkar bata gane abinda likitar ke nufi ba.

 likitar tacigaba hakika kin aikata laifi Mafi muni da wulakanci ,dan da hannuki  kika kashe bby'n ki.



 ,kinsha magani zubda ciki ta karfin tsiya dan ki zubar da ciki nan gashi kinyi nasara meyasa  uhmmmm? 

Duk zeenat najinta amman tayi shr , gabadaya takasa furtawa doctor din daidai da kalma daya.
 ,jikinta ke rawa yayinda zuciyarta ke dokawa ,da sauri addu'a take kar Allah ya jiho deeni dakin .

Likitar tacigaba kina jina kimin shr kin kyauta kennan ?
Gashi Kinsa mijinki cikin tashi hankali  Duk da  bay san actual abinda yasa cikin ya fita ba .


Jin haka yasa zeenat durowa daga kan bed din marasa lfy tamkar ba may jin jiki ba.

 ta durkusa gaban doctor gwiwa biyubiyu tana zubda hawaye.

 ,cikin in inna da tsoro tace  dan Allah doctor kiyi hakuri ki rufamin asiri I know that I made a mistake but I promise to change   .


Doctor ta zuba mata idanu kawai.
 tare da   girgizawa zeenat kai  alamun bazata iya  abinda  take rokonta akai ba.

 ,gaskiya bazan iya  boye miki ba kin cutar da  mijiki kinsashi acikin damuwa.
 ,sanar masa kadai shi zai sa ya dauki mataki akan laifin zubda masa da ciki  da kikayi da ...

 ai tun zeenat ta bingira kasa ta sume  numfashinta ya dauke cak . Tun bataji karashen maganar likitar ba .

da sauri doctor saira.
 tashiga danna kararrawa dake manne da dakin  dan neman agajin sauran likitoci ba'a fi 5 minti ba  say Ga wasu  nurse  sun shigo dakin da hanzarisu doctor saira  tace su taimaka mata.
 suka  daura zeenat akan bed suka shiga aikin akanta' amman sam numfashinta yaki dawo daidai .
say da suka manna mata oxygen .
"    Sannan da  taimako Allah suka samu numfashinta ya dawo normal ..


Some minti back

  kuka take  tare da kamkame doctor saira  akan dan Allah karta  gayawa mijita tana kuka tana rokonta  wlh muddin yasani kashe ni  kawai zaiyi . 

Doctor tace is alright ki samu natsuwa .
zeenat tace dan Allah bazaki gaya masa ba .

,kede ki samu natsuwa tukun haka doctor ta , Zauna ta dinga advice din zeenat akan maganin data sha yana da matukar illla sosai.

 dan misalin da zaki km sha maganin  nan kmr sau biyu  to wlh mahaifarki zatayi damage ta tashi daga aiki.

dan haka ki  kula da kyau tace naji doctor inshallahu  bazan sake ba amman dan Allah ki rufamin asiri karki bari mijina yasan da zancen nan .
 Doctor tace taji badan tana da niyar  zata rufa mata asiri  ba .




Zaune yake agaban table din doctor saira Jack ,  ya zubawa doctor din idanunshi kawai.
 ya dawo tamkar wani  mutun mutumi ganin yake Tunda su sanar masa daya  rasa  abinda ke cikin zeenat wani dogun long talk dinsu  zai  km zaman saurara.
 ai Duk wani bayani dazasu sake  masa  bai da wani  amfani agurinsa ahalin yanzu.

Shi  lfyr matarsa ne kawai yanzu agabansa bawani dogon turanci ba .

 doctor saira ta xuba mishi ido itama  tana jin  tausayin man din har cikin ranta .

 tana son sanar dashi abinda matarsa Tasha har yayi dalilin rasa cikin jikinta .

amman tana fargaban halin da mata da mijin zasu shiga "dan haka tayi decide kawai tabar zance  Tunda zeenat din tace bazata km ba . Can  km wani tunani yazo mata .


Dan haka ta Kira sunanshi 'ahankali  Mr aliyu ...ya dago rikitattun idanushin yana kallonta dashi  batare da Yace mata komai ba.

  tace gaskiya matarka ita  tayi sakacin da kuka  rasa bby,nku  dan akwai maganin datasha wanda sam  bai kamata Tasha ba wanda yayi sanadin zubewar cikin amman in case of next time yakamata kasanya  ido akanta sosai .

 DEENI dake zaune ya dan  gyara zama tare da  sake zubawa doctor saira rikitattun idanunsa yana jin yadda  kirjinsa ke masa   zafi da radadin rasa bbyn shi .

 gashi km doctor din na neman ambula masa  wata gubar data fi ciwon rasa bbyn shi da yayi .

Say daya furzar da iska may zafi daga bakinsa tukun yace inda Ina son na fahimci zancenki da kyau .
Kina nufin  wife dina ta sha maganin zubar da ciki ba....


 Doctor tayi saurin girgiza masa kanta 
Tace ba haka nake nufi ba .

kasan akwai wasu magunguna da bai kamata masu ciki su yawanta shansu ba.

   ,dan wasu jininsu baida karfi ,to matarka Tasha something lay dat'  deeni ya sauke ajiyar zuciya tare da mikewa tsaye yayi wa  doctor godiya, ranshi a dagule ya bar office din doctor saira yana tunanin wani irin magani zeenat Tasha haka  .

Har ya shigo dakin 
 da aka kwantar da zeenat din tunani yake akan wani irin magani Tasha har tajayo masa mumunar asara . kwance ya sameta idanunta sunyi jajur dasu alamun taci kuka .

 'ahankali  ya maida kofar dakin ya rufe tare da  janyo kujera ya zauna agabanta tare da zuba mata rikitattun idanunsa kawai yana kallonta dasu.
" atsorace itama take kallonsa yayinda zuciyarta ke tsalle  tamkar zata fasa kirjinta shi kansa yana kallon yadda kirjinta ke sama da kasa ,muryasa a sarke yace zeenat wani irin magani kika sha ?
Likita tace kinsha magani say day bata tabbatar min actual maganin dakika sha ba .

Ba Muryata kadai   ke  rawa ba har gangar jikinta kirma yake tsabar tsoron irin kallon dayake jefo mata .
 cikin in..inna tace daman sanda cikina ke min ciwo ne , shine nasha nasha felajin sai km hawaye sharrrrrrrrr.
Ya ciza lip's dinshi da karfi sannan yace okey Allah ya bamu wasu amman na rokeki ,karki sake min irin wannan gangancin ,da sauri Ta girgiza masa kai.

Byn kwanaki uku akayi discharge din zeenat daga hospital  ta warke sumul tamkar batayi ciwo da wani laulayina ba .
hankalinta ya sake kwantawa ta dawo daidai tamkar da , ganin deeni bai san komai game da zubewar cikinta .

Musamman taje har hospital ta dinga godewa doctor saira akan yadda ta rufa mata asiri da har mijinta bai sani ba  .

 Doctor saira tace karta damu amman please karki  km aikata laifi irin haka .
Naji doctor  na gode .

Dazata dawo gida ne ta biya gidansu sumy ta fesa mata labarin halin datashiga ,sumy ta rudy tana addu'ar Allah ya taimake su ,dan da doctor din ta sanar dashi wlh nasan sojan mijin nake say yasa bindigarsa yatashemu aiki ,suka sa dariya gabadaya.


Tsaye yake a gaban dress mirrow din dakinsa  sanye da bathrobe hannushi rike da karamin white towel yana goge sumar kansa da sansar  jikinsa, da alamun fitowar shi daga wanka kennan.
 ahankali ya dauki bodylation ya shafe jikinshi da shi tare da saka uniform dinshi sannan ya feshe ilahirin jikinsa da turaruka masu sanyi kamshi kokarin daukar briefcase dinsa yake .
Say gashi tashigo dakin  tana rausaya sanye da wata haddadiyar doguwar riga har kasa da'aka mata kwalliya da stone  pink.

Rigar tayi matuka yin mata  kyau ,abinka ga farar macce  sai kamshi take zubawa .

 inata sauri naxo nashiryaka  shine kashirya ko?

 Murmushi yayi har dimple dinsa yana lotsawa" tasa hannuta daidai  ramin dimple dinsa Ina son abin nan" yana kara maka kyau sosai "yace Allah ko tare janyota jikinsa yana kissing din wuyanta " sorry dear sauri nake ana jirana a office ne shiyasa  .

ok muje kayi breakfast tasoma kokarin barin jikinsa ta dauki briefcase.

 ahankali yake saukowa daga upstairs din wanda  tuni kamshin turarensa ya mamaye ilahirin parlour .
rahma dake kokarin kammalawa da aikinta ta dago idanuwa tana qare masa kallo tsab . 

Ko kallon inda take baiyi ba ballanantana yasan mutun ce ko aljana . dan gabadaya yasoma tsanar irin kallon da yarinyar ke masa .

cikin takunsa na isa da takama  yakarasa saukowa  wayarshi ya Ciro ya manna akunne cikin natsuwa yake wayar har yakaraso deaning area yana zama ya hade rai  yana jan tsaki.

 zeenat ta dago 'ahankali tana dubansa jin tsakin dayayi .

 my hrt  lfy  zeenat ta tmbye shi  tsaki ya sake ja ,yana dubanta wai ta Yaya bazaki dinga gayawa masu aikin nan naki  su dinga yin aikin akan lokaci " ba  say  zanfita na nadinga cin karo da fuskokinsu ba .
 

Tace ok kayi hakuri aza,a gyara inshallahu , better abinda ya iya cewa kennan .

bawani abincin kirki yace ba byn coffee dayasha  yamike cikin sauri yana kissing din goshinta .
 sakamakon kiran da,ake ta masa daga office .

 Har bakin compound din gidansu ta rakashi hannuta rike da jakarsa ta bude masa murfin mota yashiga .

Tana tsaye har ya fice tana daga masa hannu .Bai mayar mata sbd yadda yake jin ranshi a dagule .


Ahankali ta juyo tashiga gidan ta iske Morris na kwashe kayan breakfast akan deaning yayinda  rahma ke zaune a parlour tana kallo .

Wani irin frigitance tsawa ta dagawa rahma wanda yasa cikin rahma ya kada......ta dirkusgewa akasa waje daya jikinta na rawa  .


 Zeenat tace ke dan ubanki bakya tashi yin aikinki na munafurci  say kinga lokacin da mijina Zay sauko ko?

Jikin rahma na rawa tace  Allah madam ba haka bane .

zeenat ta sake daka mata tsawa rufen ba iska banza  kawai. nima fa kwanan nan nafara notice yadda kike bimin miji da kallo amman bari na sake kamaki kina karewa mijina kallo ubanki ,anki stupid  .

 Wai Aiki yakawo ,gidana ko kallan min miji kikezo yi?
 , rahma da jikinta Duk ya dauki rawa tace kiyi hakuri madam aiki nazo .

ok  nakara ganin wannan shegiyar bakar fuskar taki akan  mijina yana saukowa .
,uhm tayi kyacci  ,sannan ta juyo kan moris ke km  gorilla may kama maseefa , haka ake girki  agidan ubanki, kullun abinci daga Magi yayi yawa sai yayi kadan.
 idan Kinsa baki iya girki ba ki kama gabanki kafin nayi gaba dake .

dukkansu suka durkusa kasa suna bata hakuri ko kallonsu batayi ba ,ta haye sama tana juya musu  mazaune .



Tana shiga dakinta ta dauko wayarta tashiga neman  number nurse titi byn ta dauka suka gaisa tace dan Allah magani nake so wanda ,zan dinga sha sbd karna  sake daukar  ciki .

Nurse titi tace ok kiban lokaci zanyi miki  text dinsa yanzu .

Byn mintina kmr  goma da ajiye wayarta  taji sakon  shigowar message ta Mike da sauri Ta dauka ta duba.

Ga abinda tagani a rubuce.

  postornu 2 ,
You will take 2 after making sex or before 


Ahankali ta saki numfashi dan gamsuwa da abinda nurse titi ta turo mara .

AHankali zeenat Mike tsaye  tare da sake nufar  dwanstars tun bata karaso kasa  ba take aikin  kwallawa moris Kira ...moris moris 

,da sauri moris  Ta fito daga dakinsu ta tsaya tamkar soja  tana Jiran karasowa madam dinta 'ahankali zeenat ta Mikowa moris white pepper da kudi ,

Tace ungo kiyi sauri kije ubolande ki tsiyo min wannan maganin .

Kiyi sauri kije ki dawo  karki bata min lokaci km rike min magani da kyau .

 moris takarba  jikinta na rawa tabar gidan .




Bayan wani lokaci



Haka rayuwa tayi ta tafiya har lokacin suka ja sosai ...


zeenat bata km samun ciki ba sanadiyar maganin datake zubawa mahaifarta . 
Wanda shi oga deeni kwata kwata bai san da haka  ba . 

 Say ma wani irin kulawa da so  dayake bawa  zeenat din na musamman  sbd yadda yake samun hadin kanta dan tana kokarin wajen  tumama masa bed shi da kyau  .

DEENI irin mazan nan da ko Yaya suka ci abinci .
The  next thing is sex kwata baya gajiya kullum cikin ruwa suke sai day idan yayi tafiya amman muddin yana gida zeenat ce abincinsa ,ita km tana aikin turawa kanta maganin rashin daukar ciki .


Wani lokacin ma idan maganin yakare a hannunta tashiga wasan boya dashi kennan da karyar ciwo iri iri ,har sai ta nemo maganin tukun ake cigaba da gashi .
 haka ce ta dinga kasancewa   har zuwa yanzu da suke cikin shekararsu  ta biyar da auri.

 yayinda shemah keda yara biyu ga cikin na uku ajikinta.

,haka  Maryam da rukky Duk suna  sun yi  aurensu tuni har da arkin bbyn .sumy km ana can university a BUK ana karatu .


Bbu jike jiken da Ummi bata kawowa zeenat  wanda itama kawayenta ke  bata takawo zeenat din.
Ahalin yanzu  burin kowa  bai wuce yaga zeenat ta haihu ba .sbd tausayinta da family din keyi .

Cikin haka  deeni ya km samun karin girman daga captain zuwa major lokacin idan kaga zeenat ta sake gogewa da wayewa tazama cikakkiyar madam  .

 kallo daya zaka mata kasan akwai jin dadi  acikin rayuwar aurenta.




Uhmmmm  99 days is for the thief  one day is for the  owner ooooooo  ,I real pity you zeenat 😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭




MMN SUDAIS CE
[5/14, 9:08 PM] ‪+234 810 359 0922‬: 💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO



Page 45


Sannu AHankali abubuwa suka dinga zuwa  suna wucewa ciki har da kara Gini da deeni yasa akayi masa  .

 ,domin  fill ya dinba may yawa ta bayan ainihin gidansa" ya canza yanayin tsarin gidan gabadaya dan yanzu masu aiki sun koma ta baya " Sai dai Yar kofar da'aka bude wace zata dinga sadasu da parlour gidan .
,da doguwar hanya wanda kai tsaye zata kai muntu back yard din gidan .

 yayinda DEENI ke sake ji da zeenat dinsa  da nuna mata kulawa.

 say  day kusan kullum  say yayi mata zance haihuwa.
Koyace shifa    , yaji shr yayi yawa koyace shifa baiga alamun ta damu da rashin haihuwar su  har yanzu ba.
 yakama  ace kina zance zuwa  asibiti Amman say ki share kibarni ni kadai ko.
 Sai dai ta wayance tana dariya  . 


Ko yanzu ma dasuke zaune a parlour,su na sama  rungume da juna ,yana shashafa mata jiki da taba Duk inda hannushi yakai ajikinta.
 zance dayake  mata kennan . zeenat nifa  nagaji da shirun haka  har yanzu bbu wani labari.
  Tayi murmushi tana sake shigewa jikinsa nima wlh my hrt a matse nake danaga na sake samu bby , amman karkadumu mu cigaba da addu'a kawai  very soon zan baka bby zamu .

Allah yabamu masu albarka  . tace Ameen 
 tacigaba  my hrt kana son bby dayawa dole zeenat naso ya'ya ,

Dan ya'ya abin sone da alfagari .
Tace ni km kaga  zan iya zama rayuwata dakai ko babu  haihuwa .


Yayi shr  yacibaga da  shashafata cikin wani irin salo na rikitarwa .

Bakinsa Ya kai wuyanta yana sumbata koina ajikinta kafin yakai bakinsa kan lip's dinta suka soma tsotsar bakin juna tamkar wasu zakunan da suka kwaso yunwa tare da fidda numfashi sama sama .


Mikar daita  tsaye yayi  suka nufi dakinsa .
Suna shiga ya janyota suka zube kan bed ya  rungumeta tsam ajikinsa AHankali suka soma romancing din juna .


Yau kam deeni bbu yadda baiyi da zeenat akan tayi mishi stly  gurin sex ba  amman sam tace ita tsoro take ji bazata iya yin wani stly ba .

shi km ya rantse  yau Sai tayi mishi goho yaci ta baya ,Duk yadda taso ta hanashi deeni yaki yarda  dan haka yacigaba da romancing dinta tare da kamo dukiyar fulaninta yana murawa AHankali  ya juyar daita  ya zira jijiyarsa ciki yasoma mata service .
 " wani irin  ihu dadi  tasoma yayinda shi km yacigaba da zira mata  hannushi duka nakan  kirjinta "yana  aikin murzawa .
 ,say daya gaji dan kanshi sannan yabar ta ya kwanta gefe yana fidda numfashi .

Kwanciyatayi itama numfashi take fiddawa sama sama ,dan har wani zafi zafi ta dinga ji akasanta  .

Tayi sheme shame  tare da ware kafafuwanta daidai  tsaitin fanka ,wai ko zata daina jin radadin zafi .


Cikin haka bacci yayi gaba da madam zeenat batare da Tasha magani ba ,km har washegari ranar  bata tuno ba .
Say gurin la'asar ta tuna batasha magani ba .

Da gudun bala'i ta kwasa tayi samanta.
 ta bude tsakankanin side bed dinta inda take boye table din  taga wayam  sama ko kasa bata Gani ba.
, hankalinta yayi mugun tashi ta sauko da bedside din gabadaya ta ajiye a gefe  amman kwata kwata bataga alamun kwalin maganin   ba ballanantana tablet.  

 .tace wayyo Allahna nashiga uku ni zeenat  Ina na ajiye maganin nan  yanzu.
 , AHankali tasoma yamutsa dakin tana duba koina  harda  inda batayi tunanin ta ajiye maganin a gurin ba, Sai da ta duba .

 ,cikin haka oga deeni yashigo dakin ya tsaya kawai yana kallon yadda yaga Duk ta birketa dakin ne yashiga bashi mamaki .


Ya dade tsaye yana dubanta batare da sani ba ,sannan yayi gyaran murya afrigice ta juyo tana  kallo bakin kofa .

,tana ganin shi taji gabanta ya daki uku uku yanke ya fadi rassssss.take tasha jinin jikinta dan ganin yadda yake kallonta  .


AHankali ta Mike tsaye jikinta duk a sanyaye tayi masa sannu da zuwa batare da tayi yunkurin mikewa daga inda take ba .
 da ka shima  ya  amsa mata  lfy.

 yana ga Duk kin  yamutsa dakin haka?

 tayi murmushi karfin hali tukun tace wlh wani abuna  nake nema .

make nan ya sake jiho mata wata tmby ?


Cikin in...inna tace uhmmmm ...abin sarkata nake nema tun dazu .
 ya girgiza kai kawai  ya juya ya nufi dakin .


Wanka yayi ya dawo parlour ya zauna sanye da jallabiya ruwan coffee.
 tare da daukar remut ya canza Chennal zuwa saudi .
AHankali   ya dauki wayarsa yakira Umminsa byn ta dauka suka gaisa ta tmbyi zeenat yace tana lfy  sannan suka sha hirarsu.
  byn ya ajiye wayar yacigaba da kallon sa har say dayaji  an fara  Kira sallah,a masallacin dake cikin gidan ,sannan  ya Mike yayi alwala.

 ,da zai fita masallaci ma Sai  daya sake komawa dakin zeenat din ya isketa kmr yadda yabarta   a har gitse ,ya tabe baki yace shi ya wuce masallaci . 



Yana fita ko minti biyar baiyi ba .
 ta sauko parlour kasa da sauri .a frigice tasoma kiran  sunan moris tace maza ga kudi kije  siyo mata magani ,  ,wanda zuwa yanzu moris Ta kware wajen haddace sunan maganin da madam dinta ke aikanta .
Har moris Ta bude kofar fita zeenat Ta kirata ,ta tsaya tare da juyowa ,karki kuskura kiyi sakaci da magani keep it very wel for ,ko zeenat din bata fama mata ba ,tasan maganin datake siyowa  mata bana alkhari bane.

 , consider datayi idan taje wanjen siya ,a boye ake siyar mata dashi .

Zeenat na gama bawa moris  sakon takoma samanta   tana tunanin inda tablet dinta yayi .


Byn kmr minti goma shabiyar da fitar  moris sai gata  Ta dawo sakamakon securities da suka hanata fita  .

Tana dawo da sauri .

 deeni ya tsaidaita daman km ya fitarta . Shiyasa yakira number securities kar su barta ta fita . Yana tmbyrta yaga tasoma masa kame kame ya shareta ya wuce,


Tana dawowa tarasa yadda zata sanarwa  madam dinta  gashi zeenat sam bata yarda moris tana hawa samanta sama .

say rahma ,daitama aikinta kadai ke kaita km da zarar tagama take saukowa .


Moris Ta dade da dawo batare da sanin zeenat din ba .

Can zeenat Ta  duba agogo wayar  taga har idar da sallah magariba anakan kiran isha'i ta Mike da hanzari tashiga bathroom dan wani irin fitsarin data ya kwanta mata a mara.
 
,tana fitowa ta zari  hijab tana kokarin sawa   taji an bude kofa  tayi sauri ta zira hijab din atsorace sukayi ido hudu  da deeni dake  tsaye gabanta.
 Kirjinta taji  yayi  wani irin mugun bugawa.
  ta dauke idanunshi  akansa .

 tasoma kokarin dawo da natsuwarta ,amman gabadaya takasa yukurin fita kmr yadda take so .

AHankali ya rungume hannayeshi duka saman   akirjinsa  tare da zuba mata rikitattun idanushin  ya jingina da jikin kofar tare da  harde kafafunsa yana mata wani irin kallo yana murmushin .
  ,wanda yasa zuciyar zeenat ke gaf da tsayawa tsabar rudanin datake ciki   . 

Da kyar tasamu ta gyara tsayuwarta dan gabadaya kafafunta suma nauyi . kokarin zagayeshi take Ta fita  tana isa bakin kofar ya sauke kafafunsa ya gyara tsatuwarsa sosai  a bakin kofar .
 a wanyace tace my hrt ,zan wuce zanje na hado maka coffee har tasa kai zatafita ya dawo daita tare da cewa karki  damu, yasa hannu ya maida kofar ya rufe ,


Ya cillata a kan bed ya zire jallabiyar jikinsa yayi flinging daita ta Mike da sauri zata Mike ya  maidaita yasoma romancing dinta cikin zafi zafi deeni bai sarara mata ba koda yaji tana gunjin  kuka bai barta ba  Sai dayaga   bata motsi sosai sannan ya barta ya kwanta agefe . 


AHankali byn yagama hutawa ya Mike yashiga bayinta yayi wanka ya koma dakinsa shima bawai ni jima yayi  ba ya sake ficewa .
 da gajeren wando irin na sojoji da farar Riga yabar gidan gabadaya tare kulle aininhi get din gidansa haka kawai yaji bai yarda zeenat din da moris ba  Duk da moris taki fitowa ta sanar dashi ainihin abinda zeenat din Ta aiketa Sai wani  kame kame.




Zuciyar zeenat  gabadaya a cunkushe take.
 yau   tsawon kwana uku kennan batasha maganinta ba .
 
 km  Ta aiki moris siyo mata  tablet dinta .
taje har  inda tasaba  siyo mata batasamu ba.

 km  duk inda yakamata tasamu din taje amman sam   bbu .

dan haka hankali zeenat ya sake tashi fiyye da  tunanin may  karatun .

Gashi  babu wani  hutu daga oga deeni   kullum Sai yayi sex daita kafin yayi bacci .



Two weeks later 


MMN SUDAIS CE
[5/14, 9:09 PM] ‪+234 810 359 0922‬: 💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO



Page 46



Two weeks later


Gabadaya jikin zeenat yasoma samun 
Canjin yanayi.
 , Wani irinjin kasala kasala bacci bacci take ji ajikinta koda taci abinci ko wani abu zataji ya tsaya mata a kirji .


Cikin bacci zeenat Taji kmr wani abu ya tsaya mata a kirjinta kmr yadda  tasaba dan haka tasa hannuta daidai tsaitin inda take jin abun ya tsaya mata Ta dan soma  shashafawa sai taji abin yayi kasa .
Sake ,juye tayi tashige cikin kirjin deeni   sbd tafi jin  jin dadin baccinta ajikinsa, 

AHankali Deeni ya lalubo wayar dake gefen dayake ya duba time yaga uku ta wuce da wasu en mintina dan haka ya zare zeenat daga jikinsa   ya kwantar daita sannan ya  Mike ya sauko  daga kan bed daga shi  sai boxer iya cinyarsa da white single ya dan tsaya yana kallon yanayinta sannan ya wuce dakinsa.

 wanka yayi da alwala yazo ya tadda ikimar sallah" byn ya idar bai tashi daga gurin ba .
Yana zaune   yana ta addu'oinsa dayasa ba  har sanda ya jiyo kiran sallah a masallaci dake cikin estate din tukun ya Mike ya sake shiga bayi .


Kiran sallar asuba ne ya tada zeenat da kyar Ta Mike tayi bayinta wankan tsarki tayo tare da alwala .

Byn Ta idar da sallah Ta shafe jikinta da lotion pure white gold kmr yadda tasaba  kullum tare da feshe ilahirin jikinta da turaruka masu matukar sanyi  da dadi kamshi .

Duk wannan shirin da take tana yine  tana shiga bayi zubda miyo dake taruwa a bakinta wanda tarasa na Mene dan ita sam bata kawowa ranta komai a game da miyon datake zubarwa"  ganin tun last week taje Ta nemo tablet dinta da kanta ,km tana amfani dashi yadda aka sheda mata tun farko  .



Kwanciya tayi tare da runtse idanunta tana tunanin ko yaushe deeni yabar dakin 

 kirjinta taji ya sarke mata guri daya can km tasoma ganin juwa juwa cikin ya kulle .
Jin haka yasa  ,tayi tunanin kodan jiya bata ci abinci bane" ga oga deeni  km ya kwana aikin service.
 yasa Ta Mike ta dauki wayarta ta Kira number moris dan yanzu tana da waya a hannuta  tace ta dafo mata indomi da tea amman tabari indomi tayi yaji sosai aciki  tabawa rahma takawo mata .


Hakance takasance dan ko cikakken minti ashirin ba'ayi ba Sai ga rahma Tayi nouking kofar zeenat .

Tabada izinin shigowa.
Rahma ta karaso har cikin dakin tana gaisheta tare da  ajiye plate din indomi ,akan bedside ta juya tabar dakin bata jima da fita ba ta dawo da cup din tea.


AHankali   ta Mike  ta ,dauki plate din  tasoma ci abinci say dataga plate din tas.
Sannan  ta daura da tea mai kwari.
".   ta dan jingina bayan da jikin gadonta , aiko kmr cikinta jira yake taci abinci ,yasoma yamusawa yana juyawa  da gudu tayi bayi tashiga  amayar  duk abincin data ci . 



 Cikin haka deeni yashigo dakin da shrinsa na fita aiki.
 tsaye yake yana binta  da kallon mamaki ,yaushe km haka ta fara faruwa ya tmbyi kansa .
 AHankali ya maida kofar dakin  Ya rufe yakarasa shigowa dakin sosai yana  kallonta . Waje yasamu ya zauna yanacigaba da dubanta 
Har sanda yaga tana kokarin fitowa daga bayi.  


Jikinta a mace ta rarrafo jikin gado  ta jigina bayanta tana cigaba da maida numfashi  .

Mikewa yayi  ya dawo  kusa daita yana kallonta  ya dafata zai  yi magana 
 Yaga Ta Mike da sauri tayi bayi ta tsugunna tana  kararo amai kmr zata sume .
 take jikinsa yabashi abinda kedamun ba mamaki Allah ya amsa addu'ar kwallonsa yashiga ya sake shiga raga  .

  ya Mike ya rikota yana mata sannu ya kwantar daita ya akan bed ya lullubeta da bargo jikinta sai rawa yake .


A ranshi yace abu fa ya km  samu  manya iyayen son jiki da raki ,


Yayinda ita  km take  maganar zuci kardai ciki gareta alhalin bata shiryawa hakan ba.
    " wani mora rayuwarta tayi da har zata km daukar wani ciki yanzu ta  rufe idanunta tare da jan tsaki a ranta  . Yaka barinta har sai dayaga alamun bacci yasoma daukarta 


Kallonta yacigaba dayi tana bacci wanda dagani bana jin dadi bane dan  Sai juyi take tana girgiza kai . Ya cire wayar yana neman doctor saira amman sam takishiga.

ya Mike ya fice daga dakin mukulin motarsa ya dauka ya sauko parlour kasa yacikaro da rahma tana gyran parlour suna hada ido ya sakar mata harara ya fice .

A sukwane tabi bayansa da kallo tana mugun    son kallon ogan madam dinsu.
 yana da tsarin jiki may kya 
,ita dai tana matukar son shi  da aure dazai aureta  Amman tasan bazata taba samun miji kmr sa ba.
,gashi sai bata kudinta take abanza ko kallon arziki bata samu daga gurinsa .
AHankali ta saki ajiyar zuciya . Tarasa yadda  zatayi tasamu ya Amince datai .
Ko   shanawa sudingayi  , kyauta ma sai  ta mallaka masa jikinta batare ko sisinsa ba  .

tayi kwafa ta shige dakinsu tana may  ayyanawa ranta muddin tana cikin  gidan sai takashewa kanta kishirruwansa dake makale da makoshinta .



Yashiga motarsa sai asibiti doctor saira dan yanata neman layinta bata dauka ba  bai damu da masu gaishe shi dashi ba ya haura samanta kawai ya wuce office dinta  ya same zaune tana rubuce rubuce   idannuta manne da medical glass tana ganinsa ta sakar masa fuska suka gaisa fine  ta nuna masa gurin zama tana tmbyrsa madam .
 
Ya danyi murmushin ai saboda ita ma naxo  dan gabadaya bangane kanta ba yau .

Meyasa meta inji cewar doctor  ?

Nidai nashigo dakin naga  ,sai amai take kwarawa ni dai je ki duba minta dan Allah .
Dan  nasa bai wuce ciki gareta ba .
Amman ki riko kayan aiki.

 , Tayi murmushi ta Mike tashiga hada  kayan aiki ta dauki ruwan allura guda daya ta rufe glass din da  magunguna da abin awo .

Tace suna  iya wucewa suka fito ta kulle office dinta .
 suka sauko kasa zuwa inda yayi parking din motarsa yana shiga gidan ya iske  rahma kwance a parlour tana kallo TV ranshi yayi mugun bacci da  iskanci datake masa acikin gida  azubure ta Mike ta zauna tana kallonsa Dan  taji dadin  ganinta da yayi cikin mini siket.
 duk   da  bata yi tunani.  dawowar sa ba .
ta dauka ya wuce aiki kennan  . 

 Ta tabisa  da kallo .
 Har ya haura sama shida doctor saira . Sannan ta sauke idanunta akansa .

tana maganar zuci lallai yakamata ta sake Mikewa tsaye  akan yadda take  dan gaskiya muradin kasancewa tare dashi . 

Tayi murmushin mugunta ta shige dakinsu ,ta iske moris kwance tana karatun Bible ,dan ita Tunda madam tanuna  bata son zaman su a parlour ta kiyaye kanta.
 iya karta kitchen da deaning wanda duk akwai kofar shiga ta cikin  dakinsu  dazata kaita  kai tsaye .



Fitowarta kennan daga bayi byn tagama kwarara amai suka shigo dakin  sai rawar sanyi take ganinsa da doctor saira yayi matukar bata mamaki ,ta zauna tana gaida likitar ,,ta amsa tana mata yajiki tare da mata wasu en  tambayoyi .

ta Mika mata wata  Yar karamar kwallaba tayo fitsari aciki .




Byn kmr minti goma doctor saira tagama yiwa zeenat  test tagane tana da shigar ciki wanda batasan iya kwanakinsa ba , ta Ciro  drip tayi alura aciki ta daura mata ,tare da magani .Ta nuna masa yadda zai cire mata idan ruwan yakare .


Taso kwarai ta kebe da ,, zeenat din dan ta bata shawara akan cikin amman hakan bata samu ba dan   deeni na gurin .
dan haka ta Mike tare da yi musu sallama.

 sai day kmr wannce karo ta tabbatar masa akan yasa ido sosai akanta .yace  Inshallahu zankiyaye .
Yaje ya sauke doctor saira yana mata godiya sannan ya wuce gurin aiki. Wunin ranar akwance tayi byn deeni ya dawo gida dubata ya cire mata drip sannan ya km barin gidan.


Washegari ma daya shigo dakin  hannushi rike da cup din tea  kwance ya isketa dakin duk a hargitse ,  kallon tea kawai tayi taji zuciyarta natashi tun bai kai bakinta ba .

Ta Mike da  sauri sai cikin  bayi tashiga kwara  amai ,ya iso kusa daita yana mata sannu sai data gama sannan ya gyara mata jiki ya maidota cikin daki.


AHankali Ta kamo hannushi ta daura a saman cikinta ,tana hawaye tace dan Allah my hrt katausayamin kasa acire min cikin nan kabari muyi zaman haka Tunda muna son juna  wlh ni zan iya zama da kai ko bbu ya'ya .

Yayi shr kawai yana kallonta da mamakin abinda tace yayinda zuciyarsa ke tafasa yana ji tamkar ya shakota yamakata da bango ta mutu kowa ya huta.

 ,wani irin kallon ta haukace yake binta dashi tare dayin  nazarinta .

Ganin yayi shr baice mata komai ba .
 sai ta dauka ko shawara yake da zuciyarsa .
dan haka tasoma kokarin sake rokonsa .

Wani irin harara ya watsa mata wlh idan kika sake gayamin wannan bazanr magana say na kasheki yanzu . 

Take Tayi shr tana kallonsa zuciyarta na ta fasa .
ita ko tafi iskanci zai Gani kuwa ,ta juya tayi kwanciyarta tana mayar da numfashi .

 A zafafe Ya Mike tsaye sosai yana dubanta zuciyarsa iya wuya.

 dama ke muguwace km munafuka may fuska biyu ki dinga nuna min tamkar ma kin fini son haihuwa  a she abin ba har zuciyarki yake ba ,dan Allah na rokeki  karki canza niyarki ta zubda  cikin nan .

Yana gama fadar haka yabar dakin tare bugo kofar dakin da karfi ,a ranta tace mai zuciyar wahala bbu wani haihuwa da zanyi da kuriciyata na zauna na lalata rayuwata wlh  ba zai wuyo ba .

 

Yana sauko yaci karo da rahma zata hauwa sama wani iri mari ya dauketa dashi tare kwallo daita tasoma mulmula har ta gangara kasa .meyasa daga gashi yana saukowa bata bari ya bar step din ba ta hawo.

 AHankali yacigaba da sauko ko kallon inda take baiyi baiyi ba ya fice daga gidan . 

Rahma ta karkabe jikinta ta mike tsaye tana dingisa kafa sannan ta sake yin hanyar step Dan dama gyaran sama zataje yi .




Da wuri Zeenat   bacci sakamakon drip din da doctor saira tasa mata.  Bata farka ba Sai wajen  shabiyu  na dare yana kwance a gefenta shima amai ne yata daita ya cire mata ruwan dake hannuta ganin a gigice ta farka tana neman sauka ya rakata har bayi tashiga kwara amai ,gashi bbu komai acikinta komai taci baya zama acikinta sai ya dawo .
Ya zuba mata ruwa akanta ya fito daita daga ita har shi bbu wanda ya runtsa  ranar" basuyi baccin kirki ba jikinta ya sake daukar zafi , 

Tun yana jin zafi da ciwon kalmar zubda da cikin data furta masa har yazo ya daina ji ,ganin yadda take shan wahalar cikin  sai lokacin yayi tunanin Killa kodan wahalar da cikin ke bata ne yasa  ,tace acire mata  .



Wasa wasa cikin zeenat cikin  yashiga wata uku har sunje asibiti , doctor tace sabon wata zata fara zuwa awo.

  Sosai deeni ke kula daita yana bata extra love   haka Ummi amman ita duk wannan gatan datake samu  besa taso wannan cikin ba gabadaya a wurinta takura ce wannan kaddareran ciki a gurinta kmr yadda take cewa .

Shi kuwa Deeni bbu ruwanshi harkar gabanshi kawai yake yana bawa zeenat kulawa da abinda ke cikinta .

 Tundaga sanda tayi furucin zubda ciki taga yadda yayi bata sake yi masa makamanciyar maganar ba tare suke lalacewa gurin cikin .hakan ya sake bawa deeni kwarin gwiwa kula daita da mancewa da wani maganar zubda ciki datayi.

 Da daddare deeni zaune a parlour ,n shi na sama yayinda  zeenat ke  kwance ajikinsa a shwabe tace  my hrt nifa Ina son cin danwake ,.

Ya sauke ajiyar zuciya yana kallonta tare da  duban agogon wayarsa , karfe goma saura yagani yace bby kalli time fa a Ina zan samoki shi wannan abin da kike son ci?
 ta bata rai tashiga kokarin tashi daga jikinsa ta Mike zata wuce yayi saurin dawo daita dan  Tunda yasan yadda cikin ke bata wahala yake gudun bacin ranta .

Zaunar daita yayi akan cinyarsa yasoma neman layin umminsa ,say gaban Ummi ya fadi lokacin dataga kiran Deeni  kafin ta dau wayar ma addu'ar ta dinga sannan ta dauka tace  deeni lfy ?

Lfy first lov wlh wai zeenat ke son cin wani abu dan..me ake ce masa , ya dan juyo yana fuskantarta zeenat din  ,Mene sunan abin ta sake  fada masa

 ,yace yauwa wai danwake ,shine nace bari nakira ki ko zamu samu yanzu .

Ummi ta sauke ajiyar zuciya tace ba matsala kazo nan da 30 minti sannan ya kashe yana rungumota jikinsa kinga gud grammar tace azo akarba ta manne masa tana gogga masa kirjinta a fuskarsa .


Allah sarki Ummi da kanta tashiga kitchen tayiwa zeenat dan wanke .

Minti 30 daidai agidan Ummi tayiwa deeni yashigo da sallamarsa ya karba coola yayi wa ummi sallama ya wuce dan kwata kwata yanzu baya son yin nisa da zeenat din .


Yana kaimata hannu baka hannu kwarya ta dinga tura danwake tamkar mahaukaciya ya zuba mata ido kawai yana kallonta dan yasan da wuya agama cin danwaken lfy ,.

Aiko tana gama ci tayi hanyar  bayi da gudu sai da ta amayar da danwanke kaf  tukun ta zube tana nishi .
Haka ya taso ya wanke mata baki yaja zuwa dakinsa ya kwantar daita shima ya ,zagayo ya kwanta abayanta tare da rungumeta tsam .


Zeenat tarasa yadda zatayi da cikin jikinta dake damunta dan haka ta yanke shawarar kiran doctor titi byn ta dauka sukayi magana tayi hanging din kiran ta Kira sumy  .

Hello sumy zeenat ya"akayi ne kwana biyu?

 lfy inji zeenat  kina gida sumy tace eh Ina   gida  ok Ina nan zuwa yanzu lfy dai ko ?
ke dai ki bari sai nazo zakiji komai .


Tana zuwa gidan sumy ta kwanta akan kujera tana maida numfashi  sumy tace dazun ban  naga zanceki a zuciyata .
sai km naga kiranki.

 ya,akayi ne kawas da kyar zeenat Ta Mike taje ta zubda miyon bakinta ,ta dawo sumy tace A'a karde kin km harbuwa.

Kedai bari kawai sumy bazan iya jura daukar ciki irin nawa ba wlh "gyara na mutu Banda dan kaina da wannan  bakar wahalar .

sumy ta harareta ,kefa wawiyace kin zubar da cikin farko kinsha da kyar shine yanzu zaki km kwaso jiki to mekeke nufi .


Zeenat  tace taimako zaki min kmr na wannce karan nakira number nurse titi ashe ma  bata garin gabadaya.

Sumy tace eh Ai sunbar garin gabadaya da mijinta amman ita takan zo jifa jifa .
  amman  gaskiya cikin na baki wahala kalli yadda kika dawo .

zeenat tace eh shiyasa ma nazo gurinki  dan Allah sumy ki taimakmin ki kaini wani guri  inda za'a cire min cikin na .

A tsorace sumy ke dubanta zeenat sannan tace  uhmmmm wlh bbu ruwana km bbu wani guri da zan kaiki .
     ' nifa na tsorata da wancan lokacin  da kika bani  labarin irin wuyar da kike kinsha  .
Nasan duk randa Asirinki ya  tuno nima say kin sani a cikin maseefa .

 Zeenat Ta dawo kasa kusa da sumy ta zauna  Wlh bbu wani maseefar dazansaki ciki " abinda bbu may sani daga sai ke . Ko wancan Wana gayawa .

Sumy tayi waje da ido tana kallonta da mamaki  wai zeenat kina da hankali kuwa  ?
Zeenat Ta jinginar da kanta jikin kujera hawaye ya cika mata ido .

sumy tace shikennan  kiyi shr kibar kuka ni tausayi kike ba ,  kiyi hakuri ko daya ki samu tunda kinyi  kusan five years da aure  yanzu duniyar nan fa bamu da tabbas dinta . 
zeenat Ta zubawa sumy ido tana kuka tace dan Allah sumy kitaimaka.

Uhmmmm fa bazan sa hannuna ba  acikin zubar da cikin nan .
wancan danayi daga baya  say da nadama tashigeni .

 bazan iya da tashin hankali mijikin ba wlh ,gyara ki hakura , kuje ki nema kanki  zeenat ta Mike tsaye tace bazan  wlh Kinsa Allah sai na zubar da cikin nan .

Sumy ta daga kafadarta alamun Ina ruwanta kije ki zubar cikina ko naki 

Km dan Allah na rokeki karki kara zuwa mana gidan muddin Kinsa ba abin arziki bane ,zai kawoki haka kurum kijawo min  maseefar wannan friaunar mijin naki .

haka Zeenat suka rabuwar baram baram da aminyarta .
Ta dawo gida tana saka da warwara . 


Washegari  kai  tsaye  Zeenat ta dauki drop din   taxi tace yakaita duk wani asibiti  daya sani

 yace ok may taxi ya   dauketa  sai asibiti promise  waje yasamu yayi parking din  taxi din.
 ya Dan  juyo tare da   madam we ha'v  rich there.
 tace ok ta fito tana karewa hospital din kallo sannan  ta bude pursue dinta  ta Ciro kudi ta mikawa may taxi batare da tsaya jin ko nawa yakawota ba .

 takara cikin asibitin gabanta na faduwa da addu'ar ta shiga asibitin.

 babba ne sosai ta karasa reception ta zauna ganin peticent dayawa zaune suna Jira  AHankali Ta dinga karewa  reception din kallo ta kusan awa daya  zaune ba'a zo kanta ba.

 Duk tagaji  kwanciya kawai take son yi ga amai dake tasoma mata taji tamkar ta rusa ihu a gurin  dan azabar da take ji.ta kife kanta a cinyoyinta ,ita kadai tasan azabar datake sha .
Can   say ga wata nurse tazo ta dafa kafadarta zeenat ta dago da sauri tana kallon nurse din nurse tace ur card number madam zeenat nason magana sai dai yawu yacika mata baki ganin haka yasa nurse din ta nuna mata  toilet din dake kusa da reception . 

Byn Taje ta zubda miyon ta  dawo still  nurse na gurin tana jiranta tace ur card number madam  zeenat tace  I don't have card here.
Nurse tace dole say da card zaki samu ganin likita , how much for card nurse din tace family card   5k single 3k .

Zeenat ta Ciro 5k ta mikawa nurse din .
Nurse tace  name madam with full address .

Zeenat tabata wrong address nurse tayi gaba duk abin nan dake a tsorace take kar wani mugun ido yaganta.

 nurse din bata jima ba ta dawo ta mikawa zeenat card dinta .
Sannan ta rakata  zuwa  office doctor .


Doctor din macce  tana zaune tana rubuce rubuce ga medical manne a idonta sai da gaban zeenat din  ya fadi dan sai taga likitar kmr  tayi mata kama da doctor saira .
takarasa cikin office din zuciyarta na cigaba da bugawa ta ajiye mata card dinta a saman table ta zauna kan kujera a sanyaye tana kallon doctor din har zuwa lokacin bata dago ba tana cigaba da rubuce rubucenta .



MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO



Page 47


' ta Dan marairace murya tamkar mai shirin kuka tace Doctor ,sai lokacin doctor din ta dago kanta    Ahankali  tana duban Zeenat da gabadaya ta dawo kalar tausayi bbu inda baya rawa ajikinta .  Likita Tace sorry please Ina wani aiki  sannan ta janyo file dinta gabanta tana dubawa .


Tana kallonta a sanyaye tace Dan Allah taimako nazo nema gurin ki likitar.
Likitar  ta sake dagowa tana sake dubanta jin tace gurinta " kmr irin tasanta oready.
 ,likitar tace do u kwn me before?
 zeenat ta girgiza mata kai kawai alamun A'a ,sannan likitar tacigaba da abinda take tare cewa wani taimako ,zan miki .

Zeenat Tace Dan Allah likita Ina son ki taimakmin ciki gareni nake son ki zubar min dashi .

,,likitar ta sake dagowa tana mata kallon tababbiya .

Sannan Tace kina da  hankali kuwa  ce miki akayi muna zubar da ciki a asibiti nan .
 da zakice a zubar miki da ciki.

Zeenat ta sake narainarai ce murya Dan Allah doctor kiyi hakuri ki taimakmin ko nawa kike so zan biyaki wlh ko two hundred thousand ne zan iya baki muddin kika taimakmin .


Likita tayi shr kawai tana kallon Zeenat Ga koshi Ga kwana yunwa ,Amman aikin ne akwai  risk acikin sa .

,'ahankali doctor tace gaskiya ni bana yin irin wannan aiki  .
" Zeenat tace nasan kinyi iya  Nidai taimako kawai nake nema a gurinki.

 doctor ta girgiza kai meyasa kika zabi ki zubar da ciki bayan daga kallon zaasan iyayenki masu kudi ne .km gashima 

Zeenat Tace Duk ba wannan ba please help me doctor . 

Ina mijinki inji cewar doctor?

Da sauri zeenat tace bani da miji shiyasa ma nake son zubar da cikin sbd parent din zasuyi fushi dani .


Likita tace ok  zan taimaki Amman sai naji  alert tukun dan dayawanku baku zuwa da kudi sai angama aiki kuce zaku kawa daga nan shikennan

Da sauri zeenat ta Ciro wayarta dake cikin pursue dinta  tace ur account number please doctor takaranto mata account dinta ,

Take Ta tura mata 200k likita naganin alert ta sauke ajiyar zuciya tare da mikewa jikinta a sanyaye Dan tsoron aikin taje ta bude show glass din magunguna tashiga hada wasu magani har kala uku sannan ta dawo tana kallonta hannuta rike da maganin tace ta juyo ta mata allurar .

tace ok ta Mike ta juyo mata bayan tayi mata sannan ta dauko magungun  tabata tare da fada mata yadda zata sha taji dadi dabata na turawa ba irin na nurse titi ,.

Tayiwa doctor  godiya sosai zata wuce doctor tadakarta daita ,sannan taraka har  bakin get .
Zeenat na murna yau ko gobe zata rabu da jaraba jikinta  . Ta dauki drop din taxi .
 zuciyarta fari tas tamkar ammata albishir da gidan aljanna . 
 Har tazo gida murna take da farinciki.


A gajiye tashiga part dinta  tana shiga ta iske rahma a parlour ta wuce batare da tace mata komai ba Dan yanzu ta lfyr take .Sai d moris datace ta kawo mata abinci .



Tana shiga dakinta ta zube akan bed tana shafa cikinta Dan yuwan take ji moris ta hawo saman Zeenat da kanta takawowa madam abinci tayi kallon saman a she duk kyawun. Kasa da take Gani a bayan sama yake  . Zeenat taci abinci Sosai .tana gama ci tayi hanyar bayi  tashiga aikinta na kwara amai.
Har sai dataga ta amayar da abincin data kaf sannan hankalinta ya kwanta  da kyar Tasamu ta fito daga bayi ta zube akan bed Ta runtse idanunta.



Da daddare 
 'ahankali take  bude idanunta jin murdawar da cikin ya soma mata ,ido hudu sukayi da  deeni zaune, yana kallonta .

 tashiga kokarin tashi ya taimaka mata yana cigaba da kallonta yace kin ci abinci ma Kuwa?
 ta girgiza masa kai Dan yau nazo duba bbyna da wuri da fatan a shirye kike ?

Ta juyo tana kallon agogo dake manne a dakin taga karfe goma a zabure ta Mike tayi hanyar bayi Dan zubar da miyo tana fitowa ta hango magungunta a zube  akan gadon .
.
 da ganinta kasan batada gaskiya.
 ya tsaya yana kallonta yace meya faru sanin cewa da Zar ya juya zay iya ganin  magungunta yasa ta juya tayi cikin bayin da sauri ta tsugunna sananin  datayi , tabbas zai biyo ,'yasa ahankali tasoma kakarin amai .

Har ya juya Ya kalli laidar maganin say  km ya Mike da sauri yayo gurinta  a rude yana mata sannu jikinta say  rawa yake.

 bbu wani amai datayi ta jingina bayanta  tana maida numfashi tare da toshe hancinta    wayo juwa nake Gani  

 a rude yace juwa km  c km  Zeenat ?
ta girgiza masa kai tace har da kaina .

Ya dauko zai kwantar daita akan gadonta  tayi saurin sake  toshe bakinta da hancinta da hannuwanta dukka  uhmmmm karka kwantar dank    kaini dakinki  wari dakin yake shi yake sani ganin juwa . 

jikinta na rawa Allah Allah take subar dakin 

Kai tsaye  dakinsa yayi  daita .
  "ya kwantar daita akan gadon shi tare da kunna mata AC  da fan jin tace juwa take Gani .

 ba iya jikinta kadai ke rawa ba har zuciyarta bugawa take da sauri .

Yace ya kike jin jikinki yanzu ?
tace daidai wunya kawai nake ji yanzu km abinci ummi nake son ci yace ok  bari naje yanzu na karbo miki .
ya tashi da sauri ya fita daga dakin .

Tana ganin fitarsa ta Mike da gudun bala'i ta nufi dakinta tayi sauri ta dauki laidar maganin ta bude ta balli uku Tasha ta boye sauran cikin wordrob dinta .


Yana dawo daga gidan ummi ya nemeta ya rasa dakinta ya nufa ya isketa kwance akan gadonta .

 da mamaki yake kallonta zai yi magana ta  Mike zaune  zata masa iyaye da yauki ya daka mata tsawa tare da ce mata  munafuka may fuska biyu yaja tsaki ya dire mata coolar abinci  juya yabarta.

 'ahankali ta sauke ajiyar zuciya ,tare da cewa maseefaffen banza  kawai . 

Tayi shr har shabiyun dare tana jiran ko zata ji wani abu Amman shr  bbu labari .



Washegari takasance weekend deeni na gida Dan haka bata samu wani sakewar shan maganita ba.
 Dan sosai  yasanya mata ido .


Har wata washegari garin Sunday yakasa ya  tsare yaki fita koina . .

Dan haka itama  tayi kwanciyarta a dakita .

 tana kwance a daki abin duniya yasoma isarta dan har yanzu bataga komai ba .
,'ahankali ta Mike tasawa dakinta key ta dauko sauran maganin da doctor ta bata .
Ta zauna akan ta fito da magungun daga cikin kakinsu  ,ta sha .

ya saura na gobe kadai  kusan awa hudu da shan maganin na yau wanda shine second to the last Amman bataji komai ba jin bataji komai ba yasa ta dauko wayarta ta hau what's app Dan ragewa kanta damuwa .taji tasoma jin bacci km har lokacin bataji komai Dan haka  ta diro daga kan godan wayyo nashiga uku kar dai cikin bazai zube ba.
 , da sauri tashiga balbala maganin kennan tana kokarin   janyo   ruwa  daga kan Mirrow dinta zata sake kara kora wani .

taji wani irin matsanancin ciwon mara da bata jin irinsa ba tayo waje da idanunta a tsorace gabanta na faduwa 'ahankali cikin ma ya dauki zafin ciwo ta dinga murkususu tana daurewa.
 Tunda  tasan  hakan zata kasance daita .

 jin irin wanna azabar ciwon yafita daBan da wancen yasa ta kankame cikinta waje guda  tashiga mutsu mutsu daga zaune tana buga ties da hannuta taga zama ya gagareta ta kwanta kasa tana juye juye ita kam Tayi alkawari zata rike ciwon har yagama Cinta bbu mai ji .

Ai da mararta tayi wani irin murdawa ta daura hannuta akai taji tamkar mutuwartace tazo batasan lokacin da ta fasa wata razananniyar kara ba rike da cikinta wanda karan tasa gidan gabadaya ya dauki sautin muryarta.

 lokacin guda ta hada zufa tashiga kwalla ihun wahala .

Agigice deeni ya nufo dakinta say yana   murda kofa yajita a rufe gam.

Da karfi  yashiga bubbuga kofar yana kiran sunanta da karfi  Ta sake kwara wani ihun wayyo mutuwa ,zanyi .

Deeni yakoma dakinsa  a rikece yashiga neman   extra key din dakinta da kyar Allah Ya taimaka yagani .
 Ya  a frigice ya dawo jikin kofar jikinsa na rawa Allah Allah yake ya bude dakin.
' yana budewa ya afka can karshen gado yaganta kwance shame shame  tana juye da kirawa kanta mutuwa.

 da sauri ya tsugunna  ya dago ta a rude yana tmbyta kasa cewa komai tayi sai juye juye take tana zan mutu Yaya mutuwa zanyi ..

A rikice yace  Dan Allah zeenat kimin magana mana make damunki .Ina ke miki ciwo  .
Ga maganin a zube akasa , hannuta na rawa tashiga tura maganin karkashin gado tana numfashi sama sama  duk yana lura da abinda take ya rike hannuta da sauri yana kallon maganin yace meya wannan kike kokarin boyewa ?

girgiza masa tashigayi Dan zuwa lokacin bbu bakin magana a zabure ya zameta daga jikinsa tare dago maganin yana kallo yana karantawa instruction din maganin zuciyarsa yake ta buga alokaci guda wani gumi ya rufeshi Dan tabbatar da abinda yakaranta yasa  yayi saurin zaro wayarsa daga aljihun wandonsa yakira doctor saira yana tmbyrta   meyye amfanin maganin  mestrogen. Ajiki ?

'Ahankali tace masa tablet ne na zubda ciki.
 a rude yayi jifa da kwallin maganin yashiga furta innalillahi wa inna ilaihi rajiun da hannushi ya dinga nuna tsabar ya kasa magana

Wani ihun ta km fasawa .



MMN SUDAIS CE
[5/14, 9:02 PM] ‪+234 906 414 7340‬: 💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
     💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO




Page 48



Da kyar ya iya furta sunanta  Zeenat Zeenat ...meyasa kika min haka?

 nace meyasa kika min haka? 

Kuka take sosai tana juye juye hannuta dukka akan cikinta tana murkususu ciwo kmr ranta zai fita  .
" Jini kuwa say malala yake  ta kasanta.


 Ya sake daka mata tsawa yana sake   furta kalmar me namiki Zeenat?
  Tamkar zaki ya' karaso gareta ya dagata tsaye  ya kai mata wani gigitaccen mari .wanda yasa Zeenat Ta saki kara har su moris dake downstairs ,sukayo hanyar step suka yi  cirko cirko jikinsu narawa . 


Yasa hannushi daya ya shake mata wuya tare matseta da bangon dakin  kika zubar min da cikina Zeenat.
  " meyasa kika zubar min da ciki?

 ta kamkame ajikinsa  tace wayyo cikina mutuwa zanyi katamakamin" wasu marukan ya sake yaryarfa mata   tare da buga kanta da bango dakin  sannan ya saki wuyanta tayi kasa luuuuuuuu...Ta zube warwars a filin dakin tana sakin numfashin sama sama Ga azabar ciwon dake nukurkusanta.
  " Ga azabar da deeni ke gana mata  Tunda take  bata taba ganinsa  cikin yanayi makamancin na yau ba.

 idanunshi sun kada sunyi jawur gabadaya jikinsa bbu inda baya kirma tsabar tashin hankali dayake ciki .


Muryarsa na rawa yace say kingaya min ubanwa yabaki maganin zubar da ciki" hade da yin kwallo daita sai da kanta ya bugi Bago dakin ta dawo ta sake  xume kasa.
  ta kwalla wata gigitacciyar kara woyyo...... nashiga uku kayi hakuri Dan Allah kabarni mutuwa zanyi .

Kafin ki mutu yau sai kin gayamin wani asibiti kike je ya sake daukarta da hannayeshi duka  ya sake  bugata da bango take goshinta ya balle da jini .
kan kace me jini ya rufe mata  fuska , takoina jini  ke siyaya ganin yana kokarin kwance belt din jikinsa tasoma kokarin fita daga dakin ya fixgota ya shake mata wuya yana huci Ina zaki gudu kije?
 me cikina ya miki kika zubar min da abina "yau sai kin fadamin tsinannen daya kaiki asibitin da kika zubamin da cikina wlh  ko na aunaki lahira. 

Da kyar Tasamu ta riko hannuwansa duka biyu cikin kuku da tashin hankali tace Dan Allah Yaya kayi hakuri cikina mutuwa zanyi ya sake buga kanta da bango gara ki mutu kowa ya huta .
munafuka banza  may kashe ya'yan  da basu ji ba basu Gani ba . 

No . please Yaya  kamin rai dan Allah cikin zai kasheni "  
 da karfi ya km  buga kanta da bango ya fice daga dakin.
 tasan km Bai gama cin kaniyarta ba Ga azabar ciwon dake nukurkusan mararta,tayi karfin hali   ta rarrafa ta fito daga dakin da kyar tana neman inda zata buya.
   tun Bai zo yakarasa kasheta ba.
 Dabin bango ta dinga jan jiki Ga jinin na tsiyaya ajikinta hannuta dafe da mararta dake mata wani azababen ciwo da kyar tasamu   ta sauko parlour,n kasa .

Ya fito daga dakinsa yashiga nata  dakin yaga Bai ganta ba .
Ya fito da sauri yana kallon kasa yaga yadda jinin danshi ko yarshi ke malale akasa , kwalkwaluwarsa kmr ta tarwatse tsabar tashin hankali cikin zafi nama  yasoma taka step biyu biyu idanunshi sun sake kadawa Ga wani irin zafi da kirjinsa ke masa tamkar zuciyarsa zata buga .

a haukace yakarasa saukowa daga step daidai zata bude kofar fita daga gidan ya daka wata  razananniyar tsawa wanda yasa , Zeenat ta gigice  Ta afka dakinsu moris batare da tasani ba , tasakawa kofar key tare da barin key din ajikin kofar .

A tsaye ta iskesu sunyi cirko cirko da alamun sunji duk abinda ke faruwa acikin gidan , Zeenat zube kasa dakin  tana Sakin numfashin wahala  har lokacin jinin dake zuba a jikinta Bai tsaya .
Can wani tunani yazo ta Mike a zabure tana kuka ta kamo hannu moris cikin nata .
Muryarta da gangar jikinta duk   rawa suke  ,moris..moris  please ki rufamin asiri koda ogo ya tmbye wani abu kice mishi bakisan komai ba kinji..
 ,ita dai moris say girgiza mata kanta kawai take sbd kwata kwata  bata fahimci  abinda madam dinta ke nufi ba  .

 gabadayansu a frigice suke  har rahma  jikinsu Sai  rawa yake yana karkarwa .

Ga jinin nabin kafafun Zeenat .deeni yakaraso kofar kmr wani zautaccen mahaukaci  yashiga buga kofar da iya karfinshi cikin tsawa yace Zeenat ki bude kofar nan tun ban ballata da kaina ba.
 ,aiko nan rahma da moris suka rude kowace na neman gurin boya yeeeee I don't bring my self inside double wahala oooo...inji cewar rahma .

moris ko Sai kiran jisues Cris take tana karawa  oh jisues have Marcy on me , hawayen suke shabe shabe gabadayansu sun rude .



 gabadaya Zeenat  hankalinta yasoma barin jikinta nishi take sama sama  Muryata na rawa rawa  Tace Dan Allah ya'ya kamin rai kayi hakuri wlh bazan sake ba,kima sake wlh yau Sai naga bayanki da duk ma wanda ya tsaya miki .

bazaki bude min kofar ba yakarasa maganar yana huci tamkar kumurcin zaki rahma da kusan tafi moris rudewa   tace madam please help us to open  door for him this ting is become big I won go home I kwn die now please... kijin rahma  na rawa  karasa xata bude kofar moris  tayi sauri  ta fixge key din tayi jefa dashi ta jingina bayanta da  kofar tana kiran sunan jisues .

deeni Bai sake cewa komai yakoma dakinsa yana huci Zeenat ko na durkushe a dakin say kuka take tana  juye juye Dan tasan yau karshenta yazo mutuwa zatayi gashi har lokacin jinin Bai tsaya ba say bulbuluwa yake duk kayan jikinta ya baci da jin haka dakin duk jinin takoina ka kalla  gabadaya tagama sadaukarwa  mutuwa zatayi yau.
 shiyasa tasoma addu'ar neman sauki da tuba a gurin Allah kuka take tana dafe da cikinta wayyo ummina... wayyo   babana ..wayyo kuna Ina   yau ga Zeenat dinku zata mutu batare da saninku ba.
 Ta soma narainarai da idanuwa wayyo nashiga uku mutuwa zanyi Sai kuka take tana mutuwa zatayi

 aiko su moris suka  sake tsorace da rudewa suma har da kukansu shebe shabe suna kiran sunan jisues Cris. 

Bansa haka zata iya faruwa dani Allah na tuba astagfurka wa,atubu ilaik Allah na tuba Allah kasa zuciyar mijina tayi sanyi ya hakura da laifin dana aikata a gareshi .
cikinta ya sake wani irin murdawa ta saki kara .wanda yasa "
Jini ya sake ballewa tasoma Gani double  wayyo ummina kina Ina ummi mutuwa zanyi moris takaraso Dan Allah madam karki mutu zaki samu cikin wahala..
 suka ji deeni nakokarin zira key cikin kofar Zeenat Ta fasa ihu lura datayi bbu key din ajikin kofar jikinta na rawa taji kmr ta suma gurin  tasamu sauki da sausaucin  abubuwa dake shirin faruwa daita.

 wayyo Allahna wayyo ummina Dan Allah Yaya kayi hakuri kamin rai  kaji tausayina  yau mutuwa zanyi karka kasheni  da hannuka Dan mutuwa zanyi .
ya afkl dakin hannushi rike da kwalin table din data sha yau da wanda yagani kwanaki adakinta yana  kallonta da idanunshi suka maga rikidewa tamkar jini aka zuba acikinsu.

 kanta yayi ya fincikota su more's naganin haka  suka soma kokarin arcewa daga dakin sakin Zeenat yayi tare da  juyowa ya damko wuyansu da hannuwasa ya gara kansu waje daya tare da buga kan  kowace  da bango dakin sannan  yayi flinging dasu suka koma can  karshen dakin ,suka durkushe suna huci Dan kukan ma kin fitowa yayi .
 yasake yin kan Zeenat ya  cakumota.
 muryasa na rawa wlh wlh baki gayamin wanda yabaki magungunan ba say na kashe ki km a yau....



MMN SUDAIS CE
[5/14, 9:02 PM] ‪+234 906 414 7340‬: 💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
     💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO




Page 49


Wlh wlh   baki gayamin wanda yabaki magungunan  zubar da ciki ba ,zan kasheki inga uban  da tsaya miki km zan Dan iskan da zai yi shari,a dani ya sake maimaitawa.


Jikinta na rawa tashiga girgiza masa kai  hawaye nabin kuncinta gabadaya tagama fita haiyacinta ta dawo wata kala daban fuskar nan tata ta can kammanin da kyar take matso hawaye daga kumburarun idanunta .

 yayinda moris tafi  shiga tsaka mai wuya Dan bbu abinda jikinta ke Sai kirrrrrrma.

Ya shaketa da karfi idanunta sukayo waje cike  da  tsawa yace bazaki fadamin ba .
 kai ni  gurin ummi ,zan gaya maka ,a gabanta yana shake daita ,ya zuba mata barin makauniyya take hancinta da bakinta suka  balle da jini .

A tsorace muryarta a shake  Tace zan fada...Zan fada wlh zan fada  ya sake zuba mata wani  marin uban me kike jira ?

Ta fashe da wani gigitaccen kuka  jinin ya sake ballewa ta baki ta hanci,w lh  zan fada  maka gaskiya Dan Allah kayi hakuri karka kasheni  .

Jin ta kiyin magana Sai zan fada take maimaitawa yasa ya damki makogoronta idanunta suka kakkafe tana shirin sumewa yace bazaki fadi uban da yakai ki akabaki ganin zubar da ci ba .
ahankali ta dinga daga masa kanta alamun zata fada sannan ya sausauta rikon da yayi mata Amman say daya sake zuba mata wasu lafiyayyun  maruka , hawaye masu dumi da zafi gyaraye da jikin suka shiga ambaliya a kuncinta ta dinga jan zaninta tana fizgar gashin kanta ,tana kuka ta dubi saitin da moris take tsugunne tana risgar kuka Dan say lokacin tasan akan me ogan nasu ke dukan matarsa .
Yacd ,ok itace tabaki maganin ?
 tashiga girgiza masa kai uhmmmm baita bace sumy ce takaini  ,ita km ita nake aika siyo min maganin tsorace  moris tayo waje da idanu tare da dafe kirjinta.

 ,yayinda jikinta yacigaba da kirma aranta tace yeeeeeee mo daron' won  madam Fe, pa romomi,o emiko.  

 deeni   ya saki Zeenat sulale kasa ya juyo tana kallon moris da tazama kalar mara gaskiya duk ta rude Sai rawa bakinta yake takasa magana ganin yadda oga ke kallonta yasa ta fashe da kuka tace wlh karya madam take min ni dai tana aikana siyo mata  tablet Amman kwata kwata bansan ko meye amfanin tablet din ba.


 hawaye cike da idanunshi yace dake aka taru aka zubar min da cikina kennan?
 wani kara yayi yakarasa kusa da moris kmr zaki ya' damki wuyanta  ita da rahma da basan hawa ba ballanantana tasan asalin wainar da'ake toyawa ba sai yanzu,.


Hawaye cike da idanunshi yace daku aka samun damar zubar min da cikina ko.
 me cikina yayi muku Bai jira mezasu ce ba yayi wani irin juyi tare buga kansu da bango ya shakesu  yana huci Sai Ga jini  da iya karfinshi yake jibgarsu yana kwallo dasu jikin bango dakin Sai daya musu dukan mutuwa ya tabbatar da ya sumar dasu sannan ya bar su kwance agurin .


juyawa yayi Bai  ga kyallin Zeenat ba.

Ita ko Zeenat  tana fitowa daga dakinsu moris  hanyar waje tayi da Dan sauran karfin Da yayi saura .

 gabadaya jikinta yayi week  da kyar take iya  jan kafarta  tana isa gaf bakin   get din gidan jiri ya kwasheta ta zube kasa takasa tashi km daidai na n deeni ya fito daga cikin gidan  nemanta kmr an hankadoshi ,tana ganinsa tafasa gigitacciyar kara tana ihu tasoma kokarin mikewa tsaye Amman takasa cikin kuka ta dinga cewa no... please wayyo Yaya katausayamin ganin yayo kanta batare data shirya  ba   tace Dan Allah katausayamin zan fadi gaskiya  wlh ba moris bace sumy ce tafara  kai ni inda ake zubar min da ciki ,ya sauke da wani mahaukacin mari wanda yasa Zeenat tasoma ganin double Dan ko shi deeni tishi tishi take ganinsa , tun yaushe kike shan maganin hana daukar ciki ni da ban sani ba .

 Tun shekara biyar Tare da  nuna masa yatsunta biyar  Sai km ta sulale wajen sumammiya .

'Ahankali ya zube gabanta tare sanya fuskarsa cikin tafukan hannushi yana kuka mai cin rai ,tare dayasanin auren Zeenat dayayi 

 da kyar ya iya cire tafin hannushi yana kallonta hawaye kwance a fuskarsa ya dagota ya rungumeta ajikinsa  muryasa na rawa yace meyasa  Zee...nat ..?

Meyasa kika zabi kimin haka?
Why  me cikina yayi miki dakika gwammaci ki zubar min dashi alhalin kinsan Ina son abuna .

 ganin har lokacin jini Bai tsaya ba yasan.

 shikennan ya sake rasa abinda ke cikinta 

ya sake jin haushinta yakamashi  cike da  tashi hankali yayi flinging daita tare da   Mikewa yayi cikin gidan .

Ruwa ya dauko may maseefar sanyi yashiga siyaya mata ajiki  Amman sam bata motsa ba.
 yadauke yayi dakinsa daita .


Yana shiga dakinsa ya kwantar daita akan gadonsa ya dauki  waya yakira doctor saira please  doctor kizo yanzu gidana  I need ur help  tace ok am coming right now .

 ,sannan yakira faruk yace yazo yanzu yanzu  gida  yasame shi ,yayi hanging din kiran tare da ajiye wayar ,km har lokacin Zeenat na kwance bata motsa ba .



 Ko minti 20 ba'ayi ba  Sai Ga doctor da faruk A tare  suka shigo cikin compound din gidan   frigice suke kallon jinin tun daga compound din gidan har parlour,

 kai tsaye faruk yashiga neman layin deeni  HK ma doctor saira , kiran faruk  ne yasoma shiga.

 deeni Gani a parlour,n kasa ka hawo sama kasameni a dakina  kafin fk  yakatse wayar doctor jin da wanda yake wayar tace Dan Allah yace masa Ga doctor tazo fk yasanar masa yace su shigo tare .

Bbu abinda ya daga musu hankali kmr yadda ko Ina kaca kaca da jini a gidan.

Kasa karasawa cikin dakin  fk yayi byn ya bude kofar dakin Sai doctor ce tayi karfin hali shiga km har lokacin Zeenat kwance bata farka ba .

Wani irin kallo fk ke bin deeni   dashi Ga Zeenat kwance  duk ilahirin jikinta  jina jina da jini.

Da kyar faruk d doctor ke tmbyrsa abinda ya faru wanda oready tun kafin deeni yace komai  jikin doctor saira yagama bata ainihin abinda ya faru . .

Deeni yakasa cewa komai Sai girgiza kai yake " say lokacin fk yayi karfin ya karasa dakin yana kallon Zeenat dake kwance rai hannun Allah.

 zuciyar  fk ce ta buga sakamakon ganin yadda gabadaya Zeenat din Ta sauya kwararen wanda yasanta ne kadai zai iya shedata. 

Karo na biyu da fk ya sake tmbyr deeni  yace Meka mata deeni ?

da kyar ya iya bude baki yace abortion tayi  fk Zeenat ta zubar min da cikin Ga maganin hana  daukar ciki datake ta faman dirkawa cikinta har tsawon shekara biyar hawaye yabiyo byn yagama maganar tasa.

 ita dai doctor tana tsaye  tana kallon Zeenat dake kwance sai yadda Allah yaso daita  km tana sauraron duk abinda ke faruwa ,rashin ba'a bata damar taba Zeenat din bane  yasa tacigaba da tsayuwarta  .


Innalillahi wa inna ilaihi rajiun fk ya dinga furtawa Hankalisa yayi matukar mugun tashi da jin abinda deeni yace abortion ...ya sake maimaitawa. Sannan yace mutuwa tayi kome?
 deeni ya girgiza kai alamun Bai sani ba .


Fk ya dubi doctor dake tsaye har lokacin rungume da hannuwanta a kirji .
yace kin ja kin tsaya ,I think abinda yakawoki kennan ?
,eh dama nake jira aban. A zafafe fk yace to am baki please ki duba mana ita yanzu musan halin da take ciki  .

 'Ahankali doctor saira  ta karasa gabanta sosai ta Dan tsugunna tare da daga hannuta tana filli din numfashnta sannan ta fito da kayan aiki Cikin kwarewa da iyawa  gurin aiki ta .

tasoma hada allurar dazata mata da kyar  doctor saira tasomu jinin dake siyaya ajikin Zeenat  ya tsaya .

deeni da fk kallonta kawai suke suna daga zaune doctor ta mike tsaye tana duban deeni tace Dan Allah ka gyara mata jiki zanje nazo da drip yanzu zan dawo .

kai kawai daga deeni ya daga mata ba wai Dan zai abinda ta umarcesa ba  .

Sanin da fk yayi deeni bazai wani gyarawa Zeenat jiki ba .

yasa yakira wayar shemah tana dauka yace ta same shi agidan deeni yanzu yanzu afrigice tace lfy yace da sauki kedai kizo yanzu .

Ko minti goma ba'a yi ba tashigo gidan ta sake kiransa ya leko dagon corridor din da zai kai ka dakunan gida .

 yashigo daita dakin deeni kwance taga Zeenat tamkar matacciya ,fk Bai bata damar  tbmyrsa ba . deeni naganin shigowarta ya Mike yabar dakin .

fk yace ki gyarata mata jiki yanzu Ina zuwa a tsorace tace mutuwa Zeenat din tayi ne naganta haka?

 yace A'a bata da lfy ne ya wuce Dan bai son ta km masa  wata tmbyr .

da kyar shemah ta iya gyara mata jiki Dan gabadaya a tsorace take da ganin yanayin Zeenat din.
 sannan tashiga dakin Zeenat Ta dauko mata wasu kaya ta sauya mata sannan tashiga aikin goge jinin tagani gidan.

 ahaka doctor  saira ta dawo tasameta doctor tayi duk abinda yakamata tayiwa Zeenat.

 , ahankali fk ke tmbyr deeni  ma'aikata gidan?

deeni  yace suna dakinsu suma  na musu dukan kawo wuka ne .
 a tsorace fk ke  kallonsa su km me suka yi ko haukan ne yakare akansu.
 ran deeni a sake bace yaji tamkar ya Mike yaje ya sake kara musu wani dukan .

Sai daya furzar da iska  yace akwai daya da Zeenat ke aika siyan magani hana daukar ciki .
 ,ita km dayar daman haushinta nake ji km karuwancinta ya isheni a cikin gidan nan .

Shiyasa   duk na hadasu nayi musu walima.
 abin ma har yaso yabawa fk dariya amman ya dai matse 

daidai na n doctor saira  ta sauko fk yace dan Allah tashiga ta duba masu aiki yana nuna mai kofar  mata dakin .


Ita kanta doctor saira tayi matukar mamakin ganin irin dukan da deeni yayiwa masu aiki .

Ta dinga tunanin , su km me suka masa ,haka dai tabasu taimako  suma sannan tattara tayi musu sallama ta wuce .



Har dare Zeenat bata farka ba .


Su moris da rahma an farfado sai dai basuyi gigin fitowa ba ,jira kawai suke su samu hanyar guduwa .suka dinga kuka acikin daki bakaramin fashewa kawunansu yayi ba .


 Doctor ta sake dawo gidan byn sallah  magariba ta duba  jikin Zeenat .

'Ahankali Ta sauko kasa tana duban inda  deeni ke zaune  tace dole fa sai ankara mata jini deeni Bai dago ya kalleta doctor din  ba .
  'yace kina iya mata   duk yadda yadda kikaga mada ciki ma har da barinta haka .
  cikin Haka fk ya sake dawo duba Zeenat ya ji abinda deeni yace Dan haka yace shi suje a dibi nashi asamata .


Deeni yakoma tamkar mara lfy Dan ya dade baiga mace may irin halin Zeenat ba .

Suka je asibiti aka gwada jinin fk  km yayi daidai dana Zeenat din Dan haka  aka diba .suka dawo gidan doctor tasa mata jini  .



Fk ya bude dakin  moris baigansu ba  sai shirgin kayansu ,ya koma sama yana gayawa deeni ko kallonsa baiyi ba ballanantana ya amsa masa.



Karfe daya na dare daidai Zeenat ta farka  ganinta kwance a dakin deeni yasata fashewa da wani  matsanancin kuka tana kiran sunan ummi wayyo ummi ki taimakmin kizo Yaya deeni zai kasheni.

 cikin Haka tasoma  jiyo motsin shi  yana fitowa daga bayi take  tayi  mukut ta hadiye kukanta.

  tana ganinsa ta hau rokonsa Tana  bashi hakuri Dan girman Allah Yaya kayi hakuri karkamin komai .



Ko takanta Bai bi sai sautin  muryasa tajiyo.


get out from my room.

Dirowa tayi tare yin Yar wuntsele  daga gadon .

 duk da jikinta bbu wani karfi hakan Bai hanata jan kafarta da sauri  ta bar dakin  sai da tadan yi nisa da dakinsa tukun tasoma dingisa kafarta   .



Washegari da safe





MMN SUDAIS CE
[5/14, 9:02 PM] ‪+234 906 414 7340‬: 💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗





AYSHA A BAGUDO




Page 50




Washegari da safe

 Zeenat kwance akan bed dinta tana tsaka da baccinta na gajiyar dukan jiya dataci a gurin oga deeni wanda sanadiyyar haka yasa   da kyar take iya motsa kasusuwan jikinta.

" takoina ta juya  gabobbin jikinta"  tsami suke mata , sosai take baccin hatta numfashi  ahankali take fitar dashi  wanda dagani kasan na ragowar wahala ce   .


Kmr a mafarki taji an ware mata kafafunta an watsa  mata ruwan zafi 

a gigice ta zabura ta Mike zaune ta kwallara kara wayyo  cinyata  kafin ta ankare ta soma jin saukar belt takoina ajikinta tashiga kuka  tana shafa duk inda taji saukar belt.


Maza ki Mike stupid kawai munafuka may kashe ya'yan mutane.

 wayyo yaya Dan girman Allah  kayi hakuri wlh nayi danasani da nadamar aikata maka abinda nayi  .

 ,bakiyi dakinsani da nadama  ba sai ma nan gaba yarinya.
 yana cigaba da zabga mata belt .

 aurenki danayi  shine babban kuskuren dana tafka a rayuwata .

Amman wlh kema say na gana miki azabar da har ki mutu bazaki manta dani ba .

, abinda zamiki nan gaba shi zai   haddasa miki hawan jini .
 ,daga karshe  zuciyarki ta buga ki mutu mu huta domin gubace ke acikin dangi .

Yana zaginta tare zabga mata belt" maza kije kitchen ki hada min breakfast stupid more then donkey's kawai.

 da gudun bala'i tafito daga dakin biyu biyu ta dinga takasa steps , tayo kasa tana kuka tana bashi hakuri .


Cikin takunsa na isa da kasaita yakaraso downstairs hannushi rike da belte ya daka mata wata razananniyar tsawa data sake gigita zuciyar Zeenat.
 " tsayuwar uwar me kikewa mutane  da baza shiga kimin abinda nace ba.
 ko say sake cin ubanki ,shegiya may idanun chainis .
Da sauri tashige kitchen.

 shi km ya samu guri kan kujera ya zauna yana sauke numfashi  tare daura kafarsa daya kan daya yana jijigawa ran nan nashi a dagule cike da takaicin abinda Zeenat tayi masa .


Zan may dake wajen uwarki Amman sai na gama gana miki azaba wanda gaba ko rat akace ki kashe bazaki iya kashewa ba. ballanantana Dan mutun Dan km na deeni , ya fadi haka  a kasan rashi.



 Jollouf din taliya tayi masa shap shap Dan tasan Bai fiyye son cin Abinci mai nauyi ba
 sannan ta hada masa coffee dinsa na gado .

 ,ta hada komai akan Dan  madaidaici tire .
jikinta na rawa tazo ta,ajiye masa agabansa tana Mikewa tsaye  ya zuba mata mari Dan ubanki anan zanci abinci?

 idanunta da suka canza kala km suke a kumbure suka shiga zubar da ruwan  hawaye kayi hakuri Dan Allah jikinta na kirma tayi hanyar deaning .


Ya Mike da kyar tamkar jinin saurata yakarasa deaning area sai daya zageta tas sannan ya zauna ya bude colar abinci yana yatsuna fuska yana gama ganin abinda ta dafa masa  ya antaya mata shi ajiki wani irin ihu tayi tasoma sotsa jikinta .


Dan ubanki da wannan abinci zanyi breakfast  maza kije ki da fomin wani useless girl kawai  .


Gabadaya tayi mugun  tsorata da lamarin deeni Duk sanin da  tayiwa yayan nata a da" wannan karon ya sake zarce hakan ta dauki colar jikinta na rawa Ta sake komawa kitchen .


Tana shiga ta rushe da wani irin matsanancin kuka  ita kwata kwata tsoronsa take ji.
  " tarasa takamaimai abinda zata girka masa dan tasan tujarata kawai yake son yi .
 km duk abinda zata girka masa baci zaiyi ba wahala kawai yake son sata .

 ,kawai ta fashe da wani sabon  kukan  wayyo Ummi kizo ki taimakeni ki tafi dani gurinki  mutuwa zanyi agidan nan wlh mutuwa zanyi .
 tana kuka tana ambatar sunan Ummi....
' ,daga can parlour tajiyo sautin  muryasa , kukan  me kike anan  bari inzo in zaki yin may dalili yarinya 

Jin haka yasa  ta fito daga kitchen din a guje tana bashi hakuri tayi hanyar step Dan tasan bakaramin aikinsa bane yashigo din ya jibgita kmr yadda yake nufi.
 
Da sauri shima ya Mike  ya bi bayanta  kafin takarasa  kulle kofar ya afko ciki dakin tare kamo  hannuta ya murde da iya karfinsa  ta saki kara wayyo ummina dan Allah kayi hakuri a zafafe  yace na sake jin kin Kira min sunan uwa saina ganawa  arayuwarki  azaba mai radadi.
  ' wayyo  na daina wlh na daina  bazan sake ki ran sunanta  ba ,kayiwa Allah  ka sakemin hannu.......takarasa fadar haka tare da sakin matsanancin kuka mai ban tausayi " yacigaba da murda hannun har  sai dayaga  numfashinta  na neman tsayawa  sannan ya saketa  ta sulale kasa tana cigaba da rizgar kuka  . 

 Bai barta ba yashiga dukanta  yana flinging daita baki da amfani Zeenat a gurina " dama haifar min bby kika yi ,kici darajarsu .
Amman dayake muguwace kika dinga zubar min da cikina .

kin gama  cirewa zuciyata Dan burbudin kaunar danake miki.
 ,mutuwarki ta fiyye min komai ahalin yanzu .

 muguwa azaluma may fuska biyu  yadda kika dauki shekara biyar kina wulakanta jinina a rariya  haka zan dauki shekara goma Ina cin ubanki da gana miki azaba .


Inga uban da  zaiyi da zaiyi  karata ko Shari,a dani .

Da  muryarta data gama  shakewa ta dinga bashi  hakuri "
kayi hakuri Yaya wlh am ready to gave you any type of bby u won't . 
Nayi nadama kayi hakuri wlh bazan koma ba .

Mtssss yaja tsaki may zanyi da jininki Zeenat  wlh wlh kinji na rantse bana sha'awar sake zuba Spam din a cikin wannan jikin naki. 

 ke gubace yanzu a wajena babu wani amfani da zaki min  ya sake yin ball daita ta bugi bango dakin ta dawo kasa ta baje tana air....
Air...., Dan sautin  kukanta ma kin fitowa yayi Dan azaba .

Kadan kika Gani  sauran  wancen useless din sumy ko take da suna.

yana gama fadar haka  ya juya fuuuuuu a fusace yabar dakin ya nufi nashi.


 , gabadaya komai ya taru ya cakudemasa waje daya  ji yake tamkar duniya ta tsaya masa cak ta daina jujjuyawa masa yadda yake so.....

jiya da yau duk  sun zo masa da abubuwa masu muni da daci da bakanta zuciya .

Cike da bacin rai yasoma shirya jikinsa cikin kayan aikinsa .
Komai nashi ya sake canzawa " hatta da kyakkyawar  fuskarsa ta sake daukar  sauyi daban  fiyye da shekaru 20 da suka wuce wato shekarun kuruciyarsa abubuwa daya suka dinga zuwa  masa akan matakin daya kamata ya dauka akan aurensa da Zeenat.
 ,tunani iri iri ya dinga yi  har yagama shirya kansa  ya fito tsaf Sai kamshi yake zubawa amman kyakkyawan fuskarsa a daureta take tamau ya kulle koina gidan sannan  yakama Gabansa .


Tafi 2hr kwance a gurin daya barta wanda da kyar take iya motsa gangar jikinta .

Tana nan  kwance har ta soma jin   Kira sallar la'asar daga masallacin dake  cikin gidan.

  da kyar da bin bango tasamu ta Mike tashiga bayi tana kuka tana girgiza kai shikennan tarasa deeni tarasa cikin jikinta tarasa  soyayyasa data kwallafawa rai shikennan tarasa komai nata .
 tasan ko Ummi taji abinda tayi zata tsaneta ta juya mata baya.

 wayyo ni Zeenat na cuci kaina da kaina na cuci rayuwata wazan kama  meye rudeni dayasa nakasa fahimtar komai gashi yau ban kasance cikin jin dadi  a gidan mijina ba.... .sharrrrrrrr hawaye yashigo ambaliya a kuncinta.

Kuka take sosai tana nadamar abinda tayiwa kanta .
  "tare da addu'ar Allah huci zuciyar mijin nata ,ya sake sauto mata hankalinsa gareta ,ruwa zafi tasamu ta gasa gabobbin jikinta dashi .

Kusan 30 minti ta dauka tana treating din jikinta a bayi  
Ba laifi  ta Dan ji dama dama ta ragen jin zugin da jikinta ke mata.sai cinyarta inda deeni ya watsa mata ruwan zafi waje yatashi yayi shashin  baki baki.
" cikin sanyi jiki ta fito daga bathroom ta tsaya gaban mirrow tana karewa kanta  kallon yadda deeni yamaida mata halitar jikinta.
 tamkar ba nata ba hawayen masu dumi da ciwo suka sake  silalo mata , batayi kokarin maidasu ba ta barsu suna cigaba da bin kuncinta.

 ahankali tace Allah sarki sumy a she dai sai kinshiga matsala a sanadiyata duk da  kin guji abinda  zai faru akaro na biyu   , amman duk da haka baki tsira ba Dan nasan  deeni bazai barki ba kema .


Doguwar rigar ta sanyawa jikinta tashiga neman wayarta a dakin Dan takira Ummi tazo ta dauketa  Amman sama ko kasa ta nema wayarta  tarasa.

 ta zauna jugun a gefen gadonta tare zuba uban tagumi tana tunanin shikennan ni km kiyamata, ta tsaya kennan a gidan nan tunda har yanzu bbu wanda yasan halin danake ciki  a family .

 gabadaya zaman gidan  ya isheta ya gudireta tamkar tana gidan prison haka ta dinga   ji  hanyar   fita kawai  take nema  daga gidan  domin ta tsira da rayuwata datayi mata saura Amman bbu ta inda ,zata bi ta fice daga gidan .



10 shap yashigo gidan tana zaune cikin  damuwa tajiyo  motsin. shigowar motarsa  ta  Mike tsaye 'ahankali  tana hangeshi ta Window dakinta  hawayen son shi da tausanyi shi ne suka shiga   zubo mata.
 ita kanta  tasan bata kyauta masa ba.
Tasan ta cutar dashi  km ta cancanci hukunci fiyye da haka daga gareshi. Har ya fito ya rufe motarsa idanunta nakasan tana kallonsa  tana jin yadda kaunarsa  ke sake narkar mata da zuciya tare da mamaye mata ruhi da gangar jikinta .

Ganin yasoma kokarin bude  kofar shigowa cikin ainihin parlour,n gidan ne yasa tayi saurin  barin . jikin window take km  jikinta ya dauki zafi da kirma dan sai lokacin taji  wani mugun tsoro ya shigeta.
 kmr taje ta rufe kofarta taji amman sam tsoro  da fargaban abinda zai faru ya hanata motsawa daga inda take , tana nan tsaye har yashigo dakin nata .


Bakinta na rawa rawa da shakakkiyar muryata  tashiga yi masa sannu da zuwa.
 hood it .....Ya katseta sannu da zuwan ubanki zaki min.
 Wlh  kika sake min magana wanda bani ne na bukaci hakan ba , say sabauta miki jiki hariznablenimal  kawai ,zo.... nan yana mata nuni da yatsansa.
taki motsawa sai ma cigaba da kirma da  jikinta yake .

kunneki na ciwo ne baki abinda  nace ba 
 ....da kyar take iya  daga kafafunta zuwa gareshi kafin ta takaraso ya fizgota da karfi ya watsa  mata wasu ta gwayen mari tayi kara amman bbbu murya jiyo sautinta.

Dan ubanki  har wani wanka kika samu damar  yi da canza kaya ubanwa yace kiyi wanka ya shake mata wuya ,yanzu kam gabadaya muryarta tagama shekewa kwata kwata bbu  bakin da muryar bada hakuri sai daya gaji ya hantsilata kan bed  sannan yayi kusa daita ya daura kafarsa daya kan abin gadonta dayar kafar na kasa ya zuba mata rikitattun idanushin  kawai yana kallonta shi kansa yasan zuwa yanzu ta horo iya horowa  amman  zai  barta ba ko kaita gida ba tukun sai ya tabbatar daya gana mata azaba mafi radadi .
 
Yace ,oya gayamin full address din wacce Yar iskar abokiyar iskancinki .

Tasoma magana muryata bata fita ya daka mata tsawa ki bude baki kimin magana kafin na kashekeki.
 ta diro  kasa da sauri  ta bude doron din mirrow dinta ta dauki Biro da white paper da sauri tashiga rubuta  address din sumy ta miko masa .

a wulakance  ya karba yana yatsuna fuska yana gama dubawa   yayyaga paper ya watsamata a fuska ya Ciro wayarta daga aljihun bayan wandonsa yashiga gallery inda yaga hotuna wanda bana family dinsu bane..
 yace ta nuna masa wace samy ta karbi wayar jikinta na rawa tare da   fashewa da kuka .tashiga 
ta dubo masa hoton tare da  ta Mika masa wayar  .
ya masa yana duba   pis din daman  km ita din  yafi zargi tsarki yaja    sannan yabar dakin.




Yau  kmr jiya tana kwance   a dakinta tana bacci ta kamkame jikinta guri daya " sbd tsoron abinda zai faru.
 taji an take mata kafafunta  da karfi tsiya wani azababen zafi taji wanda yasa pent dinta ya jike da danshin fitsari sannan ya  watsa mata ruwa may mugun tsanyi a jikinta.  Da sauri ta mike  zaune tana kukan azaba tare da rike masa kafafunsa yayinda hawayen  tausayin kanta , yacigaba da zuba daga idanunta, takasa ce masa  komai ,sai kallonsa da ta dinga  yi da kumburarun idanunta dake cike da hawaye  tunda ya hanata yimishi magana .

Kimin shr banason  sake jin  motsin kukanki  waya baki damar yin bacci Ai kin gama bacci acikin gidan ,tunda baki nemi zaman lfy dani ba .

 kuka ta saki sosai tana girgiza masa kanta sai daya gaji dan kansa sannan ya daga mata kafafunta wanda taji tamkar ammata garafa ne km kitashi kije ki hada min breakfast .


Sallah Ta fara yi sannan taje ta hada masa breakfast dan yanzu tsoransa ya sake nunkuwa a zuciyarta fiyye da da.

Kwantar da hankalinta tayi ta shirya masa abinci a natse takai masa ,sai da taga yasoma ci sannan ta samu natsuwa a zuciyarta .



Wasa wasa sai da deeni ya dauki sama da  kwana biyar yana ganawa Zeenat azaba iri iri km kullum da kalar azabar dayake tashinta dashi .


Iya azabtuwa Zeenat ta shashi a gurin oga deeni dan kallo daya zaka mata taba mugun tausayi tayi baki ta rame gabadaya ta fita haiyacinta ko Matsin shi taji gabanta Yashiga faduwa kennan har sai yazo ya gana mata azaba ,take samun natsuwa .ita kanta sai data Rena kanta da irin muguwar ramar datayi  ko kallon mirrow bata son yi  .



Deeni ya baza yaransa wanda suma sojoji ne  wajen neman sumy km Allah  ya basu sa'a Dan basu sha  wani wahala gurin kamota ba saboda pics dinta da oga yabasu   .

   Dan suna shiga unguwar daita suka fara cin karo  tayowa wata kawarta rakiya" gurin dawowarta ne suka cafki shegiya suka danna a mota.

Kai tsaye inda oga deeni  ya umarcesu dasu kaita sukayi .
"tun a cikin motar daya daga cikin yaran deeni may suna tope yakirasa   a waya .

 Byn Deeni ya daukar  wayar ne " tope  yagaida shi wannan  yace sir gatafa mun kamota.

Deeni dake zaune office Yace  ok ku karasata kawai ganin nan zuwa anjima  amman ku soma ladabtar min daita kafin nazo tope ya amsa da ok sir angama .



MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO




Page 51



Deeni dake zaune a office dinshi  Yace ok  ku karasa daita kawai Gani nan zuwa anjima amman ku soma ladabtar min daita kafin nazo tope ya amsa da ok sir .



Rikecewa sumy tayi Hankalinta  yayi  matukar mugun tashi .
 dajin wayar da wanda taji ankira da tope yayi.
Dan duk taji abinda Suka Tautauna a wayar .
Dan a handsfree tope ya sata "wanda tarasa kowaye wanda Yace a wuce daita gashi nan zuwa .

Haka kawai taji gabanta ya daki uku uku ya fadi rassss.

jikinta yasoma   rawa rawa lokaci daya  wani irin matsanancin  tsoro yashigeta.
" wanda tunda take iya tsawon rayuwarta  bata taba tsintar kanta cikin yanayi tsoro  haka ba .

Sosai tasoma kuka  tana tunanin laifinta Ga wa en nan bayin Allah .

Ade dake ta gefenta ya Ciro Yar karamar bindigarsa  pistu ya mannata a daidai gefen cikinta . 

muryasa kwasashe Yace   u better keep ur mouth short  before I skater u into pieces .

Cak kukanta ya tsaya amman gabadaya jikinta bai daina kirma ba .
 

Har Suka kawo omole new side kuka take shape shape bbu sauti .


Daidai wani dankareren tsararen  gida may matukar kyau da tsari wanda kallo daya zaka masa kasan anyi barin kudi akansa , sukaja Suka tsaya tare da yin hon.


 wani  soja ne ya leko ta cikin wani Dan karamin huji ta jikin get din ya duba.
  yana ganin kosu waye yayi sauri soma kokarin  bude musu get .

'Ahankali ade ya cilla hancin motarsu cikin compound din gidan yayi parking dinta .

 tope ne yasoma bude kofar motar ya fito yana Mika  sannan su ade Suka biyo bayansa tare da damko bayan wuyan sumy data ci kukanta tagaji acikin mota .


Tirjewa  tayi a gurin taki move ta sake gigicewa daganin inda suka kawo makeken gidan mai cike da ban tsoro Dan Allah karku shiga dani cikin gidan nan " ku barni na koma gida kuyi hakuri idan wani abu nayi muku wlh gobe ,,zan koma school ,zan rubuta final exam dina.
, please I beg you people's should live me to go...wani irin razananniyar tsawa taji an buga mata  from no where" wanda ya dimautar da tunaninta bbu inda Bai shaking  a jikinta .
takasa jure tsayuwa tayi kasa jikinta na rawa  Ade Yace u dis girl u ar  very stupid common get up .
Sumy taki motsawa sai kuka take tana basu hakuri .

 haushin abinda tayi  yasa ade sauke mata mari guda uku a jere tare da  kamo kafarta daya yasoma janta kiiiiiiii   ya wurgata cikin wani daki may shegen duhu .

Ta sake fashewa da wani razananniyar kara tana kuka tana basu hakuri.

 ,can km  haske yagyaraye dakin taga sun soma cicire kayan jikinsu suna wurge dashi ,Suka  saura daga su sai white singlet da wando kakinsu na solider.

tsoro ne ya sake shigarta  wayyo  Dan Allah kuyi  hakuri karkuyi reping dina please kuyi hakuri idan wani abu nayiwa oganku Dan Allah na rokeku kuyi hakuri kubarni .

Ai Gani tayi suna  kokarin sunce belts dinsu jikinsu hakan  yasa ta kamkame jikinta guri daya . Gadangadan Rotimi yakaraso kusa daita Yace  ba mukawoki nan Dan kibamu hakuri ba dauuuu taji Shima ya dauketa da wani mari ba tayi aune ba  kawai taji yasoma daureta da  igiya duk yunkurin datayi gurin ganin ta kwace kanta  amman  takasa sai daya Suka  daureta tamau.
  " sannan tasoma jin saukar  belt takoina  ajikita gashi tana daure bbu halin  ta juya ko ta matsa jikinta km duk ihun da take  bbu may jinta tsabar girman gidan ballanantana azo akawo mata dauki.

  sai da Suka mata dukan kawo wuka sannan Suka barta nan  batare da sun kwanceta ba .

Daman soja da mugunta ballanantana oga da kansa yace ayi .


Daga office deeni gida ya wuce diret yana shigo cikin parlour ya hangi Zeenat na shirya deaning kallo daya yayi mata ya ja tsaki tare da  dauke idanunshi daga gareta ya hayewarsa step .

Ita km tun shigowarsa gabanta ke faduwa jikinta ke rawa tasamu  guri ta rakube tana jiran taji yau km  wacce irin kalar azabar deeni  zai mata  . 


Wanka yashiga shap shap ya fito.
  deeni dake tsaye gaban dress mirrow  byn yagama goge jikinsa yana gyara sumar kansa 'ahankali yaji an bude kofar dakinsa ..

Ya juya cikin zafin rai tunaninsa ko Zeenat ce tazo masa da wani sabon salo ,amman sai idanunshi sukaci karo da fk ....

Bata fuska yayi tare da juyawa fk baya.
 Dan tun kusan kwana uku kennan  fk ke binshi yana bashi hakuri akan abinda Zeenat tayi masa.
 ,shiyasa yau ma kwata kwata Bai dauki kiran da fk din yayi ta masa ba .

Murmushi faruk yayi tare da karasowa inda yake tsaye Wit full confidence .
Ya dafa kadar deeni major fushi kake dani shiyasa duk yau kaki daukar wata ko  .

Kau da kai deeni yayi batare da Yace masa  komai ba.
 yayi wajen wordrob din kayansa fk ya sake yin smile tare da zama kan Yar karamar stood din dake  dakin .


Deeni yagama shirinsa tsab fuskasa a daure tamau tamkar Bai taba yin wani abu wai murmushi  a iya tsawon rayuwarsa ba.

 ya dauki wayoyinsa da suke zube akan bedside .

 zai fita fk ya riko mishi hannu haba deeni kasan gurinka nazo km shine kake kokarin barina zaune.
  " juyuwa deeni  yayi ya  watsawa masa harara please live me alone tare fixge hannushi zai murda handle din kofa kennan.

 fk Yace haba deeni meyasa kake daukar zafi akan komai 'na baka hakuri akan abinda Zeenat tayi maka .

,yakamata ace zuwa yanzu ka hakura haka duk wani hukunci daya kamata  kayiwa Zeenat oready kayi .
indai ba kasheta kake son yi ba.
' ,harara ya sake zabga masa ,a zafafe Yace sakar min hannu cikin sanyi jiki fk ya sakar masa hannun kmr yadda Yace sannan deeni ya juyo yana kallonsa ,kasan Allah bangama cin ubanta ba ita da duk wanda keda hannu acikin tsiyayar min da wahalata a rariya . 

Dan haka as for now zaka iya rike hakuri ka Dan bai da wani amfani a gurina .

Deeni ya juya ya km daura hannushi kan handle din kofar ya bude yasoma tafiya fk nabinshi a baya yana sake bashi hakuri.

 amman ko juyowa baiyi ba yacigaba da tafiyarsa yana jan tsarki har ya sauko downstairs yaja ya tsaya yana kallon tsaitin da Zeenat ke rakube  tunanin abinda yakamata yayiwa Zeenat din kawai yake  kafin yafita.

 ganin haka yasa fk yashiga tsakaninsu yana cigaba da bashi hakuri .
Ya juya kawai ba Dan ya hakura ba sai Dan Bai son yawan damuwa .

 Deeni Yace wa fk zaka iya fitowa yanzu Dan kulle gidana zanyi?
 " fk yacika da mamakin zuciya irin ta deeni baya jin rarrashi kwata kwata  ballanantana hakuri har sai lokacin dayagamar saukowa da kanshi" korata kake a gidanka km yau inji cewar fk.

 deeni ya girgiza masa kai "ko daya kai dai  muje na saukeka kawai .

 haka fk yashiga motar deeni badan yaso ba ,sai Dan Bai zo datasa motar ba .

Shima deeni ya zagaya  ya shiga  yayiwa mata key ya bar gidan daidai kofar gidan  fk deeni yaja  Dan tsaya fk ya fita.
Sannan shi km  yaja motarsa yayi gaba .
 fk ya dade   tsaye a gurin yana kallon deeni da mamakinsa har ya bar hangosa sannan tashiga gida .



Kai tsaye omale new side deeni  yayi ,da sauri aka mai gadi ya bude masa get ya shigo ya  samu guri a parking lot ya parka motarsa.
 tun Bai fito ba wayan nan  sojojin Suka zagaye motar shi tare da kamewa guri daya suna jiran fitowarsa.

Cikin isa da kasaita ya fito daga cikin motar.
 take  Suka shiga Sara masa suna masa sannu da zuwa .' ya daga musu hannu  kawai batare da ya amsa ba .sannan  yayi gaba    suka bishi   abaya yana tmbyrsu suna bashi amsa cike da respect har Suka shigo dakin  da sumy ke zaune a daure guri guda .
 duk jikinta kwance da shashin belt dinsu .


, gabanta yayi mugun faduwa taji zuciyarta na neman tarwatsewa sakamakon  ganin mutumin dayasa   yasa aka kamota.

 take hantar cikinta yashiga kadawa hawaye Suka shiga sintiri a kuncinta suna  zuba .

Da sauri ade ya janyowa major kujera zama  tare da cewa sir have a sit .

Deeni  ya zauna tare da daura kafarsa daya kan daya yana jijigawa 'ahankali 'ahankali ,yayinda idanunshi ke kan sumy yana mata kallon kaskanci da wulakanci  .

  Sai daya dauki lokaci may tsawo  sannan yayi bude bakinsa  Yace kinsa abinda yasa aka kawo ki nan?

 ta girgiza masa kanta  sannan tace no sir .
 
ok baki ma san  abinda yasa aka kawoki nan ba?
 ta sake cewa eh .

 ,Yace ok tope u guys continue beating her ol till she explained wot she did by her self.

 aiko tamkar jira su tope suke Suka .
shiga jibgarta takoina suna karawa  basu ji basu Gani .

 wayyo kubarni haka I will.... I will explain please don't kill me .

"sannan deeni ya dakatar dasu ta hanyar daga musu  yatsunsa.
 ,Suka tsaya suna huci .

 Bakaramin azaba zaki karawa kanki ba' a gurin yiwa  maaikaci kamar ni karya ba "Dan haka  Ina sauraraki  inji cewar deeni .

Cike da kukan wahala tasoma masa bayani komai data sani daki daki tun daga kan  farko samun cikin  Zeenat da yadda  har tazo garesu neman solution ,da irin shawarar data bata .

Yace very gud ,  wai ke Yar iska ko?
..keda ko aure baki dashi tukun amman kinsa hanyar yadda  ake yin abortion.

 har kika bada shawarar zubar min da cikina tace Dan girma Allah kayi hakuri wlh nasan nayi kuskure.

  ,bakiyi kuskure ba tukun sai kinga yadda zan mai dake ,ke kanki sai kiyi heating din kanki .

Cikin sanyi jiki ya mike tsaye Bai tsaya wata wata ba yasa kafarsa daya ya buga kanta da bango ta fasa wata razananniyar kara sannan ta fashe da kuka .,

 A zafafe Yakira sunan  ade..

Ade  ya kame tsaye sosai tare da Sara masa.  kwanceta  ka dumin ita  is  she a Virgin.

Yana gama fadar haka ya juya musu baya yana maida hawayen takaicin abinda suka masa .


Tope  da rotimi suka soma kwanceta  tare da kwantar daita flat kasa  kowannesu yasa kafa ya take mata hannu tana ihu tana komai  ade  ya kamo kafafunta  zare pant din dake  jikinta sannan ya ware kafafuwanta sosai ya zira fingers dinsa guda biyu acikin  kasanta yaji sun shige ya sake motsa fingers dinsa ciki sosai ,yaji yadda suke yawo agabanta .
 ya tabbatar da ba virgin bace sannan ya mike cikin hanzari  yayi inda deeni ke tsaye sarkafe da  hannuwanshi duka abaya.
 ,Yace  she is nut a virgin sir .

'Ahankali deeni ya juyo yana watsa  mata wani irin mugun kallo may hade tabe baki' sannan Yace   oready kingama useless din kanki, to being a prostitu.
  , kinsa kan yadda ake abortion shiyasa kika bada gudumuwa gurin zubar min da cikina ko tace Dan girma Allah kayi hakuri wlh bazan km ba .


 'Ahankali ya,juya  yana facing din  kofar fita yayi taku daya zuwa biyu sannan ya ja ya tsaya batare da juyo ba  you guys should rep her for me for gud two  days and return her banka " sannan ya juya  yabar dakin tare da barin gidan ma gabadaya .

A zubare sumy ta mike tsaye  tana kuka tana basu hakuri amman Ina ko takanta basu bi bi ba .

,ade ne yasoma afka mata ,rotimi da tope suka ririketa  yayinda hannuwasu nakan nonuwanta suna  matsawa da iya karfinsu . sai ihu take  tana turje turje da  neman dauki amman Ina bbu mai taimakonta Dan bama gidan ba .
unguwar ma silent area ce .

Har zuwa washegari basu barta ba sai harkata suke kmr sun same abinci  sai  da Suka mata dalla dalla tukun dan kansu suka barta tare da sanya mata kayan jikinta suka maidaita  har unguwar sukayi wurgi daita   ta suka kama gabansu .



MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
 AUREN SIRRI
     💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO



Page 52




Yau kusan kwana biyu Keenan rabonta da sanya deeni acikin idanunta wanda hakan bakaramin barazana bane Ga rayuwata " rashni ganinsa yasa duk taji bbu dadi tana son taganshi  tasan halin da yake ciki koda zai nakada mata dukan tsiya ne .

Dan haka ta kudurtawa ranta yau ko ta wani hali sai ta ganshi kafin  kwanta .

Ta mike tsaye jikinta a sanyaye tashige bathroom tayo wanka ta fito tare da goge jikinta batayi wani make up ba dan ko mai bata shafawa jikinta na.

Wordrob dinta ta bude ta dauki doguwar rigar ta zirawa jikinta .
 taje  gaban mirrow ta tsaya tana duban yadda Deeni yamaidata wasu hawaye masu dumi suka zubo mata  .



Yana shigowa gidan  dakin Zeenat ya nufa dan daman yau ce ranar dayayiwa kansa alkawarin barinta gidanshi.

 yako isketa gaban mirrow tana zubda hawayen tausayin kanta  . Tana ganinsa  taja baya da sauri tare zaro idanu waje  gabanta yashiga  dokawa da sauri. Ya zuba mata rikitattun idanushin masu mugun tsorata yanzu .

 , Ganin tsaye gaban mirrow da yanayinta ya tabbatar masa wanka tayi Tana shirinyin make up ne.
" take haushin da takaicinta suka sake samun muhali a zuciyarsa" dan haka Bai tsaya wata wata ba  ya  soma   dukan ta koina ,

Yana fadin  munafuka yau din nan zaki barmin gida byn na sake cin ubanki .

wayyo Dan Allah yaya kayi hakuri yasa hannu ya naushi bakinta ,sai Ga jini  na sake jin kin km kiramin hakuri nan sai kasheki muguwa ya dinga dukanta yana karawa sai daya sake mata jina jina sannan ya rubuta mata sakinta daya ya damka mata a hannuta tare da dmko wuyanta ya wurgata cikin mota.

 sai gidan Ummi a mota ma, barin  makauniya ya dinga mata da zaran ya juyo gareta ahaka  har suka kawo kofar gidan Ummi .

Yana gama parka motarsa ya sake damka wuyanta sai cikin parlour Ummi yayi wurgi daita  . 

Ummi dake zaune tana kallon zee word taga deeni yashigo daga sama yana huci  tamkar an jiho shi  yayi wurgi da wani abu .
Wanda takasa tantance komeye Sai daga baya .

 Da sauri Ummi ta mike tsaye  tana zare   idanu waje tare fasa ihu meye haka zan Gani yau ni fadeela Meka mata deeni ? 

Gabadaya jikin Ummi ya dauki rawa da sauri  takarasa kusa da Zeenat dake kokarin mikewa tsaye  ta fashe da kuka tare rungumota jikinta .

Tana kallon deeni da idanunta cike da hawaye. yanzu sakayar dazaka min kennan deeni  .
kashe min ita zakayi "wai ma meta maka  da kamata irin wannan duka mutuwa" wanda ko dabbar gidanka banyi tunanin zaka iya   dukanta irin haka ba  ballanantana matarka .

Deeni dake zaune sai huci yake yana fidda numfashi yakasa cewa umminsa komai .
   "Ummi Ta saki Zeenat ta iso gabansa ta daukeshi da mari bazaka fada min abinda ta maka kama wannan dukan ba.


,zuciya nacinsa dan haka yakiyin magana  hakan yasa Ummi  taji haushi  ta sake kara masa wani marin tana shirin kara masa na uku ne  Zeenat takaraso da kyar ta rike hannun Ummi 
 tana kuka.

 dan Allah Ummi kibarshi haka kibar marinsa  wlh bashi da laifi ko daya akan dukan daya min laifi namishi ,shi km ya yanke min hukunci daidai da abinda na masa.

 ,Ummi Ta sake fashewa da wani sabon kuka yanzu dan kin masa laifi Zeenat shine zai nemi ya kasheki .

A zafafe deeni  Ya mike tsaye  yana huci ya dubi inda Zeenat din ke tsaye Sai mazurai take" a zuciye  Yace   ki fada mata  abinda kika min.
 bawai  laifi kawai  kika min yasa   na hunkuntaki haka ba ' yana shirin damkar makoshinta Ummi tashiga tsakiyar su .

deeni agabana zaka km dukan min yarinya wlh  kafita idona dukiyar wannan dukan daka mata Bai ishetaka ba Sai kazo gabana kakara mata . Yace wlh idan bata fidi abinda tayi da bakinta ba Sai na tabbatar dana karyata kafin nabar gidan nan . , atsorace zeenat tasoma yiwa ummi bayanin abinda tayi da bakinta .

Kukan Ummi ya tsaya cak tayi sororo tana duban Zeenat  jin abinda  take fada tamkar a mafarki ba gaske ba .can km Ummi ta sake rufe deeni da wani sabon fada dan ta zubar da ciki zaka kashe min ita , haka Allah ya rubuto cikin ba masu rayuwa bane a doron kasa  dan haka hakuri kawai zakayi da yadda Allah ya kaddaro. Allah zai sake baku wasu .

 deeni da ranshi yaga dagulewa ya baci da kalaman mahaifiyarsa. wacce yake ganin duk duniya bashi da tamkarta ,shi yake daita ita take dashi km yasan duk son datake wa Zeenat din bayansa yake  yasan ta dai fadi haka ne kawai badan ranta yaso ba. 
A sanyaye Yace yanzu first lov wannan kaddarace ko son zuciya?
 ta biyewa ra'ayinta tayi abinda ranta ke so shine zakice "haka Allah ya kaddaro' Ummi tashiga girgiza masa kai .
Kadai kayi hakuri nace bana son tashin tashina abar zance kawai .

 Yace bbu wani zance da za'a dan  Ga sakamakon abinda ta aikata min nan a hannuta na bata ,sai km tabi wani jirgin ba bana deeni ba .
,ya juya fuuuuuu cikin tsammanin bacin rai ya bude kofar ya fita tare bugo kofar da karfi .

 Ummi ta juyo 'ahankali tana kallon yadda diyarta ta dawo wata halita daban.
 ,tace yanzu Zeenat wani laifi na aikata miki da na cancanci kiyi min irin wannan sakayar .
Yanzu kin kyauta abinda kike yi  , gabadaya tsoro ya sake cika zuciyar Zeenat  Tunaninta ko dukanta Ummi zatayi dan haka tasoma ja da baya . Ummi tace Ina zaki Zeenat ni bbu abinda zan miki , Zeenat ta durkushe gaban Ummi tare da kamo kafafunta ta rike gam Tana kuka" Dan girman Allah Ummi kiyi hakuri wlh sharrin sheidan ne Ummi kiyafe min  wlh bazan sake kibawa yaya hakuri shima ya yafe min Dan takaicin Ummi rasa me zata km cewa Zeenat tayi dan haka ta rungumeta ajikinta suna kukansu tare  .


Kafin kace me labari ya bazu acikin estate Zeenat ta zubar da ciki .



Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun me naje ji kuke cewa wai Zeenat ta zubar ciki sau  ba adadi ?

 inji inna kakar  Zeenat .
Data shigo parlour habibu danta dukkansu sukayi tsit shi da matansa da yayan Zeenat din da suke uba guda "suna kallonta wai ba magana nake daku ba ,kum mayar dani tamkar wata yar isaka  kuna kallona.
 "mahaifin Zeenat ne ya yi karfin halin sauke ajiyar zuciya Yace nima yanzu yasir yake gaya min  .

inna ta fashe da wani irin matsanancin  kuka tare da daura hannu bisa kanta  tace wayyo Allah nashiga uku ni  patsima amman  anyi  gatalalliyar muguwar  yarinya dan ubanta dan  nawa ta  zubar tasan burin da naci akan cikin nan ,shegiya yarinyar ni da nake son naga nafi  kowa zuri'ar maza da mata acikin dagin nan shine dayake Yar iska ce  ta zubar ciki.
Kai yasir maza muje ka saukeni  a gidan inci uwarta har da kakarta ba indiya .
yasir ya girgiza kawai dan   gabadaya maganarta dariya ta bashi gashi bbu damar yin dariya  dan  ya hadiye dan yasan halin maseefarta Yace Ai Zeenat din ma  tana gida tun jiya .

 Tace shine dan an raina mu shiyasa  ita uwar rikon nata baza tazo tagamana "amman bbu laifi ta kada kai tana kokarin barin dakin tace naje dakaina can naci mutuncin jairar yarinya .



 Dadaren deeni ya tafi gurin big Dady sakamakon turowa da yayi yazo yana son ganinsa .

Zaune yake agabansa shida fk da yayansa mahamud Sai wasu daga cikin family deeni  yasawa big dady kukan  abinda Zeenat tayi masa kasa yarda big Dady yayi duk da yaji dama .  sai da faruk  dake zaune a parlour,n ya sake  tabbatar musu da haka ne jikinsu yayi tsanyi  big Dady Yace yanzu ita Zeenat din ce taiya aikata haka .


Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun from no there suka ji suka ji muryar inna  tana salati tashigo parlour ,n big Dady da gudu kmr an karota a rude tace kai zubairu kai  zubairu  kaga irin dukan da wannan mugun yaron yayiwa jikata tamkar Bai san ciwonta ba .

 big Dady dake alajabi abinda akace Zeenat tayi ya dago da fuskarsa  yana duban inna tare da nuna mata gurin zama. Zauna inna .
  ,zaman may zanyi Dan wulakanci bazan zauna ba .
deeni dake zaune yaja tsaki wanda sai lokacin inna ta farga dashi .
 ashe ma yana gurin .

 ta fashe da kuka tana kallo tsaitin da deeni ke zaune tace  Allah ya isa ban yafe ba yanzu ka iya jikata  irin wannan duka kmr zaka kashe min ita .
dan ta zubar da wannan wahalallan cikin naka may shirin kaita lahira .

,a zafafe deeni Yace Ai abinda naso yi kennan na aikata lahira sannan na kawo muku gawarta inyaso nima akasheni.

 cikin kuka  tace yanzu zubairu  kana jin abinda wannan jairin may mugun kan yaron yake gaya min ko.

To wlh duk shegen da Bai km dukanta ba Bai haifu cikin uwarsa da ubansa inji cewar inna  .

 big dady ya kalli  deeni Yace  bana son ka sake cewa komai .

sannan Yace inna ki zauna amiki bayanin abinda ya faru.

 taki zama sai maseefa take zabgawa akan andaki jikarta.

  bayanin me zaka min zubairu  byn nasan wahalallan cikin wannan jairin ta zubar ta hutawa ranta .

 da kyar big Dady yasamu ta ,zauna akamata bayani komai tundaga kan cikin farko da Zeenat ta zubar har zuwa na yanzu .


 tana gama jin ta mike tsaye Tana jan tsaki mtssss tare da   tacigaba da zagin deeni .
  Dan ta zubar da cikinka din baza  shine zaka mata irin wannan duka  , mara mutunci kawai  wlh bazan yarda ba ,


Ran deeni ya sake mugun  baci " dan haka a hassale  Yace da bazaki yarda ba sai kizo ki rama mata tunda dukan dana mata yayi miki ,zafi .

, zubairu kana jina da wanna gantalalan yaro ko.
Wlh  koban rama mata ba ,zamu barkar da Allah yayi mata bakar sakayar da bata da magani .

wlh ni karki dameni dan zan iya  huce haushina  akanki inji cewar deeni .

zaka dake ni nima ta matso gabansa tana zaka dakeni tantirin mara kunya kawai may dan banzar mugun halin tsiya .

 Sai da Big dady ya dakawa deeni tsawa sannan yayi shr ya rabu daita ,tana zuba maseefa iri iri.

 deeni ya mike da kyar yana kallon big dady miryasa can kasa Yace  sai da safe ni zan wuce ganin haka yasa shima fk ya mike yana mara masa baya .

Sai  huci inna take maza ka dawo nan ka kawo min takardar sakin jikata dan wlh bazata km cigaba da zama dakai ba mugu azalumi kawai.

Deeni dake shirin barin parlour,Yace tun yaushe aikin gama yagama  Ai ko baki ce ba nima bazan km ,zama daita ba.

 ,ta sake kurma kururuwa ihu yanzu  kasar min jika byn kagama moremata jiki to Allah ya isa wlh km sai kaga karshenka .

shi dai Bai km cemata komai ba ya karasa ficewa daga dakin  . 

Daidai kofar gidan fk suka ja suka tsaya faruk Yace gaskiya aboki banji dadin sakin dakawa Zeenat ba.
dan kasan Ummi zatashiga damuwa ,akan haka fk sakin Zeenat danayi  shine yafi alkhari da zaman lfy atsakaninmu ,dana dinga mata ciki Tana zubarwa a rariya gara nabarta kawai .
 ,fk Yaceto yanzu haka zaka cigaba da ?

,deeni ya daga masa  kafada tare cewa uhmmmm zaman haka zai fiyye da dai zama da Zeenat.
 nan dai fk yayita bashi shawara akan yayi hakuri ya maidaita tunda saki daya yayi mata , Yace Nagode sosai aboki zan duba maganar idan hakan zai yiwu  sai zuwa gobe kennan tare da yiwa junanasu.sallama.


Karfe tara daidai deeni yashiga gidansa ya haura sama ,a sanyaye ya bude kofar dakinsa yashiga yasoma cire shirt din jikinsa da dogon wando ya rage daga shi sai singlet da boxes.
 yayi kwanciyasa kan bed dinshi tare da runtse idanushin  yana jin zafin da radadin  abinda kakar Zeenat tayi masa.

 Ga tashin hankali daya baro umminsa ciki yarasa meke masa dadi a rayuwarsa .

Gabadaya komai ya dagule masa waje daya mafuta kawai yake nema.
 lokaci may tsawo ya dauka  kwance yana tunani abinda yaka mata yayi  batare da bacci ya dauke bashi ba .




MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
     💖💖💖
💗💗💗💗💗





AYSHA A BAGUDO



Assalamu alaikum warahmatul Allah wabakatuhu🤝🤝🤝🤝🤝

*Makaranta auren sirri ina may matukar baku hakuri domin zan dakata da novel din auren sirri anan har sai allahu ya kaimu byn sallah inshaallahu zan daura daga inda na tsaya inawa daukacin masoya wannan litattafin nawa murna da shiga wannan watan mai alfarma da albarka Allah yasadamu da rahma da alkharin dake cikin wata ameen ya Allah*



       *Tunatarwa Yana da kyau a garemu da muji tsoron Allah mu gyara halayemu mu shiga cikin watan Ramadan ina masu aminta da tasbihi Ga Allah ,lokacin Ramadan Allah na daure shidanu sannan km ana bude kofofin aljanna a kulle nata sbd haka in muna shaidanci to mune shaidanun kanmu sannan yakamata ace mun tsarawa kanmu lokacin ibada acikin wannan wata may zuwa wato watan ramadan zuciyoyinmu suke yaudaramu da kanmu muke yaudarar kanmu Allah ma daukakin sarki yace yaayyullazina amanu,to anan Allah Yana magana ne akan mutane   wa,enda kukayi imani da Allah, mu kau da kasala da lalaci mu rage bacci hira banza da surutun da bai dace ba da sauransu, domin mu samu lokacin ibadarmu Sosai duk inda Allah yace yaayyuhan nasu to Allah Yana nufin dukkan mutane walau musulimi ko kafiri azumi ibada ce da Allah kadai yasan ladansa Ga duk wanda yaji tsoronsa ya km yi shi da iklasi azumi ibadace may falala Lada wanda Allah kadai yasani ,to kunga ashe muminai suke bautar Allah da gaskiya idan kinyi sallah da sauran ibadodi domin  mutane su Gani suce kinyi to azumi fa na Allah ne shi Yana kallonki inma kinyi ko bakiyi bakiyi duk ibadar da mukeyi don ace muyi ko wani abu mukeyin riya don wasu suce munyi to musani muna afkawa cikin babbar kuskure ne munayi riya bamu da Lada ko kadan riya na daga cikin manya manya kanairai zunaibai don haka mukiyaye muji tsoron Allah karmu bata ayyukanmu na alkhari da da riya .musa hankali da kyau watanni goma shadaya muna cin muna sha ,muna  yin duk abinda ran keso ,Sai wata daya ne zai gagaremu mu tsaya mu azumce shi dayin ibadu acikinsa wannan shine watan da akwai daren wanda yake da  tarin falala ,mai tarin yawa muyi kokari mu riski wannan dare muna masu kiyamullai, allah  yasa mu dace da wannan daren ameen summa ameen*🤝🤝🤝🤝🤝




Page 53





A ranar sam deeni kasa bacci yayi saboda tsantsar fargaba da tunanin da yake ciki akan hukuncin da umminsa zata zarta akansa.
   " dan Bai san abinda zai faru  ba akan sakin da yayiwa Zeenat. farinciki ko akasin haka.

 ganin kwata kwata bacci yaki samuwa agareshi ne Yasa   ya mike 'ahankali ya  tashi tsaye  yashige bathroom , yayi alwala yazo yasoma jero nafiloli yana may kaiwa Allah kukansa .
  , koda ya idar sallah  ma guri yasamu yayi kwanciyasa.
   ' Sai daf da sallar asuba yasamu bacci ya daukeshi kwata kwata bacci daya samu baifi na awa daya  ba ya sake mikewa yayi alwalar sallar asuba yana zaune yana lazami har garin Allah yawaye  .


Misalin karfe  bakwai  daidai yayi   wanka sbd  yana son  fita da wuri sbd matsalar  hoidop din  da  ake fama dashi acikin garin Lagos sakamakon gyare gyaren titi da ake .


  yana tsaye agaban mirrow   yana  shirin  zuwa office amman  gabadaya tunani umminsa ya addabe zuciyarsa duk da ruhinsa .
   "ranshi a dagule yake shirya jikinsa sbd yasan umminsa nacan na fushi dashi Yana wannan tunanin   har yagama shirinsa tsab .



Zaune yake a cikin tafkeken   office dinsa   may zagaye da makeken tablet cike da tarin file files da takardu.

 system din dake  gabanshi yana aikin tura sakwanni ne" ya  dan  ture gefe  tare da afkawa cikin duniyar tunani abinda Zeenat tayi masa .

 hakika Bai san yadda zaiyi da damuwar data kunsa masa ba.
 , Sam yakasa hakura da abinda tayi masa Sosai yake jin zafinta har cikin zuciyarsa tsawon lokaci Yana zaune yayi zurfi cikin  tunanin .


Wani abokin  aikinsa manir ne yayi kundin balar shigowa cikin office din" byn nouking din da yayi tayi yaji shr ba respond .


 Zaune manir ya samu deeni  yayi shr yana duniyar tunani' kusan Kira biyu yayi masa" amman ko daya deeni  bai san yana yi ba Sai ana uku ne yayi firgigib ya ankara '
da an shigo office din.

 A wayance ya waske . Naunauyen ajiyar zuciya ya saki tare maida hankalisa sosai kan manir .

'Ahankali  manir yasamu gurin ya zauna akan daya daga cikin kujeru guda 2 dake ajiye dan zaman baki .
 Shr shima Yayi ya zubawa deeni  ido  kawai yana kallonsa tare da nazarinsa "tsawon lokaci suna kallon junansu batare da kowannesu Yayi tunanin  yacewa dan'uwansa komai ba .


   Har Sai da manir yayi karfin halin cewa  .

wato har yanzu dai matsalar Zeenat din ce taki ci taki ciyenwa?

 dayake yasan komai game da abinda ya faru.

 a ganina zuwa yanzu yakamata ace kasawa ranka salama akan maganar yarinyar nan . kayi hakuri kabarwa Allah komai .

deeni da Yayi shr kawai tare da kamo lip's dinshi na kasa yana cizawa 'ahankali'ahankali  shi kadai yasan yadda yake jin zuciyarsa da gangar jikinsa 'ahankali   muryarsa  a sanyaye  yace uhmmmm duk maganarta na damuna.
"  amman nafi   tunanin halin da first lov zata shiga ne kasan yadda Zeenat din take a gurinta .


Manir yayi shr ya jima yana jinjina girman alamarin sannan ya numfasa yace deeni Ina kan hanyata yanzu ta zuwa Ilorin  daman sallama nazo muyi .

 bbu wani hanzari dazan iya maka akan maganar ka matarka daya wuce..
 Sai km ya dan mike daga kan kujerar dayake zaune ya rankwafa gefen deeni  tare da kai  bakinsa daidai tsaitin  kunnen deeni,  zo kaji  wata magana.
  ,kusan minti biyu manir yayi Yana tsarawa deeni zance sannan ya dauke bakinsa yakoma gurin zamansa.
  "  a razanane deeni yake bin manir din da wani irin matsanancin kallon tare da  mamakin abinda Yace.
   manir yacigaba abinda  kawai zakayi  kennan karaba kanka da wannan damuwar dake damunka kada zuciyarka ta samu matsala .


'Ahankali deeni ya shiga girgiza kansa yana kallon manir batare da ya iya ce masa  komai ba .

 haka kawai shine maganin matsalarka Amman ka zauna kayi tunanin shawarata da kyau inji cewar manir .

Da kyar deeni ya iya bude bakinsa da Yayi masa nauyi Yace  anya kuwa manir zan iya abinda ka bukaceni da nayi kuwa?
  " manir Yace zaka iya mana Sai dai idan baka gadama ba.
 deeni ya sake girgiza kansa ,kai  bazan iya ba wlh ....


Manir ya mike tsaye  yana mikowa deeni hannunsa ' bbu dole fa cikin shawarata kaduba kagani  idan zaka iya kawai kayi "ni zan wuce Sai na dawo , jikin deeni  a sanyaye shima ya mikowa manir hannu sukayi musabaha .

manir ya wuce Yana cewa malam katashi tsaye kawai kayi abinda  ya dace ba kullum tunani ba .


Deeni ya jima zaune yana saka da warwara  akan zance da manir yayi masa wanda gaf maganar take da tarwatsa masa zuciya.

'Ahankali  cikin sanyi jiki ya , mike tsaye ya suke hannuwansa duka cikin aljihun wandonsa   yasoma zariya Yana zagaye cikin office din.
 'sannan '  ya dawo ya zauna a gefen tablet dinsa  yana jinjina girman alamarin duk ilahirin jikinsa sunyi masa mugun sanyi .'ahankali ya sake mikewa   ya koma kan kujerarsa ya zauna  yana son yacigaba da aikinsa  idanushi suka  sauka akan dan karamin fream din dake ajiye akan table.
ya zubawa umminsa ido kawai yana kallonta shi kansa ya amince tun ba yanzu ba umminsa na matukar son shi da kaunarsa fiyye da komai.
  " shima  km   haka yake matukar sonta tamkar rayuwarsa.
  " duk duniya ita kadai gareshi  'ahankali ya kai hannunshi ya dauki karamin fream din yana cigaba da kallon umminsa" yayi matukar kewarta " kusan kwana biyu Keenan rabonshi da sanyata acikin idanunshi wanda km hakan ta faru ne a sanadiyyar Zeenat ,bancin haka yasan zuwa yanzu da tuni umminsa ta nemishi da kanta.

 runtse idanushin yayi sosai Yana jin yadda kaunar mahaifiyarsa ke ratsa zuciya da gangar jikinsa "tsawon lokaci idanunshi na runtse  sannan ya budesu fes yana sake kallon umminsa  tare da  sake jin haushi da takaicin Zeenat  a ranshi.

Take yaji zuciyarsa tasoma amince masa daya dauki shawarar da manir yabashi Kodan samun natsuwasa da km kuntatawa zuciyar  Zeenat din .
sannu 'ahankali ya maida hoton Umminsa ma,ajinsa yacigaba da abinda ke gabansa .




Gabadaya parlour,n big Dady cike yake da manya  daga cikin  en'uwa  na family muhd bello khaliyal.

Big Dady ya kalli gefen da  Zeenat take  zaune rakube tare da sunkuyar da kanta kasa tana xubda hawaye .
" Yace yanzu Zeenat kin kyauta kennan da abinda kikayi ?
  mezakicewa mahalincinki idan kin koma gareshi ' ashe daman karamin tunani gareki bansani ba "Zeenat dai kanta na kasa tana cigaba da zubda hawayen nadama  ta kasa cewa komai big Dady ya girgiza kanshi kawai 'sannan  Ya maida kallonsa ga deeni  .

Kai km kuturu sarkin zuciya"  Ai ba a yanke hukunci cikin fushi kwata kwata bamu ji dadin hukuncin da  , son ranka da kayi ba .
 ,domin kuwa  har zuwa  yanzu a karkashin ikonmu kake, yakamata ace  ka kawo maganar gabamu kafin kazarta da komai .

Dan haka muma zamu nuna maka har yanzu kai din a karkashin mu kake km abin ikonmu.

Big dady ya sake juyowa inda Zeenat take " ke... saki nawa ya rubuta  miki?
 cikin kuka muryata na rawa tace nima ban sani ba .

Ina takardar sakin take 'ahankali ta tura hannuta ta zaro farar takardar daga gefen zaninta ta Mika masa .

Big Daddy ya karba ya bude Yana dubawa  yaga ashema  saki daya ne  ,take yaji wata natsuwa da kwanciyar hankali sun shige shi hamdala yayiwa Allah sannan ya sake duban deeni .
yanzu me yakamata kayi tunda saki daya ne?
 Bbu tsoro ko shakka ,deeni Yace  bbu wani abu da zanyi da wuce  kawai  Allah ya hada kowa da rabonsa .


Wlh wlh baka isa ba say kamayar daita sautin  muryar inna ta karade dakin .
 jikata ba zata zama bazawara ba' byn kagama moremata jiki ba eheeeee.
kaji min yaro da muguwar mugunta da bakar zuciya kmr irin ta firauna.
To ,wlh baka isa ba ,ke km fadeela kina zaune kin yi shr kina jin abinda wannan gatalallen "dan" naki yake fada .

Ita dai Ummi shr kawai tayi  Tana kallon  tsaitin da deeni 'ke zaune dan batasan abinda zatace ba  ,km  koma tana da abin cewa bazata iya da jarabar inna ba . 

Inna tacigaba ko baka maidaita jikata ba zata  samu wanda yafi kyau da kudi da komai "amman wlh tunda kagama moremata jiki Sai ka maidaita gidanka.
   ban da ma kaddarar aure mai jikata zatayi da kai tsami gaye da kai da tsayi awa bishiya .

abin dariya abin takaici a wulakanci deeni ya dinga  kallon inna Yana jin wani irin zafi a kirjinsa tamkar  zuciyarsa zata buga.

 a zafafe Yace to baza'a maidaita ba say kiyi duk abinda zakiyi.

 ,ni kake cewa bazaka maidaita ba , zubairu kana jinshi ko to wlh bada ni kake ba da wannan ta zaune kake tashiga nuna Ummi da hannu ,mara kunya yaro kawai may dan karan taurin kai awa na mutane farko .

 Deeni ya bude baki big dady ya katse shi ta hanyar  buga masa tsawa.
" mahaifiyar tamu kake kokarin yin sa,insa daita ,kar ka sake na sake jin bakin ka kaji dai nagaya maka  .



Dan Allah inna kiyi hakuri  Ya isa haka "  

Inna tace bai isa ba  zubairu , nace bai isa ba kai ya kalli tsabar idanunka ya gayamaka haka ko yagawa uwarsa haka ,say ni daya raina ko dan haka ko yamayar daita ko km wlh koto ce zata rabamu dashi  tare da fashewa da wani mugun  kuka ,wlh Allah yaisa tsakaninmu dakai deeni bamu taba yafe maka ba .fk yatashi ya mike dan takaici inna ya bar parlour,n .

 Da kyar big Dady yasamu ya rarrashi inna . ranshi a bace Yace yanzu yanzu  ka maida matarka inji cewar big dady .

deeni Yayi shr Yana kallonsa Yana huci .
inna tace bakaji  magana ake maka ba" kinbabbe kawai Sai faman huci kake kmr ,zaka hadiye mutane.
" deeni ya tsareta da rikitattun idanushin  kawai zafi zuciyarsa da kirjinsa suke masa .haushi da takaicin inna suka taru suka mamaye masa zuciya.

inna tace daina kallona da wayan nan mugayen idanun naka masu kama dana mage , munafiki kawai.
 
 Zeenat ce Sai Sai ta koma gidanka ko kaki ko kaso uhmmmm.
  zeenat dai kanta na kasa Sai risgar kuka take tana addu'ar aranta kar Allah Yasa  deeni Yace ya maidata.
  duk da tsananin son da take masa bazata iya juri zama dashi ba cikin wannan situation din ba.
 yayinda hawaye ke cigaba da bin kuncinta .

Wai wasa ake dakai ne ka tsai da mutane kana bata mana lokacin kowaye sa,anka anan inji wani kanin mahaifin deeni.
 shi kuwa  big dady tunda yayi maganar karshe bai sake cewa komai ba Sai idanu daya zuwaba deeni Yana kallonsa ko kifta ido baiyi  .

'Ahankali deeni yake kallon duk ilahirin wayan dake zaune a parlour kaf dinsu iyayensa ne  idan aka dauke fk wanda shima sako yashigo kawowa ya iske ana maganar ,'ahankali yacigaba da kallonsu idanunshi suka fada cikin na umminsa wacce gabadaya tazamo kalar tausayi, wasu abubuwa yake hangowa daga cikin idannun umminsa masu kama da rarrashi da ban hakuri .wanda suke nine a bukace take da son ya aikata abinda akace masa Yayi.

,ahakali ya mai da idanunshi kasa tare da sauke ajiyar  zuciya. muryasa can kasa kasa Yace na ...mai daita...


Inna taja tsaki tare da Mikewa tsaye munafiki  kawai ' daman can kana sonta iskanci ne kawai irin na  mai shayi ya tsaida uwarsa ya tsai fatan shayi , tsami gaye kawai ..
Deeni  ya dago rikitattun idanushin suka hada ido da Ummi tayi masa gargadi da idanunta alamun kar ya sake Yace Komai



Bye bye bye until after sallah missing u guys 


MMN SUDAIS CE
[6/29, 7:51 AM] 0mmer Farouk: 💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
       💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO





*Assalamu alaikum warahmatul Allah inawa dinbin masoya wannan littafin barka da sallah da fatan kunyi  sallah lfy Allah ya karbi Ibadunmu da mukayu cikin Ramadan Allah  Yasa muna cikin bayin da Allah  ya, enta daga wuta zuwa jannatul firdaus Ameen ,kmr yadda nace zan cigaba da type din wannan labarin nawa byn sallah, to a yau ne alkawari Allah yacika Allah ya nuna mana lokaci ,hakika may hankali da tunani ne kadai zai Gane yadda duniya ke gudu, Allah Yasa mudace yabamu ikon cikawa da kyau da imani ,km Allah yabamu ikon aikata ayyukan alkhari*


Page 54



 'Ahankali Deeni  ya dauke  rikitattun idanushin daga cikin idanun umminsa  ya  maidasu kan inna dake tsaye tana fama , babatu da sambatu iri iri  'km duk cikin taron mutane dake zaune a parlour bbu wanda yayi yunkurin dakatar daita daga maganganu da take .

  zuciyar Deeni  cinkushe da haushi  hade da takaicin inna" bakinciki ganinta  ke sake nunkuwa a kasan  ransa yayinda yashiga da zuciyarsa  wani irin zafi da suya zuciyarsa ke yi.
 " so yake  ya murje idanunshi Tare da cire kunyar jamar dake zaune a gurin, sannan  ya  zage kunjinsa ya zabga mata rashin mutunci fiyye da irin  wanda ta iya .
,amman Ina...tuni  idanun umminsa dake yawo a kansa" yasa ya  kasa aiwatar da komai sakamakon  gargadin dinsa datake ta hanyar kwayar  idanunta .

 dan haka  daya rasa yadda zaiyi ya fanshe tarin  wulakancin inna gareshi,sai   kawai ya  shiga aikawa inna  da wani irin mugun Kallo may hade da harara .

Wanda yasa  ,ita kanta inna dake tsaye har lokacin sake  jin  haushin DEENI  da takaicin irin kallon kaskancin da wulakancin dayake aiko mata dashi .

  "Km hakan    yayi sanadiyyar kara  hassalata ,  dan haka a tsawace  Tace ni daina kallona ,ka wani  tsareni da wa'yan nan mugayen  idanun naka  masu kama dana mage  , kana aikomin da kallon wulakancin to bada ni kake da wannan uwartaka ta zaune kake... ehee.. takarasa fadar haka tana may  jan mugun  tsaki a fili   tare da soma  kokari kamo  hannun Zeenat .


Ke tashi mu tafi , can sashina ko kya samu ki maida jikinki ki murmure daga wannan bakar ramar da kikayi " inna  tasoma kokarin mikar daita Zeenat  tsaye . 
Yayinda  Zeenat din km taki mikewa Sai ma sake cure jikinta da tayi gurin guda  alamun babu inda zata .

 ,au bazaki mike mu tafi can gurina ba ,kinfi son ki zauna inda za'a dinga miki izaya da  tsotse miki jinin jiki.
 Dan zama da wannan mugun azalumin kadai ya,isa yasa jinin   jikinki ya kafe batare kowa yasani ba "ni tashi mutafi .

 ,juyin duniya nan  inna tayi da Zeenat kan ta tashi su tafi can part dinta " amman  kememe Zeenat taki tashi .
 ganin haka yasa inna  sake tunzura, ta cigaba da tsayuwarta  tare da surfa masu maseefa iri iri km har lokacin bbu wanda yaiya cewa komai

 big dady ne "ya dan  dago idanushi yana  duban  sashin da  inna ke tsaye Tana surfa maseefa ,ya xuba mata kawai  domin    shi kansa big Dady rasa me zai cewa inna yayi...

' kusan minti goma ya dauka Yana kallonta batare da yayi yunkurin dakatar daita ko ce mata wani abu ba ' kafin daga baya  ' ya gyara zamansa Tare da  numfasawa. cikin tsantsar  ladabi da laushin murya  yasoma magana,   Dan  Allah inna kiyi hakuri ki tafiyarki abinki "tunda yarinyar nan Ta nuna  bazata biki ba.

, Say da inna ta tabe bakinta tukun  sannan tace "yo Ai ka kace min  nayi tafiyata man " tunda fadeela da danta sunfini daraja da kima a idanunku" duk irin wulakanta min jika  da wannan banza yaron nata  yayi  baku Gani ba Sai na laifin zakugani  .

,big dady sam  Bai damu ko jin mamakin  abinda inna tace ba, dan yasan kadan daga cikin aikinta. domin zata iya fadar  fiyye da abinda yafi haka  ma.

Dan haka big Dady  Bai damu da abinda tace ba ya kara   kwantar  da murya cike da girmamawa ya sake cewa  ,  Dan girma Allah inna kiyi hakuri kiyi tafiyarki tare da yiwa yaran nan fatar alkhari a rayuwar aurensu tunda komai   yazo da  sauki saki daya ne  yayi mata . Km ya maidaita .
 Duk ma da abinda Deeni yayi mata Ai bai laifi bane  tunda ita tajawa kanta . 

 ,inna  ta katse big Dady Ta hanyar daga masa hannuta,dakata...  ya isa haka karka cika min kunne" naji zan tafi amman wlh wlh kaji na rantse ,to  kagayawa wannan  gantalallan "dan 'naka yakiyaye ni" kar ya km yin gigin kai hannushi da sunan sake  taba min lafiyar jikata.

 Domin ita ba jakar gidan ubansa bace .
Big Dady yace shikennan kiyi hakuri ki yi tafiyarki zan gaya masa .

 Inna Tace da dai yafi dan wlh idan ya km yunkurin kai hannushi jikinta ba yarda zanyi ba .

  ,  da kyar da Allah da rarrashi, big Dady da sauran mutane dake zaune a parlour   aka samu inna ta fice daga parlour tana zage zage.

 'ahankali  big Dady Ya sake  numfasawa tare da  duban inda   Deeni  ke zaune ya hade  fuska tamkar hadari   suna fuskartar juna ,tsawon lokaci big Dady ya dauka Yana dubansa  ,kafin daga baya yayi masa fada sosai akan irin hukuncin daya dauka akan Zeenat din sannan daga karshe ya  bige dayi masu  nasiha  mai shiga jiki  shi da Zeenat ,akan su taru su zauna lfy.

  Yace deeni Kayi hakuri akan laifin da Zeenat ta aikata a gareka, hakika munsa  bata kyauta ba amman   ka dauka daman can haka Allah ya rubuto  cikin data zubar maka   ba masu rayuwa bane a doron kasa.

 Dan haka kayi hakuri   ku zauna lfy  hakan kadai  shine muradinmu da  km kwanciyar hankalinmu dana umminku gabadayan . 

Sauran en'uwa ma kowa ya tofa albarka bakinsa sannan 
  ,Jiki a sanyaye  Deeni yace yaji  tare da yin musu  godeya , duk da  ran nan nashi , in yayi dubu to a jagule yake .
da kyar ya samu ya  kokarta ya mike tsaye dan kokarin barin parlour har yakai daidai bakin kofar fita  .

  " cak yaja ya tsaya jikinsa har wani shake yayi  sakamakon jin sautin  muryar umminsa mafi soyuwa a zuciyarsa .
' ,kaje gida kajirani gani nan  zuwa yanzu, abubuwa dayawa  suka zo masa  tare da tsaya masa a rai .
 jin yadda ummi  tayi maganar  kadai yaisa yasan yadda ranta yayi kololuwar    bace ..
 dan gane da abubuwan dake faruwa a atsakaninsa da Zeenat kasa cewa komai yayi sai   ,   kansa kawai daya  iya daga mata alamun yaji 'sannan  Yakarasa barin parlour .



Byn kmr minti ashirin Zaune Ummi da Zeenat  suka  taddashi kan kujerar one siter hannushi rike da  waya yana daddannawa " a yadda yake operating din phone dinsa   zaka dauka kwata kwata  baya tattare da wata matsala ne" ballanantana wani abu makamanci damuwa , amman a hakikanin gsky kallo daya  zaka yi masa kasan cewa  yana tattare da kunci may tarin yawa .

 ,a fusace Ummi take kallonsa ganin yadda Ya hakince tamkar Bai san da tsatuwar wasu halitu a gurin ba.
  ,' yayinda  gabadaya ranta a dagule yake da abubuwan da ya dinga yiwa inna a gaban dangi .
  wanda inda wani ne yasanar daita zai iya yin abinda yayi" zata iya ransuwa da Allah akan sharri aka,a masa ,amman Sai gashi a gabanta komai ya faru.


 ahankali DEENI ya dago rikitattun idanushin  dasuka gama canza  kala tsabar tashin hankali dayake ciki " ya zubawa ummi yana  kallonnta ..

Ganin haka tasa  , ummi  sake hade ranta tamau dan batason yakawo mata rainin wayonsa dayasa ba "sannan  ta cigaba dubansa  .
 ,'tare da cewa  yayi maka kyau... Deeni, da duk ma  abinda kayi min,  na gode  matuka  "tun daga kan  dukar min yarinya dakayi tamkar kasamu baiwa  tare da hado min ita da  takarda saki  har kawo abubuwan da suka faru a yau .
  Dan wulakanci ma  yau kusan tsawon  kwanaka uku kennan rabon daka Tako kafafunka cikin  gidan nan  . tsabar kagama rainani   .

shr yayi still yana sauranta ya kasa koda furta mata daidai da kalma daya ce .

 , Ummi ta dubi inda Zeenat ke tsaye  wace gabadaya atsorace take dangane da  yanayin rayuwar data jefa   yayan nata ciki .
 ,ummi tacigaba' ai kinga   irin abinda nake gudar miki a cikin  aurensa, wahala da zaman kunci tattare da nadama"  Amman  kike  nace akan kinji kin Gani '  bbu wani abunda zai faru Sai alkhari  "  yanzu wa gari ya waya.
 dubi yadda kika koma dan girman  Allah tamkar wacce aka  hako daga cikin kabari .

  Da gani ba say ma an tmby ba   nasa zaman hakuri da kunci kikeyi agidansa dan nasan may hali baya  canza halinsa .

Deeni dake zaune yayi shr tare da cigaba da duban ummi kawai  batare da yace mata komai " dan ma rasa  abinda  zaice mata yayi km yana son ta fahimce shi  tasan duk abinda take tunani akansa ba haka bane amman Sam yakasa magana  .
 Ummi  ta sake juyowa inda  Deeni ke zaune  suna fuskantar juna  dashi . 

" Tambayar da zan maka yanzu nake son ka amsa min d eh ko A'a.
 daman can  ba  kai ne da kanka ,ka nemi auren Zeenat din a gurina ba?  

.'ahankali Deeni ya dagawa Ummi kansa .alamun  shine ya furta Yana son ta aura masa Zeenat din .

 Ummi Tacigaba To yanzu dan ta zubar da ciki ne yasa har ka iya  mata irin wannan dukan mutuwar ?
 Km  har da  ikirarin zaka kashe min Ita dan baka san ciwonta ba .

  Ko kana tunanin  idan ka mata illa zan barka ne kaima .
   
Kai gaka sarkin  en zuciya madadin ka kawo maganar gabana nasan yadda zanyi solving din matsalar batare da kowa yasani ba ,  shine ka tuzartata Tare da zartar  da hukunci ta hanyar  azabtar min da yarinya tamkar kasamu baiwa.

 Sai lokacin deeni yaji wani  kuzarin yazo masa Dan haka cikin   , tsanyin murya tamkar may shirin zubda kwalla Deeni soma magana  " kwarai first lov  nayi kuskure guda daya narashin sanar min ki    kafin zartar da komai  amman na rokike   kiyi hakuri.

 Amman ta ya zuciyata zatayi sanadiyyar barinta cikin kunci da cuta alhalin nasan amanarta kika damka min  acikin tafin  hannuna' ya fadi haka tare duban  tafin hannun nashi da kwayar idanushi 
  , indai  akwai wanda na cuta to kece da bansanar miki da abinda tamin ba ,kafin na zartar da hukuncina akanta . amman ki gaya min me yakamata nayi byn na kamata dumu dumu da laifin zubar min da ciki har Sau biyu tare da shan maganin hana daukar ciki Sau  ba iyaka .


Cikin zafin rai ya Kamo lips dinsa na kasa yasoma  cizawa da karfi sakamakon    hawayen dayaji  yana kokarin son zubo masa.
" wani irin nauyin zuciyarsa tayi "yana ji yadda kirjinsa ke masa zafi  da ciwo tamkar an daura masa dutse may shege nauyi a sama kirjinsa ,     .


 , Da kyar yasamu yacigaba da magana. mutane na gudun tsautsayi amman ni na zauna da nawa tsautsayin batare dana sani ba 'bana da miradin danayi gida biyu amman nayi tunani  indai tsautsayi ne   ya hau kaina  "to itama  dole tsautsayi  ya hau kanta .


,ni muradina gida daya ne kawai nake da  bukata amman tunda itama ta cin nawa zuciya gobarar datayi sanadiyyar tarwatsa min zuciyarta tarabani da abinda nafi so a rayuwata  ... to tabbas nima   say na nemo may kashe min wannan wutar .
ta hanyar musguna mata  .


Kada ka taba karya zuciyar mace kada ka taba  ruguza iyali domin cika muradinki first lov NASURULDEENI dinki babu abinda bayawa Zeenat na jin dadin rayuwar aure "tare  da sanyata cikin farinciki mara misaltuwa.

 burina na kyautata mata.
' ta yadda zan samar da murmurshi  da farinciki a fuskarta amman firt lov ki duba kiga da  irin abinda ta saka min dashi.
  gata nan tsaye  ki tmbyeta  ban kasance may adalci agareta ba A dan ,zaman da mukayi daita .'
ahankali ya mike tsaye hawaye dake makale a idanushi sukayi nasara zubowa   batare daya shiryawa hakan ba.

shin na  zalinceta ko daidai da rana daya ne.
 ki tmbyeta first lov amman duk da haka idan kina ganin banyi daidai ba akan dukan danayi mata to zaki iya rama mata ki hukunta ni  ta duk  yadda kike so.

 kece kikayi sanadiyyar kawo ni duniyar nan...
  ko mayar dani lahira kike son yi "ahalin yanzu ba zance miki komai ba.

 wlh Deeni dinki bazai taba cewa komai ba. Hawaye yacigaba da bin fuskarta .

 km ba,zan miki wata jayayya ba abisa Ga hukunta ni da zakiyi ....
 

 ,jikin  Ummi yayi maseefar  sanyi dangane da jin  Dukabinda dan nata ya zaiyana.

  ,jikinta a sanyaye  takaraso kusa da tillon "Dan" nata tana kuka  itama tare da  dora  hannuwanta duka ta riko fuskarsa dashi tana kallonsa.
 wani irin matsanancin tausayi tattare da  kaunar "Dan' nata ne  taji Ya sake   nunkuwa acikin  zuciyata .
  Yayinda kuka mai karfi ya  kufce mata" from no where  kawai ta rungumeshi ajikinta tana cigaba da kuka shima kukan yake ,yarona kayi  hakuri.
" kukan ya isa haka kabar kuka kayiwa umminka uziri bisa Ga zarginta gareka.

 amman  duk da haka umminka na neman alfarma gareka  ,na  rokeka Dan Allah kada ka juyawa Zeenat baya ,ita din  diyata ce halak malak duk duniya nan  batada wata uwar data fini.
 ,  ka cigaba da  hakuri daita "inshallahu zata canza ,zata canza ,zan sata ta canza  kaji yarona......
" Allah yayi maka albarka yadda kake faranta min ,kaima Ina maka addu'ar Allah yabaka ya'ya wayanda zasu maka fiyye da haka .

   Zeenat ,dake tsaye taji hawayen tausayin su gabadata , nabin kuncinta, tasan  hakika ta tafka babban kuskure a rayuwarta  .
' tare da  aikatawa kanta mugunta   mafi muni da radadi wanda batasan tsawon lokacin dazata daina jin zafi da ciwon  abinda ta aikatawa kanta. Da 
wa yan nan bayin Allah ba .

 Hakika ummi uwace guda a gurinta har da rabi .
 ,kodan ummi yaci ace tayi hakuri da juriya tabar cikin jikinta  .
,gabadaya tausayinsu ne ya taru ya mamaye mata  zuciyarta yayinda hawayen idanunta  suka cigaba da zuba shaaaaaaa.................... 

,kuka ne mai karfi yaci karfinta tasa  hannuta  duka ta toshe bakinta dashi   tare da rugawa da gudu ta haye saman up stairs din ummin tana gunjin kuka   .

Kiyi hakuri first love  da abinda zance inji cewar Deeni  dan  girman Allah first love kimin uziri na kara aure domin zama daga ni say  Zeenat , zai haifar da mummunar damuwa   wanda zaisa mudinga samun  matsala daita  a yadda nake jin zuciyata.

, uhmmmm Deeni bbu wani matsala ko damuwa  daza'a km samu a tsakaninku muddin Ina raye ni kaina zan koma can gidan naku" nacigable da  zama tare daku  har sai  Sanda  naga zaman naku ya daidaita.

' maganar  kara aure km bazan hannaka ba domin hanaka daidai yake . Dana shiga hakinka  tunda kayi Niyya , say day kasani bazan taba barinka ka aure matar da nasan   cewa zata fi Zeenat dina da komai  ba arayuwa.

  , say  day idan ka amince  zaka aure kasa Zeenat  din.
 Tukun zan amince da kara aurenka  . 

Km abisa sharadi  duk yayan da matar za'ta haifa maka ,zasu zauna matsayin na  Zeenat ne muddin rai  matsawar ba nata tasamu ba .

dan haka Sai km tayi kasa kasa da muryata ta yadda bbu mai jinsu tayi masa magana .

Wanda yasa Deeni yin sororo  kawai  yana duban umminsa tare da nazarin maganarta tsab .
  "exactly irin  dai abinda abokinsa manir  ya fada masa ne  .
 ,say gashi itama umminsa tazo masa da irin maganar wanda shi sam a ranshi  yake jin rashin yuwar yin haka .

,'ahankali ya samu guri ya koma ya zauna jagwab.. akan kujera  yana may fidda numfashi sama sama.. domin maganar tayi maseefa girgizasa  tare da daga masa hankali "har ma tana barazanar tarwatse masa zuciya.
,da kyar yasamu Ya daidaita' numfashinsa ya dawo normal.

  ,itama Ummi guri tasamu nan kusa dashi ta zauna  tare da kamo tafin hannushi cikin nata Tana may nazarin yanayin daya shiga  ,ka natsu ka kwantar min  da hankalinka Deeni  kada kasawa zuciyarka   damuwa.
 kasani a tashin hankali. wannan bawani abu bane so big kmr yadda ka dauka ,kusan anayin irin  hakan Sosai a wannan duniyarta tamu .

Sake , dago rikitattun  idanushi yayi  yana kallon umminsa dasu take yaji wani ya tsigar masa a kanta kirjinsa ya rike gam Tare jin wani abu ya tsaya nasa a wuya  yakasa kwakwarar motse ballanantana yace  mata wani abu.

'Ahankali ' ummi ta numfasa sannan  tacigaba maganarta   irin wannan auren kawai  zan iya yarje maka kayi.

 ,dan  bazan taba yarde maka ka  auro matar danasan  zatafi Zeenat da komai ba, baya Ga kaskantacciya   mara galihu ....

 ,da kyar deeni yasamu ya hadiye abinda yaji ya tsaya matsa makoshinsa sannan 'ahankali ya iya bude bakinsa tare da kiran sunan umminsa  haba first lov.....  ta yaya da matsayina da girma zan bige da auran kaskantacciya km mara galihu ? .

Ummi ta katse shi ta hanyar daga masa hannuta, sanin halinka da nayi ne yasa haka .

da km sanin  burin  kalar mace dakake muradi tun farko  yasa nace haka ,ko kamanta kataba gaya min irin kalar  mace dakafi son ka aura kafin daga baya kadawo ,kace min Zeenat kake so.. wanda ni bansan dalilin dayasa kacanza ra,ayinka ba.

Dan haka , bana son sake  jin komai daga bakinka ,muddin kana bukace da kara aure kmr yadda ka bukata" to say dai ka auri irin kalar yarinyar danake so....

 idan km kaga bazaka iya ba , kana iya cigaba da zama tare da matar har sanda Allah zai km azurtaku da samun wani cikin......
  "cikin sanyi jiki ya dinga  girgiza  kanshi kawai yana jin tamkar mafarki yake ba gaske bane  wai yau shi umminsa ke shirin shiryawa irin wannan auren  sbd farinciki Zeenat.....
 ,shin wani irin KAUNACE a tsakanin   Zeenat da ummi ,ai Bai sani ba a fali yayi maganar Sai ji yayi ta bashi amsa ,da kauna irin ta "da"  da uwa  numfashi ya sauke yashiga sauke 'ahankali'ahankali  yayi shr tare da sake lulawa duniyar tunani .


Tsawon lokaci sannan ummi tace kayi shr batare da kace min  komai. amincewa da auren irin yarinyar danake so "ko km  ka fasa auren gabadaya .

   Xuru yayi kawai  yana kallon mahaifiyarsa.
 abu na farko dai  baya jin zai iya duka abinda umminsa ke so ...

hakura da auren dayakeyi . tamkar Bai ruguza zuciyar Zeenat bane ,sannan km auren irin kalar yarinyar da umminsa ke so tamkar zubar da kimarsa da ajinsa ne .

shi da yafi bukatar auren maccen data amsa sunanta mace ta yadda Zeenat din karan kanta zata raina kanta .Amman Sai gashi ummi takasa ta tsare ta neman kwafsa masa .

Amadadin ya hakura duka  gara ya auri koma wace irice mace ce  kodan kuntatawa  zuciya Zeenat.

Domin  shi karan kansa yasan irin yadda Zeenat ke tsantsar kaunar shi da kishinsa , bubu abinda zai haukatata a tashin farko  daya wuce taji zai kara aure .
wani tsanyi da farinciki ne suka ziyarci zuciyarsa   a lokaci daya , tamkar wanda akawa albarshir da gidan aljanna .

 take yaji Ya amince da hukuncin umminsa .
Dan haka ya dago da rikitattun idanushin suka hada ido da umminsa 'ahankali   ya bude bakinsa Tare da cewa  shikennan first lov ,badamuwa  na amince kiyi komai kawai kmr yadda kike so ,kawai.

Ummi  tace very  gud Sai day km zanso  maganar  ta tsaya iya nida kai ne kawai bance kasanarwa da kowa ba " koda kuwa faruk ne.

 , Zeenat kuwa  idan lokacin  daya kamata tasani yayi ni da kaina zan sanar mata.sai   abu nagaba wanda umarni ne  zan baka ba shawara Ina son Zeenat tacigaba'da karatunta sannan km ka canza mata motar hawa shi deeni zugun tayi yana kallon ummi abubuwan nata sun daina bashi mamaki sun koma bashi tsoro ,'runtse  idanushin yayi Tare da cewa yaji ummi ta Dan murmusa jin ya amince tace  Allah yayi maka albarka ya albarkaci auren dazakiyi da kyar deeni  ya iya bude baki ya amsa da  Ameen  .



MMN SUDAIS CE
[6/29, 7:51 AM] 0mmer Farouk: 💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO



Page 55


Cikin wani irin  yanayi   wanda kwata kwata  ummi bata taba ganinsa ciki ba ya mike tsaye tamkar may koyan magana ya bude bakinsa yanawa ummi  sallama.
    "firt lov ni zan wuce gida yasoma taku cikin   isa da kasaita don barin dakin.
 , cikin sanyi murya ummi takira sunanshi DEENI.....Dan tsayawa yayi Tare da juyowa suna fuskarta juna da ummi idanunta ,ta xuba mishi kawai  Tana kallonsa tare nazarinsa ganin yadda gabadaya yanayinsa ya sake  sauyawa  cikin Dan  kankanin  lokaci   .


Yasa tace Ka tsaya kaci abinci Dan da alamun kana tattare da  wunya ,inyaso  zuwa anjima Sai ka wuce gida ko...shr  kawai yayi  yana kallon umminsa.

 hakika  umminsa tafi kowa sanin koshi waye Ta fannin halayyarsa  da abinda ke tattare dashi.

 Sai dai ,shi sam baiji zai iya sawa cikinsa komai  a halin dayake ciki  damuwarsa dayake tattare dashi  , kadai ya ishe sa" ba Sai yaci wani abu  , yafison  yaje gida kawai domin  yana bukatar sake nazari akan maganarsa da ummi.
 ' Dan haka   ya Dan narkar da fuskarsa  alamun baya da bukatar cin wani abu  .
  "bata rai ummi tayi ganin yadda yayi ,sannan ta Mike tsaye ta nufi hanyar kitchen .
  kabani  nan da minti goma yanzu , zan gama hada maka abinda zakaci kaji sojana ta fadi haka tana karasa shiga kitchen.
  yasan halin ummi sarai tamkar wuyan cikinsa  muddin tace Ga abinda take so ,to kuwa bata  muradin mutsu ko wani  jayyaya " Dan haka jikinsa a sanyaye ya juya zuwa ga hanyar step .



'Ahankali yashiga dakinsa" tsit ko Ina  ba  motsin komai "inda sabo ya rigada yasaba da rashin son hayaniya. daman shi mutun ne .
  "ba mai san hayani ba ballanantana km a part dinsa" komai yana nan tsab kmr yadda Ya bari  tamkar yana rayuwa a cikin dakin "wanda yasan wannan  duk cikin kulawar    umminsa ne sbd macce mai tsananin tsafta  da kyankyami .
  " kai tsaye bedroom dinsa ya wuce  ,yasoma  cire kayan jikinsa yaja towel ya daura Tare da shigewa bathroom ya sakarwa jikinsa shower yana fitowa Bai wani tsaya shafa mai ba .
  
ya bude wordrob dinsa.
 nan ma komai tsabtsab iske komai  Sai kamshi turarensa dake tashi a gurin ,  wani irin sanyi da dadi  yaji a ransa.
  " take kadan daga cikin damuwar dake tattare  dashi ta ragu .
'ahankali yasa hannu ya zaro jallabiya  coffee colour ya zira a jikinsa ba karamin kyau ta maisa ba .


 fitowa yayi daga  dakin nasa ya wuce kai tsaye ainihin main parlour din gidan ,ummi ya iske zaune ita da Zeenat suna magana kasa kasa.
"  duk da Bai san abinda   suke Tautaunawa  ba ,amman  jikinsa yabashi   maganar shi suke yi   .
Dan haka "kallo daya yayi musu ya dauke  idanushin akansu' batare da yace komai ba ,direct to dinning area ya wuce , yana jin yadda kamshi abinci ke tashi ta koina a gurin da dukkanin alamun umminsa tagama shirya masa abinci kmr yadda tace.
, ya zauna ba dan yana bukace da son cin wani abu  ba Sai Dan faranta ran umminsa.

 shr yayi Tare da runtse idanushin yayinda zuciyarsa ke bugawa da sauri da sauri 'ahankali ya kamo lip's dinshi na kasa yana dan cizawa sannu sannu. 


  Maganar da  Ummi keyi da Zeenat kuwa , bawata magana bace, illa fada da take sake yi mata akan abinda tayi Tare da bata shawarar  hanyoyin da zatabi gurin  shawo kan  mijinta cikin sauki .
 , sosai jikin Zeenat din yayi sanyi likis..
 ita kanta tasan" inda ummi bata kasance er,uwa,ce Ga mahaifiyarta ba ,hakika   yaci ace yadda Ta zubar da cikin jikinta ummi  tasa danta yakarasa tsinke igiyoyi aurensa akanta.
 amman Sai gashi  hakan bata faru ba .
Sai ma nusar daita da take akan yadda zata sake mallakarsa a tafin  hannuta.
Ummi dabance acikin mutane km zuciyarta may kyau ce ba kmr ta irin sauran mutane  ba km Allah yayi ta may tsananin zumunci ce .
  ummi   takarasa zanceta " da maza tashi kije ki kula da mijinki.
  "km cire wannan tsoron nasa danake hangowa   acikin kwayar idanuki.
Da kyar  Zeenat tasamu ta mike Tana may  dagawa  Ummi  kai alamun taji .


Kusan minti goma yayi  zaune a dinning table batare da yasan takamaimai akan  abinda  suke zantawa akai ba.
Ganin yadda umminsa tabar shi gurin zaune  tamkar wanda bashida aikin yi ,yasa  ransa yasoma sosowa.
   yana ji a ransa da zai iya zubawa  kanshi abincin , dayayi yaci yakama gabansa Dan kwata kwata baya kaunar abinda zai sashi zama inuwa daya da Zeenat .

cikin haka  ya jiyo takun alamun  ana tahowa dinning wanda ya tabbatar kansa  ba umminsa bace.
  Zeenat  ke tahowa garesa Dan  yasan takun kowanne daga cikinsu cikin sanyi jiki takaraso har  inda yake gabanta na wani irin mugun faduwa. tarasa dalilin  wannan maseefar da duk sanda zataga wannan yanayin na  DEENI  zuciyarta ke tsinkewa ,jarumta ta arowa ta mannawa  jikinta cikin dakiya tasoma   kokarin xuba masa abincin .
 shinkafa ce da miyar parpeso na  cat fish datasha kayan hadi take  kamshin abincin     ya sake tasiri a hancinsa.

 Sai data hada masa Komai yadda yakamata sannan tayi rolling din table din , plate din  abinci ya tsaya a gabansa ,har zatabar  gurin sbd bazata iya jurar tsayuwa kusa dashi ba tsabar tsoronsa datake ji karaf suka hada ido da  ummi" ta harareta tare da  yi mata alamun ta zauna  ,Dan haka ta samu guri  ta zauna cikin kujerun dake zagaye da dinning table din.
 , ganin haka yasa deeni sake  tamke fuska tamau tare da  jin wani irin matsanancin haushita 'ahankali yasoma  bude rikitattun idanushin suka  kan abinci dake gabansa.
 Cike da mazantaka ya soma cin abincin da Bai yi niyar ci ba, loma biyu yayi zuwa uku ya Ture plate din, Dan kwata kwata baya jin zai iya cin wani abinci may yawa. Dan baya jin dadin jikinsa gabadaya ma wani irin beting zuciyarsa ke masa wanda yarasa dalilin jin haka, damuwar dake tattare dashi daban ce yayinda  wannan yanayin bugun zuciyarsa yake  daban .


Bangaren Ummi  kuwa addu'ar take tayiwa yaran nata ,akan Allah ya daidaita tsakaninsu.
  ,jiki babu kwari ya mike , still Bai kalli inda Zeenat din take zaune ba.
 ita kuwa Zeenat kanta na sunkuye a kasa takasa kwakwaran motsi gurin da ummi ke zaune  yakaraso ,fuskar nan tasa tamke kmr hadari    bbu  walwala acikinta .
 ,muryarsa a dake yace first love ni zan wuce yanzu kam ,ummi ta dago Tana kallon yadda yaron nata ya hade rai Ga wata uwar rama da yayi. sosai take   nazarinsa sai ma taga alamun knr zazzabi ne  a tare dashi.

 ,deeni byn damuwar dake damunka akwai wani abu ne dake damunka  ?
 DEENI Yace , bbu komai first love .
 amman sai naga kmr baka da lfy  ? 

Sai daya dan yatsina fuska tukun ya amsa da uhm   kaina ke dan min ciwo , amman karki damu dazarar na koma  gida  zan dawo normal ,I won't rest  , .


Ummi ta girgiza masa kanta Tare da Dan murmusawa.

 bata bukatar yatafi gidansa cikin wannan  yanayin dayake ciki .
  "tafin son yadawo da farinkinsa kmr yadda yake a da.
  , duk da, ada din ma Ba wai ya kasance may yawan fara'a bane  , amman yafi wannan lokacin.
Tace  " kaje  part dinka ganin zuwa  yanzu ya shagwabe fuska kmr wani karamin yaro Yace  uhmmmm first love ni gida nake son zuwa ina bukatar  na huta.
  km akwai aikin dazanyi .
 ,ummi ta sake murmusawa tare da cewa  NO.... my Son bbu inda zaka yau muna nan Tare .
  ' Sai naga wannan kyakkyawan fuskar wannan  zakin ta koma tamkar ta cikakken mutun ,
 ,murmurshi ne  ya Dan bayyana a saman  fuskasa  ,har dimple dinsa ya lotsa "hakan ko yayi wa ummi dadi  Sosai har ta sake yin murmurshi  ,haba ko kai kaifa kayi fuska kmr kana filin daga ,haba sadaukina ka kara  Dan   sakin fuskar nan taka  ma  ,nafi son ganinta kunshe da farinciki  ta fadi haka Tana dariya ,duk abinda ke faruwa a tsakanin deeni da ummi Zeenat na zaune a dinning area Tana jinsu, wani irin filling ne na dabam ta dinga jishin a zuciyarta Ta zuba musu Idanu kawai Tana  kallonsu" ba tun yanzu suke birgeta ba , hakika soyayyar dake   tsakanin uwa da "danta"daban ce km  akawai banbanci da Sosai da sauran soyayya .
 Deeni ya Dan langwabar da kansa  Tare da cewa ni yanxu first love  wani farinciki zanyi km byn angama ruguzamin rayuwa.
  kayi farinciki yarona duniyar nan  tamu, Tana da fadi dayawa.
 km  zaka iya  samu farinciki, acikinta fiyye da wanda kayi missing,  kai dai kaje dakinka gani nan zuwa bazan taba barinka ka tafi da wannan , zazzabin danake Gani acikin kwayar idanunka ba.
 nasanka  sarai da rashin kula da son shan maganin.
Tana gama fadar  ta wuce tabar shi nan tsaye yana kallonta.

 , agaskiya baya son abinda umminsa ke kokarin son yi masa  ,amman baya da zabin da wuce  dole yayin abinda tace domin baya son damuwar farincikinta shine nashi .


Dan haka ya juya   ya km  koma part dinsa  yana may jin wani irin matsanancin bugun zuciya  kirjinsa dake masa zafi ya dafe tare da zama kan bed   ya dan jingin  bayansa da bayan  gado .

Bai fi minti biyar da shigowa dakin ba  Sai Ga  ummi  tashigo da sallamar  ita da Zeenat hannuta rike da ruwa da magani  ganinta Tare da Zeenat din ne yasa ya amsa sallamar da Ummi tayi  a ciki.
 Tare da kauda kansa gefe yana kallon wani gefe ,ummi tasamu guri kusa dashi  ta zauna  ita km Zeenat ta zauna daga gefe   akan bedside .

 , Zeenat na kallon ummi Tana gutsitsira maganin hannuta tamkar dai yadda akeyi wa yara kanana ' wanda ba tun  yau  tasaba ganin hakan a gurin ummi ba , a Duk lokacin da deeni bashi da lfy haka Ummi  take masa kasancewarsa baya son shan magani .

ummi ta Mika masa maganin byn tagama gutsitsira wa  sannan ta bashi ruwa 'Sai datayi da gaske da rarrashinsa sannan tasamu  yasha maganin  har  abun yakusan bawa Zeenat dariya yadda Ya dinga yi  amman bbu dama yi  .

Muryata A sanyaye tace sannu my hrt .....ya jiki naka .
DEENI  yayi mata  banza tamkar bada shi take ba Sai ma 
Zamo da yayi kadan ya dora kansa akan cinyar umminsa   Tare da sake tamke fuskar .

Zeenat  ta mike  ta dauko blanket ta rufe mishi Rabin  jikinsa dashi ,a ranshi yaja tsaki Tare da  cewa aiki banza kawai to  bangode ba .


A hankali ummi ke mishi hirarraki masu dadi dasaka mutun cikin  nishadi da walwala.
, ahankali ya dinga jin yanayinsa na sauyawa daga damuwa zuwa birbishin farinciki yayinda  sanyi ke rasa kowace   gaba ta jikinsa da ilahirin jikinsa har zuwa sanda  yaji ummi   take cewa , acikin gidan nan aliyu da fadeela sukayi rayuwarsu may tattare da tarihi da jin dadi wanda  bazaso taba goguwa ba .
  Tare da wani kyakkyawan terribby may matukar kyawun gaske da daukar hankali wanda ke sakasu tsantsar farinciki da walwala  a Duk sanda suka daura idanunsu akan  wannan kyakkyawan bby. farincikinsu baya misaltuwa.

  ,deeni najin haka ya sauke ajiyar zuciya domin  ya rigada ya  gane  shine wannan kyakkyawan terribby din da umminsa ke nufi.
"   nasurudeen .... Ummi takira sunanshi cike da tsantsar kulawa ya dago rikitattun idanunshi yana kallon mahaifiyarsa ,  Tare da  dage mata girarsa daya batare da Yace komai .
 ,ummi tayi murmurshi sannan tacigaba' kai kadai Allah ya azurtani ni da samu a rayuwa byn tarin shekarun danayi da aure batare da nasamu  haihuwa da wuri ba.

, dukkan wata soyayya da  uwa kadai ce  takewa , danta Ina may tabbatar maka ni uminka  ina maka fiyye dashi   ,Ina maka sonka fiyye da komai dake cikin duniyar nan.
   kai ne duniyata kai kadai  da Allah ya barmu ,ka ishe rayuwar duniya , alhamdulilllahi kana min  abubuwa dayawa   fiyye da abinda ya'ya dubu zasuyiwa iyayensu.
 , wani farinciki ya ne  ziyarce zuciyar DEENI" har ya sake gyra  kansa  kan cinyar umminsa yana dubanta da kyau  shi kansa ya tabbatar da irin kaunar umminsa garesa  .
,ummi ta kai hannuta ta shafi sumar kansa.
 , Tana may jin kaunar tilon Dan nata sosai a ranta .

 , deeni kaga  Zeenat Sai lokacin, ma ya wani tuna da wata aba wai Zeenat Dan shi gabadaya ya manta da Tana dakin ma.

 , Ummi tace karo na karshe da zan km baka hakuri akanta .
a matsayin na uwa a gareka Ina son  ka manta da Duk wani abu dayashiga tsakaninku daita  , ku koma shirya tamkar da ,ku  runkugume junanku ku , zauna lfy shine farinciki na  , kuudin  mafi kusancin yan,uwan juna  ne ,banason sake  jin komai atsakaninku baya Ga alkhari, abinda ya faru ya rigada ya faru kum Ina bukatar  wucewarsa har duniya ta nade.
 idan har kana son farincikina da kwanciyar hankalina kmr yadda kasha fada to kabar zance .
 ,sabanin haka   tashin hankali kawai zaka jefani aciki  .
domin nasan sanka nasan  halinka da  taurin kai tsiya  da zuciya.
 ummi takarasa maganata  Tana may  zubda kwalla a afrigice DEENI ya mike  zaune  daga kwanciyar da yayi  tare tari hanwayen da hannuwanshi duka  hankalinsa a tashe yace  haba firt lov  meyyyyyyyyyy  kuma  kuka...  Dan girman Allah  kiyi hakuri ki rufamin asiri zubda hawayenki maseefa ce a tare dani ,da hannushi ya dinga goge mata hawayen idanunta. muryarsa a sarke ya sake cewa first love kiyi hakuri Dan  abinda ya faru ya wuce amman may  tsayawa ne rai manta da wahala km shi Sai 'ahankali komai zai goge a memory dina amman  inshallahu zanyi kokarin naga komai wuce.

 amman itama kiyi mata magana Dan wlh bazan dauki  kalar iskanci zubda ciki ba, Dan bazai yiwu  Ina shan   walaha ana zubar min da cikina ba .
,ummi tayi murmurshi Tana may   dungure masa kai .

,yanzu ni kake gayama haka DEENI ...
  sbd baka kunya ko.... ya kashewa ummi idonsa daya.. Allah first love ba rashin kunya bane ,gsky ce kawai nafada .
 aiko  ummi ta dinga dariya  Tana wlh DEENI karaina ni dayawa ko..idan  baji kunyata ta matsayina na umminka ba .
Ai kaji kunyata ta matsayina na surukarka shi ma  murmurshi yayi tamkar bashi ba hankali  ummi takamo tafin  hannun DEENI da  Zeenat ta hadesu  guri daya ta mayar rufe hannuwansa sannan ta  mike tsaye  ta fice daga dakin gabadaya  Tare da rufo masu kofa .


Byn fitar ummi DEENI zaune rike da hannun yakasa cire hannunshi daga gareta  sannan yakasa cewa komai  tunani yake kawai ta yadda zai cigaba da zama da zeenat zuciyarsa ke bashi shawarar  hakura Zeenat  kawai  ya zauna daita dai dai ya auri kaskantacciya km maragalihu kmr yadda ummi tace ,yayinda wani bangare na zucitarsa ke bashi karfin gwiwar gara kawai yayi aure koma wace iri ce  jin saukar  hawayenta a hannushi ne yasashi saurin dawo daga duniyar tunani daya Lula .
'ahankali yaja numfashi  yana fesarwa tare sakin ajiye   sannan 'ahankali ya zare hannushi daga cikin nata , yasoma yunkurin  mikewa , yaji ta sake riko  hannu gam cikin nata Tana murzawa dole tasa shi ya koma ya zauna yana dubanta.
 Sai lokacin ya lura da   muguwar   ramar datayi.
Ya tsareta da idanunshi ganin yadda take son cika masa kunne da kuka  .

 Duk ke kika jawo matsalar nan  km inshallahu akanki zata Kare ya fadi haka,a kasan rashi.
Sautin muryata  yajiyo kasa kasa Tana bashi hakuri my hrt  Dan Allah kayi hakuri da abinda ya faru wlh bazan sake ba .

 hannushi ya sake zare ,tare da katseta da hannunshi "shiiiii....  ki rike hakuriki ko zai miki amfani a wani guri   Dan bashi da wani amfani agareni.
 maganar zaki sake ko  bazaki sake ba  Shima ba matsalata bane  haka km wannan bazan  ,my hrt  ko me..me... Da kike kirana dashi ,Shima bana son jinsa Dan bana bukata  sbd ni ba zuciyar ki bane .
,inda  kin bani matsayina haka a zuciyarki    kmr yadda kike fada .

,dabaki min muguntar da kike min ba  ,yamike  tsaye cikin sanyi jiki   yashige bathroom ya dauro alwala sallah magariba sbd yasoma kin kiraye kirayen sallah a masallaci dake cikin gidan baifi minti 3 ba ya sake fitowa yazo ya tadda sallah.

 Tana nan  zaune tamkar wacce aka dasa ,har ya idar da sallah ya zare jallabiyar jikinsa ya saura daga shi Sai short niker ya  kwanta a kan bed dinshi.
 yaja blanket ya lullube rabbi  jikinsa ,tare da juya mata baya.

 tsawon lokacin Tana zaune a gurin  batare tasan yadda zatayi ba  har sanda tasoma jiyo  Kira sallahr ishai ' sannan ta samu ta yunkura ta  mike tashiga bathroom itama tayo alwala tazo ta hada magariba da isha'i Dan tuni jininta ya tsaya ,Shima 'ahankali ya km. mikewa ya gabatar da sallah ,ya km koma yayi kwanciyasa 'ahankali yasoma runtse idanushin sakamakon baccin daya dayasoma kawo masa xiyara yaji motsin mutun kwance abayansa ........




MMN SUDAIS CE.
[6/23, 6:02 AM] 0mmer Farouk: 💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖

💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO




Page 56




Kwanciya Tayi   a bayansa ...   byn ta  cire ilahirin kayan jikinta lamo tayi  Tana shakar dadeden kamshin jikinsa.

  Lafewa tayi Sosai ajikinsa tamkar wata bby ' Tare da goga masa kirjinta a bayansa  wani irin shork...... yaji a jikinsa  tamkar an jona masa wutar electric yayinda sha"awarsa tasoma motsawa 'ahankali 'ahankali shr yayi kmr yana bacci  batare da yayi  wani kwakwaran , motsi  ba ballanantana  tagane  ko yaji wani abu dangane daita  , cikin kwarewa da yadda ya sabarmata wasannisa tasoma shafa kwantaccen gashin kirjinsa may matukar taushi , zuwa kan nipply dinsa " still shr ne ya sake biyowa baya .zuwa yanzu koina ajikinsa kirma yake yayinda zuciyarsa take dokawa da sauri da sauri .    "gabadaya gabobin jikinsa sun sauya sun fara amsar sakonninta har wani shake jikinsa yasoma .
 " ganin haka yasa zeenat tayo kasa  da hannu daidai kasan mararsa , nan ne fa yaji bazai iya barinta taci galaba akansa ba" caraf ya  cafke hannuta hade da  zabura ya Mike zaune tamkar wani zaki.
itama mikewa Tayi ta zauna ,kmr yadda yayi.   tsareta  yayi da rikitattun idanunshi  masu matukar kyau da tsoratawa . 
take  tsoron  yanayin yadda yake kallonta ya mamaye zuciyarta . wanda tasan wannan  kallon da yake mata na gargadi ne .
Amman tabarsa Tayi tamkar batasan abinda hakan  yake nufi ba .
 dan haka  ta  soma kokarin sake matsowa zuwa  gareshi  .
 a tsawace ya dakatar  daita ,da hannunshi tare da daka mata wata irin razananniyar tsawa ,data frigita zuciyar zeenat har ta sata  , mannewa da jikin gadon dakin batare da san Tayi hakan ba .
   "kallonshi take da bayyananen tsoro a saman fuskarta,take ya hadiye duk wani emotion din dayake ji a gangar jikinsa .

 Fuskashi bbu walwala Ya sauke idanunshi cikin nata Yana may  nunata da dan yatsansa ke... ...banaso iskanci da rainin wayo ,ko ance miki ni Dan iskane da bansan ciwon kaina ba da abinda nakeyi   wato Gani  jarabbabe ko?
 kin wani kwaso jiki  kina manne min" to jarabar tawa bata may dani   Dan iska da bansan abinda nakeyi ba .

Kin ma rainawa kanki hankali  wlh Gani stupid na  dinga   miki ciki ke km kina yawon  zubarwa ko .

,to wlh  baki isa ba ,bari ma  kiji wannan shine zai zama last warning din da zan miki....... kar ki sake  na km ganin kafarki a ,inda nake matsawar bani ne da kaina na bukaci hakan ba.
Bansan meyasa mu tunani ba da har na amince na zabeki
 Amatsayin abokiyar rayuwata ba.
 da ko zuciyata kin isa ki hango ballanantana har ki samu waje a cikinta da damar zubar min da jinina 

  Ke... koda kuwa mun   koma gida ne bance kizo gareni ba  ,kije ki rike mahaifarki.. ni km  na rike joystick dina da Spam dina yakarasa maganar.. ... oya out from this room before now  I finished you...Ya nuna mata hanyar  fita  da yatsanshi daya .

 Hannu zeenat ta daura aka Tare da sabon tashin hankali ,inna lillahi wa inna ilaihi rajiun kawai take ambata akasan ranta wanna wacce irin maseefa ce tajefa kanta da mijinta ciki .

 Gabadaya tashin hankali datake ciki ya hanata Ko gezau ballanantana Tayi yunkurin mikewa daga inda take zaune.
 magana take son yi Amman Sam  takasa furta kodaidai da kalma daya ce, numfashi kawai take ja ta bakinta Tana fitar dashi da kyar. al'amarin nasa yasoma girman tunaninta .  Sai da taji ya sake  buga mata wata  razananniyar tsawa .sannan ta mike tsaye da sauri jikinta na kirma  ta rarumo hijab dinta dake yashe a gefen gado  tasoma  kokarin zirawa ajikinta sannan  ta kwashi sauran kayanta a hannu taja ta tsaya tana kallon yadda gabadaya yanayinsa ya sake canzawa ,ganin  taki tafi ne yasa DEENI tattaro sauran kuzariinsa da yayi saura ya mike yakamo hannuta yana janta. mamaki da tsoro suka taru suka  hanata cewa komai ,Sai ma binshi datake ,har yakai bakin kofa ya bude Tare da hankata waje ya maida kofarsa ya rufe da karfi ....,Banda bangon data dafe da hannunta  bbu abinda zai hanata buguwa da bango .
wasu Hawaye ne masu dumi da ciwo suka zubo mata tasa bayan hannuta Tana gogewa yayinda wasu ke sake bin kuncinta.



  A galabaice ya fada kan bed dinshi ya kwanta  Tare da'runtse idanushin  gam . 'Ahankali  yaja laulausar  bargo ya lullube jikinsa. wani irin tsuma jikinsa keyi tamkar zaki Ga sandar girma sai Mikewa take alamun Tana bukatar abincin ta tsaki yaja mtssss tare dasa   duka  hannunshi  ya  dafe saman joystick dinsa   yana may sake jan tsaki akasan ranshi  mt....

Daidai tsakanin bakin kofar dakinsa ta tsaya tana  maida  kayan jikinta Sai data tabbatar da natsuwarta ta dawo gangar jikinta sannan ta nufi hanyar dakin ummi  sbd  kwata kwata bata son ummi tadago wani abu a tattare daita    .

Koda tashiga dakin ma  ummi "zaune ta ummi ta idar da sallah isha'i  Tana lazimi .

,ummi ta dubeta Tana mata kallon tsab ,batare da Tayi  magana ba ,cike da natsuwa  tacigaba'da abinda take yayinda   zeenat  ta haye saman gadon ummi Tayi kwanciyarta  lamo   tare kamkame jikinta  wani irin  kewar mijinta ce ke damunta , kuka take son yi Amman bbu dama ,damuwarta zata iya  shafar ummi.
 a dalilinta ummi zata iya muzgunawa DEENI , ita km abinda bazata so ba kennan, batasan abinda zai sake hassalashi akanta  wani irin matsanancin son take masa  wanda batasan tun lokacin data fara ba.
  " yanzu ita Yaya zatayi da rayuwarta mayye rudeta da  sha,awa cikin zubda ciki ,take zuciyarta Ta bata amsa   da rashin hakuri da godiyar Allah ne yasa kika aikata kuskure may muni ,kin zubar da ya'ya da bakisa ba ko iya rabon ki kennan  a duniya  .a boye take goge Hawayen dake bin kuncinta ,har ummi tagama laziminta da sauran addu'o,inta.
 bacci baiyi nasarar daukarta ba . 
  "Tana jin motsin mikewar ummi ta shanye kukanta Tare da goge Hawayen idanunta Amman hakan Bai hana ummi gane wani abu ,daidai inda take kwance ummi tazo ta zauna  tare da kamo hannuta ,me kike tunanin km  mamana  ? 

Kafin zeenat tace wani abu ummi ta km jiho mata wata tmbyr 
Sai ma naga kmr kuka kika yi ko? 
Zeenat ta Mike zaune  suna fuskartan juna da  ummi ,yayinda hawayen dake makale a idanunta suka yi nasarar zubowa sharrrrr....mayye   km  abin kuka  tmbyrki  kawai nayi fa, Sai km ki kama min kuka.
 ,menene yake damunki ko wani abu shi DEENI din yayi miki ,'ahankali take girgirwa  ummi kanta da kyar ta iya bude bakinta ...Ummi  na cuci kaina da kaina na ruguza rayuwar gidana da kaina bansan yadda zanyi abubuwa su dawo min daidai  tamkar da ba. basani ba a she rayuwa bata da tabbas bansa abinda na aikata zai sa na tsinci kaina cikin ,kaka nakanyi ba.
 ,inda abubuwa dake faruwa suka cigaba bana tunanin zuciyata dake kirjina zata cigaba da bugawa ,ummi kiyi hakuri ban miki adalci ba arayuwa, duk tarin laifin dana aikata gareki baki gujeni ba ko canza min takarasa fadar haka tana zubda kwalla.

Ummi ta rungumeta ajikinta tana may tausaya mata , kukan ta,isa  haka abinda ya faru ya wuce ki daina dawo da hannun agogo baya matsawar Ina raye ba zaki taba kasance cikin bakin ba , ke din diyata ce, Ina kallonki tamkar fareeda Yar,uwata , ganinki  tamkar madadince  a gurina abinda kika aikata kuskure ne ,km ya wuce  tunda kinyi nadama  ,Shima son zai sauko ,kinsa halin bakar zuciya irin tasa ,dan haka ki samu nutsuwa km kiyi hakuri da duk wani  abinda zai nuna miki kinji diyarta Sosai ummi ta dinga rararshinta .

 tana anan  jikin ummi har tasoma gyangyadi   sannan ummi ta dan bubuga bayanta kwanta kiyi  bacci ,kinji , ummi ta Mike itama samu guri nan  kusa da zeenat ta kwanta... 


Abu kmr wasa Sai  dasu zeenat suka share 
Kwana biyu agidan ummi baTare da sun koma gidansu ba.
 , kullun dare sai zeenat ta shirya takai kanta Ga DEENI Dan kar ummi tagane basu shirya ba  Amman  ,yadda take zuwa" haka take dawo da   full   gargadinsa may karfi .

ummi tasa a soma nemo mata masu aiki  kafin zeenat ta koma gidanta  .


A cikin  kwana,n a  ukun ne  suka tattara suka koma gidansu har ummin kmr yadda Ta fada .


 Kwana uku  kennan da dawowar zeenat gidan DEENI. bbu laifi al'amura sun Dan canja kadan kasancewar ummi dake  tsakaninsu .
addu'a dai ummi take sake yi  kan Allah daidaita tsakaninsu yasa zaman lfy yaci gaba da wanzuwa fiyye da hakan har karshen rayuwarsu.



Kmr yau zeenat tun safe take aikace aikace gyaran cikin gidan, aiki kawai take kmr wacce Tasha kwaya domin koina yayi kura  tunda tadawo kullum Sai tayi gyara ,,shr ,n da  ummi taji yayi yawa  ne yasa ta  fitowa zuwa kitchen din a lokacin kuwa zeenat Tayi busy gurin aiki.

Ummi tace wai har yanzu baki gama aikin bane ?
Tun asuba dakika sauko ban sake jin duriyarki ba ki bar aikin nan haka man zeenat ki huta  tunda muka dawo kike fama da aiki ki bar shi haka ,gobe ne za'a kawo miki  masu aiki ,nayiwa hajiya turai magana km ta tabbatar min da gobe goben nan za'tasa akawo .

,hajiya turai aminyace Ga ummi, sun dade Tare  tun farkon zuwan Ummi  Nigeria suka sanadin mazajensu  .

zeenat ta girgiza kai kawai  ummi gara dai  nasoma rage aikin nan kafin akawo masu aikin.
  ' kinsa bbu abinda ya'ya yafi  tsana a rayuwa shi sama da kazanta ,ummi Tayi murmushi jin dadi to ai shikennan  Allah yabada sa'a Amman kibari ki dan  hutu haka. naga ko karya bakiyi ba ,ai  yanzu nan  zankarasa nama, Kusan gamawa.
   ,mamaki yacika ummi ganin irin aikin da zeenat din  Tayi  parlour ta koma abunta ta zauna  tare da kunna  TV tana  kallo zeeyword daga nan inda take zaune suke hira da zeenat din ,kafin wani lokaci zeenat taci Rabin aikin gidan  .


Koda dare yayi ma zagewa Tayi, tashiga kitchen tashiryawa ogo DEENI lafiyayen abinci da Miya  kala biyu , farar  shikafa ce da miyar pepesoup din kayan ciki ,sannan da miyar  pepesoup  din freshe fish dataji kayan gadi sai kamshin ke tashi .

  sannan Taje ta shirya komai tsaf tsaf a  dinning  .ita km taje ta sheka wanka ta hade cikin daguwar rigar material datasha stone work Sai kalli take zuwa Ga wani kamshi na musamman dake tashi ajikinta karku manta zeenat akwai son kwalliya km taiya musamman kit gareta na kayan kwalliya  , ahankali take saukowa zuwa  parlour kasa tayi maseefar kyau dauu..sai kyali take  kusa da Ummi samu guri ta zauna  Sai dai idanunta na kallon tsaitin kofar shigowa ne ummi ta kalleta tana murmushi kai  Kai manana kinyi kyau ,yau  DEENI bazai ganeki ba zeenat tayi murmushi kai ummi har wani kyau nayi  . sallamarshi suka jiyo  ciki ciki yashigo cikin parlour, kunnenshi makale da waya yana magana ,  da saurinta ta  Mike ta  tarbeshi Tare da karbar briefcase din hannunsa Bai  hanata ba sakamakon idanun umminsa dake kansu  Amman suna hawa upstairs daidai bakin kofar dakinsa taja ta tsaya cak dan gudun tashiga dakinsa yayi mata  maseefarsa.

'Ahankali   yasa hannushi ya amshi jakarsa dake rike a hannuta  ya shige dakinsa yabarta nan tsaye .

 Byn kmr minti talatin  ya sauko jikinsa sanye da Riga blue shirt da wando jeans threeecutter   Sai kamshin turaren Hamilton Ontario ne yake tashi  ajikinsa ,  kai tsaye dinning area ya nufa inda ya hangi umminsa zaune  da alamun   zaman jiran fitowarsa suke .'
ahankali yakaraso gurin tare da  samu guri ya zauna yana   gaishe da umminsa ta amsa cikin sakin fuskar da kulawa ya aikin alhamdulilllahi ya cire wayarsa yana operating  ahankali zeenat  tayi wani irin Mikewa wanda yasa gabadaya santsar  jikinta girgizawa  most especial kirjinta dayake suna kusa da juna  ,dagowa yayi da niyar sauke mata ruwan  bala'i idanunshi yaci karo da  kirjinta .... kallo daya yayiwa Rabin nonuwanta  Ta saman rigarta ya dauke idanunshi Amman duk da haka say da   yanayinsa yasoma sauyawa notice dinsa suka nemi kwacewa , kwalkwaluwarsa tashiga circulating ya dinga jin  wani iri  ajikinsa , cikin natsuwa Tayi serving dinsa.

 bawani wani  abinci yaci sosai ba ,ya Ture plate din gefe  kasancewarsa  Bai fiyye son cin abinci may nauyi ba
, 'ahankali ya maida  bayansa ya jingina  da kujerar da yake zaune  akai Tare da Dan zamowa kadan yana duban umminsa  itama ,ummi shi take kallo tana tabe baki   ba dai har ka koshi ba ?

ya dage mata girarsa daya alamun haka  ne ,kai dai  bansan irinka ba wlh  kwata kwata baka kaunar son cin abinci , DEENI yayi murmushi kawai batare da Yacewa umminsa komai ba .
murya a sanyaye zeenat tace to ko na hado maka coffee ne?

 parlour ya dauki shr har kusan tsawon  minti goma batare da ko Tari yayi ba , Sai da zeenat din ta km maimaitawa tmbyrta tukun   muryarsa a dake  Yace.

 please....banason damuwa dan Allah aikinsa Ina  bukata   km mayye na takurani da questions.
 jin haka yasa zeenat din Mikewa 'ahankali tana jujjuya mazaunanta har tashiga kitchen idanunshi kam a kanta  abinda   ya tsaya masa a makwashi ne  ya samu ya hadiye da kyar.
 ,yana hango tahowarta da yadda take motsa  kirjinta ,yasashi sake dimauce ,take ya wurgawa kansa tmby what's wrong with me ?'ahankali yakamo lip's dinshi na kasa yana cizawa da karfi har takaraso    ta,aje  masa coffee a gabansa  baidana cizan lip's dinshi ba cikin dakiya da mazantaka yasoma sha  , sosai yasha coffee din ,ummin ta zuba masa idanu kawai  Tana kallonsa sak mahaifinsa kusan har ya so zarta muhd aliyu da komai. , Ya dubi yana murmushi ya,akayi first love ta hararesa ai nan kafi kauri Ga abinci baka , zauna kaci ba sai ruwa .tsam ya Mike, ya soma taku  first love ni zanje na kwanta bacci bacci .....nake ji tare da sakar mata murmushi ,to Allah ya tashemu lfy.


Daren ranar  sam DEENI kasa runtsawa yayi kwana yayi yana watsa jikinsa ruwa da kyar DEENI yasamu Ya runtsa sakamakon wani irin feeling da ya dinga tasoma masa  hannunshi yasa duka ya  dafe joystick  dinsa dashi yana juyi , sai wuraren asuba bacci may nauyi yayi nasarar daukeshi.

Washegari da sassafe  yabar gidan ya wuce office .
zaune yake a office dinshi aiki yayi masa yawa sakamakon matsowar  karshen wata  .

Kanshi Duke yake yana fama da aiki rubuce rubuce dake gabansa yaji   nocking din kofa kansa na Duke ' yabada izinin shigowa batare daya dago kansa ba .


Manir abokinsa ne yashigo cikin office din da sallamarsa DEENI ya amsa batare da ya dago kansa ba ' yacigaba da abinda yake" ganin haka Yasa   manir ya tsayawa  abakin  taga, yana kallon shukokin flowers din dake zagaye da  surrounder din gurin .
dan yasan tunda ya iske DEENI  kan aiki bazai taba sauraransa ba matsawar bagama yayi sanin da yayi masa na may matukar son aikinsa.


Kusan minti shabiyar yayi tsaye , sannan yasoma takowa 'ahankali izuwa bakin makeken tablet  din da DEENI ke zaune ,yaja kujera  daya ya zauna yana duban DEENI, Sai lokacin DEENI ya dago rikitattun idanunsa ya dubeshi manir  dasu .
har kagaji da tsayuwar kennan  inji cewar DEENI? 

Ba dole nagaji ba ,dan naga  alamun sai nakai Ga zama tukun zakiyi lokacina .
manir  ya mikowa DEENI hannu suka gaisha ,yaushe kashigo garin ? Dariya manir yayi shekaranjiya wlh  na dawo yau km nace nazo naganka ,ko baiyi bane ?

 , wani irin farinciki ya lullube zuciyar DEENI ya danyi murmushi har dimple dinsa ya lotsa tsantsar kyawun sa ya sake bayyana ,yana son a dinga nuna masa kulawa , manir Yace aboki lfy kuwa irin wannan farinciki haka ?
Bbu komai  nima haka na tsinci kaina.
  ,DEENI ya jingina bayansa da kujerar dayake zaune kai  yana jujjuyawa dashi ,manir Yace ya ummi da zeenat iya rigima ,sai DEENI ya yamutsa fuska sannan Yace ummi tana lfy ita dayar ce dai bansani ba .
,manir ya sake yin dariya ,badai kaki ka dauki shawarata ba.
 da yanzu an wuce gurin ,  DEENI Yace  kai...bana jin zan iya bin wannan  shawarartaka , dominta yana dayawa kai kace nasamu Yar talaka na aura ,yayinda ita km first love ke son na aure kaskantacciya km maragalihu domin faranta ran zeenat ,ni km banajin zaniya ,dan haka nake jin zan hakura da zeenat kawai ,ok ummi ta kawo maka shawarar haka kennan DEENI ya daga masa kai kawai ,to why not ,kiyi abinda tace kai ni Dan Allah rabani da wannan shirmen nan dai suka maganar suka shiga wata hirar duniya .

Wayarsa ce ta dauki karar sauti may dadi 'ahankali Yasa hannunsa ya janyota daga jikin charge yana dubawa. sunan umminsa yaga yana yawo akan screen din wayar  ,'ahankali ya zareta daga jikin charge ya manna wayar a kunnenshi tare da yin  sallama  .

 Muryarsa a shagwabe Yace Oh! No.... First love  don't do this to me please . dan Allah kibari har  nazo tukun naga kalarsu kada bad dinsu yayi min yawa ....

abangaren ummi kuwa murmushi kawai Tayi tare da  cewa  shikennan badamuwa  sai kadawo din  ok first love Nagode lov you so much , love too my son .


Manir na zaune yana kallonsa har yagama wayarsa , yana shawarar yadda umminsa ke kulawa dashi ,da yadda Shima DEENI din ke kulawa da mahaifiyarsa. al'amarin nasu mai matukar girma ne ,hira suka cigaba dayi kafin daga bisani manir yayi masa sallama ya wuce 



Karfe tara daidai na daren ranar yana kishingide akan kujerar three siter yayinda ummi ke zaune a gefensa tasa zeenat Tayi kiran masu aikin da akawo dazu ,shigowarsu yayi daidai da runtse idanunshi dayayi ...



MMN SUDAIS CE
[6/23, 6:02 AM] 0mmer Farouk: 💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
     💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO



Page 57



Karfe tara daidai na daren ranar yana kishingide a parlour  akan kujerar three siter yayinda ummi ke zaune a gefensa byn tasa zeenat Tayi kiran masu aikin da akawo dazu,shigowarsu yayi daidai da runtse idanunshi da yayi .

Baiyi tunani da gaske umminsa zata iya masa irin wannan auren wulakancin ba. ,shi ko a tarihi Bai taba jin inda akayi irin  haka ba , har suka karasa shigowa cikin parlour Bai bude idanunshi ba ballanantana yakarewa yanayinsu kallo ,zeena tasamu guri nan kusa dashi ta zauna  .

Yayinda masu aikin suka sake gaida ummi tare da oga DEENI... wanda shi kwata kwata Bai ma san ta inda zai amsa musu  ba ,dan haka yashare kawai abinsa batare da yace komai ba sai ummi ce ta amsa musu tare da musu nuni dasu tsaya can nisa kadan .  Numfashinsa ne  ya nemi tsayawa sakamakon ji da yayi yanayin sent din  parlour yana neman  canza salo km har lokacin idanunshi a runtse suke gam... bai da alamun budesu   .

'Ahankali ummi takira sunanshi DEENI.......Ya amsa batare daya bude idanunshi ba Na'am first love.
 ka bude idanunka man  ka gansu , gasu nan , 'ahankali muryarsa a sanyaye yace gaskiya bazan iya kallonsu ba first love sbd  basuyi ba  ,acanza wasu masu aikin idan akwai  ...iya abinda ya iya cewa kennan ..yayi shr tare da  gyara kwanciyasa ya juya musu baya ,shi kadai yasan yadda ranshi yake a bace  har wani sama sama numfashinsa ke yi .
  
Ummi ta maida idanunta kan Yan mata guda   hudu dake  tsaye a gabanta tana musu kallon tsab , . guda uku daga cikinsu hausa fulani ne.
   " yayainda daya daga cikinsu takasance yare sai dai tana jin hausa sosai kasancewarta Yar asalin  adamawa ce  ,basu da wata makusa ajikinsu  in aka dauke wacce takasance yare" itama rashin addani ne kawai makusanta .


Km daman ita bata sakata cikin wayanda zata hada da tilon danta ba sai ta zauna matsayin may aiki ,'ahankali ummi ta sauke ajiyar zuciya tare da basu umarnin dasu koma dakin da'aka saukesu a ciki kafin zuwa gobe.


Ita dai zeenat Yar kallo ce batada tacewa domin  bbu damar yin magana suna wucewa ya sauke naunauyen ajiye zuciya tare sakin numfashi sannan 'ahankali ya soma bude idanunshi 'ahankali ya sauke su fes akan ummisa" harara ta watsa masa shi km ya kashe mata idonsa  daya  yana may cizan lip's dinshi kmr an sikareshi ya Mike yayi hanyar step .

Washegari ummi ta sallami masu akin sai dai tabar laraba wacce ba Muslim ba domin aikace aikace gidan .


Tun daga lokacin ake kawo masu aiki iri iri gidan  Amman Sam  DEENI yakasa tantance wacce zai dauka matsayin wacce zaiyi AUREN SIRRI daita idan ummi tayi magana sai yace shi   Bai samu wacce Tayi masa  ba.

Km  ,hakan dayake yi  Bai wani damu zeenat din ba kasancewar tasan halinsa da kyankyamin tsiya .


Cikin haka DEENI ya siyawa zeenat form din jamb km a sannu 'ahankali  lokacin rubutawa yayi ,taje ta rubuta bbu laifi tasamu abinda ake  so a course din da za ta yi .


Abu fa kmr wasa duk wacce akawo sai DEENI yace A'a bata mishi ba

 cikin haka wani dare DEENI yakasa rike kasan domin sha,awarsa mai shegen  karfi ce tun yana azumi da shan magungunan har magani yazo ya daina aiki ajikinsa .

Dan haka ya yanke shawarar kawai garaje zuwa Ga matarsa ,yana zuwa kuwa yasamu kyakkyawan tarba daga  zeenat din  ,ranar tamkar sallah ce  a gurin zeenat daman itama Tayi mugun kewar mijin nata sambatu bbu irin wanda batayi ba har da kuka ,shi km yana gama savice ya Mike tare da  sake tamke fuska tamau tamkar wani zaki.
 Amman kwata kwata hakan Bai dameta ba ballanantana yabata mata rai tunda tasan ta wannan bangaren ba haka halinsa yake ba ita tadagula komai tama gode da  ,yadda yakawo kansa gareta km hakan shi yafi komai yi mata dadi .
, tun daga lokacin abubuwa suka sake yin sauki .
Jifa jifa idan takurewa oga DEENI dole alallaba aje gurin zeenat ita km duk lokacin dayazo ashirye take data bashi hadin kai  duk tana jigatawa a hannushi kasancewarta may saurin yin relex a wajen sex .



Bayan wata uku zeenat tasamu shiga Lagos state university tare da dalleliyar motarta  4mat sabuwa dal. al'amura sunyi mata sauki  rayuwa Tana gara  mata  yadda take so tare sabbin kawayen datayi a school  karku manta zeenat akwai son kawaye da daukar wanka  shiyasa duk inda taje batasamun matsala gurin tara jama'a .

Byn shekara uku 


Haniyace kawai kake ji acikin babban Holl din dake cikin PLASNUW ROWS family  estate  wanda ya tara manya da kanana na cikin dangi kasancewar lahadi karshen wata ne , km shine lokacin sada zumunci a tsakanin wannan family byn komai ya lafa .. gaishe gaishe da shawarace sharawarce ne yabiyo baya akan cigaba family anyi taro lfy yayinda kowa yakama  gabansa .



Hjy Mariya wace aka fi sani da mama ta abuja ,Yaya ce Ga mahaifin DEENI uwa daya uba, zaune take a parlour gidan DEENI ita da Ummi suna zantawa .
 
, fadeela ki cire son zuciya sannan kikawar da zarge da'ake miki  acikin dangi da mutane gari "dan ganin  zeenat diyarkice shi Yasa kika ki daukar mataki akan zamansu da DEENI yau aurensu  tsawon shekara bakwa kennan babu wani cigaba ko karuwa ta haihuwa.
 km kin  zuba ido kina kallo batare da kin dauki wani  mataki akai ba .

kibari yaron nan yakara aure fadeela  ko acikin dagin ne  ko km yaje daga waje tunda yarigada yayi na farko acikin family ,bbu lallai ko dale ya km yi acikin gidan nan.
 ummi Tayi murmushi dan itama rashin haihuwarsu yasoma  damunta amman bbu yadda taiya .
  ummi  tace karki Ga laifina Yaya ,Gani nake rashin haihuwarsu da wuri watakilla ni suka biyu amman munan muna ta addu'a .

,to kunje asibiti ne and dubanta inji cewar mama  ,ummi tace  muje km an tabbatar mana da mahaifarta lfy lau take km zata iya samun ciki at any time ,daga nan ummi Tayi shr bata sake cewa komai ba.
  ita kadai tasan  shirinta  dan  bazata iya fitowa tagaya duniya abinda tashirya akan yaranta  ba.
 wanda har zeenat  bazata bari tasani ba sai lokacin yin haka yayi ,

Duk maganar da suke acikin kunne zeenat sukayi shi " saukowa take zuwa akasa dan daukar  wayarta taji  maganar da mama takewa  Ummi akan  kara auren DEENI  shine fa tsaya tana gama jinsu kuwa  takaraso da sauri tamkar anjihota tayi zaman dirshan a gaban maman ta abuja tana rusa  kuka dan girman mama kada kimin haka kada  ki bada shawarar akaro min kishiya domin bana sonta kwata kwata  bana kaunar  zama daita.

 ,sannan ta juyo gurin ummi ,ummi  kada ki dauki shawarar mama dan Allah nima zan haihuwa kinji ummi duk tabi ta rude ta gigice tafi haiyacinta sai kuka take .mama ta daga matsa ni Dan Allah rufe min baki kin wani cikawa mutane kunne .



Karar hon ne yacikawa securities din bakin get din kunne da sauri daya daga cikin securities din yazo ya wangale babban get din gidan yana dagawa DEENI dake zaune abayan mota   hannu .
'Ahankali  direbansa yasanyo hancin matarsa rang,rover cikin farfajiyar gidan .
Kai tsaye  rumfar  da'ake parka motaci dake  kofar gidansa  direbansa ya nufa yayi parking din motar .
Sannan ya fito da hanzarisa ya bude masa murfin motar tare da kamewa guri daya yana Sara masa .

'Ahankali ya fito daga cikin  motar cikin takun nan nasa kasaita  idan bakasan shi ba zaka dauka ko tsabar  iyaye yayi masa yawa  nan haka Allah yayi sa da tafiyarsa ta  musamman kai tsaye yashigo cikin babban parlour gidan yayinda gabansa ke wani irin faduwa .

inda dai kunnuwanshi ba karya suke masa ba sautin kukan matarsa yake jiyowa da murya aunty, n sa .gabanshi ne yacigaba da dokawa ai da sauri  sanyo  kansa  cikin parlour ,ganin umminsa zaune Yasa shi sauke ajiyar zuciya tare da yin hamdala a zuciyarsa .
Domin  tunaninsa ya dauka  ko wani abu ne yasamu umminsa .

Zeenat naganinsa ta zabura ta Mike tsaye takaraso gareshi gabadaya ta gigice sai kuka take my hrt dan Allah kazo kagayawa mama bazaka kara aure ba ni kadai na isheka rayuwar duniya  dan Allah km zan haihu  Wlh nima Ina son na haihuwa  dakai .
Dan Allah ka fahimtar daita ,zan iya haihuwa nima  kmr kowace macce .ka fada mata  Bana son kishiya wlh muddin aka  min kishiya wlh  zaku rasani gabadaya dan zaniya kashe kaina, ,  jin haka Yasa DEENI  jan mugun tsaki Tare buge mata hannuta data rike shi dashi  abin haushi abin dariya 'ahankali ummi ta Mike tsaye tare da kamo hannuta ta zauna daita kusa daita haba zeenat ki natsu man meyasa kike irin haka ince , magana ce kawai akeyi ,ko  kinga anyi miki kishiyar ne duk kinbi  ki rude kin tadda hankalinki nima kina neman tada nawa .
Wasu Hawaye ne masu zafi suka zubo mata  Dan Allah  ummi kibar ma ambato min sunan kishiyar ji nake kmr mutuwa zanyi  numfashin har neman daukewa take duk hankali ummi yatashi da ganin yadda yarinyata ta dawo cikin kankanin lokaci rarashinta  kawai ummi take.,

Mama dake zaune ta ta zuba musu  ido kawai 'ahankali ta numfasa sannan tace  lallai yau naganewa idanuna abinda ake fada acikin gidan ,ashe dai  gaske ne fadeela kece kike daurewa zeenat gidin take yin wulakancin data gama .
,Dan wulakanci ma har  wani lallaba yarinya kike kan za'a mata kishiya kanta aka fara yi mutun kishiya ?
  Mama ta dubin inda zeenat  take zaune tana rizgar kuka ...ince  ciki naji ace ki  zubar har Sau biyu shine yanzu dan tsabar  iskanci,zaki cewa mutane  kina son haihuwa.
 ,da can kinsan kina so meyasa kika zubar da shi ,ummi zatayi magana mama ta dakatar daita abinda nake son kusani shine wlh wlh nasuru ...zai yi aure matsawar baki haihu ba nan da wata tara  kinji na rantse sam fadeela Banga alamun kina da tausayi ba ,ubansa ya haife shi kadai ,ya mutu ya bartshi amman shi yakare a bbu ko daya sam hakan bazai yiwu ba  ,ummi ta sautata murya tasoma bawa mama  hakuri ,yayinda zeenat ita km ke kuruwa tana  rizgar kukan har da shesheka.
 

DEENI rike da wayarsa yana daddannawa bame da niyar cewa komai amman jin abinda mama tayiwa umminsa ya so-so ranshi km ya tsaya masa arai dan haka cike da haushi da takaicin yace haba mama .......meyasa zakice haka naga itama   zeenat din diyarki bata ummi kadai bace .
Dan haka bai ka mata kice wai ummi ce ke daure mata gidin yin iskanci ba.
  " yakamata kiyiwa ummina uzirin km aure ai nine mayin  shi  idan naso  zanyiwa mamata kishiya Bai sai ansani ba  idan bangadama ba kuwa bbu ub....Ai tun Bai kai Ga karasawa ba ummi tayi tsalle ta dire a gabansa Tare da  rufe masa baki dan tasan aika aika yake shirin yi.
 ,mama dake zaune har lokacin ta dinga  girgiza kai  kawai ..
 meyasa meyasa kika rufe masa baki eh ..Ai da kin barshi  yakarasa abinda yayi Niya ince  irin  kalar taki tarbiyar kennan ,amman  kusani wata tara kawai na baku tana  cika ko haihuwa ko amarya acikin gidan.
 ta Mike tsaye  tana kokarin barin parlour ummi tabi bayanta tana bata hakuri dan ita bata son tashin hankali km koda tana so bazata iya da family muhd bello khaliyal ba.....😭😭😭



A hassle DEENI yasoma hawa step yana takawa  biyu biyu yayinda  zeenat ke  biyi dashi a baya tana kuka tana bashi hakuri dan Allah  my hrt kayi hakuri karka min kishiya wlh bazan iya zama daita ba  ... am ready to give any type of bby you wont  nima Ina son bby Allah ne  Bai km bani ba . Ta ya Allah zai km baki haihuwa  zeenat byn bakya so kyautarsa .kin butulcewa ni'ima ubangiji nki.
 idanunshi a rufe yakarasa shiga cikin  dakinsa ,warwas ya zube akan gado yana fidda numfashi sama sama kuka take har lokacin fuskarta tayi jazir abinka Ga farar macce 'ahankali tasoma cire masa takalminsa  taje ta ajiye   a inda yake ajiye takalmansa .
ta dawo ganin yana kokarin son  balle maballi gaban rigarsa Yasa takarasa da sauri tashiga balle masa ya Mike tsaye  tare da zare rigar da wando ya saura daga shi sai dan karamin boxes , kukuan ya isheni haka bana bukatar hayaniya yana gama fadar haka ya shige bathroom har ya fito kuka take tana masa magiya   tsausayi ne taba zuciyarsa duk da  tsananin haushinta dayake ji aranshi  hakan bazaisa yaga ana wulakantata ya kyale ba Dan  ko bbu komai ita din wata abace may daraja a gurin umminsa.
   dan haka cikin sanyin nan nasa yasa hannuwansa duka  ya jawota  jikinsa ya rungumeta tsam tsam  .

 Uhmmmm uhmmmm 😍😍😍😍😍😍


MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
   AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO



Page 58


 Rungume take a faffadan  kirjinsa har lokacin " yayinda  hawayen  tausayin kanta ke  cigaba da bin kuncinta"  danasani  tattare da nadamar abinda ta aikatawa kanta a can baya  ne ke damun zuciya . 
  'hakika rayuwa bata da tabbas gashi komai yana neman tsaya mata " zuciyarta kemata wani irin zafi yau tazo mata tazo mata abu mafi muni ,kishiya ...fa.
  yau ita zeenat da kanta ake kokarin  son sanya  mijin yi karo mata kishiya... Kishirya.. ta sake  maimaita  hakan akasan ranta  abinda tafi mugun  tsana  a rayuwarta kennan ,wai aba kishiya ..

  kirjinta ke mata radadi da nauyi  tamkar an dora mata dutse ita kadai tasan yadda take jin zuciyarta da gangar jikinta... wani irin maseefaffen kishin mijinta ne ke  sake tasomata fiyye da yadda take ji a da. 
  tsanar  sauran matan dake duniya zaune bbu aure ne ya dirar mata lokacin. 

 Kukanta yasoma damun tunani ,kasancewarsa mutun marason damuwa da yawan hayaniya. hakan yasa yasoma  sausauta rungumar da yayi mata daga qarshe ya ma  rabata da sansar jikinshi gabadaya.
 
, Tare da zuba mata rikitattun idanushi kawai  Dan shi sam kwata kwata bai iya wani abu wai  rarrashi ba   . ballanantana har ya tsaya wani bata lokacinsa gurin  rarrashinta .

 ,a dake taji sautin muryasa   ',malama kiyiwa mutane shr duk  kinbi kin cika min kunne da wannan bazan kukan naki  mara ma'ana  ..

ko uban   wani ne ya  aikeki wulakanta cikin  da Allah yabaki tun farko .

  Wlh idan kikasa damuwarki  tashafi lafiyar  mahaifiyata   akan maganar kishiya ..nan zan baki mamaki ..
   kishiya ...bama daya zanyi ba  har biyu idan nagama sai nayi .
   "inyaso  ki mutu sai ki kashe kanki kmr yadda kika ce  ,sha sha kawai  ya fadi hakan yana may  da jan mugun tsaki... mtssss  .

take jikinta ya dauki rawa kirrrrrrma jin maganar bama kishiya daya ba  har idan yaso zaiyi ..
  "ai ...batasan sanda ta zube  kasa ba.
  Tana kuka Tana  girgiza masa kai dan  gabadaya  kasa magana tayi sai jujjuya  kai kawai  take tana zubda kwalla. 

Wata uwar  ,harara ya watsa  mata  hade da binta da wani irin bazan kallo wanda yasan hantar cikinta kadawa wayyo hrt karka min haka dan girman Allah karka min kishi....sai km Tayi shr Tana cigaba da kuka.... bakinsa Ya tabi tare da  cewa meyya haka oya Mike ..  Mike ni kibar  min dakin kinsa fa ni bana son damuwa .

Yana gama fadar haka ya haura saman gadonsa ya dau towel daman km abinda ya fito dauka kennan .

 bathroom ya sake koma   ya sakarwa kansa ruwa tare da dauro alwala sannan ya fito kugunsa daure da towel .

mamaki ganinta   yayi   har lokacin bata bar dakin ba Tana nan durkushe tamkar yadda yabarta  ,ganin yanayinsa da km yadda yake kallonta da rikitattun idanushi masu matukar  birkita mata kwalkwaluwa ,da hana zuciyarta sukuni .
yasa  ta mike tsaye da sauri jiki  har rawa rawa yake tsabar tashin hankali ,a sukwane ta  tabar masa dakinsa  Dan tasan halinsa maseefar sa, bakaramin aikinsa bane ya shuka  mata rashin mutunci idan ma taci sa'a Bai hada mata da mugun duka ba tunda daman ya mata  gargadi kar sake ganinta    bedroom ba  .


Fitarta daga dakin  yayi daidai da sauke  naunauyen ajiyar zuciyar da yayi..
 , yayinda wani gefe na zucitarsa na Dan tausayawa mata  game da halin   rayuwar data jefe kanta ciki.

 hakika shi yasan  tana   wahalar da zuciyarta ne kawai akan  batun   kishiya .
Dan kishiya ba fashi sai ta zauna daita.

 'ahankali ya sake  sauke  wani naunauyen ajiyar zuciya tare laso lip's dinshi na kasa ...
" cikin sauri ya shiga shirya  kansa cikin wasu hadaddun kananan kaya masu matukar kyau da daukar hankali shirt  ce  ashi  colour mai gajeren hannu  sanye a jikinsa sai  wando blue  jeans  wanda suka yi matukar karbar surar jikinsa.
 ' koda yake shi din may matukar kyau ne km kowani irin kaya ya sanyawa jikinsa    sai sun  amshi karbi shi.
, cikin sanyin nan nasa da takunsa na kasaita  yakarasa gaban mirrow  ya dauki turarensa mai matukar  kamshi ya feshe ilahirin jikinsa dashi.
  ' sannan ya gabatar da sallah byn ya idar sallah ne ya sauko parlour kasa cike da isa .



 Anan  ya  iske    ,Ummi tare da zeenat zaune sunyi jugun jugun abin duniya ya damesu.

  Ummi  ta rafka uban tagumi tana  tunani duk da yasan zance dai bazai wuce akan maganar aunty shi bane . 

Yana tsaye yana kallonsu yaga  zeenat  ta   kwanta  akan  cinyar ummi tana kuka  '  tana goge Hawayen idanunta da bayan  hannuta kukan ya isa haka mamana kada wani ciwon yakamaki fa.. . Ummi bazan iya zama da kishiya ba wlh taba kirjina kiji ta fadi haka   tare da  janyo  hannun Ummi zuwa  saman  kirjinata .


Kallo daya yayi musu tare da   dauke idanunshi daga kansu..
 ya tabe baki kai tsaye  dinning area ya nufa  yaci abincinsa hankali kwance   . Sannan yacigaba da zamansa yaciro wayarsa yana  operating ..
 Km duk yana  jin abinda zeenat kecewa da yadda Ummi ke rarrashinta da kwantar mata da hankali akan bbu wata kishiya da za'a yo mata ita kadai ce bbu kari ...
 ,  Jin haka Yasa Daga can inda yake zaune yayi gyaran murya.
  ,Ummi  ce ta  juyo  'ahankali Tana dubansa  ,yatsansa daya ,ya karkada mata alamun a,a harara Ummi   ta sakar masa yayinda  shi km ya girgiza mata   kai kawai yana tabe baki.


 Ahankali Ya Mike tsaye ya dawo kusa da Ummi Ya zauna fuskarsa a hade yace  ke.....yi excuse dinmu please zata Mike kennan  ummin ta maidaita   Dan me zaka korar min yarinya tana cikin halin  damuwa ?
idan har baka shirya yin magana dani bane tana nan  kana iya barin maganar  har zuwa wani lokaci dan bbu inda zata ke koma kiyi kwanciyar kinji..
 ,koma kuwa  tayi  kwanciyarta  kmr yadda Ummi tace amman har lokacin Hawaye bai daina bin kuncinta ba  . 

Kafadarsa ya sake  dagawa alamun bai damu ba da abinda Ummi tace ba ..
 Wayarsa ce ta dauki kara sauti mai dadi  Mikewa tsaye tare da pic din call din ya manna a kunnenshi tana tafiya .

Hello ..Yaya ganin nan zuwa yanzu   sannan yakashe wayar yabar musu gidan gabadaya .

Yana fita Ummi  ta dauki wayarta takira hajiya  turai bagun farko  hjy turai ta dauki wayar  da sallamarta " bbu  abinda Ummi  tasoma tmbyrta sai  an km samu kuwa ?

  Ummi tayi hakan ne  Dan kada  zeenat din  tadago  wani abu dangane da shirinta.

 bangaren hjy turai kuwa cewa Tayi eh ansamu amman  sai dai  guda daya ce  km Tanada dan shekara ,Ummi tace kmr shekara nawa gareta ?

eh zata kai kmr 23 haka inji cewar hjy turai ok ki  kawota naganta  hjy turai tace sai dai    kibari zuwa  gobe idan Allah Ya kai mu ' latifa zata zo gurina idan zata wuce gida  zan bari  takaraso miki da yarinya ,Ummi tace ok shikennan sai sun zo din takashe wayarta  tare yiwa hjy turai godiya .



Washegari da misalin karfe hudu daidai latifa takawowa Ummi shafa. kallo daya Ummi tayiwa yarinyar taji kwata kwata  bata kwanta mata arai ba a ranta tace  itama kennan Ina Ga oga DEENI.
   tasan ma bazai wank mu,ammultu  da yarinyar ba , girgiza kai kawai Tayi byn tasa an kawowa latifa abin motsa baki .

 ,'ahankali Ummi ta Mike tsaye ta nufi wani kofa  tayi warning  din glass  tare da cewa latifa ta biyo bayanta ,  latifa ta Mike 'ahankali tabi bayan Ummi .


Wani madaidaici parlour Ummi takai latifa byn sun zauna ne Ummi tace Kira sunan lafita ta amsa kina jina latifa ..yarinyar nan bata min ba km nasan tunda bata min ba da wuya tawa mai gidan Shima  kinsa shi da kyankyami tsiya .

 dan haka  asamo wata kota gurinki ne amman dai zan  bar Ita wannan din kafin asamu wata ,dan aikin gida sbd aikin nayiwa laraba yawa ,latifa tace ok babu damuwa ,daman kuwa  akwai wata yarinya dake neman aikin gida irin wannan  amman  kibari zan   miki kokari inshallahu .
Ummi tace shikennan latifa Nagode sosai suka yiwa juna  sallama sannan latifa ta wuce .



Byn fitar DEENI daga gida kai tsaye gidan  yayansa mahamud dake cikin estate din yayi .

zaune suke shida  da Yaya Muhamud din  babban parlour baki na gidansa .
 Shr yabiya baya kafin Yaya Muhamud ya numfasa tukun yasoma magana kmr haka  DEENI  abinda yasa nace kazo nan ina nemanka ,akwai  magana may mahimmanci da nake son muyi akan company,s dinmu.
 ,kaga dai yanayin danake ciki  halin yanzu nima girma ne yake zuwa min yayinda  abubuwa ke sake min yawa ni kadai raina nake kokari akan lamuran company,s dinmu na cikin gida da sauran kasashen duniya  shine naga  yakamata ace kaima , ka'ajiye wannan aikin naka kazo mutaru mu kula da komai Tare.

 ,kasan mutane wasu basu da amana , amman yaka Gani akan lamarin .. DEENI yayi shr kawai yana sauraransa har yakai karshen zance ,sannan ya dan yi murmushi karfin hali  har dimple dinsa ya lotsa ,rasa mezai cewa yayansa yayi dan haka yace  shikennan Yaya zan duba nagani  idan hakan zai yiwu dan gsky Ina matukar son aikina km banason abinda zai rabani dashi .

 ,DEENI..yaya Muhamud ya sake kiran sunanshi DEENI ya dago da idanushin yana dubansa dasu  , wannan aikin naka  yana mahimmanci a rayuwa  Shima   km talafawa company,s dinmu  haka ,amman abinda nake so dakai  kaduba din kmr yadda kace ,nan suka bar zance suka  shiga hirar duniya har DEENI yake sanar masa da abinda mama ta abuja, tayiwa Ummi akan zeenat , Shima Yaya Muhamud din baiji dadin abinda Tayi ba .



Bayan wata biyu 


Al'amarin duniya fa yasoma damun  Zeenat  tayi mugun  tada hankali kan maganar aunty,n su Ita DEENI gabadaya afrigice take da komai , kawai burinta ahalin  yanzu bai wuce kawai ta ganta dauke da ciki ba .

amman kwata kwata  hakan yaki samuwa gareta ga lokacin na tafiya   , gabadaya  hankalinta  a tashe yake matuka.

 haka ma ta bangaren  Ummi itama  hankalinta  a tashe yake da  yadda take ganin yanayin diyar tata. 
 ,shi kuwa gogan sam  bbu ruwanshi da wani tashin hankali da suke cikin .
  ' hakar gabansa kawai yake domin  komai yana tafiyar masa yadda yake so  daga office har gida  .



Sakamakon damuwar da zeenat tasawa ranta ne har hakan yajawo   ta Dan rame kadan kallo daya mutun zai mata yagane tana cikin tension .
" Ko school ma sai da  wata friend dinta may suna halima  ta gane Tana cikin damuwa  dan haka tmbyeta ,zeenat bata wani boye mata komai dangane da halin datake  ciki ba .

 ,nan fa halima tace Ina ai baki Ga ta zama ba zeenat  kishiya fa ....Ai ni ko sunanta ban kaunar ji ballanantana tashigo min gida gaskiya kitashi tsaye tun wuri , zeenat marairaice murya hali bansa yadda zanyi ba ,bansan koina ba , hospital kawai nasa km muje ,hali tace ok kada ki damu akwai wani mutun danasan yana bada maganin haihuwa ,kibari zan rakaki gurinsa amman a sango ota dake hanyar abe okuta yake ,idai zaki zan rakaki  ,zeenat najin haka ta kamo hannunwan halima duka cikin hannuta Tana murna  dan Allah hali kitaima min koma Ina ne zani indai zan samu cikin haihuwa nidai banason mijina yayi min kishiya  dan bana kaunar zama daita a rayuwata  ta duniya  km nasan rashin haihuwar nan zai iya bawata shigo min gida .
 gara mutuwata danaga zuwan wannan rana.
 ,hali tace haba kada ki damu zan taimakamiki ai murigada mun zama daya .
Nan fa suka bar zance da zumar gobe zasu tafi songo ota .😭😭😭



Washegari kuwa da wuri zeenat tashirya har Ummi tacewa yana Ga yau kinashiri cikin sauri haka.
Murmushi Tayi kawai Tayi wlh  , Ummi lecture gareni da wuri shiyasa kika ganni haka.
  Ummi tace ok ,  koke fa haka nake son ganinki cikin walwala da kazarkazar tattare  kwanciyar hankali .
,banason ganinki cikin damuwa zeenat ta sake yin  murmushi tare da  cewa  Ummi sai ta dawo Ummi tayi  mata addu'a .


Haka suka je gurin may bada maganin Ita da hali batare da sanin kowa ba .
Bawani abu mutumin  yabata ba, baya Ga  garin magani baki    yace ta da lemun tsami ta dinga da sha  da zarar sun gama sex da mijinta har sai maganin yakare har yana sake tabbatar mata maganin bazai kai Ga karewa ba zata samu ciki  . Uhmmmm 

da murnarta dawo gida km Tayi  kmr yadda mutumin yace Tayi.
 ,tare da zaman jira tsammani , har zuwa  lokacin zuwan  period dinta, bata Ga  jini ba  , .

  Tacigaba da shan magani  ,murna kuwa  kmr ta Yaya ,dan duka  tunanin ciki gareta amman byn kmr sati daya da shanye maganin  sai Ga jini ..
ranar kuwa data Ga jinin zaman dirshan Tayi a bayi "tare da daura hannuta  duka bisa kai ta saka kuka a gurin .

 ,wunin ranar bbu inda  taje ko parlour kasa bata keko ba , ,  Ummi zaune ita da DEENI wanda Bai dade da dawo ba zaune yake  kusa da ummi suna hira ,ganin shr shr bata zeenat ba yasata  zuwa dakinta , da fari ta dauka ko bacci take ,ganinta kwance  tana sheshekar  kuka ne  yasa gaban  Ummi faduwa da sauri takaraso inda take kwance  Tana kiran sunanta ke zeenat.. lfy ki kuwa ,kukan me kike haka ?  

 Aiko zeenat naganin Ummi ta sake rushewa da wani sabon  kuka km  tashiga gayawa Ummi abinda ya faru amman sai dai ta boye bata gayawa Ummi zance zuwa gurin amso magani ba .

Allah sarki Ummi baiwar Allah haka ta dinga rararshinta Tana kuka itama. jin shr yayi yawa ne yasa DEENI biyo bayan  Ummi yaga ko lfy  aiko  yaga abin mamaki dan zaune ya  tadda ummi yayinda zeenat din ke rungume ajikinta  suna aikin kuka tamkar wayan,da akayiwa mutuwa mai zafi.
Yana ganin haka yasan iskancin zeenat din ne ya motsa  ,dan haka bai wani damu ba ko tada hankalinsa.
  " dan yasan zance gizo baya wuce na koki ,sai ma tsawar  daya dakawa zeenat din ..Tare da nunata da yatsansa daya ke....... banson wulakancin da rainin hankali fa yazaki zo ki tasa min uwa gaba da  kuka?
Ke...duk matsalar ki sai sanya mutane ciki.
 
" kinsa Allah idan baki daidaita kanki da kyau ba zan iya  ra.....
Ummi ta katseshi   ta hanyar taga masa hannu ,ya isa haka  bana son jin komai .
km ni ai baita ce tasani kuka ba, Tayi missing din kwanakin period dinta ne so shine da shirmenta  ta dauka ko ciki ne  da Ita ,sai km Ga period din Ta yazo .
  " kasanta da shririta shine ta zauna Tana kuka ,ni km tausayi tabani ,Ummi na kaiwa karshen maganarta , DEENI ya watsawa zeenat din harara ,yanzu ne kika damu da haihuwa ko da kika ji zance abinda kika fi tsana a rayuwarki ?
  Kinsa Allah zeenat ki fita daga idona  kada ki kashe min uwa da matsalarki .
,kikasa   wasa ma wlh me gabadaya zanyi in yaso ki mutu gabadaya na huta da matsalarki   , km bbu abinda zai faru Dan duniyata  zan cigaba da ci hankali kwance  byn baki raye .
 kinga karshen kishi kennan.... zeenat najin haka  ta fashe da wanj sabon kukan Ummi kina jinsa ko .....so yake na mutu yakara aure  sbd ya daina sona ...sai km  Hawaye sharrrrrr .

Dakuwa Ummi Tayi masa da hannuta  ungo nan DEENI  wani  irin rashin imani ne haka ,kake nuna mata , rashin son nata har yakai ka dinga yi mata  fatar mutuwa km a gabana DEENI... ko kunya idanuna  bakaji ba .
To  inshallahu ta Allah bataka ba km  bbu wata  mutuwa a fuskar diyata km haihuwa zatayi shi da yarda Allah .


 Zeenat fa  tashiga neman haihuwa zanga zabga tamkar zatayi hauka duk inda taji ana bada maganin  haihuwa sai karfa taje ba .

 har gurin wata sabuwar malama datazo Lagos   wacce ake Kira da malama  shema,u taje neman magani haihuwa.

 wanda mutune sukayi ittifaki akanta  muguwar Yar damfara ce daga Yola take  ,da farko Kano ta fara zuwa tana Dan farar mutane  mlm aminu Ibrahim daurawa ya fatattakota  ,shine tayo garin  Lagos . Nan ma dai zeenat taje  bbu wata nasara data samu sai kudinta data kashe  .


Cikin haka maganar da mama ta abuja Tayi akan kara auren DEENI taje Ga  kunne big Dady , musamman  yasa tazo daga abuja km  ya nuna mata sam Bai ji dadin abinda Tayi ba.

 ,inda ma shi DEENI din ne da kansa yaso kara aure wannan dadan bbu may hanashi  amman tace lallai sai ya kara aure akan wata lalura ta  matasa ko wani dalili na dabam , hakan baiyi ba dan haka bayason a km tadda zance .

Wannan batu da big Dady  yayi da km daurin gidin Ummi da take dashi yasa hankalin zeenat din kwanciya  .


Cikin dan kankani lokacin ta maida kibarta Tayi fes daita ta dawo da gayunta kmr da.

A cikin wannan lokacin ne latifa takira Ummi tasanar daita cewa  an samu mai aiki karama Yar shekara gamo shabakwai ... yanzu haka jakar kayanta a gidanta ya kwana Amma ita bazata samu damar zuwa ba ,sai dai zata turo mata da number yayar yarinyar takira ta ,tabata address din estate din murna fall cike da zuciyar ummi tace badamuwa turo min yanzu yanzu ,kinji diyarta....ummi na sauke  wayar sako yashigo tana dubawa taga suna kmr salmah Tare da number .


Uhmmmm muje zuwa 
 Fans 😃😃😃😃😃😃😃

*Please kuyi hakuri da rashin jina two days uzurirrika gareni ,da suka Sha kaina  amman  karka danu zuwa anjima nasamu time zan suburbudo muku one page more kusha sha'aninku, dashi lov you ol gyus*😍😍😍😍😍



MMN SUDAIS CE
[7/1, 9:15 PM] 0mmer Farouk: 💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
     💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO



Page 59


Al'amarin gidan kuwa gabadaya ya sake canzawa  tun daga kan mutane dake rayuwa  a cikin gidan har zuwa Ga gidan  karan kansa  .
Dan gabadaya DEENI ya gyara kowa Ina a gidan inda ya sake fadada girman  dakunan dake kasa  tare da kawatasu da ado  .
Wanda  ,a halin yanzu  yakoma  amfani da dakin sama da kasa .kallo daya zakawa gidan ya birgeka km  kasan ya fita daban da sauran gidanjen dake cikin  estate din.



Ummi bata Kira number Salmah ba sai byn data sallami shafa da kwana biyu sannan takirata 


Ranar da shafa ta tarkata tabar gidan ranar  itama Zeenat   tashi da zumar dawowa dakinta na kasa wanda DEENI ya cire mata ,dan haka bata tsaya wani bata lokaci ba tasa laraba tayi mata komai ,tare da abubuwan ta masu mahimmanci sai abinda baza'a rasa ba tabari a dakin sama .itama takoma amfani da daki biyu a cikin gidan.


 Matashiyar budurwa ce Tare da yayarta  tsaye  abakin titi .
 suna jiran mota ' sun dauki sama da rabin awa tsaye  a haka suna jiran abin hawa amman kowace mota tazo wucewa"  cike take tap da mutane .
,sakamakon cunkoson  ababen hawa da aka tashi dashi a garin Lagos.

 , aunty me zai hana muhau machine ne   , kinsa fa inda zamu da Nisa  sosai .
  , saboda ke da zaki dawo .
  Dan naga yanayin garin yau sai a slow inji  cewar  nablah.....

 , aunty Salmah  ta dan juyo ta kalli gefen inda  sisinta  ke tsaye   tare da cewa  'shikenan nablah  muhau machine din kawai Dan nima bana son dadewa .

 gaba  kadan suka  karasa  wajen yan machina, 
    malam dan Allah lawansi bustop zaka kai mu, inji cewar aunty Salmah.
 mai okada ya  gyara tsayuwar machine dinsa ta yadda za su samu damar hawa ..

 Kin hawa aunty salma tayi sai ma tmbyr mai okada take da  nawa zamu bayar tukun.

  , Atakaice dai  muna kai mutun daya  a naira dari mutun biyu dari da hamsi aunty Salma tace  Shikenan ke nablah  fara hawa.
 " dayake kaidar Aunty salmah kennan.
 muddin da kanneta zata hau machine bata yarda tafara zama a farko, sai dai tace su hau gaba ita km  ta zauna a  baya.

   'Ahankali Suka dane machine"
 dai dai bakin  filling station din dake   lawansi, suka sauka aunty Salmah ta bude jakarta tabawa Dan okada kudinsa .

 tafiya   suka soma yi zuwa inda zasu shiga motar da zata kai su surelere .

Suna tafi suna hirarsu abin sha'awa   har suka isa wajen shiga motar Masha.

, daidai Bakin get din da zai kai ka ilori Street suka sauka , tafiya kadan sukayi suka isa inda zasu .

aunty Salma tasa hannu ta tura get din gidan wanda  koda yaushe  haka yake a bude, .

 Da sallamarsu suka karasa bakin net din latifa  .  Aunty Salmah na kwalara mata Kira latifa latifa..  Amman shiru ba amsa yayinda   kofar ma take  a kulle .
Tsayuwar Minti goma sukayi  kafin daga  baya suka jiyo sautin  muryar latifa .
 ku biyo  ta nan kofar  kitchen,an kulle nan ne sbd yara .
" zagayawa  sukayi ta kofar kitchen  suka  shiga.

Latifa   naganin su tasaki murmushi ,kai kai gsky dai Salmah kunyi latti wlh    kin kuwa san nisan unguwar da zaku kuwa ?

 aunty Salma tayi dariya  wlh kinsa halin mutumin naki  hukuma ne sai da rarrashi .
duk shi ya bata mana lokaci , gashi Bai fita da wuri  ba.

 , to shikenan sai kuxo Ku tafi   tun rana batayi ba .        "ai ma hajiyar takirani  tun sassafe tamin kwantance yadda zamuje can din " da ,na so mu wuce ta mushi ne saboda akwai mota mai zuwa  can direct  sai dai kinsa jakar nablah na nan shiyasa dole sai  munbiyo tanan din .                      
  
 Latifa tace ok  ina zuwa ku shiga daga ciki  bari na amso sako  dana aika  .   

 dan Allah kiyi sauri  ba sai munshiga  ba .

ina  jakar take saboda kar  lokaci ya wuce ?latifa  ta kwallawa  mai aikinta  kira... ke uzaima ... 
"uzaima ta amsa tare da karasowa ,Gani aunty jeki dauko  jakar nablah a karkashin step yanzu .

Sannan taje tasamu yaron mijinta da ta aika tun dazu ATM tace ibrahim ya'akayi ne ,ya tura hannu ciki aljihun wandonsa ya  ciro kudi masu yawa ya mikawa  latifa Tare da ATM a saman kudin  tace yauwa  na gode.

  har ya juya ta  kiransa  ya dawo ,  akwai wa'yanda nike son  ka    dan kai mun   su inda zasu samu motar zuwa  obalende .
, yace to badamuwa ,ta koma ciki inda ta tarar har an dauko jakar nablah  ,latifa  taciro dubu biyar ta mikawa Aunty  salmah gashi kikara kuyi kudin mota dashi ,saboda yanayin hanya .

 aunty Salma ta amsa tayi  godiya, hade da yi mata sallama .
 bakomai  sai kin dawo mayi waya duk abinda ake ciki Kya sanar min ni dai addu'ata Allah Yasa tayi musu ..
  
Kai tsaye   inda zusu samu motar da zata kai su  obalende  ya, ajiye su .

,  Suna tsaye  cikin mota BRT  dayake standing suka samu ,  Aunty  salmah tace  nablah ajiye jakar kayanki   ki zauna akai  .
Sannan kiciromin wayata a jaka ki duba dealing zakiga wata number MTN karshenta 12 kikiramin ,ki mikomin.

 ,haka kuwa nablah tayi tare da  Mikowa Aunty salmah wayar .

 ta  manna wayar a kunneta tare dayin sallama. hello hjy gamu cikin motar obalende daga nan wace motar zamu shiga" daga can bangare  ummi kuwa  cewa tayi yauwa inkunzo ku hau motar mai zuwa aja sai ku sauka (a jakonde first get).
 ai kinsa lekki ko?

 "  aunty Salmah tace A,a bansan side din  ba , ina dai jin sunan waje.

 Ok ..   inda kun sauka a first get din kiyi  flashing dina.
 Aunty salam  ta, ajiye wayar..

Bayan kmr  awa daya da rabi   sai gasu     jakonde first get...


 Kiran ummi suka sake yi kmr yadda  tace .
 ok kuyi crossing main road  ta hannuku  na daman zakuga sambord an rubuta lekki road hanyar zaku biyo layi na uku .
daga hannun hagunku in kun kai kikirani

 ,nan dai suka sakeyin tafiya minti goma suka sake kiranta byn ta dauka ne tace kuna kan layin ne?
  Aunty salmah tace  Eh to zakuga cona ta hannun  hagunku  zakuga wani babban church ,dan suna tafiya ne  suna waya da ummi  tana basu direction .

 Aunty tace ga church din nan  ma mungani  to ku tsaya a wajen zaki ga get  opposite din shi .aunty Salmah tayi saurin cewa  shine.

 PLASNUW   ROWS FAMILY  ESTATE ?

 Ummi tace yauwa shine  kin iya rubuto?
Sai da  Aunty salam tayi murmushi sannan tace  ba laifi .
 ok  bani minti biyu   na kira securities din get din.
" za su tambayi sunanki aunty salam tace to ....


 Nablah ta zubawa hadadden  get din gidan idanunta kawai  wanda basan yadda zata iya kwatanta  girman sa ba ballanantana tsawonsa .

sai dai zata iya kiran get din  da JAMA GET ..wato na gidan bursunan dake garin Lagos KIRIKIRI .

   daya daga cikin securities din get din ne ya dan leko ganinsu tsaye ne  yasa shi  cewa  madam can i help you?  
who are you, looking 4 duk  a tare ya  jehowa auty Salmah tamyr dayake itace kusa dashi.
 ,  
 the person we are lokin 4 said we should Wait  4 her "inji cewar aunty Salmah mutumin yace or rigth  sannan yakoma mazauninsa "

can ya sake lekowa yace  are you salmah ?
  "auty  Salmah ta  daga masa  kai .
  'yace ok you can  come in.
tare da  bude musu Dan  karamin get suka shiga  ya nuna masu ,wani gurin yace inter and rigth ur ful name down
 ,Can  u  write ya sake tmbyr Aunty Salmah.
 tace Eh.
 byn sunyi komai har da sign sannan ya sake bude wata kofar   yayi gaba yace su biyo shi a baya.

 daidai wani katanfarin gida mai dauke da tampal ,wanda duk gidanje wajen kusan  haka gininsu  yake iri daya Kuma sun kai  guda hamsi a jere ,  banda new buildings da ake sakeyi  km kowanne gida  da number a jiki,..
     no 20 ya nuna musu  da yatsansa yace this is the place  sannan ya juya.

 Ahankali suka isa ga kofar daya nuna batare da bata lokaci ba   sukayi nouking, wata mata ce da bata wuce ki mananin shekaru ashirin da takwas zuwa   talatin ba   tazo ta bude musu  kofa   hade da  yi musu  sannu da zuwa.


 wani hadaddin falo may maseefar  kyau ya kawatu da kayan  kwalliya  wanda  yasha kyau ya gaji da kayan more rayuwar duniya .
, sukashiga hade da yin sallama ,  ga wani kamshi na musamman dake tashi ta koina a parlour,  wani irin sanyi ne ke ratsa musu tsantsar   jiki .
 take duk wani zafi rana da gajiyar hanyar  da suka debo suka  nemata suka rasa  ...

 wata dattijuwar mace ce zaune bisa kujera dake zagaye da parlour ,hannunta rike da waya, duk da ba wai saninta  nablah tayi ba  Amman take jikinta yabata da ita suka dinga commincating a waya  da auntyta .

 kallo daya  nablah da ummi sukayiwa juna" take gabansu yashiga faduwa  a tare  zuciyoyinsu ya amsa dummmmmm na minti biya kafin daga  baya ya dawo daidai.
  ,wani bakon al,amari ne , yashige su a tare wanda dukkansu basu san dalilin jin  hakan ba. a wannan kallo da nablah  tayiwa ummi  ne,  tagane yadda take  jin dadin  duniya .
 Ga km  tsabar jin dadi da   hutu na musamman da  ya bayyana a jikinta .

Gaban nablah yacigaba da faduwa yayinda  Koina na jikinta ya dauki  kirma .... musamman zuciyarta da taji tana  dokawa da sauri.

 Da  fara,ar ummi  ta tare  su ,tana musu , sannu da zuwa tare da  nuna musu   wajen  zama da hannuta   zama sukayi  suna gaida ummi .

  sannuku.. kunsha rana  Amman Kuma  kunyi sauri wlh ai nayi mamakin da kika ce kuna first get.

 aunty salam tayi murmushi sannan tace  nima  wlh haka nagani .
,yayinda ita km   nablah   ke zaune  abunta Tana  raba idanuwa  tare da    karewa koina na  parlour da  kallo .

Ajiyar zuciya kawai Ta dinga saki 'ahankali 'ahankali domin , irin gidanje datake  gani a TV  ne wai yau take zaune acikinsa, km har  zata zauna a cikinsa ta cigaba da rayuwata  zuwa na  wani dan lokaci , .

'Ahankali ta maida shanyayun idanunta   inda  ummi  ke zaune tana sake dubanta da kyau   , girgiza kanta kawai Tayi  tare da yin  zance  zuci, cikin haka ta tsinci kanta da yi musu addu'ar  hakika wasu  sun zo duniya a sa'a, Allah yasa lahirar su tayi kyau 'ahankali ta maida kanta kasa ta sunkuyar tana wasa da Zara zaran yatsun hannuta masu matukar kyawun gaske.

 Suna nan zaune a gurin  aka shigo musu  da abin sha  ,ruwa ne may tsanyi da  malt sai kayan fruit  wanda suka   dauki tsanyi suma.

, km duk nablah Tana ganin hakan ne a zahiri aka ajiye agaban su, hjy  ta gyara zamanta  tare da kiran sunan aunty Salmah ....  salmah ko?
 Aunty ta dagawa ummi  kai kawai .
 ,  wannan ita yarinyar  kennan?
  murya auty salmah ne ya daki kunne nablah .
 eh itace hjy .   

'Ahankali ummi ta saki ajiyar zuciya sannan ta dauki wayarta dake gefen kujera takira zeenat .

minti kadan byn  kiran wayar da  ummi tayi, nablah taga  wata kyakkyawan mata ta fito daga wani bedroom wanda da alamun muhalinta kennan  itama kana ganinta kasan naira tasamu gidin zama ajikinta tafiya take tamkar bazatayi ba, sai rangwada take tana zuba kamshi jikinta sanye da  Riga da sike na a tamfar super exclusive kayan sun zauna ajikinta das.
,Takaraso . ta  zauna kusa da ummi  batare da tace komai ba ,yayinda  fuskarta take  a daure  bbu wani annuri  tana kallon  nablah dake zaune a gefen aunty Salmah   taji wani abu ya dungule mata a kirji,   gabanta yashiga  faduwa  'ahankali ta dauke idanunta daga kan nablah ,tana sake jin faduwar gaba.
  

 'Ahankali ummi ta numfasa sannan ta cewa Aunty Salmah kice yarinyar   ta Mike tsaye  mana .
"     tun kafin aunty Salmah ta bawa nablah umarni ,ta Mike  tsaye cikin sanyi jiki wanda kusan  yanayina kennan akoda yaushe. 
Amman wannan karan yafi na kowani lokaci Dan gabadaya ilahirin jikina  ya sake yin  sanyi
 ,daganin irin kallon da zeenat ke mata .
    dan haka  gaban nablah yacigaba dukan uku uku  kallon tsaf  ummi  tayi mata  sannan ta lumshe idanunta .
  ita kuwa nablah tunda tayiwa ummi da Zeenat  kallo daya ta dauke   idanunta daga garesu bata  sake kallon Ida suke ba  , domin  hakan   yana cikin nasihar   da auntyta tayi  mata kafin su fito daga gida  .

Nablah kina ganin masu kudin nan iyayi ne dasu gashi mafi  yawancinsu "basuson shishigi dayawan kallo.
 ki zauna lfy da duk mutane  gidan, kitsaya a matsayin ki  ,abinda ya kai ki shi zakiyi dan Allah nablah karkisa naji kunya  a in da zan kai ki kinji Yar kanwata ...

' Ahankali nablah  ta dawo daga  tunanin data tafi  na wucin gadi tare da  dago shanyayun idanunta  tana sake kallon matar data shigo saboda jin sautin  muryarta mai cike da  tsabar iyaye wanda dagani har  da iskanci aciki . 

Ummi kina ganin  yarinyar nan  kuwa zata iya aikin gidan  nan ? Sai naga kmr tayi karama 
Amman dai ...sai km tayi shr ta  Mike tsaye tare da cewa .
  ummi zo  muyi wata  magana dake.

  Ba musu ummi tabi bayanta byn sunshiga wani  daki dake  cikin dakunan dake kasa ne , Zeenat ta   sauke ajiyar zuciya sannan tace 
,
,Gsky ummi ni  fa kwata kwata yarinyar nan banji ta kwanta min a rai ba haka km   tunda ake kawo masu aiki gidan nan, ban taba jin yarinyar da naji tsanarta farar daya a zuciyarta ba kmr  ta ,Dan haka ummi  kibari suyi tafiyarsu kawai .

 Ni asona ma    , da abar laraba , kawai  ta isa ba sai an karo wata ba ,tunda tana yin komai yadda yakamata.

 ,ummi ta girgiza kai  byn tagama jin Zeenat din tsaf..,ni km kinga Ina ganin yarinyar naji ta kwanta min wlh.
  kema kiyi kokarin ta miki tamkar yadda naji araina  kinji diyata , ba'a saurin tsanar mutun , km ,da alamun akwai natsuwa a tattare da yarinyar  .
Zeenat tayi shr tare da kwabe baki kawai takasa sake  furta   komai  ,.
Har Suka dawo parlour.

tasan tunda yarinyar tayiwa ummi magana takare .

 ummi ta zauna tare da sake duban inda nablah da Aunty Salmah ke zaune , sai data numfasa sannan tasoma magana kmr haka gsky yarinyar tayi  sai dai  Kuma   ajira zuwan may gidan   muji  me zai ce akanta , idan Tayi masa zakiji ni a waya ,idan km akasin haka ya faru ,Shima zakiji .
, nablah ta runtse idanunta kirjinta ya shiga bugawa   jin  sai wani yaganta sannan za,a dauketa aiki .
bayan duk  wannan kallon kurulla da'aka tasa gaba da shi .
,nan gaba km  sai an sake kawo mata sabon rainin hankali .
 na hada da  Kato ya ganita.
  , tsuke dan karamin  bakinta tayi   tana mai jan tsaki acikin  xuciyarta .

Aunty Salmah tace bbu komai hjy duk yadda kika yi daidai ne 'ahankali ummi ta sauke ajiyer zuciya ..  tare da  saki murmushi jin dadi.
 , Sannan tace baku ci komai ba.
 aunty Salmah tayi murmushi itama sannan tasa hannu ta dauki malt ta bude Tasha kadan  ta,ajiye amman ita nablah kasha komai tayi Dan bataji zata iya sakawa cikinta  komai ba balle ruwa gabadaya hankalinta a tashe yake da jin furucin ummi na karshe .

  sake fuskantar  Aunty Salmah da kyau ummi tayi ,  akwai check up  da',ake wa sabbin ma,aikatamu saboda sanin  ingancin lafiyar su ,so  itama za'a mata  da fatan hakan bazai zama da wata  damuwa ba.

" Aunty salma tace wannan ba wata  matsala bace Dan  na yarda da  sis na  ,💯Kuma ina da tabbacin komai normal zaku gani inshallahu ...km duk aikin dakike so zata miki Dan gwanace gurin iya aiki bbu aikin da zai gagareta ummi tayi murmushi tare da cewa Nagode sosai sannan ta kalli nablah dake zaune a gefe  shr sai faman wasa take da yatsun hannuta.

kina jin abinda yaayarki tace ?
,nablah ta dagawa ummi kai alamun taji  ,ummi tace A'a nifa bana son kyaliyya ki bude baki kmr yadda na miki ,sannan ta dubi aunty Salmah ko bata magana ne naga tunda kuka zo batace komai ba?.

Aunty tayi murmushi  ,Tana yi .
,kiyi magana mana  kinjin mutane , tare da cewa Killa har da rashin sabon,dabatayi daku bane .
 amman  tana da saurin sabo da mutane da son yara .
Ummi tace mayye sunanta ,aunty tace nablah ..sai da ummi ta sake maimaita sunan a kasan ranta wanda  hatta zeenat dake zaune  sai da ta dan juyo ta sake kallon inda nablah ke zaune a rakube ,ummi tacigaba nablah barkanki da zuwa gidana ... gidan dana, amana ne a hannuki zaki zauna tare damu na tsawon shekara biyar kmr yadda auntyki tasanar min a waya ,wai kince inkin zo bazaki koma ba sai kinyi wayannan shekaru dai kin dinga zuwa dubasu time to time to Dan Allah ki natsu duk abinda ban baki ba karkisa hannu ki dauka  in km kina bukatar wani abu kisanar dani ko  wannan   ummi ta nuna mata Zeenat da yatsanta,  zata baki matsawar baifi karfinta ba yanzu dai za,a kaiki ki huta kafin zuwa gobe zata Nuna miki aikin dazaki dinga yiwa diyata km matar dana  wacce kike Gani zaune a gabanki ,kin iya abinci ?  Da kyar nablah ta iya bude baki cike da sanyin jiki tace eh...

Itama aunty Salmah takara da cewa ta iya Sosai amman bansani ba  ko ta iya irin na yan gayu ba .
ummi ta sake yin  murmushi kawai to shikennan badamuwa koda  bata iya ba.
 da zarar tayiwa mai gidan za'a dinga koya mata har ta iya .abinda yasa kika ji Ina cewa haka mai gidan ne akwai shi da kyamkyami   shiyasa .


Aunty Salmah tace bbu komai ai hakan yana da  kyau , ummi tacigaba gidan nan  sama da kasa ne aikin share share da girki sai  abinda baza a rasa ba .

aunty Salmah tace abu na karshe da zance kafin na wuce Bai wuce kuyi hakuri da nablah domin yarinyace karama da bata wuce shabakwai ba koda zatayi ba daidai ba a tsawata mata dan bata taba yin aiki ba wannan shine karo na farko duk da nasan bata da rawar kai ummi tayi shr Tana sauraron aunty Salmah tare da addu'ar Allah Yasa oga DEENI yayi maraba da wannan matashiyar yarinya .
dan ita kanta yarinya ta kwanta mata fiyye da tunanin mai karatu uwa uba natsuwa da take Gani a tattare da ita .

Aunty Salmah ta juyo tana kallon nablah kin san ban kawo ki aikin nan ba sai da amincewarki dan haka na rokeki kiyi musu duk yadda suke so kinji takarasa fadar haka tana mai kamo hannun nablah cikin nata tamkar zata zubda hawaye ,sai duk jikin nablah ya sake yin sanyi, idanunta suka ciciko da Hawaye data dade tana boyesu take ta mayar dasu dan batason aunty,ta tagane yanayin datake ciki dan tabbas aunty Salmah naganin hawayenta sai tayi kuka itama .dan tasan ko a yanzu da take magana ma dauriya ce kawai da karfin hali irin nata.

Aunty Salmah  ta kalli ummi tana mai cigaba da yi mata bayanin ,ta zabi yin aikin nan ne sbd tana son cigaba da karatunta, dan tun 2016 tayi weac yayinda tayi jamb dinta  a ,2017 . ummi ta katseta ta hanyar tmbyeta kanwarki ce jini ?
Aunty ta bata amsa da uwarmu daya ubanmu daya itace autarmu a mata ummi tace Ga kama nan kam.
 sai dai tafiki kyau sosai aunty tayi murmushi sannan tace  saka makamakon abubuwa da suka mana yawa ne yasa ta gwammaci tazo tayi aiki dan wata uku kennan  dayin  walimarta, Shima da kyar da bugabuga Allah Ya rufa asiri muka biya mata kudin . shiyasa  data takawo wannan tunanin muka amince.
 in bancin haka baza mu taba amince ba sbd zuciyarmu ce nablah   gabadaya ilahirin Yan gidan mu muna mugun son nablah koda zamu taho har kuka mahaifiyarmu tayi.
 haka ma yan gidan mu kaf. ummi ta jinjina kai yayinda zuciyarta Ta motsa da tausayinsu .

Ummi tace karki damu Salmah da ai na kowa sannan ta sake duban inda  nablah ke rakube tamkar tana gaban sukarta yayinda Zeenat ke zaune haushi tamkar ta hadiye zuciya  haka dinga ji .

Ummi tace wani school kike son zuwa aunt Salmah tayi saurin cewa BUK dan tasan halin nablah da sanyi tsiya .

 ummi ta sake tmby wani course Shima aunty ce tabada amsa da accounting take son yi sai dai rashin mathematics yasa nace ta canza ....

Ummi takira sunan Salmah ....  ki barta ta amsa min da kanta man ai ita tafi sanin abinda yakamata daita.

Sannan  ,ummi ta tattara hankalinta kacukan akan nablah tare da zuba mata idanunta dan haka kawai taji yarinyar tayi mugun shiga ranta .
uhm nablah me kike son karanta a BUK nan dai tayiwa ummi bayanin kmr yadda aunty,ta tace dan bazata so ta fadi wani abu.
 da  daban wanda zai yi disgrace din auntyta. ummi ta numfasa ,tace sai maganar salary  nawa za'a biyata Aunty tace mudai bamu san kan yadda  abun yake ba ,Ku kukasan yadda kuke biya masu aiki tana gama fadar haka taja bakinta tayi shr.

 ummi tace eh to kmr dai shafa data wuce muna bata  dubu talatin a wata  .
Amman ita wannan bazan iya cewa Ga iya abinda za'a bata ba sai mai gidan ya dawo tukun Dan  ,ba mamaki idan Tayi ,zai iya bata fiyye da hakan .Sai km Yadda bada  kudin zai kasance za'a barsu ne anan ko km za'a rinka bata a hannuta  sbd koda zata bukaci wanni abu.
 ,dan kudin masu aikin gidannan a gurina suke km duk lokacin  suka bukaci yin wani abu dashi nakan basu abunsu  .

Aunty Salmah tayi saurin cewa A'a account dina za'a dinga turowa ummi ta sake cewa A'a Salmah kibarta ta fadi yadda take so ayi sbd hakinta ne aunty Salmah taja bakinta tayi shr .

ummi ta juyo suna fuskartan juna da nablah  tace ya nablah me kika ce ,a turawa Salmah ne ko zaki bude account naki ?

Nablah ta girgiza kai a tura a account din auntyna kawai , dukkansu dariya sukayi har aunty amman Banda Zeenat Sai ma tsaki data ja tana cika tana batsewa.

Ummi tace gsky kun birgeni dagani akwai fahimtar juna a family dinku .
, shikennan kituromin account number dinki ,yanzu dai kinga wata yayi rabi Dan haka duk abinda mai gidan yabada zaki gani ta account .
Sannan tace Zeenat taje takawowa aunty Salmah kudin mota .

Zeenat ta Mike a yangance ta nufi dakinta na kasa bata dade ba ta sake fitowa ta mikawa Aunty Salmah kudi masu yawa takarba tare dayin godiya sannan ummi ta danna intercom minti kadan Sai Ga laraba ummi tace laraba Ga sis nan kinsamu koma nace "ya" laraba tashiga bude hakora tana dariya ki dauki jakar kayanta ki kai opposite to ur room laraba ta duka tare da dauka jakar kayan nablah tayi gaba tana murmushi samun abokiyar hira Dan tunda shafa ta wuce take cike da kewa .


Aunty Salmah ta Mike tsaye to ni  nablah zanwuce itama nabla Mikewa tsaye tayi domin son yiwa auntyta rakiya.

 ummi tacewa Salmah baki bani account din ba har gashi zaki wuce aunty Salmah tace zan turo miki ta waya sannan km zan bawa mahaifiyarmu number ki sbd koda tana son magana da nablah.

 ummi tace bbu komai Sai kinjimu sukai yi sallama suka fito tare da nablah hannunsu cikin juna .

Sun Dan yi nisa da gidan kadan suka tsaya aunty  Salmah ta dube nablah da kyau tace yana Ga duk kinyi wani iri,kodai kin fasa yin aiki ne muwuce Dan nima Ina jin wani iri ajikina barinki dazanyi ?
, estate shr haka kmr makarbarta , maganar aunty Salmah ce tasa nablah sakin murmushi tare da cewa kai aunty , aunty Salmah takatseta da bawani kai aunty , idan kinji da matsi da takura ,waya kawai zakiyi min kice aunty kizo nabla ta sake sakin murmushi Wanda ya bayyana wushiryarta me matukar kara mata tsantsar kyau.
 cikin siririyar muryata me dadin sauraro  tace kina zuwa ki dauke ni peeeeeee mu wuce abunmu ko auntyna.... suka saki dariya a tare sannan suka cigaba da takawa 'ahankali har suka karaso  bakin get din estate din .
  ita km aunty Salmah tashiga  office din da suka shiga dazu  sanda zasu shigo, ta sake sa hannu da lokacin data fita ,duk nablah na tsaye tana kallosun tare da dagawa auntyta hannu har ta fice daga estate din sannan ta juyo jikinta a mace 'ahankali tasa bayan hannuta ta goge Hawayen daya zubo daga idanunta.



Da misalin karfe tara na dare tana zaune a dakin da aka mata sauki byn ta idar da sallah isha'i ta cire hijab dinta ta nike tare da shirin  ajiye akan jakar kayanta kennan taji ana nouking kofar dakin 'ahankali ta mike taje ta bude kofar  badan  tayi wa kofar key ba  .
 laraba tagani tsaye tana mata murmushi tare da cewa kizo inji  hjy dayake ita da haka take kiran ummi.
 nablah tace to ta juya  koma cikin dakin ta dauko hijab dinta ta zira har kasa ta biyo bayan laraba  'ahankali take daga kafafunta cike da sanyi jiki  da natsuwa har suka iso wani parlour.

 ,kallo daya nablah  tayi gurin tagane bawanda aka saukesu ciki bane dazu abinda yasa tayi saurin gane hakan kujerun wancan parlour da wannan ba iri daya bane , sannan komai na wannan parlour daban yake hatta pantting  laraba ta Dan duka tace hjy gata nan   ummi batace komai ba Sai ma daga  mata hannu datayi  alamun ta wuce .


Ummi ce zaune da Zeenat suna facinga din juna hira suke suna kallon Ball  hankalinsu kwance , nablah ta gaishe su da hannu ummi ta amsa mata tare da nuna mata  gurin zama .
amman ita Zeenat ko kallon inda nablah take batayi ba sai ma sake maida hankalinta datayi Ga TV .
Nablah bata zauna kan kujera ba kmr yadda ummi tayi mata nuni  waje tasamu kasa nesa kadan dasu ta tattare hijab dinta ta zauna shr kusan minti goma bbu Wanda ya sake cewa komai acikinsu daga ummi har Zeenat Sai karar TV da AC dake aiki....





MMN SUDAIS CE
[7/1, 9:15 PM] 0mmer Farouk: 💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
       💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO




Page 60




 'Ahankali ta sunkuyar da kanta kasa tana wasa da yatsun hannunta wanda kusan rashin abinyi ne kesata yin haka.

 ,haske taga ya garwaye parlour gabadaya 'koina ya dauki haske tamkar rana ce ba dare ba.
 wani irin kamshi ne mai azababen dadi  yake kusantota ,har inda take zaune ,yayinda mamallakin turaren ke tukarowa parlour zuwa indasuke haka shima kamshin ke kai kawo acikin hancin nablah .
har zuwa sanda mamallakin kamshin  ya karasa  yashigowa,  gabadaya parlour ya canza wani  irin cent na daban",  take gabanta yashiga dukan uku uku  gashi tana san  dagowa ta kalli kowaye mamallakin wannan azababen kamshi Amman takasa dago idanunta,dan ko kwakkwaran motse kasawa tayi   ballanantana tasan kowaye mamallakin wannan turaren mace ko namiji ne sakamakon  kanta dake Duke   akasa har lokacin.
 Ta kafe teas din parlour da  ido ".

Ta kasan idanunta ta hango wando jeans. wanda hakan ya tabbatar mata  da mammallakin kamshi turaren nan    namiji ne .
 "duk da   bataga komai   nashi , baya ga Zara zaran yatsun kafafuwansa da kowani ke kwance da gargasan gashi.
  'ahankali  yake takowa zuwa inda ummi  take zaune  .

Muryar ummi  taji tana cewa ka fito son ?
 tun da zu  muke Jira ... matarka tace wanka kake yi  ,'ahankali ya  juyo ga  mahaifiyarsa  yana kallonta sannan yadanyi  murmushi gefen baki .
   hannunsa yasa  ya  dauki remut ya canza channel zuwa ta  kallon Ball  sannan ya   Mike kwance kan  three site hade da cewa gani  first lov  anything for you my beautiful mum...  
Ummi  ta saki murmushi sakamakon jin dadi abinda yace  sannan tace  kai ko Allah ya shirya min kai ...tare da kai  hannuta  kai kan tilon dan nata ta shafa tautausar  sumar kansa  tana jin wani irin sanyi a ranta .

Muryata A dake  takira sunansa ' deeni.....
Ya dago rikitattun idanushi yana kallon ummi batare da yace komai ba ...
  "maganar mai aiki da mukayi dakai za'a kawo   ,to orready ma  she's here..  ta iso sauran muji meyye ra:ayinka   nidai na  amince daita hundred percent  ..

kasa kasa yayi da muryasa wanda  daman can  haka  yanayin maganarsa take .. 
Kuma yadda yayi magana  ummi  ce kawai zata iya jin meyace ..

tana ina .......?

 abinda kunne nablah  ya ji kennan.
 gata can ummi ta fada tare da nuna inda nablah take zaune ...

'ahankali ya juyo tare da  kallon  inda ummi  tayi mishi  nuni da hannuta. idanunshi ya runtse  gam sannan cikin sanyayyayiyar muryasa mai kashi jikin duk wanda tsautsayi yasa ya fada kunne shi " yace first lov...  kice ta Mike naganta ..

tsoro da fargaba tare da  frigice ne  suka taru suka kaiwa zuciyar nablah farmaki" tashi daya taji   jikinta yakama rawa  gabanta yashiga faduwa da sauri, tasoma  tunanin abinda   ya kawota  wannan gida mai cike da abun tsoro da abubuwan ban mamaki ...

sai kawai ta tsinci kanta da ambato sunnan Allah a kasan ranta  da karanto  duk addu'ar datazo bakinta Dan rage jin tsoro " take taji wata natsuwa tazota mata   aboye ta dinga sauke ajiyar zuciya .


'Ahankali ummi  takira sunata  nablah  Mike tsaye  man ya ganki ,  batare da wata gardama ba,ko bata lokaci ta Mike tsaye kmr yadda ummi tace .Amman still jikinta Bai bar kirma ba haka ma  hannuwata suna sarkafe  da juna tana cigaba da wasa dasu  " yayinda ta cikin hijab dinta  kuwa uhmmmm tashin hankali kennan 'dan kuwa  jikinta sharkaf yake  da gumi tsabar frigici datake ciki  ,duk da tsanyi AC dake aiki a  parlour hakan bai hana  gumi tsassafowa ilahirin jikinta  ba .

 idanunshi da Suke a runtse ya kafeta dasu yana kallonta ,jin shr,n da yayi yawa ne yasa nablah dago fararen idanunta dan satar   kallon  mutumin dataji an Kira da suna DEENI . take zuciyoyinsu suka buga a lokaci daya .......


Yayinda  jikin nablah  ya dauki  kirma... zuciyarta ta sake amsawa daf..daf..daf.. 'da sauri tayi kasa da idanunta ahankali ta furta  wayyo Allah na.. a kasan ranta.. mutun ko aljani nake Gani yau .

, tsabar kyauwu halitta  da Allah yayi masa .tunda take  a rayuwarta bata taba ganin mai tsananin kyau halitta  da kwar jinin irin mutumin da take gabansa tsaye a halin  yanzu haka ba .

 kusan   tsawon  minti  5 ya dauka yana kallonta batare daya bude Idanunshi ba" sannan 'ahankali ya dauke idanunsa daga gareta  yakoma ya  kwanta sosai acikin kujerar dayake "ummi  tace ya'akayi ne DEENI  naji kayi shr...  ....

Tayi.....
.
abinda kawai nablah ta iya  ji  kennan daga bakinsa , Dan gabadaya ma jitayi kunneta ya daina jin magana tsabar tsoro da rikici   hakan  km  sai lokacin hankalinta ya dawo gangar jikinta daga mummunar damuwar data tsinci kai  ciki ...
 Amman fa duk da Haka  a tsorace take da mutumin dake kwance a gabanta .

 ,ummi kuwa ta furta kalmar alhamdulilllahi yafi Sau dari kafin daga baya ta kalli nablah  a tsanake sannan tace jeki nabla ma hadu gobe  kinji ..

,muryarta nablah a sarke tace to ... sai da safenku sannan   ta juya  cikin tsanyi jiki  ahankali take tafiya yayinda itama   ummi  ta juyo tana sake bin bayan nablah din da  kallo har tabar parlour  zuciyarta na karanto mata abubuwa dayawa game da yarinyar ga wani irin tausayin yarinyar daya mamaye zuciya ...
 

Bangaren   deeni kuwa gabadaya ji yayi tamkar am masa wanka ne da ruwan sanyi  , jikinsa ya mutu murus tamkar mara lfy haka ya dinga ji ajikinsa tun sanda yabi hannu ummi  da ido .

kwarai  yaso ya bude idanunshi yakarewa  yanayinta kallo Amman sam  yakasa aitawatar da hakan , sai ma tsintar kansa da yayi da mummunar faduwar gaba a lokacin da yake kallonta .
, wanda har yanzu dayake kwance a wajen  bai daina jin yadda zuciyarsa ke bugawa da sauri  ba .. 

'ahankali yasake runtse idanunshi gam ko zai daina jin abinda yake ji  ajikinsa ,amman kwata kwata sabanin haka  Ya dinga  ji .
 Sai ma  zuciyarsa da tacigaba da  harbawa da sauri da sauri .

 abinda bai taba ji atare dashi ba kennan tun iya tsawon rayuwarsa wai faduwar gaba akan mace  ....
Macce ma , mai matsayin mai aiki ... 

ahankali ya furta sunan  da yaji umminsa  takira yarinyar dashi nab....lah... Yadda ba mai jinsa ....

 muryar matarsa yaji tana cewa ummi   ai wannan yarinyar bakaramin  daga tuta tayi ba ,  tunda har my hrt yace tayi.
 
 ummi  tace al,amarin Allah kennan nima gsky  naji dadi matuka da tamasa saboda daganin  yanayin yarinyar ba tmby akwai natsuwa atare daita .
kema kiyi kokarin ki sota a ranki " ba mamaki wata rana tayi miki amfani .

 "  dagani   bazamu samu matsalar daita ba   ", zeenat tayi murmushin karfin hali tare da kwabe baki   Dan ita   kwata kwata bata ji son yarinyar aranta ba   . tanaji a zuciyarta tamkar ta sallameta daga gidan ne yanzu yanzu .... 


 Muryata Cike da takaici tace wani   amfani km  ummi .Allah yakiyaye wannan yarinyar tayi min amfani .
ni wlh Dan  bani da iko  ne.
 tunda kince ta kwanta miki a rai .
wlh da tuni  korarta zanyi. Dan  Haka kawai nake jin tsanar yarinyar har cikin raina .


deeni dake kwance ya ja tsaki mai tsawo..Dan takaicin maganar Zeenat din  sannan ya Dan  juyo ya tsareta  da rikitattun idanunshi masu sata natsuwa a duk lokacin daya watsa mata su.

 take tayi shr ta hadiye maganar ta  ,sannan   yace I don't want to hear anything stupid here.
A Zafafe yacigaba magana haba kin cikamin kunne da shirme banzan ki .

 sannan ya dan sausauta murya tunowa da yayi ummi  natare dasu ,cikin sanyi jiki ya juyo suka hada Ido da  ummi . itama shi ta zubawa  idanunta kawai .
 Cikin sanyi ya kamo hannun ummi  cikin nasa  yana mai karkada mata kai  'ahankali yace am sorry...my first lov  .

take ummi taji wani irin sanyi a ranta  , gashi bata iya fushi da  tilon dan nata, Kuma bata son damuwarsa ,gara ace duk abinda zai same shi  ya tsaya  a kanta.

"  hannuta tasa ta dungure masa kai dashi " tace kai dai kacika maseefa wlh ai barewa batayi gudu ba danta yakasa rarrafe like father like son ai lokacin aliy ..... ganin ummi zata soma tabo labarin  dad dinsa yasa yakatseta da hanzari muryarsa  cike da shagwaba yace please first lov ya nuna mata yatsansa alamu tabashi 1 minti  sannan  ya juya inda zeenat ke zaune ta kasa kunne, kallo daya yayi mata wanda yasa ta gane abinda yake nufi tun kafin yayi magana ta Mike tsaye 'ahankali tabar gun.

 hade da cewa maseefafe banza  kawai akasan ranta in maseefarka  ta motso kowa yashiga uku acikin gida.

 sai da ya tabbatar da Zeenat tabar part din gabadaya sannan yace ok continue first lov  ummi  ta tabe bakinta sannan tace anki ayi continue din.
 dan saboda za'a yi maganar dad dinka  shine ka koranmu yarinya.

A shagwabe  yace haba first lov a gabanta zakirinka jistin din abinda dad dina yayi ya girgiza kai impossible.... Ai zaki sa ta raina ni .
Ummi Tasaki murmushi ganin yadda ya hade rai kmr mai shirin kai gumurzu sannun gyenbo sarkin son girma aiki DEENI ya yamutsa fuska jin abinda ummi tace murmushi tayi  nan dai suka cigaba da hira su ta tsakanin uwa da "da" .....


Koda nablah  ta koma dakin daaka sauketa ciki ,key tayiwa kofar saboda tsaro ,sannan  ta cire hijab din jikinta   ta tsaya tana bin jikinta da kallo yadda  take ajike  jagab da gumi tana tsiyaya  ,dariya ce  ta kufce mata, ai kuwa tashiga yiwa kanta dariya ,sosai tayi dariya har da rike ciki  saboda tuno yadda ta koma kallar tausayi dazu a parlour.
 ,a hankali  ta zare kayan jikinta dayake doguwar riga ce "ta daura zaninta data zo dashi tashiga bathroom..


Byn tayi  wanka hade da dauro alwala ta fito , duk wani abu da yazama na aladarta kafin tayi bacci  sai datayi , tare da yin addu'oi tsari ta shafe jikinta dashi ta nemi waje akan gado tayi kwanciyata cike da kewar iyayeta da yan'uwanta 'ahankali ta runtse idanunta tayi lamo akan gado wani tunanin ne  yazomata take taji gabanta yashiga faduwa. anya kuwa ... banyi kuskuren cewa bazan koma gida ba  kuwa?  duk da  lokacin dana fadi hakan ummamu  kin  amincewa tayi  da hakan.
  'ahankali" ta sauke naunauyen ajiyar zuciya a filli ta furta  kai bazai yiwa ba wlh na canza shawara gwara  narinka zuwa gida time to time ina ganin yangidamu .
 jin wannan shawara data bawa kanta ne  yasa taji wata natsuwa nasake bin jikinta ta  kudindine jikinta  waje daya a haka har barci mai nauyi yayi awon gaba da ni....


Can kuwa  bangaren  uwa da "da" ummi ce ke kokarin  mikewa tsaye  tace kai ni tashi kaje gun matarka Lada ya isa haka bacci nake ji  .
DEENI ya karyar da wuya yana duban agogon dake manne a bangon parlour sannan yace look at the Time first lov.  fast ten fa yanzu  muna hirarmu mai dadi  shine zaki koreni ko...  Cike da tsokanarsa ummi tace .. ni na isa na kor i farincikin rayuwata hasken duniyata hade ta karasa fadar haka tana kama bakinta.

DEENI  ya tabe baki kawai batare da yace komai.. ok baka yarda  Kaine duniya ta ba.. murmushi gafen baki yayi tare  da kashe mata idonsa   daya" ai na dade da sanin  wannan .
Kmr yadda  nima  kece duniya first lov ..... sannan suka  Mike atare yace muje naraki .
 har dakinta  yakaita ,ta juyo tana sake kallon dan nata Allah ya maka albarka yadda kakemin biyayya  kaima Ina rokon  Allah yabaka  masuyi maka fiyye da abinda kamin ina addu'a Allah yabani aron rai da lafiya naga jikokina wato yayanka....

  jikin deeni  na maseefa daukar  sanyi " a duk sanda mahaifiyarsa taimasa wannan  addu'ar yakan tsinci kansa cikin tashin hankali.
 ,da yanada yadda zaiyi yasamu yaran dazasu  yasamarwa mahaifiyarsa   farinciki da tuni an wuce wajen .
 batare da ya bari tayi nasa auren datake kokarin yi masa ba.

 yana son kullun yaganta cikin farinciki  fiyye da wanda take ciki  a yanzu tana  tagama fadar haka, ta juya masa baya dan bata san ganin damuwarsa.
 , cikin sarkewar murya tace  kaje abunka  ai burina  ya kusan cika "  Allah yatashe mu lfy da kyar  ya iya  amsawa da Ameen sannan, ahankali ya juya ya bar dakin direct dakinsa ya wuce   ya zauna  akan kujerar da yake zama idan zai yi aiki a system dinshi tare da sa hannushi duka ya dafe  goshinsa  dasu .

 yana matukar jajantawa kansa " hakika  Allah  yabashi komai tare da wadatashi da abubuwan more  rayuwar duniya sai dai yarage shi da abu daya Wanda yakasa daurewa wato zubar masa da ya'ya da Zeenat ta dinga yi arariya  .....




MMN SUDAIS CE
[7/12, 7:06 AM] 0mmer Farouk: 💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗





AYSHA A BAGUDO



Page 61



'Ahankali yasoma lumshe  rikitattun idanunshi Yana budesu sunnu Ahankali har ya rufesu luf... Sosai yayi zurfi cikin wata duniya ta daban .yayinda zuciyarsa  ke bugawa ,da sauri Wanda yarasa dalilin jin hakan. 
yana cikin wannan tunani ne bacci mai nauyi  yayi awon gaba dashi .


Sapanin bangaren Zeenat da" tunda ta kwanta akan makeken gadonta bacci ya kaurace daga idanunta" bbu abinda take tunani Sai mijinta.wanda tun tahowarta da tunaninsa take bacci take tashi 
" taso a daidai wannan lokacin tana tare dashi rungume  a saman fadadden kirjinsa mai cike da yalwan gashi  amman kashiii... ..
son zuciyarta da km kaddara data gitto  tasanyata zama cikin kadaici da kewar  mijinta.

'Ahankali tasa hannu    ta rarumo pillow dake kusa daita "ta  rungume tsam akirjinta,tare da fatan samun saukin abinda take ji ,a tunaninta ko hakan datayi  zai ragewa zuciyarta damuwa akan rashin mijinta kusa daita. amman sam hakan yaki samuwa gareta.
 ' domin pillow kadai bazai taba .  maye mata gurbin dumin  jikin mijinta datayi missing ba.

Dan  yarigada yayiwa jikinta  "mugun sabo da zazzafar soyayyarsa mai cike dadi da kashe tsansar  jiki.

Uhm DEENI kennan daban yake   acikin maza Haka ma soyayyarsa .
 ganin bacci ya kauracewa idanunta ne yasa, ta Mike da kyar tashiga bathroom ta dauro alwala, nafilar dare ta fara 'da zumar samun sausauci a gurin ubgj  tare da rokon Allah Ya sake mallaka mata mijinta a tafin hannuta. ,

 

Hankalisa kwance yake shakar baccinsa tamkar Yana sama jannati.
Kyakkyawar budurwar ce take kusantoshi har inda yake kwance flat akan bed dinshi tare da sa hannuta,ta shafo kyakkyawar fuskarsa mai cike da suma da annuri.

 'ahankali yasoma  bude Idanunshi tare sauke kwaryar idanushi acikin nata , tsaye take kyam . tana sakar masa kayataccen murmushin daya bayyana wushiryarta.
  'ahankali ta Miko masa zarara yatsun hannuta masu matukar kyau da daukar hankali. tamkar  jira yake ya damki hannunta tare da fizgota saman daddaden kirjinsa mai cike da yalwar gashi ya rungumeta tsam tsam ajikinsa yana sakin numfashi shima Ahankali yakai bakinsa tsaitin wuyanta  Yana shinshina kamshin jikinta  .

cikin wani irin salo yasoma cire mata kayan jikinta, bata hanashi ba har yagama cire mata kayan jikinta tsab .
  " ta saura daga ita sai pent da bra Shima 'ahankali ya zaresu yayi flinging dasu gefe  , breast dinta   masu matukar kyau "da daukar hankali suka bayyana sai sheki suke tsabar baiwar da Allah yayi musu .
tamkar wani mayyunwacin zaki   a gigice yasa hannuwansa duka ya damki  dukiyar fulaninta yasoma murzawa Ahankali Yana lumlumshe idanu, itama  kmr Jira take ta dinga narke  masa ajiki tana cire masa kayan jikinsa, habawa Ai  gabadaya deeni ya susuce ya fara romancing dinta cikin zafi zafi tare da hade bakinsu waje daya Yana tsotsa tamkar yasamu loly pop 

Cike da shauki ya birkito daita takoma kasa tare da zare mata  pent din dayayi saura ajikinta , sannan   yahaye saman   ruwan cikinta " yasoma kokarin ware kafafuwanta kana ya   tsaita kan joystick dinsa cikin kofarta, Ahankali cikin wani irin salo   ya zira jijiyarsa ciki.

 hankali kwance yasoma saduwa  daita Yana cikin kokarin yin  realize ne sautin . allahu Akbar lahu akbar .... kiran sallah da'ake kwallarawa daga masallaci dake cikin estate din ne ya farkawa dashi  a , afrigice ya farka tare da wata mummunar faduwar gaba ya Mike zaune  hannushi dafe da kirjinsa Yana waige waige acikin dakinsa.

Numfashi sama sama kawai ya dinga saki " Tare da kallon ilahirin  jikinsa dake kirma... duk abinda ya farkar dashi daga baccinsa bai bashi mamaki ba facce  ganin  jijiyarsa' da yayi a mike sambal... da km  yadda take harbawa da sauri yasa hankalinsa mugun  tashi.
  Gabadaya gangar jikinsa rawa yake zuciyarsa ce ke harbawar da sauri ,take ya   Daura  hannuwanshi duka  kan joystick dinsa ya dafe  .
 wani irin azababen  shock yaji ajikinsa Wanda yasa jikinsa sake cigaba da kirma...
 . 
  , 'ahankali ya dinga furta kalmar inna lillahi wa inna lillahi rajiun   akasan ranshi, ya jima zaune  yana maimaitawa  sannan ya samu sauki da natsuwa zuciya iya tunaninsa Bai san meyasa yin irin wannan mafarkin ba" haka nan km Bai kwanta da Sha,awar wata diya macce  a ranshi  ba ,hasali ma zuciyarsa cunkushe take da abubuwa da yawa kafin ya kwanta ,Sai dai ko daga Allah ne .
   Mike yayi Ahankali  yashige bathroom domin tsarkake kansa.

Byn yayi wanka tsarki ne  ya fito  tare da  dauro alwala yazo ya gabatar da raka'a taini fajir sannan ya wuce masjid .

 koda ya idar da sallah ma ya dade zaune Yana jimami da  mamakin mafarkin da yayi har ya dawo gida ,ya kwanta rigingine akan royal bed dinshi Bai daina jin sa some how ba .


8:00 


Daidai   Ya tashi .
duk ilahirin jikinsa  a sanyaye yashiga bathroom "wanka yayi ya fito yasoma shirin zuwa aiki .
 Yana   gama shirinsa tsam cikin uniform din su na soldier .
,  ya nufi  part din first lov  domin   yaga yadda ta tashi dan ka,ida ne muddin  gari ya waye sai yasanya mahaifiyasa a idanunshi sannan yake fita .


 da sallmar sa yashiga dakin  zaune  yasameta akan gado, tana ganinsa ta fadada fuskarta da murmushi "  tasoma masa kirari kmr yadda tasaba"  kaga namijin uban mazaje namijin  duniya yaro in bakayi bani guri" sannu zaki maza,km   jarumina    matashi magidanci son kowa kin wanda yarasa.

 "da" daya tilo " da" daya  .
 kafi Yaya dubu agurina ,sadauki ranka yadade ta dunkuleta hannuta tare da  jinjina masa  "

DEENI ya karkace  kai kawai yana kallon mahaifiyasa "yana sake jin yadda soyayyarta ke sake  ratsa kowani part na  jikinsa.

 duk duniya bashi  da sama daita. itace duniyarsa  ,shiyake daita ,ita take da shi cikin takunsa na kasaita  yakaraso har  inda take   ya zauna kusa daita yana murmushin ,duk  wannan kiraki nawa ne   ni kadai first lov sannan yace  mun tashi lafiya .

,tana murmushi tace lafiya lau  dana , yakata shi kaima ?

,ya shagwabe  fuska  kmr wani karamin yaro yace lafiya Amman ba lau ba .

 Ummi ta zaro idanu  tunaninta ko wani abu ne yana shi yin bacci .
  ,meyasa Meka ya kai dana ummi ta fadi hakan tana mai nazarinsa " Ahankali ya shagwabe fuska byn tunaninki ne ya saka gaba ya hanani yin  bacci   ummi ta sake  zaro idanu tare da sakin  murmushi  irin na manya.

Aiko  " tunanina    bai kyauta min ba wlh . 
  " Har daya hanawa tilon dana samun natsuwa" 

Deeni  yasake narke fuska yana duban umminsa , Allah first lov ki nemo shi  tunanin ki hukunta shi da kanki .

ta sake yin murmushi kusan koda yaushe agaban mahaifiyasa haka yake zama  tamkar wani jinjiri   , ummi numfasa sannanAuntyna tace  maza tashi kaje  nasan yanzu haka ko breakfast bakiyi  ba  kike shirin fita ?
 
A sukwane ya Mike tsaye yana duban ummi .
 "mkr kinsani wlh  amman  daga  wajen yin break zan wuce office , ganin yana tsaye bashi da alamun tafiya  ne  yasa tasan abinda yake  Jira ,dan haka  tashiga yimasa addu'a tare da sake nuna masa mahimmanci Zeenat a gurinsa .
 sannan  ya fice daga dakin  hade yi  mata sallama  ..


Koda ya bar part din first lov part din zeenat yashiga kwance ya tadda ita Tayi zurfi cikin duniyar tunani sannan    idanunta na kallon celling dakin da dukkannin alamun ma bata samu runtsawa ba .


 'Ahankali Yasa hannunshi  ya ja yatsun kafarta dashi ' a sanyaye ta kallosa  da idanunta tana may sauke  naunauyen ajiye zuciya sannan ta zuba masa kwayar idanunta cikin nasa hk  shima yake  kallon tare da   dan matsowa kusa da ita sosai  yana son  sake karantar yanayin  da take ciki .

 haka kawai wani lokacin  yake tsintar kanshi da tausayawa mata   ,sbd yadda take maseefar sonshi da kishinsa.

 daidai kunneta yakai bakinsa,  kana yayi kasa kasa da muryarsa yace  meke  damunki haka Zeenat .......? 'Ahankali ta girgiza masa kanta ,alamun bbu komai, ya furzar da iska mai zafi daga bakinsa .
saannan yace ok..to   meyya hanaki bacci?

 Ahankali ta  juyo ta zuba masa kananun idanunta tana kallonsa dasu sosai take jin yadda  kaunarsa ke sake  taso mata tamkar zata huda mata zuciya , tare da mamaye mata dukkan sansanr jiki .
 Sai data kalleshi son ranta sannan ta sauke numfashi 'ahankali muryata a shagwaba tace kai ne da tunaninka ya hanani runtsawa.

 ya runtse Idanunshi sannan Ya bude su  Dan sake dubanta  suka hada Ido dashi  ta lumshe masa  idanunta  tana sake tabbatar masa da iya gskyrta ta fada .

yes ....  tunaninka ke damuwana yayinda kewarka ke  hanani ke hanani sukuni ballanantana na samu sararin ishashen bacci .

, ajiye zuciya ya sauke tare da  zama  gefen bed side dinta ,yakamo tafin hannuta cikinsa yana murzawa ahankali 'ahankali .
  tsareta yayi  da rikitattun idanunshi yana kallon cikin kwayar idanunta .
  ' itama shi take kallo still  take ta dinga  jin wani iri iri ajikinta  . gabadaya tsigar jikinta suka Mike tsaye   yrrrrrrrrrrrrr......

   Bazato ba tsammani taji sautin muryarsa  meyasa kike son halaka kanki da tunani na Zeenat ?  

cike da damuwa yake magana , alhalin duk maseefar da tasameki kece silar jefa kanki  ciki.

kau da kanta tayi gefe window   ta  zubawa wajen idanu kuri batare da tasan abinda yakama tace ba .
  " ganin da yayi hawaye ne keson zubo mata ,  yasa hannusa Yana juyo da fuskarta garesa  suna sake fuskarta juna.

 yace karki soma barin hawayen nan  su zubo daga idanunki sbd bana bukatar ganinsu km basu na tmyeki ba  .
 D karfin tsiya ta ciza lip's dinta   tasoma kokarin mai da kukanta.

   inason  kin manta komai dangane da abinda ya faru baya kicanza new life  banason ganinki cikin wannan moon din "ko kinason  first lov  ta fuskanci wani abu na damunki   byn damuwar rashin  haihuwa da tasan itace  matsalar mu ,  ta girgiza kai   yace kiyi fatan samun wasu  ya'ya masu albarka  .
 maganar dayayi mata kadai Ya taba tsantsar jikinta tare kwantar mata da  hankali.
Hannuwata dake cikin nashi  tasa ta matse tafin hannushi cikin tare da danne hawayenta , muryata a sarke tace Ina sonka dayawa  my heart..... ,meyasa kaima bazaka  soni tamkar yadda nake maka ba Ina son kasancewa tare da kai bana son yin nisa daika . 

Uhmmmm  Zeenat kennan Ina sonki man abinda kika aikata gareni ne yasa soyayyarki takasa yin tasiri a zuciyarta  sannan kece kika hana wannan soyayya samu gurbi may mahimmanci,Amman dai... Sai km yayi shr  tare da   mikar da ita  tsaye   ya   mannata da gafen jikinsa yana shafa bayanta 'ahankali ,  .
  dan yasan   duk randa basu kwana tare ba "bata samun  ishashin bacci ga tarin  tunanin rashin  haihuwa da take kwana yi wanda   duk ita  tajefa kanta cikin .


 Ahankali Ya juyo daita suna facing juna  tare dadago habarta   ya zubawa  fuskarta eyes dinshi sannan  ya kai bakinsa kan nata ya tsotsan lip's dinta yace I still care about you.

  murmushin tasakar masa  Wanda ta jima batayi irinsa ba ,cikin jin dadi ta kamo tafin hannushi  muje kayi breakfast  .

 am orready late Zeenat anajirana a office nebazan iya tsayawa cikin komai ba . uhmmmm nidai  please muje kaban ko 5 minutes na hada maka  ko  tea ne kaji.
 ya karyar da kai kawai yana dubanta , atare suka jiro hannunsu sarkafe da juna har darning wanda daman komai  a kammale yake  ta zaunar da shi cikin sauri sauri ta hada mishi tea kurba uku yayi ya Mike tsaye , tasan yanzu tana sake yin wani complain .
sunanta sorry  a gurinsa Dan wannan kulawar  dataga daga gareshi tasan darajar addu'ar data kwana tana yi ne da km ummi dake tsaye a tsakaninsu har Bakin  kofar main falon din su takai shi ta Mika masa briefcase dinsa Dan bayarda da hakan sannan ta koma dakinta  ...

Direban sa wanda shima soldier ne yataso da sauri yakarbi briefcase din hannunsa hade da Sara masa sannan  ya bude masa murfin  kofar.
 ,tun kafin karosowarsa  Bakin get din gidan securities ke Sara masa har aka bude get suka bar gidan ..  

Tunda ta tashi tayi sallar asuba take kwance takasa fita ko nan dacan   tana jiran kira  daga masu gidan Amman shr ga yuwa tasoma kmr me .
  Mikewa tayi jiki a sabule tashiga bayi wanka  tazo ta canza kaya tare da  zubawa sarautar Allah Ido can taji ana nouking dakin ahankali ta Mike  ta bude kofar ummi tagani tsaye ta dan  matsa taba hanya   tashigo dakin  sannan ta  gasheta cikin sakin fuska ummi  ta amsa tace nablah ya kwanan bakunta ?

Ta Dan yi murmushi tare da cewa  alhmd  ummi tace Masha Allah yanzu dai muje kiyi breakfast daga nan sai mamana ta nuna miki aikin da zaki rinkayi ummi  nagama fadar haka ta juya itama nablah tabi bayanta ...

Falo uku  sama uku kasa uku banda dakuna wanda sunkusan goma acikin gidan , madam kmr yadda taji laraba  nakiranta da shi ita ke nuna mata  komai.

A yatsine  tace ki dauki gyaran sama kibarwa laraba  kasa  nablah tace mata  to dan batada zabi sai abinda tace ..
 har falon magidan da dakin sa komai dai ataikaice sai da aka nunamata  Kuma tun a rana tasoma aikita hade da tattaro kayanta tadawo sama  kmr yadda ummi  tabata umarni .

Misalin karfe takwas dai dai na dare nablah ta kammala da komai na aikin gidan  har part din abinci wanda tare da madam muzeenat sukayi komai wai  tana son ta kware fannin abinci mai gida dan haka gabadaya  agajiye take  likis.

Tana shiga dakinta  kwanciya  tayi  bata dade ba bacci yayi gaba daita.



MMN SUDAIS CE
[7/12, 7:07 AM] 0mmer Farouk: 💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
     💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO


Page 62



" kyakkyawar yarinyar ce dai  ta sake zuwan masa. deeni kuwa dake kwance warwars akan makeken royal bed dinshi ya zuba mata Idanunshi kawai , tundaga kan  kwantaccen sumar gashinta kanta yake binta da wani irin mayataccen kallo  mai cike da tsantsar sha,awa yayinda zuciyarsa ke  wani irin harbawa da sauri da sauri ..ganin yarinyar ta miko masa zara zaran yatsun hannuta masu matukar kyau da daukar hankali ne yasa shi azamar fizgota jikinsa batare da wani bata lokaci ba ya rungumeta tsam tsam ajikinsa tare da   cusa kanshi cikin sumar kanta yana shakar dadeden  kamshin jikinta "take  yarinyar itama ta narke masa ajiki   tana taba wasu part na jikinsa cikin wani irin salo   a haukace tamkar wani zaki DEENI  yasoma romancing din every part of her  "cikin zafi zafi ya hade bakinsu waje daya  yasoma tsotsa tare da lumshe rikitattun idanu..  ........ sosai yake juya yarinyar  yadda ya so batare da  wani abu yamasa shamaki  ba.
 daidai komai yagama faruwa atsakaninsu ne ya farka  afrigice zaune   kmr jiya yana sauke numfashi sama sama..
    tare  da karanto addu'ar da duk tazo bakinsa na neman tsari daga sharin shedan ,ganinsa mafarkinsa nasaba da sharin shedan dan gabadaya yarasa dalilin dayasa yatsinci kanshi cikin irin wannan yanayin mai cike daban  tsoro da alajabi .. hakika shi  bazai ce Ga abinda  ke damunsa acikin yan kwanakin nan dayasa yake tsintar kanshi cikin irin wannan birkitaccen yanayin ba .

 Tsawon lokaci ya dauka yana zaune Yayi shr kawai  yana tunani.
  " yayi yayi  ya gane abinda ke damun rayuwarsa  Amman Sam yakasa domin   duk ta inda ya duba bai gano  takamaiman abinda yasa yake irin wannan mafarkin ba ..... 'ahankali yasa hannushi  yajanwo  hanky  agefen bed dinsa ya goge gumin daya rufeshi . dan duk da  AC dake aiki acikin dakin bai hana Gumi  tsatsafo masa ta koina ajikinsa ba ..  .. sannu ahankali yakai idanunshi kan agogon bangon dake manne a dakin.
 karfe biyu yagani daidai ajiyar zuciya ya sauke tare da koma  yayi   kwanta lamo.... yana juyi kawai batare yasan abin yi ba dan kwata kwata idanunshi ya kyan kyashe bbu alamun  bacci acikinsu   tunani kawai yake yana juyi. ...


Washegari 

da safe byn ta idar  sallar asuba  bata  koma bacci  ba saboda tasan yanayinta domin tana  komawa bacci me nauyi ne zai dauke ta.
  " kowa Kuma yasan yadda baccin safe yake    dan haka    kishigida kawai Tayi  kan pray mate .



 karfe bakwai daidai ta fito daga dakin da'aka sauke ciki. shr koina babu  motsen kowa ballanantana mutun ya saka ran ko akwai wani  bil,adama acikin gidan kasancewar week end ce.


 tafiya take 'ahankali  cikin tsanyi  jiki , har ta iso part din ummi takutsa kai  ta shiga da sallmarta ...

nan ma shr  ba motsin  kowa ciki "can taji   " alamun  motsen ruwa a bathroom  dan Haka tabbatar da ummi tana.

" bata wani  tsaya batawa kanta  lokaci ba ta soma yin abinda yakaita,  daidai  nablah tagama gyara koina  ummi tafito daga bathroom..

 tana ganin nablah ta saki fuskarta sosai tare da yin  murmushi  . nablah   ta gaishe da ummi  cike da girmamawa .

Ummi ta amsa tana mai Bin nablah din  da wani irin kallo mai hade da mutuntaka .

 Jikinta  nablah a sanyaye takarasa toilet din ummi  tawanke koina tasss  ... sai da tabbatar data gyara duk inda aka nunamata tasss ..

Amman banda part din mai gida Dan  so take sai ta gama da koina acikin  gidan sannan tashiga  part dinsa   saboda tsaro ..

Tsaye take a bakin kofar  da zata shigar daita cikin part din mai gida.. hannuta rike da  handle din kofar  .
  "takasa murdawa tashiga a dalilin  zuciyarta da tasoma  wani irin harbawa da sauri .
 ta dinga jin wani  irin ajikinta wani  irin yanayi ne na daban ta tsinci kanta ciki  .
,yayinda   wani part na zuciyarta ke bata umarni tashiga kawai batare da wani tsoro ko fargaban ba , a tunaninta   may be ma yafita  ,duk  dai tasan  week end ce bai zama lallai yazanmato yana ciki ba.
 Amman kwata kwata fargaba datake ciki  ta hanata yunkurin kusawa cikin dakin ..
,sai da ta runtse idanunta tare da tattaro  jaruntar ta sanyawa gangar jikinta ,  sannan ta iya murda handle din a natse  tashiga dakin ,da idanun take bin  dakin da kallo Sha,awa.
    koina tsab tsab  tamkar an gyara   bbu wata alamun da zai nuna mutun na rayuwa a cikin dakin , ahankali ta kamo  gefen  lip's din  bakinta ta Dan ciza   kadan kana   ta soma abinda ya kaita  .

   Daki daya ya rage a cikin part din  da bata gyara ba Dan haka  ta kutsa  ciki ta soma da wanke  toilet ta zo kan royar bed dinshi, ahankali tasa hannuta kan  blanket  din dake rufe da gado  da niyyar cirewa ta  nike  Dan kwata kwata batayi tunanin zata samu bil ,adama  kwance cikinsa ba"  a tsorace Tayi  sauri sakin blanket din 
  ' tana zare idanu waje tare da furta  wayyo Allah nah a kasan ranta , take  jikinta ya dauki kirma ta gigice tama rasa hanyar fita dan neman tsira    daga cikin  dakin.

  tsabar  rikecewa batasan sanda ta kama  handle din  kofar bathroom ba ta afka ciki ... Ai ko  tana ganin ba kofar fita bace ta sake  juyo da   sauri ,bbu inda baya rawa ajikinta  tare da tattara kayan moupystick dinta   tabar dakin  da saurin bala'i tana haki sama sama tare  da fidda  numfashi .

A can bakin corridor din dake  tsakanin part din deeni da ummi taja ta tsaya ta sake  fidda numfashi  tare da   addu'ar Allah yasota.. ..

shi kuwa deeni dake kwance ya sake lumshe rikitattun idanunshi  kawai dan  tun  shigowarta dakin idanunshi ke bude ganin itace yasa shi  sake lafewa jikin pillow , dan shi ko yaya akayi motse zai farka.
 yadda yaga ta gigice ne  ya fi tsaya masa arai .
Dan Haka a tsanake ya tmbyi kansa  to me hakan yake nufi da wannan gigicewar dayaga tayi ?

 tabe bakinsa yayi tare da jan tsaki sannan  yacigaba da  baccinsa .

Sai  kusan azahar sannan yatashi  ,yashiga bathroom yayi wanka hade da alwala yana fitowa ya goge jikinsa ya shafa lotion  ya zira jallabiya   long  sleeve tare da fashe  ilahirin jikinsa da turaruka masu mugun kamshi da daukar hankali....
   ahankali yake saukowa daga step hannushi rike da gefen jallabiyarsa   har ya iso babban falon gidan inda ya tarar da duk ahalin  gidan zaune  .

 ya gaida ummi  yayinda zeenat ta gaidashi .

 nablah da tun 
 saukowarsa taji tana kiciniya da numfashinta  dake namen barin gangar jikinta ta gaisheshi  muryarta aciki.

Yana jinta Yayi banza daita tamkar   bai jita ba  Sai ma hankalinsa daya dauka kacokan yamayar kan ummi dake  kallo, muryarsa a dake yace  first lov ni zani masallaci ta juyo tana dubansa  tare da ce wa  To sai kadawo yarona , sa kai ya fice .

  takasan   idannu  take kallon  every step of him  dab ..dab... kmr wani jinin sarauta yayinda  duk takunsa daya ke  daidai  da bugun zuciyarta har ya bace wa ganinta idanunta nakansa km Sai lokacin  tasamu  natsuwar zuciyarta,  dan gabadaya ilahirin jikinta bbu inda bayi sake  ba .

 Muryata Ummi ce  tasa ta sake dawowa cikin natsuwarta . nablah ki dawo   kan kujera man  ki zauna kin wani je can kin rakube akasa... maza taso  kidawo nan  kusa dani kinji "ki saki jikinki damu  nan ma tamkar gida ne , a sanyaye nablah ta Mike tayi kmr yadda  ummi ta umarceta  .

Ummi tacigaba da magana . kishirya zuwa anjima akwai doctor  da zata zo ta miki test kinji  nablah  cikin sanyin muryarta tace to.....

Ummi   tasa hannu ta dauki remut tana canza channel zuwa zeeword  .

,  zeenat ta dan juyo a wulakance tana kallon inda nablah ke zaune tare da  watsa mata wata uwar  harara ..   bakinta ta tabe kawai cigaba da aikawa nablah da harara iri batare da tabari ummi taganta ba   ita dai  haka kawai take jin tsanar yarinyar har cikin ranta .

  hirar ball ummi da Zeenat keyi jifa jifa har suka gangaro kan hirar duniya   ummi ce  ke kokarin  saka nablah ciki hirartasu " yayinda   ita km nablah Ido ne  kawai  nata ko  murmushi Dan kwata kwata ita batasan ma  me zata dasu  ba' dan Haka tacigaba da sauraronsu  har zuwa  sanda mai gidan ya  dawo daga masjid  tare da wata mata suka shigo ..
byn sunyi shafta da wasa da dariya tare da mdm zeenat wanda  hakan ya nuna  alamun sun saba da junansu  sosai ba tun yau ba ..
 " ummi ta  umarce doctor din data shiga da nablah ,hakan ce takasance domin   bata tsaya wani  tmbyr ummi  ba Dan tasan abinda zatayi .

abinda yabawa nablah  mamaki bai wuce ganin  komai  na aikin likitoci dake cikin dakin ba.
  bbu abinda bbu  har gadon kwanciyar marasa lafiya akwai shi a dakin.

, Doctor din ta umarce nablah  data zauna" ta zaro sirinji acikin hand bag dinta .
 ta zuki jininta wanda hakan bai sa hankalin nablah  tashi ko daya ba saboda daman hakan  yana daga  cikin budget dinta.


 byn doctor din   ta dibi  jininta  tashiga wani daki still dai acikin dakin da suke ciki  tare da bawa nablah umarnin    Wuce wa.

 Ta Mike jikinta  bbu kwari Sai dai bbu  wata alamun damuwa ko fargaba atattare daita .

 direct hanyar step  tabi " ta nufi dakinta" koda tashiga dakin ma rasa abinyi tayi domin   kewar yan gidasu ne tattare da zuciyarta" tana ji  kmr taje tasamu  ummi  ta roketa takirawo mata number  auntyta  su gaisa .

 tunawa datayi Killa ma yanzu haka ummi na can tare da mutun da ko kafafunsa ta kalla zuciyata tamkar zata tarwatse  takeji"  yasa ta share kawai  taki koma gurin ummi ..



Sannu ahankali Yau kusan  kwanakin  nablah  goma  kennan a gidan Amman bbu Wanda yayi mata bayanin komai   dangane da jininta da a gwada.
duk da hakan  bawai ya dameta bane  illa rashin jin muryar   daya daga cikin ah'linta  ,tunanin hakan ne yasata .

 Mikewa  tsaye cikin hanzari  da niyar zuwa tasamu ummi ta taimaka ta kiramata  auntyta .

bude kofarta ke da wuya taga mutun tsaye  abakin kofarsa  yana kokarin yiwa kofar dakinsa da key .

 Da sauri ta  risinawa tana  gaishe shi  shiru yaki  amsawa   km bai da alamun zai  amsa din     sai ma dauke kansa dayayi yacigaba da abinda yake .

Jikinta yayi maseefar yin  sanyi da abinda deeni yayi mata.
Dan haka  'ahankali ta dinga daga kafafunta  yayinda   Rainta yake a dagule tana jin wani irin ciwo mai radadi   , duk da kasancewarta  mai  matukar  hakuri da rashin sauri fushi akan abu. Amman abinda mai gidan yayi ya taba   ranta  .
 domin  a rayuwarta idan akwai abinda ta tsana da Gani bai wuce tsagwaron   raini hankali  da cin fuska tare da  isgilanci ba dan zata iya dauka komai Banda su  .

ahankali   ta dinga    daga kafafunta dasuka gama sagewa ta nufi hanyar da zata sadata da ummi . dan  gurinta kadai take samun sausauci acikin gidan. 

 A tsanake yabita da Idanunshi     tare da rike kungunsa  da hannu daya yana bin bayata da wani irin matsiyacin  kallo.
  yayinda zuciyarsa ke  harbawa ko kifta idanunsa  bai da alamun yi " so yake ya tabbatarwa idanunsa abinda yake Gani a cikin  mafarkinsa ,  hajabi dake sanye ajikinta    bai hanashi yimata kallon kurulla ba "  gabadaya idanunshi sun rufe ya shagaltu da kallon Surar jikinta a bayyane ...  domin  ganinta yake murarta ba tare da wani hijabi ba   .

  Jin yadda idanunshi ke yawo a tsantsar jikinta ne " yasa  Kirjinta ke wani irin  harbawa da sauri tamkar wacce ake bugawa guduma a kahon zuwa .

Yanayin sanyita da tafiyarta yasake shagaltar dashi ba dan deeni  yagaji da kallonta ba ,ya dauke idanunsa akan ba Sai Dan gudun juyowarta cikin sautsayi.

 What lokaci tana kan step Dan ko rabi batayi ba dan kallon da kafe dashi ne ya sayayar mata jiki tare da rage mata kuzarin jikinta .. ahankali  km tasoma jin  kmr takun mutun   abaya daidai ta kai rabin step din cak.... taja ta tsaya tare da rabe jikinta gefe daya .
 alamun tana son bawa duk wani mai son wuce dama ,duk da oready jikinta yabata alamun mutumin data baro tsaye ke saukowa  sakamakon kamshin turarensa mai tada hankali da ta keji  ...

 shr kusan two minutes sannan  yazo ya wuce ta gefenta zuciyarsa na tacigaba da harbawa .duk da Bai    bari jikinsu ya tabu da juna .

 Tana nan  tsaye har yazo ya wuceta tare da    bude wata kofa ya  shiga   dan kusan  har yanzu bata gama sanin kan dakun nan gidan ba.


 ,inda tasan zata samu  ummi kai tsaye  ta nufa zaune suke ita da Zeenat kmr  koda yaushe suna kallo TV suna hira abunsu hankali kwance. Yayinda  kayan fruit ke gabansu da sallmarta takarasa inda suke  sannan tasamu guri kan Tia's ta zauna tana wasa da  Zara zaran yatsun hannuwanta.  ummi ta juyo ahankali  tana  duban nablah  byn ta amsa sallamarta  kallonta kawai take Tare  da nazarinta   .

 yayinda zeenat tunda ta juyo ta mata  kallo daya ta dauke kanta tare da  mai hankalinta kan film da,akeyi .

Sai da ummi tagama nazarinta tsab sannan ta takira sunan nablah ..

Nablah  ya'akayi ne ?
Nablah tayi kasa da kanta tana cigaba da yamutsa yatsun hannuta  a atsorace  muryarta cike da sanyi  da in...inna.. tace dan... Allah daman  ina..Ina. son nayi magana ne  da auntyna ta fadi hakan idanunta suna masu  cikowa  da hawaye. domin daukarta ko baza su kiramata auntyta bane shiyasa duk takoma wani iri   .

  Ummi  tayi murmushi kawai Tare da sake zubawa nablah ido   ganin yadda duk  ta dawo kalar tausayi ..
 ummi ta girgiza kanta sannan tace  yanzu akan   zakiyi magana da auntynki  ne duk kika dawo haka tamkar zakiyi  da kuka?
   .. gsky  nablah akwai shagwaba atare dake tasa ummi takarasa fadar haka Tare da Mika  hannu ta janyo  wayarta dake gefe tasoma   dealing number Salmah ta Miko mata  wayar tare da nunawa nablah wani daki da hannuta . Kishi Ga nan kiyi wayarki kinji diyarta .. haushi da takaici ne gabadaya suka gama turnuke zuciyar Zeenat dake zaune gurin  tamkar ta tashi ta shake wuyar nablah ta dinga a zuciyarta , tarasa yadda zatayi ne kawai yasa ta dinga  ja tsaki tana aiyana yadda zatayi da yarinyar..


wayar manne da kunnenta  har tashiga dakin  da ummi ta nuna mata ,daidai nan  murya aunty Salmah  ta doki dodon kunneta tun kafin nablah tayi magana aunty Salmah tace assalamu alaikum hjy anyi lafiya .
 murya  nablah cike da doki da  shagwaba aunty  ba hjy ba ce nablah ce .

Aunty Salmah tayi murmushi A'a nablah.. yana ji muryarki haka kmr kina cikin damuwa ?
Sai da nablah ta sauke ajiyar zuciya sannan tace bazaki jini cikin damuwa ba  , byn kewarku ta dameni duk sai aunty Salmah gigice.
 tace ko dai akwai da  matsala ne a gidan?
" nablah tace  uhmmmm fa ba matsalar komai.. in ma akwai matsalar nan bai wuce   kewarku ba .

 Nablah tacigaba aunty  baki bawa mama number wayar hjyr bane kmr   yadda  kika ce gsky    zuwa yanzu na matsu da son jin muryarta,  km  kmr naganni agabanta haka nake ji ,aunty Salmah tace Eh ban bata number ba  nafison zuwa nan da sati biyu tukun nasan zuwa wannan lokacin kingama  da sanin halin mutane gidan , ni dai abinda nake so dake ki zauna lfy da kowa Amman da kinga akwai  matsi    da  takura  just give me a cul" furrrrr zaki ga aunty ki kmr flay.

 nablah   ta saki  sanyayyayiyar murmurshin dayasa  dimple dinta  lotsawa sosai wanda hakan ke   sake fito da ainihin bawar kyawun da Allah yayi mata .

Ahankali "  tace Allah aunty bbu matsalar komai  fa aunty Salmah tace to.to. shikenan ,ki kama kanki da kyau km  ki dinga saka hijab dinki  duk inda zaki shiga a gidan .

Nablah tace har baccima dashi nake aunty Salmah Tayi  yauwa Yar gari nablah na  murmushi tasake bude baki da niyar tambayar auntyta  dip ...maganar ta tsaya ...... Tana zaro Idanu waje sakamakon hasken dataga ya  gwaraye  dakin gabadaya  duk daman can akwai  wuta a dakin  dan koda tashigo fan na aiki ..

 kwance yake akan kujera  idanunshi a lumshe yana kallonta kmr ranar farko daya soma ganinta  a rayuwasa .

 murya aunty Salmah  taji tana cigaba da cewa lfy  na jiki   shr  kin dauke wuta kmr NEPA.

A daburce tasoma in in na , A'a.......uhmmmm ba komai to yanaga duk  kin rikece kigayamin in wani abu  nablah tace Allah  bbu komai aunty to   kigaida hjy zan Kuma bawa mama number hjy  zuwa jibi inshallahu ki kwantar da hankaliki zata kiraki, itama ta matsu taji muryar autata ,da kyar nablah dake kokuwa da numfashinta ta iya bude baki  tace to aunty  sannan ta kashe  wayar Tare da  sauke wayar daga  kunnena.
har lokacin bai dauke idanunshi akanta ba wanda shi kansa basan ma Yana kallon nata ba . 

  Itama shanyayun idanunta ta zuba masa kawai  tana kallon  kwakkywar  fuskarsa dam ...taji kirjinta da zuciyarta sun amsa a lokaci  daya take ta soma jin  tsoron yanayin  irin kallon dayake mata.

 ,jikinta kuwa  Banda kirma bbu abinda yake ,takoina  gumi ya dinga   tsatsafo mata  ajikinta   Jira kawai take taji yace arrrrrrr ta arce da gudun maseefa Amman Sai kawai taga sabanin haka, domin  ko motsa bakinsa bai da alamun yi  ballanantana akai gasamun fitowar  kalma daya daga bakinsa Sai ma taga   tabe bakinsa  tare da dauke idanunshi akanta .


aransa kuwa cewa yayi munafuka kawai Tayi wani shr   kmr ba yanzu tagama   wage baki tana waya  ba..😍😍😍
Ni dai  nace uhmmmm  deeni Banda  kin fad ar gaskiya...nooooo


 komawa yayi sosai yayi  kwanciyarsa normal ganin datayi ya  kina ya kwanta ne  yasa tayi saurin juyawa da jikinta na rawa ta bar dakin har hijab dinta na neman hardeta  kafafuwanta .

" afrigece   ta dawo parlour  inda ta bar su ummi .
Ummi kadai tagani zaune  Banda  mdm muzeenat ko Ina tashiga oho ita dai tunda tasamu    ta mikawa ummi  wayarta ta bawa karfa iska  .

tayi shr sannan komai ta tuna ta dagamin kai ...

Koda tashiga dakin ma  bayi tashiga dan jin yadda   cikinta ke murdawa  ,tun sanda take tsaye gaban horo  dan sunnan data bashi kennan take jin yadda cikinta ya cure guri daya  .

toilet tayi sosai byn tagama tashiga cikin bathtub ta kunnawa kainta" shawa  ta dade kwance  tana jin dadin yadda ruwan ke rasa kowani part na  jikinta .

 sai data  soma jin kiran sallar ne a masallaci dake cikin gidan sannan  tayi alwala ta fito jikinta daure da towel zigidir tayi gaban mirrow tana goge sauran wuraren dake da ruwa ajikinta yayansa take bin koina ajikinta da kallon, yadda yanayinta  ya  canza gabadaya  'ahankali tayi murmushi tana sake kallon kanta  doguwar rigar mai dagon hannu ta zirawa jikinta tare da zira hijab dinta  ta tada ikama...




MMN SUDAIS CE
[7/12, 7:08 AM] 0mmer Farouk: 💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA .A .BAGUDO



Page 63



Byn ta idar da sallah ne ta Mike 'ahankali  jikinta a tsanyaye    takarasa  jikin window dakinta .
" ta makale hade da dan  zuge labule window kadan ,ta yadda zata ji dadin  hango  abinda ke wakana a compound  din estate din.

 Tana nan tsaye tana  kallon yadda  motocin ke shige da fice a cikin estate din ,  ta zurawa waje Ido sosai kmr mai shirin hango wani abu na daban aciki estate din, yayinda take shakar wata  iska ta musamman  mai dadi da ratsa jiki.
 wanda rabonta da jin irin  haka ta dade ,  tun kafin   shigowarta  cikin gidan.

 ,har wani lumshe shanyayun  idanunta take  sakamakon farinciki data tsinci kainta ciki.

 ,Ta dauki tsawon  lokacin  makalle  agurin tana shan iska  "karar bude kofar dakin data ji anyi ne. 
Yasa ta  dan juyo da sauri   hade da sakin labulen window.

 ahankali  nablah ta sauke idanunta fess. akan Zeenat dake tsaye kikam.. tana    mazurai . take gaban nablah Yashiga faduwa da sauri  a yatsine Zeenat ke watsawa nablah  wani irin mugun kallon wanda ke hautsina kayan cikinta  , ganin irin kallon rashin arzikin  da  Zeenat ke  binta dashi ne . yasa nablah shan  jinin jikinta.  

tabe baki Zeenat tayi sannan tace Yar iskar baiwa...  kawai abinda yakawo kennan , kin wani zo kin nemi waje a daki kin zauna kina tamkar boka dan tsabar  munafurci ,  to kike so yayi  miki sauran  aiki da yayi saura uhm ?

Nablah tayi saurin girgiza  kanta  tare da cewa  dan Allah aunty kiyi hakuri wlh na dauka ko  mungama aikin ne.

Zeenat , ta  sake watsamata wata uwar  hararar hade da kallon banza.. wanda hakan ya suka  sake  frigita zuciyar nabla dake tsaye  Amman ta dake batare da tabari Zeenat din ta gane yanayin data ciki ba  .  

Mtsssssss Zeenat taja tsaki tare da cewa dan Allah  malam ni   fito ki kije ki karasawa mutane aiki sannan km ki daura min  abinci ,Yar isakar   baiwa...   nablah tayi shr tare da dago shanyayun idanunta   tana kallon Zeenat dasu ,yayinda take jin zuciyarta tamkar zata kama da wuta tsabar takaicin sunan da Zeenat din kirata dashi .

 Zeenat tace 
Kin wani tsareni da idanunwa narai narai kina  kallona ko baza kiyi bane ?
    a tsanake batare da  wata  alamun tsoro ko fargaba ba  nablah  tace zanyi  .. 
Ok minti biyu  kacal nabaki "naganki a kitchen "idan kika kuskura kika bata min lokaci zakiga yadda zan ci ubanki a gidan nan " tana gama fadar haka 
ta juya fuuuuuu tasoma tafiya  tana  kunfar baki.

 "Nablah tayi zuru kawai  tare da  bin bayan Zeenat  da wani irin kallon mamaki da alajabi abinda tayi mata.

 dan ko kusa batayi tsammani zata  fuskanci irin wannan babbar wulakancin ba mai cike da al,mara .

Yau itace   aka aiki tajawo aka zagin mahaifinta..abanza uban ta fa aka zaga  ,ta furta akan akasan ranta, wato  silar ainkinta ne  jawo a dinga wulakanta mata uba Haka   km  ma har da kiranta da sunan  baiwa...baiwa fa takirani dashi ta sake maimaita sunan  a filli gabadaya abin yazo mata    wani iri km abazata"  tamkar ba gaske ba.
  Anya kuwa rayuwar  zata yuwu a Haka tun ba,aje koina ba an fara da zagar mata mahaifnta.
" Anya kuwa zan iya  daukar wannan kalar kaskancin da  iskanci kuwa ,abinda ta tmbyi kanta da kanta  Keenan?

 ,'ahankali ta furzar da iska ta bakinta  tana furta wlh da sake Dan   zan iya  daukar  komai na kunci rayuwa  Amman Banda  zagar min iyaye .

 ,

 ,  Mtssss  taja tsaki itama tana harara kofar da Zeenat tabi .cikin sanyi jiki ta nufi  kitchen   .

Ko minti biyu batayi da daura ruwan abincin dare ba   Zeenat takaraso ta tsaya a bakin  kitchen din tana kiran..  ke....ke.. nablah dake tsaye tana jin Tayi banza daita duk da tasan daita take sannan km   taki juyowa ...
Sai ma cigaba  da aikinta Tayi.

  Sai da Zeenat ta sake maimaita kiranta sannan nablah da ke ..Kusan Sau uku sannan nablah ta juyo a danketa tana kallon cikin idanunta Zeenat .

Zeenat tace  ,Yar iska yarinya kawai  kina jin mutane suna kiranki Amman dan dakikanci irin naki kika yi shr..ko

 nablah ta hadiye bacin ran dataji yana taso mata tun daga tsintsiyar kafafunta ,sannan  tace kiyi hakuri  basan dani kike ba"   sbd  ita kalmar   ke.. din da kika ce bata daga cikinta   sunan nablah....


 . eyyyye  Zeenat ta fadi Haka tare da  ta ware ido tana kallon nablah da mamaki ni zaki kawa rainin hankali , nablah tace kiyi hakuri aunty barainin sense bane a zafafe Zeenat  tace yi min shr stupid girl kawai ni zaki kalla kicewa ba sunanki ke ba.... Dan  bakida mutunci ,  to kisani  ni daga yau  da sunan ke ... zan dinga kiraki ,Dan Allah idan nakiraki dan ubanki  karki amsa kiga yadda zanyi dake a cikin gidan nan .. .

 nablah ta datse  lip's din bakinta na kasa da karfi gaske  jin zafin abinda Zeenat tace mata  , kusan minti biyu tsakani nablah  ta sake duban inda Zeenat ke tsaye har lokaci gabadaya gabobin jikinta sun sage muryarta cike da rauni km Haka kawai ta tsinci kanta da cewa kiyi hakuri aunty .da hannu Zeenat ta katseta .. yimin shr Dan Allah dan bana son sake jin ko muryarki ne .. km ki sauke  pot dinan  ki daura min indomi yanzu yanzu taja tsaki tare barin kitchen din.

 cike da mamaki  yarinyar  Zeenat takarasa ta zauna ranta a abace  wahake take fidda numfashi  dan   kwata kwata bata taba jin tsanar mai aikinta irin yadda take jin haushin nablah .

Gashin yarinyar kmr bata da  wani alamun tsoro atare atare daita  .

 Cikin  mintinan da basu  wuce biyar ba  ta sauke  indomi ta yuye   a plate sannan  ta sake maida pot din abinci dare kan gas .

 zaune  ta sameta   ta hankice a parlour  sai faman  cika take tana batsewa tare da hura hanci 'tana kada kafa daya ..

ahankali  nablah ta ajiye mata plate din indomi agabanta akan center table  tare da kwalbar  vitermilk kana   ta juya ,tabar parlour .
 ,banda tunanin da mamaki Zeenat  bbu abinda nablah keyi  .

ko meyasa ita takasance irin haka ba kmr ummi ba ,mai matsananin son mutane da kyautata musu" km tana lura da irin yadda ummi  din  ke matukar bawa duk wasu mutane  dake shigowa cikin  gidan, kulawa ta musamman " sabanin ita wannan bazanr matar mai kama  da mutane China .

 , 'Ahankali nablah tacigaba da aikinta na zagin Zeenat din aranta sai data gyara koina tsab .

sannan taje  tambaye Zeenat din ko akwai wani  sauran  aikin  da zatayi Dan gujewa cin mutuncinta .

 ,a yatsine Zeenat din ta dago fuskarta tamkar hadari sannan  tayi mata  nuni da hannuta alamun zata iya wucewa kawai .

 jikinta a mace tabar gurin ,  da kyar ta dinga   daga kafafuwanta tsabar gajiya datayi , yayinda idanunta suka ciciko da Hawayen batayi kokarin hana hawayen idanunta zubowa ba,sbd tashin hankali take ciki da wutar dake ruruwa a zuciyarta  tana tafe   tana   kukan zuci yayinda hawayen idanunta ke sake  cigaba da bin fuskarta...

 ahankali  ta  hau  step  daidai conar da zata kaita dakinta.
 anan suka  kusan cin karo da deeni da ba dan Allah yakiyaye da sai daita tajita a faffadan kirjinsa . sakamakon hannunta duka biyu datasa tana goge Hawayen idanunta   ..

daddaden kamshin turarensa ne  ya doki hancinta a frigice tayi  sauri  janye jikina..
  Ta makale jikin bango batare da tasan Tayi hakan ba , jikinta ya dauki rawa kirrrrrrma    hawaye km sharrrrrrr suna  sake bin  fuskarta ido cikin ido suke kallon juna ,itace ta soma janye idanunta ta  ta runtse  gam tana jinra kawai taji saukar mari ..
 ,  tsayawa yayi  cak  Shima  yana karemata  kallo up and down .

 A tsorace   tasa tafin hannunta duka ta rufe fuskarta dashi.. kijinta na sake daukar kirrrrrrma .

'Ahankali  ya ja  wani irin mugun  tsaki mtsssssss wanda hakan ya sake jefe zuciyar nabla shiga   cikin rudani .

 ,   yana  tsananin jin haushi yadda yarinyar ke behaviors kmr wata  dakiykiya   .. 
 harara ya zabga mata   kana ya sake jan tsaki sannan ya yasoma taka step  . tana jin takunsa har sai da yakurewa step din Sosai sannan ta bude idanunta  da sauri  ta fada dakinta tare  dannawa kofar key ..

.ta fada kan gado takarasa  fashewa da wani sabon  kuka.... Mai cin rai  blaming kanta kawai take ta yadda tayi sanadin jefa kanta cikin meyakawoni matsala.
 , meyakawoni cikin wannan gidan ?

meyasa na kawo kaina cikin  halaka irin haka ?
 anya kuwa nayiwa kaina adalci Dana zabarwa kaina irin wannan rayuwar ,mai cike da kaskancin da wahala ..
Anya kuwa  zan iya cigaba da yin wannan aikin kuwa ? Haka ta dinga jerowa kanta  tambayar iri iri batare da tasan abinda yakamata Tayi ba ..
yanzu irin rayuwar da zanyi kennan?
  ..Ta sake jeho kanta  tmby.
 agigice tatashi  zaune  ta jingina bayanta da jikin gadon dakin  tare da  zubawa celling dakin Ido  tana tunanin abinda yakamata tayi "shr yabiyo baya  na wani dan lokaci .

 tuno  auntynta datayi ne yasa tayi saurin  sauke ajiyar zuciya, Dan tasan ita kadai ce zata iya  fidda ita a wannan halin wulakancin datake ciki , batare wata matsala ba.  ai aikin bai zama  dole ba  ,  da sauri ta hau goge  Hawayen fuskarta  tace zan kwantar da hankalina na zuwa wani lokaci "kafin nasamu yin waya da  auntyna . ahankali ta Mike tashiga bayi ta dauro alwala sallar magrib koda ta idar ma  bata tashi ba sai datayi isha'i a gurin .
 ,  bata bi takan komai ba dan ko abinci bataji zata iya  zuwa ta sakawa cikinta ba .
 ballallantana  ta hadu da hawan jini ,da  ciwon ulcer  wato deeni da Zeenat .

 ,Ta   kwanta anan ta dunkule jikinta  cikin hijab  tare da lumshe idanunta kawai" duk da ba  wani bacci takeji ba, ahankali  tarinka jin yadda  zuciyata tasoma beating  dip....dip....  kafin daga baya tashigayi da sauri da sauri sakamakon tunowa da Mr horo datayi  ...
  "Tarasa dalilin dayasa  duk sanda tayi arba dashi  ko  ta tuno shi   take shiga cikin  tashin hankali, ba.
 ,  addu'a tasoma aciki.  zuciyarta ya Allah...ya Allah kamin tsari dashi da duk wani wani  shirin dake tattare dashi  . Allah idan zama acikin gidan nan  alkhari ne a rayuwarta  Allah kasamun natsuwa da hakuri  zama da matar gidan .
  ,idan km bbu alkhari  Allah  ka fidda cikin kowace irin maseefa cikin sauki . haka tayi tayi yan  addu'oita , har taji zuciyarta ta dan samu natsuwa daga tashin hankali data shiga na wuncin gadi ,daga karshe   bacci mai nauyi yayi gabadaita.


Acan kasa kuwa DEENI ne kwance akan thrre sites hannunsa rike da remut yayinda  zeenat ke zaune a gefenshi suna hira ,rashin ganin nablah yasa duk ummi  ta damu har   . takai ga tambayar zeenat  ita  ,  ummi tace ni kuwa ina yarinyar nablah take ne  har yanzu banga saukowarta ba ko lafiya?deeni dake zaune yaji gabansa ya fadi zuciyarsa tashiga harbawa .

"   zeenat  ta Dan yatsina fuska  kana tace wa ummi  .  ai tun  dazu kafin ki dawo  ta  sauko  taci abincinta ta koma dakinta dayake      fita ummi   tayi ,yau . Ummi ok na jita shr ne .sannan tacigaba yabon nablah yarinya mai  hankali wlh .
  Zeenat taji magannun ummi na neman saka mata ciwon kai ,ta barta da karyar data   ,sharara mata ta ba gaira ba dalili   .

 Zeenat ta Mike tsaye  tsam  tare da yiwa ummi sai da safe Dan itama yau bacci take son yi da wuri sbd tana da lecture karfe goma  daidai na safe .. .
ita data shiga dakinta da niyar   samun natsuwa Amman zuciyar tashigo mata da tunani iri iri ciki kuwa  har da maganar haihuwar da bata km samu ba har yanzu  wanda shine jigon rayuwarta  a gidan mijinta  ..

'Byn tafiyar Zeenat ummi dago Ahankali tana duban deeni tare da  kiran sunanshi..
 DEENI dake kwance  ya amsa hade da dan mikewa zaune ya mai da hankalikasa kacokan  a kan umminsa .

Ummi ta numfasa sannan tacigaba   deeni  naji  kamin shr game da zance yarinyar nan mai aiki... , gabansa ya yanke ya fadi  rasssssss ...jin abinda   ummi tace  "ya zubawa ummi ido kawai  yayi shr yarasa me zai ce mata  "  saima shiga wani yanayi da yayi .'ahankali
ya runtse idanunshi  yana Jin tamkar  ummi  ta watsa masa ruwan zafi yake ji da wannan maganar yarinyar  datayi masa.
dan zuwa yanzu ya dauka ummi tabar zance ne kwata kwata  ganin bata sake mishi maganarta ba .
"ummi tace kamin shr DEENI idan kasan baka shirya yin komai ba akai  mezai hanna ni kabarni na aiwatar da komai domin  nasan   abinda zanyi ..
 "ahankali deeni  ya bude rikitattun idanunshi ya zubawa ummi su kawai yana  kallonta ,kada masa kanta  tayi alamun abinda ta fada din  haka take nufi  .
yace  first lov kiyi hakuri Dan Allah zansan abin yi  Amman dan Allah kidan karamin lokaci kadan kinji first lov .
Ummi tayi shr can Kuma tace shikenan Ni daita  burina bai wuce nasamu abinda  nake  fatan samu daga yarinya ba .. tan Ga fadar Haka ta mike tana mishi sai da safe .

  ,Karfe shadaya daidai deeni Yashiga dakin Zeenat byn ya gama shirin bacci  cikin wasu  ratsasun kayan  bacci.m masu matukar kyau.

    batasan shigowarsa  ba tana can duniyar  tunani "ahankali DEENI yakaraso har inda take tare da   ya kamo tafin  hannuta cikin nasa Yana murzawa  sannan ta juyo 'ahankali tana sauke naunauyen ajiyar zuciya.

 ya tsareta da idanunshi kawai sannan   yace meke damunki  Zeenat ?
Ke ke nan  kullun bakya gajiya ,ki raba kanki da wannan  tunani ,kisani tunani shine abu mafi sauki dake saurin nakasa rayuwar  Dan Adama  Amman ke kin maidashi abincin cinki kullun ..,kinsa Allah ba tunaninki ke damuna ba ,halin da first lov zata shiga sanadin wani abu ya sameki nake .idan  akwai abinda kika san yana  dumunki please tell me...
tayi shr kawai tana kallonsa sun dade a haka suna kallon junansu   sannan ,  ko me ta tuna Kuma  ta sakar masa murmushi karfin hali ta matse hannushi cikin nata gam tare da  lumshe masa  idanunta ta girgiza masa kai alamun bbu komai .

Deeni yace I you sure bbu komai" ta dage masa girarta daya kmr yadda yake mata shima, har taso tabashi dariya yayi murmushi tare kwantowa jikinta  ya rungumeta  ajikinsa tsam tsam  Yana aika mata da sakwanninsa masu matukar birkita mata kwalkwaluwa ..   hannuwansa duka yasa ya zagaye kugunta  dashi  ,Haka kawai Yashiga aiyanata  yarinyar, 'ahankali ya sake narke mata ajiki yana duk inda hannushi yaci karo dashi itama cikin kwarewa tasoma  romancing dinshi .
 ranar dai kwana sukayi suna jiyar da kansu dadi  deeni yayi  Tayi batare gajiya ba  .
Iya  murzuwa Zeenat Tayi shi a hannun DEENI  har kai  saka  masa  kuka sannan  yabarta ya Mike  Yana mata korafin tacika  ragunwaci.
 ita batace masa komai ba .  washegari gari  ma da kyar tasoma tashi yayinda  da kyar ta dinga  kafafunta,  bayi tashiga  ta gasa jikinta da ruwan zafi  .

 baita tabar gidan ba Sai wuraren 9 AM .. ..




MMN SUDAIS CE
[7/12, 7:08 AM] 0mmer Farouk: 💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗





AYSHA A BAGUDO





Page 64



Tun byn fitar Zeenat nablah ke faman  aikin gyaran gidan batare da samu damar zama ta huta ba.
  ,duk da matar gidan bata nan   hakan bai hanata yin kokarin taga ta kammala da aikin ba .


Tana tsaye a kitchen din yayinda hannuta ke kai kawon   gogen kayan kitchen din  Wanda  ya zame mata  dole kullun garin Allah Ya waye sai tayi.

  laraba ce tashigo kitchen din tana yimata sannu tare da sanya hannu tasoma kokarin taimakawa nabla da  wasu  ayyukan .

 Nablah Tayi murmushi dama kinbarshi aunty yanzu zan gama ai"

Karki damu sis nima zaune nake bana aikin komai shiyasa kikaga naxo .
 gashi km Naga kmr  aikin Yayi miki yawa dan nasan yadda yanayin aikin gidan nan yake da  cin rai  km bai karewa.
  " Dan ma  Allah taimaka  madam  batanan da yanzu tasa jininki ya hau kilometers duhu.

 ,Dan har gara hjy da mai gidan akanta " Dan shi maigidan kwata kwata  baya shiga harkar mutune yayinda ita   hjy   wani lokacin   takan tausayawa mutun.

 nablah tace Haka ne  .laraba tacigaba
 amman ita madam Komai zata saka mutun Sai ta nuna maka iko da isa " Ga zagin rashin mutunci , tamkar ta haifi mutane , km duk irin  aikin da zakiyi mata idan bai gamsar daita  a banza yake a gurinta  . 

nablah Tayi shr kawai tana sauraronta  batare da tace mata ba , komai Sai ma maida hankalinta  datayi kan aikinta.

 laraba ta sake  cigaba kinsa Allah ko abinci kika dafa wannan matar , muddin baiyi mata ba wlh dole ki sake yin wani  .


Nablah dake tsaye 'tana  aikinta , tace nifa Ina ganin kmr mdm din nan taki , kwarkwar ce.......

  "Haba aiko  laraba ta kwashe da wata muguwar  dariya , kai   gsky nablah baki da kirki wlh  madam din ce kwarkwar tana mai  sake kwashewa da dariya .

 nablah ta bar abinda take ta juyo Sosai  tana duban inda  laraba take .

Kinsa Allah  wlh Ni kallon kwarkwar nakewa  matar nan  sbd wasu abubuwa dana Ga tana yi  Na marasa hankali.

"  nan dai sukai ta hirarsu tare da  zagin Zeenat din ,.
 nablah har da cewa Allah Yasa ogon madam yakarowa mdm amarya labara Tayi saurin kai hannuta ta toshe wa nablah baki ,tare da leka parlour sakamakon jin kmr  motsin mutun .
  "ganin     bbu alamun  kowa ne yasa ta dawo ta tsaya  kusa da nablah .

"ai inaganin  abinda mdm din tafi   tsana kennan a rayuwarta .
  "kishiya.... uhm zata iya yin komai akan mijinta. ba kya ganin ko inda mijinta yake bata son  ana zuwa ,ke ko kananan kaya kika saka wlh  Sai takawa mutun  miki birki da guzirin  Harare da zagin .

 ,kinji ba , ai abinda yasa  kikaji nace miki ,  Ina mata kallon kwarkwar  ,Dan some time sai inga kmr  tana  hararata byn ban mata komai ba inji cewar nablah.

 Laraba ta numfasa sannan tace shiyasa  lamarin  zaman gidan Sai kin kara da  hakuri. nabla ta sauke naunauyen ajiye zuciya sannan tace indai   hakan kike fama da matar nan  Na jinjina miki dan gsky kinyi kokari wlh.

, ai a Haka ma   bakiga   komai ba indai mdm ce  inji cewar laraba , Dan naga kmr ke  kina da wani      matsayi a  gidan" tunda har an barki kina ganin mai gidan ,gashi km har  special room  aka baki a sama.

" Mtssss nablah taja wata muguwar tsaki  matsayi ko walaha byn  bakada wata  darajar a idanun masu gidan. "nabla ta sake yin kasa kasa  da muryarta  Dan kar wani yajiyo abinda zata ce sannan tacigaba abinda zan fada din nan  Dan Allah bana son ki fadawa kowa" Amman  Allah nayi mugun tsanar mdm  Zeenat  din nan byn Haka km Ina fatan  Allah Yasa mijinta ya kara aure.
, Dan kawai nayi  kallon irin  kalar haukar da zatayi koda yake ma ,may be by the  time din   da zai kara  auren ma ,na dade da   barin gidan Dan bana jin zan  dau wani   lokaci a gidan nan .
 , laraba tayi saurin marairaice fuska   haba nabla Dan Allah kada kiyi Haka ,Karki tafi ki barni na rigada na saba dake banzan so ki tafi kibarni ba .hakuri kawai zakiyi da halinta ,kiyi abinda yakawo ki.

 laraba  da nabla suka cigaba da aikinsu  suna hira sama sama laraba Na sake  cigaba dabawa nablah labarin gidan dama estate din gabadaya ,Da yake  ita  tana fita sosai .
nabla sai murmushi take km tana kwadayin fita taga yanayin estate din  Dan tun zuwanta gidan ko get bata sake lekawa ba .


Washegari  gabadaya da gyre gyre  aka tashi  dashi a gidan.
 koina ka kalla a  hargitse  yake saboda wani gyara da  za'a a sama da km zuwan  bakuwar daza suyi daga kasar  India, kmr yadda  nabla taji  zeenat nafawa wata friend dinta datazo .

   kai kawo nablah ta dinga yi tsakanin upstairs da downstairs , kallo daya zakamata  ka gane tsansar yadda ta fita haiyacinta tsabar gajiyar dake tattare daita dole ma  kaji ta baka tausayi .

tsaye take kusa da  zeenat ta takure jikinta waje daya , byn ta gama waken kayan da Zeenat din  tayi amfani dasu ,banda harara da kallon banza bbu abinda take jiho mata .
 
 ,A zafafe Zeenat din ta kallo inda nablah ke tsaye   kinzo kin wani  tsayamin a kai kmr zaki tsotsemin jinin  jiki   ki dauki plastic ki kawai my hrt.. takarasa fadar Haka tana watsawa nablah wanimugun harara .

Nablah tasa  'hannu  kennan zata dauka  sai ga laraba tashigo kitchen  wasu kayan wando jeans da Riga   Tayi gurin  frij  .

 zeenat ta kallite  ta kalli kayan jikin laraba sannan ta watsa mata wata uwar  harara ,har  nablah ta ji hantar cikinta sun cure gurin daya  . 

 Fuskarta a yatsine Tace meyye haka kuma  laraba ...kinsa   bana son wannan iskanci a gidana .
bama na hanaki saka  irin wayan nan  kayan ba?

  Nablah ta dago ta dubi aunty laraba  jens ne a jikinta sai riga iya gwiwa .

   ok  karuwanci  kika zo yimin a gida ko me?
  , da sauri laraba  tasoma bata hakuri .
 dan Allah madam kiyi hakuri wlh  bazan sake sanya su  ba wannan mistake ne .
 ,da hannuta mdm Zeenat  ta dakarta da ita ya isa bana son jin komai  daga yanzu ma na kashe sa irin iriin wayandanan kaya muddin kina son zamanki ya daure  dani. sannan ta kallo inda nablah   tsaye  har lokacin bataje inda ta aiketa ba ,tsawa ta buga mata  ke kuma  tsayuwar uban  me kikewa mutane da bazaki wuce ba   kin wani tsareni  da shegun idanuki masu kama dana mayu..  bazaki wuce inda na aike ki ba.

Duk da  nablah taji maseefar  tsoron  yadda taga  Zeenat Tayi Amman hakan bai sa ta nuna ta fito da tsoronta filli ba a dake sannan km fuskarta a hade   ta  bar kitchen  din  hade da tausayawa kai banta.

Domin bata  ganin laifi Zeenat   sai nata domin ita takawo kanta da kanta cikin wannan maseefa.

  Ta Dan tsaya kafin takarasa parlour mai gidan Tasa 'hijab dinta  tana goge hawayen daya yasoma bin kuncinta dan  iri irin abinda   zeenat takeyi musu  yana  taba mata zuciya  sosai .

'cikin sanyin jiki  tasoma tafiya har ta iso parlour da mai gidan yake tare da  bakinsa  da sallamarta tashigo. muryata fal cike da tsoro da fargaba.

   kallo daya DEENI yayi mata ya dauke idanunsa sai abokansa  guda biyu ne  suka amsa mata  sallamar.

, ahankali cikin tafiyarta  mai daukar hankalin ga duk wanda ya kalleta  , ta karaso ciki sosai ,  ta tsugunna ta ajiye plastic din da cup's .

Banda   kallon kasa ido  bbu abinda DEENI yake mata ,'ahankali tare da natsuwa ta soma tsiyaya  musu coffee . 
cikin wata kwasatsiyar murya taji ance ke zaman me kikeyiwa mutane anan  .... oya live this place now...

   Gabanta ya dukan uku uku ,cikin tsananin tsoro hade da tashin hankali ta Mike tsaye , jikinta  ,har rawa rawa yake tasoma kokarin daga kafafunta yayinda  idanunta suka ciciko da hawaye tafff, ta bar parlour,  daidai bakin kofar main parlour  ta kusan ci karo da  zeenat da sauri taja da baya ta tsaya, tana mai sa  bayan hannuta tana goge hawayen dake bin  fuskarta.

  Zeenat ta tsaya kawai tana kallonta tare da nazarinta da kyau sannan tace  kukan munafurcin uban  me kikeyiwa mutane ,kmr ba aikin kudi kikazo yi ba tasoma maseefa tana  zaginta .

, duk yadda nablah taso hadiya damuwar dake zuciyarta  hakan yakasa samuwa , domin kuwa sabon Hawayen dake makale a idanunta ne suka samu nasarar zubowa .

  , uhmmmm daman Sai Dana gaya ummi tabari a sallemiki Dan nasan  bazaki iya tabukawa mutane komai Amman tace Sam...

Yanzu kukan iskanci me kikeyiwa mutane nablah ta girgirza kai tare da cewa bbu .


 Zeenat ta tasoma kada kai cewa   zama ayi komai din sannan   ta Miko nablah wani karamin jug mai dauke suga  tace ungo Ni  ki kaiwa    mijinta baiwar banza kawai.

,jikinta a sanyaye  km  badan ranta yaso ba  ta sake koma parlour   ...

byn ta fito ne  ma abokinsa manir yace DEENI  ina kasamo wannan fine bby din mai tsabar kyau gaskiya tamin kyau sosai  .....

Take  DEENI ya hade rai tamkar Wanda yaji wani mugun abu .. meye matsalarka daita ?

 Manir yace yarinyar ce tamun kyau kawai  , a  fusace deeni yace bakowa bace facce    house girl dina.

 dayan abokin nasa ne  yace  gaskiya yarinyar tana da kyau sosai ba karya gashi Tayi maseefar ta haduwa dayawa .
irin  wayan nan Ai  nashiga mota ne  da kewaye kasashen duniya .

 A zafafe DEENI yace  bafa nason iskanci nan naku idan abinda yakawoku kennan natashi nakama gabana .

Manir yayi dariya tare da cewa kai fa matsalar kennan to laifi ne dan mutun yaga abu ya yaba sai  km yazama abin damuwa.
Fahad  dake zaune yana nazarin deeni ya amshe da cewa   kai meyasa DEENI kike yin irin haka ne ? Kacika daukar komai da zafe.

DEENI  ya hassala  dan takaici Dan  Allah ni kun dameni da zance wata  banza yarinyar ni wlh duk na Raina da ajinku wlh .
  " da har kuka tsaya karewa wannan banzar yarinyar kallo "  fahad yace idan kai makahone baka gani  mu wlh muna  Gani ,kuma  dole mu yaba baiwar da Allah yayi .

  , 'Ahankali ya ture document din dake zube gabansa ,Coffeen  da nablah tasoma  siyaya a cup, din yasa 'hannu  ya dauka yasoma  kurba ahankali ahankali  tare da lumshe ritattun  idanunshi .

Manir da fahad  suka bishi  da wani irin kallo ganin abinda yayi . yayinda manir ya cika da mamakin deeni .

Fahad   yace  mekake nufi yanzu  da haka sai da hadeye wanda ke bakinshi sannan yace ga abinda nake nufi nan kuwa ,  kowa ya yakama gabansa.

Manir yayi murmushi sannan yace to munji amman zai siyayyamu coffee to  , juyar da fuskasa yayi wani gefen sannan yace  ai duk kuna da 'hannu ,idan baku tashi Sha ba ,kubarshi .


 murmushin fahad  ya sake yi yace  da alamun rashin mutunci  kawai kake son yimana .

DEENI  ya daga kafadunsa,  duka a alamun  I don't care .
nan dai suka mai da abun wasa atsakaninsu  suka cigaba dayin  abinda ya kawo su byn sungama ne DEENI ya Mike yace yana zuwa .

Zuwa yayi   ya canza kayan jikinsa zuwa kanan kaya  sai kamshi  mat Hamilton 27  yake zubawa   part din ummi  yashiga yana kiran sunanta  .. first lov..  were are you .

 jin shiru bata amsa bane yasashi  kutsa kansa cikin bedroom dinta kai tsaye batare da yayi tunanin wani abu .


 Ita  kuwa dake   zaune  tana jerawa  ummi  kayanta  da mai wakin yakawo dazu  a Waldrop ta  zabura ta Mike  tsaye da   sauri,  duk ilaihi  jikinta bbu inda Bai dauki  rawa ba  saboda tsabar tsoron muryar data  jiyo.

 Sosai kamshin turarensa ke kusanto dakin alamun yana gab da shigowa .   gashi   bbu  komai ajikinta  daga ita sai  daguwar riga   mai 'hannu harmless  cikin sauri sauri ta  soma neman hijab dinta .
data cire amman tarasa inda ta ,ajiye   .

har yashigo dakin , cak ta tsaya ta kasa kwakwarar motse ,jin tsayuwarsa jingine da kofa yasa take kirjinta ya buga yayinda  zuciyata tashiga  ..
  aikin da tasaba a duk  sanda , ta kasance tare da DEENI.

 shima tsaye cak  yana Kare mata   kallo  tsab wanda in ba lura mutun yayi   da kyau ba.

 ,ba za'ice  ita yake bi da wannan mayataccen  kallo ba .
 shida kansa yasan in yace yarinyar batayi ba , tabbas karya yake km  son ranshi ya fada .

    ahankali   yakaraso dakin  sosai yana sake kiran sunna ummi . kainta  a sunkuye a kasa yayinda  zuciyata ke  wani irin bugawa da sauri  cikin siririyar muryata mai cike da in inna ... tace ta.. tana.. bathroom ... 

Bai ma tsaya wani sararonta ba ballanantana  ya nuna alamun yaji abinda tace ba ,  tunda shima yaji alamun haka.
 juya kawai yayi yabar dakin cikin takunsa ,na tsanyaye namiji .

  Numfashi ta sauke tana may sa dukka  'hannuna ta dafe kirjinta dashi  tare da  sauke ajiye zuciya.
 
 wayyo Allah  wannan mutumin  ba dai  frigita mutane  ba .
 numfashi ta dinga  fitarwa  'ahankali 'ahankali har  ta dawo normal .km Sai a lokacin taga  hijab din ta washe   a gefen 'tsabar rudewa ce tasa  takasa Gani.

  fitar shi  bai fi da minti uku ba ummi  tafito tanawa nablah  sannu da aiki sannan tasamu  waje ta zauna,  tana dan Jan nabla  da hira , itama  dai ba laifi  takan dan saki jikinta ummi dan tafi zeenat sau dubu har aka kira sallah suna  tare da ummi  dan dakin tadawo yanxun saboda aikin da za'a yi Wanda ya hada  har da dakin nablah.

 Mikewa tayi nablah Tayi tare  cewa ummi Ina son  naje  nayi sallah .

 murmushin ummi Tayi  haba nablah yanzu sallah ma sai kin tambaya ,ummi girgiza kawai tare da cewa  ,jeki kawai kiyi sallahrki kinji  ..



MMN SUDAIS CE
[7/12, 7:08 AM] 0mmer Farouk: 💗💗💗💗💗
 AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗





AYSHA  A BAGUDO



Page 65




Byn ta idar da sallah magariba,tana zaune akan  praymat , tacigaba dayin lazimin daya zame mata jiki .

 har sanda taji  kiran sallar isha,i daga  masallaci dake cikin gidan sannan ta mike ta gabatar da  isha'i  tayi addu'a  sosai .

abinda ke karasa ummi  jin kaunar yarinyar nashiga ranta kennan, ita din mai yawan ibada ce ko kadan bata wasa da lokacin sallah.
  ahankali nablah  ta mike tsaye  tana nade praymat   . Gaban ya fadi rasssssss sakamakon yiyo sautin muryasa yana  yashigowa hade da sallama
yayinda mdm  zeenat ke  biye dashi tamkar wata bindi.
 waje yasamu kusa da umminsa ya zauna yana zuba mata shagwaba tamkar wani  karamin yaro . 

gabadaya kamshin turarensa yaci koina dakin  ummi ta dago idanunta  ta kalleshi  da kyau  tana harararsa wanda kallo daya zakayiwa ummi  " ka zagane  Hararar tsansar soyayyace irin  ta tsakanin uwa da "da" .

 Shima  kallon umminsa yake  yana  murmushi tare karyar da kai , ummi ta dubi Zeenat  kalli mijinki da kyau  sai Naga kmr ya  rami yau ko idanuna ne .

Zeenat Tayi murmushi sannan tace bbu wata rama da yayi ,idanunki ne kawai ke ganin hakan.

DEENI ya zabgawa Zeenat harara tare da cewa ,  rabu daita first love ai bazataga ramar danayi ba , sbd  basanin yadda ake kula da miji Tayi  ba , amman   gabadaya yau a gajiye nike ,ya fadi Haka yaba  narke fuska.
  abin ma har yaso bawa nablah dariya , Amman ta share kawai saboda ba muhalin   yinta bane.

   Ummi ta sake duban dan nata  da kyau tana  murmushin tace kai.. Sam bakasan ka  girma ba wlh , kullum shagwaba shagwaba shagwaba tamkar yau aka haifeka ,bazama ka dan rage, ka barwa ya'yanka ba .

,anhakali ya dan dago ya kalli ummi sannan yace haba first love, nasan ko duk  duniya nan zan  haifa matsayina  daban da nasu ,, sai dai  kawai zan iya hakura na bar musu sbd mahimmanci su gareni .
 , ya karasa fadar hakan ya na murmushi hade da kashewa umminsa idansa daya.
 gabadaya sukayi dariya Amman banda nablah dake cigaba da nade abin sallarta.
  Cikin sanyi jikin nan  nata kmr koda yaushe tabi gefen inda yake zaune wanda dole sai ta wajen zata bi , ta,ajiye abin sallah sannan ta juya zumar basu guri   taku daya zuwa biyu Tayi   taji  muryar  zeenat   ke.......kalmar da taji kennan cikin isa.. da takama da nunawa nil,adam  shi din bakowa bane.

 ahankali nablah ta juyo suna fuskartan juna da deeni , batare da ta kalli inda  zeenat din take ba .

 yadda take kallonsa ta kasan idanunta.
 hakan ce takasance dashi   domin Shima  takasa idanunsa yake satar kallonta, wanda duk nacin mutun bazai taba iya ganewa  hakan ba .
  zeenat tace kin wani tsaya kina kallona  ko nan zan biyoki hade da watsa mata harara sbd yadda taga rana karewa mijinta kallon tsab... cikin sanyi jiki  nablah ta hadiye abinda ya tokare mata kirji tare da karaso har inda take , murya a  dake   tace Gani .... yadda tayi maganar ce tasa zuciyarsa bugawa da sauri , ba zuciyar DEENI kadai ce ta nemi tarwasewa ba har data ummi ,dan sai data tsorata da yadda yarinyar tayi  .  cike da  isa da takama zeenat tayi kwafa tare da aiyana yadda zataci ubanta . tace kije ki hadowa my hrt coffee yanzu ki kawo  masa sauran ki bata lokaci da wannan banzar tafiyar take kmr tsutsa .

cikin sanyi murya ta amsa mata da  to..... kmr mai shirin zubda kwalla Sannan ta juya ranta  a cunkushe ,zuciyarta tamkar zata tarwatse saboda salon da  zeenat din ke kokarin son nuna mata .
 ko baiwa ce ita iyakarta kennan bata dai kaunar taganta 'tana hutawa .

tafiya kawai take 'tana tuno yan'uwanta da mamanta , batama san sanda hawaye ya wanke mata fuskarta ba .
 tasa bayan hannuta tana goge    hawayen  yayinda  wasu ke sake silalowa.
  minti biyar tsakani ta sake  dawowa dakin  hannuta dauke da  tire Byn tayi sallama a sanyaye ta janyo wata yar karamar kujerar dake ajiye a gefen ummi gabansa ta ajiye masa wani irin kallon  zeenat  ke  binta dashi may hade da harara harara ne  yasa tayi saurin barin   dakin zuwa falo   .

Bata fi yan mintina da fitowa daga dakin ba  shima yafito a natsensa sai  kamshin turaren mat Hamilton 27 ke tashi.gabadaya  yacika parlour da kashi . da sauri ta dago  shanyayun idanunta suka sauka akan  fuskarsa wayace manne da kunnensa  yana magana cikin sanyi  muryar nan tasa tamkar ana busa sarewa .
May  dadi da dadin sauraro.

 kallon da yabita dashine yasa tasha jinin jikinta hade da dauke idanunta ta sunkuyar da kanta kasa takamo  yatsun hannuta tana wasa dasu .
 yayinda gafe daya gabanta ke wani irin  faduwa har yabar dakin idanunta na kasa batayi kokarin dagowa ba sai data ta kusan minti goma ,ta tabbatar wa kanta yabar gidan gabadaya sannan  ahankali ta dago shanyayun idanunta tabi kofar da kallo . 

zuciyarta na wani irin dokawa da sauri da sauri   a sukwane  ta lumshe shanyayun idanunta masu matukar daukar hankali tace kai komai na mutumin nan    may kyau ne . Ummi daga inda take zaune ta kwallawa nablah Kira .tashigo batare da ta kalli inda Zeenat ke zaune ba ,itama Zeenat din runtse idanunta tayi tun lokacin dataji ummi takirata .

Nablah tace ummi gani Cike da girmamawa ummi ta zuba mata ido sosai 'tana  kallon fuskarta  tamkar ba , fuskar dazu ba ,sai Gani tayi yarinyar ta sake canza mata Anya Kuwa bazata fasa hadin nan ba ,karfa tazo tayi datasani . tsawon lokaci nablah najiran ummi kafin daga baya ummi ta nimfasa tace  yauwa daman  abinda zance miki  zaki iya koma dakinki  ,dan angama gyaran da za'a yi . nablah tace ta wuce  Tare  da yiwa  ummi sai da safe .'tana shiga dakin sai data frigita daganin yadda yakoma tamkar bashi ba ,komai Na dakin an canza hatta kofar dakin bayi tayi saurin shiga Shima the same tsaki taja kawai 'tana aiyana yadda ake barnar kudi a gidan zuwa gidan an gyara gidan yakai Sau biyu Keenan. Zuciyarta ta kwabeta da Ina ruwanta ,dan Haka ta soma cire kayan jikinta .

 
 11: pm



Zaune yake akan kujera dake  dakinsa  yayi zurfi cikin duniyar tunani .
yayinda hankalinsa gabadaya ke sake tashi a duk sanda ya tuna da maganar  first love  .
sai ya dinga jin  hankalinsa na sake tashi   kuma  a kullum ya daura idanunshi kan yarinyar sai ya dinga jin gabansa na tsanata faduwa wanda bai san dalilin jin hakan a tare dashi  ba.
 Wanda shi da kansa yakasa sanin  takamaimain dalilin dayasa yaji farat daya zuciyarsa ta amince da zaman  yarinyar a tsakaninsu .
a duk yan aikin da aka sha  kawosu garesa . ahankali ya sauke naunauyen ajiyar zuciya yasake gyara zamansa sosai akan kujerar dayake zaune   ,cikin sanyi jikin nan nasa tamkar macce ya matso  ya kunna CCTV camera  .

idanunsa kawai  ya zubawa camerar  yana kallonta  .
 tsaye take a gaban dress mirrow Byn ta fito daga bathroom daidai lokacin da tayaye towel din dake daure da jikinta ,tana kallon jikinta as usual da sauri aliyu ya dauke kansa  ,idanunsa a tsorace da mamaki yace subuhanallah.....domin kwata kwata  ba abinda yayi tunanin ganin ba kennan. Yaci karo dashi.

tunda yake a rayuwarsa  bai taba ganin jiki mai kyau da daukar hankali ba irin nata .
 ,Take  yaji yana samun  special reaction da sauyin yanayi ajikinsa, 'ahankali yasa hannuwansa duka ya dafe joystick dinsa dasu tare da  jingina bayansa da jikin kujerar, yana sake kallonta ,yarda towel  din tayi  tana sake kallon every part of her , ta juyawa mirrow din bayanta tana kallon  bombom dinta ahankali ta sakarwa kanta murmushi dan yawanci ba ganin bayanta take ba mostly  .
sai dai gabanta kawai take Gani  .
  ahankali ta lumshe shanyayun idanunta   ita kanta ,tasan tabbas yanayin jikinta ya sake sauyawa fiyye da da a dan wannan lokacin .

sannan ta sake juyowa 'ahankali tana kallon  manyan Brest dinta wanda suke a cike bam kuma a tsaye suke kyam abin sha'awar kowane da namiji .

DEENI dake zaune duk ilahirin jikinsa bbu inda baya rawa saboda rudanin daya shiga . hannuwansa biyu dake dafe da joystick dinsa ke kirrrrrrmama.....yana sake dafe  joystick dinsa  dasu dan yasamu  yadawo normal. Domin kuwa
 tunda yake bai taba samun kansa cikin jarabar sha'awa ba irin 
 na yau .
Na yau din km ya bambanta da sauran kowani lokaci .





MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
     💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A bagudo




*Please fan kuyi hakuri  da typing errors din dazakugani ,domin bazan koma Na duba ba ,kuyi manager  Ku gyara kuskure da kanku  sbd jiki da jini*

Page 66


Tsananin tashin hankali ne ya bayyana akan fuskasa zuciyarsa ta tsananta bugawa da sauri yayinda duk wata gaba dake jikinsa ta dauki circulating , tsawon lokacin ya dauka a gurin batare da yasan takamaiman abinda yakamata yayi ba.

 da kyar yake iya fidda numfashi 'ahankali 'ahankali zuciyarsa ke raya masa abubuwa da yawa akan yarinyar gabadaya kwalkwaluwarsa takasa daukar abinda yagani ahalin yanzu .

 'Ahankali Ya runtse rikitattun idanunsa yana sake  jin yadda gangar jikinsa ke sauyawa. 

yakasa cigaba da kallonta idanunshi dake  rufe ya budesu fess akan CCTV camera 'tana nan dai tsaye kmr yadda yaganta tun farko sai dai yanzu hannuta  rike yake da towel 'tana goge santsar jikinta . 

Da sauri  yasa hannunsa yakashe CCTV dan  bazai iya cigaba da kallon Surar yarinyar, da a haife ,ya haifeta .


 Sannu ahankali ya dinga  sauke ajiyar zuciya  tare da fidda numfashi sama sama. jikinsa a sanyaye ya Mike tsaye yana kallon yadda ilahirin jikinsa yakoma , yayinda  joystick dinsa ke  sake mikewa  tsaye sambal....

Take  jikinsa ya dauki kirrrrrrma .
 rasa yadda zaiyi control din kansa ne Yasa shi    kamo lip's dinshi na kasa gabadaya ya datsesu da hakoransa.
"   ya dinga  tsotsarsu yana daya sanin kallon abinda ya tada masa da hankali yana zaman zamansa  .

 cikin sanyin jiki yakarasa ya bude wardrobe dinsa ya zaro jallabiya ya zira ajikinsa "sannan ya bar dakin zuwa na zeenat duk da  Bai shirya  zuwa gareta ba a yau amman ba yadda Ya iya  .
ya zaiyi da maseefar da tasameshi yau dolensa yaje gareta .


  ahankali yasa hannu murda kofar dakinta  yashiga ,Byn yayi  sallama  iya lebensa.

 zaune  ya sameta gaban  mirrow daure da towel tana  kwaliyar da tazame mata jiki " dan ko bacci zatayi sai tayi kwaliya  kmr maseefa . 

Kallo daya tayi masa tayi murmushi dan  tasan tabbas akwai abinda yakawo shi  , tunda taganshi     a irin wannan lokacin ,tasan abinda yake so domin jiya ba yau ba .

'Ahankali ta mike  tsaye  Cike da shaukin soyayyarsa , zuciyarta taf da farinciki ganinsa tare da sake kallon yanayinsa.

 waje  yasamu  ya zauna a gefen gadonta hade da lumshe rikitattun idanunshi yana jin yadda giyar sha'awa ke dibarsa  .

 'ahankali  Takaraso inda yake zaune  tare da  zama a gefensa har cinyarta na gogartasa .

 hannuta , ta kai  kan joystick dinsa jin  yadda take a mike ne  yasa ta sake tabbatar da zatonta dan haka bata wani  tsaya westing of time ba tasoma shafa jijiyar  tana lumshe idanuwa, shr yayi kawai  yana jinta .
Sai dai kwata kwata bai motsa ba  har sanda yaji ta daga jallabiyar jikinsa sama  tana cigaba da shashafawa kan  jijiyarsa zuwa  cinyoyinsa tana shafa gashin dake kwance a cinyarsa.

 gabadaya tasoma rudashi masa jiki   sosai jikinsa ya yacigaba da kirma   take ya sakar mata jiki.
hade da cizan gefen  lip's dinshi, kadan  ita kuma sai romancing dinsa take tana kokarin zare masa jallabiyar dake jikinsa shima zuwa lokacin gabadaya yagama  yafita haiyacinsa ,  cikin rawar jiki yasoma tayata cire jallabiyar.
 tayi  flinging daita gefe har da towel din dake daure a jikinta sai alokaci ya daura hannusa jikinta  yasoma juyata yadda ransa keso  .

duk da ba wai yana jinta  akasan ransa bane  Amman hakan bai hana shi yin abinda ke ransa ba domin yaba aiyanata da yarinyar ne.
"  kusan three hours ya dauka yana abu daya daita batare daya koshi ba . Byn  yagama tara mata gajiya  ne ya zare jikinsa daga gareta yakoma gefe yana fidda numfashi.
gabadaya gabobinta ciwo suke ,Dan murmushi yayi tare da runtse idanunshi.


'Ahankali tasoma kokarin mikewa tsaye  Dan shiga bathroom ta tsaftacce jikinta . ganin Haka Yasa deeni saurin   fizgota jikinsa ta zube akan bed ,Ina zaki nifa ban koshi ba ?

 , Zeenat ta saki baki tare zaro kananun idanunta . Ta karyar da kai kawai alamun gajiya. 

A shagwabe tace  wlh  my  hrt  nagaji da dayawa ne km gabadaya jikina ciwo yake.
Yanajin jin haka  ya hade rai kefa matsalata dake kennan rakin maseefa.

 kinawa mutun  irin  Haka ne zai Hannani  kara aure . Gabanta yashiga faduwa haba my hrt Ai duk abin Bai kai haka ba ok shikennan zo kayi duk yadda kake so dani .

A zuciye yace  A'a bana so ,kije  kireki abinki amman ki sani  bazai yiwu Na zauna dake kadai ba, wlh  tunda baki da juriyar  dazaki iya daukata ba ,  gara kawai naje na samu type dina inyaso  ke km kije  dagajiyarki , haba kullun sai kinwa mutun wulakancin akan halalinsa mtsssssss yaja tsaki . 
 Tare da  sake jin haushin nablah akasan ransa. domin  ganinsa duk karfin sha,awartace ta maidashi haka.
,   da bai kalli surar  jikinta ba may be da sha'awarsa  bata motsa irin Haka ba . ballanantana wannan Yar rainin wayon taga iyakarsa .
 'ahankali   ta matso kusa dashi  sosai  tana sake manne masa ajiki please my hrt karkayi fushi dani .

Yayi shr  kawai tare da dan matsawa  nisa kadan daita "ta sake matsowa sosai zata kai hannuta  saman fadaden kirjinsa dake cike da yalwar gashi  .
,ya juyo  a fusace  yana watsa mata wata uwar harara  may hade da mugun  kallo wanda yasa  zeenat sha jinin jikinta.

 muryarsa  a kausashe  yace meyye haka  cikin dakiya tace nima Bai  isheni bane . Yayi murmushin gafen baki sannan   yace ai nasan bai ishiki ba kema ,tsabar iskanci ne da iyayi yasaki cewa kin gaji .

Na hakura dake Ai Kinsa halina Bana son yauki.
Ta narke murya tare cewa please now I said am sorry.
 yakatseta Bana son damuwa  please..  ta tabe baki kawai  hade da zubawa kirjinsa idanu gashin kirjinsa a kwance luf luf..dasu  tamkar wani bby "ga nipply dinsa dake kewaye da gashi Wanda  suka sake kawata fadadden kirjinsa .

 yaja tsaki ganin yadda ta xuba masa ido ya Mike tsaye yasa hannu zai dauki short niker dinsa itama ta daura hannuta a kai ya kalleta a fusace yace ke.. bansan iskanci fa ko sa'an wasanki ne kinsa Allah  bazan zauna ina karar da rayuwata akanki ba   alhalin bakida wani   amfani a wajena ya fadi hakan yana nuna kansa da yatsan hunnansa .

 tasa hannu 'tana kokarin kamo  tafin hannushi da sauri ya buge mata hannu.
 ta matse hannuta tana yarfewa  saboda azabar zafin dataji ya ratsata. Tarasa yadda zata shawo kansa  take hawayen yasoma xuba daga idanunta ya juya zai karasa inda tayi masa jifa da jallabiyarsa da sauri ta zube kasa takama kafafunsa duka tana kuka tana rokonsa dan Allah my hrt  kayi hakuri kayafemin kuskuren danayi  wlh ba zan sake ba.
 ya juyo tare da daka mata tsawa yasa hannu ya tureta yace ki sake ma ina ruwa ,abinda dai  nasani ne duk lokacin dana so km n gadamar kara aure  zanyi ,ko  baki so .

 ta hada hannayenta duka biyu tana may  bashi hakuri tana kuka tace  dan  girman Allah kamin rai  karka kara aure. duk abinda kakeso wlh zanyi maka km daga yau nadaina nuna rakina .

 harara ya sake watsa mata mezakimin naji dadi a duniyar nan zeenat ko cikakkan   da kike zubar  ne zasu sani farinciki a rayuwarta ya girgiza kai  ,kisan Allah kanki kika cuta bani ba ya nuna kansa da yatsansa domin ni zan iya  kara aure km Na haihuwa a duk sanda naso.  Maganar kin daina raki ,Shima bazance ki daina ba ,nima Allah zai hadani da daidai dani, ke  gari  zai waya.

Yanzu ma killa kin   cigaba dayin family planning dinki ko..'cikin kuka tace wlh A'a banayi nima nemar haihuwar nake.

Ok ,kima yi kece zaki kwana ciki ai tare da   daga kafadarsa sannan ya dau jallabiyarsa ya zira ya bar dakin.

 kuka ta fashe dashi mai tsananin ciwo da cin rai hade dayin danasanin mara misaltuwa . 

Shi kuwa deeni  yana fita daga dakin Zeenat dakinsa na downstairs ya shiga  .


Washegari da safe 


  Nablah tashiga dakin Zeenat domin cleaning din part.

Byn tagama gyara  komai a tsanake ,ta dubi  Zeenat dake shirin fita 'cikin wata haddaden less mai shegen kyau tamkar ba itace ta kwana kuka ba .

,tace aunty Zeenat  nagama zan iya  wucewa  ko akwai sauran aikin da zan miki ta fadi haka ne sbd sanin halinta  ?  Zeenat Tayi banza daita tamkar bata san da ruwanta ba , ganin haka yasa nabla kama hanyar fita daga dakin .


A banzace ta juyo 'tana Kare mata  kallon Cike wulakancin da  ,  kaskancin.
  sannan tace  ,ke...baiwa dawo nan   nabla taki juyowa , ke Dan ubanki bada ke nake bane  daidai nabla ta daura hannuta kan handle din kofar  ta tsaya cak batare da juyo ba  , sai yamutsewa da zuciya Tayi ,taji da 'tana jin da 'tana da halin rama abinda   wannan bazanr matar Tayi mata da ta mata  zagin fitar arziki ,.
'ahankali Zeenat ta Tako har inda nabla ke tsaye ,Dan ubanki bada ke nake magana ba  ,nablah ta hadiye wani abu daya tsaya mata a wuya sannan ta zubawa Zeenat ido kawai batare da tace mata  komai ba .
 Tasa hannu ta damki wuyan nabla  Dan ubanki wasa nakeyi dake ,duk fa wani take takenki da karewa mijina kallo dakikeyi Ina sane fa. kallonki kawai nake sbd darajar ummi amman zaki gane kurenki duk randa ummi tabar gidan tajawo kiiiiii tare direta gaban wasu  , kaya ta watsar daita natsaneki kwata kwata bana kaunar Na bude ido naganki ,km kar Na sake ganin a tsakanina ko inda nake ,dauki kayan nan ki kaimin bedroom   dina Na kasa km ki gyara mishi  . 
Stupid kawai .
, nablah ta dinga kallonta tamkar  tana kallon wata halitta ce ta daban Ahankali take fidda  numfashi  tare da tmbyr kanta Anya Kuwa matar nan Nada hankali kuwa . me take nufi dani ? Sai da Zeenat ta buga mata wata uwar ashar sannan Nablah ta Mike tsaye yayinda.
  zuciyar  ke mata  zafi tamkar ta mutu ta huta haka ta dinga  jin zafi   a kirji.
  jikinta a sanyaye  ta dauki kayan rungume ajikinta ta bar dakin .
  Tana jan kafafunta bbu abinda takeyi sai kukan zuci Tare da jan tsaki a ranta ita kadai tasan halin kunci data tsinci kanta ciki lokaci da Zeenat ke xuba mata ruwan rashin mutunci.
Wacce irin mata ce wannan  ,ita komai zata sa mutun sai tayi ,Na marasa hankali da tunani  .

'Tana tafi 'tana jan tsaki tare da zagin Zeenat a zuciyarta  har ta shiga Bedroom din deeni batare da tasani ba.

 tana shiga dakin  Tayi jefa da kayan hannuta dayake akwai duhu Sam bata lura da deeni dake kwance  ba tawani  yuyi  'tana sake zagin Zeenat din a ranta , tare da cire hijab din jikinta  tayi  jefa dashi  kan bed suka fada  akan fuskarsa daga bisani ta nufi swich light   ta kunna wutan dakin haske ya gauraye dakin gabadaya  karaf idanunta suka sauka akan bed .

Deeni ta hango   kwance yayi matashi da  da hannuwansa duka fuskarsa na lullube da  hijab dinta datayi jifa dashi akan gadon.

 take ta zaro idanunta waje 'tana rufe bakinta da hannuwanta duka  jikinta ya dauki rawa tasoma ja da baya 'tana neman hanyar gudu .

 ahankali yasa hannu ya cire hijab din dake kan fuskarsa ya jefa mata batare da ya bude idanunshi ba .yafara magana cikin sanyi  murya sai kace mai koyon magana.

  hey what' are  you doing in this room ? in low voice  da in inna  tace I'm ... I'm sorry sir.. I made a mistake is aunty zeenat send me.
 common short up ur stupid  month  there I don't won't any excuse from you just parks ur stupid things and leave the room .. ..

atsorace tasoma tattara kayan jikinta na rawa ta bude kofar ta fice dan tsananin rudewa datayi yasa ta manta Inda zata dosa tabi wata hanya da daban wanda tunda tazo gidan bata taba sanin  ba . 
anan tasamu waje ta zauna tana fidda numfashi sama sama sai daga bisani ta Mike tsaye  ahankali   tasoma tafiya ashe hanya ce mai bullewa BQ   can ta hango laraba tana aikin shanyan kayanta .taji dadin ganinta Sosai.

 takarasa har inda take 'tana murmushin ganinta  dan gaskiya bazata iya maida kanta ainihin main falon din  gidan ba  .

 Laraba  tabar abinda take ta   zubawa nablah idanu kawai tace ke kuma daga ina haka naganki   wujiga wujiga ?

 nablah ta sake yin  murmushi tana may   boye tsoro dake tattare daita ,tace wlh aunt zeenat ce ta aikeni dakinta  so gabadaya ta rudar dani shiyasa ma narasa takamaiman dakin nata shine na biyo tana nan. amman bata sanar daita   tashigar dakin deeni ba .

Laraba  tayi dariya kai nablah yanzu dakin aunty zeenat din ne baki sani ba?
Nablah ta girgiza mata kai ok to  muje na nuna miki tare suka jero laraba  nata tsokanar nablah  doguwar tafiya  sukayi sannan taga sun shigo main parlour laraba  ta nuna mata dakin aunty zeenat na kasa  .
sannan ta juya  atsorace tashiga dakin taga komai tsab sai kamshin ke tashi takoina  ta lallaba ta ajiye kayan akan bed dinta da sauri ta gyra abinda abinda baza'a rasa ba Dan dakin bawani dirty yayi ba , tabar dakin  ta haura sama tashiga dakin ta dan can yafi mata saukin shiga akan takoma parlour .
 tana shiga.dakinta  tayi jifa da hijab dinta kan gado tasoma zance zuci wai garin ya'ya naje wannan room din    ahankali tasoma cewa gaskiya nagaji da zaman gidan nan dama area estate din gabadaya
 ya fitar mata arai.

 gashin tun zuwanta gidan sau daya suka yi waya  da auntunta basu sakeyin magana daita ba.
 mtssss taja tsaki  tace kai bazai ma yiwu ba wlh  yakamata zuwa yanzu nasan iya adadin kwanakin dazan rinka kai ziyara gida domin bazan iya daukar tsawon lokacin batare dana sanya yan gidanmu ba .

 inda munayin waya akai akai ne ,ma    da sauki.a muddin  bazata dinga commincating da yan gidansu ba bazata iya cigaba da zama dasu ba wlh .

Ta bangaren  deeni kuwa nablah na fita yaja tsaki ko uban me yarinyar nan tashigo yi a wannan part  din nawa "oho" bana jin natsani  mutun kmr yadda na tsani yarinyar nan Sam bana son ganinta a inda nake duk lokacin danayi arba daita sai naji  gabana yana faduwa ,take yaji zuciyarsa na wani irin dokawa da sauri.

 ya tashi zaune tare da jingina bayansa da jikin gadon ya runtse idanunshi  yana jin yadda zuciyarsa ke dokawa da sauri yayi shr kawai yana son yasan dalilin dayasa yake jin faduwar gaba a duk sanda yaganta ko ya tunata ..





MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO



Page 67


 Duk Wuni ranar a  tsorace nablah tayi shi acikin dakin  dan kwata kwata kin yarda Tayi ta sauko Dan  bata kaunar  abinda zai sa   ta hadu  , da daya daga cikinsu,   zeenat  ballanantana ta kaita da ganin oga  DEENI  .
 Yayinda Zeenat da ummi ma Sam     basu lura da hakan ba , sakamakon suna airport dauko safeena  diyar yayan  ummi daza tazo  hutu  daga India.  Km koda suka dawo ma  ummi bata lura da rashin saukowar nablah ba .

 
Sai da daddare  ne ma da  ummi taga bataganta ba ta aiko laraba  sannan ta sauko.
 jikinta duk a sanyaye ta rakube can nisa  da ummi  ,ummi dake kallonta tun saukowarta tayi murmushi tace zo nan nablah ta nuna mata waje  kusa daita. takaraso inda ummi tanuna mata ta zauna .

 ummi  tayi shr kawai  tana nazarin yanayinta sannan ta sake kiran sunanta nablah ta dago da idanunta dake Cike da kwalla  tana kallon ummi .

Ummi tace wani abu na damunki ne?
 nablah ta girgiza mata kai tace to yana ganki haka tamkar mara lafiya muryata a raunane kmr zata zubda kwalla tace ummi babu komai   .

 zeenat dake zaune a kujerar dake kallon ta ummi ta tabe baki sannan tace meke damunta kuwa  byn iskanci da alamun fa yarinyar nan bazata iya aikin nan ba gara ma tun wuri  ummi kibari a sallaneta  takama gabanta dan daganin....hannu ummi ta dagawa Zeenat alamun ya isa still idanunta nakan nablah din. cikin sanyi murya ummi tace uhmmmm nabla ko kina son ki koma gida ne kin fasa  zama tare damu ? 

nablah tayi shr ..taki cewa komai duk da abinda tafi kaunar  ji kennan  a maidaita gidansu gurin mamanta domin 'tana Cike da kewarsu .

   Safeena  dake zaune gefen ummi  tayi murmushi  Dan tunda ta daura idanunta kan yarinyar taji tashiga ranta ,tare da wata soyayya ta , musamman .
Ahankali  ta mike tsaye  takarasa har inda nablah take zaune a rakube  ta mikar daita tsaye ta maidaita kan kujerar data tashi ita kuma ta zauna gefen kujerar  .

ummi ta xuba musu idanu tana kallonsu hankalinta  a tashe domin bata son abinda zai rabata da yarinyar .km  still  batace komai ba , safeena ta kamo tafin  hannu nablah cikin nata   tace tasoma magana 'cikin harshensa turanci ta sunan nabla kmr yadda taji ummi takiranta dashi  abinda nake so dake nablah  ki saki ranki  dan Allah , mu fa tamkar  yanuwanki ne  ummi kuma tamkar uwa ce gareki dan haka duk abinda ke damunki ki sanar mana ko ummi   kinji dayake ummi tabata labarin nablah sai dai bata sanar mata ,matsayinta a gidan ba .

 nablah ta girgiza mata kai kin ci abinci ma kuwa inji cewar safeena nablah  ta daga  mata kai alamun taci, safeena ta sakeyin murmushi yaushe kika ci byn tun byn sallar isha'i muje  zaune anan .

  kuma ummi ta tambaye laraba  tace tun safe da kika sauko bata kara ganinki ba that means ko abincin rana  ma baki ci ba.
 aunty zeenat ta ja tsaki  tana mikewa hade da kallon safeena    tace kedai   tur da hali irin naki ke Sam tamkar baki san ciwon kanki ba ,  kin wani zauna kina biyewa mai aiki dan rashin aikin yi da shishigi safeena , ta dago anhakali  ta dubi zeenat  din sannan ta   bude baki zatayi mata magana, ummi ta dakatar daita dan haka taja bakinta tayi shr.

 ummi  ta zubawa zeenat ido kusan minti biyar sannan  tace zeenat ni zaki zaga ba safeena ba  tana mai nuna kanta da yatsanta  domin kuwa ita kokari take taga ta isar da abinda nake son aiwatarwa , wa ma  yasanya bakinki cikin maganar su ko kawai tsabar rashin mutunci ne ita mai aiki ba mutun bace ko jakar gidanku ce ?

 zeenat tayi tsit tamkar ruwa ya cinyeta  dan bata taba  tunanin ummi zata tsoma baki cikin maganar ba .

dan yawanci lokaci ko tanawa nablah rashin mutunci ummi  batasanya musu  bakinta ciki , dan haka tayi saurin xubewa gaban ummi tana batawa ummi   hakuri 

ummi tayi mata banza tare da juyar da  maida hankalinta ga TV zeenat    ta dan juyo ta faki idanun ummi   ta watsawa nablah  kallon banza sannan ta sake  matso kusa da ummi sosai tana mairaice murya ummi please now sai da tayitayiwa ummi  naci sannan tace mata ta shi komai  yawuce  ta mike ta  fice daga parlour .

 ummi ta dan juyo side din Inda   telephone  din parlour yake  ta kira dakin laraba  byn ta dauka ne tace mata takawo  abinci  plate daya.

  babu wani bata  lokacin sai ga laraba  tashigo hannuta dauke da plate din  abinci da ruwa hade da drinks ta ajiye akan center table safeena ta dau abincin ta mikawa nablah.

Nablah ta amsa cikin sanyi jiki hade cemata tagode ahankali tasoma tsakurar abinci tamkar tana cin magani ummi da safeena suka xuba mata idanu  kawai suna binta da kallo.
  " komai nata mai kyau km  a natse take yinsa gata da hankali da natsuwa kuma gashi  bamay son yawan magana bace  .

ahankali nablah tasoma jiyo kamshin turarensa  wanda ke rikita mata lisafi da sata  yawon jin kasala da faduwar gaba a duk sanda taji.
 tun kafin yashigo parlour  kamshin turarensa yacika koina .
 jin yadda  gabanta yasoma  faduwa har zuwan sanda yashigo parlour gabadaya sanye yake  cikin shigarsa ta koda yaushe matukar yana gida wato  wando three counter da riga  black wani lokacin kuma doguwar jallabiya .
  " kayan sunyi matukar amsar jikinsa   Ahankali yakaraso ya zauna kusa da ummi    yana lumshe idanunshi  tare da  cewa washi .

 ummi ta kalleshi  tace duk gajiyar ce haka ,ya daga mata kai kawai ahankali ya soma  bude idanunshi karaf  suka sauka akan nablah da ke rike da plate din abinci wanda tun jiyo kamshin turarensa Yasa ta tsaya cak  takasa cigaba da tsakura abincin.take gabansa yasoma dukan uku uku.

  yayi shr kmr na minti goma yana kallonta  sannan ya   dauke  idanunshi daga kanta ya koma   yana kallon safeena  dan bazai iya jurar kallonta ba  .

 safeena  ta gaishe dashi ya amsa mata yana tmbyr yadda ta sauka , safeena  ta Mike itama tare da  yiwa ummi sallama ta wuce dakin ummi   .

Parlour ya dauki shr Na tsawon lokaci  yayinda nablah tashiga tashin hankali .
duk da ummi dake  tsakaninsu hakan Bai hanata nata shiga rudani ba ,sai zagaye plate din dake  hannuta take  gabanta nacigaba  faduwa  ta Mike tsaye da plate din abinci a hannuta ummi ta dan kalleta kadan  tace har kinyi me nablah ..meyasa Sam bakison cin abinci kinsa idan salma tazo taganki haka a rame bazataji dadi ba .

shi dai DEENI  zaune kawai yake  idanunshi na kallon sama yaji 
  muryata a shagwabe 'cikin in inna  na....na..koshi ne.
 ummi  tace uhmmmm bawani koshi da kikayi 
ki koma kitchen kici abincinki hankali kwance kinji , nablah tace to.... Sannan ummi ta juyo  tana hararar DEENI  ya dan  juyo suka hada Ido da ummi  dan tasan zuwansa ne sarai ya hanata sakewa, .
yayi murmushi gefen baki yana tambayar me yayi da idanunshi kara gyara zama yayi yana kallon  each and every step dinta yana mamakin yadda take tafiya kmr an tsamota cikin ruwa haka kawai  ya tsinci kansa da kallon west dinta sakamakon dan dagewar da  hijab dinta yayi .
   da sauri ya kauda  kansa   gefe ummi ta bishi da kallo  .Tayi shr ta sake kallonshi da kyau tana nazarinsa sosai  tace     lafiyarka kuwa  duk naga kayi wani irin  .
ya dago rikitattun idanunshi yana kallon ummi dasu yace lfy.... Amman a kasan ransa cewa yayi   ina zanyi wani  lfy byn kun kawomin matsala gida  .
   ya sake kallon inda inda ummi take yace ummi zansha coffee ta tabe baki tana kallonsa yau kuma ni zan baka ina matarka kakirata mana ya shagwabe fuska haba first love ni yau naki nake so Sha , ashe  ko baka tashi ba ya dan gyara ,ya  kwanta  akan kujerar dayake zaune yace Allah first love  yau daga hannunki zan shan coffee  dan naga yanzu anason  amin kishiya alhalin Kinsa bason kishiya .
ummi tace mai zatayi ba dariya ba sai datayi mai isarta tukun ta danyi shr tana kallonsa tace ok ta inda zaka bulo kennan naga sai wani ji kike da wannan yarinyar  ya fadi haka yana  yatsina fuska tamkar tana gun Sannan  cigaba da maimaita zan sha coffee first love.
Ummi  tasan halin da nacin tsiya idan ya kafe akan abu dan haka ta mike ta hado ta Mika masa ya amsa thank you my  first love.
 tace karkada anything for you my lovely  son.

 ni zanshiga na kwanta Allah kuma yamaka albarka ya albarkaci rayuwarka da samu ya'ya masu albarka ya amsa da Ameen sannan yamata sallama shima ya shige dakin zeenat da cup din coffee ahannusa  
 
Koda nablah tashiga kitchen din ma kasa karasa cin abinci tayi saboda oredy cikinta ya tushe da yunwa tattara ta komai  ta ajiye sannan ta dawo tayiwa ummi sai da safe ummi ta amsa mata cikin sakin fuska .


Washegari tun misalin karfe takwas ta farka tayi wanka ta shirya cikin daya daga cikin jallabiyar datazo dasu rigar black colour ce anyi mata ado da Golding stone ta daura karamin hijab wanda kusan shine karami acikin hijabanta duk da bawani make-up tayi ba Amman she look very beautiful ta nemi gefen bed din ta zauna ta zabga uban tagumi zuciyarta cike da tunanin yadda zata fita saboda tana maseefar tsoron haduwarta da DEENI idanunta suka ciko da kwalla  jin karar bude kofa yasa tayi maza ta goge hawayen fuskarta ummi ce tashiga  jikinta sanye doguwar riga  tayi matukar yin kyau tamkar baita ce  ta haifi wancen miskililin  ba  .

me kikeyi a daki da har yanzu 
Baki fito kinyi breakfast ba ?
 Nablah tayi murmushi yake tace ummi yanzu nake so fitowa sai kuma gaki mikewa tayi suka fita tare tana kamala break  ta nufi babban parlour gidan ta zauna kmr dai yadda tasaba  ahankali ummi ta juyo inda take tace nablah har yanzu kin ki sakin jikinki sai wani dari dari kike nablah tayi murmushi hade da sunkuyar da kanta kasa kamshin turarensa na mat Hamilton ne ya cika parlour da sauri ta dago idanunta suka sauka kan kyakkyawan fuskarsa  yau ma cikin kakinsa yake hannushi daya na cikin aljihun wandonsa yayinda dayan hannu ke rike da file fuskarsa a hade Sam bbu alamun fara'a atare dashi kai tsaye ya nufi kusa  da ummi ya zauna kmr mai rada yace good morning first love  morning my son da fatan katashi lafiya  .
 lfy first , nablah  tace ina kwana batare da ta dago idanunta  ba , yayi banza daita tamkar wani kurma yacigaba da maganarsa  cikin sanyi murya yace yace first  ga wayan nan file din ki ajiye min ni zan wuce office domin yau ne zan ajiye aikina ,duk ummi tajisa sarai amman ta bata fuska takira sunansa  DEENI... ya dago yana kallon umminsa.. tace baka ji nablah tana gaisheka bane ?
 Ya yatsina fuska a wulakance yace lafiya sanin haliinsa da ummi tayi yasa batayi masa complain ba akan yadda ya amsa gaisuwar da nablah tayi masa.

 sai kawai itama tayi banza dashi ta hade fuska  karbar file din tayi  ta ajiye a gefenta, phone dinsa yayi ring ya Mike a sanyaye yanayin tafiyarsa     ta kasaita    da takunsa nashi wani ne ya fice yayinda afakaice nablah ke satar kallonsa . acikin zuciyarta tace banza mai girma kan tsiya  wannan da Allah yayi shi a gidan sarauta da  baasan iskanci da zai rinka tsulawa mutane ba .


zeenat ce tashigo cikin sauri  ta katseta ta hanyar kiran sunanta ganin har DEENI yabar parlour tace  karbi  ki mikawa my hrt  nasan haliinsa zai iya mantawa yasani a tashin hankali  cikin sanyi jiki nablah  ta karba file din tana mamaki shi, maseefarsa ma bata bar kowa  ba hatta matarsa ma tsoransa take ji tamkar mutuwarta   .
    sai byn da nablah ta karbi file din  zeenat taga wautarta na nunawa nablah  tsoron DEENI a filli , gaida ummi Zeenat  tayi , ummi ta amsa mata cikin sakin fuska kmr komai bai faru ba ta zauna nan gefenta .

Nablah na fita ta hangosa   a parking lot  direbansa ya bude masa mota shima soja ne sanye da kakinsu na sojoji zai shiga nisan dake tsakaninsu  zai iya wucewa kafin takarasa garesa  tarasa yadda zatayi ita ba iya gudu tayi ba ballanantana sauri sai kawai taja ta tsaya tana kallon bayansa  can har yashiga mota sai kuma taga ya fito, yasoma takowa alamun mantuwa yayi  kowani takun daga kafarsa daidai yake da bugun zuciyata gata tsaye hannuta rike da file ganin yakusan karasowa inda take tsaye  ne yasa tasoma tafiya  hango file din hannuta ne yasa yaja ya tsaya tacigaba da takowa ahankali DEENI dake tsaye zuciyarsa tamkar,zata buga  ta kama da wuta jin saitin tafiyarta cikin sanyi ya kara hassalashi ya tsani tafiyar sanyi jiki  har taku daf dashi  zuciyarta na wani irin dokawa saboda tsabar tsoro da hannu biyu ta miko masa file  yaki amsa ya zuba mata idanunshi kawai jin yaki  amsa ne yasa ta dago kanta dake sunkuye ta zuba masa shanyayun idanunta take suka ji  wani irin shock..... Alokaci guda tayi sauri maida kanta kasa kmr ta juya da file din jikinta har kirma yake sakamakon yadda idanunshi ke yawo ajikinta da karfi ya fizge file din.  hade murde mata hannu ta saki kara mara sauri ta dan masa   daga inda yake tana mammatsa hannuta    cikin zafin rai yacewa  captain A  sulaiman kai sule tsayuwar me kikeyi  yashiga ya zauna sit din baya ta tsaya tana binsa da kallo daga bisani ta nufi cikin gida zuciyarta cike da tsanar halayansa ace mutun tamkar azarailu bai bar kowa ba tana shiga ta tarar da ummi tana tawa aunty zeenat fada Amman dataga nablah sai ta canza harshe zuwa yarensu na India  ummi ta dan kalli nablah tace kin bashi file din ta daga mata kai , sannan ummi da aunty zeenat suka cigaba da maganar su wanda ita nablah bata fahimci komai ba .

zeenat ta kalli inda  nablah take ta watsa mata harara a fakaice batare da ummi ta lura ba dan hankalinta nakan TV itama nablah bata wani tsaya ba, dan tasan abinda kallon yake nufi ta fice takama gabanta.

 ummi ta Kira suna Zeenat .
 Ta Dan juyo ta maida hankalinta kan umminsa yakamata ace kin soma koyawa yarinyar nan irin abinci da DEENI  ke so ta Zeenat  zubawa ummi ido kawai  tana sauraronta ummi tacigaba saboda kinga yanayin jikinki ke ba ishashiyar lafiya ce dake ba sannan kinsa bayacin abincin masu aiki  cikin shagwaba tace ummi to ai itama mai aikice ummi ta girgiza mata.
 mai aiki ce Amman ba kmr su take ba zeenat bana jin dadin yadda ke da mijinki kuke wa yarinyar nan "da" nakowa ne  fa.
 ki duba kigani    haihuwa kike nema sama da sheka takwas kennan kina ganin idan ke akawa taki Yar haka zakiji dadi ?  zeenat ta bata fuska tace haba ummi ya zaki hada jinina da waccen mai kama da Yar sadaka yalla idanun tamkar na mayu ummi tayi murmushi Shine kawai dalilin  abinda kika tsani   Yar mutane .
  saboda kina ganin kmr tafiki kyau , kema fa kyakkyawace km first class zeenat tawashe baki tana dariya tace ummi shiyasa kullum nake kara  sonki dayawa , dayake ance kina da kyau ba, dan haka ki dan rinka sakarwa yarinyar nan fuska ko ta sake damu zeenat  .
ta dai amsawa ummi ne kawai Amman ita Sam bazata iya mu'amula da masu aikin tamkar wasu yan'uwanta ba ,km ko babu komai ita dai Tayi mugun tsanar yarinyar .

Uhmmmm.   nah wa oooooo madam Zeenat fear God 😍😍😍😍😍😍


MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI 
      💖💖💖
💗💗💗💗💗





AYSHA A BAGUDO





Page 68



Zaune  yake rigingine  a bayan mota ,direbansa Na tukasa Ahankali.

Yayinda  Kirjinsa ke  cunkushe dayawan  tunan tunane  iri iri. Wanda zuwa yanzu yasoma suspect din wani abu ne ke shirin faruwa da rayuwarsa.  Wanda a hakikanin gsky  bazai iya cewa ga takamaiman  abinda ke son ruguza farincikinsa ba  .

Kallo daya zaka masa a yan   kwanakin nan tabbatar da hakan sannan  ka gane  sansar  damuwa dake   dawainiya da rayuwarsa  .

 zuciyarsa ke rawa da raya masa abubuwa dayawa  a game da yarinyar dake zaune agidansa .

 a duk sanda zuciyarsa  ta motsa game daita kirjinsa ne ke wani irin bugawa da sauri  .

Yayinda , tunaninsa ke yawan barin gangar jikinsa zuwa  wani bagere  na daban.

 , don't believe what's actually  happened to  my hrt  yarinya tamkar wata aljana ko mayya  ta tsarke min kowani shashi Na  zuciya  da gangar jikina ,deeni ya fadi hakan  akasan  zuciyarsa yana may   furzar da wata iska  may Tumi .

Wit that thinking har suka  iso gurin aikinsa zuciyarsa fal... da damuwa .
" sule direbansa ne ya fito da sauri  ya bude masa kofar motar  yana may Sara masa.

 , DEENI Baibi takansa ba  yasoma tafiya 'cikin isa da takunsa Na takama...

 Duk wani abu dayakamata DEENI yayi ranar  domin   barinsa aiki yakamala da komai .

 Sai dai he fell some how akan aikinsa da zai  barin Wanda yataso da tsananin so tun ba ,yau ba .
 ,amman ba yadda Ya iya da rayuwarsa  dole yabar komai ya,mayye gurbin kujerar dad dinsa a halin yanzu Dan shi  yafi  komai mahimmanci a tare dashi .

 Duk  abinda yake zuciyarsa Na makale da tunanin yarinyar  ,Wanda yarasa dalilin jin haka. duk  yadda yaso  ya yakiceta a zuciyarsa hakan yagagara domin tunaninta kokari yake ya mamaye ilahirin santsar jikinsa ,what should I do now  to stop thinking about her ?  Ya tmbye kansa yana mai rantse idanunshi gam.
 
 'Yana Cikin wannan tunanin ne wayar faruk ta riske shi ,tare da katse masa damuwar dake shirin zautar dashi , Ahankali ya sauke  naunauyen ajiyer zuciya tare da bude idanunshi ganin sunan dake yawo kan screen din wayar yasashi hanzarta   daukar wayar  hade dayin  sallama .

Bangaren faruk kuwa byn deeni ya amsa sallamar deeni ,yace aboki kwana biyu shr kayi Sika's ba'a ganinka ,wayarka ma Haka .
  DEENI yace kai dai bari kawai wlh  abubuwa ne suka sani gaba da baya ,a en kwanakin nan amman Na  kamala da komai ,sai fatan alkhari kawai ,fk yace ok kana gida ne ?

Bana nan  Ina gurin aiki amman xuwa anjima kadan  zandawo ,  kazo gobe Ina son ganinka game da aikin da ,zamuyi start .fk yayi murmushi manager da kanshi kennan ..a she zaka saduda 'cikin sauki Haka .

  ,wlh ban dauka zaka iya barin wannan akin naka daka kwallafawa rai ba .

 mtssss  DEENI ya ja tsaki  dan takaicin barin aikin nasa sannan yace yanzu  ma kama tayi . Shiyasa da km  mahimmanci dad dina    dan bazai yiwu Ina kallo wahalarsa ta tashi abanza ba ,km ko bbu komai  su ya Mahmood da ya sulaiman suyimin  kokari sosai akan dukiyata . 

Suma zuwa yanzu suna bukatar taimako. F k ya numfasa sannan  yace Haka ne ,nan dai suka shiga hirar duniya .deeni yaji dadi hirar data wanzu a tsakaninsa da amininsa Dan kashe dari ta damuwarsa ta ragu.


Ummi  kishingide akan kujera a hadadden  parlour ,gidan  yayinda safeena  ke zaune kusa da ummi tana kallon zeeyword ita kuma Zeenat  tana chatting a phone dinta .

DEENI yayi sallama hade da shigowa parlour kai tsaye ya nufi kujerar da ummi take zaune ya zauna kusa da ita  hade da daura kansa a kafadarta yana wani narkewa sai kace karamin yaro ummi tasa hannu ta shafi sumar kansa cike da so da kulawa tace da alamun ka kwaso gajiya gashi inason zamuyi magana mai mahimmanci dakai .

take yanayin annurin  fuskarsa ta dauke ,   Yar fara'ar daya shigo da ita ta ragu  duk da Bai san takamaiman mgnr da ummi zatayi dashi ba . amman  hakan Bai hanasa  cewa karki damu dani, first love bana tare da wata gajiya bara nayi freshe up na dawo muyi magana ya mike tsaye  fuska nan tasa a hade ba yabo ba fallasa yana tsokanar ummi da fatar maganar da  zaki  min may  dadi ce km wacce zata sakani  farinciki.
   dan nasan maganar ummina duk masu mahimmanci ne da dadi sauraro yana gama fadar haka yasoma takawa   ahankali cikin sanyi ya haura upstairs.

 DEENI nashiga bedroom dinsa  yacire kakin jikinsa  ya rataye yasaka rigar wanka yashiga bathroom ya sakar jikinsa ruwa .

 byn ya fito daga wanka jallabiya fara kal... ya dauko  yasanya   tare da  feshe ilahirin jikinsa da turare may dadin kamshi sannan   ya fice daga bedroom .

ummi da  zeenat har safeena duk suna nan a zaune a inda yabarsu tun kafin ya zauna safeena ta sake gaidashi  ta mike tabar gurin yayinda  ita kuma  zeenat  tashige kitchen .

Shi km ya zauna  yana  maida hankalinsa kacokam gurin umminsa yace ummi Gani.

 tace eh naganka ai sannan  ta kira sunansa deeni....Ya dago rikitattun idanushi yana dubanta dasu batare da yace mata komai ba sai dai gabadaya ya tattara ilahirin hankalinsa akanta .

  cikin sanyi muryarta  kasa kasa ta yadda bbu mai jinta sai  DEENI din .... hakika lokacin yayi da yakamata   kasan abinda kake ciki domin zaman gidan nan shr ya soma gundurata.

 , zeenat ta dawo parlour'n hannuta dauke da cup din coffee ta Mika masa.

 wata uwar harara ya gallamata sannan yace  bazaki iya ajiyawa ba ko zaki  daura min akai ne ?

  zeenat tayi murmushi kawai domin  ita duk abinda DEENI zai mata baya damunta sai ma  sake birgeta dayake  karayi.
, Ahankali ta janyo karamin stole gabansa ta ajiye masa  ta sannan ta juya ta koma dakinta tacigaba dayin chatting dinta  ganin kmr suna bukatar abasu guri .

  ummi tacigaba   a dalilin haka kaso kakara aure tun ba yanzu ba ,Ga wannan yarinyar nayi bincike akanta sosai ,irin kalar yarinyar danake son ka aura ce .

  ganin maganar da umminsa ta dauko ne yasa shi  mikewa tsaye hade da daukar cup din coffee, din tare da sanya  hannushi  ya kamo na ummi yace ummi muje dakinki .

DEENI zaune a gaban umminsa  yayi shr, ya  hada  uban tagumi kawai yana sauraron maganar ummi ahankali tace   na baka iya lokacin da naga zan iya baka akan maganar yarinyar nan Amman har yanzu ka kasa aiwatar da komai muryarta tamkar maishirin zubda kwalla tace ko so kake na mutu batare danaga kwan ka adoron duniya nan ba .
gashi yarinyar nan nablah  tana da hankali  da natsuwa babban abinda yakara jan hankalina gareta kyakwan tarbiyya da take da ita
  ta kwanta min arai matuka fiyye da tunaninka ,dan haka kabari na dangana kaina  ga iyayenta kafin  mutuwata ta riske Ni  .

   da sauri DEENI ya zaro idanu yana girgizawa ummi kai. yayinda   gumi yashiga  ka karyo masa takoina ajikinsa, jin abinda umminsa tace  hannuwansa duka ya daura a sama fuskarsa  zuciyarsa ta taru ta hade kanta  waje daya ji ya ke tamkar jinin da ruwa basa gudana ajikinsa yadda yake so ..

ahankali yaciro hanky daga  aljihun gaban  rigar jallabiyarsa yana goge gumin dake tsaftsafo masa .

 ummi ta sake kiran sunansa DEENI ...ya amsa na'am first love idan kasan bakada abinyi da yarinyar nan kasanar dani na sallameta, taka gabanta.

Tun lokacin da ummi  tafara magana deeni yake kallonta har sanda yaji tayi shr   da zancenta. Jin abinda tace ne yanzu  yasashi  danyi murmushin gefen baki ,Wanda yafi kama Dana takaici .

  muryasa kasa kasa tamkar may shirin yin  rada yace ummi kina nufin auren yarinyar nan zanyi kennan? 

 Kwarai kuwa saboda nagaji da ganinka haka domin bansan har wani tsawon lokacin zaka dauka kafin burina yacika ba , duk sa'annin aurenka bbu wanda baida "dan" kansa,  akwai mai uku mai duhu acikinsu .
  tagama fadar haka ta xuba masa  ido kawai   tana nazarinsa sosai.
 yayi shr Bai sake cewa komai ba ,   Amman kasan tun farko sai daka amince da yadda Na  tsara   kafin a kawota ?

ya daga mata kai tace to meyasa yanzu kake son  min yawo da hankali kodan kaga a bukace nake da son ganin guda jininka shine ka maida zance Na wasa   ?

  ya hadiye abinda ya tsaya masa a makoshinsa   yakamo tafin  hannuta 'cikin nasa  yace kiyi hakuri first love  kin wuce wasa awajena duk duniya banida tamkar ki kece duniyata ,  na rokeki kada kiyi fushi dani.
  ,bacin ranki bakaramin babban tashin hankali bane atare dani.
 ,ya numfasa  sannan yacigaba Dan girman Allah kiyi hakuri ki  sallameta  kawai Dan  banji zan iya  aurenta yarinyar nan ba.
 saboda banasonta ban jin akwai halitar dana tsana kmr ta.tun zuwanta gidan  first love narasa natsuwata Ni kaina  ban san dalilin dayasa Na amince da zamanta a gidan nan  ba.

 ,ummi ta hade fuska sosai tace    sakar min hannu cikin sanyi jiki yasoma  sakar mata hannuta  kmr yadda  tace .

 Ummi ta xuba masa ido kawai tana dubansa Dan takaicin abinda yace , numfashi taja ta fitar sannan tace  son Na lura so kake ka bata min lokaci, Amman kasan  ba dole nayi maka ba tun farko kaine da kanka ka bukaci kara aure.

 ,km  yan aiki nawa aka kawo gidan  kafin ita kace basu maka ba.
 
   da kanka ka  amince da zaman yarinyar a gidan fa sannan yanzu zakace ga zance Ga mgn .amman bbu komai      haka Allah yaso dani daman can bazanga jininka ina raye   ba, takarasa mgnr 'tamkar mai shirin zubda  sakin kwalla.

 muryasa a sanyaye  haba first love  karkice  haka ma akwai hanyoyin da dama daza mubi gurin cimma burinmu ba lallai sai ta hanyar auren yarinyar ba.
 ,taya za'ace  kamata da matsayina da komai Na  bige da auren  kaskantacciya irinta . Ai da auren wlh nahakura Dana cigaba da zama da Zeenat haka koda bazamu taba haihu ba .

A fusace ummi ta katseshi ta hanyar daga masa hannu sannan tace angaya maka sbd jin dadi  ne kawai   , nake son kayiwa diyata kishiyar boye ,uhm kasani badan haka bane ,kai kanka kasan dalilina zanyi aikata hakan ne kawai a dalilin  farincikin diyarta    
 
  Dan haka idan kai zaka iya hakura da kowani irin auren Ni bazan zauna ba ,nan gaba diyarta tashiga tashin hankali akan rashin haihuwa ba .

 Ok first love yanzu abinda za'a yi ya,   sunkuyar da kansa kasa sosai saboda jin kunyar abinda  zai ce. cikin wata irin raunanniyyar murya  yace first love  me zai hana tacigaba da zama agidan a matsayin mamata kawai batare da an  daura  aure  tsakaninmu ba.


 ummi ta tsare shi da idanunta  'tana  kallonsa dashi sannan  tana mamaki jin furucinsa . tamkar wani mai tabin hankali . Ahankali ta dinga aiyana 
 kode dan nata yasoma shayeshaye ne batare da sanin ba.
 
"inda wani ne yatareta da wannan banzan mgnr  da deeni yasanar mata da bakinshi ,to wlh da  kotu ce zata rabata da duk Wanda ya fada mata hakan. Amman sai gashi,  da kansa yake kokarin  fayace mata  ya gwammaci aikata lafin zina akan , yayi auren sunna da yarinyar .

Gumi yakaryowa  ummi ta mike tsaye tana  furta kalmar innalillahi wa inna ilaihi rajiun  ...'tana 
ta sake kallonshi da jin takaici acikin ranta .

ganin irin kallon da umminsa ke jifanshi dashi ne  yasashi shan  jinin jikinsa tare da   sanin  ya tafka babban kuskure daya   sake ya fada mata irin wannan mgnr.

 Duke kansa yake    a kasa yana ladamar abinda ya fadawa ummi Wanda har Ga Allah  ba nufinsa shi kennan ba" shi dai yafada ne kawai Dan yarasa yadda zaiyi da ummi .

 Tsawon lokaci ,ummi Na tsaye 'tana binsa da kallon mamaki kana     tace wlh azim DEENI you really gave me double surprise .
sannan  km bani  kunya   daman can abinda ka ke aikatawa  da yaran mutane  a gari kennan....bansani ba?

shine Dan rashin tsoron Allah  yanzu  kake kokarin ka fahimtar dani    halin ka na boye.

Da sauri DEENI  ya dago yana kallon ummi da rikitattun idanushi dasuka gama rikewa suka dawo jawur tare da matso kusa da ummi  sosai, yana may girgiza mata kanshi  tamkar wani karamin yaro.


Ummi  tasa hannu ta dakatar dashi ..  kar ka kuskura kakaraso gareni deeni fatana  Allah Ya shirya min kai shirin addinin Muslinci first love Dan Allah kiyi hakuri wlh ba hali bane nida   katashi  kabar min dakina kawai bana son ganinka  a halin yanzu.

  ayau naji kunyar kasancewata uwa agareka ,deeni ban dauka haka zuciyarka ta gurbace  ba mayagun laifuka ba .
Kullun nake yabonka 'cikin kawayena da dangina .
,dana kimtsasaine kamule may daraja a 'cikin al,umma  ashe bansani ba yaudarar zuciyata da mutane kawai  nakeyi da kyawawan halinka .

Deeni     bai daddara da kashedin umminsa garesa ba .
  " yacigaba da karaso inda ummi  take yace dan  Allah first love ki  yarda  dani karki min mummunar fahimta wlh  bantaba aikata makamanci abinda na fada ba,  baya ga mamata ta sunna. Amman Ina neman afuwarki game da abinda nace.

 ummi ta  sauke ajiyar zuciya Ahankali 'tana godiya ga Allah duk tasan ba halinsa bane .Dan Tasha jin yadda mutane da dama suke yabonsa akan kyawawan halinsa duk .
 tasan irin kalar tarbiyar da tabawa "dan"  nata.sake sauke ajiyar zuciya Tayi ,Dan tasan ba'a shedar Dan ,yau .

 Ya kamo tafin hannuta wannan karon bata hanashi ba ,ya sake cewa Dan girman Allah first  kiyi hakuri nayi nadamar fadar haka kinji .Ya fadi hakan yana langwabar da kansa ,alamun Tayi hakuri.

   hakan da yayi ne Yasa taji tausayinsa aranta yana sonta baya son ganinta 'cikin fushi da rashin hankali Dan haka  ummi   tace to  Shikenan naji Allah Ya sake Kare min kai .
Take , yaji hankalinsa ya kwanta yayinda  jijiyoyin   jikinsa da suka tsaya cak suka  daina aiki  na w wuncin gafi  suka cigaba aiki tare da   sauke ajiyar  zuciya.
Sannan  ya numfasa tare da   juyowa    yasa hannu ya dauki cup coffee ya soma kurba Ahankali ahankali .
   muryar  ummi yaji   yanzu km sai  maganar  auren ko Dan gaskiya yarinyar 'tana abubuwa masu mahimmanci dazai sa a hada zuri'a daita  .

A frigice DEENI yazaro idannu waje  coffee daya kurba bai san lokacin daya hadiye da karfi ba.
  " ai ko ya sarke shi take yafara Tari kmr ransa zai fita ummi sai faman sannu take jero masa da kyar   aka samu tarin  ya tsaya ya dago rikitattun idanunshi da suka gama canza kala ya saukesu bisa fuskar umminsa .

 yanzu ummi bazata rabashi da zance auren yarinyar nan ba ya fadi haka a kasan ransa  yayi shr can kuma yafara magana ahankali yace ummi duk wayannan ababen da kika lisafa akan yarinyar nan nifa ba ko daya da yayi min bawai na kushe zabinki bane "  Amman  zan aureta da zumar samun  ya'ya daga gareta.
 Dan a halin yanzu  gara na zauna da zeenat kadai na karasa   rayuwata daita , yakarasa fadar  kmr zai yi kuka .

ummi ta gyra zamanta  ta riko hannushi tana  sauke numfashi  ka  amince aje ga iyayenta kennan ?
   muryasa a sukwane  yace  uhm Na amince zan aureta  Amman ba Sai kinje da kanki   nemar min  AUREN SIRRI ba...  da kaina zandangana Ga  iyayenta  tunda oready kina  da address din gidansu .

    Yacigaba a gsky  first love  zan dai aureta yarinyar ne  kawai badan Ina so ba Sai Dan farincikinki .
km taza zauna matsayin  matata  sannan ta haifa miki  yaran da kike kwadayi samu daga gareta batare da ita kanta tasan da zaman nine mijinta ba  Dan sanin nine mijinta zai sa naji some how..'yana gama furta haka yayi Mike yayi waje ranshi a bace zuciyarsa tamkar zata tarwatse tsabar takaici ,ummi tabi bayansa da kallo sarai taji  yace a karshe sai dai  bata fuskanci inda maganarsa ta dosa ba ta numfasa abinda yake nufi shiyasani damuwarta daya ce ya amince mata da auren yarinyar tunda ya amince ,mgn takare .







MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
     💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO




*Assalamu alaikum warahmatul  Allah  Ina wa duk masoya wannan labari Na auren sirri fatan alkhari .yayinda duk wani   korafe korafenku  yake isowa gareni kai tsaye batare da bata lokaci ba say day yana da kyau mu kula mu gane wani  abu shi manufar  rubuta labari karan kanshi ba wai dan nishatarwa bane da biyyyewa son ranmu . Muna yi ne dan fadakarwa da wa,azantarwa Ga al,ummu ta hanyar da mutun zai samu damar ya gyara kuskurensa .da km Wanda yake da akidar aikata mummunar aiki nasan dawaya masu kawo korafinsu masoya bagudo ne, domin kuwa kaunace Silar damuwarku har takai ga korafinku ya iso har inda nake .bazan iya misalta  muku tarin kaunata gareku ba. amman ina son Kusan wani abu kuna 'cikin  zuciyar  bagudo . Bagudo ni'feyi ju km inshallahu Muna taren tare har abada*🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻  


Page  69



Kai tsaye dakinsa ya nufa ya fada   kan royal bed dinshi ya kwanta flat yana fidda numfashi ahankali.  yayinda  , kyawawan idanunshi  suka gama  rikidewa  tamkar garwashi tsabar tashin hankali dayake ciki.
 why ...why ummi why did you want's to do this to me?
 ,meyasa zakiyi min Haka ummi  ?
Meyasa kike   kokarin son cusawa zuciyarta abinda bata so ?

,bana son yarinyar nan , Bana kaunar  ganinta asalima Na tsani  kusancina  daita   domin hakan na jifani 'cikin tsananin  tunani da rasa natsuwata.
" bazan iya bijere miki ba ummi ,to meyasa  kike so ki tursasani yin AUREN SIRRI da  kaskantacciya macce?

 tsawon lokaci ya dauka yana kwance idanunshi na kallon celing dakin  gabadaya  tunaninsa a halin  yanzu ya ta,allaka ne akan abinda ummi take son ya aikata .
   ,yana son umminsa bayason  abinda zai disashe farincikinta ballanantana har  yakai shi Ga bijirewa
 umarnita.bacin ran umminsa ,babban tashin hankalisa ne,a gareshi   bancin   haka da Babu  abinda  zai kaishi auran wannan yarinyar may idanuwa tamkar Na mage  .
" mtssss yaja tsaki a ranshi Dan   duk wannan zance dayake yi  yana yinsa ne a zuci .

ahankali ya runtse rikitattun idanunshi banda yana jin bacci Sai Dan yana bukatar maido da natsuwatsa dake kokarin  barin gangar jikinsa .



Bangaren nablah kuwa  gabadaya duk wata  surar dake  jikinta  ta sauya , ta  murje ta sake yin kyau daita  Sai dai  walwalarta da kuzarinta sunka ragu.
 sakamakon  matsi da takurar da Zeenat din ke yawan yi mata, Wanda ita kanta  tarasa dalilin hakan .
km kwata kwata  bata dauki takurar da Zeenat din kemata  amatsayin wani aibu ba .

Baya  ga tunaninta Haka wasu daga 'cikin masu arziki da manyan masu hannu da shuni  sukeyiwa marasa shi km  marasa galihu irinta .

 Duk da  yawan  takurar da Zeenat din ke mata hakan    bai hanata  samun farinciki da walwala daga gurinsu laraba da safeena ba . Dan haka  ta tattara Zeenat takurarta ta watsar a gefe tacigaba da abinda yakawota  iyakarta daita aiki Wanda tasan dolenta ne Tayi shi Dan abinda tazo yi kennan .


Ranar Saturday ' nablah  na zaune ita da safeena a main parlour din gidan  sanye take 'cikin doguwar rigar material may ratsin pink and  popul yayinda  jikinta ke  rufe  da dan karamin  hijab  kmr koda yaushe.

 babu kwaliyar komai a fuskarta kasancewarta ba ma,aboyaciyar son kwalliya bace da kalekalen zamani,  sai Dan Whit lip's din data  shafawa lebenta.

 ,rashin kwalliyarta   bai hana ainihin   sihirtaccen kyawunta fitowa ba.haka ma kayataccen fatar jikinta choculate  colour ta kwance luf.  luf..koda take sanye 'cikin ' hijab  kyawunta  bai boyuwa ba..
Sai dai fuskarta Tayi fayau ..wanda  ya nuna  alamun rama atattare daita km  hakan ya sake fidda asalin siffar halittata kyawun jikinta .

Yayinda kallo daya zakayi mata kaji farar daya  tashiga ranka Wanda dama tun asali Haka yanayinta  yake 'tana  da saurin shiga rai  duk Wanda ya daura idanushi kanta , da wuya kangata kaji bata tashiga ranka ba .

bbu kowa a gidan daga ita Sai safeena   shiyasa ma ta samu dama  ta dan  sake ta  zauna a parlour Dan bata manta gargadin da  matar gidan Tayi mata  ba . 


Ahankali suke hirarsu 'cikin harshen turanci ita da safeena 'gefe daya km hankalinsu nakan TV .


Salamarsa ce da wani  wanda batasan ko waye ba ,ta doki dodon kunneta Wanda hakan yayi daidai da faduwar da gaban yayi , Wanda km  tarasa dalili  .
dan Kusan duk sanda zata gansa ko jiyo sautin muryarsa Sai  ,gabanta yayi mummunar faduwa.

 Ahankali Ya karasa shigowa parlour gabadaya fk Na biye dashi a baya .
har zata dago idanunta da niyar kallon inda suke  tafasa.
 ta maida Hankalinta sosai kan TV dake aiki a parlour tare da amsa sallama aciki batare da ta dubeshi ba Shima Dan  sanin mahimmancin sallamar datayi ne Yasa ta amsawa.
  " Dan Tasha alwashin bazata km gaida shi ba tunda baya amsa gaisuwa.

 Fk  yakarasa shigowa parlour Sosai,ahankali  idanunsa suka , sauka akan nablah dake zaune  Kusan minti biyu ya dauka  tsaye yana kallon bakuwar fuskar daya gani  agidan ,yaso kwarai ya dauke kansa daga dubanta Amman ya kasa  yin hakan.
 ,a zuciyarsa yake tasbihi Ga ubangijin halitai  Dan  rabon shi daganin kamilalliyar macce mai tarin  kyau da kwarjini irinta ya Dade ,kai shi bai ma taba ganin ba .

 Gabanta ya tsananta bugawa da sauri  yayinda a 'cikin  jikinta ta dinga jin ana  kallonta km still har lokacin taki ta yarda ta  juyo bayanta  Dan  tasan deeni ne  tsaye .
Sai dake dubanta  Wanda bata sanshi ba  km tayin hakan ne  sbd gujewa kanta wulakanci daga gareshi .

 haka kawai taji ta takura a gurin takasa sakewa shanyayun idanunta dake kan TV ta lumshe gabadaya hankalinta baya gangar jikinta ta matsu  su bar gurin  ko tasamu natsuwar zuciyarta.
 , Amman hakan ya gagara samuwa  Sai gani tayi ma  sun samu gurin  sun zauna kujerar dake facing dinta   suna  cigaba da hirarsu.

 safeena ta gaishesu  suka amsa a tare  amman ita nablah  takasa bude bakinta  ta gaidasu Sai ma mikewa datayi tsaye  'tana gyara hijab din jikinta Tayi  hanyar step .

 fk yabi bayanta da wani irin kallo .yana tunanin ko wacece ita a kasan ranshi.shima oga deeni tun shigowarsa zuciyarsa ke kanta  Amman ganin yadda Tayi musu banza tamkar bata gansu ba.
, yasa zuciyarsa ta sosu kwarai   ranshi ya dinga baci , ballanantana da  yaga fk din  yayi mata kuriiiii da idanu yana kare mata kallon, hakan ya sake   hassala zuciyarsa   ,haushinta  tare da takaicinta suka taru suka  mamaye ruhinsa. 


'Tana shiga dakinta ta kwanta ruf da ciki 'akan gado tana sauke ajiyar zuciya wayyo.. wayyo.. Allahna wannan wacce irin maseefa ce take shirin ruguzamin rayuwa ?
meke shirin faruwa dani?

 hakika wani mummunar abu Na kusanto rayuwata da Al,amurana gabadaya.
 ,domin yawan faduwar gabar da nakeyi ta yiwa a tun sanda nazo gidan nan wanda narasa dalilin jin hakan .
Ahankali ta dinga maganar  zuci  da kanta batare tasani ba .

 Ahankali taji an bude kofar dakin safeena ce tashigo ahankali 'tana kiran sunanta .


Ya km Muna zaune Muna hirarmu zaki gudo daki ,kibarnk  Ni kardai ?

kefa Naga alamun zaman kadaici baya damunki fa Sai ma Naga kmr baki jin dadi ..

 nablah Tayi murmushi yaqe may tattare da takaici  kana tace wlh bbu komai safeena km bbu abinda ke damuna ,  kawai dai Ina son Na dan kwanta na huta  ne sbd Ina dan jin bacci ,kafin Aunty Zeenat ta dawo .

Ke dai ki fadi gsky ba wannan ne dalilin dayasa kika dawo daki ba . safeena ta fadi hakan 'tana kokarin zama gefen nablah ,  nifa  Sai Naga  kmr shigowar bros ne Yasa duk kika rikece kika kasa zama .

Nablah dake kwance taji gabanta ya sake  faduwa jin abinda safeena tace dan Haka  a sukwane ta Mike zaune 'tana bin safeena  da wani  kallon mamaki   .
 Muryarta a sanyaye tace  ko daya ba abinda kike  tunani  bane ,kawai day Ina bukatar natsuwa ne.

 to Dan me ma  zan rikece nakasa zama Dan Naga  yashigorsa .
Ni  karfin shigowata daki yana da nasaba ne da banason Aunty Zeenat ta iske ne a parlour,n sbd gargadinta gareni if not me zaisa Na taso sbd wani alhalin ba zamansa nake yi a gidan ba .


Me zai sa nataso sbd wani alhalin ba zamansa nakeyi a gidan  ba ...safeena ta sake maimaita  mgnr nablah a ranta ,har ta bude baki da zumar zatayi magana Sai  km  Tayi shr sbd wayarta data dauki tsiwa, ta duba screen din wayar tana  picking din call din 'tare mikewa tsaye   dan barin dakin .
 'Byn fitar safeena nablah tacigaba da zaman shr tare da   tunani iri iri Wanda Kusan    yawancin tunanin  Na ahlin gidan su ne .


Bangaren faruk kuwa nablah Na karasa bacewa idanunshi  ya maido da hankalinsa Ga deeni tare da tmbyrsa wacce wannan yarinyar may zafi Haka ?

Wani kallon wulakancin may tattare da haushi  deeni yajuyo   yana watsawa  fk tare da jin takaicin tmbyr da fk din yayi masa.
 ,  kallon gefe ido Shima fk  yayi masa kana yacigaba ,dan Allah a Ina ummi  tasamota ko tare da safeena suka zo ?

Deeni yayi masa banza tamkar bashi da yake ba ,kai dan banzan yaro ne wlh wani lokacin kana jin mutune kake nakkasasu. Zuciyar deeni  gabadaya tagama cakudewa ta cure kanta guri daya 'ta daina  kai kawo a gangar jikinsa.
 tarasa sukunin  kanta kai kawo   tsabar takaicin fk .

Sai da fk yayi ta maimaita tmbyrsa sannan deeni ya furzar da iska may zafi  ta bakinsa tare da harde hannuwansa guri daya  a fadadden kirjinsa  ya fara mgn 'cike da  dakewa da yatsina fuska yace housemaid din ce ....

fk ya ware iduna yana kallonsa da gaske   kai amman  gsky yarinyar batayi kama da housemaid ba wlh. wannan Ai kamata yayi ace 'tana aji 'tana daukar darasi domin karatu ne yafi dacewa daita .
,deeni ya gyara zamansa  yakoma  rigingine akan kujera dayake  yana sakin ajiyar zuciya tare da yin shr ....tsawon lokaci fk Na zaune har ya fidda ran deeni zai sake yin magana Sai km yaji sautin muryarsa a sanyaye  ,sanadin karantu ne yakawota aiki .
Fk ya saki murmushi sannan yace ayya ..itama tasan abinda yafi dacewa daita kennan. 
to me zai hana ka taimaka mata kamay daita Ga iyayenta sannan ka dauki nauyin karatun nata kmr yadda kasaba taimakawa   mutane marasa galihu irinta .

Tsab deeni dake zaune yana  sauraron bayanin fk yayi masa kallon baka da hankali 'cikin sarkamewar zuciya da rashin tsoro tare da jin zafi furuncinsa   deeni yace baza,a takaimaka mata ba.
Yacigaba , wannan bazanr yarinyar da bata da tarbiyya zan dauki nauyin karatunta" yarinyar da  kwata kwata batasan me ake Kira da  respect ba kana kallon yadda ko kallon mutunci bamu isheta ba ,Ni wlh haushi ma kabani da naga yadda  ka tsaya kana kallonta tare da  zuzuta  wani wai kyau gareta  ko me mtssss yaja tsaki .

fk ya kwashe da wata uwar  dariya   matsalata da kai kennan idan baka son mutun ,wlh har naji yarinyar tabani tausayi .
Mtssss deeni ya sake jan tsaki .

Tabaka tausayi ko to ka dauki nauyin karatunta man ,Ai kaima Naga kana da karfin dazaka iya  yin Hakan.
 Fk numfasa tare cewa waneni wannan Sai Ku manya ..nan dai suka bar zance nabla suka shiga abinda yakawo fk.



Wasa wasa rayuwar  deeni gabadaya tasoma canzawa 'acikin yan watanni nan.
 rabonshi daya samu natsuwa da farinciki har ya manta tun kafin zuwan nablah gidan.
Dan  duk sanda zai hadu da yarinyar Sai yanayinsa ya sauya hakan ma ko 'cikin baccinsa ita yake ganin zaune a gefen tare da wasu kyawawan yara tana Miko masa" masu tsantsar kyawu sosai har kagara yake gari ya waye ya daura idanunshi akanta .yanzu kam yasoma gasgata tunaninsa na mayya ce yarinyar idan kuwa ba Haka bane to 'tana da alaka da mutane boye.😍😍



Sannu ahankali sule direbansa ke jansa har xuwa , unguwar gatan kowa dake iyanu - paja .



Nisa  kadan da gidan da oga deeni yabashi address sule  yayi parking ahankali  tare da juyowa baya  yace may gida mun iso Ga gidan can ya karasa fadar Haka yana nunawa deeni gidan da yatsansa .


Deeni dake hakemce a bayan mota ya sake gyara zamansa yana karewa gidan da sule direbansa ya Nuna   masa .
,tsawon lokaci deeni ya dauka yana kallon gaban  gidan tare da Allah wadai da wannan aure da zaiyi.

 yanzu irin gidan da zai nemi aure kennan  gabadaya kofar gidan a rushe yake bbu wata ishashiyar katanga Sai dan kwanun da,aka   zagaye shi dashi tsabar babu . Gabadaya unguwar a hargitse take bbu kyan Gani .

 Ahankali kalaman umminsa ke dawo dashi 'cikin duniyar tunaninsa yayinda  natsuwarsa ke kokarin shirin  barin jikinsa domin gabadaya tunaninsa ya ta'alaka ne da yadda zai nemi auren yarinyar a gurin iyayenta. Yanzu shi wani irin aure zaiyi ?Anya kuwa zai iya auren .

Tunda sule direba yayi mgnrsa ta karshe Bai sake yunkurin cewa uffan  ba Dan gudun maseefar ogan nasa ,a sukwane sule yaji sautin muryarsa 'cikin kunnenshi fita kayo min sallama da may gidan  iya abinda deeni ya  fada kennan yaja bakinsa yayi dif...


Sule ya kashe motar Tare da barin AC motar a kunne ,ya fito yana   aikin raba Idanu ta inda zaiga yaron aike .

    unguwar shr... sakamakon ruwan saman da,a kwana ana sulawa ,jifa jifa mutane ke wucewa Sai da sule  Bai yi  dacen samu Wanda zai   aika 'cikin gidan ba .
dan Haka ya koma ya jingine jikinsa ajikin mota yana addu'ar kar Allah Yasa oga ya fusata har zuwa sanda zai samu dan aike .


Fitowar wani kyakyawan  dattijo ne daga gidan yasa sule  jin farinciki a ransa  yayinda  hankalinsa ya kwanta  💯.

Dattijon dake kokarin gefta shi  yana  faman xuba  fada ,sule ya karaso da sauri Tare yi masa  sallama    yana kokarin tsugunawa dattijon yayi saurin Miko  masa hannu suyi musabaha.

suka gaisa sule Na tmbyrsa ,dan Allah baba may gidan daka fito daga 'cikin sa nake nema , dattijon ya saki murmushi Tare cewa Ai nine may gidan .

Sule  yayi murmushi yace yauwa daman may gidana ne yake son ganinka yana 'cikin wacce motar dattijon yabi hannun sule da kallo galleleyar motar dake parke nisa kadan dashi yabi da kallo.
Yace to to yaro bbu komai kana iya sanar may gidan naka Gani .


Sule ya juya 'cike da natsuwa ya sanar da deeni ,dake hakemce abayan mota ya ware kafafunsa yana jiran tsammani .
Ce  masa yakaraso nan .

Sule sake koma yasanar da dattijon.
 , dattijon Bai wani damuba yakarasa kai tsaye  har inda motar take sule bude masa sashen da deeni yake ahankali idanun deeni suka sauka akan mutumin dayake kallo yanzu a gabansa  tamkar an tsaga kara da yarinyar dake zaune a gidansa  .


Dattijon ya Mikowa deeni   hannun domin su gaisa deeni ba Dan son ranshi ba  ya  bashi hannun Sai dai fuskasa a dan sake ba yabo ba fallasa .

Yace idan bazaka damu ba kana iya shigowa daga ciki  magana ce may mahimmanci takawo gareka .

Dattijon yace bbu wata damuwa  yashigo mator batare da an rufe ba  Sai da deeni ya numfasa zai mgn sai km yayi shr 'yana may  toshe hancinsa da hanky  sakamakon wani wari kwata  daya bugu yayi nasarar shiga hancinsa  .ganin Haka Yasa dattijon janyo kofar motar ya kulle .sannan DEENI yasa samu damar soma mgn. 

 abinda yakawo gareka  Naga wata yarinyarka ne  Ina son ka aura min ita bisa sharadin deeni  yasa hannunshi yajanwo wata yar karamar jaka may shake da kudi , ya bude zan mallaka maka fiyye da  wannan kudin ..

dattijon daya Ga jiya km yaga  yau  ya kalli kudi masu tarin yawa sannan  ya dago ya kalli deeni  yana murmushi .
Kwata kwata kasa dauke idanunshi tsohon yayi daga kallon DEENI Sai ma nazarinsa da yake .


Kusan minti goma yana nazarinsa har DEENI ya tsargu kansa sannan dattijon yace yaro kennan wacce daga 'cikin yaran nawa kake so da aure  kafin aje ga mgnr kudi.
   bbu wata shakka ko tsoro deeni yace nablah....

 dattijon yace garama datazama  nablah ce Yar albarka duk  da inajin haushinta a raina   amman hakan ba zai sa nakasa  ji dadi aurar maka  daita ba .

Deeni ya sauke naunauyen ajiyar zuciya jin abinda tsohon yace hakan  ya tabbatar wa kansa samunta bbu  wani shamaki sai dai yayi mamakin yadda dattijon yace yana Jin haushin diyarsa ta 'cikin  . 

Dattijon yacigaba Sai dai ita wannan yarinyar da kake magana akanta bata nan , asalima ban san inda take ba ahalin yanzu  ,deeni numfasa sannan yace wannan ba zai zama da wata  damuwa ba muddin   ka amince zaka bani aurenta.
 ,nima tafiyace a gabana  zuwa wata kasa ,dan Haka auren kawai nake da bukata a daura inyaso idan Na dawo daga tafiyar  sai  ayi bikin kaga  itama nasan  zuwa lokacin    ta dawo .

Dattijon yaji dadi mgnr Sosai daman yana   'ciki  da abinda Salmah Tayi masa Na daukar masa yarinya, takai gidan aikatau 'byn yace Bai amince akai masa ita aiki ko Ina ba.
 ,yanzu hakan ma daya fito daga gidan  yana fada.
 " shi da Salmah ne yake ce mata ta dawo masa da diyarsa muddin batason bacin ranta ,  dan shi baya wani bukatar Taje  neman kudin  karatu yafi son ta zauna agabansa har zuwa  sanda zai aurar da abarsa .

 Ahankali dattijon ya dawo daga duniyar tunani daya lula yace yaro zuwa yaushe kennan kake son auren nata  .

Deeni yace   idan zai yiwu ayanzu Ma zan fi so Haka  dattijon yace  may zai hana yiwar hakan wannan Ai abune may sauki  tunda Sai ka dawo daga wata uwa duniya za'a yi bikin .

 Deeni yayi shr kawai yana kallon dattijon dake zaune Kusa dashi yana  kokarin amince masa batare da yasan ko shi waye ba .


'Cikin mintina da basu fi talatin ba mlm salisu ya nemo aminnansa guda hudu na nan  kusa da cikon shi biyar .

Sai  deeni da sule aka daura auren nabeela salisu gulunbe  da nasuruldeeni aliyu khaliyal    bisa Ga  sadaki naira duba dari cassssssssssss. Wanda sule yakasance wakilin deeni yayinda wani aminin mlm salisu din ya zama wakilin nablah . 


Sule yaji  mamakin wannan auren daka daura abu kmr a al,mara to daman   ogansa aure  zaiyi batare da sanin kowa , to wannan  wani irin aure ne Haka .

Byn angama daurin auren deeni ya mikowa mlm salisu jakar kudin amman mlm salisu  yaki kabar sai ma cewa da yayi nasuru ka rike kudinka domin  bbu abinda zanyi dashi .

duk da bansaka km   bansan daga inda kazo neman  auren diyata ba  Haka kawai naji Na amince nabaka auren nablah Ni kawai abinda nake bukata daga gareka shine ,idan Allah Yasa kadawo daga tafiyar dazakayi lfy kasadani Ga danginka  amman bazan karbi kudinka ba .

 Wani irin kunyar dattijon ne yakama DEENI yaji tamkar kasa ta bude ya netsina ciki dan kwata kwata baiyin tunanin dattijon zaiki amsar irin wannan kudin ba .a wannan zamanin da ake ciki,  na kaka nakayin.
 da wuya kasamu irin  dattijon duk da alamun  bbu dayake hangowa atattar dashi  muhalinsa kadai yaisa ya tabbatar wa mutun yadda yake gudanar da rayuwarsa.

  Haka kawai   deeni yasamu kanshi  da kiran dattijon da baba ...  dan Allah karkayi min  Haka  kar kace baza karba kudin nan ba 

Da farko nayi tunanin bazaka amincemin da aurenta bane 'cikin wannan lokacin danafi bukata  shiyasa kaji na daura sharadi akai .

Amman  yanzu  dattakonka gareni yafi karfin wannan kudin .
 dan Haka har ga Allah Na baka wannan kudin idan ma kana bukatar wasu zan karaka maka ..

mlm salisu yace Sam bazai karba sai wani abokin mlm salisu din yasa baki sannan  yasa hannu ya amshi jakar kudin Tare da   sanyawa deeni albarka .

  daman km  yana da bukatarsu. Sukayi sallama da zumar Sai Allah Ya dawo dashi ..


Mlm salisu Yashiga gidansa cike da murna yana duban Salmah da nurat Sai mahafiyarsu dake zaune suna tattaunawa akan batun nablah din .

Yakarasa shigowa yana murmushi Tare da ajiye musu jakar kudi a gabansu ya zuge.

 Kudin suka bayayyana bbu Wanda Bai ji tsoron ganin kudin ba sbd tsabar yawansu .

Mlm salisu yace 
Ku duba kuga ikon Allah sanadin diyata nabla Yar albarka Na samesu suka shiga dubansa da alamun tmby a saman  fuskokinsu .

, yacigaba yanzu nan Na daurawa nablah aure da wani mutumin kirki dayazo neman aurenta km shiya bani wannan kudaden da kuke Gani .

mahaiyarsu saratu wacce suke Kira mama  tace wacce nabeela kake mgnr ka daurawa aure .

,Ina da wata nabeela ne byn diyata ,ita din aka daurawa aure yanzu.
 gama sadakinta nan ya fidda wasu kudin .

Mama tace ,cewa zakayi  kasiyar min da yarinya kawai bawai ka daura mata aure ba  amman abinda zai sa hankalina ya kwanta sanin inda nablah  take a halin yanzu .
Dan haka  duk ma Wanda kabawa aurenta kabashi gaibu . Ka dai daura aure dashi ne Amman bashida mata .


 Mlm salisu ya hade rai Ke dai kika sani Yar Bakin ciki  kawai Ai ba tun yau nasan bakya son cigaba Na . Yau dai tawa ce to Na aurar daita Ga Wanda nake so km kina zaune za'a yi bikin nablah  ta wuce gidan aurenta .

Duk magangun da mlm salisu ke yi mama   Tayi shr batare da ta sake cewa komai ba sbd alamun da Salmah Tayi mata Na kar tayi mgn .

Ke km Salmah mlm salisu ya kanta  wlh wlh kinji ransuwar muslimi kwana biyu kacal nabaki  ke dawo min yarinyata may kan sa'a da kan arziki kafin nasoma cin uwarki ,dan wulakanci ke kina zaune a gidan mijinki lfy Sai  tawa Yar  ce ta iya zuwa neman abin duniya ke kar ma Na sake ganin kafarki a gidan nan muddin ba da nabeela bane shasha banza dabatasan ciwon kanta ba  yaja tsaki yana kokarin shegewa ciki kuryar  da jakar kudinsa . Gabadayansu da idanu suka bishi da shi hankalinsu ,a tashe.



Kirrrrrrrrrr... kirrrrrr ......kirrrrrrrr... karar bell  ya cika koina a gidan.
 nablah dake tahowa  daga kan  step ta hanzarta saukowa da sauri  ta nufi Bakin kofa ta bude .

Kabiru  may wankinsu Zeenat ta Gani tsaye a 'bakin kofa  yana sakar mata murmushi itama murmushi Tayi masa tare da gaidashi.

Daidai lokacin da motar deeni tasanyo kai 'cikin estate din idanunshi suka sauka akan nablah fuskar nablah  dake sakarwa kabiru murmushi .
take annurin dake fuskarsa ya dauke gabansa ya daki uku uku ya  fadi yayinda  zuciyarsa tashiga aikinta data saba wato dokawa da sauri  har sanda sule yayi parking motar  idanunshi nakansu yakasa daukewa.

 mlm nablah kennan ya gida da aiki inji cewar kabiru .
Nablah tace duk  lfy wlh ya naka aikin  Shima ya amsa mata da lfy suka shiga  hirarsu  sama sama dashi sbd sun dan saba  .

Kusan minti goma deeni yayi , zaune a mota ya kasa fitowa sakamakon dokawar da zuciyar takeyi da sauri ya dinga jin tamkar ana masa wanka ne da tafashashen ruwan zafi ne ajikinsa  yayinda natsuwarsa ke kokarin barin gangar jikinsa take gumi ya rufe shi takoina ajikinsa .
ahankali ya ciro hanky daga aljihun gaban rigarsa ya goge gumin dake tsaftsafo masa batare da ya sauke idanunshi daga kallonsu ba har zuwa sanda yaga kbr ya Miko mata kaya a wata jaka ya juya yana sake yiwa nabla  murmushi .
Wanda sauran  kadan zuciyar deeni ta tarwatse tsabar frigici  .
Ahankali yasoma kokarin fitowa daga mota byn sule ya bude masa .


 'Tana shiga gidan taje ta, ajiye kayan a inda tasaba ganin ana ajiyewa sannan  ta nufi  kitchen tasoma  aikin girki hade da wanke kayan da akayi amfani dasu, kasancewa yau Sunday ce.
 Laraba tana church ummi kuma sun fita tare da aunty zeenat da safeena ba yadda ummi da safeena   basu daita akan tazo su fita tare  tace   A'a saboda  ita bata damu da yawan fita ba ko agidansu.

  cikin sanyi jiki take aikinta da  zeenat ta gama koya mata kalar abinci da mai gidan yafi son cin ne yau aka bata    practices dan  aga yadda kwarewarta  tayi.

 kamshin turaren mat Hamilton 27 datashaka ne  ya haddasa mata faduwar gaba Wanda tun safe take jinta Haka .

  DEENI tsaye abakin Kofa kitchen din yana aiko mata da kallon tsana  byn yaje yayi freshe up .

'Cikin  tsananin tsoro da fargaban abinda zata Gani  ta juyo karaf idanunsu suka sarke cikin juna take zuciyoyiinsu ya bagu... gabansu Yashiga faduwa .
 da sauri tayi kasa da kanta ta dinga  karanto duk wata addu'a datasani  na  neman tsari .

Ahankali  ya tabe bakinsa   yakaraso cikin  kitchen   din  Sosai .
  "cikin muryasa may matukar dadi da sauraro  yace ke..uban me kike Jira da har yanzu baki gama abinci ba .

wani irin shock...ne yajata ,jikinta yasoma sheking  takasa furta komai ya daka mata wata irin razananniyar tsawa ke ..
Ba magana nake miki ba yakarasa maganar cikin kunar rai .

 "muryarta na rawa tace dan Allah kayi hakuri wlh  nakusan gamawa yace you are very stupid dake da gamawarki  kina tunanin an daukeki aiki ne dan kidinga yiwa mutane  iskanci da aikin ba'a kan lokacin ba.

 mamaki hade da tsoro sukayi nasarar lullubeta ko kwakwarar motse gagararta yayi .

 yayinda haushinta ya sake turnuke wuyan DEENI a harzuke ya fizgo hannuta yace  ke me kike takama dashi ke waye ma ubanki duk fadin Africa da har zandinga miki magana kiyi banza dani tayi kokarin fizge hannuta sai dai kashi ...ta kasa   abunku ga soja.
 gata yarinya karfin su ba daya ba , ko namiji DEENI yarike da wuya ya iya kwatar kansa.

 ranta ya baci matukar dan haka itama  fusace tace dan  Allah malam ka sakar min hannu .

kallon baki isa ba ya watsa mata sannan ya sake matse mata hannu Sosai  yana kallonta cikin tsigar wulakancin hade da sake damke laulausar fatar  hannuta.

 yace ki kwace hannu  mana idan kin isa ,  tasoma girgiza kai dan wani irin radadin azaba da takeji acikin kashin hannuta .
tayi kasa da kanta 'tana  zubda hawaye tausayin kanta domin ita takawo kanta cikin wannan maseefar datake ciki.

ashe rabon wahala ne yakawota gidan batasani ba .

 sai da yaga ji dan kansa sannan ya wurgar da hannuta nata da karfe ya juya  cikin tafiyarsa ta kasaita da jan hankalin duk wanda ya kalleshi.

 minti  goma kacal na baki kigama sannan yakarasa barin kitchen.
 ta durkusa kasa tare da  fashewa  da wani matsanancin kuka tasoma datasanin zuwanta aiki uguwar lekki ,da kyar ta iya  mike.

 tacigaba da aikin girkin hawaye nabin kuncinta sai da ta kammala da komai ta shirya akan dening area sannan tazo ta wuce ta gabansa yana kwance a kan three sites hannunsa dafe da kirjinsa har tayi step  daya zuwa uku tajiyo  shigowarsu ummi ta dawo  ahankali hade dayi  musu sannu da zuwa .

 ummi  da safeena suka bita da kallo byn ta amsa sannan  ummi tace ya naganki haka wani afrigice afrigice   nablah  ta kirkiro murmushin dole tace bbu komai ummi .

Amman naga idanuki kmr kinyi kuka cikin sanyi murya tace uhm ....dazo ne danake aiki wani abu ya fadamin a ido .

ummi tace ok sannan ta juya  gun  zeenat dake zaune kusa da DEENI tana tambayarsa ko yaci abinci  .
a harzuke ya bude idanunshi tare da watsa mata harara sannan ya juya mata baya please i don't won't any  distoping  ... now.


Zeenat bata daddaraba Ta sake tmbyesa kowani abu Nadamunsa ne . Zeenat.... yakira sunanta why are you distracting my hrt ... tace sorry  Tare da  mikewa  tsam tayi dakinta gudun kada ya wuce akanta duk da batasan sanadin fushin nashi ba.

 nablah dake tsaye kusa ummi dan oready safeena ta bar gurin  tace  bari nima na bace daga nan .

dan abinda nablah tayi noticing daga deeni  hatta  matar aurensa   ba raga mata yake  ba.
 ,Ina Ga ita bazanr bazara dan Haka  ta zame ta gudu dakinta  tabarshi da ummi .


Ummi ta zauna gefensa tana tofeshi da addu'oi  tarasa wani irin zafi rai ne haka ke damun dan nata abin fushi dama wanda bana fushi ba duk yi yake.
 tsawon lokacin yana kwance har sanda yaji kiransa daga masallaci dake 'cikin  gidan ya mike a sukwane  ya dan kalli ummi kmr zaiyi mata murmushi sai kuma ya fasa ta kira sunansa ya dago batare da ya amsa ba Kaci abinci ?

ya yasina fuska har dimple dinsa na lotsawa dan haka tagane bai ci ba .

da hannuta ta nuna masa alamun  yakoma ya zauna .
da kanta taje  dinning  ta bude kulolin abinci taji kamshin ya bugi hancinta ta zubo masa abinci takawo masa har gabansa.
Tace oya ci abinci  ahankali yasoma motsi  bakinsa first love  nifa bazan ci wannan jagwalgwalon yarinyar nan ba ummi ta koma ta zauna inda ta tashi ta hade fuska tamau takiyin magana sai idanu data zuba masa 'tana kallonsa .
 dan  haka yake wani lokacin idan yana cikin fushi dayaga ta hade rai  sai kaga yasoma shiga taitayinsa dan HK  ya dan sake fuska kadan  yasoma cin abinci yana kai lomar farko yaji kunnenshi ya dan sheking yasa hannunsa yana tsosa gun wasa wasa dai sai da oga DEENI ya tashi da Rabin plate  sannan ummi ta sakin ranta tana masa dariya tace har ka koshi kennan da dai  kakarasa cin jagwalgwalon mana shegen salo da iyayi kawai .
ya yasina fuska yana kallon umminsa yace uhmm byn manage kawai nayi wajen tura abinci ummi ta sake yin dariya tooo ..nagode dakayi manage Kaci  yagane sarai tsokanarsa ummi take dan hakabya mike yana ce mata shi ya wuce masallaci .

Ita kuwa nablah tana shiga dakinta karamin Fridge din dake dakin ta bude Tasha ruwan.
  gashi tana jin wani irin maseefaffen bacci  Amman batason tayi bacci byn la'asar  sai yanzu tasoma kwadayin rike waya a hannuta dan ko ba komai zata rinka rage mata kewargida. tajawa kanta tsaki tace kai nablah kin cika yawa wlh  karfe biyar daidai ta sauko parlour kasa tasamu lokacin duk suna kallo .
 ko kallon inda  ummi da deeni su ke zaune batayi ba  wajen  zeenat tayi tana tmbyrta  ko akwai aikin da zatayi duk da tasan ta kammala da komai kuma  laraba ma ta dan jima da dawo wa


Zeenat  ta girgiza kai kawai batare datace komai ba Shima ganin ummi dake zaune.
 dan yanzu takanyi shakkan yi mata wani abu a gaban ummi.

Nablah   ta juya takoma dakinta ta zuge handbag dinta ta dauko currency affairs 'tana dubawa ahankali har aka Kira sallah magariba.




MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO


*Waannan shafin sadaukarwa ne gareku masoyan arziki   tare da yi muku  fatan alkhari  a duk inda kuke kaunar dake tsakaninmu daga Allah ne ,Ina rokon Allah s.w.a ya barmu taren Tare  har abada sannan ya hada  fuskokinmu a jannatul firdaus Ameen*

*Mrs splendid*
*Maryam tijjani Adam*
*Safeena mukhtar getso*
*Maryam kalgo*
*Adaweeyyah*
*MMN hafeez*
*Murja*
*Fateema abuje bagudo*
*Aina,u gadan kaya*
*MMN Aliyu*
*MMN illima*
*Faiza bsbs*
*MMN sadik*


*Ina Mika godiyata gareku all auren sirri fans sakonninku yana isowa gareni kai tsaye Ina  jin dadi yadda kuke Nuna min kauna Ina addu'ar Allah Yasa kar  soyayyarsa nan ta tsaya iya social media kawai  tazarce har illa Masha Alla  kyawun tare inshallahu*






Page 70




Mikewa Tayi 'cikin sanyi jiki taje tayo alwala tasoma gabatar da sallar magriba , baita ta  Mike daga kan praymat dinta   ba har sai da Tayi sallar isha'i.


  Kwance take lamo akan gadonta ita daya Tayi shr  hannuta rike da   karamin litattafin garkuwar muslinci, hisnul muslim. 'tana dubawa ahankali  Amadadin abin da take karantawa ya dinga shiga kwalkwaluwarta sai ma wani tunani ne yazo mata .
Sosai ta afka 'cikin damuwa yayinda  tunanin  duniya ya taru yayi  mata yawa .



Tunanin gida da mamanta da  mahaifinta har ma da ah'linta,  duk shi yafi damun xuciyarta ,ko a wani yanayi en gidansu suke cigaba da rayuwarsu ?


Ko  wani hali mahaifinta yashiga lokacin daya dawo gida ya  iske bata nan ?

Allah shine masani ...ta fadi hakan 'cikin zuciyarta 'tana may langwabar da kanta gefe .
  " take nadamar rashin bin umarnin mahaifnta yashigeta, gashi takawo kanta cikin tsaka may  inda ba,asan darajarta da mutuncinta ba" to meyye amfanin zuwanta  neman kudin shiga Jami,a alhalin mahaifinta Bai yarda da hakan ba.

 Anya kuwa batayi kuskure   a rayuwarta ba ?
Anya kuwa   ko kudin tasamu zasu mata albarka datake son cigaba da karatunta dashi ? 


Ta Dade kwance 'tana tunanin rayuwarta  ganin bbu sarki sai Allah Yasa tabawa zuciyarta hakuri ......Tare da Mike  ahankali tayiwa kofar dakinta key sannan  tashige bathroom with that thinking tayi  wanka
 shape shape Tare da dauro alwala gabadaya.

 tafito 'tana goge jikinta da dan karamin  towel din dake daure ajikinta Wanda Bai Ida gama rufe  mata jikinta  ba sosai. Dan kana kallon wasu surorin jikinta a bayyane .
,sai data gama gogge koina a jikinta  sannan  daga karshe taje ta maida towel din  jikin kofar bayi.
 Ta dawo gaban mirrow ta tsaya 'tasoma kokarin tufke yalwantaccen sumar kanta gefe" Wanda tsabar yawansa   yasa da kyar take iya  tattarosu  ,Tare da tufkesu gefe daya  domin   tasamu damar  yin bacci Sosai dan wani lokacin idan ta tufke gashin a tsakiyar kanta bata tasamun natsuwar yin bacci Sosai.

 

 A Ranar DEENI Bai samu damar sanar da umminsa komai a game da  aurensa da aka daura da nablah ba. 
sbd haushin   yarinyar da yake tawainiyya da zuciyarsa km hakan yasamu nasaba ne  da ganin da yayi mata Tare da kabir mai wankinsu  .

Ko yanzu da yake zaune a dakinsa bbu komai ajikinsa facce  dan karamin wando short niker iya cinyarsa  .
  "koina ka kalla ajikinshi gashi ne kwance  sai sheki da daukar hankali suke Tare da  birgerwa  tsabar kyawun halitta da Allah (s.w.a) yayi masa , kwantaccen gashin jikinsa suna kwance luf.luf..ta koina abin  Sha,awa yayinda kan  nipply dinsa dake manne Dass da kirjinshi zagaye da gargasan  gashi , sai yazamo tamkar wani ado ne  akawa nipply din .

 DEENI ba baya  wajen kyau da tsarin jiki  shi din cikakken nmj ne guda har da rabi ,wato first class saannan  unique man   abin so da bukatar kowace  macce gashi da mugun shiga rai .
  "kallo daya zaka yi masa kaji yatafi da hankalinka . document ne da file files zube agurin yana kokarin sa hannu acikin takardun dake gabansa , ganin da yayiwa yarinyar dazu da rana  ne  ya sake  fado masa, take yaji gabansa yayi wani irin mummunar faduwa yayinda zuciyarsa  tasoma bugawa da sauri da sauri  .... hankalinsa a tashe yake mamakin da al,ajabin abinda yasashi jin haushin ganinta da kB dazu .

to meyyesa .... meyesa zanji haushin Dan kawai naganta tare da kB?
 tmbyr daya jihowa kansa kennan wanda bashida may bashi amsar tmbyrsa ahalin yanzu .

Ya Dade zaune a dakinsa hade da zubawa takardun dake zube gabansa idanun kawai  so yake  ya gano takamaiman  dalilin da Yasa yake  tunanin  yarinyar da yake ikirarin Bai son aurenta  asalima ya tsani ya bude idanunshi ya ganta near him  . rasa gano dalilin daya sa yaji haushin ganin yarinyar da kB ne yasashi sakin numfashi Tare da ajiyar zuciya alokaci guda , tsaki yaja Tare daukar  wayarsa yasoma neman layin Zeenat ,nan ma wani sabon Haushi yakamashi  yaja tsaki ganin kiran na shiga sai dai abinda network din ke Nuna  masa ana amfani da wayar cal waiting .

 Haka kawai yaji zuciyarsa Na umartarsa daya kunna CCTV camera dinsa yaga halin da gidansa yake ciki .
Dan ya kwana biyu rabonshi da dubawa.
  dan  Haka bbu wani  westing time ya kunna CCTV camera dinsa Tare da xuba cizan lip's dinshi kadan yana kallon duk wani   abinda ke faruwa a gidan da mutane dake shige da fice har zuwan sanda  nablah ta kulle dakinta Tare da  tashigewa bathroom.

 ta fito ,jikinta daure da towel ta nufi gaban dress mirrow tana gogge jikinta da towel din dake daure ajikinta Wanda yabashi damar kallon wasu daga cikin sansar jikinta . ahankali yaga ta bude man shafawarta ta lakato tasoma shafawa fuskarta zuwa saman kirjinta dake 'cike bamm....da dukiyar Fulani . 
cak yaga ta tsaya tana kallon abinda yafi daukar hankalinsa .
, Shima tsayawa kawai yayi  cak..yana kallon manyan bobbo Tare da mamakin  yadda suka sake yin  kyau da sheki ..ba kmr ranar farko da yasoma ganinsu ba .

 Itama tsayawa tayi tana  cigaba da kallon yadda nonuwanta  ke   sheki da  cikowa  kullun "tamkar ana hurasu  . 
Ta Dade tsaye tana karewa  kirjinta kallo Tare da mulkesu da cream km duk sanda ta daura hannuta kan Brest dinta sai deeni yaji wani irin mugun shock from no where ajikinshi .
 lokaci guda  zuciyarsa tayi wani irin baguwa da sauri Wanda har joystick   dinsa Bai tsira ba jikinsa yasoma shaking Amman yaki dauke idanunshi akanta sai ma sake kurawa camerar idanunshi da yayi yana sake  kallon yadda take bin sansar jikinta tana mulke koina ahankali .


Bomshort yaga ta dauko ta saka daidai cinyarta da wata yar karamar rigar hamles ko breezy bbu ajikinta hakan yabawa deeni damar hango  kan nipply dinta dake 'cikin rigar suna tsukonoshi.
" idanunshi kyam akan kirjinta ko kiftawa bayason yi   ta feshe ilahirin jikinta da turaren five eleven tayi tsab daita. ainihin sihirtaccen kyawun surar jikinta ya sake fitowa muraran . DEENI dake zaune yana kallonta duk  ilahirin jikinsa bbu inda baya rawa yayinda jikinsa yasoma mutuwa yana samun special reaction ajikinsa most especially joystick dinsa dake harbawa da sauri da sauri ya dinga ji tamkar ana watsa masa ruwan tsanyi ne ajikinsa.

Ahankali ya lumshe rikitattun idanunshi ya sake bude fess... akanta  har lokacin tana nan  tsaye gaban mirrow wannan karon ba komai take ba .
Sai dai tayi shr alamun tunani 'cikin mutuwar jiki  yakamo lip's dinshi Na kasa yasoma tsotsa ahankali ahankali   yana ji tamkar ya fixgota ta   'cikin camera  yasoma ganar daita kuranta Nayi wannan shigar datayi .

   , bashi dake zaune yana kallon jikinta ba hatta  ita karan  kanta kallon kanta take. tsarin yanayin  jikinta yana matukar birgeta ballanantana cikakken nmj irin DEENI.
 inda kaga yadda tayi maseefar kyau zaka dauka may shirin zuwa turakar may gida ce .
   " tayi wani irin juyi hade da tsalle ta fada kan bed tana murmushi  Tare da jayon pillow ta kamkame ajikinta.wayyo sauran kadan zuciyar deeni ta tarwatse ta daina aiki. dan gabadaya jijiyoyin dake aiki ajikinshi ne suka nemi tsayawa Na wuncin gadi kafin daga baya jikinsa yacigaba da kirrrrrrma... 
 " ya Dade zaune yana kallonta kwance ta kamkame jikinta waje daya kmr may jin tsanyi   ahankali yasa hannunsa ya  kashe camerar  Dan bazai iya cigaba da kallonta a yadda yake jinsa ahalin yanzu , mikewa yayi  tsaye  yana duban yadda gabadaya  ilahirin jikinsa ya sauya hatta  gajeren wando dake jikinsa ajike yake jagab, tsabar jarabar dake cinsa,ko takan documents din  dake zube a kasa Bai bi ba    Ya janyo jallabiyarsa dake rataye ya zira   ya nufi  zuwa dakin uwar gida sarautar mata . 


'Tana amsa waya yashigo dakin da sallamarsa" tsam ta katse wayar  Tare da rufe zance datake .sannan 
ta ajiye wayar a gefen bedside dinta Tare da juyowa ahankali  ta rungume shi tsam tsam ajikinta  .

yace kedawa kike waya Haka tun dazu nake kiran wayarki  busy busy?
' gabanta ya yanke ya fadi Cikin in inna ...tace uhm uhm ..wlh nida wata kawatace da muke karatu  Tare  .

Ya amshi wayar hannunta yana dubawa duk numbers din mata ya gani   birjik ,Banda numbers din en uwa. yace duk yawan numbers din nan  friends dinki ne ?,ke yawan  kawaye baya damunki ne ? 
Ta amsa masa da cewa mutane fa rahma ne my hrt  km ma yawancinsu sune suke nema  da kawance km kaga bbu kyau wulakanta mutun takarasa fadar hakan  'tana  may saka bakinta 'cikin nashi tasoma kokarin janye hankalinsa da irin kalolin salonta Tare da gaya mishi yadda tayi missing dinsa .
Ai bata idda magana ba taji ya fara xuba mata wasu zafafan wasannisa da rabonta da jinsu tun suna kan ganiyar cin amarcinsu ,Yar karamar rigar baccin dake jikinta ya zame Tare da cigaba da wasa da santsar jikinta gabadaya yagama rudata da salon wasannisa duk inda  yakai hannu ajikinta sai taji wani irin mugun shock .
duk tabi ta rude ta fita haiyacinta tare da  sake sakar masa gangar  jikinta 'cikin Haka DEENI ya afka gonarsa.
 Banda sambatu bbu abinda Zeenat take uhmmmm uhmmmm  wayyo uhm.my  hrt ....Ina sonka dayawa wlh bazan iya rayuwa bbu kai Dan Allah.. nima kasoni kwatankwacin Wanda nake maka  please now.. show me the way u loves me too.
oga DEENI kuwa tsit kake jinsa  bbu Bakin magana Sai faman aiki yake  byn komai ya lafa Wanda  da kyar Zeenat tasamu DEENI  yabarta .
ya koma ya kwanta gefenta  Tare da rungumota jikinsa tsam  yana fidda numfashi sama sama Kusan minti talatin ya dauka kwance yana  rungume daita .

Haka kawai wani lokacin yake tsintar zuciyarsa da  tausayinta sbd yadda take mugun sonshi da tsoronsa Tare da kiyaye duk wani abinda baya so....

 ahankali ya Mike Tare daita ajikinshi.
 bathroom dinta suka shiga sukayo wanka Tare sannan suka sake fitowa murna da farinciki fal a zuciyar  Zeenat yaushe rabon hakan takasance a tsakaninsu  bama zata iya tunawa ba ?


Farincikinta yakasa  boyuwa har   suka bayyana a kan fuskarta Wanda har sai da tasa  DEENI  tmbyeta .

 tace mishi bbu komai tasa hannu ta   dauko towel tasoma  goge mishi jiki dashi  itama ta goge nata  jikinta boxes dinsa ta mikomasa ya mayar  yayinda itama ta saka Yar yololuwur rigar baccinta sannan  suka sake  zubewa  kan bed whisky blanket dinta ya janyo ya lullubesu dashi ya kai hannushi yana   fasha sumar kanta duk da bawani suma gareta may yawa ba.
 yayinda  zuciyarsa takasa samun natsuwar dayake bukata .
 yana jin tamkar  Bai mata adalci bane akan   AUREN SIRRIN da yayi a yau Amman km daya tuna itace dalilin silar komai sai yaji zuciyarsa ta samu natsuwa . Ya dinga  jin abinda zuciyarsa ta aikata daidai ne.
 duk ma abinda yayi mata ahalin yanzu  itace Silar jefa rayuwarsu 'cikin gagari da  kunci  dayasa shi aikata hakan Tare da umarnin umminsa ..

da tabar masa yaransa da dinga zubarwa  da bai jin daga ita zai iya kara  aure kowace macce a rayuwarsa .


Ganin yadda dakin ya dauki shr  Na wani lokaci alamun bbu kowa cikinsa   Yasa Zeenat tunanin  ko bacci ya dauke DEENI ne .
 Wanna tunanin  datayi ne Yasa ta juyowa ahankali" karaf idanunsu suka sarke 'cikin juna  zuciyarta ta buga sakamakon wasu abubuwa data sun  fito daga  rikitattun idanunshi suna shiga nata .
Hakan ya  sake jifa zuciyarta 'cikin duniyar soyayyarsa ahankali ta sakar masa kayataccen  murmushi  'tana may kai hannuta kan kyakywar fuskarsa ta    shafa kwantaccen gashin dake kwance a fuskarsa.
 , muryarta a sanyaye Na dauka kayi bacci ne Dana jika shr ? Numfashi yaja ahankali tukun ya sauke Ajiya zuciya .

,banyi bacci ba ,ya bata amsa atakaice,shine kayi shr  kana tunani ko...yayi killing smile dinsa may sake narkar mata da zuciya ,wa gaya miki tunani nake yi ?

Xuciyata ce ta sanar dani hakan ,yanzu dai   meke damunka dan gabadaya yanayinka ya Nuna   kmr kana 'cikin damuwa ?

 Bai bata amsa ba kmr yadda ta bukata sai Murmushin da sake  yi Tare hade bakinsu waje daya ya lullubesu 'cikin bargo  .a kunneta ya rada mata ,ban koshi dake bane shiyasa kika Ga Yanayina  Haka ,tashige 'cikin jikinsa sosai tana dariya .Tare kokarin son shiritar da zance dan tasan halinsa sarai  zai iya karawa tunda yace bai koshi ba .


Kwance take tana faman bacci Wanda batasan lokacin daya dauketa ba tayi nisa sosai 'cikin baccinta.....tun daga nesa ta hango shi  tsaye  jikinsa sanye  da fararen tufafi .
Hadadden farin  yaddi ne ajikinsa mai shegen kyau gaske.
  matsowa yasoma  kokarin yi Wanda har sai da yakaraso daf..daita sannan ne  idanunta suka iya gane mata  kowane ne .
, da murmushi dauke akan kyawawan fuskarsa  yazo gabanta yaja tsaya suna kallon juna har lokacin tana tsaye fuskarta 'cike da mamaki ganinsa tsaye a gabanta yana bulbula mata murmushi matsowa yayi sosai 'cikin isa , tamkar zai shige mata jiki .

'Cikin wani irin voice da bata taba jin irin sa ba tunda take a tsawon rayuwarta ,ta tsikayo muryar shi yana fadin...
   " Amincin Allah Ya tabbata a gareki ....
kasa amsawa tayi sbd tsananin mamaki da yaki barin gangar jikinta ...hannuta ya kamo 'cikin wani irin salo yana murzawa ahankali ahankali Tare jawota gabadaya jikinsa....Ya rungume tsammmmm.haba wife ...yakike kallona tamkar bakisan koni waye ba ,da matsayina a gurinki,  ko kuwa Na zame miki wani sabuwar halitta ne Na daban ?
 Yasoma  shashafa mata sansar  har zuwa kasan mararta yana kokarin zira finger dinsa jikinta .Tayi saurin  fizge jikinta daga gareshi  ta soma  ja da baya .

kuka  may karfi ne  ya nemi  kufce mata .
  "jikinta Banda rawa bbu abinda yake tsabar tsoro takasa  kwakwaran motse  ahankali ya sake motsawa inda take Tare da fixgota 'cikin fadadden kirjinsa  take  hawayen dake fuskarta Yashiga ambaliya ,yace shiiiiiiiii...kiyi min  shr bawani abu zan miki ba ajiyar bby kawai  zan baki kina so..?
Tayi shr taki cewa komai  Duk kokarinsa nason ganin ta bude baki tayi mgn abun yagagara ahankali ya sake matseta  tsam  ajikinsa   sosai  ganin yadda jikinta yake kirrrrrrma. maimakon tayi shr sai ma karuwa da kukan  nata yayi .
kan dole ya sausauta rikonta ba dan yaso ba  Tare da kamo  fuskarta da hannuwansa duka ya xuba mata kwayar   Idanunshi 'cikin nata ....

shin bakiyi farinciki daga Nina bane wife?
  ,ni dake munka kasance matsayin mata da miji ne .
Zan baki bby kina so   kanta tasoma girgirza masa alamun , Aa .

Ahankali taga fuskarsa tasoma sauyawa tamkar ta mayyunwacin zakin daya fita  neman  abincinsa ,cak  Yasa hannushi ya dauke sai kan wata sahara mai shimfide da farin kwalle ya kwantar da ita yana cewa ki amince nabaki bby saannan  kimin magana , banason wannan shr naki yana cutar dani .
yana mgn  'yana    romancing din jikinta '  zuwa mararta ganin Haka Yasa tayi hanzari   bude baki  da niyyar mgn ta hango Zeenat rike da wuka ta nufi kan DEENI gadan gadan  zata luma masa   nablah ta kwalla wata irin razananniyar kara ... Tare da  farkawa daga mummunar mafarkinta, ahankali ta dinga  juyi akan gadonta batare da bude idanunta ba ..


Daidai wannan lokacin Shima deeni ya farka a frigece daga nashi mafarkin yayi shr kawai yana tuanani  yayinda  zuciyarshi  take maimaita mishi addu'oi,zufa ce ke karyo masa ta koina  tamkar Wanda yayi wanka.
" ya dubi Zeenat dake kwance tana sharar baccinta ahankali kwance .
Ahankali  yasoma tuno mafarkin shi , Zeenat ce da wuka take kokarin luma masa to me hakan yake nufi ? Ahankali ya dinga kallon Zeenat yana mamakin mafarkinsa shi kam bashi da ilimin  fassara mafarki  ,dan Haka yabar shi  a rudin shedan idan ma wani abu ne , yabarwa ubangiji komai.
 dama shine mafi sanin komai addu'ar yayi Tare da koma ya kwanta ya rungumo Zeenat jikinsa  'tare da  aiyana yarinyar ce rungume ajikinshi.



Washegari 


DEENI da wuri ya dawo yana zaune a parlour kasa nablah ta wuce ta gabansa ko kallon inda yake batayi ba tashigewarta  kitchen  asalima nunawa tayi tamkar batasan da  wani halittar ,bil Adama a gurin .aiki zuciyarsa ta motsa ranshi yayi  matukar baci . Runtse Idanunshi yayi tare da  yakamo lip's dinshi Na kasa yana cizawa ahankali .
to may yarinyar nan take nufi dashi ?
Bai isa ta gaishe ba kennan kome hakan yake nufi ,take zuciyarsa tabashi amsa da ka isa man   tsabar iskanci kawai da yayi mata yawa .yaja tsaki 'tare da bude idanushi ya duba agogon dake manne a parlour yanzu  karfe biyar daidai ta cika km daidai lokacin da karar bell din gidan  tacika koina  parlour.
 nablah dake wanke kayan ciki tasoma kokarin karasawa da sauri sannan ta  tsame hannuta 'tare wankewa.

 parlour  ta sake fitowa kai tsaye tayi mamakin ganinsa har lokaci zaune .
  rigingine  akan kujera ya mikar da bayansa yayinda  idanunshi suke a  lumshe tamkar may yin bacci wuceshi tayi batare da ta sake kallon inda yake ba   .
ya taje ta bude kofar zeenat tagani tsaye tana faman cika tana batsewa , tana ganin nablah ta tsinke fuska  tana  kallonta . nabla Na kokarin yima sannu da zuwa ta katseta ta hanyar daga mata hannu  sannan tace ke ....dan iskanci tun dazu  kina jin mutane shine Sai yanzu kika damar zuwa ki bude  kofar .
 Duk faduwar da gaban nablah keyi hakan bai hanata bude baki ba gurin cewa  Kiyi hakuri wlh  aiki nake yi ne shiyasa  mtssss zeenat taja tsaki 'tare da Miko mata  jakar dake hannunta  . 

 Nablah karbi jakar tana sake  mata sannun da zuwa,  yatsine Zeenat  ta amsa fuskarta babu   yabo ba fallasa nablah ta nufi dakin zeenat .

Yayinda zeenat tasoma kokarin karasowa  inda deeni ke zaune tare da sallama jikinta a sanyaye 'cikin doguwar rigar daya saukar mata har kasa dan ya rufe takalminta 'cike da kulawa takaraso gareshi ahankali ya bude rikitattun idanunshi fes akan fuskarta idanunsu  suka  tsarke 'cikin juna a yadda take kallon kwayar Idanunshi ta gane ranshi a bace yake .
dan Haka tayi sauri cewa kayi hakuri  my hrt yau ka rigani dawowa gida wlh wani lectura ne   bai shigo mana ba Sai to 4 Ina ta sauri Na dawo dan nasan baka son kadawo bana gida.
 ,tunda tasoma mgn idanunshi ke kanta km har sanda tayi shr Bai dauke rikitattun idanushi akanta ba.
Ganin yadda yake kallonta Yasa  ta kamo tafin hannushi 'cikin nata tana  murzawa ahankali ahankali, ta sake marairaice murya tana sake  bashi hkr jin yakiyin mgn  kayi hakuri dan Allah.
 tausayinta ne yakamashi ganin yadda duk tabi ta damu dan Haka yasamu kanshi  da cewa mata karki damu ..... tace Nagode my hrt 'tare da kissing din tafin hannushi ,bai ji komai ba sbd Yadda zuciyarsa ke masa wani irin  suya da takaicin rashin ,Nuna ko in kula da   waccen Yar iskar yarinyar tayi masa.

Zeenat  ta Mike tsaye bari inje in dawo ,dakinta ta shiga ta cire kayan jikinta tashige bathroom.


kitchen nablah ta koma  ta  xuba kayan 'cikin a  pot Tare xuba kayan kamshi sannan ta daura akan gas ..Ta kunna poppo ta wanke hannunta ta koma gefe ta dafe kanta  tana tunanin meyye abinda zatayi nest .
ahankali brain dinta ya dinga gayamata yadda zata hada miyar batare da tasamu wata matsala ba .
dan Haka da sauri ta juyo dan isa durawar da suke akejiye kayan amfani  ta dauki duk abinda yadace.

 ta dago da shirin juyowa sukayi karo deeni da sauri taja baya a frigice Tare fadin  a uzubillahi....Ai tun kafin takai ga karasawa ya katseta "ta hanayar daura yatsansa daya saman lebensa shiiiiiiiii kiiiiii kada ki sake kikarasa tunda ne ba shedan bane stupid girl  kawai ke gaki abinda za'a jawa hirji  ba'a yi ba ,Sai kece zakiyiwa mutane  Harara ta watsama masa 'cike da takaicin abinda yace mata yanzu.
Ta sauke numfashi  batare da tace masa komai ba .
 ta watsar dashi   Tare da bin gefenshi ta wuce taje gaban tukunyar  tana cigaba da aikinta.

Bakinsa ya tabe Tare da harde hannuwansa duka  a kirjinsa ya zubawa bayanta idanu kawai yana mamaki kalar iskancin dake dawainiyya daita .
 idanunshi dake yawo a tsantsar jikinta ne Yasa gabanta faduwa jikinta ya fara shaking har wukar dake hannunta tana yanka albasa tayi nasarar sharbe mata hannu .
take ta saki Yar kara Tare yin wurgi da wukar aiko kafin kace me jini barke Sai xuba yake.
  " tayi wajen popping da sauri tana wake jinin dake siyaya .
 ahankali yamatso ya tsaya a bayanta  har tana jin hucin numfashinsa . tamkar zai shige mata jiki ya kamo hannun yana kallon yadda jinin ke tsiyaya .
 ko Yaya ya motsa jikinsa Na gugar nata take jikinta yacigaba da kirrrrrrma tana son yi mgn Amman harshenta yaki bata dama. Sbd Idanunshi daya kafeta dasu .
 dan Haka  tasoma mutsmutsun son kwace hannuta daga gareshi .
Haushin kanshi kanshi da kashine ya kamashi don me zai kama hannunta me ma yakawo shi inda take har da Yashiga hurinminta , takaici Haka tattare da haushinta Yasa  shi ya  matse mata ciwo  da iya karfinshi .
ta saki wata razananniyar kara yayinda  Hawaye kebin kuncinta shiiiiii  short up ya daka masa tsawa..
Ta tsorata matuka Sai dai bata bari tsoron nata yayi wani tasiri ba dan Haka .
Da kyar  ta samu ta tattaro jaruntar ta sanyawa jikinta.
 'cike  dakewa zuciyar tace  dan Allah  mlm Ni kasakar min hannu ciwo yake min.....  kmr ta zuga shi ya sake damke daidai gurin ciwo yana dubanta   idan an ki sakin hannu fa  sa  me zakiyi uhm?
 nace me zakiyi ?

bazanyi komai ba km bani da abinda zanyi Amman  wlh na barka da Allah ... wai me ma Na tsare maka ne 'cikin gidan ,ka dameni ka damu rayuwata  kana son ka dinga shiga Lamarina ,nifa bana son damuwa.
 , bana shiga Lamarinka  dan me kai zaka dinga shiga nawa... au nine ma nake shiga lamarinki?
 Tace eh Haka nace ta fada 'hakan cike da tsiwa yace a she kuwa zaki mutu kwanan ya sake matse ciwon Tare wurgi da hannuta yaja tsaki tare barin kitchen .



Haka taciga dayin girki tana yi tana  Hawaye zuci da zahiri .daf da magariba ummi da safeena suka sauka tana jinyosu sautinsu  a parlour tayi zamanta taki fitowa har byn data  kammala Sai da aka  kiransa sallah taji tsiti alamun kowa yakama gabansa  sannan ta fito tashirya dinning  tayi dakinta .


MMN SUDAIS CE
[7/20, 9:39 PM] 0mmer Farouk: 💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO



Page 71



Karfe takwas daidai nablah ta sake fitowa main  parlour din domin xuba musu abinci   suna zaune  su dukkansu , har deeni suna hira.
 takaraso har dining area .
 jikinta a sanyaye   tasoma xubawa ummi da zeenat har  ma da safeena Abinci Amman taki xubawa deeni dake zaune yana chatting a wayarsa ..asalima ko  kallon inda yake zaune batayi  ba ballanantana tasan da zamansa .


 ,Shima bai wani damu da ganin yadda  ta shareeshi ba .
 ,Sai ma gyara zamansa da yayi sosai  "yana son yaga iya gudun ruwanta.

 ,tagama duk wani  abinda take  ta juya ahankali  da niyar barin parlour.
 tayi taku daya zuwa biyu taji an fincikota ta baya .
, ahankali  ta juyo a sanyaye dan ganin ko waye ya rikota hk.
 , aiko juyowarta keda wuya.
  taji saukar mari tasssss akan fuskarta .
zeenat ce da wannan aiki  nablah tasa hannuta ta dafe  kuncinta daidai inda taji saukar marin tare da tsare   zeenat  din da shanyayun idanunta tana kallonta dasu...
 take   Hawaye suka shiga sintiri a kuncinta sharrrrrrr tamkar an bude pompo ... Ba nablah da,aka mara ba hatta ummi da safeena Sai da saukar marin  Yasa suka ji shock  jikinsu  ......deeni  dake hakemce agurin  ko gezo baiyi ba ,sai ma very gud da yace a zuciyarsa ... hankalinsa kwance yacigaba da operating din  phone dinsa cike da jin dadin abinda Zeenat tayi mata..

ke.... ashe Yar iskace bansani ban sani ba?
 ,mijin nawa ne yazama abun wulakantawa da bazantarwa a  gurinki .tsabar kin rainani .

  dan ubanki shi bai isa ki zuba masa abincin bane ko me kike nufi?
Takarasa mgnrta tana may sake  ciro hannunta  zata kara mata wani marin... ummi tadakar daita . Kull karki sake ki km marin Yar,mutane .

Aiki tazo yi fa, ba bauta ba.
 Wannan Ai  wulakanci ne da tsagwaron  rainin wayo zalla  ?
Me ma yayi zafi dayakai har  da duka?
 da bata zuba masa abinci ba  ke aikin me kike  ?

 ,kinji min rainin  arziki kawai Naga mijinki ne bana ba .. can km ummi ta sausauta murya 
A,a Zeenat  nifa banason irin Haka .
 abinda kasan idan an maka bazakaji dadi ba to karka soma yiwa wani.

 ran zeenat ya kai kololuwar gurin  baci  har wani duhu duhu take Gani tsabar takaicin abinda ummi tayi mata a gaban may aikinta..
 dan hk cike da  fushi tace  wlh ummi duk ke kike daurewa  yarinyar nan  gidin yin iskancin duk datagama .
Tare da   yiwa mutane kallon Gani Gani  da rainin hankali, wlh tun wuri idan tasan ba zata  iya yin  aiki dani ba ,taka gabanta .
inda km tacigaba dayin irin  wayan nan iskancin  wallahil azim zan gyara mata zama acikin gidan dan bazan dauki rainin hankali ba  .Ta juya fuuuuuu tasoma kokari barin parlour . 

Nablah dake tsaye har lokacin  jikinta Banda rawa rawa bbu abinda yake ,yayinda Hawaye dake  idanunta ke cigaba da silalowa.
 Cike da tausayin kanta  tasa byn hannuta  tana goge Hawayen  wasu Na sake zubowa.
 ummi da ranta ya gama baci matukar  ,tace yi hakuri kijin nablah .
" nablah ta girgirza mata  kanta kawai batare da  amsa ba .

Zo ki zauna kici abinci inji cewar ummi da kyar  nablah ke daga kafafunta da suka gama sagewa tsabar takaici da tashin hankali datake ciki . safeena ta Mike ahankali tare kamo hannun nablah 'cikin nata  tana bata hakuri ,ta zaunar daita tare da turo mata plate din abincinta datasoma ci gabanta tana sake bata baki ,ummi ma hakuri taita bata.
 ,duk wannan abin da suke mata baya gabanta hk  km bai wani birgeta ba . 
Dan gabadaya Hankalinta baya jikinta .. tunaninta  ya tattara ne akan  yadda zatabar gidan ta hutawa rayuwata.

 ,akan wani dalilin zata zauna a maidaita tamkar  baiwar Ai talauci ba hauka bane km ba,a akan aka soma zuwa aikatau ba  ,duk yadda safeena tayi daita akan  taci abinci .
kasawa ci tayi Banda bakinciki bbu abinda ke dawainiyya zuciyarta .  Ta ya'ya mijinta Na mata rainin wayo ita km ta dinga wulakanta ta..sbd me...Ta tmbyi zuciyata ..take zuciyarta ta bata amsa da ,sbd ke talaka ce ....

Zeenat nabarin gurin Shima deeni ya Mike ahankali yana kakkabe jikinsa  ranshi watse da marin da zeenat  tayi mata  , murna fal cikinsa yayi hanyar step ...
Ko rabi baiyi ba .
ummi takira sunanshi  deeni ...Ya dan  tsaya tare da juyowa yana duban ummi. kaje dakina ganin nan  zuwa yanzu .




Deeni zaune a parlour ummi akan doguwar kujera ,yayinda ummi ke zaune a gefeshi ,tace tunda kadawo daga gidansu yarinyar nan nablah banji kace dani  komai ba?

 idan  kasan da cewa bazaka iya bi zabina   bane ka fito kasanar min . Ba wai ka dinga min yawo da hankali ba kmr wata abokiyar wasanka..deeni ya marairaice murya haba first love  meyye kawo wannan  mgnr ?
Wlh  naje gidan nasu km har  ,nagana  da mahaifinta  km har angama komai .

Bangane angama komai ba ummi ta tmby ?
ya juyo sosai yana fuskantar ummi da kyau sannan  yasoma mata bayanin duk yadda sukayi da mahaifin nablah har zuwa inda aka daura musu aure  tare da fito da wayarsa yana Nuna mata video dayasa sule yayi lokacin da'ake daurin ,auren . Yanagama nunawa ummi yakira number  sule tare da saka wayar a handsfree ,muryar sule direba ta bayyana raudau ,shima dai Karin bayani yayi mata  akan yadda daurin auren yakasance sannan deeni yayi hanging din kiran .

ummi naga jin yadda komai ya tafi 'cikin tsari Yasa ta saki ranta sosai ba kmr tun farkon shigowarta dakin  ba tace yauwa Haka nake son ji alhamdulilllahi 
 ,Dan har Na  dauka ko bazaka bi zabina bane ?



'Cikin sarkewar murya yace a koda yaushe banida zabin daya wuce na ummina duk abinda kike so shi nima nake so akan wannan baza mu taba samun sabani ra'ayin ba.
 farincikina shine nakasace may biyayya a gareki.
 dan Haka banida yadda zanyi  auren yarinyar shine mafuta kawai  atare dani..
  Ni km hk tawa kaddarar auren yake zuwa min zuciya bazata taba samun zabinta ba .


Tsananin tausayi furunci deeni din ne yakama ummi  Amman km bata jin zata iya canza ra,ayinta akan  qudirinta .


Parlour ya dauki shr koina yayi tsit tamkar ba masu numfashi aciki. baka jin motsin komai Sai Na sautin TV.
 ummi ta nufasawa tare da kokari kawo karshen shirun nasu ta hanyar  cewa Allah yayi maka albarka deeni duk abinda kake nema a duniya da lahira Allah yabaka. biyayyar da kake min kaima Allah yabaka ya'ya shiryayyu da zasu maka fiyye da hakan .

Ameen first love ya fada tare da Mikewa kan kujera ya daura kansa akan cinyarta tamkar dai yadda kananun yara  sukeyi  , tare da lumshe rikitattun idanunshi .

Ahankali ummu takai hannuta kan sumar kanshi dake kwance luf..luf Sai sheki suke da daukar hankali 'cikin tautausar lafazi may tsanyi ta Kira  sunanshi...NASURULDEENI ....kwata kwata bashida niyyar amsawa Amman yadda umminsa takira complete name dinshi ne yasa dole ya amsa mata da  Na,am first love a kasalance  domin yasan duk abinda yasa umminsa kiran ainihin sunan haka abu ne may mahimmanci .
dan Haka ya tattara duka hankalinsa gareta .

Banason abin nan ya dau lokaci sbd da Haka ka hanzarta raba masu kwana kmr yadda addinin Muslinci yatanadar. kwana biyu biyu ko day day ,tunda ummi tasoma mgnr raba kwana numfashinsa ya nemi daukewa cak.. ko motsi  bai yi ba  har ummi ta dasa aya. 

idanushi a lumshe suke , zuciyarsa ke mishi radadi da suya tare da takaicin mgnr ummi .
 dan Haka muryarsa a dan zafafe yace kina nufi dakinta zan dinga zuwa ? Itama ummi a zafafe tace 
 Kwarai kuwa  ko bazaka iya bane?

Ganin yadda ummi tayi ne Yasa shi cewa Ni Na isa nace bazan iya zuwa ba  Sai dai wlh Ni  kunya nakeji  yakarasa  fadar  Haka cike da shagwaba tare da yatsina fuska.

Ummi tacigaba da shafa sumar kanshi ahankali daga karshe tace daurewa zakayi kaje gareta badan ta isaba Sai dan bukatar mu .
Deeni dake kwance ya sake yatsina fuska alamun Yashiga sarkarkiyya da kyar ya iya bude baki yace shikennan first love zan ware lokaci da zanje gareta .
Ummi tace wani irin zaka ware lokaci zuwa gareta ?

Kawai yau zuwa gobe ya Isa ka tsara komai dan bamuda wani  ishashen lokaci batawa .

A kidime deeni ya Mike zaune yace haba haba first love karki min hk man  wani irin yau zuwa gobe gsky ni gobe  yayi min wuri  dan ban shirya zuwa gareta a gobe gobe nan ba .
  Amman I promise nest week  inshallahu .


Nest week Yayi nisa deeni kayi kokari kaje gareta zuwa jibi .
Tamkar may shirin rushewa da kuka yace uhmmmm alamun yaji kawai  ummi tayi murmushi jin dadi hade shafa gefen fuskarshi da tafin hannuta duk kabi ka wani  rikice tamkar may jin  tsoron yarinyar .

deeni ya zaro idanun waje yana wa ummi wani irin kallon shi din ne yake jin tsoron yarinyar da loma daya zaiyi ya gama daita.

 haba first love .. yau km nine matsoraci yana may Nuna kansa da yatsansa sannan yacigaba  tsorona ma  ya rasa inda zai kare Sai akan mace ...mace ma housemaid dina.. ummi tayi saurin daga   masa hannuta ok yaisa to Ai  kai din ne naga duk kayi wani irin tamkar kana jin tsoronta .

Alhalin nina san yarona jarumin jarumai ne..
  sadaukin nmj abin sha, awar kowace macce.
 ,kaga yarinyar nan bata da wani aibu uwa uba  tana da kyau sosai .
idan  Allah Yasa ma akaci sa'a bbys din duk sukayo kama daita .
Kaga zamu samu    kyawawan bbys  daga gareta.

 duk maganganun ummi bbu wanda yaji yafi bata masa rai kmr wai yana jin tsoron yarinyar da wai tana da kyau.
 dan Haka ranshi a bace yace Ni first love ki daina wani  cemin tana kyau .kyawunta Na banza ... tunda nasan ko kama kafar mamata batayi ba a kyau  ballanantana Ni .

banason ma ya,yana su wani  yi kama daita zanje dai gareta ne kawai sbd cika ummirniki badan wani kyawunta ko me ko me....kawai ya Mike tsaye   dan yaraba kanshi da sake jin zance yarinyar da ummi tasaka shi gaba dashi .
 dan zamansa agurin zai iya hadasawa zuciyarsa kamuwa da wani ciwo may tsanani  .


Zuciyarsa cike da Haushi ya nufi dakinsa ya murda handle yashiga bedroom tare da fadawa kan makeken royal bed dinshi da jan tsaki yayinda bakinsa ke fidda wani irin iska may zafi. hannuwanshi duka ya daura yayi pillow dashi Tare da kurawa celling daki ido tamkar may karanta wani abu..
 ,bbu abinda yake Banda tunanin yadda zuwansa gurin yarinyar zai kasance tsawon lokaci ya dauka kwance yana kallon celling dakin kafin daga baya ya sauke naunauyen ajiye zuciya may karfi gaske ..
 yafara zance zuci ta Ina zan fara ?
A zahirance zanje mata ko badinance ?
Zuciyarsa tabashi amsa kaje mata kawai a dakenka sak .... a,a kada kayi Haka ka tsaya dai ka natsu tukun kasan ta Inda yadace kaje mata..
 ya sake furzar da iska tare da jan tsaki mtssss ko ma a ya'ya naje mata dolenta ta saurareni km  Hakan  bazai hanani cin ubanta ba da wannan sabon  iskanci data tsiro min dashi ..
, har kmr Ni ya Nuna kanshi da dan yatsansa wata diya macce zatace Ina  damun rayuwarta ina shiga lamarinta .
 shi deeni da kanshi ya girgirza kanshi kawai yana sake jin haushinta ...




Ranar Wednesday yakama rana da ummi ta umarce shi da zuwa gurin yarinya.

 dan Haka tun a safeyar ranar yagama shurinsa tsab  ta yadda zai isa Gare   a saukake .

Zaune yake a dakinsa ya tasa CCTV camera dinsa ...





MMN SUDAIS CE
[7/20, 9:40 PM] 0mmer Farouk: 💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO



Page 72


Zaune yake a dakinsa ya tasa CCTV camera dinsa gaba byn ya fito daga bathroom  duk wani lungu da sako Na gangar jikinsa bbu inda bai fesheshi da turarensa Hamilton  ba .
rigar  bacci ce sanye ajikinshi  mai budadden gaba Wanda yafito da ainihin siffar ta cikakken namiji .  gashin kirjinsa Na kwance luf luf dasu  abin Sha,awar da bukatar kowace cikakkiyar mace data amsa sunanta .

 Wanda kallo daya  mace zata yiwa kirjinsa  taji hankalinta yayi mugun   tashi domin duk wata wacce may raunin Sha,awa ta kalleshi dole ne ta Mika kanta gareshi  batare da ta shirya yin hakan ba.

   kallon camerar yake batare da ganta ba .
 ko jin motsinta ko ganin wata alamar dazata Nuna masa tana  dakin ba.Gashi bai  saita Na,urar daukar  da bayi ba ballanantana yaga  ko tana ciki . 'Ahankali' yakai hannushi kan system yasoma dubo part din kasa aiko daita yasoma cin karo zata shiga kitchen hannuta rike da wata karamar Leda fuskarta a dan daure jikinta sanye cikin hijab kmr koda yaushe. 'Ahankali' ya km shiga 'cikin system dinsa ya dawo part din nablah..

,tsawon lokaci ya dauka  zaune a gurin tare da yin zance zuci irin har sanda yaga shigowar dakin hannuta rike da wasu kaya.ta maida kofar ta rufe tare da murda key..

Ta ajiye kayan hannuta a gefen bedside dinta tayi Mika may dauke da gajiya  sannan ta soma cire kayan jikinta tashige bathroom wanka .
ta Dade a 'cikin bayi km har lokaci yana zaune yana zaman jiranta fitowarta  har ranshi yasoma baci  ahankali ya furzar da iska may zafi  daga  bakinsa Tare da cewa ko me wannan Yar iskar yarinyar take a bathroom har yanzu data ki fitowa  ?

 'Cikin hk Wayarsa  ta dauki karar sauti mai dadi Yasa hannushi yana kokarin janyowa wayar batare da ya dauke idanunsh daga camerar ba.a hankali yasoma duba screen din wayar sunan fk yagani .
 Ya dauki wayar cike da jin Haushi...
  fk kuwa yana jin DEENI ya daga wayar yace amincin Allah Ya tabbata a gareka abokina ......


Deeni ya amsa tare da cewa  ya,akayi ne fk ?


Fk yayi murmushi sannan yace  daman  zance maka ne ka fito da wuri Gobe sbd sabbin ma,akanta da za'a dauka Dan zanfi son ace akai ne  kazayi musu interview da kanka.

 DEENI yaja tsaki Dan jin wani sabon Haushin daya caki zuciyarsa.
Dan Haka a fusace  yace   idan ban fito da wuri ba sai bbu Wanda zaiyi musu interview din ? 

Fk yace  uhm  akwai man sai dai  zanfi   son kai da kanka kayi musu ..


ran DEENI ya sake baci Dan hk hallasale yace to ba'a za fito da wuri  din ba kar Allah Yasa a dauki ma,akatan Dan rainin wayo kawai ..

 kai zaman  uban me kake yi da zaka ce  kafin son sai Nine  zanyi .

Fk ya sausauta murya sannan yace haba aboki  Yanaga duk ka dauki zafi ne  daga yin mgn.
   meyyesa kake yin Haka ne ?
 abi fushi da Wanda bana fushi ba duk yi kake wlh DEENI  ka dinga saurarawa zuciyarka da yawan saurin fushin nan dakake yi .
 Dan wlh zai iya kai yabaro  ...

Ya bude baki kennan cak ya tsaya  yakasa cewa komai  sakamakon ganin fitowar  nablah  daga wanka daure da towel iya cinyarta tana gogge  sansar jikinta xuwa manya nonuwanta...

jin shr DEENI yayi yawa ne  Yasa fk cewa hello ! hello !!deeni kana kan layi?
  uhm DEENI ya fadi Haka a kasalance.
 yauwa.. yanzu dai abinda za'a yi kayi hakuri dan Allah ka fito  goben da wuri sbd kaga kai ne  kafi cancarta dayin  duk wani  abinda ya dace  company s...
rike kawai  DEENI yake da waya a hannunshi  Amman gabadaya Hankalinsa da gangar jikinsa  basa  gurin fk .


Hankalinsa gabadaya ya karkata ne Ga yarinyar dake 'cikin camerar gabansa tana     feshe ilahirin jikinta da turaren kmr yadda yasaba ganin a duk sanda akaci sa'ar ya waiwayo gareta .


Hello deeni kana jina kuwa uhmmmm Ina jin dan matsala kawai wlh fk kacika  damuwa ,wani lokacin.
" ka dinga abu tamkar Wanda Bai san  darajar iyali ba mtssss yaja tsaki..
" fk ya zaro idanu  waje kmr yana gaban DEENI.

 Amman dai Kai anyi dan banzar yaro wlh yanzu  nine ma zaka cewa  basan darajar iyali ba .
Ba  laifika bane , Ai yanzu kasan dadi mace dole kace hk .
Ka manta sanda ake binka da aure kanakin   .

 auren dama kafin kayi shi , sai da aka soma bar maka wasiyya ..shine dan tsabar iskanci da  rainin hankali yau Ni zaka wa   bansa darajar iyali ba . 

Kar Allah Yasa ma kafito gobe  da wuri inda ka cika ..DEENI yayi shr kawai yana sauraron fk  yana kallon  nablah data  ta nufi Dan karamin fridge din dake  dakin ta bude .

A can bangaren nabla kuwa  byn ta bude fridge  taga drinks kala kala tayi murmushi jin dadi Dan tasan aikin safeena Dan tunda tazo gidan fridge din ya daina kasancewa bbu komai cikinsa .
cike da murna  tasa hannun ta dauki hollandia yougoth ta bude tare da kafa bakinta  Tasha Sosai sannan ta nufo gadonta rike da sauran tana lumshe  shanyayun idanunta tare da ajiyar kwalin hollandia din a gefen bedside.. ta kwanta ruf da ciki batare da sanyawa jikinta komai  tana sake lumlumshe idanuwa.
 zuciyar  DEENI ta buga da sauri ya saki ajiyar zuciya ahankali har fk yajishi.... 
Fk  yace wannan irin wulakancin ne kana jin mutane kayi musu shr sai fama wani  sakin numfashi da ajiyar zuciya kakeyi  .

  ko kana sex ne da matarka   Na kiraka batare da saninaba?

 DEENI ya sake  sakin  numfashi tare da wata ajiyar zuciya yana jin yadda gabadaya jikinsa yasoma samun sauyin yanayi  kafarshi kawai ya dinga motsawa yana  jijigata a kasa.
 ,karfin hali kawai yake gurin sauraron maganganu fk sai daya furzar da iska  may sanyi sannan yace wannan  ba damuwarka bane .
  km bai zama lallai  kasani ba.
 ,shiyasa nace maka bakasan darajar iyali ba.
 kaji Haushi ,indan kasan darajar iyali look at the  time   you called me... DEENI  yakarasa fadar haka yana jan tsaki ....


fk ya daga Idanunshi  yana kallon agogon dake parlour,nsa karfe shadaya daidai yanzu ta buga yace kai dai anyi dan iska wlh  idan iskancinka ya motsa hk kake .

Deeni ya Tari numfashinsa ,ba hk nake ba .
kadai kiyaye dan gaba fk yaja tsaki tare da hanging din kiran gabadaya.

DEENI yayi killing smile sannan  yacigaba da kallonta har sanda ta kwanta batare da ta saka komai ajikinta  ba yace very gud .
yarinya kinsa daidai  hakan ma wata dama ce gareni .

tunda Ga sanda yaga tashi hollandia nan  yasa mgn ya kare  sai yadda yayi daita. 
  " dan ita da farkawa sai yayi mata allurar dazata rage mata karfin maganin ajikinta.

 ahankali ya Mike tsaye hade da kamo lips dinsa nasa  yana cizawa ahankali ahankali tare da sa hannunsa yakashe CCTV camera .
sannan ya dauki ruwan allura da sirinji yakarasa  jikin wata kofa ya bude Yashiga sai Ga wani bogulari glass ya bayyana .
ya zuge glass din  cike da natsuwa .
wata kofar ce again ta sake bayyana may kama jama door ..  hannushi yakai jikin bangon gurin ya dauki key yasoma kokarin bude kofar tare da turawa ahankali   sai gashi a 'cikin dakin nablah ....


A natse yake daga kafafunshi har ya iso inda take kwance ya tsaya cak yana kare mata kallo ahankali yakai hannushi zai taba bayanta .

Amman yakasa kawai ya xuba mata idanu yana cigaba da  kallonta yayinda  zuciyarsa ke tsanata bugawa da sauri.

 gefenta ya dawo ya zauna jikinsa Na rawa rawa da kyar ya iya  jarumtar sanya hannuwanshi duka ya juyo daita.

Yana juyota ,towel din dake daure a jikinta ya kwance  Idanunshi fes akan fresh bobbo dinta da suke tsaya kyam sai sheki  suke da daukar hankali.
 ya kafesu da rikitattun idanushi  zuciyarsa ta tsaya cak ta daina harbawa Na wuncin gadi  kafin daga baya tacigaba .

'Ahankali' Yashiga kokuwa da numfashinsa dake neman tsayawa .

jiyake iskar dake aiki  dakin tayi masa kadan gabadaya reaction din jikinsa ya sauya  joystick dinsa ta Mike sambal..jikinsa yacigaba da kirrrrrrma ahankali ya zare towel din dake jikinta gabadaya ta fado jikinsa ..
DEENI najin dirar dukiyar fulaninta bisa kirjinshi tunin ya gigice tare da soma wasa da albarkatun kirjinta...sosai yake shashafa Brest din hade da murza kan nipply dinta duk ya rude ya ruda  mata  jiki da salonsa .

 Lip's dinshi  ya daura akan nipply yana mata wani irin tsotsa  ahankali ahankali tare da zagaye  akan nipply  dinta da harshensa .

ta yadda bazata ji zafi ba dan shi kansa yaga alamun ba'a taba shan kan  nunawata  ba.

 duk ya rude ya gigice yasoma manta kanshi da km wace yake tare.
  dukiyar Fulaninta banda shan matsa bbu abunda suke yi  a hannunshi .

'Ahankali' ya kai hannunshi kasan  mararta yana shafawa yana wasa da  gurin .
Ita km dabatasan a duniyar datake ba Sai wani  kamkame shi take batare da saninta ba .
   'Ahankali' ya zira fingers dinsa cikin kasanta yana fingering dinta yayinda bakinsa da lips dinsa   still Na kan nonuwanta yana  aikin sarrafa albarkatun kirjinta ..'cikin wani yanayi  jikinta yasoma shaking batare da ta bude idanunta ba.

 tsintar hannuta yayi ajikinshi tana mayarsa masa  da martani 'cikin wani irin salo .. gabadaya yagama fita haiyacinsa tunda takai hannuta jikinsa ya sake rudewa tamkar yadda shima ya fiddata 'cikin hankankalinta.
 a 'cikin baccinta ta dinga jin wani irin abu  yana tsarga mata a duk tsantsar jikinta tunda Ga tsinyar kafafunta har zuwa tsakiyar kanta . most especial kasanta da kirjinta .

 ,kirjinsa take shafawa 'cikin natsuwa  .
Tare da murza masa gashin dake kwance a faffadan  kirjinshi  hade da kamo nipply dinsa dake zagaye da gashi tana murzawa ..
wani irin numfashi DEENI yake fitarwa may  gwaraye da dadi.
tare da sake bada himma gurin gigitata mata jiki ta hanyar  sake zira yatsansa  'cikin   kasanta da kyau ta yadda zai samu damar  bude hanyarsa .
 dan ko Rabin fingers dinsa yake shiga kasanta  ballanantana akai Ga uwa uba joystick ..

 Mirgina  daita  yayi ta dawo kasanshi tare da gyara mata   kwanciya sannan ya cire rigar baccin dake jikinsa tare ware mata kafafunta  ya sauke bakinsa 'cikin kasanta ya zira  harshensa ciki yashiga soucking dinta..ita wayyo  Sai faman turo masa kasanta takeyi ,yayinda take  can 'cikin duniyar baccinta Wanda  tunaninta ya ta'alaka akan  irin mafarkanya  data saba yi ne .

DEENI  tsaita kan  kaciyarsa  'cikin kasanta yana kwaroro addu'ar saduwa da iyali  . ahankali ahankali yake bi daita  daidai kan kaciyarsa tashige 'cikin  jikinta  yaga tayi wani irin zabura kmr zata tashi tare da kwalla wata irin  razananniyar kara ..
can   km ta koma luuuuuuuu sharaf akan bed  wani irin azaba ta dinga ji ajikinta Wanda bata taba ji irinsa ba.

 dan radadin ya ratsata fiyye da fahimtar may karatu ..wani shock DEENI yayi shima  sanda yaga ta   kwallara kara ganin ta koma  tayi shr ne yasa shi sakin numfashi da karfe gaske.

 a natse ya sake gyara mata kwanciya .
"wani irin gurnani take Na azaba Amman Ina DEENI bema san tana yi ba dan oready yayi nisa ..

 Haka DEENI yashigeta da karfe sbd ,ba'a 'cikin hayacinsa yake ba .

Kwata kwata bai  mata da wasa ba tun 1 : am yake kanta har 3 : am sannan ya sarara mata shima ba dan yakoshi ba ,Sai dan tausaya mata da yayi sbd yasan shine mutun Na farko daya soma shigarta.
 'ahankali' ya dagata ya koma gefe ya jawota jikinsa ya rungume tsam tsam .
 duk da shima ba  farkon yinshi  kennan ba  Amman ya dinga jin jikinsa wani iri. sakamakon rufafiyar  hanyar daya huda babu sauki .
 yana nan rungume daita tsawon lokaci kafin daga baya ya kwantar daita ya Mike ya je ya dauko doguwar 'riga acikin kayanta ya saka mata tare da dauko sirinjin daya shigo dashi yayi mata allura. Sannan yakarasa ya  bude kofar shigowa dakin dan yasan dole ummi tasan .
Lamarin  aika aikan da yayi yarinyar mutane sannan  ya tattara inasa Ina sa yabar dakin .Ta hanyar daya shigo..



Yana koma dakinsa ya zauna a gefen bed dinshi tare da xuba uban tagumi ,yana zance zuci.
Oh  God Menene Haka nashigar yarinyar mutane da  karfi ?

Meyasa banbita 'ahankali' ba tunda nasan bata taba  yi ba ?

 Ta ya'ya   zaka sani tunda kakasa control din kanka akan karamar yarinya ..
Kawai ya tsinci zuciyarsa tana  bashi amsa da hakan ..
oh shiiiiit ba Haka naso ba wlh naso na bita 'ahankali'.
 sannu ya Mike rungune da hannuwanshi duka a bayansa  yasoma sintiri a 'cikin dakin ,yaka kai ya kawo yarasa me ma kamata yayi .

Tsawon lokaci yana zariya darasa abinyi daga karshe dai yashige bathroom tare da shiga  'cikin bathtub ya zauna  kuna shawa ,'ahankali' ruwa ya dinga sauka akashi  yana ratsa koina a sansanr  jikinshi... ya lumshe rikitattun idanunsa kawai tare afkawa cikin duniyar tunani .

 Duk zuciyarsa tayi masa sanyi Amman  yasan bai bi daita ta hanyar data dace ba gurin saduwa daita ....

Zuciyarsa ta dinga dusashe aibun abunda ya aikata .. 
Yayinda  dinga   jin tamkar ya aikata 
 Dade  a game daita .. after ol matarsa  ce bai kamata ma ya zauna yana damun kasa da wani  banza  tunanin ba .
Dan Haka zuciyarsa ta bashi karfin gwiwar mikewa yayi  wanka tsarki may hade da alwala ya fito ...

Ya zira jallabiyarsa tare da  shimfida praymat yasoma gabatar da nafuloli da addu'ar Allah Yasa kwallonsa yakai Ga  shiga raga ...

bashi ya yanke nafilolin dayake ba sai daya soma jiyo kiran sallah daga masallaci dake'cikin gidan .
sannan ya katse .Ya zauna yana laximi har zuwa sanda  aka tada sallah ya Mike ya gabatar da sallah asuba yakoma ya kwanta ya lumshe rikitattun idanushi.





Da safe  ,Sai daya makara gurin tashi  sbd bai wani samu ishashen bacci Sosai. 
Haka dai yashirya 'cikin sanyi jiki  ya nufi dakin ummi ya sameta rigingine akan gado hannuta rike da carbi tana laximi ..
 safeena taganinshi ta  Mikewa tsaye tana  gaidashi sannan tabar dakin takoma parlour ummi .

'Ahankali' ummi ta xuba masa idanunta tana kallonsa tare da nazarinsa har ya karaso har inda take ya zauna gefenta.
 first lov mun tashi lfy ,ya fadi hakan kansa Na kallon kasa ta amsa cike da kulawa   tana may  sake dubansa da kyau  deeni shr yarasa ta Ina zai soma yiwa ummi bayanin aika aikan daya sula ....
da n Haka kawai ya Mike tsaye  yana cewa mata first love kimin addu'a Ni zan fita office Amman dan Allah  ki rike waya ahannu ki .
Inda nakai office  zankiraki akwai abinda nake son zan sanar dake ummi tacigaba dubanshi tana mamakin abunda yace  .

Ko baka da lfy ne ummi ta tmbyeshi ?
Lfy lau nake first love ki dai rike waya a hannunki ummi  tace to Allah Ya tsare a  dawo lfy   . Ya fice daga daki cike da takunsa nan nasa may daukar hankali.

byn fita DEENI   ummi tashiga tunanin me DEENI yake son gaya mata da har yakasa kasa duban idanunta yanasar mata  lallai ko wani irin mgn ce Wannan tana girma  km matsala acikinta domin yaron ta  baya boye mata komai daya shafeshi ..


Byn kmr minti talatin da fitarshi  kiranshi yashigo wayar ummi .
jikinta ummi har rawa  yake gurin    dauka wayar  tare da sallama ,ya amsa muryarsa a kasalance..
 sai km yayi shr uhm deeni Ina jinka tun byn fitarka hankalina yake a tashi kasanar dani abinda yake damunka tun kafin zuciyata ta buga?
Deeni  ya runtse Idanunshi Sosai tare da  fidda numfashi dan yana  jin kunyar abunda zai fada din .. sannan yace uhm daman nace ...Sai km ya sake yin shr..
 kace me ... DEENI ?
Kamin mgn man..
  " ummi ki natsu  kokarin nake yi kennan  sanar miki daman akan yarinyar nan ce .
uhm   meyasamu  yarinyar Ina sauraronka ?

'Ahankali' ya sake sauke ajiyar zuciya sannan yacigaba a atakaice wlh  fist love  aika aika nayi mata  tare da sani ba .... dan Allah first love  kije ki dubata  tana 'cikin wani hali ..inna lillahi wa inna ilaihi rajiun ummi tashiga jerowa bbu kwakwatawa.

 ta Mike tsaye rike da wayar tana salallami yanzu DEENI  abinda ka aikata kennan shine  kagagara gaya min sai a waya idan wani abu yasamu diyar mutane mekake son nacewa er uwarta uhm ?
 
Muryarsa a sanyaye yake am sorry first love tare da  hanging din kiran dan bai son jin tashin hankali  umminsa zatashiga  ..jiki Na rawa ummi ta nufi dakin nablah kwance ta isketa tamkar wata matacciya akan bed.
  gabadaya gashin kanta ya tarwatse ko fuskarta ba a iya hangowa ummi ta fashe da kuka tana karasa gareta tare da daga hannuta .taji ya sake .
aiko gigice tayi hanyar bayi da sauri ta dibo ruwa tashiga kwara mata ...




MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗





AYSHA A BAGUDO



Page 73



Duk yawan  ruwan da ummi ta dinga watsawa nablah bata farka ba asalima ko motsawa batayi ba .

hankalin ummi yakai kololuwa gurin tashi batasan lokacin data isa Inda nablah ke kwance ba ta rugumota  gabadaya ajikinta tana jijigata tare da kiran sunanta.
 nablah.. nablah please nablah kitashi still shr km  bubu wata alamar numfashi a tare daita ummi ta tsorata da ganin halin da yarinyar mutane take ciki .
 "agigice ta dauki wayarta tasoma neman layin DEENI kira daya ya dauka yana first lov..... ummi ta fashe da wani irin matsanancin kuka  sannan tace kai wato kana can kana lamarinka kabar yarinyar mutune 'cikin halin ha,ulai to wlh kazo Dan ubanka dan ka kashe yarinyar mutane sannan ta ajiye wayar batare da ma ta katse ba tacigaba da jijiga nablah tana kuka da kiran sunanta  .

Ba'a yi cikakken min shabiyar ba sai Ga deeni ya iso tare da  doctor din dake duba maikanta gidan Allah Yasa  bbu kowa a gidan Zeenat ta tafi makaranta yayinda safeena sun fita tare da laraba zuwa just right .


  a rikece  ya karasa shigowa dakin   idanushi kyam...  akan nablah dake kwance sa da zuciyarsa ta buga ya juyo da sauri   yana tmbyr ummi wani
 halin take ciki .
 ummi ta dubeshi tare da  watsa masa wata uwar  Harara  shi kansa  bazai iya cewa ga  irin rudani daya shiga ba sanda ,yashigo dakin  yaga  halin da yarinyar mutane take  ciki ba .

 banda ambaton sunan Allah bbu abinda yake a kasa  zuciyarsa  ya kasa  cewa komai Sai nuni da yayiwa likita  data soma yin abinda yakawota.

 domin  ji yake  Ina ma kasa ta tsage ta bude yashige ciki  ya huta da wannan abun kunya daya aikata.
 hakika bakaramin aika aika ya aikatawa yarinyar ba.
 gyaran muryar da doctor  din Tayi ne  ya dawo dashi daga duniyar tunanin daya afka Na wuncin gadi .

Dan Allah kataima kai kamin ita xuwa  dakin kasa nasamu damar dubata inji cewar doctor .

 deeni dake tsaye tamkar an dasashi  Sai lokacin ya dawo 'cikin natsuwarsa.
  Take suka sake  hada ido da ummi kallon kallo suke yiwa juna.
 'Ahankali' yayi nodding kanshi kasa tsabar kunyar data rufeshi   da taimakon ummi doctor tasamu tasoma duba nablah .
 still idanun ummi Na DEENI ta kafeshi  da idanunta tana mamakin abinda ...

 doctor ta dago   Tana  duban  ummi tace gsky madam wannan abu yayi tsanani dayawa gashi Ni yanzu banida kayan aiki a hannuna km Na duba nan  bansamu abubuwa dazan mata amfani dashi ba.
 amman Mafi sauki Ku tafi hospital mafi kusa daku .
deeni ya tsareta da idanushi   yana mata wani irin duba Na tabin hankalin kana  a hassale yace  ke wace irin stupid doctor ce dabata san kan  aikinta ba.
 I think  doctors suna yawo da kayan aikinsu  ne shine ke zaki zowa mutane empty hands mtssss yaja tsaki ummi  nagama jin abinda doctor tace .
ta kira direbanta tana kokarin daukar nablah . cak deeni Yasa hannushi  ya dauki nablah cike da sauri ya nufi motarsa daita daidai lokacin da  ummi takarasa fito ta kira sunanshi deeni .... ya tsaya yana jiran jin abinda zatace.. kai min ita 'bayan 
 mota da hanzari yakaita byn motar ummi ya kwantar daita ummi tashiga da sauri deeni ya ma zagayo ya bude gidan gaba zai shiga .
a fusace ummi ta dakatar dashi  don't try to enter into this car becouse I don't want see you in it.
 ,a rude deeni  ya kyame tamkar Wanda akayiwa wanka da ruwan sanyi  yana  kallon ummi jin kalmar data fito daga bakinta tuni jikinsa ya kama rawa rawa ya sauke   Idanunshi kan fuskar nablah dake kwance tamkar wata  matacciya '.
cikin rawa murya yace ummi... ummi batare zamu tafi  ba   deeni ya fadi hakan 'cike da tashin hankali yayinda idanunshi suka gama canza kala tamkar garwashi  ...Kule
What are you wanting for   driver me to  bankole hospital inji cewar ummi deeni ya bude baki zai sake yin mgn kennan   Kule  ya figi motar  da gudu yana danna hon  da karfin gaske har securities din dake bakin get din  estate  suka Mike tsaye cirko cirko ..


Da sauri deeni yashiga motarsa.. sule yaja suka bi bayan motarsu ummi lokaci daya ummi da deeni sukayi parking .

 deeni ya bude motar da sauri ya fito batare da ya tsaya sule ya bude masa ba .Yashiga reption tare da wata doctor suka fito deeni ya sake daukar nablah yayi ciki daita ya direta a matanity .


Doctor tare da wasu nurse guda 2 suka soma bawa nablah   taimakon gwagwa .
doctor tace deeni yayi musu excuse sannan ta bude kafafun nablah zaro idanun waje  Tayi sbd yadda taga gaban nablah yayi doctor ta dubi ummi da kallon tsoro. madam repy dinta akayi ne ?
Ummi ta bude baki da kyar tace uhm mijinta ne yayi mata wannan aika aika..
 doctor ta girgirza kai kawai tare da soma yi mata  treatment na musamman tace Sai fa amata stitching a gurin inda hk ba .
zata iya samun matsala gaba .  ummi tace please do anything possible to help her I don't want to lose her  ummi ta fadi haka hankalinta a tashe.
 gabadaya ta fita haiyacinta tamkar itace bata da lfy  har tabawa doctor din tausayi Dan haka doctor  Tayi ta bata hakuri akan ta kwantar da Hankalinta bbu abinda zai samu yarinyar .

'ba dauki dogon lokaci ba  akagama dinke nablah tsab . deeni Na tsaye yana faman paturo a reption  yaga an turo nablah akan gadon marasa lfy  bata ko motsi tamkar wata matacciya ...
ya hanzarta bin bayan nurse din dake turata zuwa dakin hutu Yashiga . An kwantar daita tare da daura mata drip.. sosai ya motso kusa daita ya xuba mata rikitattun idanushi tana kare mata kallo gaba daya tagama fita haiyacinta batama san a duniyar datake ba ..haka kawai ya dinga jin tausayin yarinyar yana tasomasa tun daga kan tsintsiyar kafafunshi har xuwa kanshi  ya gwaraye da jinin dake aiki a jikinsa tare da circulating  koina jikinshi ya dade tsaye agabanta kafin daga baya ya Mike yaje jikin Window ya tsaya .
Daga Inda yake yana hango Kule da suke suna zaune suna hira .
Ran deeni ya sake hassala wato su basu da matsalar komai hirarsu ma suke hankali kwance yaja tsaki yana sake joyuwa ya kwalli nabla still har lokaci bata motsi .


Bayan awa hudu dayiwa nablah dinki.
 da duba lfyrta har yanzu bata farka ba ..
 abinda yakara tada hankali ummi kennan  tsoro may tsanani yashigeta kada fa Yar mutane ta margaya  a hannunta ..

Zeenat ma koda ta dawo bata iske ummi  a gida ba .takira ummi  tana tmyrta Inda take.
 " ummi ta sanar mata da suna hospital nablah ce bbu lfy tayi tsam da ranta Na wani second wannan tace ok... kawai  tare da cewa sai ta dawo 

Ummi gaban doctor tana tmbyrta meyasa har lokaci nablah bata farka ba asalima ko motsawa batayi..
Doctor ta zubawa ummi Idanu tana sauraranta har ummi ta dasa aya sannan tace  uhm yadda abin yake .. yarinyar ne tayi dogon suma  mai tsanani shiyasa km daman  hakan yana faruwa yayin fist nig.

 doctor tayi shr sannan ta  numfasa tare da yin gyaran murya kana  tacigaba akwai wasu dalilai   guda uku  da zai iya  mace takasance 'cikin irin wannan yanayi Na dogon .
May be ko taki  yarda da mijin nata  ko shi mijin yafi karfinta kinsa kowane nmj da irin tasa  halitar da Allah yake masa  to idan akaci sa'ar mace ta hadu da irin .
me wannan babbar halitar km yashigeta da karfi to irin wannan kan  frigita mace har takaita Ga  suma.

 To itama may  radadin Hakan
 ne Yasa tayi   digon suma Wanda a tunani  yakamata ace ta farka zuwa yanzu am sorry to say   gsky  rashin farfadowarta har yanzu  yana da nasaba ne da tablets din da,akayi mata amfani dashi kafin saduwa daita .  
 km  wannnan ba wani  abu  bane mai tsanani inshallahu tunda anshawo kan matsalar zata iya farka at any time  .


Suna 'cikin Haka deeni yashigo office din gabadaya jikinshi a sanyaye yake duban umminsa. doctor tadago idanunta tana kare masa kallo tsab hk kawai jikinta yabata shine mutumin da yayi wannan aika aikan .
ummi ta juyo  itama tana kallonshi tare da  watsa masa Harara me kashigo yi?
 ko an nemeka ne anan  oya get out ... Ummi Ta fadi hakan tana  Nuna masa kofa fitar  da yatsanta alamun ya fita daga office.
Deeni  ya marairaice fuska  hb first love karki min hk man .
  nace kaje waje kawai  banson ganinka Inda nake.
 kai if possible ma kabar asibitin nan  gabadaya ..jin abin umminsa tace ne  yayi sanadin da zuciyarsa ta tsaya cak ta daina aiki Na wani lokaci tukun tacigaba da bugawa da sauri da sauri  jiyake mgnr ummi ba iya kunnenshi kadai ya tsaya ba har zuciyarsa yake jin komai .
 gabadaya zuciyarsa tagama  jagulewa .
 hakuri kawai  yake son bawa umminsa akan fushin data dauka dashi  amman  yana tsoron tashin hankali dazata sake jefashi ciki .idan ya km furta wata kalma .
ba shakka yasan  ya,aikata  kuskure may girma wanda har takai Ga umminsa bata son ganinsa kusa daita .   shi kansa baisan abinda kuskuren sa zai haifar ba kennan da bai aikata abinda yayi ba. 
 hakika yasan umminsa tana matukar kaunarsa da kaunar duk abinda yake so  zata iya   mika dukan   rayuwarta sbd kaunar da take  masa ,bbu abinda umminsa take so da Gani kmr shi a rayuwarta   amman gashi yau sanadin abinda ya aikata Yasa  ummina tana korarsa   kusa daita.
 take nadamar mara iyaka tashigi zuciyarsa  yasan da bai yiwa yarinyar amfani da tables masu karfi ba da bata shiga halin datake ciki ba .
  muryarsa can kasa kmr mai koyon mgn yace Dan girman  Allah first love kiyi hakuri da abunda nayi nasan nayi kuskure sannan ya juya a tsukwane  ' ya fice daga office din  tare da jin  kanshi wani iri wani iri da kyar yake iya daga kafafunshi .


'Cikin dare nabla ta farka taji duk ilahirin gabobin jikinta sun mutu Ga wani irin  zafi da kasan ke mata.
 lokacin data farka idanun ummi biyu tana zaune kan praymat tana addu'oi  ganin ta bude ido ne  Yasa ummi karasowa da sauri  kusa daita tare da cewa sannu   nabla ya jikin ?

Nablah ta runtse idanunta kawai Dan batasan abinda yasameta ba da har  ummi take mata sannu  ba.
 ita dai ta farga taji kasanta wani iri sannan hannuta daure da drip ..ummi tace ya kike jin radadin jikinki .

Da kyar nablah ta bude bakinta da suke a bushe tace da sauki .

Alhamdulilllahi Allah yakara sauki tana son tmbyr ummi abinda ya sameta Amman bakinta yayi mata nauyi ..


Da safe byn deeni yayi wanka ya shirya yashigo dakin Zeenat yace idan tagama suje hospital Zeenat ta yatsina fuska sannan tace ka  wuce kawai idan Na dawo daga school zan biya DEENI ya wuce kawai batare da wata damuwa ba.


A asibiti din ma koda deeni yaje ya iske ummi aikin   lallabata nablah   akan ta zauna Amman taki sai  hawaye ne kawai  suke zubo mata hade da cewa wlh ummi bazan iya zama bane shiyasa  ummi ta kada kawai  hade cewa sorry kinji nabla inshallahu zaki samu sauki kinji nan badadadewa .
'ahankali' yakarasa shigowa 'cikin  dakin sosai ya gaida ummi ta amsa fuskarta a Dan sake ba kmr jiya ba sannan ya  tsaya jikin bango ya xuba hannuwanshi duka  'cikin aljihun wandonsa yana dubanta batare da yayi mata sannu ba  .
A ranshi yace Dan two hours din danayi akanki  Ina aiki ne  shine duk kika dawo   hk lallai yarinyar kina da aiki fa ..

kuka sosai nabla take tana rokon ummi  Dan Allah ummi kikiramin  auntyNa  ko mamana naji muryarsu wlh Ina jin ajikina  mutuwa zanyi deeni dake tsaye Idanunshi akanta har lokaci  kadan yarage dariya ta kufce masa gabadaya duk ta dawo wata kala .


Ganin kukan datakeyi ne Yasa ummi cewa ya isa hk kibar kuka Haka kar wani zazzabin ya sake rufeki .
zankira miki auntyki Amman ba yanzu ba sai kin kara samun sauki kada taji muryarki hk.
 kisa hankali yatashi da wannan kukan naki   ummi nagama fadar haka ta fice daga dakin zuwa office din doctor .

 'Ahankali' nabla tacigaba da kukanta tare da jin radadin ciwo sosai akasanta Wanda ta rasa dalilin jin  hk .

 'A sukwane ' DEENI yasoma daga kafafunshi yana takowa 'ahankali' har yazo gabanta ya tsaya .. idanushi kyam  akanta , nablah dake kuka har lokaci ta dan tsagaita kukan nata  jin tsayuwarsa a gabanta.take numfashinta yasoma kokarin barin gangar jikinta tarasa yadda zatayi da rayuwarta    da kyar tasamu   numfashinta ya dawo daidai .
km har lokaci deeni Na tsaye akanta  batare da yace daita komai ba.
 Sai ma rikitattun idanunsa dayake binta dashi  duk   sai yaga ta sake  ramewa idanunta suka sake fitowa waje  Sosai .. kyakywar fuskarta tayi fayau daita  alamun tana 'cikin tashin hankali da damuwa ..
yarasa abinda yakamata yayi.
 sannu zai mata ko km cigaba zai yi da kallonta .

Jin kanta Yayi mata nauyi ne sbd  tsayuwar da Yayi mata kai Yasa   ta dago shanyayun  idanunta masu cike taf da Hawayen  karaf idanunsu suka sarke cikin juna zuciyoyiinsu ne suka buga a lokaci daya itace tasoma kokarin dauke idanunta gefe tana shesheka .. shiiiiiiiii kin cika min kunne da Wannan bazan kukan naki ,ji yadda kike wani bude baki kmr wata  stupid kina wa mutane kuka.
Kukan naki ma  abin  kazanta mtssss yaja tsaki may tsawo wlh tun wuri ki warke daga wannan ciwon naki Na iskanci  kada ki saka min uwa 'cikin  zarriyar jinya .

Ta juyo a fusace tana watsa masa wani irin mugun kallo may tattare da tsansar tsana tace  Dan Allah Ni  malam rabu dani  Ina ma ruwanka  da ciwona .
wlh kama damu dani tunda har kazo Inda nake batare da an gayyatoka  , mtssss taja tsaki.

 Ni kike jawa tsaki dan ubanki ya fadi haka yana Nuna kirjinsa  da dan  yatsansa ta sake  juyo idanunsu suka saje sarke wa cikin juna ta dade tana kallon kwayar Idanunshi Wanda Hakan Yasa zuciyar deeni  bugawa da sauri .
har 'cikin jikinsa yake jin idanun nata .
'Ahankali'  ta  watsa masa wata uwar  harara sannan tace eh an jamaka tsaki ubana ne kai dabazan ja maka tsaki ba mtssss mtssss mtssss  ta sake jan wasu .
Hankalinsa a tashe  ya matso sosai kusa daita har tana jin saukar  hucin numfashinsa ajikinta .
tayi saurin  kau da kanta gefe tacigaba da kallon  Window dan gaba daya atsorace take dashi karfin hali ne kawai irin nata dan jikinta har rawa rawa yake .
'ahankali'  ya Miko  hannunshi yana shirin damkar  lips dinta.
 ummi ta turo kofa tare da sallama cak ta tsaya  tana dubansa ..
'Ahankali' ya dunkule hannushi ya tura cikin aljihun wandonsa yasoma ja da baya da baya har  yakoma Inda ummi tabarshi dazu yacigaba da tsayuwarsa  yana tunanin abinda yakamata Yayi yarinyar Wanda zaisa tasan shi din ba abokin gwabzawarta bane.
 ya furzar iskar may zafi ta bakinsa sanda zuciyarsa tace ka manta da wannan bazar yarinyar . Ka nemi 
 yadda zaka  shawo kan umminka kawai ..
Numfasawa    ummi tayi  byn tagama  kallonsu sannan  takarasa  shigowa dakin ta zauna kusa da nabla tana yi mata.

Tsawon lokaci  deeni ya dauka tsaye kafin daga baya ya  dubi inda ummi take  ya sauke ajiyar zuciya sannan yace  ummi Ni zan wuce office daman naxo Na dubaki ne .
   atakaice ummi tace ok Allah  Ya tsare.
 da murmushi ya amsa da Ameen ummina nagode  Sosai da addu'ar ki gareni  .
Allah yakara miki hakuri dani . 
Ya fita yana jin  dadin ganin yadda fuskar umminsa ta sauya ..

Hk ma koda yaje office bini bini zai kira yaji yadda suke.
Hk ma  Zeenat  tazo duba nabla sai dai a tsaitsaye dan ko cikakken minti goma batayi ba wuce shima sbd ummi tazo if not bbu inda zata dan wata common hause girl.

su safeena da laraba ma sun zozo Dan Kusan tare suke zuwa kawowa ummi abinci .. .


Daga office DEENI bai koma asibiti ba.
  gida ya zarce dan kada ma yarinyar ta dauka  sbd ita yaje .

Yana   Yashiga part dinsa wanka yayi ya daura alwala ya gabatar da sallar asr ya shafawa jikinsa lotion may dadin kamshi  tare da mulke sumar kanshi da mayyuka iri iri masu sa taushi .
ya sanya kananan kaya ajikinshi  wando three quarter da Riga hamles ya dawo parlour,sa ya zauna tare kunna AC ya kwanta yana kallon tashar CNN idanunshi ne kawai akan TV Amman hankalisa gabadaya yana gurin nablah tunanin yadda yaborata a asibiti kawai yake dawo masa yana masa yawo a brain dinsa .
Dan cinza lip's dinshi yayi kadan.
  daya tun sanda yake sarrafata jiya akan bed  da yadda ya dinga jin nipply dinta Na fitar da wani dadi sanda yake tsotsarsu.ahankali yakai hannushi ya Dan shafa sumar kanshi.
 sosai ya lulawa 'cikin duniyar tunani tare da sake tuno moment din da sukayi Having.
 bai ankara ba yaji kiran sallah magariba da sauri ya Mike ya fada bathroom yayi alwala yazo ya zira jallabiyarsa brown colour ya tafi masjid .. 

daren ranar da kyar deeni yasamu bacci duk tunani halin da nablah take ciki ya adabi ruhinsa da gangar jikinsa tare da hanashi sukuni say da dare ya tsula sosai sannan yasamu bacci barawo ya dauke shi .

da safe ma Haka nan yasamu ya shirya ya tafi office da kyar yake aiwatar da tarin ayyukan dake gabansa duk Inda ya juya baya jin dadin rayuwarsa .. yabar abinda yakeyi  yayi shr kawai  yana zance zuci da zuciyarsa .
Meyyesa meyyesa nake yawan tunanin wannan bazar mara kunyar  yarinyar   ?
Take zuciyarsa ta bashi amsa da.
 sbd abinda kayi mata shiyasa Ya girgirza kanshi kawai ya dinga  fidda numfashi sannu sannu .



Satin nablah 1 asibiti aka sallamosu  Dan bbu laifi   taji sauki sosai sai dai takan Dan ji radadin  zafi ciwa  kadan kadan  akasanta .

ummi ta daukewa duk wani  aikin komai Na gidan  tace Sai ta kara  warkewa sosai .

duk wanna abunda ummi take yiwa nablah kwata kwata  bai wani   birgeta ba ko kadan  .
Dan ita ba Haka taso ba  .
 tasone ummi takira mata  auntyta tazo ta tafi   daita gida,inyaso daga can bazata sake  ganganci dawo ba ...


Yanzu duk dare ummi sai taje ta kulle nabla a dakinta  sannan   wucewa nata dakin tare da  key .
 da safe karfe goma daidai take zuwa ta budeta.

  km duk Wannan dremar da ummi   take deeni na sane da komai sharewa kawai yayi.
Dan ba  wani damuwa yayi  ba.
Dan    shima bai yi wani  tunanin zuwa Ga yarinyar ba acikin wannan yanayin da,ake ciki ba  .


Manage please banyi editing ba 

MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
     💖💖💖
💗💗💗💗💗





AYSHA A BAGUDO




Page 74 



'sannu ahankali  nablah ta dinga samun sauki sakamakon irin kulawar da ke mata ..
Allah sarki ummi bawar Allah duk wani abu datasan ya dace tayiwa nablah ,amatsayinta Na Virgin  wacce aka akayiwa shigar sauri .
Tayi  wanda ita kanta nablah batasan dalilin dayasa ummi take mata hankan ba .
dan bakaramin kulawa ummi take  bata ba dangane da aika aikan da DEENI yayi mata  .
 dan yanzu bbu inda bata takawa da kafafunta   .

Wanda  hatta kb ba'a barshi a baya ba wajen zuwa duba nablah .
 Tare kayan dubiya daidai karfinshi .Ya Mika mata  ledar dayazo mata dashi may ruwan yellow da ratsin baki baki  ajiki .

'Ahankali' nablah Tasa hannuta ta karba hade dayi masa  godiya  jin dadi.
 koda bata bude ledar ba idanunta sun gama gane mata abinda kB yazo mata dashi 
,kankana ce da ayaba sai abarba a 'cikin ledar.

 Yayinda  hakan  yayiwa nablah dadi Sosai a zuciyarta hakan km har 'cikin ranta taji kb ya birgeta matuka.
 dan Haka ta sake sakin jikinta dashi sosa suna ta hirarsu 'cikin Nishadi da annashuwa .

'cikin Haka deeni ya dawo daga office on expected ya gansu tsaye abunsu hankali kwance   suna  sheka dariya yayinda kb ke tsaye da kodadiyar wandon Jeans da rigar polo tsab dashi  .
 Dan Shima gayen  bbu laifi   yana  nashi kyau daidai gwargwado ..
sai dai ina ..kwata kwata Bai  kamo kafar DEENI  da  komai Na rayuwar duniya ba.

wani irin buguwa kirjinshi yayi da karfi gaske kanshi yayi  masa nauyi tamkar zai tarwatse sakamakon ganin nablah da kB da Yayi tsaye sunawa juna murmushi.

Mamaki da tashin hankali ne suka caki zuciyarsa a lokaci daya.
Ahankali yacigaba da takowa 'cikin takunsa Na kasaita da jin shi wani ne. 

Ta kasan idanushi yake kare musu kallo tsab tare da sake  mamakin yaushe ne  shakuwa  may karfi irin hk Yashiga tsakaninsu batare da da sanin ba .

har yazo kusa da Inda suke tsaye Amman basu lura dashi ba.
  " Sai daya zo daf  da shige su ne nablah taganshi .sbd fuskarta dake facing dinsa .
 tsam.. Tasha   jinin jikinta da irin kallon kasan idon dayake aiko musu .
Dan Haka batare da wata damuwa ba dan matsawa kadan  domin bashi hanyar wucewa.
 dan dama  tsaye take abakin kofar da zai Kai mutun main parlour din gidan.

 har yashige  ciki idanunshi basu daina hango masa ita Tare da wani nmj   tsaye   Wanda bashi bane.

 kai tsaye dakinsa ya nufa ya bude fridge ya ciro ruwan   faro  may tsanyi .
 yakafa robar abakinsa yasoma Sha  bai ajiye ba Sai daya shanye ruwan  Tare da yin flinging  da robar gefe  ya sauke naunauyen ajiye zuciya  .
 yaje ya kunna AC da TV kana  ya zauna  kan kujera  yana fidda  numfashi sama sama gabadaya duk wani farinciki daya dawo dashi gidan"  ya nema ya rasa.

 zaune Kai yake  akan kujera yana aikin jijiga kafafunsa a kasa tare da xunduma kanshi 'cikin  tunani na  gaira ba dalili .

Shr yayi tare da   xubawa TV parlour,sa , idanu kawai .Wanda idan ba tsayawa, kayi masa   kallon tsab zaka dauka a zahirance abinda  da'ake gabatarwa a TV yake kallo ...sai dai abun ba hk bane .
Idanunshi ne kawai  akan TV Amman hankalisa gabadaya  da tunaninsa  yana waje inda ya baro nablah tare da wani   .wani ma wanki gidansa...

A zuciye ya furzar da wata iska may zafi yana jin haushin kansa da kansa .
 taya  zai zauna akaron banza kawai yana tunani yarinyar da Bai da tabbas din cigaba da rayuwa daita .... amman duk da Haka abinda yaki bacewa a idanushi .... to me hakan yake nufi ?
 meyasa naji  bbu dadi sbd na ganta da kb yaje howa zuciyarsa tmby ?

Take zuciyarsa tabashi amsa da sbd aurenka da yake kanta.
Ai ba ita kake tunani ba   . aurenka kake tunani km shine musababin dayasa kaji bbu dadi a ranka . Ahankali ya runtse Idanunshi tare da hura iska ta bakinsa ..
tsawon lokaci ya dauka  zaune a gurin  yana aikin saka da warwara .

  kiran sallah magariba ne ya maidashi 'cikin natsuwarsa ya Mike jiki a sanyaye ya shige bathroom yayi wanka Tare da dauro alwala ya saka jallabiyarsa ya nufi masjid .
ba shi ya dawo gidan ba sai byn sallaar isha'i.

 yana dawo ya tadda su ummi tare Zeenat suna hira .

Zeenat na ganinsa ta Mike tsaye  tana zuba yauki tamkar zata shige jikinsa.
 tace har kadowa my hrt  sannu da zuwa ya nufi dining area ya zauna tare da amsa mata  kawai dan har lokacin zuciyarsa cike take  da almara da wasiwasi iri iri.. 

 'ahankali' Zeenat ta iso inda yake zaune sai kamshi take zuwa ta koina ka kalleta ta hadu iya haduwa bbu makusa ahankali ta duko wajen kyakywar fuskarsa  tabashi peck a daidai dimple dinsa  sannan  tasoma bude kuloli dake ajiye akan dining table.
 miyar  banga soup ne acikin   kula .  Sai dayar kular data bude shi km  ferfesun cat fish ne dayasha kayan piece da Curry   da tuwan shinkafa ta zuba masa tare ajiye masa a gabansa  ta zauna kusa dashi tana dan jansa da hira sama  ganin yanayin da yake ciki Wanda hakan  yana Nuna mata alamun yana 'cikin damuwa . Yadda Zeenat ta dinga masa Yasa zuciyarsa tsanyi har ya nema kashi hamsi 'cikin damuwarsa yarasa .

 bawani cin abinci kirki yayi ba sosai sbd yanayin da  zuciyarsa take 'tattare da kunci . Har yagama cin abinci idanunta Na kashi ta sake tsareshi da idanunta muryata a raunane tace  har ka koshi kennan? Bai amsa mata ba sai dai girasa  daya, daya dage mata Al,amun Haka uhm  ..
tayi murmushi kawai a ranta tace  komai yayi kyau yake masa.
 bbu abinda  zaiyi a rayuwarsa da ba zai masa kyau ba, hatta bata rai idan DEENI  yayi sai taga tamkar an kara masa  kyau ne .
shiyasa kullun kaunarsa ke sake mamaye  zuciyata.
 , duniya da abinda ke 'cikin da za'a tmbyeta abinda tafi kauna da son kasance tare ,byn soyayyar Allah da manzonsa the next thing is her husband  .. a tare  suka Mike ta kamo tafin  hannushi 'cikin nata tana murzawa ahankali ahankali . ta nufa dakinta  dashi.
 Bai mata musu ko wani  ja in ja ba ,Dan Shima zai fi son kasancewa tare daita .kodan halin damuwar da yake ciki ..har suka shigo 'cikin dakin hannusu Na 'cikin juna .. a tare suka zauna idanunta 'cikin nasa Shima ita yake kallo da rikitattun idanushi still har lokacin hannusu Na sarke da juna.

 muryata a sanyaye tace my hrt meke damun zuciyarka  duk sai naga kmr  kana 'cikin damuwa?
Yayi shr kawai batare da yace mata komai ba .
Ta sake kwantar da murya   please now  tell me what's wrong with you Dan Allah karkace min bbu komai ko rashin haihuwata har yanzu ne ?

Haka kawa ya tsinci bakinsa  da ce mata eh jikinta ya sake sanyi sosai  tacigaba nasan dama  dole hk ya dinga damunka tare da  daga maka hankali wani lokacin, Amman ka yarda dani wlh yanzu bana shan tables  asalima Ni kaina haihuwar nake so a halin yanzu ta fadi hk tare da rungumeshi tsam ajikinta...
 kayi hakuri mijina may nema yana tare da samu inshallah nasan Allah bazai barmu  hk ba kodan  yadda kakasance may taka tsan tsan da dokokin Allah ..sai lokacin ya bude baki  yace may zai hana ki amince da kanki kisamu ummi akan kina son Na kara aure take sauran farar dake fuskarta ta dauke dip ...gabadaya duk wata annuri dake fuskarta ta dauke ..kana kallon yadda kishin mijina ya Muna baro baro a idanunta jikinta a mace  tace hb my hrt da kaina zan je nace a min kishiya ta girgirza kanta kawai kaima kasan  wannan ba abune may   yiwu ba.. takarasa fadar Haka tana may shigewa 'cikin jikinsa tasoma taba wasu gurare ajikinsa Wanda tasa yana saurin hawa net work..
" kokari son yin mgn yake Amman Ina ahankali ta janye hankalinsa da kalolin salonta tare da mannewa ajikinsa sosai suka shiga murzar junansu suna cire juna kayan jikinsu har zuwa  lokacin da komai ya wakana  tana rungume ajikinshi tana zuba masa shagwa ..shi kansa  yasan yasamu kulawa daga matarsa Amman hk Bai hanashi tuno yadda yaga nablah da kB ba ..a dakinta Yayi wanka tsarki da zai wuce dakinsa ne tace my hrt ka kwana anan man.
 ka kwana biyu rabonka da kwana a dakina.
 sai dai kaxo ka wuce Yayi murmushi gefen baki tare da cizan lip's dinshi kadan  sannan yace sorry  akwai abinda zanyi ne a dakina idan km zaki bini ne oya.. let's go .
ya fadi hakan yana may Miko mata tafin hannushi har Mike tana kokarin kamo hannushi 'cikin nasa sai km  tace kashiiiiiiiii yi tafiyar kawai Na tuna  nima karatu zan kwana yi dan Ina da test gobe ... ya daga kafadunsa al,amun I dont care .. ahankali Ya juya tare da  wuce dakinsa .Ko byn dashiga dakinsa ya kammala abinda zai yi ya zube kan makeken royal bed dinshi. Ya runtse Idanunshi gam Dan son yin bacci ..


daren ranar da kyar deeni yasamu  runtsawa  duk ta Inda ya juya nablah  yake Gani tare da kB gabadaya ganin da Yayi musu ya addabi ruhinshi da gangar jikinsa tare da hanashi sukuni.
Bacci yafi bukatar yi akan tunanin banzar daya tasashi gaba .
Amman abun yagagara  say da dare ya tsula sosai sannan Allah Ya taimakeshi bacci may cike mafarkin yarinyar iri iri  ya dauke shi .

Washegari da safe ma a kasalance .deeni Yayi shirinsa tsab  Na zuwa office 'cikin  haddiyar suite ash colour sai kamshin turare  yake xubawa .

ya nufi dakin ummi suka gaisa duk  da zuciyarta cike take da jin haushin abinda tilon dan nata yayi.
 Amman hakan bai hanata yi masa addu'ar data saba yi masa a kullun ba .
Allah Ya tsare min kai a dawo lfy. Hakan yayi masa dadi Sosai har yaji zuciyarsa ta sauya tasamu natsuwar dayake bukata...
 yace Ameen my first love .
fuskarshi dauke da murmushi farinciki Yashiga dakin Zeenat byn sun gaisa yasha coffee a tsaitsaye yabawa Zeenat peck a goshi ya mata sallama itama addu'a tayi masa .


Ya fita escort dinsa suka takama masa baya suka fice daga estate din.

 sunzo daidai jakonde first get zasu dauki hanyar da zai sadasu da obalende kawai deeni  ya tuna da  Yayi mantuwa wasu document a dakinsa .
 km bazai iya  tafiya aiki batare  document din ba   dan Haka ya Dakar da sule direbansa .


Sule park here I need to go back home  have  forget some document at home you  go ahead with the escort I will be there later .
 "sule yace boss mai zai hana kabari Na kai ka gidan ka dauko ko km  ka Kira madam so that Ni sai nakoma Na amso   maka  ba Sai kayi driving da kanka ba.
 
 daidai deeni ya Mike da niyar fitowa daga motar ya dawo ya zauna wata katuwar harara deeni ya wurga masa 'cikin tsawa yace dan Allah Malam Ni fitar min a mota jakin wani gari ne  kai ? Kai zaka  gaya min abinda ya datace dani . Ko umarnin dana baka ne ba zaka iya bi ba ..yakarasa fadar yana may jan tsaki.
 sorry boss sule ya fadi Haka da sauri Dan yasan halin may gidan nasa.

 deeni ya sake jan tsaki Sai daya gama shan kamshinsa ,tukun ya fito daga byn motar Wanda tuni sule ya dade da fitowa daga 'cikin motar deeni Yashiga deriving seat tunda ya fige motar bai tsaya  ba Sai gida .


Yana shigowa  gidan  da nablah yasoma cinkaro hannuta rike da plet ta nufi kitchen bayanta yabi da wani irin kallo .

 tare tsaida idanushi kyam akan   west dinta sakamakon karamin hijab din data saka Wanda  Bai ida saukar mata ba.
Har takarasa shigewa  kitchen din rikitattun idanushi Na kanta.
 sake balance yayi yana kallon each  and  every step dinta yana mamakin yadda take tafiya 'cikin tsanyi jiki tamkar an tsamota daga'cikin ruwa. jin gabadaya yanayinsa yasoma samun sauyin reaction may tsanani . Yasa  a rikece yayi saurin dauke idanunshi akanta dan bazai iya jurar cigaba da  kallonta irin hk  ba .

 A hankali yakamo lips dinsa Na kasa yasoma tsotsa da iyakacin karfinsa yayinda  yake  sake jin yadda gobbin jikinsa suke narkewa tamkar ana watsa masa ruwan tsanyi .. da kyar yasamu ya dawo 'da natsuwatsa cikin gangar jikinsa sannan yasamu damar   hayewa  saman dakinsa.
 ya dauki  document din daya maido shi ya fito daga dakinsa.

Daidai nan itama nablah ta fito daga kitchen  ta soma kokari  taka step atare suka daura kafafunsu .

Daura kafafunsu yayi daidai da bugawar da zuciyoyinsu yayi atare Wanda kowannesu yaji wani irin shock Na musamman   ajikinsa.

 ahankali ahankali suke taka step din kowannesu da tunanin dake   zuciyarsa da yake .
  

Kwata kwata nablah  bataji wani tsoro ko fargaba a ranta.
 Na  rashin  bashi chance din wucewa ba har kafadunsu Na neman gogar juna tayi saurin   gucewa.
  take zuciyar DEENI tayi wani irin razananniyar bugawa da sauri tsam yayi da ranshi yana mamakin jarumta da karfin halin irin na yarinyar kwata kwata bata shakkarsa ballanantana ta Nuna alamun   jin tsoronsa .

har yakarasa saukowa daga step din zuciyarsa cike take tap  da tsansar al,ajabinta .


Da sauri da sauri ya tafi office sbd yana da meeting karfe shadaya daidai gashi yabata lokaci a gida yana hawa sama.
 Kingsley ya bude masa kofar office dinsa yace sir everyone is present they are all waiting for you .
 Sai da DEENI ya duba agogon Rolex din dake daure a tsintsiyar hannushi sannan yace Ok let's go.


Meeting ya dauki sama da awa uku ana tautaunawa inda Mayan ma'aikata companys din ke tashi  daya byn daya suna fadar albarkaci bakinsu da irin cigaban da companys tayi .
da km matsalar da company take barazanar fuskanta ta hanyar handame wasu makudan kudade sama da billion dari Wanda km ana suspect din wasu daga 'cikin aminan mahafin deeni dine suke da hannu aciki .

Zaune kawai deeni yake yana sauraron kowa daya byn daya " byn yagama sauraron komai daga manya worker's din company's ya numfasa Tare da cewa duk wannan ba wani matsala bane . zansan yadda zanyi handover din komai. Sai duk Wanda Na kama yana da hannu a ciki  bincikena   sunansa sorry .

Deeni Ya koma office dinsa domin gabatar da  ayyukan da dake gabansa .


Yana 'cikin aiki   fk yashigo ya bashi hannu suka gaisa Tare da zama yace aboki meyye sirrin ne ?
Naga kwana biyu nan kanata walwala da Nishadi please let me know the secret ..

deeni ya dago rikitattun idanushi ya zuba masa kawai  yana masa wani irin kallo sannan yace Kai fa dan iska  yaro ne wlh  .
Meyasa kafiye samun ido  ne akan lamarina?
 
dan Allah mlm let get down to the business fk yayi murmushi ya  mutun yaga sauyi bazai tmby ba.

 A said  let get down to the business deeni ya sake maimaitawa   take suka fara zance aiki tunda daman abinda yakawo fk din  kennan byn sun gama aiki fk yakoma office dinsa  .


Fk Na fita deeni yaso cigaba da aikinsa Amman yakasa Sai ma lulawa da Yayi 'cikin duniyar tunani 'ganin yakasa aiwatar da koma ne Yasa ya Mike ahankali' ya koma kan doguwar kujerar dake office dinsa ya Mike Tare runtse Idanunshi ya dafe gashinsa da hannusa daya yayinda dayan  hannushi ke sama ruwan cikinsa   sannu 'ahankali' tunaninsa yasoma canza salo zuwa wani guri Na daban sosai  ya sake runtse Idanunshi gam .

Da gudu nablah ta fito daga bedroom hannuta rike da doguwar rigar dake jikinta ta nufo inda deeni ke zaune yana kallon ball ta fada jikinsa tana xuba masa shagwaba iri iri.
 bbu shiri Yayi wurgi da remut din hannushi ya sake janyota  jikinsa sosai ya matseta gam yana shakar daddaden  kamshi turaren jikinta  har ya bude bakinsa zai yi mgn tayi saurin hade bakinsu waje daya tashiga tsotsar bakinshi .

tsawon lokaci ta dauka tana sarrafa harshenta 'cikin bakinsa batare da ya katseta ba .
Wani tsutsa takewa lips dinsa tare da  taba duk inda hannuta yaci karo dashi ajikinsa. 
gabadaya tagama rikita masa brain da salonta daga byn ta Kamo hannuwanshi duka ta daura a saman kirjinta tana lumshe masa shanyayun idanunta .
 Ai take oga deeni ya dimauce a sukwane ya tura hannushi 'cikin rigarta ya zaro nonuwanta duka  ya daura lips dinsa kan nipply dinta ya fara tsosa tamkar wani tsohon maye  yana lumlumshe idanu .
Yayinda dayan hannushi km ke faman  aikin  murza kan   nipply dinta dayan  Tare son rabata da kayan jikinta ta. langwabewa tayi  a kirjinsa tana lumshe ido ya Kamo lips dinta ya fara tsotsa Tare da cigaba da romancing din ta hanyar cire mata kayan jikinta take itama tasoma balballe masa boturar gaban rigarsa har tayi nasarar rabashi da kayan jikinsa . 'ahankali'takai bakinta kan nipply dinsa tasoma yi masa wani irin tsotsa Na fitar da mutun hankalinsa .
daga nan komai  yacigaba da wakana nablah tayi matukar gigita shi da salonta gabadaya tagama rikita masa lisafi byn komai ya daidaita yana kamkame daita ajikinshi kuka yake mata tamkar wani karamin yaro I love you beelah ....you are the besty woman in this world and you are the only woman I loved pass please tell me did you loved me ya fadi Haka yana may Kamo fuskarta da hannuwanshi duka yana kallon 'cikin  kwayar idanunta.. 'ahankali 'ta kada masa kwayar idanunta tare da  yamutsa fuskarta alamun A,a .
 , Ai take ya gigice ya sake marairaice murya please now beelah tell me you love me....


kaiwa deeni wawan duka da fk Yayi ne  Yasa shi  farkawa da sauri daga dan baccin daya soma yi deeni ya Mike zaune Tare da shafo gefen fuskarshi da hannushi yana kallon fk tsaye bisa kanshi  ..

A tsorace fk yace Kai Dan iskan wani gari ne ?

 office din ma  jaraba kakeyi har  da irin wannan  sambatun.. wacece km beelah ....?

kallon mamaki deeni ya sake  bishi dashi can km  jikinsa a sanyaye yace I don't know .

dan Allah mlm karka rana min hankali man ya kana mafarkin  yarinya har kana saduwa daita a mafarki kana mata kuka ta soka .... Amman kace min  wani I don't know.i don't know din shegiya 
Dan Allah malam kasanar dani 
 wacece wannan yarinyar datayi winning din heart dinka hk?
  fk ya sake jiho masa wata  tmbyr data razana zuciyarsa .
,take gumin dake tsaftsafo masa yasoma digawa yana bawa lungu da sako na gangar jikinsa hankalisa a tashe yake  duban fk....

  Kukan dana tarar kanayi  aciki mafarkika   ya  Nuna min yadda  ka afka 'cikin tafkin kogin soyayyarta please tell me wacece  wannan yarinyar may sa'a   data yi winning din xuciyarka Haka?
 deeni yashare gumin daya rufeshi sannan muryarsa a kasalance yace dan Allah mlm karabani da zance wata yarinya nace maka bansani ba. 
 km wlh karka sake  Damuna   da zance wata yarinya can .
   yana gama mgnr ya Mike yashige toilet din dake manne da office din sa yabar fk tsaye da mamaki .

Fk ya dade a gurin yana saka da warwara Tare da tunanin iri iri numfashi ya sauke Tare da yin ajiyar zuciya sannan ya bar office din cike da zargin DEENI.


Karfe hudu daidai motar deeni tashiga 'cikin  estate din Tare da motocin escort dinsa dake biye dashi a baya .

 sule ya daidaita tsayuwar  mota yayi parking kana ya fito da sauri ya bude gidan baya Inda oga deeni ke hakimce abunsa hankali kwance Sai da yagama  shan kamshinsa sannan ya yunkura  ... fitowar nan dazai yi idanunshi suka masa arba da abinda ya kusan tarwatsa zuciyarsa da gangar jikinsa .
abinda yake ji ajikinshi  ba iya zucitarsa kadai ya tsaya ba har cikin kwalkwaluwarsa .. idanunsa akansu kyam  nablah ce tsaye da kB  may wanki .. tsaye suke  murmushi kmr wan karan   tare da mgn Wanda baisan abinda kB din yake fada mata ba Wanda koda yaushe idan yagansu tare take yawan murmushi da farinciki..

cike da  karfin zuciya yakarasa fitowa daga 'cikin motar   yana gyara suite din  jikinshi yasoma bada step 'cikin kunar zuciya yayinda gabadaya Hankalinsa ya tattara garesu.....


Can bangarensu  nablah kuwa ahankali suka cigaba da hirarsu yayinda kB din ke kokarin fahimtar  daita sirrin dake  zuciyarsa ta hanyar ce mata gsky mlm nablah kina  matukar birgeni da yadda kike kama kanki a 'cikin estate din nan.
 sabanin yadda naga sauran ma,aikatan estate din sukeyi   .
Tayi murmushi kawai tare da cewa Nagode da yabawa
...uhm Ai  godiya kadai bazata wadatar da zuciyata ba facce.
 Idan 
 ki amince min da abinda zuciyata  take son sanar dake ..
Ta sake yin  murmushi har wushiryarta ta bayyana Wanda hakan yabawa asalin  kyawun fuskarta fitowa fili .  sannan tace meyye shi abinda zuciyarka take son fada ?
Yayi murmushi sosai sannan  ya gyara tsayuwarsa da kyau ta yadda zai sake birgeta sannan ya samu damar amayar da abinda ke ranshi .
kalma  daya ce tak mara wuya gata da saukin fada a baki .
 idan har ta miki zaki  fahimceta da  saurin km tayi tasiri a zuciyarki  gabadaya nablah ta tattara duk wata nasuwarta  gareshi yayinda zuciyarta ta bukatu kwarai  da son jin abinda zaice mata  tare da addu'ar Allah Yasa ba abunda take tunani bane yake son sanar daita ..uhm Ina jinka daidai lokacin da bai fi taku biyar deeni ya iso garesu ba km duk kusan mgnrsu takarshe acikin kunnenshi suka fadawa.

 kB  yacigaba  abinda zuciyata take son  fahimtar dake  sai km harshensa ya harder yasoma   in inna yace Ina ...Ina sonki......

 
 zafin zuciya da buguwar zuciya ne suka tasowa DEENI   alokaci guda..

 deeni ya runtse Idanunshi gam yana jin yadda zuciyarsa ke tafarfasa dan dama tuni ya yafara zargin Haka atsakaninsu tun kallon da yaga yaron yana mata a kwanakin baya .

Gadabada idanuwansa sun gama rufewa ya karasa gurin zuciyarsa tamkar zata tarwatse bai tsaya wata wata ba ya dauke kB da wani gigitaccen mari take jini ya balle ta hancinsa ta baki ..
 a frigece kb ya dago yana duban daga Inda saukar marin ya fito  ogansa ya Gani tsaye a gabansa tamkar mashi wani duba yakewa boos din nasa  tare da neman dalilin jin saukar mari .

 yayinda Shima  DEENI yake binsa da wani irin  kallo may cike da tsansar tsana .
  kana yace tsayuwar me kakewa mutane anan Dan ubanka  gabadaya kb ya rude ya gigice yarasa bakin mgn Sai ma juyawa dayayi da sauri  yakama gabansa ahankali' yake daga kafafunshi da oready sun gama sagewa da mamakin may gidan nasa .


Wani irin zafi ne ya caki zuciyar nablah lokaci da deeni ya dauke kb da mari batare da Yayi masa komai..
 tayi saurin runtse idanunta hawaye takaici suka zubo mata. wa tunaninta haushinta da deeni yake ji ne  ya shafi kB mutumin da bbu ruwansa km yasan martaba da mutunci  mutane ba kmr shi ba .
daya kasance mugu . Wanda kowa   wulakantace ne a gurinsa.


Bata ankara ba taji ya fixgota da karfin gaske ta dago shanyayun idanunta tana kallon  deeni dasu Wanda   gabadaya kamaninsa da yanayinsa  sun gama canzawa .

Ta  bude bakinta zatayi mgn a zuciye ya dauketa da mari wanda yasata durkushewa agurin tana kuka da takaicin kasancewarta a cikin gidan tadoma tirjewa da son kwace hannuta garesa ganin hk  yasoma janta yana kaiwa tsakiyar parlour gidan yayi wurgi daita  yana fida numfashi  Allah yaso bbu kowa akasan gidan .

muryasa a hassale yace dan ubanki an gaya miki  kofar gidana wajen  dandalin  soyayya ne .. ta Mike da kyar tana dafe da gefen cikinta zuciyarta tamkar wuta Dan takaici abinda yayi mata kana tasoma mgn 'cikin daga murya kofar gidan naka wata tsiya ce  daba za a iya zama ba 
.....Ta karasa fadar Haka tana jin mugun tsaki ..

a fusace ya 
   nunata da yatsansa wlh  Na sake ganinki da wannnan dan iskan yaron a kofar gidana  zan kasheki da hannuwana .
ya cure  hanuwansa  waje daya kana  ya waresu tare da  Nuna mata yadda zaiyi daita.

 nablah ta zaro idanu waje tana kallonsa jin kalmar zai kasheta da hannuwanshi..
Ok baki yarda ba ko try and see..Ta tsaya sororo tana masa wani irin kallo may cike da tsansar tsana  ita fa zuwa yanzu tafara tunanin mutumin dake tsaye a gabanta ya fara samun tabin hankali ko km daman can yana da tsohon ciwon hauka Wanda ita bata sani ba ....a zuciye yasa  bayan hannushi ya  buge mata baki ashe mgnr zuciyata ce ta fito fili ....
Ya daka mata wata razananniyar tsawa  da karfi gaske.
 Wanda ya kusan tarwatsa zuciyar nablah Dan tsoronsa daya soma shiga zuciyarta .. Ni ne mental ya fadi Haka ya Nuna kirjinsa da yatsansa  tayi saurin girgirza masa kanta well...zaki san mental ne Ni Sai ranar dana sake ganinki da wani Kato a kofar gidana .. nabla  ta  sake durkushewa a kasa ,cikin azaba kuka  Amman  Haushin wulakancin da DEENI Yayiwa kb  yafi radadin marin da Yayi mata da bakaken maganganun sa gareta. 

*Afuwa afuwa afuwa kuyi hakuri da rashin jina kwana biyu .. hakan ya faru ne sakamakon rashin lfy danake fama dashi Wanda ahalin yanzu sai dai nace alhamdulilllahi  domin  bangama warkewa ba karfin hali ne kawai Dan Haka  zaku daina jina ol the time please Ina bukatar adurku* 😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭




MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO





*I really appreciate all my fans and all washers that called me when am sick thank God I recoved  God bless all , and  I pray for the people that are sick may Almighty Allah liet there wings up Ameen I so much loved you  fans remain bless  once again i appreciate all ur effort on me*🤝🏻🤝🏻🤝🏻 


Page 75




 A zafafe  Ya qakaraso har zuwa inda take a durkushe sbd yanayin  takaicin da yake ciki.
  'dan bakaramin  yamutsa masa tunaninsa tayi ba musamman lokacin daya daura idanushi akanta  tsaye  da kB.
 ji yayi kansa nayi masa wani irin Sara tamka zai rabe gida biyu .
zuciyarsa kuwa zafi take masa tamkar zata kama da wuta.

   Kuka take  Sosai Na fitar hankali.
 may taba zuciyar ma'abocin sauraro kallo daya zakayi mata kaji  tausayinta ya tsargamaka km duk rashin imaninka idan kaga  halin datake ciki wlh  Dole ka tausayawa rayuwarta .
  

 A halin da take ciki bata  tunanin duk duniya akwai mutumin data tsana da kin gani ......sama da mutumin dake tsaye a gabanta   ...

 Kukanta da halin datake ciki ko ajikinsa "asalima kwata kwata  bai damu ba.
km bai jin ajikinsa  Hakan zai zama damuwarsa sai ma tarin haushinta da takaicinta dake daskare a kasan rashin  .
gyara tsayuwarsa  yayi sosai tare da rungume hannuwanshi duka a saman fadadden kirjinsa ya zuba mata rikitattun idanushi yana kallon yadda take kuka , kusan minti Goma ya dauka tsaye  yana aikin  kallonta batare da yace mata komai ba.

 jin kukanta yaki tsayawa ne yasa  zuciyarsa  cunkushewa guri daya  tasoma dugunzuma     tamkar  ana diga masa ruwan dalma .
Kafin ya ankare  yaji 
Ta sake kara sound din kukanta  may tsanani cin rai da  tsuma zuciyar ma'aboci sauraro  tare da    dagula   lisafi  .


Shr kawai yayi yana tunanin abinda yakamata Yayi gabadaya ilahirin jikinsa sun gama sagewa duk da sanyin AC dake aiki a parlour hakan Bai hana zufa keto masa ta koina ajikinshi, so yake yayi magana Amman km yakasa dan bazai iya yi ba, dan ko yace zaiyi mgnr muryarsa bazata fito ba dan hk Ya runtse rikitattun Idanunshi gam hade da Dan kamo lip's dinshi Na kasa yayita tsotsa  ahankali yana jinta tana risgar kukanta dayaje jinsa  har 'cikin ranshi  .
 baya kaunar ya bude idanunshi ya kalleta cikin yanayin halin datake ciki .
 km bai jin zai iya furta mata  daidai da kalma daya ce  a yadda yake jin kansa 

Dan hk yabarta tacigaba da kukanta wa tunaninsa idan ta gaji  dan kanta  zatayi shr amman Ina saima ji yayi ta kara sautin kukan sosai .
 Ai take  haushinta  may gyaraye da tsansar takaicin abinda tayi masa Ya sake ya harzuka zuciyarsa .
  bazato taji saukar rankwashi a tsakiyar kanta .
Da sauri tasa hannuta ta dafe gurin tare  da sakin wata irin  razananniyar kara Wanda ya farga da ummi dake zaune a part dinta .

 idanunta suka sake kawo ruwan hawaye may  dumi .. ya murde mata kunne da karfin gaske ta sake  saki wata  kara... tare da cewa wayyo  Allahna .... Wayyo Allahna ...wlh Allah Ya isa ban yafe mak.....ai kafin takarasa taji Yasa bayan hannushi ya buge mata baki.
 da sauri ta sanya hannyenta dukka akan  bakin nata tana may zuba mishi shanyayun idanunta Wanda suke cike taf da ruwan hawaye .

Sannu ahankali  ya bude idanunshi fesss suka sauka akan  Kwakyawar fuskarta may cike da haiba yana mata wani irin kallo may tattare da tsansar tashin hankali . shiiiiiiiiiii kawai ya iya cewa.
  ba shiri ta hadiye sauran  kukanta Dan wani irin tsoronsa ne taji  Ya caki tsakiyar  zuciyarta.

 yayinda  gabadaya ta canza  takoma wata kala  daita  abar tausayi  Banda tsine masa da zaginsa bbu abinda take a kasan  zuciyarta ...

daidai wannan lokaci ne 
 ummi da safeena suke saukowa daga upstairs sakamakon jin tashin sautin kukan yaki karewa   km har zuwa time din DEENI   na nan  tsaye rungume da hannuwanshi .

Da sauri ummi takaraso Inda suke  tana tmbyrsa lfy ?
ganin irin  kukan da nablah keyi.
DEENI  yayi shr kawai yaki cewa komai sai ma  cigaba da kallon nablah da yake  batare da ya amsa tmbyr da umminsa tayi masa ba .

 Ahankali ummi ta dago nablah dake durkushe a kasa   . 
tana tmbyrta lfy nablah make faruwa ? Me yayi miki ? Hk  ummi ta jera mata tmby .

 shr kake jin  nabla dan  bbu bakin mgn  sai ma kukan da take risga da iyakacin karfinta  har da shesheka .

Ummi ta sake juyo inda deeni ke tsaye Wanda xuwa  lokacin ya sake gyara tsayuwarsa tare da cire hannushi a saman fadadden kirjinsa ya mai dasu 'cikin aljihun wandonsa yana ciciza lips dinsa .

Deeni....ummi   takira sunansa muryata  a kausashe. Kasa amsawa yayi  tsabar Haushi sai ma idanunshi daya dauke daga kan nablah ya maidasu gareta .
 me yasame yarinyar mutane take kuka irin haka?
 ko wani abu kayi mata ta jiho masa tmbyr a jere ..?

 Kafin yace wani abu sai daya  numfasa tukun sannan ya sauke ajiyar zuciya" tare da   yatsina fuskashi" muryarsa a marairaice may cike da tsansar shagwaba kana   yace Gata nan a gabanki first love ta fada miki abinda akama mata .

 ummi ta bata rai sosai tana dubansa sannan tace bafa nason rashin mutunci deeni ....

Kafita idona Na rufe  ...abinda kayiwa yarinyar mutane kawai  nake son sani ba wanin rainin hankalinka daka sabawa yiwa mutane ba .

 Shima  hade rai yayi Sosai fiyye da dazu sannan yace haba  first lov ya a gaban yarinyar zaki dinga yimin hk  "salon kawai   ta raina mutane byn nima hk naganta bansan abinda ya sameta ba. 

 yana gama fadar hk ya cire hannushi daya cikin aljihun wandonsa" yabar daya ciki  tare da   juyawa ahankali yasoma daga kyawawan kafafunshi yasoma  takawa sannu ahankali 'cikin takun nan nasa  may matukar daukar hankali , Ya nufi bedroom dinsa  .. ummi tabi bayansa da kallon mamaki tana may  tabe bakinta  a ranta  tace rainin km Na nawa...
 


Yana shiga bedroom dinsa yaje ya zauna 'bakin gado yana fidda numfashi ahankali ahankali tare da tunanin matakin dayaka mata ya dauka akan kb da ita kanta yarinya.
a dazu daya gansu ji yake tamkar numfashinsa zai fuzge ne daga gangar jikinsa sbd wani irin radadin azabar daya shigesa ...

Zuwa lokacin tuni safeena ta kamo hannu nablah dake kusa da ummi  xuwa kan kujera tana tmbyrta abinda ya hadasu  da bros dinta. yayinda ita km nablah taki cewa komai sai kuka da take .


Ahankali  ummi takaraso kusa dasu ta zauna itama.
 " tmbyr duniyar nan bbu irin Wanda ummi da safeena basuyi mata ba Amman Sam nablah  taki cewa Ga abinda aka mata sai hawaye ne kawai ke fita daga idanunta ..

tun tana kuka a zahirance har ta dawo kukan zuci .. yadda taga ummi duk ta damu ne.
 Yasa duk  jikinta yayi tsanyi Sosai ta sausauta kukanta tare goge Hawayen idanunta .. jikinta a sanyaye  ta bude bakinta Da kyar tamkar may koyon mgn  takira sunnan ummi ...

ummi ta amsa tare da juyowa ahankali ta zuba mata idanun  kawai  tana kallonta hade da nazarinta ... sannan tace uhm nablah Ina sauraranki mekike son cewa ?
'cikin muryata may matukar sanyi da ban tausayi tace da Allah  ummi  Ina son zuwa gida naga mamana da sauran yan'uwana, takarasa fadar haka hawaye da yayi saura a idanunta yasamu nasarar silalowa  kan  kuncinta .

 ummi tayi shr for the mean time   tana cigaba da nazarinta sannan daga baya tace shine daman  abinda Yasa ki kuka hk ?

Nablah ta girgirza kanta da sauri  tana duban kasa.

  to fada min meyye abinda yasaki kuka ? Ko km  waccen babban kobon ne  yayi miki wani abu?

  muryata a raunane tace a,a ummi bbu komai fa  Dan tasan koma ta fada mata  , abinda yayi mata ba komai za'a yi masa ba ya rigada yacita  bulus..

Shikennan amman zanso ki kara yin hakuri.
 zaki je gida inshallahu Amman ki Dan bani lokaci kadan da kaina zan kaiki har gidan naku  kinji .

kinga yanzu shirye shiryen   zuwa India nakeyi   tare da safeena zamu wuce har da Zeenat.

 ke .. zaki cigaba da kula da al,amuran gidan .
 Da zarar Na dawo  duk da ba'a gidan nan zan sauka ba ,zan koma gidana  zaki je gida kiga family dinki  kinji .

gaban nabla yayi wani irin bugawa da sauri hankalinta yayi mugun tashi   jin abinda ummi tace ta dago ahankali tare da zubawa ummi shanyayun idanunta kawai dan takara tabbatar da abinda taji tace .
Ahankali ta 'cikin hijab dinta  tasa hannu ta  dafe daidai  saitin zuciyarta dake harbawa da sauri da sauri .

 bata jin zata iya zama ita day ranta acikin tanbatsetsen   gidan irin hk may cike da abubuwan ban tsoro "duk da tasan bada laraba za'a ba . amman ,hankalinta yayi mugun tashi  .
Sake kafe ummi tayi da   shanyayun idanunta tana kallonta da kyau yayinda sauran Hawayen  idanunta  suka cigaba silalowa .  kadan ya rage zuciyarta batakarasa bugawa ba.
 sbd rudanin da take ciki   muryarta Na rawa  tace   Dan girman  Allah ummi kiyi hakuri kibarni Na tafi tunda kuma tafiya zakuyi bazan iya zama Ni kadai raina  acikin  gidan nan ba wlh ni tsoro  nake ji takarasa fadar hk wasu  Hawayen  nakarasa  zubowa  tare da hade hannuwata guri daya ta curesu  may   nuna alamun a tausaya mata .....

 safeena dake zaune  ta kamo tafin  hannuta 'cikin nata tana murmushi cikin   hadadden turancinta tace Kai nablah badai tsoro ba wlh.
  kiyi hakuri kiyi zamanki kmr yadda ummi tace bbu abinda zai sameki inshallahu.
Ga laraba nan tare zaku zauna.
  duk kinbi kin  wani frigice  daga jin za'a barki a gida.
 nifa Na dade  da gane wayonki so kike ki gudu wlh , safeena ta karasa fadar hk tana murmushi tare da  duban saitin da ummi take ..

Murmushi ummi tayi kawai Dan tun ba yau ba itama  tasan yarinyar  ta gaji da zama dasu.
 , tun ba'a je koina ba.

 Amman tasan ba laifin  yarinyar bane  .. laifin mutane gidan dake frigitata ..
 "Dan hk ummi tayi murmushinsu irin Na manya kana tace  wai  hk ne nablah kina son ki gudu daga 'cikin family dina?

 take   nablah ta sake rudewa  a frigice take kallon ummi  tana  girgirza mata  kanta . muryata a sarke tace wlh  ummi ba hk nake nufi ba  Ni dai tsoro kawai nakeji.

 safeena ta Mike tsaye sbd  wayarta data dauki kara sautin may dadi  ta nufi dakin ummi.
 tabar ummi da nabla zaune a gurin  suna cigaba da zantawa.


Byn kmr minti shabiyar sai Ga DEENI ya sauko byn ya sauya kayan jikinshi zuwa wasu kananan kaya" masu shegen kyau da daukar hankali.
 wando jeans ne  three quarter da whit top  wanda  gaban riga akayiwa rubutu  da ratsin baki kmr hk   super man  sai kamshi turare ke tashi ajikinshi.
 ta koina ka kalleshi dole kaji  yashiga ranka  . idanushi kyam akan nablah dake zaune a gefen ummi . 

 Ya dan tabe bakinsa sannan ya samu guri ya zauna kan kujera dake  facing din ta ummi tare da dan  zamowa jikinshi  kadan  yana may yatsina fuskashi sannan muryarsa a sanyaye yakira sunan ummi ... first love ....

Ummi Ta  bar abinda take ta dago tana dubansa ya kashe mata Idoshi daya kana yace mata  am feeling hungry... ummi tace  Allah ko? Ya daga mata cike da shagwaba Ok   sai kabari matarka ta dawo tabaka abinci  .

...haba first lov meyasa kike min   hk ne  yanzu ?
Ni wlh Gani nake ma gabadaya kin canzamin kin daina sona da ji dani kmr da .
km nasan shiga tsakaninmu akayi wlh  amman nasan maganin abu yakarasa fadar hk yana sake tamke fuskarshi ...

ummi tayi murmushi ,ta  nan km zaka bullo ?

 Bbu wani ta nan zan bullo ai gsky   Na fada.
Uhmmmm to yake son shiga tsakanin "da" da uwa ?

Mayun dake rayuwa damu  acikin gidan nan ya dan dauke numfashi sannan  yacigaba Allah first love  kinsan dai sarai  banason Amin  kishiya. amman gabadaya sai wani   kokarin kike ki  hadani  da wasu which,s bad .. 
 ummi  tana jinsa har ya  dasa aya amman Tayi  masa banza tamkar bataji shi ba  tacigaba da abinda take .
ahankali km a shagwabe yabar wancen zance  yasoma yiwa  ummi naci yunwa yake ji .. 
Ummi  tasan halin nacinsa km tun da yace yana son cin abinci tasan yuwan oready tagama cinye cikinsa . 

Dan hk  kawai  tace  nabla taimaka dan Allah ki shirya masa wani abu may sauki  kinji diyata ko zai rabani da wannan nacin nasa  ..

DEENI da idanushi ke kan  umminsa  Ya  tsina fuska tare da cewa yanzu first lov  wannan yarinyar ce  zatayi min wani  girki?
   yarinyar da kwata kwata bata iya komai ba.
 ,Kai nifa banason   cin jagwalgwalon abincinta wlh nablah ta dago shanyayun idanunta da niyar kalonsa sbd yadda taji tana sakin maganganu karaf idanunsu suka sarke cikin juna ya watsa mata wani matsiyacin kallo wanda yasa ta dauke idanunta da sauri yayinda  zuciyarta tashiga dokawa    .

wannan km son ranka ka fada  kawai dan kaji dadin bakinka amman mgnr  jagwalgwalon abinci take dafawa karya ne wannan  domin bbu  Inda girki nablah bazai shiga ba a duk  fadin  Africa.
cin jagwalgwalon abinci km sai dai kar a km domin yanzu kasoma   .

dan Allah  rabudashi kinji nabla tashi maza kije ki samar masa  wani abu me sauki .

Nablah ta Mike tsaye amman gabadaya ilahirin  jikinta bbu Inda baiyi sanyi ba ..ita kanta ba,a son ranta take masa wasu abubuwan  ba  darajar ummi kawai yake ci agurinta .
 A sanyaye  ta nufi kitchen "ahankali yabi  bayanta da kallo  yana tabe baki   tunda daman ta gababshi zata wuce km shi yakan so yaga yadda take tafiya kmr an tsamota 'cikin ruwan tsanyi .
  "yana juyowa  idanushi karaf 'cikin Na umminsa sukayi four eyes ..  yayi saurin dauke idanunshi . waskewa yayi tare da sosa  byn keyarsa alamun kunya sai dai ya sake  hade ran nan nashi tamkar yana filln daga ..uhm kawai ummi tayi tana murmushi da girgirza Kai..


 nablah ta dade tsaye a kitchen tana saka da warwara abinda zata daura mishi may  sauki wanda bazai dauki lokaci  ba.
  zuwa can ta yanke shawarar  dafa masa jollouf din cuscus .

ta hada masa haddadiyar jollouf din cuscus  Wanda ta wadatu da kayan hadi carrot green beans da piece koda da hanta a mamadin nama kamshin Curry da tyme ne kadai ke tashi ta barwa laraba gyaran kitchen din ta zubo masa cuscus din shake da  plet ta fito hannuta rike da plet  .
  

Tun daya jin motsin tahowarta gabadaya   Hankalinsa   yakarkata gareta Wanda shi kansa Bai San dalilin dayasa yake jin hk a tare dashi ba.

 har takaraso ta janyo   wata Yar karamar stood  ta ajiye masa plet din abinci akai hankalinsa Na kanta ahankali ta juya zata koma kitchen taji sautin muryarsa ke....... 
Ta juyo tare da dan  tsayawa darajar ummi dake zaune a gurin.
 zoki  kwashe wannan banzar abincin da kika ajiye ance miki Ni jaki ne ?

A ranta ko tace Ai kamafi  jaki hauka agurina .
ya buga mata wata razananniyar tsawa  tsayuwar uwar me kikewa mutane ?

 zuciyar tamkar zata tarwatse tsabar takaici da  tashin  hankali  a kufule takaraso tasoma kokarin daukar plet din ummi tace barshi nablah  yi tafiyarki kawai .

ta juya   ...Ta koma kitchen Inda ta iske laraba tana aikin gyara kitchen tasaka hannuta  tare sukayi komai sunayi suna  hira ..... .

Tsawon lokaci ya dauka zaune yana operating din phone dinsa  batare ko kallon arziki yayiwa abinci ba.
 hakan kuwa  yayi mugun batawa ummi rai" tare da   hassalata .
dan  duk da tsananin son da takewa tilon "dan" nata hakan bazai sa  taga yayi  ba daidai ba ta kasa yimasa mgn .
Dan hk a kufule   tace wannan km  wani sabon salon  wulakanci ne hk ?
Ya dago yana kallon umminsa tare dage mata girarsa daya alamun tmby ?
 minti biyu kacal Na baka ka fara cin abinci nan tun kafin raina, bai Kai Ga baci ba.
 abinda ya tsani ji da gani kennan bacin ran umminsa .
km yakasance shine zaiyi dalilin shigarta halin damuwa .
dan hk bbu wani ja inja ko bata lokaci yasoma tsakurar abinci yana ci tamkar yana cin magani ba dan rashin dadin abincin ba sai dan tsagwaron wulakanci irin nasa.

Nablah na kitchen taji ummi Na kiranta da sauri ta  amsa tare da barin abinda take ta fito.
 ,yauwa nablah jeki dakina dan Allah kicewa safeena tabaki jakata ki kawo min kinji.
  ta juya kennan taji sautin muryarsa ke....dawo ki kwashe wayan nan abubuwan ..dole ta sake juyowa takaraso Inda yake duk ilahirin jikinta  rawa  yake.
 wani irin abu taji ya dunkule mata a kahon zuciyarta ,ahankali tasoma kokari hada kayan abinci data kawo masa wanda bawani cin arziki yayi ba .
  ummi ta dakatar daita  ta hanyar cewa   barshi nablah karki hada komai agurin nan .

Sannan tayi facing din DEENI da kyau tana harararsa kana   tace kabari  laraba tazo ta shige dasu   .
aikin nablah a gidan nan girki ne kawai  .

Sai daya yatsina fuska tare da  tabe bakinsa tukun yace   Ok Ai  duk daya ne   first lov Dan aiki Dan aiki ne, bbu wani bambanci   da may girki da may  shara da sauran ayyukan gida duk dai  Yan aiki ne ..

Duk Yan akine  Amman ita wannan  nata aikin may lasisi ne wanda kasan da hk  ko kana daja ne?
 uhmmmm first lov Ni Na isa Naja dake ..ok
Yi tafiyar ki kinji nablah ..




Karfe biyar daidai matar gidan tashigo gidan agajiye fuskarta  cike  da izza da Mulki da nuna  isa .
ta zauna tare da Kiran washi Allahna sannan tace ummi sannuku da gida .
  ummi  ta dubeta  tana murmushi may cike da nuna  tsansar kulawa da soyayya kana tace yauwa mamana ya gajiya da karatu ?

Kai ummi wlh karatu nan kwata kwata  bbu sauki. 'cikin hk nablah ta fito daga kitchen takaraso har  inda Zeenat ke zaune tayi mata sannu da zuwa tare da tmbyrta abinda za'a daura Na dare .

Sai data yamutsa fuskarta sannan tace  daga dawowata zaki zo min da wani  mgnr abinci tun mutun bai gama huta wa ba  tamkar wasu mayunwata mtssss taja tsaki.
Ita dai nablah dake  tsaye bata sake cewa komai. sai ma ummi ce, tace haba mamana ki dinga bin yarinyar nan ahankali fa kinsa bawai ta taba zuwa aikatau bane wannan shine first time dinta .
to ai tace ummi daga sannu da zuwa sai mgnr abinci .
to ya isa hk wannnan duk ba laifi bane dan ta tmby. Ni dai dan Allah ki dinga sausautawa yarinyar nan  yanzu dai gaya mata abinda zatayi.
 inji cewar ummi  "
sai da Zeenat ta sake yatsina fuska sannan tace paten doya  zakiyi min   .
..muryar  nablah a sanyaye  ta amsa da to  aunty.
  Amman banason yayi kauri yayi ruwa ruwa ..takarasa fadar hk tana duban sashin da ummi take ummi ku mezaku ci  ?
Duk abinda mamana zataci .

Zeenat Tayi murmushi tare da cewa Ok  amman  shi    my hrt ki mishi poundo yam da miyar ugu sauran ki yiwa mutane shirme  .

Hk nablah  ta sake koma kitchen Wanda zuwa  lokaci har  laraba ta kammalawa da gyaran kitchen din ta fita zuwa wani aikin Na daban.

 ahankali take bare doyar zuciyarta tamkar zata buga  tsabar bakinciki zamanta ciki gidan ta hada source Na asaro.


Kusan awa biyu da shigar nabla kitchen.
   ' sai Ga Zeenat tashigo da waya a hannuta  tana yatsina fuska da baki sannan tace wai har yanzu akin kikeyi baki gama ba?

 nablah da ranta yake a bace matuka .
 a dakile tace   eh aunty sauran kadan Zeenat  taja ta tsaya tana rike da wayarta har lokaci ita dai nabla dataga tana aikin  dadaddana waya wanda   batasan abinda take yi ba.
 km kusan duk sanda take girki a kitchen sai tashigo tayi mata tsaye a ka  da waya a hannuta.


 byn ta fita ne  sai ga laraba tashigo  tace nablah ....
Ta juyo tana dubanta batare da ta amsawa laraba.
 kinsa me aunty take miki Inda tashigo kina girki . nablah ta girgirza mata kanta ahankali alamun batasani ba .
 to wlh video take miki .

Nablah ta Dan tsorata da mgnr  har idanuta suka Dan fito waje video km name?
 oho Nima bansani ba wlh  amman nima hk take min lokaci da nake mata girki.
 bangane video ba to tayi me dashi  ... ?
nablah ta sake tmbyr laraba .
 uhm kawayenta take turawa idan kin yi mistake sai kawayenta suzo har gida su zageki tasssss nima hk ta min kwanaki kafin kizo takira kawayenta sukazo suka minrashin mutunci da zagi iri iri bbu halin ramawa ... .
  "nablah nagama  jin karshen zance laraba taja tsaki tana jin jina girman  al,amarin Zeenat.
 sannan tace wanna km iskancin sai dai suyi miki shi  Amman Ni ....ta nuna kirjinta da dan  yatsanta daya .
wlh bazan dauka ba sai dai hakan yayi  sanadiyar barina gidan nan daman km hk nake so.
 laraba ta kwashe da dariya nablah kennan Ga tsoro Ga ban tsoro .nan dai suka bar zance suka shiga wata hirar har zuwa sanda nablah ta sauke girki  tare  da shirya dinning .
sannan ta nufi dakinta bata km fitowa ba har sai data daidaici lokacin dayakama tayi serving Nasu  abinci.

 sannan ta fito jikinta sanye da doguwar rigar wace ta kama jikinta  sosai.
Wanda  daga samanta kana hango tundun nonuwanta yayinda kasan rigar  keda Shep din flay ta nade  kanta da dan  karami 'bakin  mayafin ganin darene hakan  datayi , ya sake fito da ainihin  sihirtaccen siffar kyawun ajikinta.

 ahankali take daga kafafunta 'cikin takunta may matukar daukar hankali  kmr koda yaushe .. takaraso dinning area .
sai dai me kawai ganinsu  Tayi  zaune tuni sunyi nisa 'cikin cin abinci Amman Banda oga deeni Dan Haka ta juya zata wuce taji Zeenat  takirata da sunan datafi tsana a rayuwarta  ke..... nablah ta dawo ahankali ta tsaya batare da tace komai ba .Kusan minti Goma   tana nan tsaye amman kwata kwata Zeenat bata da niyar cewa mata komai.
 sai byn data gama cin abinci ne tukun ta dago fuskarta a tsine tana duban nabla dasu .
 hk nace kimin asaro bance miki  may ruwa ruwa nake so ba .
mamaki da al,ajabi  kalar iskancinta ne ya mamaye zuciyata .amman a dake tacigaba da tsayuwa a gurin sbd bata da halin tafiya taja mata kan wani sabon tashin hankali.
 magi nawa ma kika saka acikin abinci ?
 nabla tace daidai Wanda zaiji.
 nifa banason albarzazanci a gidana akaida magi shida a pot daya ya isa .
 jiki a sanyaye nablah tace to shikennan zan kiyaye inshallahu,karma ki kiyaye taja tsaki Zeenat  nagama fadar hk ta Mike tsaye tana kakkabe jikinta tabar gurin .
ba nablah dake tsaye ba  hatta ummi bataji   dadin abinda Zeenat din tayiwa yarinyar ba.
 amman taki saka musu baki dan batason tana yawan  shiga tsakaninsu tunda tare zata barsu  ..

da kyar nablah ta daga kafafunta .takarasa ficewa daga gurin ta nufi BQ ta zagaya Inda Anan dakin laraba yake da fara,a laraba ta tarbeta tana dariya sai yau Allah yayi  zaki  zo min ?
Murmushi nablah Tayi wanda har wushiryarta ya bayyana ta gaida laraba hirarsu suka Shagayi sosai dan ba ita tabar part din laraba ba.
 sai wajen takwas da rabi Na dare  tare suka ci abinci da laraba sannan ta baro part din  .

Tafiya take sannu ahankali 'cikin sanyin jiki da natsuwa ,ahankali iskar damuna ke kadata kasancewar lokacin ruwa da'ake ciki Wanda kusan yanayin garin Lagos kennan, basu rabo da ruwa sama kasancewar basu da rani da damuna koda yaushe 'cikin ruwa sama suke .

Daidai ta kawo wajen parking space ta jiyo motsi ta dan jiyo ahankali idanunta suka sauka akan fahad abokin deeni kawai ta kauda kanta ta juya tacigaba da da tafiyarta a tunanita Bai ganta ba.
"  kawai ta tsinci muryarsa haba Yan mata irin wannan shan kamshin hk Ai akalla ko gaisawa munyi,duk da cewa zuwan nan  danke nayi , inji cewar fahad Wanda oready tuni har yasha gabanta.

Take kirjinta yashiga dukan uku uku fatanta kada Allah Yasa ya furta mata kalmar so...dan ita tsoron kalma take
Km  bata jin har 'cikin   zuciyarta lokacin yin soyayyarta yayi.
 domin tafi son ko zatayi soyayya sai ta kammala da karatunta so that sai tasamu daidai da matsayinta .
dan hk a gaugauce zuciyarta cike matsanancin  tsoro tace Ina yini .
lfy lau nablah ya gida da aiki?

Kanta ta dago da sauri tana dubansa jin ya ambaci sunanta dan batayi tunanin yasan da zamanta a gidan ba . ballanantana har yakai ga sanin sunanta . yacigaba Ina son ganinki km sbd ke naxo gidan nan zuciyarta ta sake bugawa da karfin gaske..
 Ahankali Ta maimaita abinda yace Tare da  dan ware shanyayun idanunta akansa .
yace uhm amman idan nagama da DEENI zansa a min kiranki da fatan ba zaki ki zuwa ba.
 fuskarta a daure tace Allah yabani iko tana gama fadar hk da sauri ta juya tasoma kokarin barin gurin dan ganin DEENI dake tahowa Inda suke tsaye .
duk da saurin datake hakan Bai hanata jin sautin muryoyinsu ba kasancewar sun biyota a bayanta ne..

Fahad deeni yakira sunanshi a kausashe kafita daga idanuna Na rufe meyasa baka jin shawara ne shege kawai may shegen daurin kan tsiya.. 

Fahad ya kwashe da dariya sannan yace Kai km meyesa kacika girman kan tsiya da kafiyar maseefa Allah bai haramta min yarinya ba amman Kai kana neman ka rabani da soyayyata.

 Na dade da kamuwa  da matsanancin kaunar  yarinyar nan amman kwata kwata ka kasa ka tsare ka hanani fahimtar daita .
meyasa zaka hanani isar da sakon zuciyata gareta ?

Ok  hk kace ?
DEENI yakarasa fadar hk cike da huci yana kallon tsakiyar idanun fahad..

Yes hk nace idan km kaima kana sonta ne kafito ka kasanar   sai  Na janye maka dan bazan taba iya cigaba da son abinda kake so ba.

bawai ka dinga kokari hanani isar da sakon abinda zuciyata ta kamu da matsanancin so ba 
Kasan Ni ..kasan halina km kasan koni waye idan ba son yarinyar nan nake da gaske ba bazan takura kaina akanta ba .

Wulakance  DEENI yake masa wani irin duba cike da tsansar tashin hankali yayinda gabadaya yanayinsa yagama sauyawa.
 akansa zuciyarsa yace wannan wace irin maseefa ce hk .
Tun bai gama da matsalar kB .
Ga fahad wanda shi ya dan kwana biyu dayi masa zance yarinyar.

Ahankali Fahad yace deeni kana son yarinyar nan fiyye da yadda nake sonta wlh .
idan har kasan  kana sonta  zan janye amman muddin   baka sonta to kabari  na shiga sawun manemanta kawai  .
Kai wlh Azimi ko rantsuwa nayi bazanyi kaffara ba wlh son yarinyar nan  kake yi km so may tsanani fahad yakarasa fadar hk yana share gumin daya fufeshi duk da isakar dake kadawa .

Sai DEENI  daya furzar da wata  iska ta bakinsa  may dumi sannan a zafafe   yasoma managa muryarsa cike tashin hankali billahi azim fahad zaka jawowa kanka maseefa ne kawai .
 km hakan zai iyayin sanadin da zamu samu  mugun matsala may girman gaske da kai idan ka sake furta kalmar....




MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO




*Uhmmmm uhmmmm abin 'cikin kwai Ina jinjina gareku members Na AUREN SIRRI fans  hadin kanku tattare da zaman lfyrku yana matukar birgeni Ina matukar alfahari daku wannan shafin sadaukarwa ne gareku  kuyi duk yadda kuke so dashi Allah yabar zumuncin dake tsakaninmu har ila yaumul kiyamati ina addu'ar kar Allah Yasa zumuncin nan ya tsaya iya social Media kawai* 


Page 76


Idan ka sake furta kalmar Cewa Ina son yarinyar nan wlh zan bata maka rai fahad ,
 narasa Inda zan ajiye soyayyarta sai gun house girl dina ?
kuka fa... amman wlh ka cuceni  kasan cewa Ina da tarin dukiyar da ni kaina bansan adadinsu ba.
 km ta ishe nazabi duk kallar  mace datayi min a 'cikin duniyar  "ya  "ko ta gidan uba wace km ko a wani kasa take ba wai wannan bazar house girl din ba .
Kai bama Ni ba ya nuna kirjinshi da yatsansa  ko wanda  nake tare dashi  yafi karfin yayi soyayya da house girl .


Muddin har zaka cigaba da kudirinka akan yarinyar nan to wlh kaji narantse maka  kana daidai ne da raba abotarmu tare da duk wata halaka dake tsakaninmu .

yana karasa fadar hk yayi gaba 'cikin matsanancin fushi da Bai San dalili yinsa ba hk zalika baisan meyesa duk sanda yaga yarinyar da wani nmj ba wani ya nuna alamun yana sonta  hankalinsa ke mugun tashi ba .

Ko 'cikin parlour ma rigima ce sosai suka dinga yi da DEENI da fahad akan nablah har ummi ta tmbye fahad din abinda ya hadasu.
Bai tsaya boye mata komai ba  ya sanarmata .

ka kyale wannan rigimamme kaji  kayi abinda yakawoka kasan halin deeni sarai ba sai Na tsaya gaya maka ba ummi tacigaba nablah takai mace da kowani da namiji zai so.
Domin  Tana da halayya nagari da za'a so mace domin su.

 dadi ya rufe xuciyar fahad sosai jin abinda ummi tace yayinda deeni ya dago sukayi four eyes  ya watsamasa wata uwar Harara tare da jan tsaki .

Banda wani uziri may karfi  to wlh koni zan iya shege maka gaba akan neman aurenta dan takai mace iya mace.
 sai dai kashi...akwai wani sirrin boye dake tattare da yarinyar wanda zai yi maka nakasu.
 ummi takarasa mgnrta Tana sauke numfashi .

Ahankali Fahad ya furta kalmar inna lillahi wa inna ilaihi rajiun  wayyo Allahna tare da dafe daidai saitin zuciyarsa dake bugawa da hannuwanshi duka. alamun zuciyarsa bata ji dadin zance ummi na karshe ba .

DEENI dake rike da wayarsa yana aikin chatting  yayi musu banza yacigaba da abinda  yake .
dan tunda ummi tasaka baki 'cikin mgnr Bai sake cewa komai ba  sai ma kokuwa dayake faman aikinyi da numfashinsa dake neman barin gangar jikinsa.

Gabadaya hankalin da yanayin fahad ya canza take ya  koma kalar tausayi .
Yayinda  zuciyarsa  ke  wani dokawa da sauri a frigice  yace dan girman Allah ummi kitaimakamin kiyi wani abu akai wlh nayi mugun kamuwa da mugun son yarinyar tun farkon ganina daita.
 Ina ji a raina matsawar bata kassnce matsayin matata ba zan shiga wani hali.


 a hassale DEENI  yabar abinda yake ya sake dagowa  yadakatar dashi yana huci kana yace Kai wani irin jaki ne kai ?
Dabaka fahimta" da wani irin yare  kake son A sake maka bayani akan yarinyar nan.
 Ni kaina  hanya may bullewa na gayama akanta shine karabu da soyayyar yarinyar nan amman kake ci min fuska to wlh kayi Na farko kayi Na karshe duk lokaci daka sake cewa kana son wacce yarinyar sai Na fasa maka baki . ba fahad ba  hatta ummi sai da karshen mgnr deeni tasakata dry .aiko fahad ya dinga dariya yana fadin DEENI rikicin gangan .
fahad yace wlh baka isa ba tunda Kai ba sonta kake yi ba .
ta ya'ya Ni zaka hanani km wlh bazan barta ba sai Inda karfina yakare tunda ba matar wani aure bace .
 zan jirata har sanda sirrin boyen zai tashi daga kanta a zafafe deeni ya Mike tamkar wani mayunwacin  zaki bazoto  fahad ya ji an  damki makoshinsa .

Ummi ta Mike a frigice Tayi kansu sbd tasan halin zuciya irinta danta .
Meyye hk deeni daga wasa zaka maida mgn fada..barshi first lov wlh bbu wasa acikin wannan mgnr sannan 
 Ya tsare fahad da idanunshi ka   sake maimaita abinda kace dan ubanka wlh  sai dai uwarka ta sake  haifo wani bakai ba .

Idanuwan fahad sukayo waje sbd mugun shakar da deeni yayi masa ummi shiga tsakaninsu Sosai tana  ka sake nace deeni ko bakaji ne.
 shi kuwa shr yayi yana damke da wuyan fahad  da iyakacin karfinsa.

 kokari fahad yake ya kwace wuyanshi amman Ina yakasa dan  bakaramin riko deeni yayi masa ba  ,sai zufa ne kawai ke keto masa takoina ajikinsa  duk da sanyi AC dake aiki a parlour hkn Bai hana  jikinshi yin  sharkaf da ruwa ba .
so yake yayi magana Amman ina ya kasa dan bazai iya ba  ko yace zaiyi mgnr muryarsa bazata fito ba dan hk yasoma mutsumutsun kwace kanshi  sai da ummi tashiga tsakaninsu Sosai sannan da kyar da   yataimaka Allah ummi tasamu  DEENI ya saki wuyan  fahad.

 aiko yana sakinsa Tari ya sarke makoshin fahad   Ya dingayi Tari yana damke da wuyansa  da kyar ummi tasamu ta zaunar dashi Tana yi masa sannu tare da kawo masa ruwa .

DEENI ya zauna yana sakin numfashi sama sama tare da furzar da wata  iska may zafi ta bakinsa .
Ahankali  ya runtse rikitattun Idanunshi gam ji yake tamkar numfashinsa zai bar gangar jikinsa ne sbd wani irin radadin azabar daya caki tsakiyar zuciyarsa lokacin da fahad din ke furta kalmar yana son yarinyar.
 fada ummi ta dinga yiwa deeni  sosai tare da ce masa Inda ya sake yiwa fahad wani abu wlh zai hadu da fushinta .

 Jin abinda umminsa tace ne yasa ya dinga karanto duk wata addu'a dayasan zata sanyaya masa rai .
Wlh deeni   batason jin wani sabani yashiga tsakaninka  da fahad akan wannan zance .
Sannan ta jiyo Inda fahad ke zaune wanda zuwa lokacin gabadaya yafita daga haiyacinsa sai numfashi yake saukewa ahankali ahankali yana rike da wuyansa dake masa wani irin radadin azaba .

tace Dan girman Allah  kayi hkr fahad kaji kasan halin abokin naka  rigimamme ne na bugawa ajarida banason dan Karami abun nan yazama silar lalacewar abotarku kaji dana .

bbu komai ummi komai Ya wuce amman ummi shi meyasa zai hanani son yarinyar byn ya tabbatar min da ba sonta yake ba .

Kai dai kabar zance kawai bakomai bane sai fitina irintasa .
 nan dai ummi Tayi  tayiwa deeni fada daga karshe ta hade su gabadaya tayi  musu fada sosai 'sannnan tabar parlour tanawa tilon Dan nata addu'a.

cikin hk Zeenat takaraso parlour ta taddasu jikinta sanye cikin doguwar rigar may mugun kyau da tsansi sai daukar hankali take kmr koda yaushe dan Tana kaunar sanya dagayen riguna  Sosai.

A mutunce suka gaisa da fahad ta juya Ga mijinta wanda tun shigorta idanunta da hankalinta ke kansa Tana nazarin yanayinsa .
ganin yadda fuskarshi da yanayinsa suka sauya yasa takaraso kusa dashi  da sauri  tare da kamo tafin hannushi'cikin nata Tana murzawa Tana kallonsa tare da  tmbyrsa my hrt meyesa Meka hk?

 dan gabadaya itama tsintar kanta Tayi 'cikin damuwa da tashin hankali ganin halin dayake ciki hakan km  ya mantar daita komai ciki har fahad dake zaune yana bin deeni da kallon mamaki wai yau shi deeni ya rufe ido kan mace   yayi masa rashin mutunci..

Kokarin shegewa jikinsa take Tana sake tmbyrsa abinda ke damunsa  ahankali ya dago rikitattun Idanunshi ya xuba mata yana kallon kwayar idanunta ganin yadda tadamu da son sanin abinda ke damunsa .

Ahankali Idanunshi ke bin koina ajikinta batare da yace mata komai  irin shigar datayi ta daukar hankali yasa shi damke hannuta Sosai 'cikin nashi sannan ya Mike tsaye manne daita a gefen jikinsa .
yayi hanyar dakinshi daita.
Muryarsa a kausashe  yace Kai km Malam idan ka gaji da zama kofa a bude take kana iya wucewa yacigaba da tafiyarsa yabar fahad a gurin yana binsa da kallon mamaki.


Kwance nabla  take akan gadonta sai faman juyi da tunanin DEENI take wannan wani irin nau,in jinsin  mutun ne shi kwata kwata kowa ba abakin komai yake a gurinsa ba .
 takama gadara sunyi masa yawa to ko dukiyarsa ke rudarsa ko kyawun dayake ganin yana dashi ne  ?
 Haushi da takaicinsa ne suka taru suka lullube ruhinta yayinda  zuciyarta ke mata wani irin radadi da zafi tamkar zata tarwatse haushinsa ta dinga ji sosai har cikin ranta.
 datana da iko wlh da sai Tayi masa shegen  dukan tsiya ko zata samu saukin radadin da zugin da zuciyarta ke mata akan wulakacinnsa gareta.
 shr shr Tana nan kwance taki tashi  tana  jiran Dan  sakon  Kiran da fahad yace zai yi mata .
amman taji shr hakan yasa ta gane may be wannan azzalumin ne ya hanashi .
kafafudunta duka  ta daga tare da cewa huta roro  akasan ranta daman ita  badamuwa tayi ba ..

Bangare fahad kuwa deeni ya wuce zuciyarsa  cike da mamaki iri iri da alhinin abinda abokinsa yayi masa jikinsa a sanyaye ya Mike ya fice daga parlour,n.
 yana fitowa ya  shiga motarsa ya tayar  ya nufi babban get din estate din.
Yayinda   ke  deeni  tsaye jikin Window yana hangosa sanda yayiwa motarsa key.

 ya dauki wayarsa yayi dealing din number securities din 'bakin get daidai lokaci da wani daga cikinsu ya mike tsaye  yana kokarin budewa fahad get Kiran deeni yashigo babansu ne ya dauka cike santsar biyayya  tare da cewa hello sir hade gaisuwa DEENI bai tsaya bin takan gaisuwar ba.

 yace kaga motar nan da may motar da tafita yanzu banason  sake ganinsa 'cikin compound din tell all the securities no one  allowing  ya km takowa 'cikin estate din nan.
 Ok sir deeni ya katse wayarsa tare da juyowa ahankali ya idanushi suka sauka akan  Zeenat dake zaune tana kallonsa.
 idanunshi da yanayin yadda yake kallonta din ne yasa takasa tmbyrsa dalilin dayasa  ya fadi HK  yana gama kallonta yashige bathroom dinsa ..


Byn ya fito daga bayi ne yazo kusa daita ya zauna yana mata duban kasan ido tare  da hadeta da jikinsa yana shinshina wuyanta .
Kokarin bude bakinta take so take tasan meya hadasu da fahad  yayi sauri manne bakinsa kan nata 'cikin kwarewa ya cafko lips dinta jikinsa har yake ya makaketa gam ajikinsa yanawa bakinta wani irin tsutsa Na fitar hankali .
ahankali yashiga rabata da kayan jikinta yana yin  filinging dasu gafe sannan  yashiga sarrafata da iyakacin karfinsa sosai itama take bashi hadin kai dan batason mijin nata  yaga gazawarta sai dai jarabarsa tasoma damunta .
ayi mutun ko 'cikin fushi yake zai iya saduwa da iyalinsa  matsawar zai samu.
  km ko byn yagama ci  fushin Na nan tamkar ta zaki .

Gabadayansu  sungama fita haiyacinsu jira kawai taji kaciyar cikin kasanta yayinda  sauran kiri yashigeta  ya tuna da yau ranar kwanta nan nablah ne .






MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO



Page 77



Ahankali ya zare jikinshi daga gareta yakoma gefe  ya kwanta  yana fidda numfashi sama sama Dan gabadaya a bukace yake .
Jin ya tashi daga kanta ne yasa ta  birkito da sauri    tana facing dinsa eyes into eyes suke kallon junansu .
 idanuwanta ta kafeshi dasu masu dauke da tambayoyi iri iri .
gashi bbu   damar tmbyr Dan batasan abinda tmbyrta zata haifar  ba. kasancewar  tasan halinsa kmr yunwar 'cikinta  .

 Dan hk tacigaba da kallonsa kana Tasoma  kokarin kai hannuta saman fadadden kirjinsa.
Bai hanata ba Dan yasan ya rigada ya daurata akan network takai limit din bukatuwa dashi.


 ahankali    ya dinga jin  hannuta a tsantsar ajikinshi Tana shafa gashin dake kwance ajikinshi.
  ai wani  shaukin  yaji ya tsarga masa tun daga tsintsiyar kafafunshi har zuwa tsakiyar kanshi yayinda joystick dinsa ke sake mikewa har wani sheki take  tsabar son abincinta  Baisan  sanda ya fizgota jikinsa ba ya rungumeta gam yana sakin numfashi ahankali km tare da daura hannushi kan sumarta yana  shafa gashin kanta zuwa bayanta Kusan minti Goma tana rungume ajikinshi tare da shige masa tana sake  yamutsa masa lissafi.
Gabadaya tagama fita haiyacinta  burita ahalin yanzu Bai wuce Yayi sex daita ba .
Koda  round one ne tunda oready ya rigada ya tsokono mata sha,awarta .
amman Ina sai ma  lura datayi    Bai da niyar kusantarta.

 gashi tana jin yadda joystick dinsa ke sake   Mikewa   sambal tana kara girma  alamun a bukace take da muradinta .

Ahankali tana rungume ajikinshi ya dinga sakin numfashi tamkar Wanda yayi gudun falfalaki  .

 gabadaya wani irin kewar   yarinyar ne ke   bijero masa ta koina ahalin da yake  ciki ,so yake su hade ko zai samu sausauci abinda yake ji a gangar jikinsa game daita.

 zuciyarsa ke gargadinsa da  kada yaje ya isketa idanunta biyu .
dama yayi zamansa tunda Ga wata matarsa Tasa  nan kwance ajikinsa wanda yaga alamun abukace take  daya ratsata .
, Amman Ina hakan  Ba may yiwuwa bane gareshi ya fadi HK akasan  ranshi  duk yadda yake  tunanin yanayinsa Na rashin hkr   yake .
Bai Kai    yashiga hakin wani ba .
' cikin wannan tunanin dayake ne .Ya dinga jin saukar numfashin zeenat ahankali ahankali alamun   bacci yayi nasarar daukarta wanda daman hk take da saurin bacci .


 ahankali ya daura rikitattun idanunshi akanta yana lumshe su  ganin yadda take sharar  baccita hankali kwance . Dan hk ya rabata da jikinshi  ya kwantar daita tare da gyara mata kwanciyarta sosai ya  lullubeta da blanket may taushi .


Sannan ya Mike  tsaye ya maida boxes dinsa yaje gaban dorom din mirrow dinsa ya jawo .
ya ciro  injection  tare kunna CCTV camera dinsa yana kallonta tun daga sanda tashigo gidan byn ganinsa daita tsaye da fahad har zuwa sanda tashigo dakinta tayi wanka da sallah Ta kwanta bacci .
 awo Kusan uku kennan da kwanciyarta a lissafinsa  dan haka cike layi  ya nufi dakinta ,ta Inda yasa ba shiga .



Kwance take 'cikin wando iya cinyarta  da wata Yar yololuwur  Riga bacci  may zip a gaba   masu matukar kyau da taushi yayinda gashinta  ke kwance luf  ...sun  baje kan fuskarta sannan Ta rungume  pillwo  akirjinta gam ta matse  dayan pillow a tsakanin cinyoyinta .
bacci take cike da kwanciyar hankali.
 " idanunshi ya tsura mata tare da furta.

 fatabarakalhu fii ahsanul
 khalikin ....

'cikin sanyin jiki yakarasa ya haura saman gadon  Inda take kwance. ahankali yasa hannushi ya janye pillows din duka gefe .
Sannan ahankali yayi   mata allura  a damtsenta tare da mayye mazaunin pillows din 'cikin hikima ya zuge zip din gaban rigarta wani irin ajiyar zuciya ya sauke da karfin gaske  tare dasa hannunsa a hudar cibiyarta yana shafa cibiyarta zuwa kasan mararta ahankali yana lumlumshe idanu.

 idanunshi ya maida kan Brest dinta lokaci daya kwalkwaluwarsa tasoma birkicewa batare daya sani ba, hannushi duka ya daura kan nonuwanta ya damkosu  ya dinga shafawa yana murza kan nipply dinta.

Ita kuwa 'cikin bacci ta dinga jin wani irin felling Na fitar hankali jin hk yasa ta dauka mafarkin data ,sabayi ne, ahankali tasoma sakin jiki tana narkewa ajikinshi ta matsoshi Sosai tare da dago masa nonuwanta da kyau shi kuwa cikin zalama ya daura lips dinsa kan nipply dinta ya dinga lasa yana Dan ciciza kan nipply din da hakorinsa ita kuwa gabadaya ilahirin jikinta yagama sakewa kasanta  sai tsiyaya yake tasa  hannuwanta duka ta matseshi  gam ajikinta tana sakin numfashi tare da sake tura masa nonuwanta.
 aiko gabadaya ya rude ya susuce yagama fita haiyacinsa bbu abinda yake sai aikin sarrafata 'cikin wani irin shauki da Bai taba tunanin zai kasance ciki ba .
ahankali 'cikin mutuwar jiki ta cusa hannuta cikin sumar kanshi tana cakudawa yayinda shi km sai nukurkusanta yake 'cikin iyawa da kwarewa ya sake maneta da jikinsa ya manne bakinsa kan nata cikin sa'a da kwarewa ya samu ya cafki laulausar harshenta jikinsa har rawa rawa yake tsabar fita haiyaci .
ya makale gam gam ajikinsa bakinsa na manne danata  tamkar wacce  ake shirin kwacewa masa ita .


Wani irin tsutsa yake bakinta nafita hankali 'cikin baccinta take kokarin son kwace bakinta daga gareshi sbd jin yadda yake tsotsar lip's dinta tamkar yasamu lollypop 'cikin wani irin sauti yace shiiiiii wayyohhhyyy sannan ya sake kamkame ta ajikinsa yana cigaba da sarrafa harshenta 'cikin shauki 'cikin fitar hankali Ya dinga bata hot kiss da taba duk Inda hannushi yaci karo dashi ajikinta.
 cike da wani irin shaukin yasoma ware mata kafafunta ya sauke bakinshi kasanta ya zufa harshensa ciki yashiga soucking dinta yayinda ita km sai faman turo masa kasanta takeyi  tana shiiiiii uhmmmm shiiiii a can duniyar mafarkinta wani irin gurnani yaji  tana yi  wanda hkn  ya tabbatar masa tsabar  dadin take ji ne sosai ya dinga soucking dinta ita km sai zuba sambatu take zubawa ahankali ya cire bakinsa   yasoma kokarin neman hanyarsa.
 har Allah yabashi sa'a.
 ya da kyar yasamu ya shige 'cikin   hanyarsa yasoma bata haddadiyar  joystick dinsa may dadi da gardi da mantar da mutun 'cikin duniyar dayake .
sosai yake aikin hakarta  da iyakacin karfinsa.
 yana jin sanda tasoma zafafa karfinta tana sake ware masa kafafunta sosai  shi km sai aikin cinta yake ba kaukautawa yana jin sanda tayi realize ya sake matse gam ajikinsa .
Sosai yacigaba da murzata cause shi baya gajiya gurin yin sex kasancewarsa may tsananin sha'awa da tsantsar son saduwa da macce .
gashin yana jin dadinta har cikin tsakiyar kanshi domin ita nablah irin matan nan ne da namiji baya gajiya da mu,amula dasu.


Bangare zeenat kuwa kwana tayi tana juyi daga karshe tasoma lalubar inda tasan  deeni zai kasance .
 wayam taji Dan hk sannu ahankali 'cikin mayyen bacci ta soma bude idanunta har takai Ga budesu duka amman  bata ganshi ba a dakin  ta Dan Mike zaune  tana  mika hade da salati.
Yayinda still  take jin  jikinta  wani iri  tunani tayi ko yashiga bayi ne duk da bataji motsin alamun yana ciki ba. ahankali takoma ta kwanta tare kudindine jikinta guri daya ta koma baccinta .



 sai  da deeni yayiwa nablah    ci  biyar masu rai da lfy tare da juyata yadda ranshi keso sannan ya barta ya Mike tsaye yana sakin numfashi  ba Dan ya koshi ba .yasa boxes dinsa ya goge mata Spam din dake  kasanta sannan ya   maida mata Yar yololuwur rigarta da bombashort  dinta.
 ya bi ta hanyar daya shigo ya bar dakin zuwa nashi dakin.
Wanda  har zuwa lokacin bacci zeenat takeyi tare da takure jikinta guri daya   .

 wanka yashiga byn ya fito ya hada coffee yana sha tare da kunnan TV Dan kwata kwata ji yayi gabadaya baya jin bacci ya haura kan bed inda zeenat ke kwance ya janyota jikinsa ya kwantar daita kan fadadden kirjinsa yana shafa sumar kanta. 'Cikin bacci ta rungumeshi tare da shigewa  jikinsa .




Washegari a kasalance nablah ta tashi gabadaya ilahirin gabobin jikinta ciwo suke mata .
Yayinda kasanta ke mata wani irin radadi may gauraye da dadi dadi .

 zaune take a tsakiyar gadonta tana son  tuno irin mafarkin datayi a daren jiya wanda yakasa bace mata .
so take ta tuna fuskar mutumin dayake saduwa daita a kullun  'cikin mafarkin.
 shr tayi tare da zuba uban tagumi ta runtse shanyayun idanunta gam domin son gano wani wani abu.
 amman kwata kwata abun yacitura.
 Dan kasa tuno fuskar mutumin tayi  .
Dan hk ahankali ta Kai idanunta kan agogon dake manne da bangon dakinta.
 karfe bakwai tagani daidai Dan haka atsorace  ta Mike tsaye da kyar tashiga bayi tayi wanka tsarki kmr yadda tasaba .

Ta fito ta gabatar da sallah ta nufi downstairs kitchen tashiga ta hada komai Na breakfast sannan Ta koma dakinta ta kwanta lamo duk ilahirin jikinta a sanyaye yake duk ta Inda ta motsa Tana jin feelings din hannun mutumin da batasan ko waye ba agangar  jikinta .
 sosai tayi zurfi 'cikin duniyar tunani komai daya faru daita daki daki  'cikin mafarkinta.
 take tasoma jin jikinta yana sakewa da budewa wani irin ruwa ne taji yana tsiyayowa daga kasanta ahankali ta dinga sauke numfashi yayinda zuciyarta ke wani irin bugawa da sauri  da sauri.
 ta Dan dade zaune kafin ta farga da lokacin yin breakfast din mutane gidan yayi .
ta Mike tsaye a hankali taji jikinta ajike duk tayi whet  numfashi ta sauke sannan tashiga bayi ta cire part dinta wani ruwa tagani   ta Dan tsaya shr Tana kallo ruwan  wanda  ya tabbatar mata da ruwan sha'awa ne.
 Dan hk tayi tsarki sosai sannan  ta sake koma parlour,n kasa .

Zuwa lokacin kowa Na gidan ya hallara akan dining table  yana break har  deeni  jikinta a sanyaye tasoma  kokarin karasowa gurin ahankali deeni dake zaune yaji zuciyarsa ta buga da karfi a sukwane  ya tattara hankalinsa duka  gareta yana kare mata  kallo takasan idanunshi. yayinda duk daga kafarta daya daidai yake da bugun zuciyarsa har takaraso Inda suke ta tsaya ta gefen ummin Idanunshi nakanta  idan kalleshi bazaka taba cewa ita yake kallo ba .


'Cikin sanyi jiki da sanyi murya may kashe zuciyar ma'abocin sauraro tace ummi Ina kwananku tayi gaisuwar 'cikin jam,i bbu Wanda ya amsa mata sai ummi da safeena.
 ummi ta tsareta da idanu  Tana dubanta 'cikin sakin fuska  tace lfy nablah ya kokari .
  da kyar nablah ta bude bakinta tace Alhamdulilllahi shr ummi tayi Tana nazarita har zuwa lokacin da zeenat ta Mike tsaye  ta nufi dakinta hk ma safeena.

 yayinda shi km deeni ya  manna epis a kunnenshi yana operating din phone dinsa bandan yana sauraron wani abu.
  hkn  yabawa ummi damar karewa yanayin yarinyar kallo tsab  tare da cewa zauna mana nablah .ba musu ta zauna tana dari dari kar may gidan ya hantareta abin mamaki bbu abinda yace asalima bataga ya kalli Inda datake ba  .


Ummi ta numfasa kadan byn takammala dayin break.
Tana duban  yanayin yarinyar kmr bata da lfy .
 ummi tace baki da lfy ne ?
Ahankali nablah ta sunkuyar da kanta kasa ta hade yatsun hannuta guri daya  tana wasa dasu tare da girgirzawa ummi kanta .

ummi ta kamo tafin  hannuta cikin nata tace talk to me nablah make damunki yanayinki ya sauya dayawa  ?

 Kasa cewa komai tayi sai ma Hawayen  daya ciciko a idanunta.
  baki da lfy ko ?
Ummi ta sake maimaita tmbyrta hawayen dake makale a idanunta ne suka zubo kan kuncinta sannan ahankali ta gyada mata kan

 Ok Ina ke miki ciwo ?

Da kyar ta bude baki Tasoma mgn 'cikin in .inna wl..h.Wlh ummi bbu Inda kemin ciwo . amman ina ji ajikina banida lfy .
ta Dan dago ahankali ta saci kallon Inda deeni ke zaune hankalisa kwance km still epis Na nan manne da kunnenshi yayinda idanushi ke runtse . hakan ya tabbatar mata da baya sauraronsu Dan hk tacigaba Allah ummi Ina ganin kmr  aljanu sun shafeni dan Kusan duk  daren duniyar nan  sai nayi mafarkin  ana saduwa dani wanda sanda nake gida bana jin wannan yanayin  . shiyasa ma nake son zuwa gida ,tana karasa fadar Haka ta sunkuyar da kanta sbd kunyar dataji ta lullubeta.

  afrigice deeni ya bude rikitattun idanunshi fesss suka sauka a kanta zuciyarsa ke dokawa da sauri yana dinga jinshi wani iri wani iri tamkar ana masa watsa masa ruwan tsanyi ne  gabadaya zama gurin ya gudireshi   ahankali yasoma kokarin dauke Idanunshi akanta ,karaf  suka hada ido da ummi gabansa  yaji ya sake bugawa tare da    dukan uku uku waskewa Yayi yana shafa sumar kanshi.

Ummi ta watsa masa Harara domin tasan wannan ba aikin aljanu bane .
aikin tilon "Danta" ne Dan hk  ta girgirza kanta kawai tana cigaba da kallonsa tare da  turowa nablah plate din abinci ba musu tasoma ci Dan daman wata irin yunwa take ji may tsananin kasancewar jiya bata ci komai ba ta kwanta .
byn tagama ci abincin ne ummi ta kamo hannuta  ta mikar daita suka nufi dakinta tana kwantar mata da hankali akan abinda tasanar mata tace  bbu wani aljanun da suka shafeki nablah  hakan Na yawan faruwa da wasu mata musamman idan macce ta balaga  ke har wasu matan aure hakan Na faruwa dashi Dan Haka kada ki sa damuwa a ranki .nan dai ummi tayi ta mata bayani abubuwa akan mafarkin nata har nabla ta saki jikita sosai  sukayi ta hira har da safeena ..




Karfe uku daidai Na yammacin ranar 






MMN SUDAIS CE
[8/8, 10:07 PM] Ummu Haneef: Allah ya yafemana baki daya
[8/8, 10:09 PM] 0mmer Farouk: 💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO




Page 78



Karfe uku daidai Na yammacin ranar 

deeni  kwance bisa three star a hadadden parlour,n  gidansa sanye yake cikin wandon three quarter   black colour da whit hamles .
  hannushi rike da remut control "ummi tashigo parlour,n fuskarta dauke da murmushi  ta zauna kan kujerar dake facing din shi .
sannan tayi Kiran nablah dake kitchen .
Nablah  ta amsa da sauri tare da shigowa parlour,n da sallamarta.
 yauwa diyar albarka jeki dakina zakiga wasu  kayan wanki kulle .
ki dauka ki kaiwa kabir.

 nablah tace to ummi  ta juya ahankali tabar parlour,n   zuciyar deeni tashiga wasi wasi na kasancewar yarinyar tare da kb  yaji tamkar ya  kirata  ya hanata zuwa  Aiken,  amman babu yadda Ya iya da rayuwarsa  Aiken umminsa.

Ummi takira sunanshi tace son daman Ina son magana dakai ,Dan gane da yarinyar nan, da zamu bari 'cikin gidan nan.

 ummi tadaka da zancenta  domin jin abinda DEENI zaice .

Dagowa Yayi ahankali ya tsurawa umminsa rikitattun idanunshi masu frigita mutun yana mata wani irin kallo tamkar  yau ya fara ganinta, kana daga bisani ya maida hankalinsa wurin TV yacigaba da kallonsa.

 ummi tayi murmushi kawai sbd tasan halin tilon  "Dan" nata  miskili ne na bugawa a jarida.
 " tasan tunda Yayi hk ba magana zaiyi ba Dan hk tacigaba da kallonsa can km tace son wannan tafiyar dazamuyi  shine rigth time din dayakamata  kasan yadda zakabawa yarinyar nan kulawa yadda yakama, kar azo tana samun cikin amman fitinar ka  data matarka ya hana cikin zama  . nidai kabita ahankali shiyasa ma zan barmaka ita  Dan    Ina son Na ganni da Yan digwi digwi, takarasa maganar tana murmushi yayinda deeni Yayi shr yana sauraron inda maganar umminsa ya Dosa.
 zuciyarsa cunkushe da takaici ,ji yake tamkar ya hadiye zuciya  ya mutu ko zai huta da mgnr yarinyar da ummi tasanyashi gaba dashi.
   ahalin yanzu ji yake zuciyarsa na tsinkewa agame da  almarin yarinyar amman ita ummi kwata kwata taki gane hkn .
ahankali ya Mike zaune yana yatsina fuska  badan yaso ba sbd ganowa da Yayi umminsa so take tagane ko ya damu da lamarin yarinyar ne.
 Dan hk muryarsa a dake yace zaman me zata min first love ?
 ki maidaita gidansu first love  kawai so that idan kun dawo sai dawo domin bbu abinda zata min Dan ko ta zauna banida lokacinta .
ummi taji dadin kalamansa sosai domin Haka take son ji amman ta share tayi kmr bataji dadin abinda yace ba .

 wani irin kallo ta watsa masa tana tabe baki banason shirme banza deeni zamanta ne 'cikin gidan zakace bbu abinda zai maka to wlh tun wuri ka bude baudaudun kunnuwanka da kyau ka saurareni banason dangin mahaifinka su sake zuwa min da wata matsala cewa nike daure muku gindi Dan gashi nan ana yawo dani 'cikin estate dina cewa natare muku a gida . 
A fusace DEENI yace kibari su first love  ,su fadi duk abinda suka gadama bakinsu ne amman abinda nasani ne bbu Wanda yaisa ya fadi a gabana da ban gyara masa zama ba .
Uhm to meyye ruwana ma da maganarsu  nifa ba bahaushiya bace ballanantana hakan  ya  dameni .
Ni dai  Ina gargadinka kada ka sake Na dawo Na tarar da wata matsala.
 Kai ina son   labarin samun karuwa ya iske India   kafin Na dawo Ina fatan ka fahimci inda zance Na yadosa ?

DEENI ya lumshe rikitattun idanunshi zuciyarsa cike da farinciki abinda ummi tace Domin  shikansa yana matukar  son yara sosai  sai dai Yayi mugun tsanar  yarinyar. 
 gyada mata kai kawai Yayi domin  ya kasa cewa komai .

 'cikin rashin kula da yanayin daya shiga  tace amatsayina Na mahaiyarka Ina son nabaka umarni  ka gaugauta rage tsanar yarinyar  nan a ranka  kafin tafiyarmu  bance kasota dole  ba.
 km Hk kazali bance ka tsananta kinta ba .

tsai deeni Yayi yana kallon umminsa da kyar ya iya sarrafa harshensa ya furta.
 ya  km kike son nayi  mata first love ?
 harara ummi ta watsa masa hade da cewa bansani ba.
 sai  km maganar allura dakake yi wa yarinyar mutane ka daina kada kayi tunanin bansa komai ba.
Nasani  kyaleka kawai nayi.
Yanzu  anyi maganar zaman yarinyar ciki gida kace dama am maidata gidansu bakada time dinta .
 amman  ka iya bin dare gurin yi mata allurar bacci Dan mugunta . yarinyar nan  matsayin matarka  take  duniya ce kawai banason tasan da zaman kana da wata matar  byn zeenat amman km bazanso zalinci yashigo 'cikin lamarin ba .
mamakin kalaman ummi ne suka hana DEENI mgn sai faman ciciza lips dinsa yake yayinda zuciyarsa tasoma yimasa tsanyi a gane da  yarinyar  .
ganin ummi ta maida Hankalinta wurin TV hakan yabashi tabbacin tagama maganarta  Dan hk ahankali ya saki ajiyar zuciya da karfin gaske wanda har  Yasa ummi ta waigoshi  da sauri   ya lumshe mata idanunshi yana sake  sauke naunauyen ajiye zuciya  kana ya lankwasa  muryarsa first love...yakira sunan ummi  Dan Allah kiyi hakuri amman Ni wlh kunya nake ji ,naje mata kai tsaye .
km Ina ganin idan tasan abinda ake ciki akwai matsala sannan burinki da kike son cikawa  bazai cika ba .
amman duk yadda kike so hk zanyi banida  zabin  daya wuce naki .
I'm ready to obey ur decision  yakarasa mgnr yana  sakin numfashi.
 ummi ta tsare shi da idanunta tana nazarin yanayinsa sai km taji  tausayinshi yayi mugun kama ta . Tace  shikennan zaka iya mata amfani da tablet  Na  bacci marasa karfi sosai  amman Banda allura ..
Shr Yayi ya koma ya kwanta batare da  ya sake cewa komai ba .
Dan gsky shi Bai yarda da wani  tables Na bacci ba.
 yafi ganewa allura ta yadda kafin safiya karfin allurar  zai saketa .
Tazama tamkar ba'ayi komai daita ba ..

nablah tsaye ita da kB jikinta sanye cikin hijab dinta har kasa Baka hango komai Na jikinta. sai tafin hannuta shr tana tsaye  tare duban inda kb  yake byn ta Mika masa kayan wanki  .
Ya karba tare da ajiyewa kafin ya juyo yaga har ta bar gurin Dan Haka ya hanzarta biyo bayanta da sauri yasha gabanta . Wanda hkn Yasa  gabanta yashiga faduwa .
 Yayi shr kawai yayi ,ya  zuba mata idanunshi   tare rungume hannuwanshi duka bisa kirjinsa .
 ganin shirun Yayi yawa ne km gashi ya tsareta da idanunshi  Yasa ta kauda shirunasu ta hanyar cewa Ina jinka kB kayi shr kaki cewa komai gashi ka tsaidani anan .

 Da kyar yasamu ya hadiye abinda ya tsaya masa a wuya sannan yace nablah kennan gabadaya kwanakin  nan narasa gane kanki da Inda kikasa gaba   duk  kin bi kin canza min wlh bana jin dadi yadda kike min  ,km wlh  hkn dakike min  bakara jifa zuciyata 'cikin damuwa kikeyi ba ya fadi hkn yayi shr  yana jiran jin abinda zata ce ..
Gani yacigaba dayin shirun ne Yasa tace  uhm kayi sauri kagama mgnr ka   Dan wlh  sauri nake  Ina da abin yi "daga jin yadda take maganar kasan atsorace take  ya numfasa kana yacigaba nima aike nake jira akan mgnr da mukayi ranar naji kinyi min  shr kin sharen zance  kwata kwata zuciyata tashiga damuwa akan rashin samun attention dinki .
ko boss Yayi miki wani abu ne randa yaganmu ?

 tabe baki tayi tare da girgirza masa Kai bbu abinda Yayi min amman a gsky nidai   Ina son kasan banida interest din yin soyayya a halin  yanxu burina Bai wuce naga nasamu illimi may zurfi ba kafin nasoma soyayya .

 Karki damu nablah  muddin kika amince da zaki aureni Ni km wlh zan iya jiranki har sanda zaki gama karatunki.
 uhmmmm ta sake girgirza masa kanta sannan muryarta a sanyaye takira sunanshi kabir.. ... Wanda hakan ya sake tsuma zuciyar kb wanda har tsigar jikinshi suka mike tsaye .... yrrrrrrrrrrrrrya ya dinga Bazai iya hakura daita ba . bazan  iya maka wannan alkwarin ba  km bana son kace zaka  kajirani.

 badan komai ba ,sai sbd yanayin  halin rayuwa.
A halin  yanzu zuciyata wankakkace km kubudadda bata San komai ba game da abin Yayi kamanceceniya da kalmar  so.

 kar nazo nayi  maka alkwarin ko nace maka  kajirani naxo daga baya  zuciyata takamu da  son waninka.
  kaga idan hk takasance bazaka ji dadi ba.
 daga karshe kace Na yaudareka naci amanarka  abinda banaso jin kennan. kalmar yaudara tashiga tsakaninmu , Dan hk Na rokeka da girman Allah
.kabar kabar zance soyyayar nan.
  " kabari mucigaba da zumuncin da muka faro  tun farko  domin  yafiyye min wata soyyaya can.. takarasa fadar Haka tana furzar da  huci may zafi ..Karki damu nabla ai Ni nace naji Na gani  zanjiraki har zuwa lokacin da zaki kammala karatunki  idan kinji kina sona...

a hassale muryarta Na rawa  takatse shi ta hanyar cewa  nace karka jirani Kabir..kabir  ka nemi matarka a gaba ko dole sai ni zaka aure. ranta abace ta juya fuuuuuu zata wuce da niyar barinsa gurin Yayi  sauri janyo hijab dinta da hannushi.
 Ta juya  a fusace tana masa wani irin mugun kallo may tattare da tsansar takaici takasa ce masa komai sai shanyayun idanunta kawai  data zuba masa  km still hijab dinta Na rike a hannushi yaki saki  daidai  wannan lokacin zeenat ta dannowa motarta 'cikin compound din estate din ta nufi parking  space.
 tayi parking idanunta ya sauka akansu ta bude motarta ,ta fito tana danna key din hannuta ahankali  ta riskesu 'cikin wannan halin .
suna kallon junansu yayinda nablah ke mishi kallon tsana may cike da tashin hankali .
 shi km Yayi tsaye rike da hijab dinta yana kallon kwayar idanunta wanda in basani kayi ba wlh zaka rantse da Allah  kallon love sukewa juna .

  da mamaki zeenat ta bar jikin motar tana binsu da matsiyacin kallo har takaraso basu ankara daita ba sai data buga musu tsawa tare da cewa  kB wannan wani  irin tsagwaron iskanci ne  da wulakancin hk ?

A frigice kb ya juyo tsaitin dayaji mgnr Yayi saurin sakin hijab din nabla .. yana soso keya.. Daman iskancin da kuke yiwa mutane a gida kennan idan bamunan ?

 .. nablah najin hk jikinta yasoma rawa rawa  hawaye suka  cicciko a idanunta tashiga furta kalmar inna lillahi wa inna ilaihi rajiun abinda take gudu kennan gashi yafaru .
 shiyasa take son raba kanta da kB da wata alakar    soyayyar dayake son damunta daita  .
tun Bai jawo mata tashin hankali da maseefa  ba. km tacigaba da rayuwarta har zuwa sanda ummi zataje India ta dawo takama gabanta ..

Shima kB  take  jikinshi ya dauki rawa jin lafazin  mdm  zeenat din .

kuna jina inagn  kunmin shr awa tsofafin kurame abinda kukeyi kennan ko?
 Kai Kabir da kake son  bata rayuwar  yarinyar mutane idan kawarka  akayiwa hk zakaji dadi?
Tsit kake jin mlm kb bbu 'bakin mgn .
Idan sonta kake ai bata Haka  zaka biyo ba?
   ke km karamar Yar iska may hijabin sharri maimakon ki dauke Dan iska da double slap  amman dayake kema isakarce  Yar,uwarsa sai  kikayi  tsaye kina kallonsa.
 jin hk Yasa Hawayen dake makale a idanunta samun damar zubowa sharrrrrrr.....muryata cike rudani  da in inna tace wa..ll..ahi   wlh aunty ba abinda kike tunani bane  Na rantse miki da girman  Allah bbu komai a tsakaninmu wlh shi.... yimin shr stupid girl kawai "sannan ta juyo tana sake  kallon inda kb ke tsaye  ya kasa cewa komai .
gabadaya kunyar mgnr zeenat tasa shi jin wani iri ajikinsa  ya dinga ji tamkar kasa ta tsage yashige ciki.

 daga yau kB banason sake ganinka da yarinyar nan  ,ko sbd Kai aka kawota aiki gidan nan ?

Bakinshi Na rawa yace a,a madam  to karka sake Na km ganinka daita.
 idan ba hk ba wlh you be fired .
Tana kaiwa  karshen mgnrta ta juya tashige 'cikin.


 nablah dake tsaye tana xubda Hawayen takaicin abinda kb yajanyo mata. 'cikin kuka tace kaga irinta ko kb ?
 kaga massefar da kakeson jefani ciki ko?
 amman bbu komai Na gode da abinda kayi min da kabarni nayi tafiyata da yanzu  hk bata faru dani ba.
  kiyi hakuri nablah wlh nima ba  hk naso ba .

bbu wani hkr dazaka bani kawai Ni  ka cuceni tunda kabari akayi zargini akan abinda bantaba aikatawa ba  . Daga karshe Ina hada ka da  girman Allah kafita harkata ko gaisuwa Na yanke a tsakaninmu ta juya ahankali tasoma daga kafafunta tana kuka da takaici zargin da zeenat tayi mata .


Bangaren zeenat kuwa tana shiga main parlour din gidan  ta tadda ummi   tana kallo bata lura da deeni dake kwance a gun ba .
Kallo ma kike ummi ana shirin yimana fasadi  acikin gida ?
ummi ta juyo da sauri gabanta Na wani irin  faduwa ,da kyar tace meya faru zeenat?
Me kika Gani ?

 uhmmmm wlh wancen Dan iskan  yaron may wanki ne.
 may yake da suna ma , da Ni har Na manta  sunanshi ummi  tace kB yauwa wlh ummi yanzu nan naganshi rike da hijab din yarinyar nan nablah.
 daidai nan DEENI dake kwance ya Dan maida hankalinsa kansu    gabashi wani irin  dukan  uku uku .
Take  zuciyarsa tashiga   bugawa da sauri da sauri tun Bai ji me zata ce ba . da kyar yacigaba da jan numfashi  . 

zeenat tacigaba wlh ummi kibaria a sallami yarinyar nan  kawai tun kafin ta daukowa mutane magana azo ana kuka damu .
 nidai wlh bbu ruwana bbu hannuna ciki.

 Dan Allah mlm kiyiwa mutane shr idan bazaki fadi alkhari ba inji cewar ummi Ok hk ma zaki ce ummi ?
to nayi shr bazan  sake ganinsu nayi mgn ba. duk abinda yabiyo baya .... ummi ta katseta ta hanyar cewa bbu abinda zai biyo ba sai alkhari hb mamana meyasa kike yin hk ne ?

DEENI da gabadaya hankalinsa yasoma barin gangar jikinsa ya  gyara  kwannciyarsa  kan three sit tare da runtse rikitattun idanunsa gam batare da yace komai ba sai numfashi yake fiddawa .

 ummin taja bakinta tayi shr  tunowa datayi DEENI   na kwance a parlour Dan gabadaya zeenat dince ta rikitata Dan  batason DEENI yaji komai . ahankali ummi ta juyo inda yake kwance ganin bbu wata alamun yaji wani abu  Yasa ta sauke ajiyar zuciya  wa tunaninta Bai ji komai ba tayi zeenat alamun tashiga hankalinta  itama zeenat din sai lokacin ta lura dashi amman bata damu dayaji ko kada yaji ba .tunda tasan shi ba may shiga shirgin mutane bane .
amman bata sani bane kwance kawai yake runtse da idanunshi amman gabadaya hankalinsa yana tare dasu tare da jin jikinshi  tamkar ana watsa masa garwashi wuta. 

 ...jiki a matukar sanyaye nablah tashigo parlour,n kanta akasa sbd duk taji abinda zeenat din  ke  fadawa ummi .
Dan hk tasa guri tarakube kanta jikin Bago parlour,n Banda kirrrrrrma bbu  abinda ilahirin  jikinta keyi .
 Ga zufa sai keto mata yake ta koina ajikinta .

Tsayuwar me kikewa mutane a wajen ki wuce kije kiyi min aiki stupid girl kawai inji cewar zeenat wlh mutuncinki kike zubarwa bana wani ba.

Inda   kinsa karuwanci ne a ranki ai da baki zo neman..... short up there deeni ya bugawa zeenat wata razananniyar tsawa data nemi frigita dukkansu   tsit parlour,n yayi  zeenat ta zuba masa ido tana  kallonshi  da mamaki  .

 kar dai yadaina tsanar yarinyar  kmr yadda ta zata?
 to meyasa zaiji Haushi Dan tace idan tasan karuwanci ne a ranta Kai dole akwai wani dalili jikinta yabata hk.
  dubi yadda kamaninsa suka sauya kmr itace kb yakamawa hijab .
 ya katse mata tunani ta hanyar cewa  Bason shiga shara ba shanu kin gane ko?

Bai jira amsarta ba ya  juyo inda nabla ke rakube yana jifanta da wani matsiyacin kallon take zuciyarta ta motsa.
 tsoro may tsananin yashigeta yayinda hankalinta  gabadaya yakara tashi Tasoma fargaban abinda zai mata.
 ,ganin ya  gyara kwanciyarsa ya juya musu baya.
 Yasa  nablah ta dinga sauke ajiyar zuciya a boye tare da yiwa zeenat din Allah shikara a ranta. kema kiji yadda naji a raina.

Ummi tace kinga abinda nake gudar miki ko mamana amman bakiji mgn idan kika soma nacin mgn bakiji baki Gani .
 ummi daga fadar gsky km sai cibi yazama kari  . Deeni najinta kmr yatashi ya yaryarfa mata maruka ko zata shiga hankalinta .
 amman darajar umminsa yasashi kyaleta  .

Ummi tace Hk ake fadar gsky da wulakancin mamana wannan yarinyar ce karama ahankali zaki  nutsar daita ta yadda zata fahimci ce ki.
 bari Shima kb din zan hada dashi ne  zanshiga tsakaninsa daita.
 zeenat  ta wuce fuuuuuu cike da fushi tayi dakinta .
 Shi kuwa deeni cewa Yayi a ranshi dama kin barshir first love Ni.... nasan yadda zanyi dashi 


Itama nablah lallabawa tayi  tashige kitchen Dan nan  yafi mata saukin shiga akan ta wuce dakinta . 


Karfe tara  Na daren ranar deeni  Yasa akayi masa Kiran kb .
wanda tun lokacin da sakon Kiran boss din  nasa yasame shi ,yasha jinin jikinsa.
Km  hankalisa yayi kololuwar tashi fiyye da tunanin may karatu .

kb   durkushe gaban boss dinsa tamkar Wanda zai yi masa sujjada tare da sunkuyar da kanshi kasa sosai  yana kallon center rock din dake shimfide a gurin.
 yayinda DEENI ke zaune kan kujera may zaman mutun daya system ne a gabanshi yana aikin tura sakwanni ta yanar gizo.. kwata kwata yi yayi tamkar Bai San da zaman wani halitta ba agurin asalima gabadaya hankalinsa baya 'cikin parlour,n Kusan awa daya da wasu Yan mintina sannan ya dago rikitattun idanunsa ya zubawa kb yana kare masa kallo may tattare da tsantsar tausayi..... domin shine dalilin zuwansa   'cikin estate din .
km zamansa yake amman a yau yana jin bazai  iya cigaba da zama dashi ba.
 deeni ya Dan gyara zamansa tare da dauko wani envelop ya bude bakinsa  da kyar  Kira sunan  kb ......
kb yayi saurin dagowa tare da amsawa yana duban boss dinsa a tsorace ... deeni ya Miko masa envelope din batare da yace masa komai ba .. jikin kb Na rawa yasa hannu biyu yakarba yana sake duban deeni .

Deeni ya numfasa tare dayin gyaran murya sannan  yace  yau  jumma'a  km yau ce ranar daza bar aiki tare dani kb .sakamakon son shiga gonata dakake kokarin yi .
amman dana son zan iya hukuntaka da hukunci mafi  tsananin .
amman nakiyi sbd kana bani tausayi Dan hk  Ga  wannna emvelope din.

 check din million biyu ne ciki  naba nasan zasu  isheka kaje  kacigaba da rayuwarka tare da kula da mahaifiyarka da kannenka ...
.tun kafin DEENI yakai karshen mgnrsa hawaye sungama wankewa kb  fuska bakinsa na rawa rawa  yace Dan girma Allah boss kayi hakuri duk da bansan gonarka danake kokarin shiga ba  wlh ko nashiga ginar ma  abisa rashin sani ne boss .
 kb yakarasa fadar hk yana may  zubda guntun wahaye  .
uhmmmm deeni ya girgirza Kai.
 Kai dai ka tafi kawai kmr yadda Na umarceka idan ma kudin ne suka maka kadan ka sanardani zan kara maka .
  km ko ba yau ba duk sanda wata lalura ta sameka kana iya samuna zan taimaka maka  tunda tun farko nayi niyar yin hk .
Allah sarki kb sai kuka yake yana bawa deeni hkr amman Ina... deeni Bai km sauraransa ba tunda yagama mgnrsa ta karshe .

Dan  hk kb ya Mike jiki a sanyaye yana kallon deeni ya bar parlour,n tare da tunani iri iri akan wacce irin gonace yake son shigarwa may gidan nasa ..
Da wannan yabar gidan zuciyarsa tap cike da bakinciki rabuwa da may gidansa dan bakaramin karawa yake dashi ba . bai bar tunani da wasi wasi ba har yakarasa dakinsa ...


 Shima deeni Mikewa yayi ahankali  byn kb ya fita ya nufi dakinsa km sai lokaci yaji hankalinsa ya kwanta yayinda  natsuwarsa tasoma dawo gangar jikinsa.

 uhmmmm su oga deeni manyan yan dubiya 😍😍😍 loly





Washegari gari tunda nabla  ta hada musu breakfast takoma dakinta bata sake  fitowa ba.
Koda rana ma  bata bari sun hadu ba.  hk ta dinga wasa buya da zeenat da may gidan  domin bata kaunar abinda zai hadata dasu.


Sannu ahankali  tafiyarsu ummi ke sake motsowa sosai nablah ta km samun ummi da mgnr akan  Dan Allah tabarta taje gida har su dawo amman ummi  tace Aa tayi  ta zauna har su dawo ba dadewa zasuyi ba .
Yanzu idan kika  tafi gida .
 wa zai dinga kula da gidan Ai bbu tsari abar gida hk  bbu kowa ?

to shikennan ummi Na hakura zan zauna har Ku dawo  amman  Dan Allah Kiramin auntyna mugaisa .

 Ummi tayi murmushi tare da cewa  shiyasa nake kara sonki nablah akwai ki  da saukin kai.

Ummi  takira mata  aunty salmah ta Mika mata wayar ta mike tsaye tare da barin  gurin byn aunty salmah ta dauka suka gaisa tare da Dan taba hira da tmbyr mutun gidan gaba..
 duk  kowa lfy yake sai dai  akwai matsala fa  agida gaban nablah ya fadi  amman kada ki damu hjy tace min zatayi tafiya ko ? Nablah ta amsa mata da eh amman da zarar ta dawo zan dawo gida gabadaya Dan gsky nagaji da aikin  nan  wlh .
km wata irin matsala ce a gidan ?
da fatan ba wani abu ne yasamu  baba ko mama ba?
Aa matsalar dai daga baba  ne amman karki damu  idan kinzo zakiji komai ki kwantar da hankali kiyi abinda yakai kinji.
Dan  bakiji yadda hjyr ke yabonki ba .
nan dai sukayita hirarsu sosai wanda  Yasa hankalin nablah kwantawa sosai sannan  sukayi sallama  taje ta mikawa ummi  wayar .takama gabanta.


Yau bbu kowa agidan daga ita sai laraba dake BQ .
Km tana zaton may gidan ma yafita tuni  Dan bata ji motsinsa ba .
Dan hk  ta fito ta kulle gidan gabadaya takoma sama  tasaka garen wondo jeans da Yar shit .

 gurin TV ta nufa ta kamo tashar tinwatinwa  ta dinga tikar rawa da iyakacin karfinta sai da taji tasoma jin juwa  tukun saurarawa kanta  daga karshe  tashige Jim din deeni Da karambani irin nata ta dinga  motsa jikita  wani abun ma batasan yadda ake amfani dashi ba amman dayake wayayyiyace  hk taita motsa jikinta .. ashe duk abinda take deeni Na zaune yana kallonta ta 'cikin CCTV camera dinsa.. girgirza Kanshi  kawai yayi tare da tabe bakinsa.
 yanzu ko 'cikin tasamu taya zai zauna ajikinta da wannan iskancin datake?
 ya fadi hk a kasan ranshi hk tacigaba da tsalle tsallenta a cewarta tana  motsa jiki .
 birgeshi yarinyar keyi ko sha'awarta  yake,?
 shi dai Bai sani ba.
 km bashida wanda zai bashi amsa.
  yana nan  zaune yana kallonta har tazo tacire kayan jikinta  ta ajije ta saura bbu komai ajikinta..  zigidir daita  tashiga wanka ya daina gani abinda take yana nan zaune ta fito daure da towel tana goge jikinta ta shirya 'cikin wani  arnen  wando da riga.
Yayinda  gaban rigar a tattare take tamkar breezy ..
 safeena ce tabasu da wasu kannun  kaya masu yawa daman Ga nablah mayar son English dresse ..
 kayan  sunyi matukar yi mata kyau .

Ta kama gashinta a  tsakiyar kanta tayi kyau sosai ita kanta Bai sai angaya mata ba tasan ta hadu iya haduwa ..
 'cikin hk taji karar Bell yacika gidan ..
 yana kallonta 'cikin sauri takarasa shirinta  ta dauko zunbulalen hijab dinta ta zira  tayi hanyar  downstairs da sauri har hijab dinta Na harta .



MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
       💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO



Page 79


Gyara hijab din jikinta tayi sosai tare da fito da Zara zaran yatsun hannuta sannan tasoma taka step ' biyu biyu cike da hanzarinta takarasa 'bakin kofar ta bude .



Zeenat ce tsaye  ummi da safeena suna tsaye a bayanta sai faman  yatsina fuska zeenat din keyi ,domin ta tsani abinda zai hadata da ganin fuskar yarinya ko a da.
Ballanantana km  ,yanzu da take jin  tsanarta na nunkuwa a zuciyarta fiyye da duk wani abu data tsana a rayuwarta  sakamakon  ganin da tayiwa yarinyar  da kb.


  sai cika take tana sake  batsewa     .
  ganin irin kallon da zeenat din ke aiko mata da shine Yasa gaban nablah faduwa da sauri wanda kusan  itama akaron kanta batason abinda zai dinga hadata da madam din  ..
  amman bbu yadda ta iya da rayuwarta dole sai haduwarsu takasance as far as tana zaune gidan .  dayake Allah yayi nablah da karfin hali sai ta dake tamkar bataji komai ba ajikinta  .
  "muryarta a sanyaye tace sannuku da zuwa tare da karbar bakar ledar dake rike a hannu zeenat din zata karbi handbag din hannuta ta hanata tasoma kokarin sanyo kai ciki parlour Dan hk  tasa nablah yin saurin koma Daga ciki da baya Dan basu hanyar wucewa .

Daya byn daya suka  shigo suka zauna da kyar suna sauke numfashn gajiyar dake tattare   dasu.
 A natse nablah  ta sake cewa    sannuku  da zuwa, ummi ce  kawai ta amsa mata da yauwa nabla sai safeena.. amman ita zeenat kwata kwata ko kallon inda take batayi ba ballanantana tasakawa ranta zata amsa wanda itama hakan Bai dameta ba .

Nablah nagama fadar hk ta juya ta nufi kitchen Dan shirya musu dinning wanda oready tarigada tagama  girka musu abinda zasu ci .
sai data shirya dinning sannan ta dawo inda suke tace ummi abinci yayi ready.
 yauwa nablah sannu da kokari kinji har 'cikin ranta take jin dadin yadda ummi din ke mata .
  ' ta juya zata koma kitchen taji sautin muryar zeenat ke.....nabalah ta juyo  taja ta tsaya tare  da bata dukkan wani attention dinta batare da ta amsa mata  ba .
tunda tasan sunan datake kiranta dashi kennan ko baiwa .


 ..take this key go and park my logiest in side my car ahankali jikinta a sanyaye tasa hannuta ta amsa key din motar  .
ta nufi kofar fita waje ummi dake zaune tana hutawa tace maza safeena bita ki tayata shigowa da kayan Dan bazata iya shigo da kayan ita kadai ba .


 cike da natsuwa da nishadi suna hirarsu  da safeena suka dinga shigowa da kayan wanda duk  kayan da zasu tafi India dasu ne .

yayinda zuwa lokacin tuni zeenat da ummi suna kan dining ummi kadai  ke cin abinci sai safeena data zo Daga baya .

Amman zeenat Zaune kawai  take akan dining table Ga abinci gabanta taki ci  sai faman yatsina fuska take Dan Sam jitayi bata ra'ayin abinci .

ummi ta dago idanunta  tana dubanta dasu sannan tace  .
  ya kika cin  abincin ba ko duk gajiyar ce hk ?
sai data km yatsina fuska kana tace ko daya ummi .
bana dai najin ci ne kawai.
 to a dafo miki wani abun mana ?
 ta girgirza kanta ummi ta kada Kai kawai sannan tacigaba da cin abincinta..


Nablah tsaye a kitchen hannuta rike da plet wanda  tuwan shikafa ne  gayarta" sai mai da yajin data ranbata ciki.
 da magi "ta yanyanka albasa kanana  ta kwashi kayan makulashen, da safeena tazo mata dasu .
ta  fito ,ta nufi dakinta km duk lokacin oga deeni Na nan hakimce kan kujerarsa ya tsura mata idanunshi ta 'cikin camera'rsa.
 har tashigo dakinta ta  zauna tare da ajiye plet din hannuta da ledarta   ta cire zunbulalen hijab dinta tayi flinging dashi gefe , Tana fidda numfashi Dan gabadaya hankalinta a tashe yake da son cin tuwan, daya zame mata jiki yanzu wanda duk  randa ma ba'a yi tuwan  ba, ji take tamkar zatayi hauka .
sai dai taci shinkafa da yaji da oil.  
 kmr an tsikareta  yaga ta Mike tsaye  ahankali  tana Mika  da jijiga ilahirin  jikinta  alamun gajiya  .

Ahankali take bata step 'cikin takunta Na daukar hankali km koina na motsawa ajikinta.
 fridge yaga ta nufa  ta bude ta dauki maltina da holandia yogurt da zuma ta juyo tana cigaba da girgirza jiki tamkar tasan wani  yana kallonta .

Km  duk wannan lokacin deeni Na nan  zaune yana kallonta da rikitattun idanunshi ya tsura ma surar jikinta may daukar hankali da dagula lissafi ido.
domin duk motsin datayi komai Na jikinta rawa yake yi most especial nonuwanta dake cike bamm da kirjinta wani irin zirrrrrrrr yaji tundaga tsakiyar kanshi har kan joystick dinsa ya Kai hannu kan joystick dinsa ya dafe  yana gyara mata zama da kyau .

ita kam Ina tasan yana gidan ma  har yana kallonta sha'anin gabanta kawai take hankali kwance.
   har ta  zauna kan bedside ta bude maltinarta ta juye duka 'cikin cup da zuma sannan ta bude kwalin hollandia Shima  ta juye rabi  ciki.
  idanunshi kyam akanta har bai son abinda zai yimasa shamaki da kallonta   ..
shi kam dariya ma abun nata yaso,bashi .
ganin   yadda ta tara abubuwa a gabanta tana kokarin turawa cikinta .
ya  girgirza Kanshi  a hankali Ya furta wannan yarinyar batada wata matsala a rayuwarta asalima a kallon dayake mata bai hango tana tattare da wata  damuwar duniyar nan  ba .
  a natse yake  kallonta  tasoma cin tuwanta tana shiiiiii shiiiii da bakinta alamun yaji yayi yawa ciki, har tagama cinye tuwan tasssss ta lashe plet din tasssss .
ta dauko holandia dinta datayi missi da yogurt da zuma ta juya da spoon suka hade waje daya ta kafa Kanta ..
 bata ajiye cup din  ba ,sai data shanye  sannan ta km Mikewa tsaye da kwalin hollandia a hannuta   tashiga jujjuya jikinta a hankali.. can km yaga tafara tikar rawa bbu kidi da bakinta kawai take wakar tana tikar rawa  Daga karshe ma ajiye kwalin holandia tayi tacigaba da tikar rawa bata ji bata Gani.

 shi dai ya zuba uban tagumi yana kallon yarinyar daya tsana tare da mamakin dama Haka take da son rawa maseefa kmr ba daxu nan tagama tikar rawa a parlour ba.
  lallai zeenat tayi gsky data kirata da may hijabin sharri .
duk da kasancewarsa mutun marason hayaniya da rashin son shi da mace may son rawa amman sai yaji yarinyar ta Dan birgeshi.
 wanda a da komai nata Haushi yake bashi ba. yanzu kam yasan bawai yana son yarinyar bane amman komai nata yana bashi sha'awa ..

La'asar nayi tashiga kitchen domin daura girkin dare.
 Shima sai lokacin yasamu damar  fitowa  da shirinsa Na zuwa masjid.
 Sam ita batasan yana gidan ba .
sai yanzu da take ganin saukowarshi Daga step.. hankalinta yayi mugun tashi gabanta yashiga dokawa da sauri  tare da mamakin daman yana gida bai fita ba .
 ta kunna kida a gidan  Tasha rawarta yadda ranta ke so  ?
  tmbyr datayi  kanta kennan take zuciyarta ta bata amsa da may be bacci yayi may nauyi  shiyasa sautin bai dame shi ba.
 wayyo Allah Nagode maka.
 da baiji ,dana sha maseefa  mugun mutun kawai may kama da horo.

 ta gabanta yazo ya wuce sai kamshi turarensa Hamilton's yake zubawa takoina .
gabanta ya tsananta faduwa da sauri kmr yadda Shima yatsinci kanshi ciki jin matsanancin faduwar gaba.
 bata gaida shi ba sai ma dauke kanta datayi gefe ...



Misalin karfe tara Na daren ranar deeni kwance a parlour,n sa kan three star yana kallon tashar CNN yayinda gefe daya km hankalinsa da tunaninsa gaba daya baya gurin TV  yana gurin  yarinyar da yake jin ya tsana.
 ,gabadaya kewarta ce ke dawainiyya da zuciyarsa da gangar jikinshi .
Wanda yarasa dalili dayasa yake yawon jin hk a tare dashi acikin Yan wannan lokacin.

 sosai yayi zurfi 'cikin duniyar tunaninta .
'cikin hk  zeenat ta fito parlour,n bbu kowa sai shi data hango kwance. 
 a hankali tasaki murmushi tare da  takarasa inda yake ta dau remut takashe TV sannan ta kwanta flat bisa fadadden kirjinshi tasoma wasa da wasu part din jikinshi .
ajiyar zuciya ya sauke da karfi gaske ,sannan ya zuba mata rikitattun idanunshi da suka gama rikecewa suka canza kala tsabar jaraba dake cinsa .
...a sukwane ya cusa hannushi 'cikin sumar kanta yasoma yamutsawa ahankali yana lumlumshe  rikitattun idanunshi magana yake son yimata amman yakasa Dan bazai iya furta komai  ba a halin dayake ciki.
 koda yace zai yi mgnr ma muryarsa bazata fito ba .
Dan hk ya daura lips dinsa kan nata yashiga tsotsa 'cikin iyawa da kwarewa.
cikin wani irin mutuwar jiki yana jinta ta sake mannewa ajikinsa tare da shafa joystick dinsa dake Mike tun kafin ya kwanta ajikinsa  ya lumshe idanunshi da kyar ya samu ya furzar da iska may zafi.
 jikinsa a mace  ya zare  bakinsa 'cikin nata  kana da kyar mgn dayake son yi, fitowa  yakira sunanta zeenat......da muryarsa a dashe tamkar ta mashaya 'cikin kunneta yashiga yi mata mgn  please stop this  now..kinsan fa bamu kadai bane a gidan kibari muje Daga ciki .

tana jinsa tayi masa shr tare da cigaba da wasa da joystick dinsa tana mammatsa kan kaciyarsa ta 'cikin Three quarter,n dake sanye a kungunshi.
 dauke numfashi yayi Na  wani lokaci sannan Daga baya  yacigaba da numfashiwa ahankali ahankali ,kana ya sake  fizgo wata mgnr da kyar zeenat at anytime wani Daga 'cikin su first love zai iya saukowa fa.... amman Ina tayi nisa da kwadaituwa da mijinta duk wani  bayaninsa baji take ba  burinta  kawai tajita tsundum 'cikin duniyar maaurata .
kalmar dayake ta nanata mata  Keenan 'cikin Dan fitar da sautin muryarsa  domin gabadaya sha'awa ta dasar masa da murya .

cigaba kawai tayi da aika masa da zafafan wasanninta kala kala wanda suke sake kashe masa jiki Daga karshe ta sake  hade bakinsu waje daya ta kamo lips dinsa cikin kwarewa  tana tsotsa tana sake narke masa tana  romancing dinsa Shima sosai yake jinsa on top ..yasoma maidata mata da martani 'cikin zafafan wasannisa masu birkita mata brain bakajin komai a parlour,n sai sautin  nishinsu  dake fita ahankali ahankali yakasa tsaida hannushi guri daya sai shafarta yake .

 ahankali yasoma jin kmr motsin saukowa Daga step cak ya dakata da abinda yake  tare da son kokarin rabata da gangar jikinshi amman ta manne masa gam 'tamkar cungum sai aikin shafa duk inda hannuta yacikaro dashi ajikinsa take.
 tana fidda wani irin numfashi har mai shi yakarasa  saukowa gabadaya bai samu nasarar rabata da gangar jikinshi ba .
a sukwane ya juyo domin ganin kowaye 'cikin mutane gidan nablah ya gani tsaye tana masu wani irin duba may cike da tsansar tsana da mamaki.

 wacce yunwa ne  yatasota Daga bacci.
 ta fito Dan samawar cikinta  abinda zata ci .
ta iskesu 'cikin wannan halin  .
take yaji gabansa yayi wani irin mummunar faduwa wanda bai San dalilin jin  hakan Ba  .

Cigaba tayi da kallon   yanayin da suke ciki a parlour take ,byn tarin daku nan dake gidan duk bai isheshen  ba sai sun zo nan .
su ma  rasa inda yayi musu dadin kasancewa tare  da junansu  sai  main  parlour ,n gidan  wato kowa ma yazo  yaga abinda suke aikatawa.

  ido 'cikin ido nablah da deeni ke kallon juna Harara ta zabga masa tun kafi shi ya rigata aiko mata, Dan tasan kadan Daga 'cikin halinsa ne.
 ta tabe bakinta tana  ja tsaki ahankali yana kallonta tasoma kokarin shigewa kitchen tare da cewa Yan iskan mata da miji kawai ....

Karaf 'mgnr ta fada cikin kunnenshi yayinda zeenat kwata kwata batasan a duniyar datake ba tun kafin takarasa shiga kitchen din taji sautin muryarsa data fito da  kyar ke............. Cak ta tsaya tare da juyawa tana sake zabga masa wata uwar harara yayi mamakin yadda take kallonsa a wulakance sannan yace mekeke cewa ?

A frigice nablah take kallonsa Dan batayi tunanin zai jiya ba  .
Ko zai ji abinda tace ba kasancewar can kasa makoshinta tayi mgnr .

Muryarta Na rawa tace Ni fa bance komai ba. nace kizo nan yana nuna mata kusa dashi da hannusa tare da kokarin mikewa zaune da zeenat din manne  ajikinshi.. Haushi ya sake turnuke zuciyar nablah ganin sunki rabuwa da junansu.
 ita kam zeenat sai faman aikin romancing din mijinta take duk da zuwa lokacin tasoma sanin abinda ke wakana a parlour,n
 jin yarinyar datafi tsana  ce a rayuwarta  Yasa ta sake Lafewa ajikinta mijinta ..

Bazakizo ba?
 yana sake  maimaita hk   a fusace  ..
Jikinta yasoma rawa Dan Allah kayi hakuri zanzo amman wlh Ni  tsoro nake ji .
ok tunda bazaki zo bari Ni Na taso da kaina.
 ai nablah Na ganin yasoma kokarin mikewa tare da raba zeenat da jikinshi wacce ta sauke wata  naunauyen ajiye zuciya Dan rabata da Yayi da jikinshi .

 ta kwasa da gudun maseefa tayi hanyar step Shima ya biyota  bayanta da sauri abinka Ga dogon mutun km jayent .

Tana gama shiga dakin ta maida kofar da sauri tana kokarin yi mata key ya bamko dakin yashigo yana mata wani irin duba tare da maida kodar ya rufe da key .
 ya nufota gadan gadan .
A gigice nablah ta rike fuskarta hade da sakin kara lokaci guda ta nufi bathroom Dan neman tsira ... fincickota yayi yana huci ta fado saman fadadden jikinsa wani irin shocks sukaji a tare kuka   
 ta fashe dashi Dan Allah kayi hakuri me nayi maka kabiyo Ni har daki ?

A halin  banyi maka komai  ba.
 Ahankali take raba jikinta danashi tashiga  ja da  baya da baya Shima yana binta har ta  kai jikin bango .
 yayi kusa daita sosai lokaci daya taji ya damki kugunta gam ya rike yana mata wani irin duba may cike da tashin hankali bata taba ganinsa 'cikin wannan yanayin ba sai yau aiko take takara sautin  kukanta  tana kokarin son kwatar kanta Amman takasa 'cikin wani irin huci  ya matso da fuskarshi daf da nata  suna fuskantar juna har tana saukar  hucinnsa a fuskarta kafin Daga baya  yasoma mgn  mu zaki cewa Yan iskan ?
 yana karasa fadar hk yayi jifa daita saman bed kafin yasoma nufota tashiga ja da baya tana girgirza masa kai tana hawaye sosai ya matso  kusa daita yana sunce belt din wandonsa .
Tayi saurin cewa  Dan girman Allah kayi hakuri kada kadake Ni .
jikina bayason duka.
 Allah ko ?

Yar talaka tukuf dake zakice jikinki baison duka ai ki kwantar da hankalinki ba dukanki zanyi ba ya sake yin kusa daita ya durkuso suna facing juna lokaci daya ya damki sumar kanta tuni fuskarta ta canza launi ta dawo kalar tausayi..Ya zuba mata rikitattun idanunshi yana kallon yadda kamaninta ya sauya.

 you see zakisa nayi hunting naki.... meyasa zakice mana Yan isaka? yakarasa mgnr yana sake jan sumar kanta  ta girgirza masa kanta Dan kasa mgn tayi  tsoro da fargaba ne suka mamaye zuciyata da km rashin sanin abinda zai faru   
 gabadaya hankalinta ya sake tashi matuka  .

 Wel ki natsu da kyau ki cire wannan tsoron da nake hangowa a idanunki   Dan ba dukanki zanyi ba iskanci da kikara ma,aurata dashi zanyi dake a yanzu so that once kema zaki karar da kintaba yin iskanci..

 although ma ai kina yin iskanci ko bakiyi ?
Ta girgirza masa kanta da sauri .
 Allah ko..
 to bari yau kawai Na koya miki yadda akeyi stupid girl kawai ya soma kokari Cafkota zuwa jikinshi  ta zame  da sauri ta  diro Daga kan bed din tana yarfe masa  hannuwanta dukka  tamkar yadda kananan  yara kanyi idan sun tsorata .





MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
       💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO




Page 80


Ahankali yasoma Daga kyawawan Zara zaran yatsun kafafunsa zuwa Inda take.
  Yayinda nablah dake tsaye kirjinta  yacigaba da bugawa da sauri da sauri . 
 "hankalinta yayi matukar mugun tashi da ganin yanayinsa .
 ta  kalleshi da shanyayun idanunta da suke a tsorace domin  son tabbatar da abinda yake shirin aikata mata.

 ganin da gaske yake. sbd sake motsawa da yake yi gareta,  Yasa muryarta a dake km atsorace tace Dan malam dakata .....wlh  karka sake ka motso inda nake ko ance maka Nima Yar iskar ce irin ku? 

 uhm Yan iska muke  har ke ma ...domin kema kina yin naki iskanci a boye ...   shiyasa kema yau kawai nake son  nayi iskancin dake a bayyane  so that kema zaki karar watarana  .
  "yana gama fadar hk yasoma balballe boturar gaban rigashi da hannuwanshi duka.. faffadan kirjinsa may cike da yalwan gashi suka  bayyana.

 aiko tana ganin hk hankalinta ya sake tashi matuka, tayi  saurin runtse shanyayun idanunta , sannan ahankali ta bude su fess bisa kirjinshi .

take  ta sake aro wata  jarumta  ta sanyawa gangar jikinta kana ta bude bakinta da kyar tana jan tsaki tare da zabga masa wata uwar harara....  tace Dan wulakanci kawai  da kake kokarin son keta min haddina, ta hanyar yin iskanci dani Ni matarka ce?
 ta fadi hk tana nuna kirjinta .
Ya dage mata girarsa daya tare da kashe mata idonsa daya ,Alamun eh .

A tsorace tasoma   girgirza masa kanta wlh A,a karya kake bazan taba kasance hk a gareka ba .
 garama ka koma wajen matarka. amman wlh bazan bari ka aikata wani abu dani ba.
  tasoma wage wage a dakin Dan neman tsira Daga maseefar dake son kusantota .
  "tayi wuf ta sake nufar bathroom ganin yakusan isowa gareta.
 yasa hannusa daya ya  riko hijab dinta  'cikin zafin nama.
 tayi luuuuuuuu zata fadi Allah Ya kiyaye bata Kai ga kasa ba  ta tsaya cak  da  kafafunta .

ya fixge hijabin dake sanye a jikinta  tare da yin filinging dashi yana aiko mata da wani irin kallo may tattare da tsabar sha'awarta .

Ta kwalla wata irin  razananniyar kara...wanda har ya fargar da safeena dake kwance a dakin ummi tana chatting a wayarta .

hatta zeenat dake kwance a parlour,n kasa  sai datajiyo sautin  karar nablah ,dadi yakamata sosai , ta saki Murmushin mugunta .
 tare da cewa yau yarinya kashinki ya bushi a gidan nan, tunda kika shiga track din deeni .
Allah Yasa ya miki mugun duka daga karshe ya  koraki   gidanku gaba daya Na huta  .


Safeena dake   zaune a dakin ummi , ta Mike tsaye tana duban shashin da ummi  ke  kwance .
 baccinta take sosai har da munshari  wanda hakan ya tabbatarwa safeena bataji   karar sautin nablah  ba .
Dan  ko  motsawa ummi ba tayi ba  .
Dan hk itama bata wani tasheta  ba .
Tabarta tasamu   wadataccen   bacci . 
Ta fice daga dakin 

Allah sarki nablah...
 rasa yadda zatayi da rayuwarta  yasa takoma  da baya da baya ta sake  manne jikinta da  bago dakin .
  Tana masa wani irin  duba cike da tsansar  tashin hankali da matsanancin tsoro.
  jiran kawai take taga  yadda zaiyi daita .

 rikitattun idanunshi ya tsurawa surar jikinta  ganin komai na jikinta a bayyane .
Yar yololuwur Riga baccin dake  jikinta ta manne mata sosai...  wanda hatta kan nipply dinta Bai tsira ba yana hango  tsukakun kan nonuwanta.

 sosai yake kallonta  tsirararta yayinda wutar  sha,awarta ke sake taso masa tana sake  tunzurashi zuwa gareta .
  ahankali ya hadiye wani miyo  daya tsaya masa a makoshinsa . kana ya koma lips dinsa Na kasa duka ya turasu cikin bakinsa yana tsotsa ahankali ..ya yacigaba da kusanto inda take.

 gabadaya Atsorace take daganin yanayinsa  takasa koda kwarkwar motsi ballanantana ta tsirar da kanta Daga gareshi  ..
har yakaraso inda take tsaye aiko yana zuwa bai tsaya wata wata ba ya hadeta  da kirjinshi ta sake sakin wata  karar.... lokaci daya kwalkwaluwarsa  tagama birkicewa jin tudun nonuwanta saman kirjinshi..
  " gabadaya ya rude ya susuce ya fita haiyacinsa bbu abinda yake so da bukata  sama daya fara soma sarrafata.
 'cikin wani irin shauki ya sake matseta da jikin bago yana fidda wani irin numfashi may gyaraye da zafi  zafin dadi.....daidai wannan lokacin safeena takaraso 'bakin kofar tana Kiran sunanta ..
Agigice nablah ta kallo kofar da sauri   tana shirin amsawa kennan yayi saurin hade bakinsu waje daya..
Cike da jarumta   tasoma kicin kicin kwace bakinta Daga nashi ..amman takasa sbd yadda  ya rike 'bakin nata gam...'cikin sa'a ya capko laulausar harshenta jikinsa har rawa ..rawa.. yake ya makaleta gam yana wa 'bakin nata  wani irin tsutsa Na fitar hankali ...
 
Jin  motsi kicinniyar da safeena ke ji ta 'cikin dakin. yasa taki wucewa ta sake Kiran sunanta nablah nablah  !!! 

 Uhmmmm uhmmmm tana kokari son fixge jikinta Daga gareshi . Amman Ina oga deeni bbu sauki sai ma toshe mata hancinta dayayi ganin bazata bashi hadin Kai ba .
Take  nufashinta ya tsaya  cak ...Tana shirin barin gangar jikinta ...Ai bashiri ta bude  bakinta sosai  tana  fidda numfashi .
 hkn ko yayi masa dadi yacigaba da sararfa harshenta 'cikin nasa yana mata wani irin tsotsa Na fitar hankali tare da tattaro miyon bakinsa ya dinga  zirara  mata 'cikin nata... Dole tasa nablah tashiga  hadiye miyonsa batare da tashirya yin hkn ba. yayinda km sakwanninsa  kebin kowane loko da sako na gangar jikinta Shima km abinda yake so kennan ta amshi sakwaninsa ta yadda dole tasoma jin feelings akansa.

nabla ...meke faruwa dake ne ? Inji cewar safeena  Tana nocking din kofar...
 nablah najinta km tanason yin mgn amman bbu dama.
  jin shirun Yayi yawa ne  yasa safeena  kama gabanta takoma daki..

Ahankali ya sakar mata baki tare da sauke naunauyen ajiye zuciya.
Ahankali 'cikin mutuwar jiki ya juyo daita ya manneta da faffadan kirjinsa yana gogo mata gashin dake kwance a faffadan kirjinsa atare suka  jin wani irin shock tamkar an jona jininsu da electric shock ..take tsigar jikinsu gabadaya ta Mike tsaye yrrrrrrrrrrrrr   shr sukayi suna maida numfashi sama sama ....'
cikin sanyi jiki ya daura laulausar tafin  hannushi saman mararta yana shafawa ahankali ahankali yana lumshe rikitattun idanunsa kokarin janye hannushi tai amman sai taji ya rike hannuta gam da dayan hannushi,  yana cigaba da shafa kasan mararta, ya Dan matsa kasan mararta kadan  dayaji Alamun kmr Yayi tauri.
 ta saki Dan kara mara sauti kana  Yayi kasa da hannushi ya tura cikin pent dinta, yasoma  shafa gashin dake kwance a kasanta tare da  kokarin zira  fingers dinsa cikin jikinta.
 ta kamkame jikinta guri daya taki barinsa yakarasa inda yake son zuwa.
  tare da fashewa da wani matsanancin kuka may cin rai .
muryarta a razane tasoma mgn Dan girma Allah Na rokeka kada kayi iskanci dani kaga Ni yarinya ce karama da bansan komai ba please... please...
'Cikin wata irin  murya may saukar da kasala yace shiiiiii  ai nasani to meyye  fito dake 'cikin wannan lokacin ? Da har kika katse mana jin dadinmu nida matata ?

 Ta Dan yi motsi da bakinta Alamun zatayi mgn  sai km tayi shr  batare data furta komai ba.
Sai  kirrrrrrma... da jikinta yake .
duk sanyi AC dake aiki a dakin hakan Bai hana gumi tsatsafowa ilahirin jikinta ba """""""""

Dan  murmushi mugunta  Yayi har dimple dinsa ya lotsa batare data ganshi ba .
 yayinda har lokacin hannushi daya Na rike 'cikin nasa km yana cigaba da shafa mararta sannan  km yaki sakar mata hannu daya .cike da tsoron .
ganin yatsansa nashirin ratsa 'cikin kasanta ne tasa dayan hannuta ta rike masa hannu 'cikin cool voice dinta may matuka kashewa mutun  jiki  tace stop please bazan iya ba ..
yadda tayi mgnr 'cikin sanyi  muryarta Yayi tasiri har 'cikin jikin  deeni Dan gabadaya jiyayi  jikinsa yagama mutuwa murus....Bai saurara mata ba yakai bakinsa kan wuyanta yana soucking dinta.
 ita kam bata iya sake cewa komai ba .
sai manne jikinta datayi danashi tana jin yadda yake mata wasu irin abubuwa.
Sosai ya dinga shafa sansar jikinta yana romancing din jikinta. 'cikin iyawa  kwarewa ...
Ya dinga shan bidirinsa shi kadai  yana son ya daurata akan network itama tasoma sabawa. ahankali taji numfashinsa Na fita haka km jikinsa yayi sanyi,  lokaci guda ya dinga sauke ajiyar zuciya yana fidda huci ,ya lumshe rikitattun idanunshi ahankali. muryarsa a sanyaye   yace tmbyrki fa nayi amman kimin shr ko naciga gaba ne ?

Da sauri Ta shiga girgirza masa  kanta Alamun a,a Ok  meye fito dake ?
  ya sake maimaita tmbyrsa 'cikin in ..innanir muryarta tace uh.m uhm .daman yunwa nake ji ne   ....

Yunwa nake ji ya sake maimaita kalmar yana juyo daita suna facing junansu.
 ya tsura mata idanushi kawai yana kare mata kallo may dauke da tambaayoyi iri iri amman bbu damar yi .
 " gabadaya tausayinta ne yakamashi tare da   ratsa kowani sashi Na gangar jikinshi yana
  sarrafa   ' jinin jikinsa ...
sai daya sauke naunauyen ajiye zuciya. fuskar nan tashi  a hade yace muje  kitchen kici abincin .
gabanta ya buga da sauri Ta kalleshi da shanyayun idanunta.
  ya Dage mata girasa daya Alamun eh.. tsam tasha jinin jikinta tana sake  jin yadda tsoransa ke sake bin jikinta tasan may be wata mugunta kawai zai sake shirya mata   .
   take  dabara tazo mata Dan Haka  tace Ok muje ya nuna mata kofar da hannunshi Alamun tayi gaba.. Amman sai ta girgirza masa kanta .
Jikinta a sanyaye tace kai dai kashiga gaba tukun  ,Bai ji komai ba har 'cikin  ranshi,  ya Kai hannushi  zai  kamo nata  tace uhmmmm muje kawai ..
ya bude kofar Yayi kmr taku uku zuwa hudu ,ta juya  da  saurin maseefa ta koma dakin  ..ya juyo da sauri ya yabiyo bayanta Amman Ina... kafin yakarasa bakin kofar har ta rufe dakin da key .
 sai kawai ya tsaya shr ...  yana duban kofar dakin batare da yace komai ba  .
  "  tunanin yarinyar da mamakinta yakamashi  wato nan ganinta   wayo tayi masa kennan ko me ?

ya dage kafadunsa duka  ala,mun matsalar ce . sannan ya laso lips dinsa na kasa tare da   cicizawa ahankali ya juya  yacigaba da tafiyarsa parlour ,n kasa yaje bai Ga zeenat ba .
Dan Haka ya zarce  part dinta  kai tsaye Dan yasanta da saurin bacci  .
kwance ya sameta har tasoma yin, baccin kuwa kmr yadda yayi tunani.. bynta yaje ya kwanta .
ya janyota jikinsa yayi tare da rungumeta tsam yana kaiwa wuyanta sumba ahankali ya fara shafarta hannushi yakasa tsayuwa waje take itama tasoma maida masa da marta wanda daman a bukace take dashi romancing din junansu suke son ransu Daga nan suka afka duniyar ma,aurata  yana jinta sanda tayi relez ya sake matseta ajikinsa yacigaba da murzarta ..



Zeenat kwance a bisa jikinsa tana sheka baccin gajiyar sex din da sukayi Amman shi Sam nashi baccin yayi masa kaura ,bbu abinda yake sai hada pics din yarinyar yake a zuciyarsa Daga sanda tazo gidan zuwa lokacin daya soma ganinta ta fito Daga wanka da km yadda take masa abubuwa a dake bakasafai take shakkarsa ba ya tuna sanda take shagalinta dazu lafiyar Allah  har zuwa abinda ya faru atsakaninsu a yau din nan  ahankali yacigaba da tunanin sanda yake Havin sex daita da irin gudumuwar da take bashi, duk da ba,a 'cikin haiyacinta take ba amman hkn Na matukar gamsar dashi yayi wani irin juyi tare da rungumo zeenat dinshi ,ya samu kanshi da raya yarinyar ce , ahankali ya lumshe rikitattun idanunshi..



Byn kwana biyu .

duk 'cikin kwanakin nan ba zai samu zama ba sbd tafiyarsu ummi dake motsawa  gashi gida da office ayyuka sun cakude masa .
gefe daya km zuciyarsa da gangar jikinshi suna matukar Sha,awar yarinyar tare da kewarta.

 Dan hk ya tsaita camerarsa sosai ta yadda zata dinga daukar masa duk abinda yarinyar zatayi da kyau ..



Yau Monday 'cikin shirin zuwa office ya fito jikinsa sanye cikin wando ash colour da riga Long sleeve pink sai court ashi dake saman rigar . Shigar tayi maseefar karbar jikinsa.
 takoina deeni ya hutu matuka kwawu ne dashi har dana fita fatar jikinshi sai sheki yake da daukar hankali  sai kamshi turarensa  Hamilton ne kawai ke tashi ta koina ajikinshi 
  'cikin sauri yana waya ya fito Daga dakinsa  tun Daga kan step ya hangota sanye cikin doguwar rigar malaria tana aikin goge jikin kujera.

 ya tsura mata idanunshi kawai  yana binta da wani  mayataccen kallo wanda Yasa har tasha jinin jikinta .
Taji ajikinta ana kallonta  ta Dan  juyo ahankali idanunsu suka sarke cikin juna.
 zuciyarta ta buga da sauri.
 tayi saurin fara dauke nata idon yayinda shi km yacigaba da binta da kallo.
Ahankali yake binta da wani irin kallon .
ganin yadda  takara yin  kyau daita tayi fresh sosai jikinta ya sake gogewa sai kyalli fuskarta  take. kasancewar yayi kwana biyu bai sanyata  cikin kwayar idanushi ba .

Ya katse wayar da yake tare da karasa saukowa gabadaya parlour,n zeenat dake fitowa Daga dakinta takaraso gareshi da sauri  tare da shigewa  jikinshi .. har kashirya kennan my hrt ?
Na shirya sauri nake ban coffee nasha ya fadi hk yana may tsaida idanunshi kyam a kanta zeenat tayi sauri ta nufi  dinning area .

Hakika idan dai ba kallon tsoro yake yiwa yarinyar ba ,kallon may shigar ciki yake mata shr yayi yana binta da ido, duk inda tayi acikin parlour  yaki dauke idanunshi a kanta har ta tsargu da irin kallon da Yake  mata ta Dan juyo da niyar satar kallonsa idanunsu suka sake sarkewa cikin juna aiko ta zabga masa wata uwar harara tare da dauke idanunta tacigaba da yin aikinta a natse .. ahankali ya samu guri ya zauna kan kujera yana sauke ajiyar zuciya yayinda zuciyarsa ke cike da tunani iri iri....


  zeenat ta dawo hannuta rike da cup din coffee ta zauna kusa dashi tamkar zata shige masa cikin jikin tare da  Kai cup din  bakinsa  ya bude bakinsa ahankali yana kurbar  coffee din kmr bai son Sha har dai yashanye  sannan Mike tsaye  yana yi mata sallama ya wuce office dinsa zuciyarsa cunkushe da tunanin yarinyar  .

sule direbansa ke tukasa sai securities dinsa dake binsa a baya .
Daidai inda aka saba  parking mota sule ya nufa yayi Parking din motar ya fito da sauri ya bude masa  byn mota sai daya gama sham kamshinsa sannan ya fito  'cikin isa da nuna shi wani ne ..
'Cikin takun nan nasa may matukar  daukar hankali yake tafiya cike da isa da izza ya nufi  kofar office dinsa kasancewar akwai tarin aikyyukan  a gabansa da zai yi .
 yana shiga ya zauna kan kujerarsa yana jujjuyawa ahankali ahankali  tarin file files ne da document wanda zai saka hannushi ciki  zube a saman makeken table ,batare da bata lokaci ba yasoma yin abinda ke gabansa ..


     a yau ne su ummi da zeenat har da safeena zasu bar kasar zuwa kasar ummi ta haihuwa karfe 9:30 am  deeni yayiwa su ummi rakiya zuwa murtala international airport dake garin Lagos  har da nablah cikin Yan rakiya .. lokacin da jirgin kuwa  zai tashi , da kyar deeni ya janye zeenat dake jikinshi tana faman zuba masa shagwaba iri iri suka wuce tana Daga masa hannu . 


Can kuwa bangaren nabla zaune take ita kadai a byn mota tana wasa da yatsun hannuta kwata kwata bata son abinda zai sa takasance tare dashi cikin inuwa daya sbd yadda take jin bbu a dadi a ranta a duk sanda zata kasance tare dashi .
 yayinda deeni da sule direbansa ke gaba sai surutu sule yake zubawa marasa kan gado da ma,ana  amman deeni ya shareshi batare da ya dakatar dashi sbd hankalinsa daya maida kacokan kan nablah dake zaune abaya .
 tsaita mirrow din  yayi sosai ta yadda zai ji dadin kallonta  tare da kafeta da rikitattun idanunshi yana kallon yadda ta dake ta hade ranta tana kallon gefen titi.

 ,sule direba yakira sunanta tare da cewa gsky mlm nablah zakiyi kewar su hjy.

 ta Dan juyo kadan tana murmushi wanda ya bayyana wushiryarta asalin sihirtaccen kyawun fuskarta ya fito sosai .
sannan  tace wlh kawu  sule dayake Haka take ce masa.
 tacigaba cikin zakakkiyar muryarta  shiyasa ma naso komawa gida har su dawo amman bbu komai Ai ummi tace min  bajimawa zasuyi ba sosai  .

hk ne wannan sai dai  zaki Sha zaman kadai ci ,wannan ba komai bane inda da sabo Na rigada nasa ba .
 wai a wace unguwa kike ne a 'cikin garin  Lagos din nan ?  Ya sake  tmbyrta Ta bude bakinta kennan da niyar bashi amsa .. taji deeni ya buga masa wata uwar tsawa tare da ashariyya , a unguwar  uwarka take. kajimin jakin mutun  kana tuki kana damun mutane da surutanka Na banza marasa kan gado. kaki maida hankalinka kan abinda ke gabanka sai zuba kake  ko dobbobi ka kwaso ?

 Muryarsa Na rawa have Sorry boss baza,a sake ba Allah Ya huci zuciyar boss.
 deeni yaja tsaki tare da katseshi ta hanyar taga masa hannushi Alamun ya isa....karka Dame Ni wlh bawani ban hakuri  ...ko yanzu ka Miko min key din motata kayi gaba .
Wlh  sule kaji Na rantse  idan baka maida hankalinka ba ,kakusan barin aiki tare dani....

sule yayi tsit kana ya maida hankalinsa sosai kan deriving .
Nablah dake zaune abaya motar zuciyarta tamkar zata kama da wuta takaici da haushin abinda deeni yayiwa sule ita rayuwarta ta tsani wulakanci da cin fuska .wanda 
wannan  duk halinsa bai dauki kowa abakin komai ba .motar tayi tsit bbu wanda ya sake cewa komai .
  har suka zo gidan ranta a bace yake  wanda Shima ya lura da hakan Amman ya share tamkar Bai San da zaman wata bil Adama acikin motar ba sai ma lips dinsa daya kamo yana tsotsa ahankali   .

Sule nayi parking  nablah  ta da sauri tashiga ciki ta nufi dakinta kai tsaye Shima nashi dakin ya  nufi nashi tare da zubewa kan Royal bed dinshi yana fidda numfashi ..



Karfe 1:30 pm  daidai Na ranar jirginsu ummi ya sauka a kasar india koda suka sauka agajiye dukansu suke Dan Haka wanka kawai  suka fara yi suka kwanta sbd basa tare da yunwa ..




MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
       💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO




*Praise be to Allah who spares our lives till this mement*


 *Taqabbalallahu minni wa-minku may Allah s.w.a accept this worship from me and you may he forgives our sin may we live to witness more wit health*

*happy eid kabir to  all my fans*


Page 81 



Tun byn dawowar su Daga airport ,deeni
ya shiga part dinsa bai sake yunkurin fitowa ba ,har zuwa  sanda ummi takirasa ta sheida masa sun isa lfy .
yana part dinsa  kwance ..


Karfe daya daidai na daren ranar .
 "deeni zaune a tsakiyar makeken royal bed dinshi.
 bbu komai sanye ajikinshi   sai boxes iya cinyarsa gashin jikin nan nasa  masu matukar kyau da sheki suna nan  kwance luf luf dasu abin sha'awar kowace cikakkiyar macce .
 ,  system ne, gabanshi  yana aikin  sarrafata ,ta hanyar   tura sakwanni ta yanar gizo .
, yayinda gefe daya km cup din coffee ne da flasks ajiye akan bed side dinsa , yana aiki yana  korawa ahankali .
Sosai ya dukufa akan abinda ke gabansa  Kawai yaji yarinyar ta fado masa a rai... take gabansa ya yanke ya fadi rassss. Rassss. zuciyarsa tashiga harbawa da sauri  da sauri .
  Cak ya dakata da tura  sakwanni da yake .
 , ya zubawa system din ido  kawai yana kallon  rubutun dake rubuce ciki .
 "zuciyarsa ce tashiga aiyano masa kyawun surar  jikin  yarinyar da yanayin miskilancinta da rashin tsoron dake tattare daita  . 
Wannan tunanin  daya zo masa ne  ya dagula masa  lissafi.
  " ya tsaida gangar jikinsa da barin aikata abinda yake.
 ciki  har da aikin dake gabansa .
shidai a iya sanin  da yayiwa zuciyarsa yasan ba  wai son yarinyar yake ba ....Amman yarasa dalilin da Yasa take yawon fado masa a rai akoda yaushe .
gida da office bashida sakat km  bbu abinda yake da bazata zo ta  hana zuciyarsa tsukune da natsuwa ba .kwata kwata,
Baya samun kwanciyar hankali da farinciki  har sai idan yana tare daita .


Shr yayi a gurin yana  nazarin kanshi da kanshi kafin Daga baya 
 wani irin feeling ya soma taso masa from know there  ahankali ahankali har ya mamaye duk wata kafa dake da tsiro a tsantsar jikinsa.
 ilahirin gashin jikinsa su dinga mikewa daya byn daya .
. gabadaya komai Ya tsaya masa cak  ...

bbu abinda yake so da bukata ahalin da yake ciki wanda ya wuce kasancewarsa da yarinyar.
 'cikin tsanyin jikin  nan nasa yasa hannunsa ya ture system din dake gabanshi tare da  kwantawa  flat akan bed dinshi yana Mika hade da salati.
"  yana jin yadda reaction din jikinsa ke sauyawa cikin lokaci kankani 
 Take  joystick dinsa dake Mike.. tasoma harbawa 'cikin shauki da bukatuwa da muradinta .
a tsukwane  Yasa hannuwanshi duka ya dafe  kan joystick din nasa dake harbawa. yarasa yadda zaiyi da kanshi  gashi kwata kwata  bai shirya zuwansa  gurin   yarinyar  a wannan lokacin ba..

'Cikin wannan halin dayake ciki ne Wani tunani  yazo masa take ya Mike zaune da azama ya kunna cemarsa.
 yaga ko idanunta biyu .
  "zaune ya ganta rungume da hannuwata duka  bisa cikinta yayinda  idanunta ke  runse Alamun may jin  bacci.

 kusan minti biyar tsakani  yaga tasoma bude shanyayun  idanunta 'sannu ahankali har  ta waresu fess a  saman   celling dakin datake zaune  ta zubawa fankar dake juyawa a dakin ido .

Sosai ta tsurawa fan din idanunta kawai tana tunani yadda take jin  cikinta na yawon motsa mata  , ahankali km  take ji wani abu Na jujjuyawa acikinta  tamkar yadda fan din  dakin ke motsawa ahankali.

 muryata can ciki take tmbyr kanta meke shirin  faruwa dani , nablah ?
Meyye acikina da yake yawon motsawa lokaci zuwa lokaci ?


  cike da natsuwa ta Dan  gyara zamanta lokaci daya km  ta karbi sako amsarta Daga brain  Dinta .
akan ta daina damun kanta da tunani "wannan ba wani abu bane , may be  yanayin cimar da take ci  ne ya canza mata halittar jikinta tare  da kara mata    girma.
 dan ahalin yanzu wani irin girma tayi fiyye da tunanin may karatu .

Shi dai  deeni zugun yayi yana kallonta ta 'cikin camerasa .
 "can  km yaga ta Mike zumbur tamkar wace aka tsinkara  ta nufi fridge da sauri , ta dauko   zuma da hollandia yogurt dinta.
ta hadesu guri daya tamkar yadda tasaba yi.
 ta Kai cup din bakinta tana mai runtse idanunta tare da  Sha.
 kunnunwata suka yatsuna sakamakon jin gardin zuma da holandia datayi mixed .

 cikin natsuwa ta,ajiye cup din hannuta  tare da komawa mazauninta ta  jingina jikinta da gadon dakin.
ta  tsurawa kanta Idanu ta 'cikin mirrow dake facing dinta tana kallon Yadda gabadaya yanayin jikinta.
Komai nata  ya sauya tun Daga jikinta fuskarta har zuwa brest dinta da suka sake canzawa da girma  sukayi suntuma suntuma dasu tamkar ana hurasu.
  " Dan kasa tayi da rigar baccin dake sanye a jikinta .
 take nonuwanta masu matukar sheki da daukar hankali suka bayyana.
 so take ta sake bambace  yanayinsu ada ,da yanzu amman sam takasa saida tunaninta akansu .

Wannan abun da deeni yagani .
 Yasa  take wani irin zazzafan  ciwon kai may tsanani ya tasomasa tsabar sha'awarta ,data tsirga masa tun Daga tafin kafafunshi har zuwa tsakiyar kanshi. 
 ya kamo lips dinsa na kasa duka ya tura cikin bakinsa yana cizawa da karfi tare da  Mikewa  tsaye  'cikin layi, dafe da joystick dinsa cike da mutuwar  jiki ya nufi  dakin datake.
 yasoma  nouking  ahankali .

Sanin da nablah tayi bbu kowa cikin gidan Daga ita sai shi, Yasa tana jinshi tayi masa banza sai ma sake gyara zamanta  datayi .
can taji sautin muryarsa 'cike da isa  yace   ke ..kizo ki bude min kofa  ko gidan ubanki  ne dazaki wani kulle?
 muryarta a dake batare da wata tsoro ba ko shakka tace ba gidan   ubana bane" gidanka ne   km baza'a bude ba .

Ok yau ma wani sabon salon  iskanci ne ya motsa maka ,kawani kwaso jiki  ,gani shasha da bansan ciwon kaina ba, sai Na tashi Na bude maka kofa  ko ... To wlh  kasani Ni bana daga 'cikin jerin kalar wa'yan nan mata" marasa aji da kamun Kai"  ballanantana kasamu wannan damar  akaina takarasa fadar  mgnr tana jan mugun  tsaki  mtsssssss  .

 Deeni yayi sokwototo yana sauraronta tamkar wani karamin yaro  batare daya katseta ba har  tadasa aya ,sannan a zafafe yace Dan ubanki ni Keke gayawa hk? Itama a fusace 
 tace angaya maka waye Kai dabaza,a gaya maka hk ba ?

kinsa Allah kika kuskura nashigo dakin nan  batare da kin bude min ba ,zan ci ubanki km inyi iskanci dakike kirana dashi ..
nablah dake zaune ta   gyara zuwa kwanciya kana tace bismilla ina jiranka nima a shirye nake da kai .

hk kika ce?

 tace uhmmmm ance din kayi duk abinda zakayi ciki har da hadani da red card nabarin gidan nan .

 ya sake buga kofar da karfe tamkar zai balla tace wai lafiyarka kuwa yau ?

Dan Allah malama  me  zan maka ne da kake damuna  Na bude maka kofa ?
A fusace yace ubanki zaki min .
Muryarta can kasa kasa ta yadda batayi tunanin jiyota ba tace ba dai ubana ba wlh .

Deeni dake tsaye a bakin kofar dakinta   dafe da jijiyarsa, ya zaro idanunshi waje sakamakon jin abinda tace .
 Da mamaki yace mekika ce ?
 A fusace itama tace 
Abinda kunneka ya jiyo maka shi nace .
 cike da al'ajabinta yacigaba da tsayuwa a gurin yana mamakinta.

Kusan minti Goma  ya dauka yana tsaye ,ganin taki bude masa  kofar ne  Yasa shi  juyawa cikin matsanancin fushi   yakoma dakinsa da kyar ya fada kan bed dinshi yana fidda huci may zafi  .. daman Shima bawai zaiyi wani abu ne daita ba. 
 kawai so yake ya Dan rage zafin sha'awarsa  daita .
 ko zai dan samu relief din feeling din daya bijiromasa.
 tunda yaji muryarta rass daita sannan  idanunta biyu  yasan bata Sha drinks din daya saba mata amafani dashi ba gurin sata bacci may nauyi .

 wannan daren dai gabadaya deeni bai samu runtsawa ba.
 yayi shine cikin tashin hankali. idanunshi biyu sai juyi yake dafe da mararsa  wani irin sha'awarta ce ta dinga taso masa km duk sanda ya duba camerasa zai Ganta  idanunta biyu tana juye juye akan gadonta .
da Alamun itama tsoro ne ya hanata runtsawa .

 bakaramar azabar sha'awa yaci ba a daren ranar .
  koda zeenat ta dinga kiransa ma kasa daga wayar  yayi gabadaya domin yana cikin  halin  tashin hankali..


Washegari tun asuba fari ya fito daga part dinshi ya nufi masjid .
Km Koda  ya dawo ma Daga masjid din bai bawa kansa  wahalar komawa upstair ba .
 ya zube nan  a parlour,n kasa ya  kwanta kan three star  , dafe da kanshi da hannushi daya .
 Yayinda Dayan   hannushi km ya daura shi saman mararsa dake  kulle yana shafawa sbd  joystick dinsa da Mike har lokacin ko zata kwanta .

 
Bangaren nablah kuwa sai da garin Allah ya waye sosai sannan  ta tashi taje tayi wanka tashirya jikinta 'cikin wata haddadiyar  doguwar rigar material  har kasa may rantsin stone  green and white ta gyara sumar kanta ta kwanta luf luf ,kana ta tufke da rebon  bbu  kwaliyar komai a fuskarta ,sai hodar data Dan shafawa fuskartata .  km hakan bai hana ainihin sihirtaccen kyawun fuskarta bayyana ba.
 tayi kyau matuka abunta Kai tsaye parlour kasa ta nufa sai kamshin turaren data fesawa  jikinta ne ke tashi takoina  . 

Da deeni tasoma yin tozali yana kwance akan kujerar Three tsar wanda tun jin motsin saukowarta ya cire hannushi dake saman mararsa ya dan bude idanunshi  yana facing din step din,  ya   tsura mata rikitattun idanunshi kawai yana kallonta.
 tuni gaban nablah yayi wata irin  mummunar faduwa.
 tashiga matsanancin razana da ganinsa .
 zuciyarta  tashiga dukan uku uku taji tamkar ta juya ta koma daki zuciyarta ta kwabeta da aikata hkn ai ma zai dauka taji tsoro ne  da hk kawai tacigaba da saukowa da kyar 
ahankali daga step din har  takarasa saukowa gabadaya parlour,n zuciyar Na wani irin dokawa da sauri .

 har lokacin  deeni Na nan kwance kan kujerar Three tsar bai dauke idanunshi akanta ba" yana  cigaba da kallonta  tare da  amsa waya da,aka yi masa yanzu   ,Daga yadda taji yana narkewa da zuba shagwaba a wayar  tasan shida   mahaifiyarsa ne .

  eyes into eyes suke kallon juna ita dashi take ya yatsuna fuska tuno iskanci datayi masa daren jiya  .
ya watsa mata ,wata uwar harara may frigita zuciyar duk  wanda akayiwa shi.
, itama bata  tsaya wata wata ba ta rama tare da dauke  idanunta akanshi ta cigaba da tafiyarta . Tsuru yayi mata da ido yana kallon bayanta da west dinta , mamakin karfin hali irin nata ne yacika zuciyarsa.
 shi tunda yake a rayuwarsa  bai taba  samun maccen da take sainsa dashi ba.
 ,Kai har   'cikin maza ma bai taba samu ba  .

 kitchen ta nufa bata ko sake waiwayar Inda yake ba ,duk da tagabanshi ta wuce .
 breakfast ta hada masa ,may sauki Dan itama yau a kasalance ta tashi .. soyyayen ship's  da kwai tasoma yi , sai jallof din supegeting datasha kayan hadi .
 taji nama da dry Fishe.
 take koina ya dauki kamshin girkinta .
 , sai ruwan shayi data dafa masa  wanda yasha kayan kamshi .
  "agurguje ta kammala da komai ta zubawa laraba nata ta, aje.
 tajera komai a dining km  duk aikin   nan da tayi a tsorace tayi shi.
 domin wa tunaninta zai isketa har kitchen din ne yaci kaniyarta kan abinda tayi masa daren jiya. Amman sai taga sabanin hk.
 ya shareta yacigaba da abinda yake a ranta tace banza  Dan iska kawai  da alamun naci bulus ..

 har lokacin datagama shirya dining  waya yakeyi da ummi Daga karshe taji ya ambaci sunan zeenat.....'cikin sanyi muryarsa
 hkn yasa ta gane zeenat din ce ta karbi wayar .

 cikin natsuwa tazo  zata sake wucewa ta gabanshi  ,cike da haiba  take daga Zara zaran yatsun kafafunta har tazo daidai inda yake kwance.
 kadan ya rage ta gifta shi .
taji ya fixgota da karfi tsiya .
 Atsorace
Tayi luuuuuuuu sai saman fadadden kirjinsa afirgice ta dago tana dubansa da shanyayun idanunta.
 gabanta Na wani iri faduwa .
 yunkurin mikewa tasomayi  domin raba jikinta danashi tare da tunanin kalar rashin mutunci da zata  zabga masa .
taji ya  damki west dinta da hannuwanshi daya  yana  maidata saman kirjinsa .
 bbu yadda ta iya da rayuwarta.
 Haka takoma ta kwanta lamo ajikinsa tana shakar daddaden kashin turaren  jikinsa may matukar sanyi da sanyaya rai .
  Yayinda faduwar gabanta  ya tsananta ganin yadda deeni yakamkameta ajikinshi .
abinda bata taba tunanin zai sake shiga tsakaninsu ba kennan wato sake hada jikinta danashi .
shiyasa gabadaya ta rikece ta birkice tasoma 
  mutsu mutsun yunkurawa Amman takasa dan bakaramin runguma yayi mata ba.
 Yayinda  hannushi daya ke rike da waya yana  yacigaba da hirarsa da matarsa "
 yana lumlumshe  idanunshi . 
 Kusan minti Goma ya dauka yana hira da zeenat  kafin Daga baya yayi hanging din phone din ya ajiye wayar a gefensa tare da kai Bakinsa daidai  tsaitin wuyanta yana shinshinawa hade da goggoga mata gashin dake kwance a fuskarsa  kana ya dire bakinsa  'cikin kunneta yana hura mata iska .
 wani irin shock taji ajikinta...wanda bata taba jin irinsa ba .
tsirga jikinta gabadaya suka Mike tsaye ta dinga jin wani iri wani iri yayinda  bugun zuciyarta ya sake  karuwa .
 Muryarsa can kasa kasa  tamkar ta mekoyon mgn  yace kin wani lafewa mutane ajiki kina jin dadi .
 ayi mgn kice ke ba Yar iska bace alhalin kin iya isakanci kala kala .

 ,Duk da yanayin rashin kuzarin da take ciki hakan bai hanata sanyawa jikinta jarumta ba.
  muryata a dake  cike da tsiwa  tace ai bani Na kawo kaina ba .
kaine kajawoni  da kanka sannan  km gashi ka hanani tashi.
 , Allah ko ?
Tace uhmmmm yanzu ma ka sakar min jiki kagani idan zan kara  daidai da  second 1 ajikinka.
 yaciji  gefen kunneta da karfi ta saki kara da muryarta  mara sauti kana  ta sake mannewa ajikinsa sosai .

  a shagwabe tace wannan km wani irin sabon  salon  iskanci ne da cin zali? 

A Dan fusace Yace Na sake jin kalmar iskancin nan abakinki wlh zan gwada miki yadda ake yinsa ganin idanunki   tunda 
Ke komai isakanci ne a gurinki bakida tunanin bambance iskanci da bauta ba .

 Wlh Ni ba baiwa bace kada ma ka km kusantani da kalmar  baiwa, takarasa fadar hk muryata tamkar may shirin zubda kwalla Dan jin zafin kalmar .
,taji zafin kiranta da baiwa da Yayi kwarai fiyye da Kiran da matarsa ke mata  .


Sai daya numfasa tare da sauke naunauyen ajiye zuciya  kana yace Bari nasanar  miki da abinda baki sani ba .
ke tamkar baiwa ce gareni nida matata km kada ki taba tunanin zaki tsira daga tarkona Amman nasan  bazaki gane hkn ba sai nan gaba .. 
ya fadi hk yana sake rungumeta tsam tsam  ajikinshi .

kalamansa sun maseefar  huda mata zuciya tare da   ratsa kowane shashi Na gangar jikinta suka ratsa tsakiyar kirjinta kana sukayi mazauni a tsokar dake ajiye akirjinta suka zauna daram a inda bazata manta ba.

 ahankali ta dinga  maimaita kalmar baiwa... baiwa  ce ke agareni nida matata .
to me hakan  yake nufi?
 ta tmbyi zuciyata tun kafin Brain dinta yagama  seculating " kawai taji wani  murmushi takaici may gyaraye da hawaye masu dumi sun zo mata  take hawaye masu zafi da ciwo suka  shiga bin kuncinta.
 muryata cike da in inna..
 jikinta har rawa rawa yake gurin cewa wlh wlh Ni ba baiwarku bace.
 ba km  zan taba kasancewa baiwa a gareka ba ballanantana  wata matarka can .
 kasani Nima  diya ce may yanci tamkar kai ba  baiwa ba .

Sannan ba sai ma nacigaba da zama daku ba tukun har zankasance baiwa a tare da Ku .....

" deeni Yayi Murmushin mugunta yana cizan  gefen bakinsa  har dimple dinsa ya lotsa ....wanda hakan ke karawa kyakywar fuskarsa wani  kyau Na musamman.
Ta kawar  da fuskarta gefe  Dan bata son kallonsa da duk wani abu may kyau dake tare dashi.
Gane hakan da Yayi ne  Yasa hannunsa ya  juyo da fuskarta suna fuskantar juna sosai .
 " duk kigama tashen balagarki ni nan zanyi daidai dake sannan zanyi  maganin tsiwarki  .

 ta bude bakinta kennan da niyar    bashi amsa mgnrsa .
 " taji lips dinsa ya sauka  cikin bakinta bai tsaya bata lokaci ba ya cafko laulausar tongue dinta ya  hau  tsotsa 'cikin mutuwar jiki. dole tasa tayi  mukus ajikinsa badan taso yin hkn ba. Dan tsabar  takaici salon wulakancinsa   runtse shanyayun idanunta tayi 
 tana jin yadda zuciyarta ke sake  dokawa da tafarfasa tamkar  zata  tarwatse a kan iskancin  da deeni yake mata.
 wasu tunanin daban daban ne   ke zuwa mata a game da wannan salon iskancin  daya dauko mata .
ba komai yake nufi daita ba facce so yake yaketa mata haddinta yakaita ya baro  .
Ya dade rungume daita ajikinshi yana aikin shan bakinta da harshenta ..da kyar tasamu ya sakar mata lips dinta cikin sarkewar murya tace Dan girman Allah kayi hakuri ka sakar min jikina nifa ba matarka bace to meyyesa kake son taba min  jikina?

 lumshe rikitattun idanunshi yayi tare da kamo tafin hannuta cikin nashi ya tsarkesu guri daya sannan  ya Kai kan hancinsa yana shakar kamshin tafin hannunta mai taushi tamkar ba diyar talaka ba .
ta kula da yadda jikinsa ya sauya ta hanyar jin joystick dinsa na harbawa 'cikin jikinta ahankali Tasoma yunkurin  sake  Mikewa da iyakacin karfinta  ya kara matseta tsam  a jikinsa..
 cikin muryarta mara sauti tace wayyo Allahnah ..wayyo marata bayana kirjina  ciwo suke min nagaji wlh kasakar min jiki bayana  yagaji .....


Har kasan zuciyarsa ya dinga jin  tausayinta nashigar shi, yana ratsa kowane lungun da sako na gangar jikinsa.
 ya dinga jin wani iri  akasan ruhinsa .
 tausayin  ne  ?
Ko  km sha,awarta yake Yasashi yaji wannan yanayin akanta.
 har yaji  bazai iya cigaba da abinda yake mata  ba.
  shi dai bai sani ba  Amman yasan zuwa yanzu ya daina jin haushinta  da tsanarta cikin zuciyarsa .

ita kuwa kara tsorata tayi sosai da yanayinsa  tarasa yadda za'tayi dashi  so take yabarta ta Mike ko tasamu  sausauci .
hk kawai   ta tsinci bakinta Na furta  masa ka sakeni dan girma Allah nagaji dayawa ... km  yunwa nake ji.

Jin hk Yasa ya sausauta rungumar da Yayi mata sosai  , ahankali yashiga mikewa  tare daita ajikinshi .
ya daurata akan cinyarsa ya tsura mata ido yana  kallonta  da tausayinta tamkar zai yi kuka.

 itama  shanyayun idanunta ta dan  zuba masa kawai tana kallon kwaryar idanunshi masu 'cike da haiba da suka dan sauya kala fari zuwa green green.. wasu abubuwa ta dinga ganin  suna fitowa Daga cikin kwayar idanunshi suna shiga cikin  nata wanda Haka Yasa ta dinga  jin jikinta tamkar ana mata wanka da ruwan iceblack  .

Ahankali ta runtse idanunta domin bata son jin wani abu agame dashi.
Shima hakan ce takasance dashi kusan ma har ya fita shiga  rudanin da tashin hankali  jin shrn yayi yawa Yasa ta bude idanunta fesss cikin nasa kallonta yake har lokacin   'cike da karfin hali  ya  waske ta hanyar cewa kin fanshi kanki ta hanyar bani hakuri da hadani da mahalicina bancin hk da kin gane kuranki yau . Can runtse rikitattun idanunshi uhmmmm yauwa nayi saurin yi miki afuwa ubanwa kika zaga jiya? ya karasa fadar hk yana bude idanushi. gabadaya jikinta ya dauki rawa jin abinda yace tayi shr taki cewa komai sai hawaye ne kawai ke bin kuncinta yana jin yadda jikinta ke shake amman yayi tamkar Bai ji ba tmbyr ki fa nake kina jin mutane dan iskanci bakin Na rawa muryarta 'cike da in ..inna tace ba da kai nake ba fa...idan bada  Ni kike ba .
Da ubanwa kike kukanta ya Karu sosai ni kabarni nayi tafiyata ba da kai nake ba .
Ok kinji tsoro kennan ? Allah sarki nabla bata San sanda ta daga masa kanta da sauri  ba alamun eh.
Yace better a she ma ke karamar rasa kunya ce tayi tsit takasa cewa komai dan gabadaya a atsorace take dashi . Yacigaba
 duk da nasan  dani kike nabarki  tunda kinji shr.
 kin tsira daga gareni if nut da kinga kudi kince kashi ne .
 
Common get up on lap's stupid kawai  kin wani zauneni dare dare da wayan nan bombom din naki masu kama da ... zumbur ta Mike tsaye tun  Bai Kai  karshen zance yayinda 
  hawaye fuskarta ke cigaba da silalowa. gabadaya Hawayen daya gani suna fitowa  daga idanunta ne ya nemi  hargitsa masa lissafi.

 ita kuwa tana jin yadda yayi shr yaki karasa mgnrsa Yasa  ta  juyawarta  da sauri tana kunkuni  cikin ranta tasoma tafiyarta.

 cikin sanyi jiki ya gyara zamansa yana  bin bayanta da kallo  .
 ganin ba hanyar   kitchen ta nufa  ba.
 Yasa shi cewa ke ba yunwa kika ce kina ki ba ?
Ta dan juyo kadan tana watsamasa wata katuwar  harara tare da turo bakinta gaba  muryarta 'cike da shagwaba tace an fasa  cin abinci . Ya zaro ido 
Yana nuna kirjinshi da yatsansa alamun dashi take .
Taja tsaki kana ta daga masa kanta.
 ya soma kokarin tashi  ..Ai tun kafin yakai Ga mikewa   ta kwasa da mugun  gudu tayi hanyar  step atsorace yake kallonta tamkar yabita .Amman ya fasa  ko meya tuna oh masa ya  shareta  ya nufi dining area yana sauke numfashi ahankali ahankali yana jin wata natsuwa ta musamman dake bin gangar  jikinsa wanda kusan duk sanda zai kadaita daita .
Haka  zai dinga  jin kanshi deeni on top.

 
  dakinta ta nufa da sauri  tare  da yiwa kofar key tana  sauke numfashi sama sama tana  tsinne  masa a cikin ranta .


Yau ma kmr nablah byn ta fito daga bathroom rigar bacci ce kawai   sanye ajikinta iya cinyoyinta wacce ta bayyana nonuwanta da asalin  surar jikinta .
ta tufke sumar kanta da rebon ta feshe sansar jikinta da turaruka kala kala masu   sanyi kamshi wanda duk 'cikin kyautar safeena ce dataje shopping ta tsiyo mata wani irin  sihirtaccen kamshi ne yake fita Daga jikinta wanda duk wani cikakken namiji  idan ya Shaka dole bukatar diya mace ta tsirga masa .



'Cikin sanyi jiki deeni byn yagama duk wani abu daya zama Na al'adarsa kafin bacci ya nufi dakinta  wanda tun lokacin data fito daga bathroom take shirinta  yake zaune zaman  jiranta. 
ahankali yakarasa inda take kwance ya tsurawa  surar jikinta idanunsa  kawai yana kallonta..  'cikin mutuwar jiki yakarasa ya zauna inda take kwance tana baccinta 'cikin kwanciyar hankali   Yasa hannu ya shafo hip's dinta yana hadeyar miyon daya tsaya masa a makoshinsa .
  tsabar farinciki ganin irin shigar data yi masa yau bai San sanda ya zauna ya janyota jikinsa sosai ya  rungumeta tsam tsam  tare da hade bakinsu guri daya itama akaci sa'a ta bude bakinta 'cikin magagin bacci aiko ya  cafko laulausar harshenta.

Wani irin tsutsa yakewa   harshenta da lips dinta  . itama cikin bacci tasa tafin hannuta duka ta kamo gefe da gefen fuskarshi ta  cafko nashi harshen Tana tsutsa tare da  kamkame shi ,so take ta bude  idanunta Amman takasa sbd baccin dake cikinsu.
 loma tayi takasa cigaba da abinda take .
 ya Dan dakata   da romancing din da  yake mata  yana kallonta .
ganin ta maid hannuta jikinshi    tana cigaba da tsotsar lip's dinshi Yasa  ya sake  matse gam a daddaden kirjinsa yana cigaba da sarrafa jikinta. bakinshi manne da nata .
ya kwantar daita yana yasoma rabata da rigar baccin dake  jikinta har  ya zareta rigar gabadaya  ta saura Daga ita sai pent Shima ya zare ya Kai lips dinsa kan nipply dinta yana dan zagaye kan nipply dinta da harshensa ya Kai hannushi kasan mararta yana shafa gurin ahankali ahankali Daga karshe ya ware kafafunta ya zira fingers dinsa daya  cikin kasanta yasoma mata fingering taja wani irin numfashi ta sauke da karfi ta kamkame jikinta tana nishi da kyar.
 duk abinda take yana kallonta.
 idanunshi ya tsura mata yana cigaba da fingering dinta idan Yayi sai ya Dan tsaya sai yaga ta soma lalubar inda   hannushi yake  ta daura a kasanta shi km ganin hk Yasa tuni jikinsa ya fara rawa  yayita fingering dinta ahankali ya sauke bakinsa kasanta ya zira  harshensa ciki sosai  yashiga soucking dinta ita km tsabar dadin da take jin yanabin duk wata kafa ta jikinta Yasa ta dinga turo masa kasanta tana shafa sumar kanshi sosai ya dinga soucking dinta yayinda duka hannushi ke kan dukiyar fulaninta yana aikin murza kan nipply dinta ,gabadaya ya rude ya susuce yafita haiyacinsa  tare da  ruda mata tsansar jiki .
bbu abinda yake sai aikin  soucking dinta  yayinda ita km ke sake ware masa kafafunta sosai  ahankali yake ruda mata jiki da salonsa Na fidda mutun 'cikin hankalinsa . lokaci guda ya zare harshensa daga kasanta ya maida kan brest dinta yana tsotsa yana lasar jikinta gabadaya kamamaninsa sun gama sauyawa   Brain dinsa yasoma birkicewa Yasa hannusa  ya dinga murzata da kan nipply dinta.
 ita km cikin wani irin yanayi shi baiyi kama da me yin bacci ba .
hk kazalika  bai yi kama da wanda  idanunshi ke bude   ba.
 ta dinga turo masa kirjinta tana matso shi sosai .
 ai take brain dinsa  ya sake  birkicewa Shima daman abinda yafi so kennan cikin zalama ya dinga tsotsar kan nipply dinta yana lasar gefen nipply din tare da ciciza kan nipply din da hakorinsa sai nishi nabla take tana shiiiiii ... shiiiii da bakinta tamkar may cin yaji yagabadaya jikinta ya gama sakewa kansata ya jike jagwab  sai tsiyaya take ta kagu bai shigeta ba.
 sai aikin manne masa take tana turo masa kirjinta ganin yaki shigarta har lokacin sai aikin romancing dinta yake Yasa tasa   duka hannuta  ta matseshi  tsam ... ajikinta tana sakin numfashi da karfin gaske ,tare da sake turo masa dukiyar fulaninta  aiko gabadaya ta ruda shi takai shi wani  limit Na bukatuwa.
wani irin rawa jikinshi keyi zuwa lokacin Shima a matse yake dayajishi cikin jikinta.
 " ahankali km cikin mutuwar jiki ya sake  matsota sosai  suna fuskantar juna daita yayi kissing din eyes dinta ya tsotsi lip dinta yana ware kafafunta  ita km tasa hannuta cikin sumar kanshi tana cakudawa tare da dago kirjinta tana goga masa kan nipply dinta a kirjinshi .
ai bai San sanda wani shauki ya tsigar masa  tun Daga tafin kafafunshi  har zuwa kan joystick  'cikin zafin  nama ya cire short niker din dake jikinsa wanda daman dashi kadai yashigo dakin .
  wani irin karfi ne yazo masa kana  ya tsaita joystick dinsa cikin kasanta Amman taki wucewa Kai tsaye  duk da  tsiyayar  da kasanta keyi ,sai daya sake yunkurawa  da karfi kana ta shige sosai.
 , yasoma aiki bai ji bai gani ita km tana bashi hadin Kai yadda yakamata.

 wani sweet  yaji takara yi masa fiyye da kowani lokaci da yake having sex daita  Dan hk  Yasa hannuwanshi duka ya tallabo bombom dinta sama da kyau  ya dinga  zira mata  jijiyarsa ... ta Dan saki kara  mara sauti kana ta kamkame shi gam ajikinta..Tana sakin numfashi , yayinda shi km sai aikin nukurkusanta yake yana tsotsar kunneta.
 take tsigar jikinta gabadaya suka Mike tsaye yrrrrrrrrrrrrr ....duk ta inda tayi bbu sauki gurin manage deeni Dan aiki kawai yake babu sausauci  yana fidda numfashin dadi yana jin lokacin da karfinta yakaru sosai ta sake  kamkame  shi ,Shima  kamkame yayi ajikinshi tsam  yana aikin sarrafata tare da hade  bakinsu guri daya ..a tare sukayi release jikinta yas sake gabadaya ya mutu murus tare da Lafewa  kan bed tasoma kokari raba jikinta danashi Amman yaki yarda..
 ya manne mata gam  tamkar cungum  yana cigaba da aiki ganin yaki sakamarta jiki Yasa ta kamo fuskarshi duka da hannuta  tana son cire bakinta 'cikin nashi sbd wani irin tsotsar dayake yiwa bakin nata.
 'cikin wani irin sauti yace uhmmmm wayyyyyo don't do this to me please ..sannan ya sake kamkameta ajinkish  yana cigaba da sarrafa harshensa cikin nata cikin wani irin shaukin dadi ya dinga sex daita yana taba duk inda hannushi yaci karo dashi ajikinta take wani sabon felling ya sake zuwa mata tacigaba da bashi hadin Kai .
tafin hannusu ya hade guri daya yana yamutsawa da murzawa  ahankali ahankali yana sake  hakarta da kyau ta yadda zatayi enjoy ..

 wani irin dadi nabla keji wanda bata taba jin irinsa ba a iya tsawon rayuwarta km bata kaunar  abinda zai raba jin dadinta ko shiga tsakaninta da wannan dadin  .
 ita da kanta take sake bawa deeni hadin Kai da goyon baya wanda shi km daman abinda yake so kennan Dan hk bashi yabarta ba sai dayayi sex daita sau   shida masu rai da lfy sannan ya sarara mata ya zare joystick dinsa Daga jikinta yana sauke numfashi tare da kokari rabata da gangar jikinshi yaji ta rungume gam Dan hk  ya sake kwantowa jikinta sosai   ya rungumeta yana fidda numfashin.
 shr tayi tana matse jikinta , ahankali ya lumshe rikitattun idanunshi tare da birkitota ta dawo samanshi ta kwanta lamo saman fadadden kirjinsa tana fidda numfashin sama sama .


 ahankali 'cikin wani irin yanayi yashiga  gyara mata gashin kanta daya soma bajewa .
Dan kadan ya rage rebon din data tufke gashin  bai Ida fita ba .
Yasa hannushi ya zare rebon  din gabadaya sumar kanta suka  baje suka  rufe mata fuskarta Yasa hannushi ahankali  yana  tattarawa .
ya mai dasu bayanta yana shafa sumar  ahankali tare da tsurawa beauty face dinta  ido yana kallon yadda idanunta ke lumshe tana  mutsu mutsu ajikinsa .
yayinda joystick dinsa ke sake Mikewa ita kanta  tana jin motsinta har 'cikin jikinta hannushi dake kan sumar kanta ya maida kan pointers noise dinta yana ja ahankali a ranshi yake yabawa da tsabar kyawu halitar da Allah yayiwa  jikinta.
 duk da kasancewarta black beauty Amman wani iri sihirtaccen kyawu gareta uwa uba kasanta dayake jinsa zamzam  tamkar sugar ...ya lumshe rikitattun idanunshi tunawa da Yayi da yadda ta dinga kuka randa yace zaiyi iskanci daita ..
 ya danyi murmushi gefen baki tare da furzar da huci may dumi. ahankali ya bude bakinsa ya furta nabla kennan ....wanda wannan lokacin shine  karo Na farkon daya furta kalmar sunanta .
kina gudun nayi  iskanci dake a bayyane .
 km Ina yi datake a boye  batare da saninki ba .

 da badan sirrin dake tsakaninmu dake ba dana yi sex dake  a bayyane ta yadda  zaki fi haukacewa akaina..
 rashin sonki kawai zai hanani aikata  hkn  da km gudun abinda zai faru  a tsakaninmu .

bancin hk da kinji yadda  sauran mata ke ji a duniyar ma,aurata  ....ya karasa mgnr zuci yana Kai bakinsa kan lips dinta yanacigaba da tsotsa ahankali yana lumlumshe rikitattun idanunshi .
itama sake mannewa tayi ajikinshi Tana tsotsar nashi lips din  'cikin Haka yaga numfashinta ya soma sauyawa yana  sauka ahankali ahankali Alamun takoma baccinta..
  Dan hk ya maidata gefe ya kwantar daita ya janyo  blanket may taushi ya lullubeta dashi kana  ya Mike sannu cikin tsanyin jikin  nan nasa ya ziro duka kafafunshi kasa ya Mike tsaye ya juya da niyar daukar short niker dinsa  yaji hannuta cikin nashi ta rike gam tana murzawa ahankali ... ya juyo da sauri gabansa Na  wani irin dokawa  idanunsu suka sarke cikin juna take zuciyarsa ta tsinke tashiga bugawa jikinsa ya dauki kirrrrrrma.. tsuru yayi tare da tsura mata rikitattun idanunshi yana dubanta a tsorace.......




MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO



Page 82 


Itama kallonshi take da shanyayun idanunta da suka gama canza kala .'cikin wani irin yanayi   ta maida idanunta ta lumshesu. Ruf  tana may fizgoshi zuwa  jikinta ta rungume tsammmm tamkar za'a kwace mata  shi.
   ,cikin mayen bacci tace where are you going to?
... please kada ka tafi  kabarni cikin wannan halin , ka zauna tare dani har abada.
 " yayi shr kawai yana dubanta batare da   ce daita komai ba, sai ma  tsurawa dan karamin bakinta ido da yayi.
 " gabadaya a dan frigice yake da ganin  yanayinta.
 " kayi shr can't  you talk to me  ?

 ko baka mgn ne ?

Ya girgirza mata kansa kawai  tamkar wani kadangare ko irin tana kallonshi din nan.
,cikin wani irin sanyi jiki da tsabar Sha,awarsa tashige cikin  jikinsa sosai  tana goga masa nipply dinta a kirjinshi.
  "muryarta can kasa kasa ta sake bude bakinta ahankali please talk to me now ...
tana girgirza kirjinsa da hannuwanta  .
 kullun kana zuwa min  cikin baccina, kayi having sex dani ka wuce kabarni cikin tarin damuwa.
 yau kawai ka kasance tare dani to spend the only night wit me please .


,deeni nagama jin abinda tace yasan bata 'cikin sense dinta  giyar bacci ne kawai ke yawo daita.
  Dan hk ya rukunkumeta sosai ajikinsa shima .
 yana sakin numfashi tare da kai Bakinsa tsaitin wuyanta ya sumbata .
  Sannan da kyar ya iya bude bakinsa ,what should I do for you now?
 ,ta sake mannewa ajikinsa sosai tana sake goga masa nipply dinta stay with me  till  the only night that's what I won't from you, idan km bazaka kasance tare dani ba ka fada min sunanka kawai  ......

meyasa kike son sanin sunana ?
Ta dan bude shanyayun idanunta da suke a rikice tsabar shauki hade da mayen bacci ta zuba masa tana dubansa dasu kana ta maidasu ta lumshe.
 sbd Ina sonka..

 bana son  abinda zai nisantani da kai ,wanda hakan zai iya sanadiyar yanke min jin dadi dake gudana a tsakaninmu.
 ,ya sauke naunauyen ajiyar zuciya  bai San  sanda murmushi ya kufce masa ba , ya matseta tsam tsam ajikinshi yasamu kanshi da jin dadin abinda tace.


 " oh  nablah  why did you fall in love with me .... please kada zuciyarki takamu da soyayyata course am not ready for ....sai km yayi shr yakasa karasa mgnr shi. ya zarce da kaiwa jikinta gabadaya kiss yana sake ruda mata jiki da salonsa..
 " wayyohhhyyy  stop  doing this to me please kace min kaima kana sona that's the only thing I won't from you.
Murmushi ya sake yi yana may sake  kamkameta a kirjinshi. Ok let's be friends nab.lah.. yana fadar Haka ya cigaba da ruda mata sansar jiki da sarrafa harshensa ajikinta ta hanyar lasar duk inda harshensa yaci karo dashi.
 Tasoma kokarin rabashi da jikinta tana may juya masa baya ala,mun tayi fushi dashi .
Ahankali 'cikin mutuwar jiki yabi bayan nata da kallo ya dinga ji aranshi  tamkar yabarta ya kama gabansa  kawai .
 amman km sai yaji bazai iya aikata hkn ba .
 sai ma ji da Yayi zuciyarsa Na wani iri dokawa da sauri .
Dan  ganin abinda tayi jikinsa a sanyaye ya kai hannushi jikinta yana lalubarta da son juyo daita gareshi. amman taki juyowa sai ma janyo pillow  dake gefenta tayi ta rungume tsam  ajikinta tana fizgar numfashi da kyar tana fesarwa .


 gabanta yakomo ya janye pillow  da karfi ya maye gurbin pillow yana kokarin hadeta da jikinshi taki yarda   uhmmmm ni kabarni tunda you don't have  interest on me . please live me alone km as for today  karka sake zuwa inda nake.
 ,Ta sake  runtse shanyayun idanunta  gam  tana may  kawar da fuskarta  gefe yayinda zuciyarta tashiga kai kawo wajen sarrafa kanta, Daga baya ta dawo tana  bugawa da sauri da sauri.
 wanda  Yasa azahirance  deeni  ke   hango yadda kirjinta keyin sama da kasa tsabar tashiga damuwa .
   rikota yayi sosai ajikinshi,   suka shiga kokuwa dashi, wlh baki isa hanani zuwa inda kike ba  kina matsayin matata ta sunna , dole zan zo miki, a duk sanda nake so km  na gadama. sosai suke kokuwa daita.
 ita tana kokarin  yabarta ya daina ruda mata jiki da salonsa tun da bayada ra,ayinta.
 shi km yana kokarin ganin yayi winning din zuciyarta ta yadda zai mallaketa gabadaya.
 cikin sauki  "ya dinga rarrashita , sai yaga tamkar ba shi  bane  mutumin dayake aikata hakan a gabanta .
   daga karshe yasamu nasarar sake dulmiyar daita, cikin duniyar ma'aurata.
 dan wasu zafafan romancing  ya dinga aikawa jikinta   wanda hkn Yasa wani sabon   feeling yabijirowa  jikinsu.
 kai tsaye  hanyarsa ya sake daukewa  cikin wani irin  shauki da kwarewa wajen sarrafa mace yasoma having sex daita.

 manta komai dake 'cikin duniya ,  nablah tayi ta rukunkume shi gam  ajikinta tana dago masa kasanta da nonuwanta sosai , tare da karban dukkanin wani  sakwanninsa masu matukar haukata zuciyar mutun, da mantar da ruhin mutun cikin duniyar dayake.
 bbu abinda deeni yake sai  sambatu yake zubawa ,tun lokacin da yasoma making lov daita yasoma jefo mata kalamansa zafafa masu kashe jiki please nabla karki barni wayyohhhyyy wlh zan shiga tashin hankali ,duk sanda kika barni.
 ,kin taka rawar Gani acikin duniyata bazan so rabuwa dake ba .


you real fit my nature .
you are my type please don't live me ... am  happy  whenever am having sex with you, sosai deeni ya haukace mata, yana faman zuba mata sambatu iri iri har da  Na fitar da mutun cikin hankalinsa. gabadaya deeni yagama kashe duk wata gaba dake jikin nabla.
 tana jin mgnrsa suna sauka akunneta da ruhinta yana bin   duk wani lungu da sako na gangar jikinta.
Ahankali  deeni ke  sake bi daita yana  hakarta cikin salonsa, wanda yake sake rikita ZUCIYAR  nablah domin zautar daita  .
bakinshi yaka cikin kunneta ya zira harshensa ciki yana mata wani irin soucking .
wani sweetness nablah ta dinga ji yana mata yawo ajikin tunda Daga tafin kafafuwanta har zuwa  cikin tafin hannunta ,ta dinga jin  tamkar ana caccaka mata allura ne  ciki tafin hannunta tsabar dadi datake ji.
A rude ta lalubo tafin  hannushi cikin Nata ta sarkesu guri daya  tana murzawa ahankali ahankali, cikin mayyen muryata irin ta wanda yagama fita haiyacinsa tace  ,to meyasa baka sona byn kana jin dadina.....takarasa fadar hkn tana sakin kara da muryarta mara sauti sakamakon hakarta dataji yayi da karfi ta ja numfashi da kyar ta sauke sannan tacigaba da mgn a shagwabe . koma dai menene   Ni dai Ina sonka........
 shiiiiii shiiiii !!! nab..lah , bazaki gane bane ,idan na soki akwai matsala ,amman kada ki damu zuwa yanzu Ni kaina  nasan  kina da  gurbi da matsayi acikin zuciyata  Na musamman...
  to gaya min sunanka please ta katseshi ta hanyar ce masa hk ....
 
sosai deeni yake bin duk wata hanyar, daya San  zai gamsar daita da kanshi" hankalisa gabadaya ya gushe.
 kwadayinta ne kawai ke cin ranshi .
 wani irin shaukinta    yake ji, yana ratsa masa ilahirin gabobinsa  yayinda ita km sai naci   take  mishi  ya fada mata sunanshi.
 please now tell me ur ,name so that  I will keep  it in my memory.

Takarasa fadar hkn tare da  ,sa tafin  hannuta duka ta kamo fuskarshi dashi  tana kallon cikin kwayar idanushi .
,Shima kallonta yake yana cigaba da sex daita  ahankali yake binta 'cike da natsuwa domin samun bukatarsa ta biya  .
 Bakinshi ya maida cikin kunneta 
da kyar ,ya iya bude bakinsa ya fizgo mgn 'cikin in inna  .
am..am.. N . ALIYU By name yana gama fadar hk ya zarce da soucking din cikin kunneta tsigar jikinta suka Mike tsaye  gabadaya.. ta kamkameshi  ajikinta tana fidda  nishin dadi sama sama tare  ,da murna jin sunanshi .

 duk yadda    deeni ke son mace jaruma wacce zata iya daukar bukatar shi , nablah ta zarta tunaninsa ,domin tsab take daukesa da lalurarsa tare bashi hadin Kai da goyon baya.
  ,shi kanshi yana jin da yasan zai sameta hk da bai yarda yayi auren sirri daita ba .....


 baka jin motsin komai a dakin sai nishinsu dake fita ahankali ahankali, gabadaya sun gama  fita cikin haiyacinsu.
  juyata kawai yake yadda ranshi keso .
Sosai  suka dinga  gamsar da zuciyoyinsu sai dayaji  Kiran sallar farko daga masallaci dake'cikin gidan, sannan ya sarara mata ya zare jikinshi daga nata .
 ko motsin kirki batayi tsabar gajiya daya lura tana tattare daita .
 ,ya goge mata Spam din dake zube a kasanta   sosai ta yadda bazata taba  gane anyi komai daita ba.

 kana ya sumbaci goshinta da hancinta zuwa lips dinta .
ya maida boxes dinsa jikinshi ya nufi dakinsa .. kai tsaye bathroom dinsa ya nufa zuciyarsa wasai dankare farinciki  tamkar wanda akayiwa albishir da gidan aljanna, wanka yayi 'cike da Nishadi da farincikin nablah ta furta masa kalmar  ,tana sonshi .



 Bangaren nablah kuwa Bacci  mai nauyi  take  dan koda gari ya waye kasa tashi tayi da wuri.
Dan gabadaya ilahirin jikinta ciwo yake mata ,most especial ciyoyinta da suka rike mata .
 da kyar ta iya  Mikewa zaune tana kallon  celling dakin hade da yin  salati  tana son tuno mafarkin datayi jiya.
 ahankali ta dinga hada pics din  abubuwan da suka  faru a tsakaninta da mutumin daya Kira kanshi da  N. ALIYU  Wanda bata San kowa waye ba ,mutun ne  ko aljan ,amman a zuciyarta tafi bawa mafarkin nata mazauni da aljanine yayi nasarar  aureta  ,duk da addu'ar datakeyi kullun kafin tayi bacci .
  ,km yake yawon saduwa daita 'cikin baccinta.
a bin bai wani tsaya mata a rai ba 

sai ma addu'ar ta dinga yi cikin zuciyarta Na neman tsari Daga sharrin su da kaidinsu , tunda tasan kusan  hakan Na yawon faruwa Ga al,umma da dama  .

tayi shr kawai  tana son tuno face dinsa da yanayinsa ,duk iya tunani tayi akan son gano kamanin fuskarsa   amman abin yagaya. domin kasa tuna komai tayi har ma taji kanta yasoma Sara mata alamun  ciwo hkn ya sake tabbatar mata da tabbas aljanine yashigo 'cikin rayuwarta .
 dan Haka kawai ta Mike tsaye da kyar ta nufi bathroom, abu biyu kawai tasan ta rike a memory dinta  game dashi sunan shi da km yadda ya dinga having sex daita.
 jikinta a sanyaye ta shige bayi tana mamakin mafarkinta .

Wanka tsarki tayi tare da dauro alwala gabadaya tazo ta gabatar da sallah. 
Tana idarwa taje gaban mirrow as usual tana kallon kanta wani kyau takara Na ban mamaki bbu Wanda zai ganta ya yarda Daga inda ta fito komai Na jikinta ya cicciko tayi wani irin fresh daita .
Ta juya da sauri ta nufi kitchen sakamakon tuno may gidan datayi .
 cikin sauri tasoma hada masa breakfast sbd  lating datayi .
Shap shap ta hada masa abin kari taje tashirya dinning.
 " sannan Tasoma da gyaran gidan Daga karshe tashiga dakinsa dan gyarawa .

zaune ta tadda shi a bakin gado kunnenshi manne da   waya yana magana 'cikin tsanr farinciki sam bazakace shine  mutumin nan  may shegen girman kai tsiya bane  da nuna isa da izza   ,mutumin da ganin murmushi ma aiki ne indai batare  da umminsa zaka ganshi ba.
  km  da alama shida umminsa ne ke mgn a wayar  ,kallo daya tayi masa batare da  bi takansa ba  tasoma aikinta cikin tsanake .

Sun jima suna waya da ummi  Daga karshe taji yace gata nan    aiki take first love .
bangaren ummi kuwa dariya tayi tare da cewa deeni  kennan.. Ok  hadani daita tunda naxo banji lfyrta ba . 

Lfyrta kalau fa first love sai ma sabon tsakanci data tsiro dashi wanda Ni ba  dauka zanyi ba .
,naji nidai bani ita' ya Mikawa nablah wayar   suka gaisa da ummi .

Nablah nayi fushi dake tunda nayi tafiyar nan hankalina ke kanki amman ke ko damuwa dani bakiyi ba ko ?
'Cikin muryar shagwaba tace Allah ummi ba Haka bane, wlh kina raina km  Na damu dake sosai  asalima idan Na tunaki har kuka nake.
Wlh ummi  abun yayi min yawa  Ga kewar gida  .
  ,Ok ya gidan komai dai lfy ?

Lfy lau  Ni ummi zaman gidan ne kawai  ya dameni wlh koina shr bana jin dadi Komai . gashi aunty laraba  ba ma, ba wani zaman gidan take ba .

Ayya karki damu zan dinga kiranki akai akai da landline din parlour,n domin na dinga jin abubuwan dake faruwa.

 deeni yasanar min  daya turawa sister dinki kudin  salary dinki  har da kari ma akai ,ta dago ido tana dubansa , kawai taga ya kashe mata idon daya .Tayi saurin  Kai da fuskarta tana cigaba da sauraron ummi .
 dan hk kada kisa damuwa a ranki kema zaki iya Kiran Yan gidanku  da wayar kinji .

Muryarta can kasa kasa tace to ummi an gode da karamci Allah yabada Lada , uhm nablah kada ki damu Ina jinki har cikin jinina, km zan iya yi miki komai a rayuwa  muddin bai fi karfina ba .
,amman Ina son ki dan rage cin zakin nan dakike sbd lafiyarki ,
 nablah tayi tsai da ranta tana tunanin yadda ummi tasan tana shan zaki .
kina jina nablah  uhm Ina jinki ummi, inshallahu zan daina.
 Ok me kike so nakawo miki idan zan dawo.
Nablah  ,ta dan yi murmushi jin dadi sannan tace  duk abinda kika kawo min Ina so.

murmushi ummi tayi itama  to yayi zan taho miki da special tsarabarki ,to ummi Na gode Allah yakara girma sai kin dawo Allah dawo dake lfy ta tmbye safeena ummi tace sun fita tun safe da zeenat .

 ok ummi ki gaishe min daita har da aunty zeenat  ma  takarasa fadar hk tana may yin sallama da ummi ta Mika masa wayar .

Firt love sai wani biyewa wannan  yarinyar  kike yi yarinyar da bata jin mgn Ga rashin kunyar tsiya  .

 bbu ruwanka son da yarinyar nan indai abinda nasaka shi zaka min bawani complain ba .
Haba first lov farinciki zeenat kawai kike so bakya tunanin Ni halin da zanshiga ... Ni kaga sai anjima mayi mgn ta kashe wayarta .
Ita km nablah ko kallon inda yake  bata sake yi ba tacigaba da aikinta .

Ahankali 'cikin sanyi jikin nan nata Tagama gyara koina a dakin , yayi saura kan bed dinshi ne kawai ya saura wanda yaki tashi sai ma kwanciya  da yayi flat yana shafa mararsa yana kallonta .
yayinda ita km taki ko kallon inda yake ballanantana tace   masa ya tashi.
 Haushinta ya Dan ji a rashin  ganin taki yi masa mgn gashi shi km  hanya yake nema dan yasamu damar  ya latsata .

 ,ganin bashi da niyar tashi  ta gyara bed din yasa ta juya abinta 'cikin sanyi jiki zata bar mishi  dakinsa ...taji ya fixgota da karfin , ta dawo da baya da baya luuuuuuuu zata fade kasa  Allah Ya takaita.
 sai data bige gefen kugunta da abin gado ,sannan ta fada saman fadadden kirjinsa .
 aiko agigice  ta fashe da wani gigitaccen kuka may cin rai .
 tana kallon  kwayar idanunshi tamkar ta shake masa wuya Dan takaicin abinda Yayi mata .
atsorace ya Mike zaune tare daita ajikinshi ya rungumota  yana kokarin kai hannushi gurin ciwon  ta buge masa hannu wayyo cikina wayyo Allah sai murkususu gefen cikinta take tana kuka tana tsine masa .
 ,hakuri  kawai yake son bata amman yakasa bude bakinsa sai cire hannuta da yayi wanda ta dafe gurin ciwon dashi  ya maida nashi yana murza mata gurin ahankali .


Kusan minti Goma ta dauka  rungume ajikinshi tana kukan radadin ciwon data ji.
 ahankali Yasa hannushi ya dauko man zafi yana 
  faman shafa mata agurin .
ahankali ta dan soma  rage jin zugin da ciwon  nata kemata  .
tasoma kokarin  tutturesa da hannuta.
 ,dan Allah  mlm ka sakar min jiki duk kabi ka kaneniye min jiki  ko dole ne mugu kawai Allah Ya isa wlh . 
Matseta yayi sosai ajikinshi yana Shiri hade bakinsu guri daya ..karar sautin wayarshi ne ya dakatar dashi Daga aikata abinda yayi Niyya Wanda tun dazu ake kiranshi yaki dagawa sbd ganin Wanda ke Kiran nashi .
  Dan hk ya bige mata bakin tsiyawa ya sake   rungume ajikinshi .
Ta fashe da wani sabon kuka ,yayinda shi km Yasa hannunsa daya ya dauki wayar tare da mannata a kunnenshi . muryarsa  A hassale Yayi sallama yana cin magani .

Can   bangaren kuwa  ,
fk ne  ya amsa sallamar 'cike da farinciki   yana tmbyrsa  ko yana gida .

deeni dake zaune  rungume da nablah ya sake rungumota jikinsa da kyau sbd ganin Tana son subuce masa sannan yace Ina gida ya,akayi ne ?
 nothing daman fahad ne yanzu yakirani wai yana kiran layinka  kaki dagawa, gashi securities sun hanashi shigowa wai kai ne  kace kada su sake barinsa  ya shigo.

 Muryar deeni a dake  yace yes.. I said it ko akwai Wanda zai karya min doko ne ?

Fk yayi murmushi kawai sbd sanin halin taurin kan deeni .
 kai fa Dan bazan yaro ne wlh  .
  idan iskancinka ya sauka akan mutun to km  shikennan mutun yashiga uku .
to yanzu km me fahad din yayi maka daka yanke wannan danyen hukuncin akansa ?

Bbu ruwanka da duk wani hukunci dana yanke   ,fk yace yanzu hk zai ta tsayuwa a waje ?
Uhm kabarshi kawai  idan yagaji  zai kama gabanshi .
 ta yaya zaka ce abarshi  ?

Koma wani  irin  dalili ne Yasa  zaka hanashi shigowa ,gsky bakayi daidai  ba .
Kai ,kwata kwata ma hkn bai  dace ba wlh .
ka dinga sara kana duba bakin gatari fa .
ba wai ka dinga abu ,bbu    tunani ba . 

A hassale Deeni yadakatar dashi  Dan Allah ,Ni mlm ka sauraramin kar dameni da wani surutanka can Na bazan da wofi .
Ina ma ruwanka ciki  naga  Wannan ba matsalarka bace tsakaninmu ne nida shi km  komai zai daidaita idan lokacin yin hk yayi bawai ka kirani kana kawo min  kabli da ba,adi ba .
 ok shikennan  Allah Ya shirye ka deeni, Dan gsky kana bukatar addu'a wlh  , Ameen idan da gaske kake. yakarasa fadar hk  tare da yin  hanging din Kiran ..yacigaba da wasa da jikin nablah yana romancing dinta.

 hannuwanshi duka ya tura 'cikin hijab din dake sanye ajikinta ya diresu akan dukiyar fulaninta kadan ya rage bai sume a zaune ba .
Tsabar shauki daya dibeshi ,yana sakin numfashi da kyar tare matso daita  jikinshi sosai suna jin dumin juna.

ranta yayi mugun baci da takaicinsa , fizge jikinta tayi  tare da  juyowa  sosai suna fuskantar juna.
 gabadaya Gani tayi kamaninsa sun sauya sai wani irin kallo yake aiko mata dashi masu kashe jiki da zuciya.
 tsare shi tayi da shanyayun idanunta itama  fuskar nan tata a hade tamkar hadari a fusace tasoma mgn 'cikin fushi da Daga  murya .wai kai wani irin mutun ne sbd Allah ?
Meyasa kake min irin  hk ne?
 nifa gsky bana son abinda kake min haba sai ka dinga min wasu abubuwa  tamkar wata matarka ta aure wlh zan dinga kai kararka gurin mahalicina ya saka min akan abinda kake min .

 Hb Ni wannan jarabar  taka  tasoma isata   Ina fari kullun hannuka nakan jikinta wlh
Yadda kake min kai ma sai an samu wanda zaiyiwa yarka fiyye da ...caraf ya cafki bakinta 'cikin nasa yakashe  bakin tsiwa  .
runtse idanunta tayi kawai tana kokarin son  kwace bakinta cikin nashi.
 ,yayinda kirjinta ke wani irin bugawa da sauri tamkar ana buga mata guduma a kahon zuciyarta tsabar tsoron da frigicin dake dawainiyya da zuciyarta .

 rikota yayi sosai sunata   kokuwa cikin sauki ta dinga ganin tamkar bashi bane mutumin dake   tsotsar bakinta. idanuwanta suka dinga haskoma mata  cewar N ALIYU dinta ne ba wannan mugun ba .
  take ta kawar da haka a ranta tana neman tsari acikin zuciyata da addu'ar kar Allah Yasa  shedan yayi galaba akanta .
tun lokacin da take rungume ajikinshi yake son bata hkr amman yakasa dan bai San yadda zata dauki abun ba ,farincikin ko akasin hk .
  dan hk kawai yayi shr yacigaba   da jefa mata wasannisa zafafa masu kashe jiki.
 tana jinsu suna sauka cikin jikinta tamkar dai yadda N. ALIYU dinta ke mata 'cikin mafarkinta  gabadaya hankalinsa yasoma gushewa Daga jikinsa  .



 Da kyar tasamu ta tattaro jarunmta ta sanyawa jikinta da iya karfinta da Allah yabata ta fizge Daga jikinsa. tana sauke numfashi da ajiyar zuciya at the same time shima numfashin yake fiddawa  sama sama.
 taja tsaki tare da dubansa da nazarin halin dayake ciki  sannan tace Allah Ya isa tsakani dakai   wlh .
da rabar jikina  da kake Sha kullun .
aikin banza kawai mutun sai jarabar tsiya  kamar wani mayye tayi gaba tabarshi nan zaune yana bin bayanta da kallo dan shima kasa ce mata komai yayi ,oh my god ya furta ahankali meyesa meyasa bana iya control din kaina akan yarinyar nan ? 

Meke damuna ne akanta ?

Meke shirin faruwa dani?


Me tafi sauran mata dashi da take gaya min duk abinda yazo bakinta ?

Shit... gsky deeni kana kwabsawa fa dayawa akan yarinyar nan, da alamun  kana son yarinyar ta rainaka dayawa .
hk ya dinga mgn zuci da fili yana tmbyr brain dinsa , zuciyarsa ta bashi amsa daya shareta kawai.
 ,kai bazan iya ba wlh.
 to ka dinga cin ubanta da azabtar daita ,nan ma ya  girgirza kai alamun bazai iya ba   I can't .
 ya furta da kwausashiyar muryarsa .

 me zai hana ka dinga daure mata fuska kawai  kmr da ..gara gara ma wannan yabawa zuciyarsa amsa Yana shafa sumar kanshi da tafin  hannunshi...


 Duk wunin ranar nablah a dakinta tayi shi.
 zazzabi ne mai zafi  ya rufeta sbd kukan  data yi Ga xugin da gefen kugunta kemata.
 tarasa inda zatasaka ranta taji dadi arayuwarta  gabadaya a atsorace take da zamanta , ita daya a gidan take tarasa dalilin dayasa may gidan yake mata hk ba .

 Misalin karfe shida Na yammacin ranar kwance take akan gadonta Tana faman kuka yashigo har dakinta ganin duk wunin ranar bata fito ba ,kwance ya iske a kan gado tana kuka sosai jikinta sanye cikin wata  doguwar riga , cikin wace tazo dashine Daga gidansu .
Gashin kanta a baje sun rufe mata fuskarta .

 sai kuka take har da shesheka , ahankali yasoma Daga Zara zaran yatsun kafafuwansa har yakaraso har inda take kwance  ya tsaya,cak  tare da tsura mata rikitattun idanunshi kawai  .. tun sanda taga yasoma Daga yatsun kafafuwansa ta kawar da fuskarta gefe kirjinta Na wani iri bugawa da sauri da sauri .

Muryarsa a dake yace ke....wani irin shashanci ne hk ?
Idan ma wani abu ne damunki bazaki yi mgn ba sai ki zauna kinawa mutane kuka .

Ta Dago ahankali tare da tsareshi da shanyayun idanunta tana dubansa sannan  taja tsaki kana tace meyye matsalarka dani ?

In ce aiki nazo yi gidan nan km Ina yi yadda yakamata , please dan girma Allah kabarni na huta , yaya ne da maseefa ko kana Bina bashi ne ?

Ni kike gaya hk ranta a bace tace angaya maka me zakayi .
cak Yasa hannunsa duka ya dauke sama yayi hanyar steps daita ahankali yake taka step din daita ajikinshi.
 har ya fito harabar gidan  inda motocinsa suke jere ya zaro key din motarsa daya ya dannan ya bude ya zaunar Daita ciki ya tattara gashinta ya maudasu baya, tare da yafa mata Dan karamin mayafinta da ya riko mata sannan ya zagaya ya bude mazaunin direba yashiga yayi motar key tare da  fige  motar da gudu ya bar gidan  ..

 


Manage please banyi editing ba 🙏🏻🙏🏻🙏🏻


MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
 AUREN SIRRI
     💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO




Page 83


Ganin yadda Ya fige motar da gudu maseefa  Yasa kukanta ya Karu sosai, hankalinta yayi matukar mugun tashi tsoro tattare da fargaba ne sukayi nasarar   lullube duk wani  ilahirin jikinta, abubuwan da yake mata sun fara isarta Amman tarasa yadda za'tayi dashi.

 takaicin hk Yasa ta kife kanta bisa cinyoyinta tana sake resgar kukanta mai cin rai da  suma zuciyar ma'abocin sauraro .

Daidai jankode first get taji  ya Dan sausauta gudun motar tare da daukar hanyar Aja.
 " tafiya kadan  sukayi  ya soma alamun tsayawa  ya gangara gefen titi yayi park din motarsa, tare da  zuba mata rikitattun idanunshi kawai yana kallonta  da sauraran yadda take risgar kuka da iyakacin karfinta.

 jin kukan nata yake har 'cikin zuciyarsa yayinda gefe daya km ya dinga ji  tamkar ana diga masa ruwan dalma ne a kirjinshi , yana jin yadda sound din kukan nata ke fita da karfi har da shesheka .

runtse rikitattun idanunshi yayi tare da dafe daidai saitin zuciyarsa da tafin hannushi sakamakon yadda yake jin  zuciyarsa na bugawa da karfe ...

bai jin zai iya yi mata mgn a yadda yake jin kansa Dan hk yabarta tayi kukanta mai isarta sannan ahankali  yaji  tasoma yin  shr  tana jan numfashi da kyar da sauke ajiyar zuciya.


Jin ta daina kukan Yasa shi bude rikitattun idanunshi, ya  ya Ciro hanky agaban aljihun rigarsa ya goge fuskashi wanda ya jike da gumi sharkaf tsabar tashin hankali daya tsinci kanshi ciki .


Ahankali ta dago kanta ta maida gefen titi tana kallon motocin dake giftawa time to time ...

 gyara  zamansa yayi da kyau yana fuskantarta ahankali ya Dan motso   kusa daita tamkar zai shige cikin jikinta  Yasa hannunsa duka ya mtaso daita yana mai  juyo da fuskarta yana kallon kwaryar idanunta batare da yace mata komai ba . kawai taji  ya hau  goge mata Hawayen dake   fuskarta, yana cigaba da  kallonta hade da yin  nazarinta..

 
Sannan ya hade tafin hannushi cikin nata .yana kokarin fixgota jikinshi taki yarda ta makale jikinta da kujerar tasoma kokarin cire hannuta cikin nashi ,Yayi saurin sake damke hannu nata cikin nashi sosai ta yadda bazata iya kwacewa ba.

 wani irin zafi yaji ,jikin nata ya sake dauka fiyye da sanda suka baro gida  ,km yana jin yadda da zafin  ke fita yana  shiga jikinsa tare da ratsa kowane shashi Na jikinshi  .
 ya kai hannushi gefen wuyanta "nan ma zafi yaji  tamkar garwashin wuta hankalinsa yayi maseefar  sake tashi sosai .
, wani  irin abu ya dinga ji   mai kama da so.. yana masa yawo a sansar  ajikinsa tare  da kokarin kawowa zuciyarsa farmaki take duk wani kuzari dake jikinshi ya nema ya rasa ..tmby ya jihowa zuciyarsa da ruhinsa kar dai yakamu da soyayyar yarinyar ne, batare da yashirya yin hakan ba ?
Kai hkn ma ba zai taba yuwa ba , take km wani part Na zuciyarsa yashiga  karyata hakan .

yasan ya taba son auren zeenat .. km koda ummi ta hanashi aurenta alokaci, bai tsinci kanshi 'cikin wannan tashin hankali dayake ciki ba ..

 Wani irin sanyi yake ji ajikinshi tamkar ana masa wanka da ruwan sanyi akan yarinyar duk wani buga da zuciyarsa zatayi ,tana yi akan yarinyar , mamaki ne fal yacika zuciyarsa to me hakan yake nufi dashi km ?
Ya tmbyi kanshi .
Wayyo Allah ahankali yashiga furta hasbunallahu wani'imal wakil yana yi yana sake  nanatawa 

da kyar yasamu ya dinga fizgo  numfashi yana fitarwa ,ahankali ahankali  da sauri ya saki hannuta dake sarkafe da bashi  yayi  reverse ya dauki  hanya zuwa 'cikin gari ..


Tafiya sukeyi tamkar wasu kurame bbu may cewa Dan ,uwansa qala.kwanensu da abinda ke damun ,shi  yana wata duniyar tunanin yadda yake jin yarinyar akasan zuciyarsa gabadaya Gani Yayi tana neman mamayeshi da komai nashi .
,yayinda ita km haushin kasancewarta tare dashi guri daya  Yasa tarasa walwalarta da sukuni...

 Dan ko kallo bai isheta ba ,dan tunda ya tada motar ta km maida fuskarta gefen titi .
 
,shi km yacika fammm tamkar zai hadiyi zuciya  ganin halin ko inkula data nuna masa.
Cikin sanyi jiki  ya sake  Ciro hanky ya goge fuskashi Dan wani irin gumi ne ke karyo masa duk da AC motar dake aiki ,sannan  ya maida hankalinsa Ga tukin da yake ..


A bakin wani big super market yayi parking ya fito ya kulleta acikin motar yashiga ciki .

tun Daga shigowarsa work's din gurin suke gaida shi 'cike da girmamawa , wasu ya amsa, wasu km ya Daga masu hannu kawai .

hatta manage gurin biye yake dashi abaya suna tattaunawa ahankali ta yadda bbu mai jinsu ..

Kaya  ya zazzaba wayanda zasuyi  amfani dashi  ya fito.
 manage gurin na rike da ledodi guda biyu daya mai girma daya Yar karama ,deeni   ya bude motar yashiga ya  zauna tare da  karbar  ledar dake rike a hannun manage ya ajiye a sit din baya ,ya Dan kalleta ,kadan yaga fuskarta a hade tamkar hadari har lokacin taki sakin fuskarta haka kawai ya tsinci kanshi da jin faduwar gaba .
gabansa yashiga dukan dakan uku uku.
  ....karamar ledar ya sake amsa ya cilla mata bisa cinyoyinta batare da yayi mata mgn ba. Ta zabura ta Mike zaune tana gyara zamanta Daga Dan kishingidan datayi tana kallonsa  , bai bi takanta ba  ya dauke kanshi gareta shima ya tamke fuskarshi sosai fiyye danata  ,
 ya tadda motar  ya hau  kwalta ,bai damu  da yadda manage din ke Daga masa hannu ba yana masa fatar a sauka lfy  ..karatun alqur'ani mai girma ya kunna  Kira'ar SUDAIS cikin suratul  ra'ad ya 

Da wani irin kallo take binsa dashi 'cike da tarin maseefa  Amman sai tasamu kanta da shan jinin jikinta sakamakon hango yadda Ya hade rai bbu halin aikata abinda tayi Niyya ,Ga km karatun alqur'ani mai girma daya soma  ratsa sansar jikinta  ta komawa ahankali ta lefe lamo..  a kujera.
 ta Dan Daga kanta sama idanunta a lumshe tamkar mai jin bacci ..tana jin yadda sautin  karatun ke tashi itama tana bi cike da natsuwa .

Ya Dan juyo ya saci kallon Dan karamin bakinta dake motsawa sannu sannu .

Can taji ya rage sautin karatun  yasoma waya cikin harshen turanci wanda yake yinsa 'cike da kwarewa tamkar yaren  uwarsa da ubansa  ..

Cikin sanyi muryarsa taji yana cewa  kina office ne  ?
Ita dai batasan  abinda Na cikin wayar yace ba. ok ganinan  zuwa yanzu  wata yarinya zankawo ki duba min lfyrta ,sannan ya ajiye wayarsa yacigaba da tuki .


A harabar wani katanfarin special hospital yayi parking ya kashe motar ya juyo da dubansa gareta ,tare da tsura mata Rikitattun idanunshi.
 ,jikinta   yake kallo musamman tsaitin inda ta buge kana ya maida idanunshi kan kyakywar fatar  fuskarta.
 idanunta sun Dan  kumbura sbd kukan datayi .
 fuskarta tata tayi fayu daita ,Amman duk da haka bai hana sihirtaccen kyauwunta fitowa ba ,km tayi masa kyau sosai .

,lumshe idanunshi yayi ya Dan kamo lips dinsa na kasa   yana ciicizawa ahankali ahankali  sai km ya saki Murmushin tare da tura yatsunshi hannushi 'cikin sumar kanshi yana shafawa  a zuciyarsa ya furta mutun may kyau ako wani hali yakasance mai kyau ne domin kyawunsa bai boyuwa ..


 Ta tsargu da kallonta yake sbd idanunshi dake yawo ajikinta Ahankali ta bude shanyayun idanunta da suke a runtse tana dubansa dasu  jin  yayi parking km  idanunshi nacigaba da  yawo ajikinta ..

wata uwar harara ya watsa mata tun kafin tayi challenging dinsa  tare da daure fuska tamkar bashi takama yana kallonta ba.
 itama sake  hade ranta tayi tamau tare da turo bakinta tana jan mugun tsaki .... Ahankali km ta furta aikin banza kawai mlm...

Ba zato balle tsammani taji saukar  rankwashi a tsakiyar kanta.
 dafe gurin  tayi tana kallonsa da shanyayun idanunta.

Idanunta suka soma kawo  ruwa .
Ya murde mata kunne da karfi .
ta saki kara .mara sauti sannan ya buge mata bakin tsiwa  ,ta kama bakinta da hannuwata duka tana mai zuba masa shanyayun idanunta wanda suke zubda hawaye .


A hassale yace ki duba 'cikin wannan .. yana mai nuna mata ledar dake saman cinyarta  akwai hijab ki ciro ,ki suturta jikinki  dashi ,sannan ki fito Dan bazan iya fita dake, da wannan shigar  ta Yan isaka ba .
Kisa  nima mutane su dauka nima haka nake ..

Ba musu ta hau bude ledar tun Bai kara mata wata izayar ba wasu  dogayen hijabai tagani  colours biyu .
 dinki zamani masu shegen kyau da daukar hankali, duk da ranta a dakugule yake  Amman hakan bai hanata jin dadi ba,domin  sai daukar idanun suke dagani ma ba dinkin Nigeria ba ,Dan yafi mata kama dana kasashen larabawa.. ta zira ajikinta tafito tana gyra zamansa da kyau ..


Yana gaba tana binshi a baya duk inda suka gilma  sai kallonsu mutane ke yi.
 ,yayinda ake ta gaidashi 'cike da girmamawa wanda har itama bata tsira Daga samun nata gaisuwar ba ..



Kai tsaye office din. Doctor saira Jack ya nufa daita ....




manage please wlh akwai uziri cika alkwari kawai  nayi

MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO


*Where are you murja come close this page is for you only i'm so existed for ur care, thank you so much ,Allah yabar kaunar dake tsakaninmu mara algus ,kin nuna min  karamci da aikin girma, bagudo taga karamcinki   km ta yaba Allah yakara arziki ,ke din ,daban kike  acikin mutane, bakowane mutun ne tamkar ki ba, you are so special*🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻




Page 84



Da sallama abakinsa  yashiga office din yayinda nablah ke biye dashi abaya tamkar wata sabuwar halitta ta daban sannan ta maida kofar office din ta rufe takarasa shigowa ciki sosai .
zaune suka iske doctor saira sanye cikin kayan aikinta Na cikakkiyar doctor idanunta manne da farin medical glass ..tana ganinsa ta fadada fuskarta da murmushi Tare da Dan   Mikewa  tsaye kadan  tana gaidashi tana mai  nuna masa gurin zama da hannuta.

 ,ya zauna yana may   amsa gaisuwarta fuskarshi ba yabo ba fallasa .
 sannan tayiwa nablah dake rakube a gefe tsaye nuni da kujerar zama  .


Nablah ta zauna '  a daddare 'cike da  natsuwa tana karewa office din kallo sbd yau shine karo Na farko data ,taba shigowa irin wannan hospital din na masu hannu da shuni ,kai har ma  da  office din gabadaya.
Hk   kawai ta tsinci kanta da jin wata irin mummunar faduwar  gaba.

 batare da wani bata lokaci ba deeni yashiga yiwa doctor saira   bayanin abinda ya ke tafe dashi ,akan so yake ta duba masa   lfyr yarinyar dayazo daita .

Doctor tayi murmushi  tana kallon shashin da nablah ke zaune kanta a sunkuye  tana wasa da yatsun hannuta tasoma tmbyrta abinda ke damunta 'cikin harshen turanci.

 nablah tayi tsuru tsuru da idanu takasa cewa komai sai da doctor saira ta sake maimaita tmbyrta" sannan muryarta a sanyaye tace bbu abinda ke damuna fa . Km ni fa lfy lau nake babu inda kemin ciwo  .

Deeni ya juyo ahankali yana kallon Dan  karamin bakinta da take tsukeshi a duk sanda zatayi  mgn 

A Dan fusace Yace ke banson iskanci ki sanar mata da abinda yake saki zafin jiki bawai ki tsaya kina wani  batawa mutane lokaci ba ..

A dake itama tace to bbu abinda yake damuna sai km  nayi karyar ciwo .

Yaja tsaki yana cizan gefen lip's dinshi    kana yacigaba da mgn.
" doctor karki sake tmbyrta" ke dai ki duba min lfyrta kawai . 


Doctor saira tayi murmushi duk da batasan matsayin yarinyar gareshi ba ,Amman sai taga sunyi matukar dacewa da junansu .
tace Ok sir  ,amman mr DEENI baza'a yi hk ba ,ciwon nan  ajikinta yake yakama mu Dan daji wani abu Daga bakinta first  so that za'a San ta inda za'a soma duba lamarin .

 DEENI yayi shr tare da dauke kanshi bai sake tsuma musu baki  ba sai ma  phone dinsa daya Ciro  yasoma operating.

 ita km doctor saira ta sake maida hankalinta sosai a kan nablah .

yauwa  kanwata Ina jinki  yi kokari ki sanar min da abinda ke damunki da kyar dai doctor saira tasamu nablah tace mata  wani abu .
A gsky Ni bana jin ciwon komai ajikina ,sai dai sometimes hk  nakan ji  motsin wani abu acikina... 'cikin wani irin yanayi na shock DEENI ya dago rikitattun idanunshi ya zuba mata yana kallonta ,ta Dan tsuke bakinta ganin yadda yake kallonta sannan  tashareshi  tamkar batasan ita yake kallo ba, tacigaba da mgn da muryarta a shagwabe.
 Amman Ni doctor Allah  Ina ganin kmr appendix  ke damuna.
 ba doctor saira ba hatta deeni sai da mgnrta, ta kusan sashi dariya .
Aiko yayi saurin juyar da kanshi gefe yana fitar da sanyayyir murmushi .
hk kawai  ya tsinci kanshi 'cikin wani irin farincikin Na daban km mara misaltuwa .

Doctor saira ma dariya tayi sosai sannan tace ba kece zaki yanke hukunci abinda ke damunki ba, computer ce zata sanar mana.
 " mu dai inda ke miki ciwo kawai zaki sanar mana . 
A Dan hassale tace to...bbu inda ke min ciwo baya Ga motsin danake ji acikina .

 doctor saira ta  mike tsaye byn tagama sauraron nablah . tace Ok  biyoni muje  tayi gaba
  Nablah taki tashi  sakamakon wani tsoro dayashigi  zuciyarta alokaci guda.
Domin  ,gabadaya tunaninta ya tafi ne akan allura za'a yi mata ,gashi km  ita bbu abinda ta tsana sama dashi .
 dan shegen  tsoron allura gareta  kmr me .
Dan haka ta gyara zamanta  taki mikewa tabi byn doctor.

Deeni dake zaune har lokacin ya sake   juyowa inda take zaune  yana dubanta ganin taki mikewa tsaye Yasa shi  ,tsura mata idanun shi  kawai yana kallonta tare da  hade ranshi  tamau  tamkar yana filin Daga ..yayinda  tuni zuciyarsa tasoma yamutsewa ta cure guri guda , yasoma manta inda yake jira kawai yake ta tunzurashi.
 wani irin kallo yake aiko mata  dashi may tattare da tsantsar tashin hankali, km  wanda yake mata  nuni da Babu sausauci acikin  lamarinsa idan yatashi antaya mata  rashin mutuncinsa .

Dan hk tayi zumbur ta Mike tsaye  .
da sauri jikinta Na wara tabi byn  doctor saira ..Ya naunauyen ajiye zuciya yana bin bynta da kallo wayarsa ya dauki sautin kida yay pic din Kiran  sannan ya Mike tsaye tare da manna wayar a kunnenshi ..


Kai tsaye dakin gwaje doctor saira  tayi da nablah sannan  ta hadata da wata nurse tace a soma mata  scanning din appendix tukun .

Nurse  ta umarce nablah da ta kwanta akan Dan wani madaidaicin bed wanda akewa mutane Scan akanshi .

bbu wani  musu tabi umarnin   nurse  din.
Tare da  Daga rigarta sama kadan kmr yadda nurse din ta sake bata umarni.

'Cikin iyawa da kwarewa akan aikinta nurse ta soma  yi mata scanning .
 gefen cikinta fati maida hankali akai Amman bata Ga komai  ba' km bbu wata alama ta appendix a cikinta   Dan hk tayo kasa kadan gurin mararta nan taga wani abu kmr gas.... a saman maharfarta Dan hk tashiga binciken gurin sosai.


 cikin minti Goma tagama  yiwa nablah scanning km tare da gano abinda ke cikinta km  duk wannan lokacin   doctor saira Na tsaye akan idanunta akayiwa  nablah komai .

Nurse ta bata umarni sauka.
Nablah  ta Mike ta sauko Daga kan bed din tana gyara rigata da hijab dinta  . 

Suna fitowa Daga dakin scanning office din  doctor saira suka koma kai tsaye inda ,
 deeni ke zaune zaman   jiransu .



Ga mamakin   Doctor saira bataganshi  'cikin  office din ba .

Dan hk  hannunta rike da  takardar scanning din ta zauna a mazauninta tare da nunawa nablah dataja ta tsaya gurin zama .

byn ta zauna ne doctor saira ta gyara zaman medical Glass dinta sosai sannan  tace are married ?
nablah tayi saurin  girgirza mata  kanta .

 mamaki da alajabi yacika  zuciyar doctor to kinsa kina da ciki ne ?

Afrigice nablah ta dago  tana yiwa doctor din wani irin  kallon rainin hankali sannan km wata siririyar murmushi ta kufce mata.

 'cikin lfy doctor Ni ciki ta nuna kirjinta da yatsanta doctor ta Daga mata kai .
Ba dai Ni ba wlh sai dai wata nablah daban Amman Ni  banida da ciki komai, byn Na cin abinci danake da. 

Doctor tayi shr  tana kallon nablah da nazarin bata da cikakkiyar lfy.

 da fari da suka zo ta yaba da yarinyar amman yanzu dataji batada aure km Ga ciki ajikinta  Yasa taji yarinyar ta fice mata arai.

 ,ta girgirza kai kawai    tace you are three to four months pregnant .

Nablah taji kirjinta ya buga da karfi take zuciyarta tasoma rawa bakinta Na rawa tace  Aa wlh Ina jin fa wannan computer din taku tana da matsala har ta nuna muku karya.
 'cikin lfy ...ya Ina zaman zamana  zaki kakaba  min ciki .
kai wlh Ni ban  yarda wlh may be dai result din wata nablah ne bani ba ,ki de sake dubawa da kyau  shiyasa fa tun farko nace miki bbu abinda ke damuna kika matsamin kika manage sbd   kinsa sharrin da  zaki kulla min Keenan .

Doctor saira ta numfasa kana tace ,ki yarda da karki yarda you are pregnant.

Nablah tayi sororo tana duban doctor saira .
A matsayin may tabin hankali yayinda itama doctor din ,ke mata kallon hk .
da kyar nablah  ta iya hadiye miyon bakinta tsabar gigicewa datayi kana bakinta Na rawa tace Ni nan da kika ganni Virgin ce Ni  gaba da baya.
 ban taba sanin wani da namiji ba tunda nake a rayuwata,  ta yaya yanzu zaki zo kice min ciki gareni Na yarda .

ganin da doctor saira tayi bil 'haki nablah bata yarda 'cike gareta ba Yasa ta dauki wayarta ta kira wata nurse daban 'cikin Yan mintina da basu biyar ba sai Ga nurse tashigo doctor saira  tace ta dibi jinin nablah taje ta gwada mata ... hk kuwa akayi  aka dibi jinin nablah wanda gabadaya hankalin nablah a tashe yake km atsorace take.

 Amman data tuna bbu wani namiji daya taba having sex daita sai taji hankalinta ya kwanta ta Dan samu natsuwar zuciya  sai dai hakan bai hana  gabanta dokawa da sauri ba.

'Cikin  haka Kiran deeni yashigo wayar doctor saira .
 byn doctor ta dauka  yake tmbyrta ko  angama duba nablah. 

 Cike da natsuwa doctor saira tace   anyi mata scanning  .
Km  Na sanar  mata da abinda muka  Gani ajikinta ,  amman taki yarda ,ta fada masa hk atakaice batare da tasanar masa da ciki ke Ga nablah ,Dan hk  nace a mata  gwajin jini domin sake  tabbatarwa. 

yanzu dai  zuwa nan da 1 hour result zai fito , Dan hk  zaku Dan tsaya zuwa anjima kadan  domin  karbar  rasuit .
  deeni  yace Ok  bbu  damuwa  turo min ita kawai   ma  dawo zuwa  anjima din.

Sukayi sallama sannan ta sanar da nablah abinda deeni yace.
 jikinta a  sanyaye    ta Mike ta  fice  Daga office 'cike da jin haushin doctor din .



Cike da natsuwa yake tukinsa yayinda sanyi AC  da kamshin 'cikin  motar ke  ratsa kowane shashi Na zuciyoyinsu .
 tafiyar suke tamkar ta farko fitowarsu Daga gida .
 bbu  mai cewa dan'uwansa komai.


Yayinda zuciyar nablah ke 'cike da matsanancin tsoro da frigice hk kawai zuciyarta takasa natsuwa dashi sai zare ido take .
Burinta bai wuce ta ganta a gida ba.

Shima km sai faman falfala  gudu yake a saman kwallata batare dayace mata komai asalima ko kallon inda take zaune bai yi ba .

tana kallonsa taga ya wuce titi jakonde first get bai karya kwanar estate dinsu ba .
,take gabanta  ya  shiga   faduwa da sauri .
 ta Dan juyo ta saci kallonsa Amman sai taga gabadaya hankalinsa baya gareta .
 sitiyarin mota kawai yake juyawa   . 
Da gefen ido deeni yake kallonta yana nazarinta 
Murmushi yaso kufce masa ganin yadda ta gigice lips dinsa na kasa ya kamo yana cizawa ahankali yana cigaba da tukinsa.
 jinsa yake 'cikin wani irin  yanayi Na daban Dan hk  ya nufin sabon gidansa daita Wanda aka gama a last month din daya wuce .

Muryarta da jikinta gabadaya rawa yake mgn take son yi Amman takasa Dan hk ahankali  ta daura hanunta saman nashi ....
" wani irin  sanyi dadi yaji  yacaki zuciyarsa  da  kaiwa gangar  jikinsa ziyara tare da neman tarwarsa masa zuciya..

Da kyau tasamu ta fizgo mgn bakinta  'cike in... inna.... 
tace please Ina zaka kai Ni ?

Ka maidani gida mana .

Ai gidan zan kaiki ..ya bata amsa batare daya juyo ba .

ta fashe da wani irin gigitaccen kuka wlh ba hanyar gida ka dauka ba.

 Allah Ni dai ka kaini gida Ni tsoro ma kake bani wani irin sanyayyayiyar murmushi yayi sannan ya gangara gefen titi ya tsaya yana kallonta ita km sai kuka take tana rokonshi yakaita gida.

 'cikin sanyi muryarsa ya Kira sunanta tare kamo tafin  hannuta cikin nashi  yasoma murzawa ahankali ahankali yana kallon Zara zaran yatsun hannuta yana sake murza 'cikin tafin hannunta .
wani irin suka dinga ji ajikinshi gabadaya wani irin feeling ne ya tsigar musu take ta tsaida kukanta tare da dago shanyayun idanunta da suka canza  sbd kuka datake .

Kin fi son muje gida ne?

Ya jiho mata tmbyr  tayi saurin Daga masa kai alamun eh.
 ,Ok ki kwantar da hankaliki bbu abinda zan miki . inda zamu shima tamkar  gidan agurinmu.

 'cikin wata irin sanyayer muryata mafi soyuwa gareshi km may kashe masa jiki a duk sanda yajita ,tace a'a Ni dai kar ka kaini koina please .
ka maidani gida kawai .


Murmushi kawai yayi tare da kamo lips dinsa yana cizawa  yana  cigaba da murza tafin hannunta mai taushi da tsantsi .
muryarsa a kasalance yace ok zan maidake gida Amman ki bari mukarasa inda zamu zan dauki abu ne a gidan sai na maidake gida .
yana gama fadar hk yayiwa motar key.

Hankalinta ya Dan kwanta kadan  ahankali ta dinga  sauke ajiyar zuciya  jin abinda yace ta koma ta maida bayanta cikin kujerar motar ,Dan ba yadda ta iya  dashi sukai cigaba da tafiya hannuta cikin nashi yana aikin murzawa gabadaya ya sauya mata yanayin jikinta da wani irin  azababen felling ,wasu siraran Hawayen suka shiga bin kuncinta.


Ahankali  yasoma  rage gudu motarsa  yashiga  'cikin aja .
Wata kwana ya karya ya dauke wata hanya daban  tunda Daga shigowarsu layin  hankalinta ya sake mugun  tashi .
gabadaya ta dawo wata   iri daita   kallar tausayi still bai zare hannushi cikin nashi ba  . Komai Na unguwar daban yake tunda Ga kan gidanjensu har zuwa motocin dake gilmawa ..

Daidai wani makeken gida mai shege girma  taga yaja ya tsaya yana yin hon yayinda.
 gabadaya gidan manne yake da Glass takoina sai kyalli yake  get ne mara tsawo zagaye da gidan km shine  kadai  bai kasance Glass ba.. tana ganin a zuge get din gidan, hankalinta ya sake tashi fiyye da da , ta fashe da wani Sabon kuka ta rike  hannushi gam cikin nata . wani iri ya dinga ji ajikinshi ganin ,yadda take 'cikin halin   damuwa.
  Gabadaya yaji zuciyarsa ta cunkuse guri daya ya tsani kukan nata  mai cin rai da narkar da zuciya .

Ahankali ,ya cilla hancin matarsa cikin farfajiyar gidan yayi park  a parking space sannan ya juyo.
 ya kalleta da wani irin yanayi muje ko .

Kin fitowa tayi hade sakin sabon kuka bakinta aa rawa tace Allah bazan shiga gidan nan ba,Ni ka maidani inda ka daukoni .

Tsayawa yayi kawai yana kallonta  sannan yace lallai yarinya  Ashe zakiyi azumin kaffara ,Dan wlh azim kinji Na ratse sai kin shiga gidan nan  koda kuwa mutawa zakiyi byn kinshiga  ..
Ta watsa masa wata katuwar harara tana hawaye ya jawota jikinsa yana kokarin shareta mata Hawayen dake bin fuskarta ta buge masa hannushi .
Ni karbani banason batare da yace mata komai ba Ya sakar mata jiki  Ya fito Daga motar ya bude inda take a tukure a zaune .
 ya gyara hannun rigashi yana nadewa yasoma kokarin ciccibota.
 ta saka kara wlh karka daukeni zan fito da kaina uhm kibari kawai Na hutar dake .
Ya sankuce tare da  sapabata a kafadatsa yasoma tafiya daita ta sake saki wata razananniyar kara ..
kinsa Allah kimin shr kinga gidan nan akwai mutane  kar su dauka kowani abu zan miki.. alhalin taimaki miki kawai zanyi to ka sauke  nashiga da kafafuna.
Ganin yadda take yasa shi yin tunanin sauketa  tun bata jawo masa matsala ba.

 ya sauketa ahankali batare da wani garaje ba  suka jera tare  yana rike da hannuta cikin nasa daidai kofar shiga ya janyota jikinsa ta gabansa ya daura hannushi akan glass din. Take kofar ta bayyana 'cike da mamaki da tsoro nablah ke kallon wani irin  hadadden parlour Wanda tunda take rayuwarta bata taba ganin irin parlour ba.
To a Ina zata Gani ?
 koina aciki gidan Glass kana kallon kanka ciki. take ilahirin jikinta yasoma kirrrrrrma yayinda zuciyarta ke cigaba da bugawa. hannuta ya janyo suka shiga kofar ta maida kanta ta rufe tana masa welcome da zuwa.

 Muhammed  aliyu khaliyal  you are welcome......  abinda ya sake frigita zuciyar nablah kennan tace wayyohhhyyy Allah wani irin gida ne wannan kakawo
 tamkar gidan yankan kai ?
,ya tabe bakinsa  yana dubanta tare da cewa Yar kauye kawai dube dan Allah yadda kika koma .. mtssss yaja tsarki ya barta nan ya nufi step din sama  inda dakinsa yake ta gudu tabishi abaya tana kuka .....

 suna shiga dakin taga yasoma cire kayan jikinsa ya saura Daga shi sai short niker iya cinyarsa ya janyota jikinsa tare da kokarin zare hijab din jikinta ta kamkame jikinta guri daya taki barinshi ,sai dayayi amfani da karfinshi sannan yasamu ya zare hijab din yayi filling dashi .
ya manna bayanta da kirjinshi hannuwanshi zagaye da kugunta kana yasoma tafita daita.

 gaban mirrow yakaita tare da ,daura  bakinsa  kan kafadarta yana shinshina gefen  wuyanta wani zafi yaji jikin nata ya sake yi yana son bata maganin zazzabi Amman yana tsoro so yake yaji abinda doctor zatace ,'cike da sanyin nan nasa  ya maida  hannushi kasan  mararta yayi shr kawai  yana son yaji motsin datace tana jiki acikinta ,aiko atare suka jiyo motsin bby .
ya lumshe rikitattun idanunsa dan farinciki daya tsinci kanshi ciki . Addu'a yake akasan zuciyarsa Allah yasa  abinda yake tunani ne yake zai  tabbata .

Ahankali ,ta dago shanyayun idanunta da sukayi luhuluhu.
 ta zuba masa ta 'cikin mirrow  tana kallonsa Shima daidai nan ya dago nashi . idanunsu suka sarke cikin juna take wani irin shock sukaji atare ,ya kifta mata idanunsa duka tare da  kashe mata idonsa daya sannan yace me doctor tace miki  yana damunki da kika ki yarda dazu ?

Ta dan yatsin fuskarta alamun bataso tmbyr dayayi mata ba.
 Tayi shr taki cewa komai yayi sama da hannunshi yana kokarin damko breast dinta ta katseshi  ta hanyar rike hannushi kana  tace nifa bangane kan doctor din ba ,da Inda  mgrta ta dosa .

yace Allah ko..?
 tace uhm a ranshi yace zaki gane ne yarinya  sai randa sirrin boye ya bayyana kanshi tukun  .
 "Ta tsura masa ido ta 'cikin mirrow din  ganin yadda yayi  shr yana aikin yawo da hannunshi a sansar jikinta  .  Muryarta a kasalance yace oooooo dan Allah Ni kabarni bana jin dadin jikinsa ,kawani zo zaka Dame Ni ..

 Yayi  kan Italy bed dinshi yana may  fixgota saman fadadden kirjinsa zo nan yar kauye kawai ..tafada jikinsa tana sakin numfashi ya  tsura mata ido yarasa me zai sake cemata kawai ya zarce da romancing dinta yana wasa da albarkatun kirjinta wani shauki ne ke  shiga jikinsu  Daga ita har shi Dan har gara  gara ,ita ma akan shi .

Dan shi gabadaya susucewa yayi ,ya wani iri , komai Ya tsaya masa burinsa bai wuce kawai  yaji shi cikin duniyar kasanta  ba .
 sosai ya dinga romancing dinta ita km kufkufce masa Amman yaki barinta abinda yafi so ajikinta su  yafi  damuka da hannunshi.. sai daya Dan ragewa kanshi zafi daita sannan ya kwantar daita.

" ya Mike tsaye  yashige bathroom .wanka tsarki yayi may hade da alwala sannan ya fito kungunshi daure da towel tana ganinsa ta runtse idanunta har sai dataga yasoma
Shiryawa 'cikin wasu haddadun kanana kaya masu shegen kyau da daukar hankali ya fito fess abunsa cikakken namiji mai ji da kansa sai kamshin ne ke tashi ata koina ajikinsa .

Tunda yake shiryawa take binsa da kallo har yagama shirinsa shanyayun idanunta  Na kansa, duk yadda taso dauke idanunta akanshi takasa aikatawa hakan sosai taga yayi mata kyau fiyye da kullun .

Ahankali ya tako har zuwa gabanta ya tsaya ya sunkuyo suna musayar  numfashin junansu muryarsa can kasa tamkar ta mai koyon mgn yace wannan kallon fa ?  

Tayi saurin dauke idanunta tana girgirza masa  kai batare da tasan tayi hakan ba . Yacigaba  Kadai ki cinyeni fa da wayannan idanunwa naki please..


Wani irin matsanancin kunya taji ya dirar mata Na kamata dayayi tana kallonsa ta dinga jin wani iri a tsansar jikinta.. yayinda  zuciyoyinsu ke bugawa da sauri a tare ...Ya sake matsota sosai yana hura mata iskar bakinshi  .
shi kasa rasa gane kanshi yake matsawar yana tare daita ,take yake losing  control dinsa yasoma sakin layi yana kokarin son hade bakinsu guri daya ..

Hannuta Tasa tana tura kirjinshi da karfi yayi baya ta Mike da hanzari ta nufi kofar fita Daga dakin ya damki damtsenta fuskarshi bbu alamun wasa ya maidata kan gadon data taso .

Ki kwanta ki huta ki jirani  yanzu zan dawo ba jima zanyi ba Ina acikin gidan  kanta dake  sunkuye ta Daga masa  alamun taji Dan hk kawai taji , Allah Allah take ya matsa kusa daita dan wani irin maseefar kunyar hada ido dashi take yanzu murmushi yayi mara sauti  yana tabe  baki ..mara kunyar karya kawai ya furta hkn a can kasan makoshinsa..



Yana juya baya  ta Mike zaune tare da  dirowa Daga kan gadon ta rike kugunta tana jijiga jiki aikaine mara kunyar karya ,Ni Sam ba mayya bace wlh da zakace kada Na cinyeka .
 kaine dai mayye mai son taba jikin da ba halalinsa  ba , takarasa fadar hk tana murguda baki 'cike da tsiwa   .

Ya bude kofar da sauri  tare da tsura mata rikitattun idanunshi tamkar ya dawo inda take yayi maganin bakin tsiwa sai km ya fasa sbd sauri da yake .

Ya girgirza kanshi kawai yace  yarinya zamu hade ne dake very soon ba dai takamarki maida min da martani ba ,to zan dau mataki akanki tsaye yake rike da handle din kofar   ..

Taja da baya tana zaro ido waje da mamaki  jikinta Na rawa  a ranta tace  Anya kuwa mutumin nan ba aljani bane ko mayye ? 

Yana gama fadar hk ya juya abinsa.

 kofar taje tayiwa key  jikinta Na rawa  ta zare key din sannan ta dawo ta bude fridge din dakin ta dauko karamin kwalin holandia mai tsanyi ta bude tare da kafa kai sai data shanye tasssss sannan ta ajiye kwalin saman gadon ta koma ta zauna tana sake karewa koina kallo tamkar a aljannar duniya take.

 ahankali idanunta suka sauka akan wani makeken hotonsa dake manne da jikin bango dakin.Ta tsurawa hoton ido kawai tana kallon tsansar kyawun halitar da s.w.a yayi masa  . sanye cikin kakinsa Na soldiers  kakin sunyi matukar karbar jikinsa tare fidda kyaunsa .

Tsuru tayi masa tana son gano inda muninsa yake tsabar kyawun halitar da Allah yayi masa duk nacinta hk ta hakura ta kwana tana lumshe shanyayun idanunta ..


Motsin dataji a 'cikin dakin   ne  Yasa ta  farka a frigice ta bude idanunta tana ambaton sunan Allah  tare da  kallon inda yake tsaye  sanye yake  cikin wando three quarter  da riga hamles wato ma ya dade da dawowa dakin  tunda gashi har ya sauya kayan jikinsa  .

 yana ganin irin farkawar datayi yakaraso gurinta da sauri ya zauna kusa daita tare da janyota jikinsa sorry please Na tashe ko ?

  wani iri taji ajikinta jin  yadda yayi mata tmbyr .
ta dinga  kallonsa tamkar zatayi kuka muryarta a sanyaye sannan km a shagwabe tace yanzu Dan Allah kadawo Amman ka kasa tashina nayi sallah jibi yadda lokacin bautar ubangijina ya wuceni baka tasheni ba .

Wlh allah zunubin akanka Allah zai daura tunda kana sane na makara gurin bautarsa ,tana gama fadar hk tasoma kokarin  janye jikinta Daga gareshi  tana yatsina fuska.

Ya rungumeta  sosai ajikinsa yana fidda wani irin  numfashi mai hade da shauki .

bai sanda yace kiyi hakuri banason Na tadda ke .. Daga baccin da kikeyi ne sh...... cak ya datse harshensa kafin yakarasa abinda zaice .. dan Allah Ni sakar min jiki  bana son irin abinda kake min.

Ni dai dan Allah  ka dinga yin nesa nesa dani  Hb sai ka dinga yi tamkar zaka shige min jiki .

Ya girgirza kanshi kawai yana murmushi jin dadi a ranshi yace Na yaushe kuma ai aikin gama yagama yarinya .

Wata katuwar harara ta watsa masa 'cike da takaici halinsa mikewa zatayi da karfi  yayi saurin maidaita yace please bi ahankali man kin wani tashi da karfi hk  ..

Ba' za'a bi ahankali ba jikinka   ko nawa ka?
 jimin mutun da tsirfa kawai , ta sake yunjura da karfen da yace kartayi ta shige bathroom din dake manne da dakin .

Wayyohhhyyy kadan ya rage deeni bai sume ba  sbd ganin yadda ta sauka da karfi .Ya tura hannushi 'cikin suma kanshi yana yamutsawa tare laso lip's dinshi Na kasa ,yana nan zaune tagabatar da sallar magriba da isha'i sannan ta Mike takarasa gabansa tashi muje ka kai ni gida  ........




MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
     💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO



Page 85


'Cikin wani irin shauki Na fitar hankali ya fixgota  .
ta fado saman fadadden kirjinsa me cike da yalwar gashi , hancinta ya sauka daidai inda yafi jin  kamshin turarensa  .
 Wanda tun sanda ta kabbarta sallah ya cire rigarsa da single dinsa.

  lumshe shanyayyun idanunta tayi  sbd dadin  kamshin turarensa data Shaka me sanyi   tada  sha'awar diya mace.
     Yawo yashigayi da laulausar hannunshi a sansar jikinta yana aika mata da sakwanni salonsa masu gigita mutun .
sosai yashiga  romancing dinta batayi yunkurin dakatar dashi ba sbd zuwa lokaci itama tana so da km  jin dadin irin abinda yake mata. fuskarta ya hade danashi ,idanunshi Na 'cikin kwaryar idanunta , hancinsa Na gogan nata bakinsa daf danata suna fuskantar junansu, sosai yake busa mata hucin numfashinsa a fuskart tare da cire mata hijab din jikinta ya ajiye gefe.

Gurin cire hijab din ma sai taba wasu wuraren dayasan tana jin dadi a duk sanda yayi hkn .
Taja ajiye zuciya da kyar ta sauke.
 " yawo  Yashigayi da harshensa kan lips dinta Na sama dana  kasa kafin Daga baya ya hade bakinsu guri daya yashiga tsotar bakin sai daya Sha bakinta son ranshi sannan ya sakarmata lips yana sake fesa mata huci numfashinsa mai zafi da kyar  ya iya   bude bakinsa Yace  fizgo mgn gida kike son ?

Jikinta a mace ta lumshe masa shanyayyun idanunta alamun eh .

baki son gidan nan ?

Nan ma idanunta ta sake lumshe masa Wanda suka gama canza launi tsabar fillings dake dawainiyya  a jikinta 

Yayi shr kawai tare da tsura mata rikitattun idanunsa  batare da yasan abinda zai sake ce mata ba.

a hankali ya birkito daita upside down suna fuskantar junansu, wani irin naunauyen ajiyar zuciya ya sauke sakamakon tudun nonuwanta daya tukare da  kirjinsa , wani irin yanayi ya tsinci kanshi ciki maramisaltuwa,bai sanda ya rungumeta tare da manneta da kirjinshi jin tudun nonuwanta ajikinshi ya kara rikitashi da rudashi 'cikin mutuwar jiki  ya kai bakinsa Yayi kissing din saman dukiyar fulaninta .

wani irin shock ta dinga ji  ajikinta.
 ta kauda fuskarta gefe   tsabar kunyarsa data ji ya saukar mata 'cikin lokaci guda .
ya dinga kallon jikin  yarinyar da a haife zai iya haifarta ,cike da natsuwa yake shashafa mata jiki da ruda mata   sansar jikinta.
 , so yake ya mantar daita komai dake 'cikin duniya gabadaya tare  da dasa tunaninsa 'cikin Brain dinta  , duk inda yataba ajikinta taushi  da santsin yake ji Wanda hkn ke sake birkita masa tunansa akanta .

Taushin fatar  jikinta kwata kwata ya bambamta da jikin ya'ya talakawa ,talakan ma  kmr mlm salisu .
 , ciki wata irin kasalliyar muryarsa me tattare da shauki , yakira complete name dinta na..bee..lah..........
Wanda bai sanda sunan ya fito Daga bakinsa..

 yadda taji yakira complete name dinta ne sake   yakashe mata jiki ahankali ta juyo fuskarta tare da maida shanyayyun idanunta 'cikin nasa tana kallon 'cikin kwaryar idanunshi da suke a rikice  tare da jin wani irin shock a sansar jikinta .
da mamaki da dinga kallonsa duk da tasan haka sunan nata yake Amman bata jin Wanda ya iya sarrafa harshensa gurin iya Kiran sunata ba tamkar yadda yakira din ba .

Abinda yashiga bata mamaki da al'ajabi daman yasan complete name dinta Amman kullun yake kiranta da ke......

meyyasa ...sai km yayi shr yana cigaba da kallonta tare son yin nazarin abinda zai ce ,dan baya son Yayi abinda zai kwabsawa kanshi .


Kusan minti biyu ya dauka yana nazarin abinda zai ce kafin Daga baya ya sake bude bakinsa .na..bee..lah..Ta lumshe masa  idanunta tana sauraronsa ,da matsuwar  son jin abinda yake son fada mata.

 meyyasa bazaki bari muyi zaman mu anan har zuwa sanda su first love zasu dawo ?

Tayi saurin girgirza masa kanta alamun bazata iya ba ,yayinda lokaci daya idanunta suka ciciko da hawaye shiiiiii ...Ya daura yatsansa daya kan bakinta ..kar ki sake ki Bari Hawayen su zubo tayi saurin maida kukan tana sakin ajiyar zuciya tare da kallon 'cikin idanunshi .

 Jikinsa a mace ya kamo lips dinsa na kasa yana ciccizawa  tare da  runtse rikitattun idanunusa yana fidda numfashi , ahankali  ya bude idanunshi Fess bisa beauty face dinta  yana dubanta .

meyasa kike son bani ciwo kai ne ?

Muryarta cike da  shagwaba da rauni  ta cunno masa tsukaken karamin bakinta dabaya gajiya da shansu tace me km nayi maka  yanzu?
 dan nace ka Kai Ni  gida  .Ya tsura mata idanunshi masu matukar kashe mata jiki yayinda hannuwanshi Suka ki tsayuwa guri daya ajikinta itama sosai take son kasancewa tare  dashi , gashi bai taba nuna mata alamun yana son saduwa daita ba iyakacinta dashi romancing dinta.

 ahankali yake cigaba  da sarrafa jikinta tare da matseta gam ajikinsa yana sakin numfashi bakinsa yakai 'cikin kunneta yana mata soucking ahankali yaji tana mikewa ajikinsa ya km Rungumeta tsam tsam yana lumshe rikitattun idanunsa tare da sakin murmushi domin ya lura tana matukar son wannan salon nasa.
 km take takebashi hadin Kai a duk sanda yake aika mata dashi .




'Cikin hk wayarsa ta dauki karar   sauti me dadi ya runtsen rikitattun idanunsa da kyar kana ya bude su yana sake kallon kwaryar idanunta Wanda zuwa lokaci tuni sansar jikinta sun sake sakewa da macewa da shaukinsa  sakamakon hannushi dake yawo ajikinta. ahankali ya Mike  tare daita ajikinshi ya zauna tare da zaunar Daita akan cinyarsa ya janyo wayar yana duba me kiransa da wannan lokaci ganin sunan dake yawo akan screen din wayar  ne Yasa shi hanzarta daukar Kiran hade da yin sallama da muryarsa data komai tamkar ta mashaya ...Yace mu wuni lafiya first love yana mai kamo hannu nablah 'cikin nasa yana murzawa Wanda hkn ke sake samun nasarar kashe ilahirin gabobin jikinta da aikawa ruhinta wani shauki Na daban.

 ,jin ya ambaci sunan umminsa yasa ta Mike cike da sanyi jiki domin bashi damar zantawa daita Yayi saurin kamota jikinshi  ya maidaita Inda ta tashi yana kallon kwaryar idanunta hade da sakar mata wata uwar harara .

Tsintar Kanta  tayi da kasa ramawa sbd yanayin shaukin datake ciki dan hk ta xuba masa shanyayyun idanunta tare da narke masa ajiki tana jin tamkar suka kasance hk har illa Masha Allah.

Can kuwa bangaren ummi amsa masa tayi da lfy son ,ya jikin nablah ?

Ya numfasa stil idanunsu Na 'sarke 'cikin juna ya kai bakinsa ya tsotse lip's dinta kana Yace da sauki first love .


Kirjin   nablah Yayi wani irin shock tare da matsanancin baguwa  da sauri sakamakon tuno da abinda doctor ta sanar mata a yammman yau...tunani tashigayi  yanzu idan Shima doctor din  tasanar masa da karyar 'cikin datayi mata

 yazatayi da rayuwarta?

 waza tace Yayi mata ciki?

Take zuciyarta shiga bugawa da karfin karfi tamkar ana buga mata guduma .
 atsorace ta dinga addu'ar akasan ranta Allah kada kasa  doctor dinan  tasanar masa da komai idan yakoma .

Dan ita bbu abinda zai sake maidaita wannan hospital din ,kallo kwayar idanunta yake sosai  yana kallon yadda gabadaya yanayin jikinta ya sauya tare da hango tarin tsoro da frigici dake  cikinsu .

Ummi ta numfasa tana sake tmbyesa me doctor tace yana damunta son?


Gsky first love  bata sanar min da takamaiman abinda yake damunta ba .
 ta dai ce min ,na dawo Amman oready nakirata nace mata tabari zuwa gobe da safe ,dan tsaya yin wani aiki  shiyasa ...


Ok ka maida hankali sosai  gurin kula da lfyr yarinya nan  dan Allah son  ka dinga bata duk wata  kulawar data dace.

DEENI Yayi  murmushi gefe bakin yana me kamo lips dinsa nakasa ya dan ciza sannan Yace  gsky first love kina ji da yarinyar da alamun ta sace miki zuciya  .

Dole ne DEENI "da"Na kowane, km ko bbu komai Ina jin yarinyar har 'cikin raina .
alright my first love Karki damu Ina bata duk kulawar  data da dan ma  yarinyar na da maseefar taurin kan tsiya har tasoma bani ciwon kai .

Hakuri zakayi DEENI kasan yarinya ce nablah dabatada dabara sai yadda akace daita.

 sannan gobe idan Allah yakaimu zamuje hospital da zeenat Ina bukatar a sake duba min lfyrta .

DEENI Yace Ok Allah Yasa adace, ummi tace Ameen tare da jin dadin abinda Yace .
sosai furucinsa Yayi mata dadi.
Km  har 'cikin ranta taji dadin  yadda ya nuna kulawarsa akan diyarta tayi tasamasa albarka da addu'ar Allah Ya albarkaceshi  da samun zuria masu albarka.

 ya amsa da Ameen first love Ina zeenat din take  yana cigaba da kallon yanayin nablah da tarin damuwar dake tattare daita ...gata ummi tayi saurin Mikawa zeenat wayar .

Zeenat Na karbar wayar ta fashe masa da kukan shagwaba .
muryarsa a dake Yace meyye hk km ?

 Daga karbar waya zaki soma da cikawa mu...sai km Yayi shr tare da canza salon mgnrsa Ok kuka ma zakiyiwa mutane sbd dadi Yayi miki yawa ,kina can   tare da fisrt lov kullun kina ganinta Ni kin barni nan da kewarki ko?

Wani irin dadi ne ya rufeta  tarasa Inda zata saka ranta dan jin dadin furuncinsa .
 muryarta cike sanyi dadi tace haba my hrt dole nayi kuka duk wunin yau fa banji muryarka ba gashi gabadaya numbers dinka sunki zuwa kmr Na mutu naji.

 Yace emmhu .tace Allah kuwa  da gaske nake tana sake shagwabe masa tamkar tana gabansa .

Meyye ya hanaki mutuwa?

  ta sauke naunauyen ajiye zuciya  haka ma zakace ko ?

Yace uhm to me kike son nace miki zeenat ... byn hk kece da wata irin mgn wai kmr ki mutu idan kin mutu ance miki zama zanyi hk. 

aurena zanyi .
dan hk gara ki zauna a duniya watakilla idan kina raye bazan samu damar  yi auren ba .  ya fadi hk yana kashewa nablah idanunshi tamkar itace zeenat din.

Wani sabon kuka ta fashe masa dashi Wanda da ji kasan Na shagwaba ne ummi kina jin my hrt ko addu'ar mutuwa yake min shi km yaje Yayi aurensa ...
ummi tayi murmushi irin nasu Na manya barshi bazaki mutu ba inshallahu mamana kuna nan  tare muddin rai har  ya'ya da jijikoku .

Murmushi  kawai DEENI sbd yana  jin abinda umminsa tace dan  handsfree ya maida wayar .

Bilhaki mgnr da DEENI Yayi  yata bata sosai duk da  abinda ummi tace mata bai hana cigaba kukanta ba .
 aiko take haushi ya kamashi  zuciyarsa tasoma  tsukewa  guri daya, ya  sake damkar hannu nablah dake 'cikin hannushi, ta saki kara mara sauti tare kayyyyyyyyyyyyy..


Ahankali ya dan sausauta rikon da Yayi mata yana cigaba da murza tafin hannunta 'cikin wani irin salo.

Sannan yakatsewa zeenat kukan datake ta hanyar ce mata Ok dan kinga first love Na daure miki gindi shine kike son rainawa kanki hankali.
  
 A kausashe yacigaba da mgnr ke wata irin  mace hk  me kishin jaraba dan ke kadai Allah ya haliceni ya karasa  fadar  hk yana furzar da wani huci me zafi har bisa fuskarta nablah    ta runtse idanunta gammm tana jin yadda  wani irin tutukin bakinciki ke tasoma tun daga kasan zuciyarta ....


Shr  yayi kawai    yana mamakin kishi irin Na zeenat yarasa wani irin maseefaffen  kishi gareta ,ita dai sai dai ta zauna ita kadai gashi ba iya daukarsa  take ,ya raya dare gabadaya daita  ba .
Amman  data ji zance zaiyi  aure duk zata bi ta rude ta dinga kuka.


Sosai take bashi hkr akan kada Yayi mata kishiya ita bata so... Yace is Ok a bar wannan zance  meyye labari yanzu.
 ya katseta ta hanyar cewa hk dan yasan  idan ba hk yayi mata baza barshi ya huta da wannan kukan nata mara dalili ba Wanda Daga karshe zai iya tada hankalin umminsa.

'Cikin sanyi muryarta may cike da kirsa tace nayi missing dinka irin sosai din nan Ina ji araina tamkar Na dawo gareki  dan banason abinda zai sani yin nisa da kai. gabadaya kewarka Na neman zautar dani ta karasa fadar hkn tana sake sakar masa wani kukan shagwabar is Ok nima nayi miss dinki to the ext.....'cikin wani jin haushi me tattare da takaicinsu ,nablah ta fizge hannuta 'cikin nasa Wanda yake ta aikin murzawa yana lumlumshe Idanu tare da Mikewa tsaye ta juya ahankali 'cikin sanyi jiki 

Bynta yabi da wani irin kallon mamaki   yakasa karasa  abinda yake son fada .ya dinga mamaki yarinyar ,dan tun sanda taji ya ambaci sunan zeenat ,ya lura da yanayinta ya canza .. 


To me hakan yake nufi ?

Kardai abinda yake tunani ke shirin faruwa koma yace ,yana kan faruwa,yarinyar tamu da  sonshi  kmr yadda ta tabbatar masa acikin baccin ta.

 ,ya tsura mata  rikitattun idanunsa yana kallonta ta bude fridge tare da daukar kwalin    holandia  data yi saura ta  bude  Tasoma sha tana sake jin wani karin haushi a kasan  ranta gabadaya ruhinta a jagule yake.

 ahankali ta sake Daga Zara zaran yatsun kafafunta ta nufi kan doguwar kujerar thrre tsar dake dakin ta zauna tana sakin numfashi tare da kauwarda idanunta gareshi Daga wayar da yake da bazar matarsa .....


Har lokacin idanun DEENI Na kanta.
 sosai ya tsura mata ido yana son sake nazarin abinda tayi .

Yanzu idan sonshi take meya kamata yayi ?

Ya aikawa zuciyarsa wannan tmbyr ,ka zauna daita kawai kucigaba da rayuwarku zuciyarsa ta amsa masa da hkn .

Take km wani Shashi na xuciyar tace masa kulll karka fara ka manta me aiki ce  km kaskantacciya mara galihu ce acikin talakawa ,talakan ma diyar mlm salisu me wanki hula ...take zuciyarsa tashiga shawagi acikin gangar jikinsa .
Wanda zuwa lokacin tuni nablah dake zaune ta Mike a gurin tayi kwancyarta tare da runtse shanyayyun idanunta ..

Zeenat kuwa jin shirunsa yayi yawa ne Yasa dinga cewa hello....hello....my hrt kana kan layi kuwa  da kyar ya iya bude bakinsa aqagauce Yace mata uhm Ina jinki. dan gabadaya hankalinsa da natsuwa baya gareta yana gurin nablah dake kwance  ta kamkame jikinta alamun sanyi take ji .ya saki wata naunauyen ajiye zuciya sannan Yace Ina jikin .
Nan dai  suka cigaba da hirarsu ta tsakanin miji da mata yayinda har lokacin  idanunshi nakan nablah ya tsura mata ido Daga karshe Yacewa zeenat  bacci yake ji yana bukatar hutu .
tace Ok my hrt gud night sweet dreams  love you my hrt ,Yace love you too yayi hanging din Kira  .

'Cikin sanyi jikin nan nashi ya  Mike tsaye  yasoma takawa ahankali zuwa Inda  take kwance   ahankali yakaraso ya tsugunna a Gabanta tare da kamo yatsun hannuta'cikin nasa yasoma  yamutsawa wani irin  abu me kama da shocking tasoma ji ajikina yana mata yawo Wanda takasa bambace komeye shi .Ta bude shanyayyun idanunta tana yatsina fuska alamun bata ji dadin hkn ba .
Kana ta sauke ajiyar zuciya me nauyi tare da lumshe idanunta ..

Ya tsura mata rikitattun idanunsa masu matukar kashe mata sansar jiki. Sannan  Yace meyasa kika dawo nan kika barni Ni ?

Mgnrsa ta dan bata mamaki Amman sai tayi shr  batare da tace masa  komai dan koma ta bude bakinta mgnrta bazata fito ba .

Yacigaba da kallon kwaryar idanunta yana sarrafa hannushi 'cikin nata Domin shi DEENI ma'abocin son wasa da tafin hannu ne akoda yaushe km yayi Saar samu  me irin tafin hannu dayake so ...
duk da taushin hannushi hkn bai hanashi   maseefar kashewa tafin  hannushi kudi gurin siyan mayuka masu saka taushin hannu .
'Cikin kwaryar idanunta yake kallo tare da cewa .

Kin fada tarkon sona ko?

 wani irin abu taji me nauyin gaske ya tsaya mata akirjinta tare  tokare mata zuciya ,ta Mike zaune da kyar tana ta nuna kirjinta da yatsanta, tana jin yadda zuciyarta tashiga harbawa da sauri da sauri Ni ..Na fada tarkon sonka?
 ta fadi hk  tana nuna kirjinta tare da maimaita abinda Yace ?
Ya dage mata girasa daya alamun hk abun yake .

Saboda zan fada tarkon sonka ?

Ya dage mata kafadunsa duka alamun Shima bai Sani ba .

Allah Ya tsareni da fadawa tarkon sonka DEENI ta  fadi  hkn tana may  hade ranta tamau....

Yayi murmushin nan nasa Wanda ke kara kawata fuskarshi kyawu kana Yace abinda baki sani ba yarinya kin fada tarkon sona kin yi zurfi ciki  har kin nutse . Na miki sambade bade acikin zuciyarki tamkar murjanin tausayi .

 Ta dinga kallon bakinsa da  kwaryar idanunshi da mamakinsa, ta ya zai yi mata wannan fassarar ?

Idan har ba kya sona meyesa kishina yayi tasiri ajikinki har ya  fallasa sirrin  ke boye cikin zuciyarki?

Inda kasan abinda ke'cikin zuciyarta DEENI .. da bakace Na fada tarkon sonka ba. 

 uhm wani irin murmushi ne yaso kufce masa  jin ta ambaci sunansa kai tsaye batare da darrrrr ba ,takan birgeshi gurin rashin jin tsoronta ...

Ya janyo hannuta duka tare da mikar daita tsaye ya mannata da bagon dakin ya hadeta da fadadden kirjinshi cike da shauki yakai bakinsa saitin wuyana yana kissing dinta taji wani irin zummmm Na shocking me hade da baybireting .
yayinda da dinga jin gabobin jikinsa Na sakewa ahankAli  ya lumshe rikitattun idanunshi 'cikin fizgar numfashi Yace 

,ki yarda kina sona yarinya . 

Jikin a mace itama tace Idan har zan kasance 'cikin jerin masoyanka DEENI... hakika banyiwa kaina adallaci ba ,nifa Banga abin so atare da k...da sauri Ya cafki bakinta da karfi.. yana musu wani irin mugun  tsotsa 'cikin zafi zafi ..
 "sai daya ladabtar da bakin dake masa tsiya sannan ya zare bakinsa yana me sakin numfashi hade da mai da idanunshi 'cikin nata .

Shr kawai tayi tare da tsareshi da shanyayyun idanunta  tana kallonsa takasa ce masa komai  wasu hawaye ne masu zafi da ciwo suka shiga bin kuncinta . 

Muryarsa a sarke Yace shiiiiii da kin adana kukanki watakilla zai miki amfani a gaba ..

meyasa kake min irin haka ne uhm ta fadi hk a shagwabe tana turo masa dan karamin tsukeken bakinta. 
da alamun kina bukatar Na sake feeding dinki ko?
 yasoma kokari sake cafko lips dinta tayi saurin tura lip's dinta  'cikin bakinta tana dubansa.. rungumeta ya sake yi tsam ajikinshi 'cikin wani irin yanayi Na shauki da mugun jin bacci ta riko tsintsiyar hannushi Domin duba lokaci 12 ta gota da Yan mintina dan haka ta sakawa ranta danganar zuwa gida dan bazataso aganta dashi da irin wannan lokacin.

 'Cikin idanunta yake kallo har lokacin yace ..Kya..lli kyalli  yadda soyayyata  ke daskare 'cikin kwaryar idanunki da  dawainiyya da ruhinki Amman dayake dakinkiya ce ke kin kasa ganewa  yana gama fadar hk bai bata damar cewa komai ba Yace muje ki kwanta dare Yayi , yasoma tafiya daita tana manne ajikinshi  har kan bed Ya kwantar daita tare da lullubeta da husky blanket kana ya Kai bakinshi 'cikin kunneta Yace ki taimaki kanki  ki cire kishin matata acikin zuciyarki Domin tazarta ki a komai Na rayuwa ...sannan ya juya ahankali ya rage mata karfin AC dakin sannan ya fice  Daga dakin .

Byn fitar shi Daga dakin  ,hankalinta yayi mugun tashi tarasa Inda zata yiwa mgnrsa mazauninta a zuciyarta  ..
to me yake nufi ne daita?  kodan yaga tana sakar masa jikinta yana yadda yaga dama shine zai dauka ta kamu da sonshi ne ?
 da kyar tasamu ta Mike cike da mayyen bacci taje ta kulle kofar tare da zare key  tazo ta kwanta tana cigaba da tunanin abubuwan da suke faruwa atsakaninsu, wani irin bacci ne yakawo mata farmaki from no where  ...


Abinda nablah bata sani ba lokacin da DEENI ya dawo dakin  tana bacci. yayi mata amfani da spanin night Na bacci 'cikin hollandia yogurt din datasha, Wanda tun sanda yasoma zargin tana da shigar ciki yake mata amfani dashi batare da saninta ba..

DEENI bai dawo dakin ba sai guraren 2 na dare lokacin da na'u:rarsa ta hasko masa ita 'cikin duniyar bacci ....




Kwance suke akan gado hannuwanshi duka a saman nonuwanta ba kaya gabadaya ajikinshi cike da natsuwa ya tsurawa surar mata . idanunshi yana kallon kyakywar surar jikinta may matukar daukar hankalin da taushi  .
Ahankali yashiga murza nonuwanta kafin Daga baya ya daura bakinsa kan nipply dinta yana musu wani irin tsutsa yayinda ita km bata 'cikin haiyacinta sai bashi hadin Kai take tare da turo masa dukiyar fulaninta da kyau ta yadda zai ji dadin sarrafasu sosai gabadaya hankalinsa baya tare dashi burinsa da muradinsa ya isa Inda yake son shiga cike shauki yasoma having sex daita ba shi ya barta ba har sai daya Sami jin dadin dayake bukatar Daga gareta ,tare da   gamsu iya gumsuwa sannan ya zare joystick dinsa Daga kasanta ya rungumeta tsam ajikinshi yana cigaba da wasa da kirjinta .



Washegari DEENI yashigo dakin datake .

 sanye 'cikin wasu hadadun suit light blue sunyi maseefar yimasa kyau "kyawun haibarsa da nagartaccen annurin fuskar nan tashi Na nan bbu abinda ya canza agareshi ,sai ma wani kyawun da kwarjin dataga ya sake yi mata ba kmr jiya ba .
  * fuskar nan tashi a daure tamau tamkar yadda tasoma ganinsa tun  farkon zuwanta gidansa matsayin me aiki  .

Kallon ido cikin ido suke yiwa junansu , kowannesu sai da tsigar jikinsa ya tashi nablah tayi sauri janye shanyayyun idanunta Daga kallon rikitattun nasa ido, tun bai km mata wata fassara ba ..

Bakinta yayi mata nauyi tamarasa me yakamata ta farayi ,gaishe da shi zatayi ko kwalleshi zatayi yacigaba da tsayuwarsa ?

Mgnrsa ce takatse mata tunani da muryarsa me saka mara jin mgn natsuwa ,ta daki dodon kunneta Gabanta yabada darammmm yayinda zuciyarta tashiga harbawa da sauri... ta dago shanyayyun fuskarta tana sake kallonsa .

Zaman me kike yiwa mutane dabazaki shirya ba alhalin kinsa kina da zuwa karbar sakamakon...

Zuciyarta tacigaba  harbawa da sauri da sauri jin abinda yace .

Bakin Na rawa muryarta da in ..inna..tace   wani sakamakon  zanje karba ?

Yace bansani ba minti biyu nabaki ki shirya ..

Wlh Ni bbu wani hospital da zanje garama kayi tafiyarka Inda zaka ya fiyye maka alkhari .

Ke banson iskanci ko sa,an wasanki ne da Ina mgn kina maida min martani  ban   darajar mahaifiyata ke har isa Na tsaya  Ina bata lokacin akanki ,taimaka miki kawai za'ayi badan kinsa ba . Ta dinga kallonsa tana mamakin wani irin mutun ce shi da canza yanayi baya mishi wahala yanzun nan zaka ganshi tamkar mutumin kirki anjima zakaga ya sauya ..

Miryarta 'Cike da in inna ..tace to..to.ni Na gode  bana son taimakon naku  ko dole sai an taimaka min ..bata ankara ba taji ya buge mata bakinta , hannu tasaka da sauri ta dafe bakin nata saboda zafin dataji ya ratsata fiyye da tunanin me karatu kafin kace me tuni hawaye sun fara gudu bisa kuncinta.

Yaja siririn tsaki yana hararrata sannan ya raba ta gefen ta zai wuce kana Yace minti biyu kacal nabaki ki shirya ki sameni a parlour ..

Muryarta can kasa kasa ta yadda tasan ba zaiji ba tace wlh Allah Ya isa bazanta taba yafe maka ba ....tsayawa yayi cak Daga tafiyar dayake dan jin abinda tace hakika kunnenshi bai ji masa karya ba.
 Allah Ya isa tayi masa DEENI ya fada yana juyowa ....sai dai Ina..tuni tayi nisa tashige bathroom .. ahankali yakaraso yana murder handle din kofar yajita gammm.. Yace zamu  muhade ne zaki gane bakida kunya  yarinyar tana jin motsin tafiyarsa tayi saurin bude kofar tana kallon bayansa kmr ance ya juyo suka hada ido tamasa gwalo da harshenta tare da saka hannuta bisa idanunta ..

Ta sake koma 'cikin bathroom din da sauri  ta kulle ..

Samun kansa yayi da sakin murmushi tunda yake a rayuwarsa bai taba haduwa da wawiya yarinyar irinta ba ,ya sake sakin wani murmushi Wanda shi kansa baima San yanayi ba ..

Nablah naganin ya fita daga dakin ta fito ta shirya kanta  'cikin wata doguwar rigar Wanda DEENI ne ya siyo mata shi a shopping sanda ya dauko Daga gida .
sosai tayi kyau ta dauki daya Daga 'cikin turarensa ta fashe ilahirin jikinta dashi sannan ta saukowa jikinta a sanyaye cike da jin tsoron abinda zai biyo baya ..

zaune ta ganshi ya harde a kan kujera tare da tsurawa hanyar  step idanunsa.
 tuni gabanta nablah yashiga faduwa da kyar ta iya karasa saukowa hannuta dafe da kirjinta tana sakin  numfashi ga wani azababen faduwar gaba daya tasomata .
  bai dauke rikitattun idanunsa akanta ba har sanda takarada saukowa hawaye ke neman kwace mata ahankali tayi saurin maidasu sbd irin kallon dayake aikomata dashi.

 oh my  God bazanyi kuka ba nablah kada kiyi kuka ki daure idan DEENI yaga hawayenki zai rainiki ,hawaye kadan ya fito daga idanunta  tasa yatsanta tare da dauke Hawayen  ...sai data daidai kanta sannan taje  Inda yake zaune ..

Xumbur DEENI ya Mike zaune yana dubanta karki sake karawa kanki laifi ta hanyar bata min lokacin ..wuce muje ya nuna mata hanya da hannunshi hk ta shige gaba tasoma tafiya tamkar wace kwai ya fashewa aciki shi km  yana biye daita abaya daidai bakin Glass din kofar fita.
 taja ta tsaya sbd batasan yadda za'tayi ba  yakaraso tare da daura yatsun hannushi saman glass din  kofar.
 ta bude ...suka fice ta maida kanta ta rufe ...


Tunda motar DEENI ta kunna kai 'cikin harabar hospital din nablah tasoma zare ido tana jin yadda  zuciyarta ke tsalle tamkar zata fasa kirjinta ta fito DEENI ne yasoma fitowa tare  da bude mata  motar da kansa ..



Zaune suke a gaba doctor saira DEENI ya sauraron bayanin doctor wani irin yanayi mara misaltuwa ya tsinci kanshi  ciki abubuwa masu yawa  da mahimmanci sun same shi a arayuwa, Amman bai kai wannan matsayi da mahimmanci ba .
Yama rasa takamaiman me zai yi ahalin dayake ciki.
 , farinciki ganin wannan rana ko kuma kukan murna ?
Wanne ya dace a gareshi a irin wannan ranar me tattare da farinciki ?
 rike yake  da farar takarda a hannusa  har lokacin yana karanta abinda ke ji . 

ahankali ya maida idanunshi kan nablah dake zaune tamkar andasa wacce gabadaya jikinta  kirrrrrrma yake . tun sanda  doctor tasoma mgn yayi shr tare da tsura mata rikitattun idanunsa dan son ganin wani irin reaction zatayi.

Murya doctor saira ta daki dodon kunneta Gabanta yabada darammmm tsabar frigice datake ciki.
 Ki karbi  takardar kikaranta abinda kika kasa yarda dashi tun jiya kennan ciki gareki har tsawon wata hudu...

Cike da tashin hankali DEENI ya riko hannun tare da  saka  mata farar takardar a tafin hannunta ,jikinta Na rawa rawa tasoma karanta abinda ke jiki . 'Cikin tuttukin bakinciki da tashin hankali hade zafin nama ta zabura zata Mike tsaye DEENI ya riko hannun tare maidaita da sauri yana cewa wani irin iskanci ne hk ?

Kada ka sake dangantani da wannan kalmar dan Ni ba Yar iska bace Ga katuwar Yar iska nan a gabanka kana kallo tana min sharri .tasoma yayyaga result din ta sake zabura ta Mike tsaye tana me watsawa doctor saira takardar ajikinta tana huci ...

 doctor saira ta dinga kallon piece din takardar dake watse a  jikinta tana kallon nablah tare da mamaki yarinyar ...

Yes .... wallahi wallahi wallahi idan kika km cewa ciki gareni sai Na tsinka miki mari , ko kwalkwaluwarki zata dawo jikinki ..Tana me  nunata da ,dan yatsanta  ke ba aikin likita  yakamaceki ba kwasar bolar titi shi yafi dacewa dake ..

 haba kunjimin  mata da jaraba tsiya  kin bi kin dameni da zance wani  ciki...ciki  gareni alhalin ba hakane bane .

Idan ma har ciki gareni sai dai ubanki ne Yayi min.
Doctor saira ta Mike tsaye  a fusace tana duban nablah  a xuciye ta Ciro hannunta zata tsinkawa  nablah wani mahaukacin  mari ..zaraf DEENI ya riko hannunta tare da cewa kar ki sake doctor.....


Barta ...DEENI barta ta mareni a tunaninki idan kike mareni bazan rama bane ko me?
 
 shiiiiii haba duk kin bi kin cikawa mutane kunne da hayaniyar banza  .. wannan ai haukan karya kike yi   da borin kunya..Ya karasa fadar hkn yana sakarwa doctor saira hannu .

Idan ita doctor tayi miki karya result din shim a karya ne Yayi miki...?

Doctor saira da ranta yaga baci a fusace tace Ka dawo daita nan da wata biyu ta ganewa kanta abinda ke cikinta ko zata dawo 'cikin Hankalinta stupid girl kawai .. kina Yar  yarinyar ki dake  kinsa yadda akeyin 'cikin idan banda ke dakikiya ce ai yakamata kinsa ciki gareki  when last da kikaga period dinki ?


Wani zufa ne ke karyawo nablah takoina ajikinta tayi shr tana tunani rabonta da ganin period dinta .
A atsorace jikinta a sanyaye  ta dagawa doctor saira yatsunta uku alamun wata uku kennan.

 Ok wannan shine step Na farko da mace zata gane tana da shigar ciki Amman dayake mahaukaciya  ce ke kika kasa gane hkn ...

Jiikin nablah yashiga kirrrrrrma  har da karkarwa takoma ta jingina da jikin bango office  tana duban daya byn daya kallon DEENI da doctor take tamkar wasu halitta Na daban da bata ganin irinsu ba.

 sosai jikinta ke cigaba  kirrrrrrma nan ko doctor saira tasamu abinyi tashiga xuba zance tana sakin maganganu marasa dadi Ga nablal gara tun lokaci bai kure miki ba kije ki nemo Wanda yayi miki ciki ...ZUCIYAR nablah ta cika da damuwa ta tsaya cak...Ta daina aiki Na wuncin gadi kafin Daga baya tacigaba da bugawa da sauri da sauri ji take maganganu doctor saira ba a iya kunneta kadai suka tsaya ba har 'cikin zuciyarta take jin komai sbd dacin kalmar doctor gareta..

 kuka ta saki mai cin rai da ban tausayi muryarta cike da kuka da tashin hankali ta shiga furta kalmar  inna lillahi wa inna ilaihi rajiun meke shirin faruwa dani ?

 Yayinda doctor saira tacigaba da surutai kusan yadda wasu doctor suke ballanantana idan  sunji ciki bbu aure ..

ba yanzu ne  zakiyi kuka ba sai ma kin rasa Wanda zai karbi wannan  shegen 'cikin n.....wata irin razananniyar tsawa DEENI ya bugawa doctor yana aika mata da wani irin mugun kallon me tattare da tsana Wanda yasa take tashiga hankalinta  ..a hassale yasoma mgn 'cikin tashin hankali meyesa wasu Daga 'cikin likitoci basu da imani ne ?

 Dame kike son taji ?

Wlh idan wani abu yasameta sakamakon wannan zantuttukan naki marasa ma'ana, bazan barki ba .. 
 
Tsaye nablah take ajikin bagon tana fezgo numfashi  da kyar tamkar me cutar Asma  tana fesarwa tare da  duban DEENi rasa Inda zata nufa ne yasa ta nufo Inda DEENi ke tsaye yana dubanta 
'Cike da  tashin hankali da frigice ta matso kusa dashi  sosai  ta riko tafin hannushi 'cikin nata .
 tana kallon  fuskarshi takasa mgn  so take ya karyata mata abinda taji doctor tace yazama ba  gsky bane karya ne ko result din banata bane .

 kallon kwaryar idanunta yake yana mai jin tsananin tausayinta har 'cikin ransa gabadaya duniya ta cukude masa waje daya  bai taba sanin hk tashin hankali irin wannan dayake ciki yake da muni ba .

Sosai take kuka har daNa fitar hankali ita kanta bai taba  tunanin rayuwarta  zata  kasance 'cikin wannan maseefa  me cike da rudani ba  rawar da jikinta keyi yasa .. kafafunta suka Gaza daukarta tayi kasa luuuuuuuu DEENI Yayi saurin tarota ta fada jikinsa ya rungumeta tsma  ajikinshi gabadaya halin  tashin hankali daya ganta ciki yasa shi mantawa ko waye shi da km Inda yake  .
can km ta fexge  jikinta Daga nashi da iyakacin karfinta .

 tayi zaman dirshan a kasa tana tattara kan  takardar data yayyaga Domin sake karanta abinda ke jiki .. Amman Ina aikin gama yarigada yagama ..ba dama .
 dan bbu komai dazata iya Gani ballanantana har  takaranta .

tashiga kuka tana sambatu iri waye yayi  min hk ?

Wani mara imani ne da tausayin ,yayi min ciki ?

Wani la'ananne  Wanda bazai taba gama wa da duniya lfy ba Yayi min wannan cin zarafin ?

Kuka take tana buga kasa da tafin hannunta tamkar wata zautacciya.

 ba DEENi dake ake tsinewa ba hatta doctor saira sai data dawo tana tausayawa yarinyar ganin bil hakkin batasan da zaman 'cikin jikinta ba ..

DEENi yasoma  matsowa zuwa Inda take zaune tana kukanta me cin rai daban tausayi tayi sauri dakatar dashi kar ka motso Inda nake tasoma ja da baya  tamkar taga wani abun gudu Bai saurareta ba yacigaba da binta ya fixgota tare da Rungumeta   ajikinsa yana fexgar numfashi ...
 ,




MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO




Page 86


Runtse idanunta tayi gammm..... wasu zafafan hawaye Na tsiyaya akan kuncinta  karo Na farko data ji wata mummunar qiyayyar wanda yayi mata wannan aika aikan ya shiga zuciyarta daram ya zauna  tare da huda duk wasu gabobi da jijiyon dake aiki acikin a sansar  aikinta.
 ,koda kuwa ba halitar bil Adama bane ,wato aljani .. kuka take sosai har dana fitar hankali 


Kokarin zamewa take daga gangar jikinsa duk da yadda take jin kanta ajikinshi amman takasa raba kanta dashi  dan sake rungumeta deeni yayi tsam ajikinshi yana fidda numfashin ,'cikin wani irin matsanancin kuka tafara mgn da muryarta da soma dashewa ni ka sakar min jiki  ...

kabarni nace ...

Kabarni  Naji da maseefar data sameni....

 Ni nablah ke dauke da 'cikin  shege yau ...  DEENI yashiga girgirza   mata kanshi batare dayasan ya aikata hkn ba   ... 

Kana jin abinda doctor tace  ciki gareni fa har Na tsawon wata hudu amman kake rungume dani ajikinka  ...takarasa fadar hkn  tare da fashewa da wani sabon kuka me cike da cin rai da girgirza zuciyar ma'aboci sauraro...

 ahankali DEENI ya sausauta rungumar da Yayi mata ajikinshi yayinda jikinta ya sake daukar kirrrrrrma  sun kusan minti ashirin  a haka , kafin daga baya  ya dagota cike da kulawa ya tsura mata rikitattun idanunsa ,yana kallonta. da kallon yanayin tashin hankali datake ciki .

,rasa yadda zaiyi da rayuwarsa ,yasashi  cigaba da kallon cikin kwaryar idanunta kawai.s sannan ya hadeye abinda yaji ya tsaya masa a makoshinsa .

yayinda doctor saira ke tsaye tana kallonsu tamkar wasu jaruman shirin  fillm .gabadaya al'amarin Nasu ya zauta hankalinta tare da girmama tunanita .
  "Barinma Yadda taga deeni ya rude da gigicewa akan yarinyar ko shine Wanda  Yayi mata 'cikin wa tunaninta iyakacin abinda zai yi kennan..
 
  Ahankali yacigaba da kallon yadda   kukan ke galabaitar daita .
  "tayi mugun fita haiyacinta.
Ahankali  yasa hannushi ya kamo tafin  hannuta 'cikin nashi  yana shafawa da baya hannushi ahankali  'cikin sarkewar murya yakira sunanta da sanyyayiyar muryasa .
 da kyar ta bude shanyayyun idanunta ta xubasu  'cikin nashi batare data amsa masa ba.

 ,Ya lura gabadaya jikinta a sanyaye yake ko dan yatsanta bata iya motsawa,kokarin son dagota yayi ta zame jikinta daga gareshi..

 kabarni DEENI bazan iya tashi ba.... ta sake  tsananta kukanta  me tsuma zuciya .

 Muryarta a sanyaye ta dinga furta kalmar...wayyohhhyyy Allahna.
.

 wayyohhhyyy Na shiga uku  ..waye  Wanda yayi min wannan cikin da bai  kasheni  gabadaya Na huta  daganin wannan ranar me tattare da bakin ciki rayuwa ba?
  ... wayyo Ni nablah me zancewa mahaifina   dayace kada nazo aikatau ..?

Me zancewa   yan'uwana da suka tattara  dukkan wata  yardarsu da amanarsu gareni" tare da amincewa dani   ,?


 Wayoyyy wayyyyyoo Ni nablah wazan ce yayi min ciki......? Kuka take hade da sambatu iri iri .

,tausayinta ya sake kama doctor saira ya mamaye zuciyata sosai   har batasan sanda hawayen tausayin yarinyar yashiga  tsiyayo mata ba .
   , ahankali ta zare dan siririn medical glass din dake manne da fararen idanunta  ta goge Hawayen dake tsiyayo mata tare da maida medical glass dinta tana cigaba da kallonsu , ...


 Mikewa nablah tayi da kyar tana layi... yayinda gafe daya km  tasoma ganin  juwa juya.
   batare data juyo ta hankalta da irin kallon tausayin  da doctor saira ke mata  ba.
  " ta fara tafiya cike da damuwa da rudanin rayuwa....

 DEENI ya zabura ya Mike tsaye  ya biyo bayanta da sauri  yana Kiran sunanta tare da kokarin dawo daita amman taki  sauraronsa ,sai ma fizge jikinta datayi  daga nashi  tacigaba da "Daga kafafunta da kyar ..

 tafiya daya biyu zuwa uku tayi DEENI yayi nasarar sake  damkota gareshi  Ina zaki  a hk...?


Ki natsu man musan abinda yakamata a yi duk wannan kukan naki  bashi ba sulotion atare dake .....

zubewa tayi ajikinsa tare da sakin wani irin gigitaccen kuka.
  ahankali tasa hannuta ta  dafe  daidai tsaitin zuciyarta  datake jin yana mata zafi  tamkar zata tarwatse..
"   ta manne  ajikinshi tana sakin numfashi da kyar tare da lumshe shanyayyun idanunta hawayenta Na tsananta zubowa, yayinda  zuciyarta ke dada karyewa sbd mummunar halin data tsinci kanta ciki ..


 Ahankali ta bude shanyayyun idanunta data  lumshe ,tasoma ganin dakin Na jujjuyawa daita ...juwa take Gani sosai Domin zuwa lokacin bata ganin komai dake 'cikin dakin hatta   bakin dake cikin idanunta yasoma yin sama da kasa alamun juyewa .

DEENI ya  dake rungume daita a jikinshi yana kallon yadda idanunta ke son kakkafewa Yayi saurin yin kasa daita  , kafin ya ankare tuni  ta saki wata irin naunauyen ajiyar zuciya me karfi gaske .

 Yayi saurin saka hannunshi duka  yana jijiga fuskarta da iyakacin katfinsa  tare da Kiran sunata a rude  na..bee..lah.. na..bee..lah  dan girman Allah  Kada ki min   Haka please.... ki natsu musan abin yi tukun  yana cigaba da girgirzata  Can yaji gabadaya takarasa sakewa ajikinshi .....ya tsayawa  cak ..... yana dubanta da rikitattun idanunsa....

Gani Yayi bata numfashi ya dago  fuskarta da sauri yana dubanta sannan a rude  yasa byn hannushi a hancinta .

Amman  kwata kwata bai ji wata alamun 
 numfashi a atare daita ba .

'Cikin wani irin tashin hankali da matsanancin  fargaba ya Mike tsaye daita.
Yayinda , jikinshi ya dauki  wani  rawa yana Kiran sunnan doctor .......

 kai tsaye kan dan madaidaicin gadon marasa lfy ya nufa  ya kwantar daita yana sake Kiran sunan  Doctor.

 ,yayinda doctor saira itama  tazagayo daga inda take tsaye.
 da  mugun saurinta  tare da  kallon abin mamaki yadda DEENI ke sake ya rudewa akan wannan  yarinyar dabata gama Sanin  kowacece gareshi ba .

 da dan hanzarinta takaraso inda nablah ke kwance tamkar wata matacciyar gawa dan bbu inda ke motsi a sansar jikinta..

Cike da natsuwa doctor saira  tasoma dubata  suma tayi doctor saira  ta fadi hk tana duban Inda  DEENI ke tsaye  rike  da hannun nablah yana mammatsawa ko zata dawo haiyacinta..

suma ... DEENI ya furta hkn da karfi jikinshi Na sake daukar  rawa duk jikinshi bbu inda baya tsatsafowa da ruwa gumi tsabar tension din dake zariya a gabobin jikinsa.

 ,Ok please doctor  taimaka min  kibata taimakon gaugauta please.

Abinda nake kokarin  son yi kennan ..

DEENI ya saki yatsun Hannu nablah  da kyar .

 ya shiga zariya acikin makeken  office din yana furta duk wata addu'a dayasani Dan neman sausauci a gurin Allah.

 da taimakon Allah dana doctor saira aka samu  numfashi nablah  ya dawo daidai yasoma sauka ahankali ..

 doctor saira ta sauke ajiyar zuciya ganin numfashin nablah ya dawo daidai ,shima DEENI sai lokacin hankalinsa ya dan kwanta ..

Doctor tace muje mr DEENI Ina son magana da kai, ya gyada mata kanshi kawai batare yace mata komai ba sai ma  zuwa yayi ya  zauna kan kujera yana furzar da huci me gauraye da tashin hankali.

Doctor saira   ta zagaya ta zauna tana dubansa Na wasu Yan dakiku sannan ta saki numfashi kana tace .
  "yanzu Mr DEENI yakake ganin za'a bulowa Lamarin  yarinyar, kaga dai yadda ta daga  hankalinta akan 'cikin jikinta ?

 Jikinsa a matukar sanyaye yayinda gabadaya yanayinsa ya sauya 'cikin lokaci daya da kyar ya iya bude bakinsa gurin cewa ki barni daita kawai   zansan yadda zanyi handover din koma ta yadda  komai zaizo da sauki .

Wlh yarinyar tayi matukar tabani tausayi sosai yanzu kowaye mutumin da Yayi mata 'cikin ?

Nima abinda nake son sani kennan DEENI yabata amsa da hkn.

A gsky idan ba,zaka damu ba zanso nashiga 'cikin lamarin binciken Wanda Yayi mata 'cikin jikinta ...Wannan ba damuwarki bane ba km hurunmin ki bane  da son sani Wanda Yayi mata ciki DEENI ya katseta ta hanyar ce mata   hk ...

A dan kausashe yacigaba da kaina zan nemo duk Wanda Yayi mata hkn sannan Na zartar da hukuncina akansa .. 

Ok hk ma Yayi 
  Amman  kasoma da rarrashin ita yarinyar  firstly  ko zata tuna  Wanda Yayi mata haka  kafin   ka zartar da  komai.

Yace uhm alamun yaji ....

Cike da natsuwa Ta tsura masa ido kawai  tana sake dubansa da nazarinsa sosai  kana tace dan Allah in maka wata tambaya Inda bazaka damu ba ....

Ya dago rikitattun idanunsa ya zuba 'cikin nata kana ya sake ce mata uhmmmm...

Ina son sanin matsayin yarinyar nan a gurinka? ..Yayi tsaida da ranshi tare da yin  shr yana nazarin abinda zai ,daga karshe da yace mata cousin's muke daita . Ok shiyasa naga duk hankalinka ya tashi to Allah kiyaye gaba .. doctor saira nagama fadar hk  ta Mike tsaye tana gyara farar rigar jikinta ta nufi kofar fita   Domin son  zuwa duba peticent dinta  ..



  Kusan awa daya da fitar doctor saira sannan  nablah   ta farka ... da wani matsanancin  kuka har da shesheka deeni dake tsaye akanta ya matso sosai kusa daita ..yana shafa sumar dake baje a kanta.
Ahankali  ya dinga jero mata  sunnu babu kwaukwautawa.
 , shr kawai tayi tana kukanta batare datace masa komai ba.

 Yasa hannunshi ya dagota tare da jinginar daita .sannan ya zauna kusa daita ganin yadda ranta ke a jagule da bacin ran halin datake ciki.
 yasashi  Mikewa  tsaye 'cikin tsanyi jiki Ya nufi dan karamin fridge din doctor saira ya dauko ruwa mai tsanyi ya zuba mata a cup ya kara mata cup din a daidai lip's dinta, yashiga bata ruwan da kanshi .

Sai dai kadan Tasha ruwan ta cire bakin daga cup din tare da jan naunauyen ajiyar zuciya.. DEENI ya ajiye cup din a gefe daya , ya tsura mata idanunshi yana kallonta ji yake tamkar ya rungume ajikinshi ya rarrashita ,hk yaji ..'cikin muryarsa  kasa kasa yakira sunanta tare ,
 Da kamo  tafin hannuta 'cikin nashi yana shafa byn hanunta da nashi hannun  ahankali ..
bata amsa masa ba ,sai numfashi da take saki akai akai  .

 muryasa a kasalance ya sake Kiran sunanta nabeelah kallonsa tayi da shanyayyun idanunta.
 ido cikin ido suke kallon junansu , gabanta yashiga  faduwa da sauri   Wanda Shima sai dayaji  hkn atare dashi ..

wai garin Yaya hk ta faru dake ne ?

Shr tayi bbu amsa dan  gabadaya wata irin kunyarsa ce ta rufeta ta kasa cewa komai sai kallon 'cikin idanunshi da take ..sai da suka dauki sama da minti goma a hakan suna kallon juna ko wannensu ya kasa dauke idanunshi daga kallon dan uwansa , km kowannesu da abinda zuciyarsa ke sakawa ...


 DEENI ne Yayi karfin halin janye idanunshi daga 'cikin nata kana  yace tmbyrki fa nakeyi ?

Da kyar  Ta iya bude bakinta Wanda Yayi mata nauyi  Ta dan  turo tsukakken  karamin bakinta 'cikin wata irin  murya Na Wanda yaci kuka ya koshi tace wlh Allah bansan ya'akayi hk ta faru dani ba ,  takarasa  fadir hk wasu siraren hawaye nabin gefen idanunta daya tare da sunkuyar da kanta kasa .

,dariya taso  subuce masa Yayi saurin dannewa.. ai kuwa kiyi gaugawa sanin yadda akayi kikayi ciki .Ko km tuna  Wanda Yayi miki ..

Ta dago da sauri tana dubansa ta km fashewa da wani gigitaccen  kuka Ni wlh Allah bansan inda zan nemo Wanda Yayi min ciki nan ba tana  fadar hkn ta km maida kanta ta sunkuyar .

 ...Ya km danne dariyarsa a karo Na biyu , to yanzu ya za'a yi kennan da 'cikin jikinki ? 

Tayi shr  kawai tana tunanin yadda zatayi da 'cikin jikinta can km  wani tunani yazo mata.. kanta a sunkuye tayi saurin cewa zansha fiya fiya  kawai .ko zan rasa raina gara Na rabu da abinda ke cikina akan Na haifeshi   .take gabansa yashaga faduwa yana girgirza mata kanshi ..

Ki kashe kanki kike nufi da abinda ke 'cikin ?

Ta daga masa kanta batare da ta dago ba .

 ,kinsa hukuncin Wanda ya kashe kanshi da gangan, ballanantana ke dake dauke da   wani ran ajikinki ..

'Cikin kuka  tace eh nasani  amman Na zabi mutuwa dana haifi dan dake 'cikin  cikina wasu Hawayen suka sake sulalo mata tashiga kuka sosai ...


   Ok kinaji yanzu ...ki natsu ki bar kukan nan hk . Sannan kibar komai a hannuna , ki Bari zan yiwa doctor bayani ansan yadda za'a yi da 'cikin idan ma takama a zubar da 'cikin  sai ayi hk  da ayi asarar rai biyu gara arasa 'cikin tunda shi bawani girma Yayi ba  Ni zan taimaka miki ,

 nablah najin hk tayi tsai da kukanta  cak... tana shasheka ahankali ahankali tare dagowa.
 ta xuba masa shanyayyun idanunta da suka gama canza launi tsabar frigici da tashin  hankali datake ciki maramisltuwa ..




MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO




Page 87



Hannuwanshi duka ta damko  'cikin nata  sosai ' tana sakin wani sabon kuka me cin rai tare da cewa idan kuwa kayi min hk deeni bansan irin farinciki da zanyi ba arayuwata  ,jikinta har rawa yake gurin fadar hk tacigaba mgn rabuwa da wannan 'cikin shine muradina a halin yanzu. Ni kaina wlh sai yanzu Na tabbatar da 'cikin jikina km duk hanyar da zanbi gurin salwantar dashi wlh zanbi tashiga jijiga hannushi dake 'cikin nashi Tana wani irin kuka me cike daban tausayi . 

 Jin abinda tace yasa gabadaya  gumi yasoma tsatsafowa ajikinshi takoina  tsabar tashin hankali da tsinci kanshi ciki .
,  dan ko numfashi ma da kyar ya dinga fitarwa ahankali ahankali yana kallon  'cikin idanunta abinda ya dade  shekara da shekaru yana nema shine yanzu Allah Ya amsa addu'ar sa yabashi ake kokarin  , za'a zubar ......
  .da kyar yasamu ya tattaro dan abinda yake son ce mata .


Karki damu tunda har  nace zan taimaka miki zanyi ne . sai dai mu bari muga zuwan doctor .. Nagode.. Nagode.. Nagode..deeni  bazan taba manta taimakonka gareni ba  ,ta sake fashewa da wani matsanancin kukan ..

Cike da sanyin jiki da tausayin kanshi ya Zare hannuwanshi dake  'cikin nata ya Ciro daya Daga 'cikin  wayoyinsa   ya turawa doctor saira sakon  test ..kana ya janyota jikinshi ya rungumeta tsam  yana shafa bayanta kusan minti biyu suka dauka ahaka sannan ya dagota cike da kulawa da tausayawa ya tsura mata rikitattun idanunshi is Ok kukan ya isa hk kinji.
  " ta daga masa kanta kawai tare da cigaba da kukanta domin ita kadai tasan  irin radadin da zuciyata  ke ji a game da 'cikin jikinta .
,ranshi a matukar bace yacigaba da kallon yadda take wani irin kuka Wanda yasan hkn zai iya shafar lafiyarta da dan dake  cikinta .
  "dan hk ya furzar da wani iska me gauraye da huci kana yace haba..meyasa kika fiyye fitina  da wahala ne?

Nace miki  kiyi shr hk zan San abin yi ko so kike nazare hannun 'cikin lamarin 'cikin jikinki ?

Tayi saurin girgirza masa kai.
 Ok ki bar kukan nan hk bana son jin sautinsa kwata kwata .
,nan ta sake girgirza masa kai alamun taji .

Kina jin yunwa ?

Tana jin yunwar Amman ta girgirza masa kai alamun bata ji .

Byn kmr minti goma shabiyar  sai Ga doctor saira tashigo  office din hannuta rike da wasu  file files tana yiwa nablah sannu da jiki .

 , nablah ta daga shanyayyun idanunta Tana dubanta tare daga  mata kanta alamun da sauki kana ta zarce zuwa mazauninta Tana jiran isowarsu 

 DEENI bai tsaya jiran saukowar nablah  ba. Ya sanya mata hijab dinta  ya nade hannun suit dinsa ya dauke cak.. ya rungumeta ajikinshi yana kallon 'cikin  kwayar idanunta  ji yayi tamkar ya tsotsi pinky lips dinta da suka sake yin ja .
, ahankali yakarasa Inda doctor take zaune  ya zaunar Daita kan kujera yana sake gyara mata zaman hijab din  kanta sannan shima ya zauna..

Yana maida hankalinsa sosai kan doctor saira .sai daya sauke naunauyen ajiyar zuciya sannan ya soma dacewa doctor wani taimako nake son kiyi min akan cikin jikin yarinyar nan dan Allah  idan har zai yiwu Ina son a cire mata 'cikin jikinta ....

Doctor saira tayi shr Tana sauraronsa har  sanda  ya dasa ayar mgnrsa , sannan tace gsky mu  hospital din nan bama abortion domin doka ce me karfi idan aka kama mutun da laifin aikata hakan.
 nablah najin hk  ta zamo kasa da sauri Tana marairaice fuska da murya ,yayinda hawayen dake makale a idanunta suka soma ambaliya suna tureneniyya gurin fitowa  ta hade hannuwanta duka  guri daya tasoma rokon doctor

 ,dan girman Allah doctor ki taima min ki cire min 'cikin jikina, dan girman mahammadu rasulillahi s.a.w  ki agazawa rayuwata ki rabani dashi , idan ba hk ba wlh mahaifina zai kashe Ni takarasa fadar hk Tana sakin wani irin kuka me sotsa rai gefe daya km  jikinta ya sake daukar kirrrrrrma tasoma rarrafowa Inda doctor ke Zaune.
 A dan hassale DEENI yace wai meyye hk kike yi ?
 bakiga magana Mukeyi  daita ba ta yadda za'a rabaki da 'cikin jikinki ba. wlh idan kikasa wasa sai kin haifi 'cikin jikinki da izinin Allah.
 ta juyo da sauri ta rarrafo zuwa gurinsa ,tana kuka dan girman Allah kada kamin hk  DEENI.... karigada kayi Niyya taimaka min dan girman Allah kada kafasa ..

To wlh Inda har kina bukatar taimakona

 to ki natsu kibar kukan nan  hk tun ban hassala dake ba, Na canza ra'ayina ba  ,tasa byn hanunta da sauri tashiga  goge Hawayen dake siyaya a idanunta .. kayi hakuri gashi Ina gogewa .

To ki natsu sosai dan Ina bukatar natsuwarki a halin yanzu ta Mike  ahankali Tana kakkabe jikinta da sake  gyara zaman hijab din    jikinta..kana tace  zan natsu kaji ..gabadaya ta gigice ta rude , ba DEENI ba" hatta doctor saira sai da  tausayin yarinyar ya dinga  ratsa jinin jikinta .

 DEENI ya maida hankalinsa sosai kan doctor saira tare da ce mata  doctor ki taimaka please kisan yadda zakiyi ki rabata da 'cikin jikinta Doctor tace Ok shikennan zan taimaka.

 nablah tayi saurin cewa  yauwa doctor Nagode sosai Allah Yasa kifi wannan matsayin . Doctor saira bata bi takan nablah  ba tacigaba da mgnr dan ta lura yarinyar bata 'cikin sense dinta.

 ta Mike tsaye tashiga wani daki a duk acikin office dinta taje  tattaro duk wasu abinda tasan ana amfani dashi gurin abortion tazo ta zubesu gaban nablah.
 tace  yanzu dai zabi ya rage naki ,kinga wayannan abubuwa ?

 nablah   tashiga duban abinda ta zubesu gabata tare da  dagawa doctor kanta  , sizos ne zube 'cikin wani dan madaidaicin tire da wasu karafe birjik . Doctor tace  kinga wayannan abubuwa  to dashi ake cire ciki .
idan kin amince za'a cire miki ,Amman 'cikin dayan biyu ,rayuwa ko mutuwa wane kika zaba ?
. nablah tayi shr kawai Tana tunanin abinda zata zaba yayinda gefe daya km  dade ya rufe DEENI zuciyar deeni  tunaninsa ko taji tsoro ne yasa yaji tayi shr  Amman Ga mamakinsa sai ya tsinci sautin muryata 'cikin dodon kunnenshi muryarta cike da  kuka tace  ,bbu komai doctor nazabi kowane daga ciki  Ni dai burina Bai wuce  kicire min wannan 'cikin ba .
 doctor tayi shr tana dubanta hade da nazarinta. DEENI ya dinga aikawa nablah da wani irin  kallo me cike wahalar fassarawa kallon mara  hankali yake mata .

  a fusace yace doctor bada wannan a sake samo wata  dabarar yi.
 ita km nablah ce take doctor ki taimaka please ...  Ke kiyiwa mutane shr da bazan 'bakin nan naki duk kinbi kin cikawa mutane kunne .

Doctor ki taimaka iya abinda yace kennan yayi shr tare da xubawa nablah idanunsa .

,take  km wani dabara yaxo ma doctor saira 
Tace kada kadamu  zan taimaka mata akwai  wasu kwayoyin da za'a iya mata amfani dashi yanzu Wanda zai  saka 'cikin ya hade guri daya zuwa nan da wata uku sai Ku dawo asaka injin a markade  'cikin gabadaya ta yadda bazata matu ba .

DEENI yace shikennan hkn man yayi  Na gode sosai doctor saira tace karka damu ai taimakon juna ne.
 ,nablah tashiga yiwa doctor saira godiya sosai har  da bata hakurin rashin kunyar datayi mata da farko .
murmushi tayi kawai doctor tayi  Tana me sake   tsananta  jin  tausayin yarinyar acikin  ranta . 
 "Doctor ta hada mata magungunan  kala kala Na kara kafiyar jiki da karin jinin ta xube su gaban deeni .

 DEENI ya dauka tare da   juyowa Inda nablah ke zaune zugun daita duk tagama  fita haiyacinta .

yace zaki iya tafiya?

 ta dan daga masa kanta alamun eh yace Ok Mike muje ko..

Jiki a sanyaye suka baro office din doctor saira zuwa harabar hospital din wanda sai a lokacin deeni yasan yanayin da garin yake ciki .

Ahankali  DEENI ya daga idanunshi yana kallon sararin samaniyya yadda hadari ya hadu sosai kafin kace me tunin ruwa yasoma saukowa da karfinshi.
  Kai tsaye Inda yayi parking din motarsa suka nufa yayi saurin  bude mata gidan gaba  tashiga ta zauna shima yazagayo  yashiga ya zauna yana Mr  tada motar  yasoma gudu  ahankali  kmr bai son yin tukin  ,yayinda ita km gabadaya ji take tamkar zuciyarta ta buga sbd wani mugun haushinsa  dataji yakamata.
so take yayi mugun gudun sosai tamkar  zai tashi sama ko 'cikin dake jikinta zai jijiga daga nan ya zube ta hutawa ranta.

 dunkule jikinta tayi guri daya tana sakin numafashi ahankali  sakamakon dan ruwan daya soma tabata
wani irin zazzabi ne  may zafi yasamu nasarar rufeta, jikinta ya dau zafi sosai  tamkar garwashin wuta.
 jikinta ya dauki rawa ganin hk yasa  DEENI ya juyo ya dan saci kallonta ganin yadda take rawar tsanyi yasa rage AC matar tare da   Ciro blue suit dinsa ya lullube mata jiki dashi  ..

Sannan ya maida hankali  Yacigaba da tukinsa .
  " yana  tunani yarinyar.
Da   irin zaman dayayi da zeenat ,ya dinga  tunawa da yadda abubuwa suka dinga faruwa a tsakaninsa daita daki daki da yadda ta dinga samun ciki tana zubarwa .
 
 a ransa yace dama baitace zata fara haifa min  yara ba ?
Ya sake tuna sanda yayi  mafarkin   da yarinyar.
 ta haifa masa wasu kyawawan  bbys masu kyau  tana Miko masa  .

Taja numfashi da kyar ya fesar  ,ashe gaske  hkn zai kasance atsakaninsu  itace din uwar ya'yansa ba zeenat ba   ahankali ya furta wannan wace irin kaddarace hk ?

Bai San sanda hawaye ya tsiyayo  masa ba , ya Ciro hanky a gaban aljihun rigarsa ya share hawayensa  yacigaba da tukinsa ahankali ya sake  juyowa yana dubanta  yadda ta kamkame jikinta ya tabbatar masa da sanyi take ji sosai dan hk ya Kai hannushi ya kamo tafin hannuta'cikin nashi yana murzawa wani irin zafi yaji ya ratsa nashi  tafin hannu.
 ya matse hannuta sosai 'cikin nashi yana cigaba da direving .
  'Kai  tsaye gidan glass ya nufa daita. batayi mgn ba sbd Yadda take jin jikinta.
 " byn yayi parking ya fito yazo ya bude mata kofa ya ganta still  a rakube tamkar kazar da ruwa yayi mata duka.
  ya tsaya kawai  tare da tsura mata rikitattun idanunsa kana yasa hannushi duka yacicci bota ya nufin 'cikin gidan daita .
  dakin jiya  ya nufa daita ya kwantar daita 


Sanyi sosai ya sauka a garin ya hade da sanyi AC jinta take tamkar wacce ake kwarawa runwa sanyi .. 
Layin  umminsa yafara nema tare da manna wayar a kunnenshi byn ta dauka suka gaisa yace mata yanzu nan muka  dawo daga hospital ...

Ya jikin nablah din ?

da sauki first love .
  nablah ta lalubo hannushi 'cikin nata ,ya juyo batare da yacigaba da mgnrsa ba  tashiga  girgirza masa kanta yayinda  bakinta ke  motsawa ahankali Amman baya jin abinda take cewa .
ya dan  matso sosai kusa daita  yakai kunnenshi daidaita saitin bakinta domin jin abinda zatace a kasalance yaji tace dan girman Allah kada ka sanarwa ummi komai game da 'cikin jikina ka rufa min asiri  wlh bansan da wani ido zan kalleta ba.
  takarasa fadar hkn wasu siraren hawaye nabin gefen idanunta yace is Ok Ni ma bagaya mata zanyi ba .

Ya juya yayi  nesa  kadan daita  tare da cigaba da wayarsa ummi tace Ina jinka son me doctor tace yana damunta wlh bakaga yadda Na damu ba ?
 ya katse zance da cewa  sirrin boye ne ka shirin   bayyana.

 ummi tayi shr tana tunanin me hkn yake nufi ?
Sirrin boye ne ke shirin   bayyana ta sake maimaita hkn  can km ta harbo jirginsa  tace Kai dan Allah ? Yace Allah kuwa first love.

wata nawa dan Na dade da zargin ciki gareta wlh  yayi kasa kasa da muryarsa ta yadda nablah bazata taba jiyosa ba ,yace kyalli  hudu hkn yasan ummi ta gane wata hutu yake nufi  tayi ta murna tana kwararo addu'oi Ga 'cikin da ma nablah gabadaya. daga karshe tace Allah Yasa wannan 'cikin yakawo sanadin da diyata  zata samu nata ,da kyar deeni yayi karfin halin amsawa da Ameen .yace ya kunje hospital din?
Ummi tace muje yanxun muka dawo sai dai bamusa likinta da zai dubata , appointment aka bamu yace Ok nan suka dan taba hira Daga baya sukayi sallama.

Tun sanda yagama wayarsa  da umminsa Ya dawo kusa daita sosai ya zauna  yakasa aikata komai sai binta kawai yake da idanun   ko yaya ta motsa sai yayi mata sannu .

Ahankali ta tabo  wandonsa idanunsa ya zuba mata atunaninsa bada gangan tayi ba ,sai dai can kmr minti biyu ya sake jin takara tabosa .

Muryarsa a sanyaye yace menene nablah?

Hadiye yawun da suka zo mata tayi kana tayi mgn da muryarta data gama disashewa tsabar kuka ,sanyi yayi min yawa ,da kyar ya iya gano abinda tace ....
Kashe AC yayi gabadaya ya dawo ya zauna yana nazarin abinda zaiyi ganin yabata lokaci a zaune  yasa shi tashi yashiga bathroom din dakin  ya tara bucket tare da kunna tap din ruwan zafi .
ya dawo dakin ya jawo towel dinsa .

Zaune ya tayarda ita ya jingina bynta  da pillow ,tare da tattara gashin kanta  ya nannadesu ya warware Rebon  dinta ya tufkesu guri daya..


Ledar shipping din da Yayi mata jiya ya janyo ya bude  ya fito mata da wasu kayan bacci masu dama ya ajiye agefe .


Idanunta kawai ta tsura masa tana kallonsa yayinda gabanta yashiga dukan uku uku sai da gyara yanayin fuskarsa tare da tamketa da kyau tamkar bai taba dariya ba iya tsawon rayuwarsa .

Kana ya fara cire mata rigarta byn ya zuge zip din, hannu ya Kai zai balle breezy dinta ,tayi saurin rike mishi hannu tana girgirza masa kai tare da cewa uhmmmm ...

Mezaka min ne?

Ta furta hkn muryarta Na tsananta rawa ,hade fuskarshi yayi sosai sannan ya bata amsa da hadiyeki zanyi kana yacigaba da balle breezy dake makale da jikinta  ya cireta gabadaya  ya ajiyeta a gefe .

Batare da wani bata lokaci ba ya tsoma  towel din 'cikin ruwan zafi ya ciro ya matse sosai  ya fara  shafe mata goshinta zuwa saman dukiyar fulaninta , sanyyayiyar ajiyar zuciya ta sauke da karfi tare da runtse shanyayyun idanunta wuyanta da kirjinta kadai  yake aikin gogewa   ga ruwan da zafi sosai da kyar Tasamu ta hada kalmomin bakinta tayi  mgn ..

Please karka konamin kirjina fa .....sai lokacin ya lura da cewa nan kadai yake aikin gasawa ..

Janye komai yayi dangane da tarin shawa,arta dake fizgarsa gareshi yacigaba da gasa mata  duk wani lungu da sako na gangar jikinta sosai ita kanta take jin dadin abinda yake mata .


Ruf da ciki ya maidaita yacigaba da gasa mata bayanta zuwa bombom dinta, bata yi kokarin hanashi ba dan itama  tana jin dadin gashin da yake mata  har Saida ruwan zafin suka huce  sannan  ya Mike tsaye ya maida bucket din ya sake dawowa lokacin har bacci yasoma daukarta   .

Ya tsura mata rikitattun idanunsa yana kallonta a zahirance bata bambamta da komai ba irin na ya'ya masu hannu dashuni ta fannin jikinta da halayyanta  ..

Wani bangare Na zuciyarsa yace  ka renata gashi  km ita ke shirin zama uwar danka ko yarka ,sosai ya tsurawa surar jikinta ido.
 dubita santaleliyar yarinyar duk wata gaba ta jikinta a cike take bammmmmm barin ma   kirjinta daya sake cika tare da tsaya kyam..
  gabadaya  bombom yagama budewa   komai yaji ajikinta sai sambarka  duk ta yadda yake son macce takasance nablah ta zarta hkn ..

Da sauri Ya kawar da rikitattun idanunshi akanta yakarasa gareta ya saka mata kaya ya gyara mata kwanciyarta sosai shima ya kwanta  abayanta tare da rungumeta  tsam tsam ajikinshi yana sakin numafashi ya   lullubesu  da blanket .

ranar kam bbu wani zance zuwa   aiki ya manne mata  duk Kiran da ake masa ma baya dauka daga karshe yakashe wayar gabadaya.

  bacci sukayi sosai deeni ne yasoma tashi ya gyara mata kwanciyarta tare da lullubeta ya mike tsaye  ya nufi dakinsa  wanka yashiga  shap shap  ya fito tare da alwala yazo yagabatar da sallah ya canza kaya jikinsa zuwa wasu daban ya  fice Daga gidan byn ya kulle nablah a daki Kai tsaye planums rows family estate ya nufa  . Yana paka motarsa sule direbansa ya taso da sauri yana gaidashi deeni ya fito daga mota yana amsa bbu yabo bbu fallasa ,kana yasoma tafiya 'cikin takun nan nashi  zuwa 'cikin gidan yayinda sule ke biye dashi a baya .murya cike da ladabi sule yace boos wai Ina kashiga ne kwana biyu ?
Deeni ya juyo a dake tare da cewa akwai matsala ne ?

A'a Na dai Ga banganka bane shiyasa Na tmby Ga mutane nata zuwa neman taimako .be kara cewa komai ba Yacigaba da tafiyarsa 'cikin isa .boos Amman kadawo kennan bazaka sake fita ba ? Deeni  ya sake juyowa a fusace yana duban sule da wani irin kallo  wanda sai da sule shan jinin jikinsa kana yace idan ka kuma zuwa min da wayannan tmbyoyin zan dakatar dakai a aiki dani ,Ni dai waye a under din wani ?

Sule yayi saurin cewa Kai ne boos , Allah huci zuciyarka boos ,ya sake katseshi kadai ji abinda nace banson shishigi please sannan ya km juyawa yashige gabadaya laraba Daga nesa Tana hango abinda ke faruwa ita kanta so take tasan wani hali nablah take ciki domin ta kwana biyu rabonta daita gashi bata damar hawa upstairs gashi yanayin me gidan daban yake bazama ka iya kallonsa Kai tsaye ballanantana ka iya tmbyrsa ,karasawa tayi gurin sule Tana tmbyrsa ko yana ganin nablah shima bawani gamsashiyar  bayani yayi mata ba hk taja jikinta ta koma part dinta .

Bashi ya dawo gidan ba sai daf da magariba yashigo gidan yasa key ya bude dakin datake ciki  can ya hangota rakube a can a karshen gado ta kifa kanta bisa cinyoyinta da alamun ta kuka take da saurinsa yakaraso Inda take ya haye kan gadon tare da janyota jikinshi ya rungumeta tsam atare suka ji wani irin  shock ,da shiga wani yanayi na  daban . yayinda zuciyayoyinsu yashiga bugawa da sauri da sauri  daf ..daf
.lafewa tayi sosai ajikinsa tana shakar daddaden kashin turaren jikinsa.
 yayinda   bugun da zuciyata ke sake tsananta   kawai taji hawaye na sauko mata bisa kuncinta ahankali yake jin sautin kukanta har da shesheka ,ya dagota a kasalance yana kallon kwayar idanunta tare da dago habarta yana sake kare mata kallo yarasa me zai mata tasamu natsuwar dayake so atare daita.
 rasa yadda zaiyi ne  yasa shi hade bakinsu guri daya yashiga tsotsan bakinta  yana lumshe rikitattun idanunshi ,bata yi yunkurin dakatar dashi ba sai ma idanunta data sanya 'cikin nashi suna kallon kwayar idanun junansu .
ahankali ,salonsa da yanayinsa ya fara sauyawa zuwa bukatuwa daita.
 dan duk jin jikinshi yake wani irin iri gabadaya ji yake yana tsananin bukatarta ahalin dayake ciki .
hannushi ya fara yawo dashi  ajikinta yayinda still bakinsu Na hade guri guda ganin wasan nashi nason wuce misali yasa ta rike hannushi gamm tare da zame bakinta 'cikin nashi ta fashe masa da wani irin kuka tallabota Yayi sosai zuwa jikinsa ta fada jikinsa yana shafa sansar jikinta cike da natsuwa ahankali km yana rarrashin sosai tayi kwanciyarta ajikinsa atare suke fidda numfashin may gauraye da shauki  daidai kunneta ya Kai bakinsa tashi muje kici abincin nasan zuwa yanzu kina bukatar hk ?

tayi shr taki ce masa komoi ,duk da kusan abinda yafi tsana kennan a rayuwarsa yayi mgn ayi masa  kyaliya .
 "Amman hk ya dannewa zuciyarsa domin bata kulawa ta musamman ya mike tare daita ajikinshi Tana manne ajikinshi har babban parlour gidan ya zaunar daita akan kujerar dinning area ya bude ledar daya shigo daita kamshin gadashiyar kaza   ya bugi hancinta ta hadiye wani miyo  sbd tsananin yuwanr dataji ya taso mata yana  dawainiyya daita.
 sannan yaciro wani takeway wanda akayi raping dinsa da wani farin abu ya bude .
 ,nan ma wata hadaddeyar fridrice ce datashi kayan hadi sai kamshi Abinci ke tashi takoina sai  kwalayen hallondia dake ajiye fiyye da biyar sbd yasan Tana matukar son shanshi .

Sannan ya tsura mata ido yana  dubeta ganin ta rafka uban tagumi yace mata  Bismillah ahankali ta tsaka yatsun hannuta  tasoma cin abinci yayinda shi km ya zuba mata ido yacigaba da kallonta  kawai yana kallon yadda take sarrafa yatsun  hannunta gurin diban abinci zuwa bakinta .
abin sha'awa komai tayi sai yaga Tana birgeshi gashi komai nata daban yake  dana sauran mutune, tamkar ba me shiga ciki ba .
bbu laulayi komai bbu wani abu wanda ya danganci tsirfa irinta masu ciki.
 komai tasamu cin abunta take a ranshi ya furta Yar baiwa me baiwa iri iri ..har tagama cin abinci idanunshi nakanta yakasa dauke idanunshi akanta  ya balballo mata maganin jinin da doctor saira ta jibgomusu  ya Miko mata tare da ruwa tasa hannu ta amsa  Tasha .
ta sake ballo wasu Tasha.
 tayi overdose dan maganin yayi mata saurin aiki yadda tayi din ne abin  yakusan sashi dariya Amman ya danne dan kada yarusa shirinsa  yacigaba da kallonta muryarsa a sanyaye yace kina bukatar wani abu byn wannan ?
 ta girgirza masa kai kawai .

Bakinki Na ciwo ne?

Muryarta cike da shagwaba tace a'a .
Ok amsawa ne bazakiyi ba.
 ,ta yatsina fuskarta alamun yasoma damunta .
Kinyi sallah ?

Tace a'a Tana turo masa dan tsukaken bakinta bai San  sanda ya kai bakinsa kan lips dinta  ya tsotsa sosai ya mannota da jikinsa   yace ki saki jikinki sosai ta hk ne maganin zai yi saurin aiki ajikinki idan ba hk ba zaki haifi bbynki Ni bbu ruwana fa.
 ...ta narke fuska tamkar me shirin sakin kuka .

Yace Ok kuka ma zakiyi Ok ?
Tashiga girgirza masa Ok ki daure ki saki zuciyarki ki dinga walwallaki taamkar da ta hakan ne komai zai daidaita..
 " muryarta a sarke tace to ...yace muje kiyi sallah ki kwanta  ki huta .ta Mike tsaye shima ya Mike tare da rungumeta a gefen jikinsa ya sake nufar dakinta.

  
Akwana a tashi bbu yuwa agurin Allah 

Yau kimanin 3 weeks kennan da tafiyarsu zeenat india ummi tasaka zeenat gaba Yau zuwa wani babban asibitin birnin India Wanda ya amsa sunanshi may dauke da kwararrun likitoci domain a sake duba mata lfyr diyarta a karo Na uku .

Duk wani bincike da test test anyiwa zeenat shi yayinda gabadaya sakamakon yanuna lfy lau take km bata tare da wata matsala ajikinta.

 likinta ya shedamusu at any time zata iya daukar ciki domin abincikensu da sukayi yanzu hk mahaifarta a bude take dan hk ko yanzu mijinta yasadu daita zata iya samun ciki idan Allah yaso.

Ummi ta sauke Naunauyen ajiyar zuciya sannan  Hankalinta ya sake kwantawa tunda ansha gaya masu hk a duk hospital da suke zuwa .
ummi ta numfasa tare da yiwa bayanin akan yadda zeenat din Tasha zubar da ciki da irin  magungunan data dinga Sha domin hanata daukar ciki .
Likita yace duk da hk madam  Allah Bai dora mata wata matsala ba lfy lau mahaifarta take bbu abinda yasameta Wanda zai hanata haihuwa sai dai ko wani ikon Allah yacigaba zamu dai mu daurata akan magani Wanda zata soma amfani dashi anan kafin Ku wuce inshallahu da yardar Allah zata samu, idan Tana da rabo. hk suka dawo gida zuciyoyinsu cike da natsuwa barin ma kada  zeenat taji labari ..



Bangaren deeni kuwa  kusan sati uku Yayi a gida batare da ya fita ko nan da can ba har  aiki ya tattarashi a gefe tare da kashe wayoyinsa.
 sosai yake bawa nablah kulawa ta musamman da kafa kafa daita duk wani abinda yasan zai faranta mata shi yake mata .ita kanta ta dan saki ranta sosai dashi .
yayinda zuciyarta take ganin kirkinsa da imaninsa gareta zuciyarta, ta aminta dashi  har tabashi matsayin  wani jigone Na rayuwarta dan yadda yake mata ko shi yayi mata 'cikin jikinta iyakaciinsa kennan.
duk wani aikin office da yakama yayi ,sai yayi shi agida sosai yake bata  lokacinsa ya  tabbatar da tana cin abinci da Tasha magungunan nata Na karya akan lokaci yayinda shakuwa ke tsananta  shiga tsakaninsu ahankali ahankali sakamakon wuni da sukeyi tare da  kwana guri daya


 



MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
 AUREN SIRRI
     💖💖💖
💗💗💗💗💗





AYSHA A BAGUDO



*Jinjina gareku group Na  kainuwa writer's lallai Ku masoya nah ne  Wanda duniya tabari  nasan da zaman  hakan batare da Ina cikinku ba, hakika  bagudo na yinku  sosai da sosai km  ta yaba da kaunarku gareta sannan tana  alfahari daku a duk inda kuke ,domin Kun cancanci fiyye da hk agarenta ,sosai kuka shiga    raina  ba karya,  Ku din masoya ne na daban,  Ina matukar jin dadin  yadda kuke kaunar labarin AUREN SIRRI wannan shafin sadaukarwa ne Ga duk wace take 'cikin group Na kainuwa writer's Nagode sosai  Allah yabar zumunci da kauna inshallahu km  ana taren tare*🤝🏻🤝🏻🤝🏻 





Page 89



A hankali ya yunkura zai tashi daita ajikinshi, tayi saurin Kai hannuwanta dukka ta zagaye cikinsa dashi 'cikin raunanniyyar muryarta tace please deeni 
 ka zauna kada ,ka fama ciwonka  ....dole Tasa ya koma ya zauna ba dan yaso ba.
  " sai  dan gudun  abinda zai  sameta idan ya matsa lallai sai yatashi da karfi kmr yadda yayi Niyya ...yadda take kwance  ajikinshi yasa yakara jin gabadaya notikan dake daure da jikinsa  suna  neman kwance masa da son fallasa abinda ke boye zuciyarsa  wanda hkn km zai iya jawo afkuwar komai atsakaninsu batare daya shirya yin hkn ba ,kamo lips dinsa na kasa  yayi yasoma  ciccizawa ahankali ahankali.
 ,wani irin  zazzafan shaukinta yake sake  jin yana bin jini da "bargon jikinsa yana bayawa kowane part Na ruhinsa sako na musamman ..
ahankali ya runtsa rikitattun idanunshi sanda yaji ta zare hannuwanta ajikinsa tana sakin numafashi da kyar tamkar me cutar asma .

Idanunsa ya tsura mata yana kallon cikin kwayar idanunta dake walanniya  suna aikin  jujjuyawa, sosai ya tsura mata idanushi kawai Tana aikin kallonta hk kawai    ya tsinci  kanshi da kasa  ce mata komai sai ma Kai hannuwanshi da Yayi  yakamota ya  mannota da kirjinsa yana sakin naunauyen ajiyar zuciya .kana  yakai bakinsa  daidai shashin wuyanta yana shinshinawa da sumbatar duk inda bskinsa yaci karo dashi , hade da  goggomata gashin dake kwance a fuskarsa .

jin Yayi  saitin kunneta yasa  ta dago hannuta 'cikin mutuwar jiki a dan tsorace ta dora akan bakinsa sbd kwata kwata bata shirya jin abinda yake son fada mata ba.
 'cikin sarkewa muryarta tace please kayi hakuri man sbd Gani irin kallon dayake antayo mata ...

 lumshe rikitattun idanunshi Yayi  yana shakar kamshin tafin hannunta mai taushi  akan bakinsa .
 "ta kula da yadda yake yi din km  tasan bakaramin aikinsa bane ya canza salon yanayinsa zuwa zafafa wasannisa masu hautsina mata lissafi .
dan hk tayi sauri zame hannuta ahankali zata tashi da sauri Ya rukunkumeta ajikinsa tare da shafo wasu wuraren a sansar ajikinta kana ya dire" hannuwanshi  akan tudun nonuwanta  da suke cike bammmmmm dasu abin bukatar kowani cikakken namiji, ahankali yake   shafo saman nonuwanta yana lumshe ido ,   ta dan saki kara 'cikin sanyi muryata mai dadi tace . 

Wayyo  NASU...RUL..DEENI zan suuuume ..me .. maka  fa ...

Har 'cikin kasan zuciyarsa yaji maganarta tashigeshi "ya rinka jin wani irin abu me kama da  sonta yana kara fizgar zuciyarsa gareta  .cike da kuzari 
ya sake rukunkumeta sosai ajikinshi yana mamakin wannan abu  dayake tawainiyya dashi akowani lokaci koda kuwa baya tare daita .
 'cikin natsuwa km yashiga  mamakin yadda Sam bata shakkarsa , kalli yadda ta ambaci sunansa yanzu kai tsaye batare da wani tsoro  ko fargaba ba .
Wanda  ba duk mutane ke kiransa da sunan Kai tsaye ba ......

Ita kuwa tsoro ne yakamata  domin ita kanta ji tayi kawai sunan nashi ya fito daga bakinta batare data shiriyawa hkn ba.yawo yashigayi da hannushi a sansar jikinta batare da Yayi la'akari da irin raunin dake kafarsa  ba .
 rasa yadda zatayi dashi ne yasa tasoma mutsun mutsun ajikinshi  tare da ce  masa tana jin yunwa ,tasan yanzu zai kyaleta.
Hk kuwa ta faru dan sausauta rungumarta Yayi yana sakin  numafashi da kyar.
 ya juyo da fuskarta daidai tashi suna fuskantar junansu sosai yayinda kowanensu Na shakar numfashin juna  atare suka lumshe idanuwansu take km  zuciyoyiinsu suka shiga bugawa atare muryarsa cike da shaukinta.

 yace a Ina kika San sunana hk ?

Tayi shr tana tunanin inda taji sunan  yayinda gabadaya zuciyarta ta cika da  frigici da  tsoron tmbyr da Yayi mata  idanunta suka soma ccikowa da wasu Hawayen. 

 Muryarsa a kasalance yace ba kuka nace ki min ba ,amsa kawai zaki bani . Ina kike San complete name din na ?


Muryarta cike da in ..inna tace uhm ammm daman ajikin hotonka dake manne a dakin sama nagani .

Ya lumshe rikitattun idanunshi yana cigaba yawo da hannuwanshi ajikinta yace  Kinsa kuwa  kin fi kowa iya sarrafa harshen gurin iya Kiran sunana ....yakarasa fadar hk yana bude rikitattun idanunsa masu kashewa Mata sansar jiki.
 
Ta tsurawa kwayar idanushi ,idanunta itama  kawai Tana kallon yadda Ya dawo mata tamkar wani karamin yaron goye  sannan ta bude bakinta da kyar  .

,kowa fa kace ?

Ya kashe mata idonsa daya alamun hk abun yake "abinda ke sake narka da zuciyar nablah kennan har ta manta da Wanda take tare ,ta dinga jinsa ajikinta   tamkar shi din nata ne na har abada.

Yayinda  mgrsa Tasata jin kmr  ana mata wanka da ruwan sanyi ne .
 ,har da ummi da aunty ze...cak  ta katse harshenta gurin karasa mgnr  take km gabanta ya yanke yashiga  dukan uku uku sakamakon tunowa da zeenat din  datayi .

da tuna ashe fa deeni datake tare dashi ahalin yanzu  mijin wata  ne, wanda  tafi so da kauna fiyye da  komai dake 'cikin rayuwar  duniyar nan.
Shine  ,take tare dashi  har take rayuwa dashi tamkar wani  mijinta . 

Ya kika yi shr yarinya
kikarasa Kiran sunan matata man ?

Ta runtse idanunta Tana jin yadda bugun zuciyarta ke sake karuwa kirjinta Na mata wani irin  zafi da radadi Wanda tarasa name ne ?
 
Ok bazaki iya karasawa ba ,sbd kin fara  son mijinta  ko ?

Ta bude shanyayyun idanunta  da suka gama canzawa tsabar tashin hankali data tsinci kanta ciki  ta watsa su 'cikin   kwayar idanunshi kana ta girgirza masa kai wasu zafafan  hawaye suka samu nasarar  biyo kuncinta .
Ya dan yi murmushin  gefen baki yana me kamo lips dinsa na kasa yanacigaba da ciccizawa  ahankali, sannan ya sauke ajiyar zuciya da karfi.
  
Kina  kishin    matata ko nablah  ?

 Unexpected taji ya jiho mata tmbyr tun bata gama  jimamin wancen ba ..


Muryarta a matukar sanyaye tace a'a wlh bana kishi matarka  sannan km bana jin sonka 'cikin zuciyata Ni kaina bansan abinda yasani kasa karasa Kiran  sunan nata ba .
 ya girgirza Kanshi  kawai domin sanin dalilin dayayi ,kana yace  zaki sani ne inda lokacin hk Yayi .

  dan kin rigada kin  makaro yarinyar dan tuni soyayyata tagama da zuciyarki tsab "kin fada  atafkin  kogin  son mijinta kin nutse  kiris ya rage miki  zuciyarki ta mace akan shaukin soyayyata  ....Ya fadi hk yana me sakar mata  killing smile dinsa me sake kashewa Mata ilahirin  jikinta akanshi.

 Allah Ya tsareni da macewa akan sonka deeni   ta fadi hkn muryarta  cike da kuka tana mikewa tsaye ahankali yayinda wasu Hawayen takaicinsa  suka sake  biyowa kan  kuncinta.
 " kalli yaddda kike kuka nablah akan soyayyata da kishin matata Amman kice a'a , wlh Ni ba akanka da wani banzar kishin matarka nake kuka na ba.
 Ni.. Ni ..abinda yasani kuka daban takarasa fadar hk muryarta cike da in inna ,yayinda  wasu siraren Hawaye suka sake  silalo mata .

ya Miko mata yatsun  hannushi alamun ta taimaka masa ya Mike tsaye , bbu wani  mutsu ta Miko masa tafin hannunta duka.
 ya riko nata hannuwan  cike  da wani irin sabon  shaukinta , ya Mike  tsaye  yana Kiran washhhhhh washhhhhh ita km ta damke yatsun  hannushi sosai tana mishi sannu dan a tunaninta ko zafin ciwon ne yasakashi yin hkn  .

Ya gyara tsayuwarsa da kyau yana rungumeta ajikinshi muryarsa can kasa kasa cike shaukin feelings yace ok gaya min abinda yasaka ki kuka yanzu ...?
 
Ni km idan kika gaya min wlh  na miki alkwarin bazan sake aikata miki shi ba , ballanantana har yasa  kiyi asarar hawayenki akanshi ..ta girgirza masa kanta kawai tare raba jikinta dana shi tana fezgo numfashi ..kana muryarta a shagwabe tace Ni muje yunwa nake ji...

Hannuta 'cikin nashi suka nufi parlour,n ta nufi kan kujera dashi da niyar zaunar dashi ,taji  yace Kai Ni  dinning ..
 can din ta kaishi ya zauna da kyar yana sake Kiran washhhhhh Allah nah ...  yayinda   jini ya dinga diga tun Daga kitchen har zuwa dinning area ..har zata zauna ta tuna da bbu komai lullube  ajikinta.
 ta sake komawa cikin kitchen din ta dauko hijab dinta ta zira.

ta sake fitowa  hannunta rike da wani dan karamin  towel Wanda tagani a rataye  kitchen din.
 da moupystick tana goge jinin daya bata gurin .
tana kallon yadda Ya tamke fuskarshi tamau ya hade rai yana zabga mata harara  tamkar bashi ba.
 ko km Wanda aka aikowa da sakon  mutuwa .
, har takaraso gareshi ta daga kafarsa mai ciwo ta tasaka towel din a karkashin kafarsa Bai ce daita komai ba ,dan yana jin wani irin mugun  haushi ,da duk  wani aikin wahalar dazatayi ahalin yanzu .yayinda yake jin zuciyarsa yanzu zai iya zamemeta tamkar bawanta akan cikin jikinta .
Ahankali   ta zauna tasoma yin  breakfast din 'cikin natsuwa  tana dubansa da mamakin sauyawarsa alokacin.

Byn kmr minti shabiyar sai Ga wayar sule direbansa, yace gasu sun karaso, muryarsa a dake yace ok ,ya dan juyo yana kallon inda nablah ke zaune ta zuba masa shanyayyun idanunta  ,ki tashi ki koma daki abinda ya iya ce mata Keenan .

,haushi da takaicin yadda yayi magana yasa ta   Mike a zabure zata tashi yayi saurin   runtse rikitattun idanunshi gammmm  yana Kiran sunanta 'cikin sanyayyiyar muryarsa na..bee..lah .
Ta amsa da Na'am tana me zagayowa    daidai indayake zaune  .
ta tsaya itama tana dubansa ,har sanda ya bude idanunsa ya zube su 'cikin nata .

Kina ji ko.. ki dinga bin jikinki  ahankali please... so that maganin da kike Sha zaifi saurin yin aiki ajikinki ,ta yadda komai zaizo mana  'cikin sauki Amman idan kina zabura irin hk fa akwai matsala .

,taji dadin abinda yace sosai har haushinsa dataji, azuciyarta ya ragu    ,ko bbu komai tana matukar  jin dadin yadda yake nuna kulawarsa akanta shiyasa wani lokacin  take manta kanta da mijin wacce take rayuwa har ta dinga  jinsa 'cikin  ranta, sbd Yadda yake tsananin yin kafa kafa  da 'cikin jikinta  , muryarta a sarke tace Nagode sosai da kulawarka gareni  km inshallahu zan dinga yi ahankali ..

Ya lumshe rikitattun idanunshi tare da cewa Karki damu  kije kisha magungunanki ,ki kwanta ki dan huta tace to tana me kokarin barin gurin.
 ya juya ahankali  yabi bayan da wani irin mayataccen kallo me cike da tsansar sha,awarta .


Byn kmr minti goma ya Mike tsaye da kyar yaje ya bude glass door din  yana me  baiwa Dr saira hanyar shigowa ciki waw tun bata karasa shigowa ba sbd Yadda tsarin gidan yayi matukar birketa .

Tashigo ahankali  har da sule Wanda ya dawo shima  tamkar wani bagidajen dan  bakauye dashi  tsabar kallon tsarin  gidan ,duk da yasan sanda aka fara ginin gidan.da sanda aka ganashi  Amman Bai dauka tsarin gidan  zai kasance irin  tamkar akasar turai ba . ahankali yashiga furta Masha Allah lakuwata illa billah

Deeni Bai bi takan yadda yaga sule ya rude yana  kallo da wage wage gidan ba.
 ya zauna rigingine akan two star  yana nunawa doctor  saira dake tsaye har lokacin gurin zama.

 ta zauna tana gaishe shi  tare da tmbyr me jiki ,yace taji sauki sosai.. sule ya juyo da sauri tare da  cewa , boss waye km  bashi da lfy ?

Deeni Ya yatsina  fusaka yana watsa masa wata uwar  harara kana yace ba'a sani ba .
 "km wlh mlm kada ka sake ,kayiwa mutane wasu  saqagogun  shirmeka  anan .

Sule yace sorry boss baza a sake ba da izinin Allah Amman fa gidan ya kero iya keruwa Allah sanya alkhari da zuria masu albarka.

 deeni Bai San sanda yace Ameen  sule Nagode sosai .
Ashe dai kana da  hankali wani lokacin ?

Sule ya washe bakinsa  yana dry jin dadi abinda boss dinsa yace .

Deeni ya bukaci dr saira ta fara duba mishi kafarshi tare da mata bayanin abinda yasame shi.
 takaraso har  inda yake zaune  tana duba kafartashi  .

tace garin Yaya hk ta faru Mr deeni ?

 Sautsayi ne kawai doctor yayi mgnr a takaice .
Ok gsky ni yanzu banzo da wannan shirin ba ,Na dauka ma ko game da yarinyar nan ce ,yanzu abinda za'ayi kabini muje zuwa  hospital sai ayi treating din gurin yace Ok babudamuwa  ya Mike tsaye  da kyar suka bar parlour,n sule Nata faman ratafa masa sannan bbu kaukautawa.

 nablah Na tsaye jikin Window glass din dakin  tana kallon yadda yake daga kafarsa daya  da kyar.
 taji wani irin abu ya caki tsakiyar zuciyarta tare da maseefar jin tausayinsa raunin dayaji a sanadiyarta . Yayinda  zuciyarta ta shiga harbawa daf ..daf... daf..
ta runtse shanyayyun idanunta  'cikin sanyi jiki takai hannuta ta dafe saitin zuciyarta dashi Tana jin komai dake  jikinta yana  kokarin sauyawa akan deeni .

 Ahankali ta furta oh! Allah  Ni nablah meke shirin faruwa dani ne akan wannan bawa naka ?  

Ko dai abinda yake yawan fada kullun akansa ne ke shirin faruwa dani ?

Kar dai Na fada tafkin soyayyarsa da gaske batare dana sani ba ?

Tayi saurin girgirza  kanta tare da cewa  hkn ma bazai taba faruwa  ba domin nidashi bamu dace ba sannan zamu taba son junanmu ba .

Ta dade tsaye agurin tana saka da tunanin iri iri  akansa ,kafin daga karshe taje ta zube akan bed ta kwanta tana sakin naunauyen ajiyar zuciya da karfi hade da runtse idanunta badan tana jin baccin ba sai dan umarnin daya bata ..


Bayn sunje asibiti akai yiwa deeni duk wani abun da ya dace tare da yiwa kafar  bandage .
 sule ya maidoshi gida shi km yakara gaba .


A rakube yaganta bakin gadon dakin tallabe da fuskarta da duka hannayenta wanda take jikinsa yabashi cewar tunaninsa take yakaraso Inda take ahankali yana dingisa kafarsa daya  , Murmushin da bayi zato ba ne ya samu nasarar kufce masa, rungumeta yayi tsab ajikinsa yana cewa tunaninnawa  km  Na me ne ?

 ,ta kalloshi a frigice tana shagwabe fuska tare da cewa  why deeni ka tsorota Ni fa sosai  ..Ya narke mata ajiki shima yana shagwabe mata tare da cewa am very sorry dear ..Amman please ki dan rage tunani sbd condition din da kike ciki ,jin abinda yace yasaka jan tsaki ,tana tmbyr kafarsa ya lumshe mata rikitattun idanunshi batare da yace komai ..

Akwana a tashi 'bbu wuya gurin Allah km sannu ahankali   cikin hukuncin Allah deeni ya warke sumul  yasamu  saukin kafarsa sosai har yana tafiyarsa  yadda yakamata tamkar da.

 yayinda 'cikin jikin nablah shi km  ke sake girma  da bunkasa da bin jikinta, barin ma  fannin nonuwanta da duwawukanta suji lbr , domin nonuwanta sunyi wani irin girma da  cika naban mamaki sunyi mata hake hake a jirjinta ,
Yayinda duwawukanta km suka  dan baje sukayi fade dasu.
 sai jikinta yabada wani  Shep me kama da coka cola .
ta murje sosai tayi haske tayi fresh ta  canza sosai  Ga duk Wanda yasanta ada idan yaganta bazai yi saurin ganeta ba .
sbd da Yadda gabadaya yanayin  jikinta yasamu sauyi Na musamman .

Bangaren su ummi kuwa komai Na tafiya daidai yayinda duk sanda zeenat ta tada hankalinta kan komawa Nigeria, ummi ke nusar daita tare da kwantar mata da hankali, abinda yasa ma basu dawo ba har zuwa  wannan   lokacin likitan daya daurata zeenat akan shan maganin ne yace su dan  tsaya  akwai abubuwan daza'a yi mata  .. yayinda duk abinda ke wakana  a game da 'cikin nablah dake jikin nablah  duk ummi Na sane da komai.
Km  gabadaya ta gama shirya yadda zatayi da 'cikin nablah batare da duniya tasani ba .


Wata sabuwa inji Yan caca ..... wata uku Na cika   ba sai ciwon kirji  ya sarface nablah ba .

Bashiri  ta tada balli ita fa tarasa gane kan komai yace da rarar ciki yakai wata bakwai zasuje a saka inji ya markade Amman gashi har 'cikin Na neman haurawa Amman yayi mata shr .

Idan km ya fasa taimaka mata ne kmr yadda yayi Niyya to yabarta takama gabanta, ta karasa fadar hk  tana sakarwa  deeni wani irin   kuka me bantausayi da cin rai  . Deeni yayi shr kawai tare da tsura mata idanushi yana kallonta batare da  yasan yadda zai bullo mata ba .
 gabadaya hankalisa atashe yake akan abinda take so yayi mata  yayinda , zuciyarsa gabadaya gaskiya take son fada mata akan bazai iya barin a zubar gudan jininsa ba ,Wanda Bai sani ba ,ko kwansa ke nan a duniya , Amman yana jin tsoron tashin hankali da zai biyo baya da Wanda zata shiga ciki idan yasanar mata da hkn  ,babu  shakka shi zai iya Mika rayuwarsa gareta a yadda yake jinta a zuciyarsa  a halin yanzu amman bazai iya rabuwa da 'cikin jikinta ba .muryarshi can kasa .. tamkar ta karamin yaro me koyon mgn yace kiyi hkr nabeelah  ban fasa taimakon  ba.
 har yanzu  akwai wannan niyar a zuciyarta amman ki dan kara min lokaci akwai abinda nake yi ne yanzu , km shi zubar da ciki yana bukatar wani a kusa da mutun  . tacigaba da kukanta  tana  girgirza masa kanta alamun bata yarda ba  .

Yanzu me kike so nayi yanzu ? 

Ni dai ka ajiye komai ka taimakamin ka bari arabani dashi please tana me hade hannuwanta dukka tana kuka tana rokonsa ..Ya sake shr yana tunanin yadda zai biyo mata .duk ta inda ya biyo mata sai goce masa ..

Kuka take sosai Akan   a zubar da cikin  domin zuwa  lokacin  cikinta  yakai   watan ' bakwai cif  kennan dan har  cikinta ya dan dago kadan 'tamkar an kifa mata kwarya akan cikin nata.

Sosai ta tada hankalinta har numfashinta Na neman daukewa sbd Yadda ta dingayi  bbu arziki deeni ya dauketa sukayi hospital ,abin takaici suna zuwa basu iske dr saira ba.
 wai bata ma  kasar gabadaya hk suka juyo zuwa  gida zuciyar deeni fes...da yadda Allah Ya tsara  masa komai batare da yasha wahala ba . Akan hamyarsu ma riko hannushi tayi 'cikin nata tana kuka  ,dan girman Allah kada ka maidani gidanka ka Kai wani hospital din ,a markade abinda ciki Na huta wlh baba zai tsine min idan har Na haifi abinda ke 'cikina.

Daidai me gadin gidansa ya bude masa get ya zare hannushi yana juya sitiyarinatar yace   bbu wani hospital dazasuje akan zubd ciki ba'a kamasu ba . 
tana   kuka tace kaine za'a kama ?

Ta Yaya baza'a kamani ba byn da saka hanuna za'a yi kisan Kai tasha kukanta tamkar  Wanda tayi  'cikin shegen gaske  har zuwa   washegari ranar aikin kuka take ita a zubar da 'cikin jikinta  taki cin komai 
Nan deeni yashiga rarrashita wai tayi hkr kawai ta haifi abinda ke 'cikin dan bata sani ba ko shine silar arzikinta. ta Mike tsaye daga inda take zaune tana cewa wlh bazan hkr Na zauna Na haifi 'cikin  shege ba , wata irin janyowa deeni Yayi mata ta fado saman cinyoyinsa ya kalleta  fuskarshi tamkar zaiyi mata kuka yace ki rufa min asiri...sai km Yayi saurin canza salon  mgnrsa jikinsa Na rawa yace  kina jina ko.. ki bar mgnr zubar da  'cikin nan please  . 

Wlh kaji narantse bazan bari ba daga zuwa aiki Na koma gida da tsarabar ciki ba bazai yiwu ba sai dai asan yadda za'a yi da wannan maseefar ..a fusace ya katseta yana zaro mata rikitattun idanunshi kar ki sake nakara jin kin Kira 'cikin nan da maseefa ko wani abu makamanci shege ....ta Mike a harzuke tana masa wani irin duba sannan tace an Kira sa da maseefa maseefa maseefa km shege meye zakiyi min kai bama a son taimakon naka .
Daman can Kai mugun ne kagareni wlh nayi kuskure amincewa dakai amatsayin wanda zai taimakamin tasoma kokarin fixge hannuta daga nashi ,amman ya damki hannun da karfin tsiya yana duban yadda ta hargitse tafita haiyacinta .kasake nace banason taimakon tana wani irin kuka ..

Muryarsa a kasance sannan cike da rarrashi ya maidota jikinsa ya rungumeta tsam ajikinshi yana shafa bayanta ahankali ahankali tare da cewa    am sorry bazan sake yi miki ihu ba .

Yanzu ki natsu  Ga shawara me sauki  idan tayi miki sai mubi .

Ya dagota tare da zaunar daita kan cinyarsa kinga Yanzu Ni bbu abinda narasa Na rayuwar duniyan nan nablah ..
..  komai Allah Ya azurtani dasamunsa a rayuwarta ta fanin arziki da nasaba  Amman  sai Allah Ya jarabeni  ta wajen rasa ya'ya har biyu .
 kinga atakaice  banta samun haihuwa ba kennan ,yashiga yi mata nasihon  masu  ratsa jiki da sanyaya zuciya  da kawo mata misalin  iri iri  ,kinga kema  ba rawa kikeyiwa Allah  ba yabaki 'cikin jikinki ba ,  sannan km ke kanki  kisan takamaiman Wanda Yayi miki 'cikin nan ba ko ba hk ba ?
 Jikinta a sanyaye Ta daga masa kanta  alamun eh .

Ok yanzu idan nace miki. Ki  haifi  'cikin jikinki Ni Ina so kibarmi shi har illa Masha Allahu fa ......?
ta dago  shanyayyun idanunta Tana kallonsa tare da nazarin abinda yace din kana taja numfashi da kyar ta fesar  tace kaima kasan hkn bazai yiwu ba ta cigaba kukanta tana  kokari mikewa daga jikinshi  ya sake  maidaita yana cewa  Karki ce bazai yiwu ba nabeelah ,shine abu mafi sauki a gareki da zai yiwu ,zan taimaka miki Na karbi 'cikin jikinki ke km da zarar kin haihu ki zan sallameki da alkharu masu tarin  yawa ciki ma har da nauyin karatun ki zan dauka har ki gama .
 tayi shr kawai Tana sauraronsa har yagama mgnrsa bata sake cewa komai ba .
,kin amince da wannan tsarin  muryarta a raunane tace bawai bazan iya amincewa bane Amman Ni.. tsoron matarka nake ji idan tasan da haka Ga km ummi   takarasa fadar hk tamkar zata zubda hawaye ....kada ki damu da matata ko first love ,nasan yadda zanyi daita idan mgnr ta fito.
 ke dai ki natsu kawai km ki kwantar min da hankalinki bbu abinda,zai faru inshallahu.
 " kinga nima Na taimaka miki alokaci dakike neman taimako to Ni meyasa bazaki taimaka min  ki haifa min 'cikin jikinki ba ?

Ganin yadda ya narke mata ajiki  yana shirin yi mata kuka yasa  ta kamo tafin hannushi 'cikin nata tana murzawa 'cikin sanyi jiki  kmr yadda Ya sabam mata dashi, muryata cike da shagwaba tace shikennan Na amince , murmushi  sosai deeni ya dinga yi harda Kai hannushi kasan mararta yana shafo dan tudun cikinta.
 ita kuwa sai binshi  da kallo nablah take cike da jin takaicin haihuwar dazatayi bbu aure . idonta har da Hawayen tausayin kanta .
bata rai tayi sosai ganin irin dryr dayakeyi tace kowace matar arziki  agidan mijinta take haihuwa fari . Amman Ni zan haifi 'cikin da ban ma san ko na waye ba.
 hawayen mgnrta datayi  tana kuka shi ya hargitsa masa lisafinsa har ya tsaida dryr murnar dayake  ita kuwa tana ta kukan zuci da badini.

Ya rungumeta tsam  ajikinshi yana tura hannushi 'cikin jikinta sosai yana shafa cikinta tare da cewa  ki bar kukan nan  hk waye yace miki zaki haifi 'cikin jikinki bbu uba ?

Ni zaman me nike kennan ?

ai Ni ne uban 'cikin jikinki yanzu tunda yazama nawa  yakarasa fadar hk yana  kashe mata idonsa daya yana cigaba da murmushin farinciki .

Sake bata rai tayi sosai tare da turo   masa dan tsukaken bakinta gaba   tana kukan shagwaba. ajiyar zuciya ya sauke .

Ya Kai bakinsa ya tsotsi lips dinta yana kallon 'cikin kwayar idanunta shi dai gsky baya son ganinta 'cikin yanayin tashin hankali sosai yayita rarrashita dabata baki har ta hakura ta mikawa Allah lamarinta ....


MMN SUDAIS CE💗💗💗💗💗
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
     💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO 



*wannan shafin sadaukarwa gareki ke kadai domin ,Kin cancanci fiyye da hkn a gurina  Hauwa'u A usman jidda marubuciyar kadddara tah,  gaisuwa tare da fatan alkhari a duk Inda kike , Nagode kwarai  da gaske bisa  kaunarki  gareni ,   nima Ina  kyawun sonki  dajinki har 'cikin raina  irin sosai din nan* 



Page 88


Rayuwar deeni gabadaya ta canza 'cikin Yan kwanakin da basu wace  asharin da wani abu  ba.
 ,rabon shi daya samu kanshi 'cikin  natsuwa da farinciki  irin hk a zuciyarsa har ya manta .
  matsuwa Yayi yaga yadda 'cikin jikin nablah zai bayya ya tona asirin kansa . 
domin hkn shine cikar burinsa.
 " sbd shi ahalin yanzu idan akwai abinda yafi so da kauna bai wuce 'cikin dake  jikin nablah  ba .
 wato burin rayuwarsa   ..... Gama wayarsa kennan da matarsa ya Mike tsaye  zuwa dakin da nablah take .



Jingine take akan makeken  gadonsa  yayinda Wani irin zazzafan  zazzabi me zafi da tsuma gangar jiki , yasamu nasarar cafketa  .
 sakamakon ruwan saman da ake kwana da yini ana shekawa a garin Lagos wanda ya hade mata da yanayin gurin tare da  sanyi gidan glass.
  " cikin rawar jiki ta Kai hannuta ta dan janyo tautausar  blanket dinsa dake nade a gefe daya   me cike dadadden   kamshi turarensa    Wanda yacika mata hanci takoina Yayi Kane Kane acikin  zuciyarta.
 ta lullube sansar  jikinta dashi .
wani  irin numfashin take fitarwa ahankali me gyaraye da zafi zafi zazzabi .
 .
 " yayinda, ta cikin blanket din ta  kudindine jikinta guri daya sosai take rawar sanyi  hakoranta har karkarwa suke  da junansu, har zuwa  sanda deeni yashigo dakin ya tadda  ita 'cikin wannan halin.

 Kai tsaye gurinta ya nufa da sauri  ya haye gadon   hade da zamo da  blancket din data rufa jikinta  dash.
Yayi shr  tare da    tsura mata rikitattun idanunshi kawai  yana kallon yanayin datake ciki .
da kyar tasamu  tasanya hannuta ta  fexgo bargon dayake rike dashi   ta sake maidashi jikinta tana cigaba  rawar sanyi  .
Kana ta sunsukayar da kanta.
  'cikin sarkewar muryarya tace masa Ina wuni... batare da ya amsa ba Yacigaba da kallonta kawai .dan ba gaisuwarta yafi bukata ba ...
 ganin yanayinta yasa shi   
cewa.

  baki da lfy ne ?

 Shr tayi masa itama  taki ce masa  komai tamkar yadda Yayi mata  sannan taki dago idanunta .

 ya motso sosai kusa daita har yana jin hucin zafin zazzabi jikinta,  gabadaya tana jin yadda  gigice ya  rude ajikinta Amman taki dago idanunta ta dubi yanayinsa ..
 yace talk to me now please  what's wrong with you ?
Wasu zafafan hawaye suka cicciko idanuta kawai ta tsinci kanta da gyada masa kanta. Alamun bada da lfy ..
 ,take yaji zuciyarsa tayi  wani irin  matsanancin bugawa da karfe har yasamu kanshi da dafe  tsaitin zuciyarsa da hannuwanshi duka yana cigaba da kallonta  .
Yayinda gefe daya km ya   daura alhakin ciwon nata  akanshi .
Domin da baije  ya   bata  sama da awanni yana  hira  da zeenat dinsa  ba.
, may be  da yanzu bbu wani abinda zai sameta .

runtse rikitattun  idanunshi Yayi sosai yana jin zafi sosai har 'cikin zuciyarsa , tare saukowa Daga kan gadon batare da ya sake  ce mata komai ba .

 " jikinsa a sanyaye ya fitce daga dakin zuciyarsa cike da tsananin tausanyinta Wanda yanzu ya zamemsa jiki . 

Fitar shi da kmr minti shabiyar ya sake shigowa dakin   hannushi rike da Whit  lailon da ruwan roba.

 ,   ya sake hawowa  kan bed din ya   km yaye bargon  Wanda zuwa lokacin tuni ta kwanta ya tada ita zaune km still jikinta  rawar sanyi yake .

ya ballo magani da ruwa .
 " yayi mata alamun ta bude bakinta Amman taki sai miko masa tafin hannunta datayi .
 yasaka mata  maganin tare da jan yantsun hannuta sai  dataji wani  iri ajikinta   sannan  ta saka maganin abakinta Tasha ruwa. 
 tana kokari koma ta kwanta yayi saurin tarota  jikinshi , muryarta  Na rawa  tace please...kabarni  kar ka  takura min dan Allah  ...

ki dan tsaya man maganin ya dan  narke so that sai ki kwanta.
 tashiga girgirza masa kanta tana  kuka da son kwatar  kanta Daga gareshi .
 yasa yadda zatayi dashi ne .
yasa  dole ta hakura ta kwanta lamo ajikinshi  badan taso ba sai dan yafi karfinta.
 gashi ita km bata da wani kuzari ajikinta ..

Kusan minti goma tana rungume ajikinshi ya janyo wayarsa yayi dealing number Dr saira tare da saka wayar a handsfree .

Byn dr ta dauka  yasoma  sanar  mata da rashin lfyr nablah da maganin dayabata Amman   har yanzu zazzabi bai sauka ba .
Ga    rawar sanyi da jikinta  keyi sosai har lokacin .

 Dr saira tace the nest thing  kawai da tana da miji ne .
Sai  nace worming din jikin mijinta zai iya taimaka mata ta dawo daidai Amman tunda bbu kana iya kawota ayi mata injection   .
deeni yayi shr yana sauraron Dr .
kafin daga karshe   yace alright  tare da hanging din Kiran Yacigaba da kallonta .

Runtse shanyayyun idanunta  tayi kawai domin taji duk abinda doctor din tace .
 Ta dinga  jin bbu dadi a ranta domin kuwa duk sanda zasu kasance tare tana jin aranta suna aikata zunubi ne.
 Me girma gaske  tunda tasan ita din ba zaman matarsa take ba sannan ba muharramasa bace . Amman bbu yadda ta iya da rayuwarta akan deeni .
  ko ta nuna masa bata ra'ayin yataba mata jiki ba saurarinta yake ba abu guda dayafi kwantar mata da hankalinta shine  yadda baya saduwa daita .

 Ahankali ya maidaita ya kwanta tare da  lullubeta duka ilahirin jikinta  sosai  kana ya  Mike tsaye  ya bar dakin .

Kusan awa daya tsakani  ya km dawo wa dakin.
  "  Babu komai  sanye ajikinsa sai  Short niker iya cinyarsa da gashin jikinshi dake kwance  luwai sai sheki suke .
  wanda zuwa wannan lokacin tuni nablah ta dade  acikin duniyar gajimare .

 .'cikin bacci kawai taji ana manne mata ajiki da   shafa wasu wurare a sansar jikinta  kmr nonuwanta da kunneta zuwa wuya da yake aikin gogawa gashin fuskarshi .

ahankali tasoma bude shanyayyun  idanunta har ta budesu duka cike da mayen bacci .

Deeni  tagani  manne da jikinta yana wasa da albarkatun kirjinta da iyakacin karfinsa tamkar wani maye . 

Ciki wani irin mutuwar jiki  tasoma son raba jikinta dashi ,yasa hannushi duka  ya fexgo 'cikin jikinshi sosai ya matseta gam tare da kai bakinsa 'cikin kunneta .
ki natsu man bbu abinda zan miki fa . 

Yacigaba da mgn  ai kin dai ji abinda doctor tace  kina bukatar taimako some one like me ?

 Tasoma girgirza masa kanta, alamun a'a .

Ya dakata da abinda yake mata  tare da kunna dum light din daki ya tsurawa  beauty face dinta idanu , kana yace kin taba ganin nazarta iya abubuwan danake miki ?
Ta girgirza masa kai batare da tace komai  ba .
to ki Bari Na taimaka miki kmr yadda Dr tace . Sbd jikinki ya dawo normal .

Muryarta  a sarke tace A'a ni gsky bana son kusancinmu tare  guri daya ,wlh domin yin hk ya haramta a tsakaninmu ..

Ya dage mata girasa daya yana cigaba da kallon 'cikin  kwayar idanunta sannan yace is Ok ki Bari nataimaka miki yau kawai  so that , today  will be the last day da zan km rabar jikinki .
,yana karasa fadar hkn ya sake  janyota 'cikin jikinsa sosai har tana jin dumin jikinsa naratsa kowane shashi Na gangar jikinta.
 tare da   zarcewa   da aika mata da wasu zafafan  salon wasannisa Wanda ke  sakata manta ko ita din  wacece sannan km da Wanda suke tare .

 ahankali ya rabata duk wasu  kayan dake sanye ajikinta shima ya zame short niker dinsa..
 Suka  saura Daga  zigidir haihuwar iyayensu . Be tsaya westing time ba 
 ya  daura hannuwanshi duka yazagaye nonuwanta dasu yana murza kan nipply dinta ahankali ahankali ta yadda zai mantar daita ki da ranshin son abinda yake mata.

  sosai yake murzata da murza kan nipply dinta yana lumlumshe mata  idanuwa . 
  "ahankali ya zira harshensa ciki kunneta yasoma soucking din 'cikin kunneta sosai  tare da cigaba da murza kan nipply dinta.
Take taji gabadaya duk wata kafar gashi dake jikinta sun Mike tsaye ....
  'cikin jin wani  irin yanayi ta manne mishi ajiki , tasoma aika masa da martani 'cikin irin abinda  dayake mata .
tasoma murza kan nashi nipply din da  shafa gashin dake kwance saman fadadden kirjinsa.
  ,wani irin shock deeni  yaji yana yimasa yawo sansar  ajiki  may tattare da shaukin dadi .
Komai Yayi masa ruf da dugu .
abinda bai taba faruwa ba kennan atsakaninsu romancing din jikinshi  a zahirance km  idanunta biyu .
 ",hkn yasa gabadaya yanayinsa ya sake sauyawa , ya rude ya susuce yafita haiyacinsa gabadaya  tare da sake damko nonuwanta sosai yana murzawa ,a halin dayake jin kanshi da badan kada ya rusawa kanshi shiri ba.
Da  Yayi me gabadaya kawai  domin yasan ko yace zai zarta hkn ma bazata hanashi ba a yadda yaga halin data afka ,kwana Yayi yana murzata batare da Yayi wani abu daita ba. Km a hakan shi yasamu bayan bukatarsa atare daita batare datasani ba .
 

 Firgigib zeenat ta farka Daga mafarkinta wai Ga mijinta can tare da wata suna saduwa da junansu  tamkar  wasu ma,aurata  ,Wanda har ta farka Allah Bai nuna mata fuskar matar ba .
ta Kai idanuta ta dubi Inda ummi ke zaune tana lazami ta fashe da wani irin matsanancin kuka zuciyarta Na bugawa da sauri da sauri ,kardai yakasa hakuri da kanshi ya fada 'cikin duniyar neman mata ,hankalinta Yayi mugun tashi .
Ita kan kanta ummi Gani yadda zeenat ta farka a frigice yasa tayi saurin Kai karshen  laziminta  ta Mike zuwa gareta tana tmbyrta .

Nan ta km fashewa da wani kukanta takasa fadawa ummi komai game da mafarkinta ummi tayi shr tana nazarunta kafin tace mata mafarki kika yi ne mamana ?

Zeenat ta Daga mata kanta Ok kiyi addu'a ki kwanta mafarkin alkhari daga Allah ne yayinda mafarkin sharri km daga sheidan ne  ta bude baki muryata cike da kuka tace ummi Ni Nigeria nake son komawa wlh Ina ji ajikinna   wani abu mummuna nashi rin faruwa dani takarasa mgnr tana sakin wani kuka .

Ummi Ya isa kuka bbu wani mummunar abinda zai same ki sai alkhari kinji mamana ki natsu sosai may be kin kwanta batare da kinyi addu'a ba ,km Yawancin mafarki ba gaskiya bane nan dai ummi tayi ta rarrashita har tasamu ta natsu ,tare suka koma bacci Wanda baccin zeenat yazama rabi da rabi ,dan da zaran ta rufe idanunta matar take Gani rungume ajikin mijinta .....

Washegari da safe


Koda Nablah ta farka bata Ga deeni kusa daita ba kmr yadda tayi bacci tabarshi manne a  jikinta ba .

Wanka tayi jikinta bbu kwari ,tasaka  wasu hadadun English wear's mai igiya  abaya .
tunda Daga   kasanta  har  sama .

yayinda gaban rigar yake cure guri daya  Wanda ya fidda asalin kirjinta ta dauko bomshort dinta tasaka Wanda ya zame mata jiki koda kuwa kayanmu Na hausa fulani zata saka sai tasakashi ..

Ta gyara sumar kanta dake baje tare da shafa masa oil tasaka babban rebom ta tufke gashinta a tsakiya ta gabanta km ta dibi wani gashin ta murdashi sosai tayi tustin, kana ta sake shi.

 ta dauki turarikansa masu dadin kamshi ta fashe ilahirin jikinta dashi .
tasaka jumbulelen hijab din Wanda ya rufeta har tsinyar kafafunta kana ta ziro hannuwata waje  .

Ahankali ta sauko parlour gidan  bata Ga deeni tayi shr tana tunanin inda yaje hk . Ta daga kafafunta ,
Takarasa ta kuna TV ta kamo tashar suna TV Inda ake gabatar da karatun alqur'ani mai girma, tun daga fatiha zuwa Nas  .
A hankali  tasoma bin karatun tare da shigewa 'cikin  kitchen.

 tunanin abinda zata daura tashigayi ga dai komai nan Na amfani a kitchen din, Amman bbu abin sarrafa Na abinci .

hankali zuciyarta ta yanke mata  hukun da tsayuwar datake ko ruwan tea ta daura .

Jona ruwan zafi tayi taja ta tsaya tana karewa kitchen kallo duk da ba wannan bane  karonta Na farko data  taba shigowa ba.
 Amman duk sanda zata shigo sai taji ya burgeta har tayiwa kanta sha'awarsa.

 dowawarsa kennan Daga dan fitar da Yayi domin samo mata abinda zataci hannushi duka rike da ledodi ya ajiye a dining tare da nufar dakin dayabarta kwance  Amman bata nan .
ya dan zauna Jim zaman jiranta, wa tunaninsa ko tashiga bathroom ne .
 nan ma yaji shr bbu alamun hk ya km mikewa ya  dawo parlour bai ganta ba .
Kamshin turensa datayi amfani dashi ne ya sanar masa da Inda take .

Itama datake tsaye 'cikin kitchen din taji gabanta ya fadi xuciyarta tasoma rawa sakamakon jin takunsa Ahankali  zuwa Inda take ta fara tattara duk wata natsuwarta guri  daya ta sanyawa jikinta. bata son abinda zai yi sanadiyar haduwarsu guri daya ko hada idanunsu sbd abinda ya faru atsakaninsu daren jiya tasoma tuno yadda ya dinga juyata akan bed yana aikin romancing dinta tuno hkn km yasa komai Na jikinta ya sauya tasoma jin wani irin reaction atare daita from no where bata ankara ba taji sautin muryarsa 'cikin dodon kunneta.

 me zakiyi ?

Keda baki da lfy muryasa ta katsemata tunaninta shr tayi batare da tace masa komai ba sai shanyayyun idanunta data zuba masa tana kallonsa.

 ki fito Ga breakfast can Na kawo miki Karki daura komai asalima bana bukatar naga kin km shigowa  kitchen din da sunan  dora wani abu .

Bazan tayi masa tare da dauke idanunta akanshi tacigaba da abinda take yi shima ya juya ya koma parlour kusan minti biyar yana jiran fitowarta bata fito ba ya sake biyota kitchen din .

,yayinda hkn Yayi daidai ta dauko kettle   ruwan zafi Wanda ta jona ruwan tea aciki ta juye 'cikin glass  Flak's din ta dauko zata rufe taganshi tsaye agabanta  Wanda ganin yanayinsa  Yayi sanadiyar da xuciyarta ta harba da sauri tashiga baguwa.
 ,zuciyarta km  tashiga rawa rawa Daga bugawar datake sbd  ganin irin kallon dayake binta dashi mesaka mara jin mgn shiga hankalinsa .

Ke..... banson iskanci da taurin kai fa kodan kinga Ina lallabaki sbd 'cikin dake  jikinki shine iskancinki yake son girmama.

 ko Ni ne mutumin da Yayi miki ciki ?

ya jeho mata wannan tmbyr da muryarsa datake a tsarke  .

 Tayi saurin girgirza masa kanta . 

To me nagaya miki ?

, Zuciyarta cike da matsanancin tsoronsa  yayinda  muryarta cike da  rauni  tace. Kace  nabar aikin .

Ok  Ban isa bane shiyasa kika cigaba dayi  ?

Nan din ma  girgirza masa kanta tayi .
,
To wlh  kishiga hankaliki dani tun ban canza ra'ayina ba,
 na fasa yin taimakon ba .

Yana gama fadar hk bai tsaya batawa kanshi lokaci ba , yajanyo hannuta da niyar fito daita Daga kitchen din  gabadaya ta zube masa ajiki sukayi kasa luuuuuuuu ... lumshe rikitattun idanunsa Yayi sosai  yana shakar kamshin turarensa Wanda ke  gauraye da kamshin jikinta.
 sai ma yaji cent  din kamshi turaren  ya fita daban ya sauya ajikinta  .

Kokarin son kwace jikinta anashi tayi Amman sai taji yasa hannuwanshi duka yazagaye kugunta dashi yakara mannota da jikinshi  yana sake lumshe rikitattun idanunsa.
 tare da sakin wata naunauyen ajiyar zuciya yasoma yawo da hannushi ajikinta muryarsa a kasalance yace kitchen din ma sai

 kin shigo da hijab ?

Yacigaba ki dinga hutawa kanki da sanyashi hk man , domin duk da saka shin din da kike bashi ya hanaki yin ciki ba ..

ranta Yayi mugun  bace da jin abinda yace mata  taja tsaki .
..tana me turo masa dan karamin  tsukaken bakinta tare da zabga masa wata uwar harara .

Shima yana gama fadar mgnrsa yazarce dasoma kokarin  cire mata hijab din jikinta gabadaya  ,ta kwakumi hijab din tana saki kara sbd kayan dake sanye ajikinta, tare da cewa yanzu Ina ruwanka

 da hijab dina sbd Allah ?

Kabarmin abunda dan Allah  ,cikin jikina km da kake mgn  kasani ba'a yawon banza nasamu ba dazaka zo kana wani  cewa duk wani saka hijabin danake bai hanani samun ciki ba, takarasa fadar hkn tana sake  yunkuwa domin raba kanta dashi .dan tasoma tsanar maita da naci irin tashi kullun burinsa ya rabi jikinta .
 , uhmmmm ..Na fiki sanin ba'a yawon banza kika samoshi ba yakarasa mgnr yana zarcewa da cire mata hijab din dake lullube da jikinta wani irin shock   yaji alokaci guda  abu biyu suka shiga  yawo acikin brain dinsa, tare da circulating kaiwa kowani shashi Na  sansar jikinshi farmaki ,jin dirin dukiyar fulaninta da km  yanayin shigar jikinta.
 Wanda shine ya  tsiyo mata kayan.
 take ya hadiye wani miyo daya tokare masa makoshinsa ya tsura mata rikitattun idanushi yana kallonta ba yau yasoma ganinta 'cikin irin  wannan shigar ba sakamakon duka kayayyakin datake sakawa shine ya tsiyo mata sannan ya dauke doguwar rigar datazo dashi ya boye kawai dan yafi son ganinta hk. Amman km shigarta ta yau tasha bambam da koda yaushe tare dashiga rai da  daukar hankali .

Sannu ahankali 
Yasoma jin yarinyar tana shiga ranshi sosai fiyye da tunanin me karatu ta dinga   bin kowane shashi Na gangar jikinsa. Ta zauna daram acikin memory dinsa .


Take km yashiga yawo da hannuwanshi a sansar jikinta tare da mammatsa mata jikinta tamkar yadda akewa mutun tsusa.
 itama lumshe shanyayyun idanunta tayi sannan ta budesu  ta zubesu 'cikin nashi suna fuskantar junansu.

 muryarta a shagwabe tace wai meyyasa kake son yi min irin  hk  ne ? 



Ya dage mata girasa daya alamun shima bai sani ba.
 ,ta zabga masa  harara tare da   cewa wlh   kasani  sani .. dayake tagane nufin abinda yayi  mata din .
,ya kashe mata idonsa daya yana cigaba da romancing din jikinta Hankalinta yasoma kololuwar gurin tashi takoina ajikinta wani irin feelings take jin  yana mata yawo, gashi tana jin yadda kasanta yasoma jikewa alamun tasoma tsiyaya.
 tarasa wani irin mutun take zaune dashi  shi da Sam baya gajiya da romancing din jikinta. wani lokacin idan ta tsinci kanta 'cikin tunaninsa da tunanin irin  abubuwan dayake mata kawai zata tsinci kasan  tajike  jagab tana tsiyaya. tasoma  tunani ko dai shine mutumin dayayi mata 'cikin dake  jikinta?

 Amman km  idan ta tuna ai shi bai taba kusantarta ba sai wannan tunanin yakau a zuciyarta.
Sam deeni  yakin barinta Yacigaba dayawo da hannushi Daga karshe yazaro Brest dinta daya ya daura bakinsa kan nipply dinta yasoma lasa da harshensa  yana tsotsa tare da lumlumshe rikitattun idanunshi .... 
 itama sosai take jin dadin abinda yake mata wani sabon fellings ne yatasomata  yayinda a zuciyarta ke  cike da fargaba yadda yake mata tamkar wata matarsa  ko karuwarsa, shi kwata kwata  baya fargaba ko jin  tsoron taba lafiyar jikinta ,km duk Inda yagama ajikinta tabawa yake Kai tsaye batare da wani shamaki ba ,
Wani lokacin abubuwa sa sukan tsaya mata arai har tadasa ayar tmby akansa ?

Sosai yake tsotsar nonota tare da kokarin ciro dayan da  hannushi daga mazauninsa , batare da yasaki  dayan  brest din nata ba, taji wani irin karfi yazo mata ta turesa gefe 'cikin rashin sani flask din dake cike da ruwan zafi ya fado masa a kafarsa .

Ya daga karfasa da ruwan zafin ya zube masa yana jin wani radadin  ciwo, gurin maida kafar Ashe kan glas din flasks din ya dauro batare da saninsa ba,   zaro rikitattun idanunsa Yayi waje tare da zuba mata idanunshi kawai yana kallonta batare daya nuna  alamun jin zafe ataredashi ba ,ta Mike da sauri jin faduwar flasks  .
zaro idanuta tayi itama tana kallon  'cikin kwayar idanushi ganin ruwan zafin ya wanke masa kafa Ga km kwalba flasks din tashige masa kafa  har guri biyu .


Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun .

ta dinga furta 'cikin kasalliyar muryata da mugun sauri takaraso gareshi Hankalinta a tashe tana tmbyrsa bai ji ciwo ba ,byn km Ga ciwon tana Gani a zahirance .

Rikitattun idanunshi kawai ya xuba mata yanacigaba da kallonta duk ta rude tarasa yadda zatayi da ranta gurin taimakonsa.
 Wanda shi km duk Inda tayi binta yake da idanunshi yana jin tana sake shiga zuciyarsa da rabashi da duk wani abu dayake takama dashi. sautin muryarsa taji .
Kizo ki cire min kwalbar.... ta dago shanyayyun idanunta da suka ciccika da ruwan hawaye ta  zuba 'cikin nashi idanun  da suke dauke da rikice iri iri najin zafin  raunin ciwo tare da  girgirza masa kanta alamun bazata iya ba.

 muryarsa washagwabe  wannan karon yace dan Allah ki taimaka min  kiciremin zafi nake ji sosai . yayinda zuwa lokacin tuni ruwan hawaye dake idanunta sun soma tsintirin tureneniyya zubowa kan kuncinta  tana hawaye jikinta Na kirrrrrrma ta dawo  daidai tsaitin kafarsa ta Kai hannuta kan kwalbar data shigar masa kafa .
Muryasa  a sanyaye yace cire min da sauri please tun nima ban sakar miki kuka ba ...tana fezgewa ya runtse idanunshi gam yana cewa washhhhhh washhhhhh ..Allah nah sannun ahankali ta cire masa dayar kwalbar dake kafarsa take jini yashiga ambaliya Ga km ruwan zafin daya zube masa akafa ganin yadda jinin ke zuba ya sake Daga mata hankali.

 tashiga kuka sosai tana kallonsa shi kam ko ajikinsa ganin halin yadda ta damu da ciwonsa ya fimasa komai dadi arayuwarsa.
 yasan ko bbu komai zuwa wannan lokacin yana da wani muhalli acikin zuciyarta. kallonshi tacigaba dayi tana kuka duk da dauriyarsa tayi maseefa birgeta Amman har kasan ranta take jin tausayiinsa Na ratsa kowane part Na gangar jikinta da jinin jikinta.

 muryata cike da kuka tace dan Allah kayi hakuri wlh  nasan duk laifi nane.

 da ban tureka ba dabaka kone ba da jin ciwo.

 kayafe min dan Allah 

ka yafe min..
..  ka yaFe min  Allah bansan hk zata faru ba .


Dan tsukaken  bakinta kawai yake kallo yadda lips dinta ke juyawa idan tana mgn .
wani tunani yazo mata take 'cikin rawar jiki tasoma tofa masa addur kuna akafarshi ,KULNA YA NARU KUNI BARDAN WASALAMUN ALA IBRAHIM ta dinga maimaiwa  agurin ta dauki sama da mintina 30 durkushe tana karanto masa addur a .
yaji dadi Sosai har 'cikin zuciyarsa  yake jin hkn har ma yaji ya daina jin radadin ciwon kafarsa .
 yasa hannusa  janyota tare da dago da fuskarta suna fuskantar junansu idanushi ya kada Yayi jawur jijiyo hannushi suka Mike sukayi rada rada .
ta tuna sanda ta taba ganinsaa 'cikin irin wannan yanayin lokacin da kb ya furta mata kalmar so .
hkn Na nufin ko yanzu ma ranshi a bace yake ?

Wani irin tsoro ne da frigice ya ziyarci zuciyarta ahankali ta km yunkurin bude bakinta da kyar  gurin sake bashi hkr dan Allah kayi...batakarasa fadan abinda bakinta  Yayi Niyya ba , taji bakinsa kan nata wani irin perfect unexpected kiss yashiga bata lips to lips mouth to mouth cak komai ya tsaya mata duk wani jijiya dake jikinta da naurorin dake sarrafa duk wani motsin jikinta suka tsaya , kwalkwaluwarta ta daina aiki .
bugawar  xuciyarta ya tsaya cak hannuwashi duk ya sanya ya tallabo wuyanta tare da sanya kwaryar idanushi 'cikin nata .
yana kokarin fahimtar da wasu abubuwa masu wuyar fassarawa.. ahankali yashiga kising din lip's dinta Daga bisani yazarce zuwa 'cikin bakinta ya dinga tsotsan harshenta  tamkar wacce za'a kwace masa ita sosai ya tsotseta tass jin numafashinta yana neman tsayawa ne yasa shi sakar mata 'bakin yana fexgo numfashisa da kyar .
kyakywar mazauni Yayi mata akan cinyarsa yayinda   kowannesu  zuciyarsa ta dulmiya 'cikin duniyar tunani.
 Da sake sake iri iri kokari Yayi gurin tattaro natsuwarsa ya dawo daita  jikinshi  ya zaro wayarsa  daga  aljihun gaban  rigarsa yasoma  dealing number sule direbansa.
  sule Na dauka Yayi gaisuwa bakisa Na rawa  batare da deeni ya amsa masa ba da mamaki nablah ta dinga kallonsa yadda taga ya daure  fuska tamau yasoma mgn 'cikin  kausarshiyar muryasa ,kaje kataho min da dr saira yanzu yanzu nan..

 muryar sule direba Na rawa  rawa ganin deeni Na yana kokari  katse Kiran yace zuwa wani gidan kennan boss ?

A hassale yace zuwa sabon gidana yakarasa fadar hk yana hanging din Kiran tare da cigaba da dubanta yana sauke numfashi kana ya Kai bakinsa tsaitin kunneta yace zaki iya min wani taimako ?

Tayi saurin Daga masa kanta alamun zatayi .

ya sake sausauta muryarsa can kasa sosai ta yadda zai sake kashe mata jiki yace ki taimaka kije kici abincin nasan kina jin yunwa..
Tace uhmmmm wlh  bana jin Yun...shiiiiii bana son mutsu ke dai kije kiyi yadda nace tayi shr kawai Tana wasa da yatsun hannunta batare da tadaga  Daga Inda take ba .

yasan halinta tunda tayi irin wannan shirun nata batashi zatayi ba dan hk ahankali .....



Please kuyi hakuri da typing errors banyi editing ba 


MMN SUDAIS CE
 AUREN SIRRI
     💖💖💖
💗💗💗💗💗





AYSHA A BAGUDO



*Jinjina gareku group Na  kainuwa writer's lallai Ku masoya nah ne  Wanda duniya tabari  nasan da zaman  hakan batare da Ina cikinku ba, hakika  bagudo na yinku  sosai da sosai km  ta yaba da kaunarku gareta sannan tana  alfahari daku a duk inda kuke ,domin Kun cancanci fiyye da hk agarenta ,sosai kuka shiga    raina  ba karya,  Ku din masoya ne, na daban,  Ina matukar jin dadin  yadda kuke kaunar labarin AUREN SIRRI wannan shafin sadaukarwa ne Ga duk wace take 'cikin group Na kainuwa writer's Nagode sosai  Allah yabar zumunci da kauna inshallahu km  ana taren tare*🤝🏻🤝🏻🤝🏻 





Page 89



A hankali ya yunkura zai tashi daita ajikinshi, tayi saurin Kai hannuwanta dukka ta zagaye cikinsa dashi 'cikin raunanniyyar muryarta tace please deeni ..........
 ka zauna kada ,ka fama ciwonka man  ....dole Tasa ya koma ya zauna ba dan yaso ba.
  " sai  dan gudun  abinda zai  sameta idan ya matsa lallai sai yatashi da karfi kmr yadda yayi Niyya ...yadda take kwance  ajikinshi yasa yakara jin gabadaya notikan dake daure da jikinsa  suna  neman kwance masa da son fallasa abinda ke boye 'cikin  zuciyarsa  wanda hkn km zai iya jawo afkuwar komai atsakaninsu batare daya shirya yin hkn ba ,kamo lips dinsa na kasa  yayi yasoma  ciccizawa ahankali ahankali.
 ,wani irin  zazzafan shaukinta yake sake  jin yana bin jini da "bargon jikinsa yana bayawa kowane part Na ruhinsa sako na musamman ..
ahankali ya runtsa rikitattun idanunshi sanda yaji ta zare hannuwanta ajikinsa tana sakin numafashi da kyar tamkar me cutar asma .

Idanunsa ya tsura mata yana kallon cikin kwayar idanunta dake walanniya  da  aikin  jujjuyawa, sosai ya tsura mata idanushi kawai Yana aikin kallonta.
 hk kawai    ya tsinci  kanshi da kasa  ce mata komai sai ma Kai hannuwanshi da Yayi  yakamota ya  mannota da kirjinsa yana sakin naunauyen ajiyar zuciya .kana  yakai bakinsa  daidai shashin wuyanta yana shinshinawa da sumbatar duk inda bskinsa yaci karo dashi , hade da  goggomata gashin dake kwance a fuskarsa .

jin Yayi  saitin kunneta yasa  ta dago hannuta 'cikin mutuwar jiki a dan tsorace ta dora akan bakinsa sbd kwata kwata bata shirya jin abinda yake son fada mata ba.
 'cikin sarkewa muryarta tace please kayi hakuri man.
 sbd Gani irin kallon dayake antayo mata ...

 lumshe rikitattun idanunshi Yayi  yana shakar kamshin tafin hannunta mai taushi  akan bakinsa .
 "ta kula da yadda yake yi din km  tasan bakaramin aikinsa bane ya canza salon yanayinsa zuwa zafafan wasannisa masu hautsina mata lissafi .
dan hk tayi sauri zame hannuta ahankali zata tashi da sauri Ya rukunkumeta ajikinsa tare da shafo wasu wuraren a sansar ajikinta kana ya dire" hannuwanshi duka  akan tudun nonuwanta  da suke cike bammmmmm dasu abin sha'awa da bukatar kowani cikakken namiji, ahankali yake   shafo saman nonuwanta yana lumshe idanunshi ,   ta dan saki kara 'cikin sanyi muryata mai dadi tare da  cewa . 

Wayyo  NASU...RUL..DEENI zan suuuume ..me .. maka  fa ...

Har 'cikin kasan zuciyarsa yaji maganarta tashigeshi "ya rinka jin wani irin abu me kama da  sonta yana kara fizgar zuciyarsa gareta  .cike da kuzari 
ya sake rukunkumeta sosai ajikinshi yana mamakin wannan abu  dayake tawainiyya dashi akowani lokaci koda kuwa baya tare daita .
 'cikin natsuwa km yashiga  mamakin yadda Sam bata shakkarsa , kalli yadda ta ambaci sunansa yanzu kai tsaye batare da wani tsoro  ko fargaba ba .
Wanda  ba duk mutane ke kiransa da sunan Kai tsaye ba ......

Ita kuwa tsoro ne yakamata  domin ita kanta ji tayi kawai sunan nashi ya fito daga bakinta batare data shiriyawa hkn ba.yawo yashigayi da hannushi a sansar jikinta batare da Yayi la'akari da irin raunin dake kafarsa  ba .
 rasa yadda zatayi dashi ne yasa tasoma mutsun mutsun ajikinshi  tare da ce  masa tana jin yunwa ,tasan yanzu zai kyaleta.
Hkn ce  kuwa ta  faru dan sausauta rungumarta Yayi yana sakin  numafashi da kyar.
 ya juyo da fuskarta daidai tashi suna fuskantar junansu sosai yayinda kowanensu Na shakar numfashin juna  atare suka lumshe idanuwansu take km  zuciyoyiinsu suka shiga bugawa atare muryarsa cike da shaukinta.

 yace a Ina kika San sunana hk ?

Tayi shr tana tunanin inda taji sunan  yayinda gabadaya zuciyarta ta cika da  frigici da  tsoron tmbyr da Yayi mata  idanunta suka soma ccikowa da ruwan  Hawaye. 

 Muryarsa a kasalance yace ba kuka nace ki min ba ,amsa kawai zaki bani . Ina kike San complete name di na ?


Muryarta cike da in ..inna tace uhm ammm daman ajikin hotonka dake manne a dakin sama nagani .

Ya lumshe rikitattun idanunshi yana cigaba yawo da hannuwanshi ajikinta yace  Kinsa kuwa  kin fi kowa iya sarrafa harshenki gurin iya Kiran sunana ....yakarasa fadar hk yana bude rikitattun idanunsa masu kashewa Mata sansar jiki.
 
Ta tsurawa kwayar idanushi ,idanunta itama  kawai Tana kallon yadda Ya dawo mata tamkar wani karamin yaron goye  sannan ta bude bakinta da kyar  .

,kowa fa kace ?

Ya kashe mata idonsa daya alamun hk abun yake .
"abinda ke sake narka da zuciyar nablah kennan har ta manta da Wanda take tare ,ta dinga jinsa ajikinta   tamkar shi din nata ne na har abada.

Yayinda  mgrsa Tasata jin kmr  ana mata wanka da ruwan sanyi ne .
 ,har da ummi da aunty ze...cak  ta katse harshenta gurin karasa mgnr  take km gabanta ya yanke yashiga  dukan uku uku sakamakon tunowa da zeenat din  datayi .

da tuna ashe fa deeni datake tare dashi ahalin yanzu  mijin wata  ne, wanda  tafi so da kauna fiyye da  komai dake 'cikin rayuwar  duniyar nan.
Shine  ,take tare dashi  har take rayuwa dashi tamkar wani  mijinta . 

Ya kika yi shr yarinya
kikarasa Kiran sunan matata man ?

Ta runtse idanunta Tana jin yadda bugun zuciyarta ke sake karuwa kirjinta Na mata wani irin  zafi da radadi Wanda tarasa name ne ?
 
Ok bazaki iya karasawa ba ,sbd kin fara  son mijinta  ko ?

Ta bude shanyayyun idanunta  da suka gama canzawa tsabar tashin hankali data tsinci kanta ciki  ta watsa su 'cikin   kwayar idanunshi kana ta girgirza masa kai wasu zafafan  hawaye suka samu nasarar  biyo kuncinta .
Ya dan yi murmushin  gefen baki yana me kamo lips dinsa na kasa yacigaba da ciccizawa  ahankali, sannan ya sauke ajiyar zuciya da karfi.
  
Kina  kishin    matata ko nablah  ?

 Unexpected taji ya jiho mata tmbyr tun bata gama  jimamin wancen ba ..


Muryarta a matukar sanyaye tace a'a wlh bana kishi matarka  sannan km bana jin sonka 'cikin zuciyata Ni kaina bansan abinda yasani kasa karasa Kiran  sunan nata ba .
 ya girgirza Kanshi  kawai domin sanin dalilin dayayi ,kana yace  zaki sani ne inda lokacin hk Yayi .

  dan kin rigada kin  makaro yarinyar  tuni soyayyata tagama da zuciyarki tsab "kin fada  'cikin  tafkin  kogin  son mijinta kin nutse  kiris ya rage miki  zuciyarki ta mace akan shaukin soyayyata  ....Ya fadi hkn yana me sakar mata  killing smile dinsa me sake kashe Mata ilahirin  jikinta akanshi.

 Allah Ya tsareni da macewa akan sonka deeni   ta fadi hkn muryarta  cike da kuka tana mikewa tsaye ahankali yayinda wasu Hawayen takaicin mgnrsa suka sake  biyowa kan  kuncinta.
 " kalli yaddda kike kuka nablah akan soyayyata da kishin matata Amman kice a'a .
, wlh Ni ba akanka da wani banzar kishin matarka nake kuka na ba.
 Ni.. Ni ..abinda yasani kuka daban ne takarasa fadar hk muryarta cike da in inna ,yayinda  wasu siraren Hawaye suka sake  silalo mata .

ya Miko mata yatsun  hannushi alamun ta taimaka masa ya Mike tsaye , bbu wani  mutsu ta Miko masa tafin hannunta duka.
 ya riko nata hannuwan  cike  da wani irin sabon  shaukinta , ya Mike  tsaye  yana Kiran washhhhhh washhhhhh ita km ta damke yatsun  hannushi sosai tana mishi sannu dan a tunaninta ko zafin ciwon ne yasakashi yin hkn  .

Ya gyara tsayuwarsa da kyau yana rungumeta ajikinshi muryarsa can kasa kasa sannan km cike da matsanancin shaukin feelings yace ok gaya min abinda yasaka ki kuka yanzu ...?
 
Ni km idan kika gaya min wlh  na miki alkwarin bazan sake aikata miki shi ba , ballanantana har yasa  kiyi asarar hawayenki akanshi ..

ta girgirza masa kanta kawai tare raba jikinta dana shi tana fezgo numfashi ..kana muryarta a shagwabe tace Ni muje yunwa nake ji...

Hannuta 'cikin nashi suka nufi parlour,n ta nufi kan kujera dashi da niyar zaunar dashi ,taji  yace Kai Ni  dinning ..
 can din ta kaishi ya zauna da kyar yana sake Kiran washhhhhh Allah nah ...  yayinda   jini ya dinga diga tun Daga kitchen har zuwa dinning area ..har zata zauna ta tuna da bbu komai lullube  ajikinta.
 ta sake komawa cikin kitchen din ta dauko hijab dinta ta zira.

ta sake fitowa  hannunta rike da wani dan karamin  towel Wanda tagani a rataye  kitchen din.
 da moupystick tana goge jinin daya bata gurin .
tana kallon yadda Ya tamke fuskarshi tamau ya hade rai yana zabga mata harara  tamkar bashi ba.
 ko km Wanda aka aikowa da sakon  mutuwa .
, har takaraso gareshi ta daga kafarsa mai ciwo ta tasaka towel din a karkashin kafarsa Bai ce daita komai ba ,dan yana jin wani irin mugun  haushi ,da duk  wani aikin wahalar dazatayi ahalin yanzu .yayinda yake jin zuciyarsa yanzu zai iya zamemeta tamkar bawanta akan cikin jikinta .
Ahankali   ta zauna tasoma yin  breakfast din 'cikin natsuwa  tana dubansa da mamakin sauyawarsa alokacin.

Byn kmr minti shabiyar sai Ga wayar sule direbansa, yace gasu sun karaso, muryarsa a dake yace ok ,ya dan juyo yana kallon inda nablah ke zaune ta zuba masa shanyayyun idanunta  ,ki tashi ki koma daki abinda ya iya ce mata Keenan .

,haushi da takaicin yadda yayi magana yasa ta   Mike a zabure zata tashi yayi saurin   runtse rikitattun idanunshi gammmm  yana Kiran sunanta 'cikin sanyayyiyar muryarsa na..bee..lah .
Ta amsa da Na'am tana me zagayowa    daidai indayake zaune  .
ta tsaya itama tana dubansa ,har sanda ya bude idanunsa ya zube su 'cikin nata .

Kina ji ko.. ki dinga bin jikinki  ahankali please... so that maganin da kike Sha zaifi saurin yin aiki ajikinki ,ta yadda komai zaizo mana  'cikin sauki Amman idan kina zabura irin hk fa akwai matsala .

,taji dadin abinda yace sosai har haushinsa dataji, azuciyarta ya ragu    ,ko bbu komai tana matukar  jin dadin yadda yake nuna kulawarsa akanta shiyasa wani lokacin  take manta kanta da mijin wacce take rayuwa har ta dinga  jinsa 'cikin  ranta, sbd Yadda yake tsananin yin kafa kafa  da 'cikin jikinta  , muryarta a sarke tace Nagode sosai da kulawarka gareni  km inshallahu zan dinga yi ahankali ..

Ya lumshe rikitattun idanunshi tare da cewa Karki damu  kije kisha magungunanki ,ki kwanta ki dan huta tace to tana me kokarin barin gurin.
 ya juya ahankali  yabi bayan da wani irin mayataccen kallo me cike da tsansar sha,awarta .


Byn kmr minti goma ya Mike tsaye da kyar yaje ya bude glass door din  yana me  baiwa Dr saira hanyar shigowa ciki waw tun bata karasa shigowa ba sbd Yadda tsarin gidan yayi matukar birketa .

Tashigo ahankali  har da sule Wanda ya dawo shima  tamkar wani bagidajen dan  bakauye dashi  tsabar kallon tsarin  gidan ,duk da yasan sanda aka fara ginin gidan.da sanda aka ganashi  Amman Bai dauka tsarin gidan  zai kasance irin  tamkar akasar turai ba . ahankali yashiga furta Masha Allah lakuwata illa billah

Deeni Bai bi takan yadda yaga sule ya rude yana  kallo da wage wage gidan ba.
 ya zauna rigingine akan two star  yana nunawa doctor  saira dake tsaye har lokacin gurin zama.

 ta zauna tana gaishe shi  tare da tmbyr me jiki ,yace taji sauki sosai.. sule ya juyo da sauri tare da  cewa , boss waye km  bashi da lfy ?

Deeni Ya yatsina  fusaka yana watsa masa wata uwar  harara kana yace ba'a sani ba .
 "km wlh mlm kada ka sake ,kayiwa mutane wasu  saqagogun  shirmeka  anan .

Sule yace sorry boss baza a sake ba da izinin Allah Amman fa gidan ya kero iya keruwa Allah sanya alkhari da zuria masu albarka.

 deeni Bai San sanda yace Ameen  sule Nagode sosai .
Ashe dai kana da  hankali wani lokacin ?

Sule ya washe bakinsa  yana dry jin dadi abinda boss dinsa yace .

Deeni ya bukaci dr saira ta fara duba mishi kafarshi tare da mata bayanin abinda yasame shi.
 takaraso har  inda yake zaune  tana duba kafartashi  .

tace garin Yaya hk ta faru Mr deeni ?

 Sautsayi ne kawai doctor yayi mgnr a takaice .
Ok gsky ni yanzu banzo da wannan shirin ba ,Na dauka ma ko game da yarinyar nan ce ,yanzu abinda za'ayi kabini muje zuwa  hospital sai ayi treating din gurin yace Ok babudamuwa  ya Mike tsaye  da kyar suka bar parlour,n sule Nata faman ratafa masa sannan bbu kaukautawa.

 nablah Na tsaye jikin Window glass din dakin  tana kallon yadda yake daga kafarsa daya  da kyar.
 taji wani irin abu ya caki tsakiyar zuciyarta tare da maseefar jin tausayinsa raunin dayaji a sanadiyarta . Yayinda  zuciyarta ta shiga harbawa daf ..daf... daf..
ta runtse shanyayyun idanunta  'cikin sanyi jiki takai hannuta ta dafe saitin zuciyarta dashi Tana jin komai dake  jikinta yana  kokarin sauyawa akan deeni .

 Ahankali ta furta oh! Allah  Ni nablah meke shirin faruwa dani ne akan wannan bawa naka ?  

Ko dai abinda yake yawan fada kullun akansa ne ke shirin faruwa dani ?

Kar dai Na fada tafkin soyayyarsa da gaske batare dana sani ba ?

Tayi saurin girgirza  kanta tare da cewa  hkn ma bazai taba faruwa  ba domin nidashi bamu dace ba sannan zamu taba son junanmu ba .

Ta dade tsaye agurin tana saka da tunanin iri iri  akansa ,kafin daga karshe taje ta zube akan bed ta kwanta tana sakin naunauyen ajiyar zuciya da karfi hade da runtse idanunta badan tana jin baccin ba sai dan umarnin daya bata ..


Bayn sunje asibiti akai yiwa deeni duk wani abun da ya dace tare da yiwa kafar  bandage .
 sule ya maidoshi gida shi km yakara gaba .


A rakube yaganta bakin gadon dakin tallabe da fuskarta da duka hannayenta wanda take jikinsa yabashi cewar tunaninsa take yakaraso Inda take ahankali yana dingisa kafarsa daya  , Murmushin da bayi zato ba ne ya samu nasarar kufce masa, rungumeta yayi tsab ajikinsa yana cewa tunaninnawa  km  Na me ne ?

 ,ta kalloshi a frigice tana shagwabe fuska tare da cewa  why deeni ka tsorota Ni fa sosai  ..Ya narke mata ajiki shima yana shagwabe mata tare da cewa am very sorry dear ..Amman please ki dan rage tunani sbd condition din da kike ciki ,jin abinda yace yasaka jan tsaki ,tana tmbyr kafarsa ya lumshe mata rikitattun idanunshi batare da yace komai ..

Akwana a tashi 'bbu wuya gurin Allah km sannu ahankali   cikin hukuncin Allah deeni ya warke sumul  yasamu  saukin kafarsa sosai har yana tafiyarsa  yadda yakamata tamkar da.

 yayinda 'cikin jikin nablah shi km  ke sake girma  da bunkasa da bin jikinta, barin ma  fannin nonuwanta da duwawukanta suji lbr , domin nonuwanta sunyi wani irin girma da  cika naban mamaki sunyi mata hake hake a jirjinta ,
Yayinda duwawukanta km suka  dan baje sukayi fade dasu.
 sai jikinta yabada wani  Shep me kama da coka cola .
ta murje sosai tayi haske tayi fresh ta  canza sosai  Ga duk Wanda yasanta ada idan yaganta bazai yi saurin ganeta ba .
sbd da Yadda gabadaya yanayin  jikinta yasamu sauyi Na musamman .

Bangaren su ummi kuwa komai Na tafiya daidai yayinda duk sanda zeenat ta tada hankalinta kan komawa Nigeria, ummi ke nusar daita tare da kwantar mata da hankali, abinda yasa ma basu dawo ba har zuwa  wannan   lokacin likitan daya daurata zeenat akan shan maganin ne yace su dan  tsaya  akwai abubuwan daza'a yi mata  .. yayinda duk abinda ke wakana  a game da 'cikin nablah dake jikin nablah  duk ummi Na sane da komai.
Km  gabadaya ta gama shirya yadda zatayi da 'cikin nablah batare da duniya tasani ba .


Wata sabuwa inji Yan caca ..... wata uku Na cika   ba sai ciwon kirji  ya sarface nablah ba .

Bashiri  ta tada balli ita fa tarasa gane kan komai yace da rarar ciki yakai wata bakwai zasuje a saka inji ya markade Amman gashi har 'cikin Na neman haurawa Amman yayi mata shr .

Idan km ya fasa taimaka mata ne kmr yadda yayi Niyya to yabarta takama gabanta, ta karasa fadar hk  tana sakarwa  deeni wani irin   kuka me bantausayi da cin rai  . Deeni yayi shr kawai tare da tsura mata idanushi yana kallonta batare da  yasan yadda zai bullo mata ba .
 gabadaya hankalisa atashe yake akan abinda take so yayi mata  yayinda , zuciyarsa gabadaya gaskiya take son fada mata akan bazai iya barin a zubar gudan jininsa ba ,Wanda Bai sani ba ,ko kwansa ke nan a duniya , Amman yana jin tsoron tashin hankali da zai biyo baya da Wanda zata shiga ciki idan yasanar mata da hkn  ,babu  shakka shi zai iya Mika rayuwarsa gareta a yadda yake jinta a zuciyarsa  a halin yanzu amman bazai iya rabuwa da 'cikin jikinta ba .muryarshi can kasa .. tamkar ta karamin yaro me koyon mgn yace kiyi hkr nabeelah  ban fasa taimakon  ba.
 har yanzu  akwai wannan niyar a zuciyarta amman ki dan kara min lokaci akwai abinda nake yi ne yanzu , km shi zubar da ciki yana bukatar wani a kusa da mutun  . tacigaba da kukanta  tana  girgirza masa kanta alamun bata yarda ba  .

Yanzu me kike so nayi yanzu ? 

Ni dai ka ajiye komai ka taimakamin ka bari arabani dashi please tana me hade hannuwanta dukka tana kuka tana rokonsa ..Ya sake shr yana tunanin yadda zai biyo mata .duk ta inda ya biyo mata sai goce masa ..

Kuka take sosai Akan   a zubar da cikin  domin zuwa  lokacin  cikinta  yakai   watan ' bakwai cif  kennan dan har  cikinta ya dan dago kadan 'tamkar an kifa mata kwarya akan cikin nata.

Sosai ta tada hankalinta har numfashinta Na neman daukewa sbd Yadda ta dingayi  bbu arziki deeni ya dauketa sukayi hospital ,abin takaici suna zuwa basu iske dr saira ba.
 wai bata ma  kasar gabadaya hk suka juyo zuwa  gida zuciyar deeni fes...da yadda Allah Ya tsara  masa komai batare da yasha wahala ba . Akan hamyarsu ma riko hannushi tayi 'cikin nata tana kuka  ,dan girman Allah kada ka maidani gidanka ka Kai wani hospital din ,a markade abinda ciki Na huta wlh baba zai tsine min idan har Na haifi abinda ke 'cikina.

Daidai me gadin gidansa ya bude masa get ya zare hannushi yana juya sitiyarinatar yace   bbu wani hospital dazasuje akan zubd ciki ba'a kamasu ba . 
tana   kuka tace kaine za'a kama ?

Ta Yaya baza'a kamani ba byn da saka hanuna za'a yi kisan Kai tasha kukanta tamkar  Wanda tayi  'cikin shegen gaske  har zuwa   washegari ranar aikin kuka take ita a zubar da 'cikin jikinta  taki cin komai 
Nan deeni yashiga rarrashita wai tayi hkr kawai ta haifi abinda ke 'cikin dan bata sani ba ko shine silar arzikinta. ta Mike tsaye daga inda take zaune tana cewa wlh bazan hkr Na zauna Na haifi 'cikin  shege ba , wata irin janyowa deeni Yayi mata ta fado saman cinyoyinsa ya kalleta  fuskarshi tamkar zaiyi mata kuka yace ki rufa min asiri...sai km Yayi saurin canza salon  mgnrsa jikinsa Na rawa yace  kina jina ko.. ki bar mgnr zubar da  'cikin nan please  . 

Wlh kaji narantse bazan bari ba daga zuwa aiki Na koma gida da tsarabar ciki ba bazai yiwu ba sai dai asan yadda za'a yi da wannan maseefar ..a fusace ya katseta yana zaro mata rikitattun idanunshi kar ki sake nakara jin kin Kira 'cikin nan da maseefa ko wani abu makamanci shege ....ta Mike a harzuke tana masa wani irin duba sannan tace an Kira sa da maseefa maseefa maseefa km shege meye zakiyi min kai bama a son taimakon naka .
Daman can Kai mugun ne kagareni wlh nayi kuskure amincewa dakai amatsayin wanda zai taimakamin tasoma kokarin fixge hannuta daga nashi ,amman ya damki hannun da karfin tsiya yana duban yadda ta hargitse tafita haiyacinta .kasake nace banason taimakon tana wani irin kuka ..

Muryarsa a kasance sannan cike da rarrashi ya maidota jikinsa ya rungumeta tsam ajikinshi yana shafa bayanta ahankali ahankali tare da cewa    am sorry bazan sake yi miki ihu ba .

Yanzu ki natsu  Ga shawara me sauki  idan tayi miki sai mubi .

Ya dagota tare da zaunar daita kan cinyarsa kinga Yanzu Ni bbu abinda narasa Na rayuwar duniyan nan nablah ..
..  komai Allah Ya azurtani dasamunsa a rayuwarta ta fanin arziki da nasaba  Amman  sai Allah Ya jarabeni  ta wajen rasa ya'ya har biyu .
 kinga atakaice  banta samun haihuwa ba kennan ,yashiga yi mata nasihon  masu  ratsa jiki da sanyaya zuciya  da kawo mata misalin  iri iri  ,kinga kema  ba rawa kikeyiwa Allah  ba yabaki 'cikin jikinki ba ,  sannan km ke kanki  kisan takamaiman Wanda Yayi miki 'cikin nan ba ko ba hk ba ?
 Jikinta a sanyaye Ta daga masa kanta  alamun eh .

Ok yanzu idan nace miki. Ki  haifi  'cikin jikinki Ni Ina so kibarmi shi har illa Masha Allahu fa ......?
ta dago  shanyayyun idanunta Tana kallonsa tare da nazarin abinda yace din kana taja numfashi da kyar ta fesar  tace kaima kasan hkn bazai yiwu ba ta cigaba kukanta tana  kokari mikewa daga jikinshi  ya sake  maidaita yana cewa  Karki ce bazai yiwu ba nabeelah ,shine abu mafi sauki a gareki da zai yiwu ,zan taimaka miki Na karbi 'cikin jikinki ke km da zarar kin haihu ki zan sallameki da alkharu masu tarin  yawa ciki ma har da nauyin karatun ki zan dauka har ki gama .
 tayi shr kawai Tana sauraronsa har yagama mgnrsa bata sake cewa komai ba .
,kin amince da wannan tsarin  muryarta a raunane tace bawai bazan iya amincewa bane Amman Ni.. tsoron matarka nake ji idan tasan da haka Ga km ummi   takarasa fadar hk tamkar zata zubda hawaye ....kada ki damu da matata ko first love ,nasan yadda zanyi daita idan mgnr ta fito.
 ke dai ki natsu kawai km ki kwantar min da hankalinki bbu abinda,zai faru inshallahu.
 " kinga nima Na taimaka miki alokaci dakike neman taimako to Ni meyasa bazaki taimaka min  ki haifa min 'cikin jikinki ba ?

Ganin yadda ya narke mata ajiki  yana shirin yi mata kuka yasa  ta kamo tafin hannushi 'cikin nata tana murzawa 'cikin sanyi jiki  kmr yadda Ya sabam mata dashi, muryata cike da shagwaba tace shikennan Na amince , murmushi  sosai deeni ya dinga yi harda Kai hannushi kasan mararta yana shafo dan tudun cikinta.
 ita kuwa sai binshi  da kallo nablah take cike da jin takaicin haihuwar dazatayi bbu aure . idonta har da Hawayen tausayin kanta .
bata rai tayi sosai ganin irin dryr dayakeyi tace kowace matar arziki  agidan mijinta take haihuwa fari . Amman Ni zan haifi 'cikin da ban ma san ko na waye ba.
 hawayen mgnrta datayi  tana kuka shi ya hargitsa masa lisafinsa har ya tsaida dryr murnar dayake  ita kuwa tana ta kukan zuci da badini.

Ya rungumeta tsam  ajikinshi yana tura hannushi 'cikin jikinta sosai yana shafa cikinta tare da cewa  ki bar kukan nan  hk waye yace miki zaki haifi 'cikin jikinki bbu uba ?

Ni zaman me nike kennan ?

ai Ni ne uban 'cikin jikinki yanzu tunda yazama nawa  yakarasa fadar hk yana  kashe mata idonsa daya yana cigaba da murmushin farinciki .

Sake bata rai tayi sosai tare da turo   masa dan tsukaken bakinta gaba   tana kukan shagwaba. ajiyar zuciya ya sauke .

Ya Kai bakinsa ya tsotsi lips dinta yana kallon 'cikin kwayar idanunta shi dai gsky baya son ganinta 'cikin yanayin tashin hankali sosai yayita rarrashita dabata baki har ta hakura ta mikawa Allah lamarinta ....


MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗





AYSHA A BAGUDO

  
*Cassssssssssss cassssssssssss bestyna hasana danlarabawa come close this page is for you only anzo  gurin  kisha karatu lfy  Ina matukar yinki ,irin sosai da sosai din nan ,kaunar dake tsakaninmu Allah yabarta har illa Masha Allah, cassssssssssss cassssssssssss bestyna  jinjina ta musamman gareki ummu sabir* 





Page 90



Daure yake da towel a kugunshi sai Dan karamin towel din dake rike a hannushi Yana tsane ruwan jikinshi a gaban mirrow dakin wanda dagani  wanka ya fito ya tsaya , yayinda ita km take zaune  har lokacin tana fama da rarrashin  ziciyarta da son cire dafin dake daskare a kasan qirjinta wanda ke shirin tarwatsa zuciyarta .
 " tunanin ahlinta da tunanin irin rayuwar data jefa kan ciki take .
 tana zaman zamanta lfy gaban iyayenta masu matukar kaunarta da tattalinta takowani bangare basu son damuwarta ,sai gashi ta kawo kanta 'cikin halaka da bata San barin cikinta ba ,idanunta duka cicciko da ruwan hawaye komai yarigada ya  cakude mata guri daya  .
" abinda ta fito nema tasamu har ma fiyye da yadda tayi zato  amman bazasu yi mata amfani komai  yadda ta tsara  hkn a rayuwarta. ahalin datake 'cikin yanzu komai Na rayuwa yasoma  fice mata  a ranta , tunawa datayi da  yadda mahaifinta yaki yarda da zuwanta aikin nan yace ta zauna tayi aurenta tunda shi  bashida halin dazai barta  cigaba da karatunta  amman taki , tabiyewa son zuciyarta da son cima burinta nasamun wadataccen ilimi tazo aikatau  gashi tun ba'a je koina ba kadaddarar data kawota tana neman yin tangaliliya da rayuwata .

 Ashe Hk   kadaddarar rayuwarta zata zo mata  kennan  Batasan ba ?
Ta furta hkn 'cikin ranta ,Ida nasan Hk rayuwa zata kasance wlh da banzo ya Allah kaya femin idan wani laifi Na aikata maka saka jarabini da samun wannan ciki takarasa tunaninta hawaye na bin kuncinta sharrrrrrr sharrrrrrr.

Gashi nayi ciki batare datasan wanda ya shammace ya dirka min  ba ,yabarni  da mikin da har duniya ta nade bazansan ranar warkewarsa ba .

Me zancewa  mijin dazai  aureni   a game budurcina dazan rasa gurin haihuwa ?
  "sosai tayi zurfi 'cikin tunanin rayuwarta daki daki ahankali ta sauke naunauyen ajiyar zuciya tana dauke Hawayen idanunta  da tafin hannunta.tana kallon  sanda  deeni ya dauko lotion Yana shafawa a ilahirin jikinshi hankalisa  kwace yake yin komai da   da fesawa jikinshi   turare masu sanyin kamshi  ta mirrow suka hada idanu dashi.
 ya dage mata girasa daya alamun tmby ,ta girgiza masa kanta kawai batare da tace masa komai ba sannan yakarasa Inda  wordrob dinsa yake ya dauko short niker wanda  bai gama kaiwa gwiwarsa ba     da wata riga me budadden gaba da shara shara  wanda dagani  Na shan iska ne, Dan gabadaya sifar qirkinshi a bayyane yake.
   .
Yayinda  gashin jikinshi ke  kwance luuuuf luuuf dasu sai sheki suke suna daukar hankali..
.. ahankali yakaraso har  Inda take zaune ta zuba uban  tagumi tare  da tsura masa shanyayyun 
idanunta  tana kallonsa  da sha'awar  yadda yake da tsananin tsafta da kyalkyale jiki tamkar mace   .

son take  tagano  muninsa  ko wani makusa dake jikinsa  amman abun ya  faskara domin kasawa  ganin hakan tayi .
 " sbd baiwar kyawun halitar  da Allah yayi masa bbu ta inda zata kushe shi in dai ajikinshi ne  ...yana zuwa ya janyota jikinsa ya rungumeta tsam Yana shinshina wuyanta da sumbatarta  tare da kai bakinsa 'cikin kunneta.

 kin yi shr kina ta aikin  tunani da  kallona ..wani irin yanayi na daban  ta tsinci kanta ciki duk da ba yau ne karo na farko da jikinsu ya hade da juna ba.

Please nabeelah tunanin nan  ya isa Hk ,ba dan komai sai Dan   lafiyarki data bby Nah .

Ta dago da sauri  tana watsa masa shanyayyun idanunta  jin abinda yace .
 "yes bby nah  ne halak malak tunda kin amince zaki haifa  ki barni min  kinga kuwa  dole nakirasa da bby nah .
 "ta lumshe idanunta batare da tace masa komai ba sai ma wani irin   tausayin kanta da shi kanshi  dake shirin jefa rayuwarsa 'cikin rudani  da tashin hankali rayuwa akan 'cikin jikinta  taji ya mamaye zuciyata .. kwantar daita yayi sosai akan bed  shima ya kwanta yasoma murzata a frigice  ta Mike  zaune ta matsa kusa dashi  tana masa wani irin duba ya sanya hannushi ya   janyota jikinshi  sosai ya rungumeta tare da bata hot kiss a wuyanta..
. mgn tafara yi masa da sanyayyiyar muryarta .. deeni Dan Allah ka kyaleni bacci nake ji .
Ni wlh yanzu ma tsoro kake bani.
  Ni kadai nasan irin mikin danake ji a'cikin zuciyata game gibin da rayuwarta tasamu .
 gashi km Kai kullun da irin salon dakake zuwa min dashi  wanda narasa muhalin da zan ajiye hkn a xuciyata .
Sai  ka dinga min wasu abubuwa tamkar wata matarka ..kaji tsoron Allah fa akan abubuwan dakake min ni yarinya da bansan komai ba takarasa fadar hkn jikinta a sanyaye.
 , sake janyota jikinshi Yayi  sosai tare da cusa hannushi duka 'cikin rigarta  Yana shafo kirjinta sannan  yace ni nasan   abubuwan danake daidai ne ... amman kina iya ajiyesu a duk muhallin da Yayi miki acikin zuciyarki  matata ko akasin Hk ..

Kulllum kullum sai kin min mita akan jikinki yakarasa fadar Hk  muryarsa a fusace ,duk iskacina baki   taba jin nace zan  kusanceki ba .


Ko nabata cewa zan ciki ?
Ta zaro shanyayyun idanunta waje tana  girgiza masa kai da sauri .

Ok da Ina son saduwa dake nabeelah , da tunin an wuce gurin"
 Dan zan iya yin son  raina dake koda  amincewarki ko babu  ..amman bake ce a gabana ba.. ya karasa fadar Hk Yana zarcewa da romancing din jikinta bijirewa ta sake yi  Da son  yin mgn ya hade bakinsu guri daya .
Yana tsotsa tare da shafa tausarsar  surar jikinta da kasan mararta yana jiyo Dan tudun cikinta .
tun tana nokewa da fexgewa daga gareshi har ta hakura tabarshi yana romancing din jikinta .
'Cikin dabara  deeni ya rabata da kayan dake sanye a jikinta ta saura Daga ita sai pant da son rabata da bra din ma  sannan ya cire nashi nonuwanta dake cike  bammmmmm yake ta aikin murzawa son ranshi tare da bata zafafan kissing  takoina a sansar  jikinta.
 ita kuwa sai mimikewa tasoma yi  tana gantsarewa tare da kara turo masa nonuwanta da alamun sakwanninsa a zahirance zasuyi aiki kmr yadda  yanayinta ya nuna masa .
Sosai  ya sauya  salon wasannisa zuwa wani shaukinta na daban ,hkn yasa tayi saurin  dawowa haiyacinta hade da  sakar masa kuka me frigita zuciya.. 
dole tasa deeni  yabarta ya rungumeta tsam tsam ajikinshi Yana jin yayi release ajikinta batare da yashigeta ba, ya Mike zaune   Yana meda numfashi  ahankali ahankali  . Ya juyo daita suna fuskantar junansu  sosai hawaye suka shiga bin kuncinta ji take tamkar ta saki  ihu  kozata   samu saisauci akan salon rainin hankali  da deeni yake son  shigo mata dashi kullun da salonsa gareta .

 muryata a sanyaye tace wayyo nashiga uku wace irin maseefa ce wannan  Na kawo kaina ciki ..Ya tsura mata ido yana kallonta da kallon Dan tsukaken bakinta  .tare da cewa nine maseefar nablah yana nuna qirjinsa  ?
  a razane tadago idanunta  tana kallon 'cikin nashi idon.
 Dan jin abinda yace muryarta cike kukan   shagwaba tace Ni.. Ni nace kaine maseefa ?

  jikinsa a mace  Ya dage mata girasa daya ,yana me  tamke fuskarshi sosai  tare  da hawayen dake zuba yayi daga idanunta  ganin taki tsaida ruwan hawaye yasa harshsa yashiga  lashe hawayen dake silalowa  ..

  bakinta ta bude zata sake yin  mgn Ya sake hadewa da nashi  guri daya shiiiiii kar ki  wahalar da kanki gurin cewa komai ..
 " Duk abinda  nayi nasan bbu kuskure ko daya aciki ,km daidai nayi  bbu wani sabon Allah ciki idanuta ta sake  zarowa waje tana yi masa duban tababe km mara hankali bata dauke idanunta akanshi ba taji  cak  ya dauketa Yayi  toilet daita yana tsokanarta da matsoraciya kawai kalli duk yadda kika dawo  wanda hkn ke nuna min  kina feeling ayi sex dake ..
ta turo masa Dan tsukaken bakinta wlh ni a'a abinda banta yi ba ta Yaya zai dameni .
 Allah ko ? To ko zaki gwada ne yau kawai kiji yadda abun yake ?

Tayi masa banza da sake turo masa dan karamin bakinta da alamun kina bukatar Na sake feeding din bakin nan naki  ko?
Tayi saurin son janye bakinta amman Ina kafin ta ankare tuni ya Kai  bakinsa kan lip's dinta yana  tsotse  sannan yakarasa  shigewa bathroom  daita .
tashiga uhun da kuka  bata son iskanci dayake mata  Dan girman  Allah deeni  kabarni  banason wanka nan sanyi nake jiki  ..dolenki kiyi wanka yarinya dan da  alamun kinji Dade keme ajikinki .

 Allah wlh banji dadin komai ba .
asalima wlh bansan yadda  zanji dadin  ba .uhm  tare da tsundumata 'cikin bathtub nan ma dai sai daya bata lokacinsa yana murzata becouse baya gajiya daita.
 nablah irin matan nan ne da mutun kwata kwata mutun  bayajin yagaji da mu'amula dasu .
Saida yayi yadda yake so daita sannan ya daukota tana kuka ya fito.
 nan yashiryata shima ya sake shirya kanshi suka fito parlour,n kasa  ..


Tea yaje ya hada musu suka sha sannan ya kunna masu tagameme plasma dake manne jikin bangon parlour.
 " Mikewa  tsaye yaga tana   kokarin yin .
 ya janyota jikinshi Ina zuwa km ?
 ta shagwabe masa fuska tamkar zata sakar masa kuka ,zuma da hollandia nake son Sha ya zaunar daita ya Mike yaje yayi mata  mixed dinsu guri daya har da spanin night dinsa  ciki yakawo mata tana gama Sha tasoma narainarai da idanuwa tana lumshewa alamun jin bacci  ,  ya janyota ya  kwantar saman cinyoyinsa  yana shafa sumar kanta ,take bacci yadauketa ...


Karfe shabiyu daidai ya nufi dakinsa daita inda nan ne masaukinsu tunda suka zo gidan .zafafan sawannisa masu shiga jiki da rikitarwa deeni yashiga aika mata yana bin kowani part Na jikinta yana sarrafawa 'cikin kwarewa ya cire Yar doguwar rigar daya sanya mata ahankali nablah ke nishi dadi domin amsar sakowanin da sansar jikinta ke yi daga manage deeni .
sai wani ciccije lip's take tana kara bankaro masa kirjinta dayake aikin tsotsa tana Mike kafafu da waresu sbd itama wani irin shauki take ji a gabadaya ilahirin jikinta.. kasancewar mafi yawa daga 'cikin mata idan  cikinsu yakai wani stage suna bakuta mazajensu tare  dasu ,  to hakan ne yakasance da nablah tana 'cikin irin wayan nan jerin mata ,dan wani irin mugun shauki take ji ajikinta yana mata yawo da son jin jijiyarsa  ta ratsa kasanta.
 " batun tsiyaya kuwa  ma ba'a mgnrshi  dan tuni tagama jikewa jagab daita.
 deeni ya dau lokaci sosai gurin juyata ,yayinda kowannesu Na jin dadi abinda ke faruwa a tsakaninsu gabadaya sun   manta aduniyar da suke ciki sai aikin nishi kawai suke suna muzar juna.

'Cikin wani irin mugun shauki deeni ya gangara zuwa kasan mararta yashiga lashewa yana mata tafiyar tsutsa da harshensa wani irin ihun dadi tasa masa  batare da tasan a duniyar datake ba.
 ta cusa hannuta 'cikin laulausar sumar kanshi tana aikin yamutsawa da yin  shiiiiii shiiiii da bakinta tamkar me cin yaji.
 " ahankali deeni ya dinga tafiya da harshensa har zuwa  kasan mararta motsi da bakinta tashiga yi Wanda Bai San abinda take cewa ba ..ahankali ya dago yana me Kai kunnenshi daidai bakinta ta saki wani irin ajiyar zuciya da karfi tana dan Mikewa sakamakon zare harshensa da Yayi  please meyasa kabari kacigaba please now....

Dawowa  Yayi kasanta yashiga soucking dinta yana murza kan nipply dinta, hauka ne kawai nablah batayi ba aranar sannan bbu irin sambatu dabatayi ba pl  kada ka cire idan ka cire zan mutu kacigaba kawai wlh Ina sonka sosai nayi missing dinka kwana biyu kadaina zuwa min Dan Allah kadaina yin nisa dani .
, ganin yadda gabadaya ta mace acikin duniyarta tana faman sambatu  yasa deeni  yi mata rumfa da kirjinshi  bata yadda zai danne 'cikin jikinta ba, wanda daman bawani girma 'cikin  Yayi ba .
yakasancewarta me karamin ciki . ahankali  ya zira jijiyarsa cikin jikinta , yana shiga kuwa ya kusan haukacewa saboda wani  irin mugun  dadin dayaji takara yi masa fiyye da kowani lokacin saduwarsu daita.
 " hannuwansa  duka ya tokare gefe da gefenta  yasoma aikin Cinta yana gurnani dadi .
ita kanta bakaramin dadinsa take ji ba ajikinta.
 sosai takai hannuta tana shafo  fadadden qirjinsa da murza kan nipply dinsa  har dan hawayenta  dadi nablah ta dinga fitarwa .
deeni bai bar nablah ba sai da Yayi mata ci shida  ba dan yagaji ba yabarta sbd  tausayinta da  abinda ke 'cikinta yaji wanda zuwa lokacin har dan 'cikinta yana Dan motsawa ahankali  alamun yasamu  karin karfin  .

Zuwa Yayi ya hada musu ruwan wanka me dumi yaje ya sakata bathtub nan ma rungume take ajikinshi hannunshi duka bisa tudun cikinta dake motsawa ahankali ya lumshe idanunsa yana jin  wani irin  dadi  Na dawainiyya da ruhinsa
. wasu Hawayen farinciki suka nasarar   xubo masa .
zuciyarsa tayi masa sanyi da dadi .
wai  shine yakusan yin Dan kansa?
 ...wani sabon farinciki ya lullubesa da zuciyarsa  yayi mata wanka amman bana janaba ,shi km   yayi wankan janaba ya fito rungume daita ajikinshi ya kwantar daita yana mata pick  a goshinta yazo ya rungume tsam ajikinshi yana shakar kamshinta mai sake rikitashi ya lullubesu batare da kowani Na kaya ajiki ba . hannuwanshi duka saman 'cikinta  yana shafawa da jin sanyi zuciya , har bacci ya dauke shi cike da wani sabon  feelings dinta  ..

Sai gurin hudun dare ya farka daman bawani ishashen bacci Yayi ba yasoma lalubarta wanda itama da alamun bata gaji dashi ba.
 tashige 'cikin jikinsa sosai tana narke masa cigaba da shafarta Yayi wanda daga karshe ya dawo  kasanta ya   Dan ware kafafunta Yayi mata kwanciyar rigingine shi km ya daga kafafunta sannan  ya taho ta karkashin kafafunta yasaka jijiyarsa ciki jikinta wani irin jummmm taji ajikinta tamkar ana jona mata wutar lantarki  ta bude shanyayyun  idanunta tana dubansa dishi dishi take ganinsa yayinda shi km  tamkar wani mayuncin zaki yashiga yin sex daita sosai yake jinta har 'cikin kwanyarsa Kusan yadda  daman kowace mace me  ciki take .
abar bukatar kowani cikakken namiji ce ,sai Kiran sallah Na biyu deeni  yabar ya Mike  tsaye  sbd yasan maganin ya kusan gama aikinsa ajikinta ,ya sanya mata daguwar rigarta  ya lullubeta da bargo yana me  kissing din lip's dinta ..





Washegari a gajiye ta tashi ,jikinta a sanyaye tayi komai nata har zuwa kan  wanka tsarki.. tayi jugun daita tana tunanin abinda ya faru daita daren jiya sosai jikin ya mutu kuzarinta Yayi kasa ta lafe akan bed tamkar me jin sanyi  Amman tunda  taga alamun shirin zuwa office deeni  yake ta Mike zaune tare da saka masa  kuka ita Sam  baza zauna ita kadai ba acikin gidan sai dai ya zauna shima ko km ya maidaita inda ya dauko..
 ya tsura mata rikitattun idanunshi daidai sanda yake karasa saka takalmin kafarsa daya itama  tsare shi tayi da shanyayyun idanunta.

 cigaba da abinda yake Yayi yana  sauraron  kukanta wanda inda da sabo yarigada yasaba dashi zuwa yanzu .
Sai dayagama shirinsa tsab ya juya gareta sosai yana fuskantar kallonsu take tana cigaba da kukanta ,shi din ma yau wani irin  kallo yake mata wanda ya tabbatar masa da lallai akwai abinda yayi mata shamaki 'cikin farincikinta da walwalarta akan farkon ganinsa daita sosai fuskarta da sansar  jikinta gabadaya suka nuna masa rauninta da damuwar datake ciki.. muryarta cike da kuka tace Allah idan ka fita kabarni ni kadai bazan zauna ba ,duk yadda zan bar gidan sai na yi .. gabansa yayi mugun faduwa jin abinda tace  yayinda ahankali km kirjinshi da zuciyarsa suka shiga bugawa da sauri da sauri  sakamakon tunanin da zuciyarsa ta jefeshi dashi akan barin nata da yake kokarin son yi ita kadai  a gidan yarinya ce karama wanda bata San ciwonka kanta da jikinta ba ,idan wani abu yasame 'cikin jinkita ,shi yake da babbar hasara baita ba  Dan ita idan tarasa 'cikin jikinta sai mata taji dadi .


  dan hk batare da wani bata lokacin ba ya amincewa kanshi  kawai gara  suje office din tare su dawo tare hkn shine kadai kwanciyar hankalinsa ..
 muryarsa a sanyaye yace  shirya muje .... ita km batare datasan inda zai nufa daita ba ,tabiyo shi abaya , still tana kuka wanda shi kwata kwata abinda yafi tsana keenan daga gareta yawan kukan nan nata  yana matukar cin ranshi da hargitsa masa lissafi.
 ita Sam   abinda yakamata tayi kuka da Wanda Bai kamata ba duk yi take ..

Tafiya suke tamkar wasu  kurame yayinda kowannesu ,zuciyarsa da abinda take tsaka masa a game da Dan,uwansa , ganin yadda yayi mata shr  yaki ce mata komai  yasa tacika fam  tamkar zata fashe ta janyo tissue dake ajiye acikin motar ta goge face dinta dashi Tana sakin ajiyar zuciya  tare da maida kanta gefe daya tana mamakin miskilancinsa ..  yayinda shi km  haushin kukan datake yi ne  yasa ya gabadaya ya shareta ya maida hankalinsa kan tukinsa ...

A 'bakin wani babban mall yayi parking ya fito ya kulleta yashiga ciki Bai jima ba ya fito hannushi  rike da leda mai dan girma byn ya zauna ya dan kalleta fuskarta a hade ya ajiye  mata ledar saman cinyarta batare da Yayi mata mgn ya hau kwalta da kallo take binsa dashi cike da bacin rai amman Hk kawai tasamu kanta da kasa sauke masa kwadon maseefar datayi Niyya sakamakon hango fuskarshi datayi tamkar anyi gobara komawa tayi ta lafe 'cikin seat ta daga  kanta sama , idanunta a lumshe tamkar me bacci ..

 Ta bayan  harabar ma'aikatar Nasu yayi parking ya kashe matarsa ya juyo da dubansa gareta tare da tsira mata rikitattun idanunshi , ahankali yake dubanta yaga har face dinta  yatasa saman fatar idanunta sun Kumbura , amman duk da hk sai yaga tayi masa kyau sosai , lumshe rikitattun idanunsa Yayi ya cije lips dinsa yana me sakin murmushi tare da tura yatsunsa 'cikin sumar kanshi yana aiyana yadda zai samu kyawawan bbys daga gareta ..

Tar ta bude eyes dinta dan daman duk abinda yakeyi tana kallonsa kawai pretending tayi kmr me bacci .

Harara ya watsa mata ya daure fuska sosai  kmr bashi ne yanzu yagama murmushi ba , itama  hade rai tayi sosai ta turo masa dan tsukaken bakinta gaba..bazato   taji saukar bakinsa kan nata lip's din . ahankali  ya kamo fuskarta da duka tafin hannushi yashiga tsotsar lips dinta dayafi kaunar da so 'cikin nashi .. idanunta suka sake kawo ruwan hawaye masu dumi amman Bai saki 'bakin nata ba sai daya Sha son ranshi sannan ya sakar mata 'bakin tare da gyara mata hijab din dake sanye ajikinta.
 ya bude ledar daya daura mata bisa cinyarta ya fidda nikaf ya Mika mata  kana  muryarsa a dakile yace ki suturta jikinki da kyau ki fito muje ba musu tayi yadda yace shi km ya riko ledar suka shiga 'cikin company din ta baya wanda sirarrun mutane ne kawai zasu iya ganinsu  ..


Yana gaba tana biye dashi abaya  duk inda suka wuce sai taji ana gaishe dashi 'cikin girmamawa har itama ta samu nata tsarabar gaisuwar . Kai tsaye gurin special hanyar shi yabi ya tsaya gurin  lift  itama ya tsaya tana jira daga gareshi tana kallo ya  daddana kofar lift din ta bude 'ya janyo hannuta suka shiga atare, wani irin abu taji ajikinta  me kama da vibrating ya kamata ,ta kamkame jikinta 'cikin wani irin tsoro  daman kmr yasan zatayi irin wannan kauyancin zatayi shiyasa  ya sanyata 'cikin jikinshi muryarsa a sarke yace mlm ki natsu karkiyiwa mutane shirme anan  'cikin minti biyu sai Gasu  a flour 7 inda office din  deeni yake, kofar ta sake budewa  suka fito  ..

Suna shiga office dinsa ya nuna mata gurin zama ta zauna a direrece  tana karewa office din kallo tashiga yi  komai naciki office din tsaf tsaf abin birgewa  da sha'awa tamkar yadda yake me tsananin tsafta ajikinshi  hk komai nashi yake . Yadda take kallon office din hk take kallonsa tamkar wani sabon halita agurinta, ko ma irin yau din nan tasoma ganinsa.

  takowa yayi ahankali har zuwa gabanta ya sunkuyo numfashinsu ya gyauraya  yaNa bugar hancin  junansu.
 sosai  yayi kasa da voice dinsa.

 wannan kallon hk fa ?

Yanzu nace kin fada tarkon soyyayata kice karya ne , alhalin Ga zahirin gsky nan ina kallo acikin kwayar  idanunki ..

Murmushi tayi me gyaraye da bacin rai da takaici mgnr dayake yawon yi mata akan tana son shi ...

Kadamu kanka akan Ina sonka deeni ... kullun baka gajiya akan furta wannan kalmar .
 Nifa gsky  nasoma gajiya da jin wannan kalmar daga bakinka wlh azim kaji rantsuwa dan muslimi kennan nasurudeeni bana sonka bana sonka......!!!

yaji wani irin abu ya cike tsakiyar zuciyarsa .
Take km zuciyarsa tashiga bugawa ,yayi shr kawai tare da  runtsa rikitattun idanunshi yana jin yadda kirjinshi ke tafarfasa da zafi  akan lafazinta gareshi ..

ta sauke naunauyen ajiyar zuciya tana sa hannuta ta tura kirjinsa dake neman hanata sauke numfashi sosai  yayi baya kadan ta Mike tsaye  da hanzarinta tana sakin numafashi kana tacigaba ..idan kana tunanin   Ni nablah Na afka tarkon  sonka ne wlh kamakaro deeni.. amman nasan  bazaka taba  gane hkn ba sai nan  gaba.
  can km ta hassala tasoma yi masa mgn 'cikin fada fada hb ka dameni kullun da mgn daya Ina sonka Ina kishinka ..hk son yake ?

Ko ance maka hk ake yin  so duk da bantabayin soyayyar ba wlh nasan ba hk akeyin so ba ....dan hk Ni mlm ka saurara min  kada ka kuma damuna da wani zance sonka nake .
wayanda sukaga zasu iya son naka ,suje suyi tayi   ,sunji zasu iya ne Amman banda  ni  nabeelah salis gulumbe takarasa fadar hkn tana nuna kirjinta da dan yatsanta .

Fesssss ya bude rikitattun idanunshi akanta ya zuba mata yana kare mata kallo hakika ita din daban take ko acikin darurukan mata akan aji ...Bai taba tunanin level dinta da tsaurin zuciyarta  ya Kai hk ba ,km har ma yaso yazarta tunaninsa  ...
ya taka sannu  har inda yakoma  ta tsaye tana sakin numafashi mgnr datayi da kyar ..

Ya hadeta da kirjinshi yana fidda numfashi me gyaraye da bacin rai yana jiwo  tudun nonuwanta da 'cikin jikinta ya sake ya sake busa mata hucin numfashinsa sannan muryarsa a hargitse yace Ni kike dagawa sautin murya nabeelah.?

Yanzu har munzo wannan stage din ?

 kinsa Allah kina sona nabeelah  tamkar kiyi hauka  amman dakinkancinki yasa kika  kasa ganewa ..

tayi masa wani irin kallo bashi da hankali ko mara  lfyr ,  kana tace wlh Ni ba dakikiya bace kullun da'anyi mgn kacewa mutun dakiki alhalin Kai .....sai km tace Ni dai gsky ni ba dakikiya bace ..
sai waye dakiki idan bake ba ?

Oho.. shima dakiki ai yasan kanshi amman wlh ni ba dakiki ba.. ya hade fuskokinsu guri daya yana busa mata hucin numfashinsa me gyaraye da zafin shauki uhm abinda Ni dake bamusaniba wani bakin almari Na shirin  faruwa da zuciyoyinmu wanda bamu san ko meyee ba ..

kana ya kamo hannuta  duka   ya rike Yana mata massaging wani irin abu taji Yana shocking din jikinta yayinda gabadaya tsigar jikinta suka Mike tsaye ..

Muryata a raunane tace wani bakon al'amari ke shirin    faruwa da zuciyarka wanda bakasan  ko meyye ba.. amman banda tawa zuciyar datake  tsarkarka km kubudadace dagareka..
Ya janyota sosai tare da manna bayanta da kirjinshi hannushi km ya maida kan cikinta ta rantse idanunta dan kwata kwata batason tunowa da 'cikin jikinta Yacigaba da shafa 'cikin yana jin motsin da 'cikin ke yi akai akai yanzu sosai fiyye da ko wani lokaci 'cikin hk wayarsa ta dauki kara sautin wakar India me dadi yasoma tafiya daita ajikinshi yaje inda ya zube wayoyinsa ya dauki wayar  yana sunan umminsa yagani ya danna wayar yana manneta da kunnenshi tare da yin sallama .

Bangare ummi kuwa bayan tilon dan nata ya dauka suka gaisa da tmbyr nablah yace tana lfy first love alhamdulilllahi daman nace Na sheda maka  yanzu jirginmu zai tashi inshallahu  ya lumshe idanunsa yana sake shafo tudun 'cikin jikin nablah tare da  cewa Ok first love Allah yakawo Ku lfy tace Ameen  ya 'cikin jikin nablah Yayi girma sosai ne ?

Ya sake lumshe idanunshi yana sake budewa yace uhm girma kadan nan ne first love to Allah yarabasu lfy shima ya amsa da Ameen,nan sukayi sallama daita tana sheida masa lokacin da jirginsu zai sauka Nigeria. 
 ahankali yakarasa  ya zaunar daita akan Cushing din data taso kijirani har indawo  duba wani abu.

Ta tabe bakinta kawai  tana  gyada masa kai .

 yana fita itama ta Mike tsaye tasoma zagaye office din tana duba koina  tare da yabawa da yadda  tsarin office din yake .
Sosai komai Na cikinsa yabata shaawa , Daga karshe taje wajen dorawar dake zagaye da makeken table dinsa  tana Yan dube dubenta har ta bude wata dirom taga tulin  kudi masu yawa  da basan iyakarsu ba ,ta dauki dari biyar aciki  sbd ita kadaice karama aciki ragowar duk 1k ne  ta fice daga office din .
Tasoma tafiya ahankali tana kallon mutane dake Kai kawo hanyar dataga wasu masu yanayi da Yan doko suna faman aiki bi.
", nan ta nufa step tagani me shegen tsawon gaske Yayi secul kmr snake ,tasoma tafiya batare da kowa komai ba 'cikin ranta.
 da kyar tasamu ta isa can harabar ma'aikatar byn tafiyar data dingayi tana hutawa .

 tana kawo bakin get me gadi ya tashi ya bude mata get yana mata kallon kurilla..
 " ta  fito gabadaya bakin titin dayake shr da karancin jama'a  tana Yan duba dubenta tana kallon masu fice dashige.. wata hanya tabi data hango wata yarinya  me saida plantenchirps wacce bata wuce age mate dinta ba .
km daman tunda zasu shigo tagatan taji plantschips din yashiga ranta    ta siya ta samu guri daga 'bakin titin ta zauna jimmm can km ta Mike tsaye  tashiga tafiya ahankali tana jin dadin yadda isakar gurin ke kadata rabonta da shan iskar waje irin Hk har ta manta ..



Tsaye yake abakin office din nasa "byn ya dawo office be taddata a inda yabarta ba.
 " hankalinsa a matukar tashe ya fito yana duban ta inda zai hango bulowarta Dan baiyi tunanin nisa tayi ba .. kowa yaganshi sai ya gaishe shi cike datarin mamaki ganin  manage deeni da Sam ganinsa ba'a asamu 'acikin sauki Amman gashi ayau a arha abakin office dinsa .
danna waya kawai yake yana neman layin fk  batare daya dago ya kalli tarin  masu gaishe dashi ba . Can km wani tunani yazo masa ya koma Office dinsa 'cikin sauri   Yana Kiran sunanta tare duba agogon dake daure da tsintsiyar hannushi shr yaji yayi yawa yakara tsayawa for 5 minti .
 " 'bakin kofar toilet din yaje yayi nocking still bbu respond kara nouking yayi still no answer ahankali yaji zuciyarsa ta buga ..da sauri  Ya bude kofar yashiga Gani Yayi yawam bbu ita bbu alamunta.
 wani irin uwar ashar ya saki tare da sake  fitowa waje da mugun sauri.yanzu kam yasoma tunanin bata kusa dashi dan jikinshi Bai bashi hkn ba ..

Da maseefa ya isa bakin get da sauri Yana Kiran eze... me gadi da karfi muryasa tamkar zata tar watse da gudun bala'i eze yakaraso daga inda yake zaune yana aikin gadi yace sir am here  ..ka budewa wata yarinya  get ?

Eze yace sir Yan mata dana budewa get yau  suna dayawa bazangane ko wacce yarinya daga ciki kake nufi ba .

deeni ya dauke shi da wani mahaukacin mari guda biyu ajere you are very stupid eze ...wata yarinya me sanye da hijab har kasa ta rufe idanunta da wani 'bakin abu ...

A frigice eze ya amsa masa da yesss yes. sir Na bude mata .... Tun dazu ta fita ..
Kutumar ubanka.
 ubanwa yace ka bude mata ?
ya karasa fadar hkn alokaci guda tare da sake nufar eze gadan gadan wani irin gigitaccen mari ya sake sauke masa sannan ya shake masa  makoshi Yana sambatu .

Ubawan yace ka bude mata get nace ?

 ya fadi Hk  Yana girgizashi wallahi idan banganta ba ,sai Na batar dakaima anemeka anrasa.......kafin kace tunin gurin ya fara cika da jama'a duk Wanda yazo yaga manage ne sai yakama gabansa 'cikin hk fk yakaraso gurin da sauri tare da riko deeni yanason kwace makoshin  a eze hannushi kar Yayi kisan Kai .
Wai meyye hk deeni ?


Meye ya hadaka dashi ?

Ka sake ba girmanka bane ,a fusace yace girman shegiya me zanyi da irin wannan girman still hannushi Na rike da eze wanda ya kusan shekawa lahira tamkar deeni zai yi kuka yace eze ka cuceni kagama da rayuwata tunda ka bude mata get .
Wai kan wata yarinya kake mgn ?
Anya kuwa wani abu Bai taba brain dinka ba..deeni  yayi  wurgi da eze  Yana sakin numafashi gabadaya ya rude yashiga tashin wani irin duba yake wa fk wanda yasa yaja baya kadan ..muryasa a fusace yace Kai ne mahaukaci bani ba domin ni sanan abinda nake ..wa ma yakiraki nan ?
Bar nan kafin Na sauke maka naka yanzu yana nuna masa hanyar da yatsunsa shi kam eze tunda yaji deeni ya saki wayarsa yashiga furta sorry sir  am sorry   sir bbu abinda eze ke aikin fada rike da wuyansa Yana rawar jiki .
deeni ya dawo tamkar wani zautaccen mahaukaci sabon kamu 
,hankalinsa a tashe yashiga Kiran Ugo  Sunday Kingsley Hk ya dinga Kiran escort dinsa dake zagaye dashi oready  Yana me  sake nufar 'cikin company .

 securities din 'bakin get da escort dinsa kafin kace me tunin sun iso gareshi Suma hankalinsu atashe domin yadda yanayin boss dinsa ya sauya, sun San  babu lfy ..  umarni  yashiga basu da  kwantancen  nablah da irin yanayin shigarta dake jikinta.

  can km ya tuna da CCTV camera din dake zagaye da ma'aikatan ya juya da mugun  sauri yakoma office din da securities masu kula da gurin suke tamkar zai tashi sama.

'Cikin sauri   suka soma yin  rewaning  CCTV camera yana tsaye jikin bango rungume da hannuwanshi duka a saman fadadden kirjinsa sai dai gabadaya hankalinsa da idanunsa sun tattara ne akan CCTV  shi kadai yasan irin halin tashin hankali dayake ciki ahankali aka fara tariyo masa tundaga shige da ficen mutane dake 'cikin company  har zuwa  sanda yashigo tare daita da fitarta  da hanyar da tabi ai bai San sanda ya fito a gigice ba fk Na kokarin janyoshi da tmbyrsa wace yarinya wannan ya tada hankalinsa akan Amman Ina kwata kwata hankalinsa Bai jikinsa ballanantana  ya tsaya sauraronsa  a 'bakin titi yake   yana wage wage ta inda zai ganta amman Ina  bbu ita bbu alamunta securities da escort dinsa kuwa tuni  sun  bazu gurin nemanta  ..







MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
     💖💖💖
💗💗💗💗💗





AYSHA A BAGUDO




*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION✍🏻*





Page 91 




Wani irin kallo Fk yake yi masa na  mamaki, mai d'auke da alamomin tambaya iri iri ,acikin   ransa yake ayyana abubuwa da dama, shi dai yasan ko akan Zeenart matarsa bazaiyi wannan haukan  haka ba, kuma a iya saninsa da tunaninsa  bai san shi da wata mace ba byn matarsa zeenat, kuma gashi ya gani da idonsa  a CCTV tare suka shigo, to wacece wannan yarinyar?    tambayar da yayiwa kanshi kennan ganin bamai bashi amsa  idan ba Oga Deeni ba, yasa shi nufar shi gadan-gadan. 



Babu wani alamun tsoro a tare dashi  ya kalli Deeni yace " wai kai Malam akan wacce banzar yarinya ka tada hankalinka haka?
, ka wani gigice ka fita daga hayyacink.......

 Wata muguwar shaƙa Deeni yayiwa Fk, a fusace yace " don't, don't ever try to call her fool again, da ganin yadda yake maganar kasan kwata-kwata baya cikin hayyacinsa, ƙura masa ido Fk yayi a matuƙar galabaice, sannan   km da kyar maganar ke fita Daga bakinsa  yace " ni Deeni? 

 Deeni ni kakeyiwa haka akan mace? 

 sakin sa Deeni yayi, sannan yayi baya ya naushi katangar dake gefenshi , hade da furzar da iska me dumi  daga bakinsa, hannuwansa daya  nausa, yabi da kallo kana  ya kalli Fk yana tsura masa rikitattun idanunshi   " please go, i don't want hurt you.
, kallonsa kawai Fk keyi cike da mamaki da alajabi  ya buɗe bakinshi zaiyi magana Deeni yace " i said go,  a fusace.... shiru Fk yayi ya kasa ce masa komai sai huci takaicin abinda deeni  Yayi masa ke cin xuciyarsa .
 Wani irin  kallo  Deeni ke yi masa shima   da jajayen idanunsa da suka gama canzawa tsabar tashin hankalin dayake ciki .
 yace " get out from here, live me alone a matuƙar tsawace yayi maganar jikin Fk a sanyaye yabar wajen cike da mamakin Deeni da kuma san sanin wacece  yarinyar da Deeni ke wannan mugun haukan akanta. 




Yakai wajen 15mns  sannan Escort   da Securities  ɗinsa suka dawo, batare da ita ba.
 kansu a ƙasa tsabar jin  tsoronsa  suka ce " we a so sorry sir, a fusace yace " sorry for whats idiot, ya juya a fusace ya  nufi office a hanzarce yaje wucewa ya kalle inda  Ezze yake tsaye a rakube  jikinsa har lokacin rawa yake  " wlh wallhi idan ban ganta ba ko, ka kuka da kanka, ya wuce fuuuuuu tamkar zai tashi sama .

,  yana  shiga office ɗin ya sandare a tsaye, saboda tsabar mamaki ganinta ,wani irin  kallo yake yana mata yana  mamakin ganinta ya kasa furta daidai da kalla ɗaya ce.
 a kishingiɗe ya iske ta akan 3 sitter ta ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya,  gabanta ga table nan da mineral and soft drinks ne masu sanyi gaske  akan table ɗin, sai chips & plaintain with eggs, cikin kwanciyar hankali  take cin abinta. 



Cikin nutsuwa ta ɗago shanyayyun idanunta  ta kalleshi dasu.
 ,her face with silent smile, cikin isa ta miƙe tsaye  tana wata irin shigeyar tafiya da ita kanta batasan ta iyata ba .
 sai karairaya take ta nufo shi, shiko saboda tsabar mamakinta ya kasa koda ƙifta idanunshi ne akanta , sai da tazo daf  dashi ta yadda kowannen su yana jiyo bugun zuciyar dan ,uwansa ta tsura masa shanyayyun idanunta tana kallon cikin idanunshi .
, kallonshi take  eye's to eye's babu  wata alamar tsoro ko fargaba  tace " sorry Dady in future, kasan mace mai ciki da kwaɗayi , gudun karna ɓata maka tym yasani fita na siyo da kaina ta ƙarasa maganar tana kallon chips ɗin data siyo.
, tana wani irin  yatsina face,d inta  takowa tayi ahankali  zuwa inda aka aje tissue ta ɗauko tazo gabanshi ta tsaya .
 tashiga goge masa gumin dake tsatstsafo masa, sannan  tacigaba da magana " 

yanzu '  sai ka gane wanda baƙon al'amari ke shirin faruwa  dashi  tsakanin ni da kai .
Kaga sai muga wanda ya kamu da son wani?

, dan in tabbatar maka da hakan shiyasa nayi maka haka, ka dainayi min gori kullun  akan ina sanka deeni.. ka kuma daina yi min maganar akai-akai, ka daina damun kanka akan maganar  ina son ka, dan babu kowa acikin  zuciyar Nablah ta faɗa hkn tana nuna masa saitin zuciyar ta da yatsan hannuta .

  NASURUDDEEN!!!  ka yarda kai ne ka faɗa tarkon son NABLAH.
, ba nablah ce ta faɗa  sonka ba.
 ji duk yadda ka zauce, ka fita daga hayyacin ka akan Nablah..

, ta dafa  daidai saitin zuciyarsa dake ta faman bugawa da karfi , tace " ko ka yarda ko kar ka yarda wannan zuciyar ta kamu da matsanancin soyayyar nablah .
ta juya tana tafiya tare da cigaba da mgnrta yayinda  kwata kwata bbu Kai acikin  "ZUCIYAR  Nablah ...



Komawa tayi ta zauna tana sakin numafashi da kyar   " au na manta ban faɗa maka ba na buɗe drower ka na ɗauki ɗari biyar na siyo chips, so na mayar maka da canjin.
 am so sorry ban faɗa maka ba kafin na ɗauka  .
, shiko tsaye kawai yake ya kasa yin komai saboda tsabar mamaki,  takowa yayi ahankali har  inda take zaune ya tsura  mata rikitattun idanunshi   ya kasa  komai.
 , wani irin abu yake ji yana taso masa akan yarinyar yana tokare masa kahon zuciyarsa .
, yayinda ya rasa dalili da duk abinda zatayi masa baya jin haushinta, sannan  baya iya yi mata komai.
, amma ya tsaida tunaninsa akan saboda cikin jikinta ne.
, niko nace Oga Deeni kenan.....
, ganin yadda Ya  tsura  mata ido bako ƙiftawa yasata hura masa iska a fusakarshi   " Malam lafiya irin wannan kallo haka kar fa ka cinyeni ?

 Dan murmushi gefen baki yayi tare da rungumota jikinsa ya rungumeta tsam tsam kamar wani zai kwace masa ita.
, jinta a jinkinsa yasa Shi  jin wata irin  muguwar kasala .
tayi lif a faffaɗan ƙirjinsa tana shakar daddaden kashin turarensa me Daga hankali .
ahankali , kowannen su ke  sauke ajiyar zuciya .

Muryata a matukar sanyaye sannan a hankali tace " ka yarda kana so na ko? 

 ka yarda kaine ke sona  bani ce ke sanka ba ko? 

 shiru yayi ya kasa ce mata  komai dan bai san takamaiman amsar dazai bata ba.
, jikinta ta zame Daga nashi  a hankali ta kalle shi tare da cewa .

 " Deeni kana so na? 

Tsura   mata rikitattun idanunshi  yayi kawai ya kasa cewa komai, bai san sanda  ya sake  rugumota  ba.
, duk sukayi shiru kowannensu  da abinda yake tunani a ransa.
, shi kansa bai san mai yake ji  akan yarinyar ba.

,  wayar sa ce ta soma ringing yana ji wayar ta katse aka ƙara kira, a kunnenshi  ta raɗa masa kayi picking ko Ummi ce.
, a hankali ya saketa .
Ta miƙe kwance agurin Shi km ya maida hankalinsa kan Kiran da ake masa  , ganin sunan  Fk ne akan screen ɗin wayar yasa shi jan  tsaki. 
Ahankali km ya furta dan matsala kawai .sannan ya sake tattara hankalinsa akanta tare da kamo duka hannuwata yana massaging dinsu ahankali.
 ya dan hade fuskarshi sosai tamkar bashi ba  yace ki bani   just 20 minti zan kamala da wasu ayyuka ne .
  please Na rokeki  kada ki sake fita koina ,baki ji yadda zuciyata taji ba lokacin danaganki  kina taka step da kyar gurin sauka kasa ... 

Kada ka sake jin komai akaina deeni sbd ni bakowa bace a gurinka facce mai aikinka ..

 rikitattun idanunshi ya zuba mata itama shi take kallo sai taji wani iri ajikinta muryarsa a kasalance yace karki sake aikata irin abinda kika yi min yau.
" nace Ga abinda nake so ..ke km kiyi naki son xuciyar.
 Sosai  ya hade ranshi  yana cigaba da mgn ke ko ba'a nan ba .
Ko a Ina ne ,nace Ga abinda zakiyi kika saba umarnina .
 "zaki hadu da fushina wanda ba zai yi miki dadi ba ..
yana gama fadar Hk ya Mike tsaye fuskarshi cike da  fushin mgnr dayayi yanzu ..kallonshi da kallon office dinsa take tana mamaki sharudansa daya gindaya mata wanda ko ada can Bai taba gindaya mata su ba .

Menene aibun fitar datayi  ?
 Ta tmbyi kanta .


Yau kusan watanin uku kennan rabon data Mike kafafunta a matsayinta Na me ciki kullun yana tsare daita a gida ..
Tarasa meyye Nashi na tsanani da kafa kafa daita tamkar wace zata gudu..

 daman itafa  da biyu ta matsa sai ta biyo Shi duk da batasan office dinsa zai kawota ba.
 tana son taga gari ,gari yaganta  Amman dayake maseefaffen ne Shi zai wani ce kar ta sake ..
 taja wata uwar  tsaki  tana mgn itafa bata son takura gsky tagaji da zama guri dayan nan  tamkar wata bokanya takarasa fadar Hk tare da sake jan wata mugu war  tsaki .
ganin tunani bazai fesheta ba yasa ta runte shanyayyun idanunta ..

 duk wani motsinta na ranar saita tuna yadda Dan karamin bakinsa ke gindaya mata sharadi da yadda taganshi 'cikin tashin hankali sbd fitar datayi .wani lokacin tayi dry wani lokacin tayi murmushi har sanda bacci yasoma fizgarta akan doguwar kujerar dake office din batare data cire takalmin kafafunta ba ...


Yana shigowa ganin irin kwanciyar datayi ne wanda kadan yarage ta fado kasa ,yasa shi saurin karasowa inda take kwance   ya gyarata yayinda zuciyarsa ta tabbatar masa da bakaramin gajiya tayi ba gurin sauka daxu, har hkn yasata yin irin wannan  baccin wahala.

Tsugunawa Yayi a Gabanta tare da zare mata takalmin kafafunta ahankali Dan kada ta tashi fuskarta idanunshi ya tsurawa fuskarta yana kallonta cike da shauki.
 yana kallon sumar  dake kwance a saman goshinta wace ta kusan hadewa da girarta Yacigaba da kallo..tabbas tana da matukar kyau har dana fitina da daukar hankali tare da fizgar zuciyar mutum zuwa gareta koda kuwa Bai Niyya ba.

 tsawon lokaci ya dauka yana kallonta yana jin yadda maganadisun kaunarta ke sake huda kahon zuciyarsa da bin kiwane part na  jikinshi. bakinsa ya Kai kan lip's dinta yabata light kiss kana ya janyo kujera ya zauna yana jiran sanda zata farka ..

Ba ita ta farka ba sai wuraren biyar  saura ..kawai taganshi a Gabanta yana kallonta tare da murza tafin hannunta 'cikin nashi . yatsina fuska tayi tana kokarin mikewa yayi saurin taimaka mata ta tashi Amman still  fuskarshi a daure take har lokacin ya zaunar daita ya kawo mata ruwa mara tsanyi ..ta karba Tasha tana bata fuska .ganin yadda Yayi da fuskarshi yasa taji bbu dadi a zuciyarta 

Tarasa fushin nashi Na menene yake ?

Gabadaya Yanayin fuskarshi yasanyata jin faduwar gaba ta Mike da kyar tare da bude bakinta fitsari zanyi ...Ya nuna mata kofar toilet batare da tace masa komai tashiga shi km yasoma harhada abubuwansa ..tana fitowa .


Kallonta yayi yace " kin gama ci wayan nan abubuwan? 
  fuska ta yatsina tace " eh! , "ok tashi mu koma gida, " to kawai tace ta miƙe tayi gaba yana binta a baya, shiko a ransa Allah Allah yake su ƙarasa gidan dan ya biya buƙatarsa, sanin da Yayi yau su Ummi zasu dawo, yasan idan baiyi yau ba zai  daɗe baiyi ba .
dan yasan Zeenart da nacin tsiya, ballanantana sun dau wani lokacin basu tare.
 ,kuma gashi yana so ya maidaita gida da wuri kafin su ƙaraso.

, a mota ya kira sule direbansa  yace yagayawa laraba  tashiga ta  gyaran koina a gidan har  ɗakin Nablah ta gyara, ya  amsa  masa da toh, boss .

 tuƙin kawai yake dan hankalinsa gaba ɗaya baya jikinsa, sha'awarsa takai maƙura hankalinsa sai sake  tashi yake , yana yin parking ya sureta .
bai direta a koina ba sai a bedroom dinsa , yana ajeta .
ya fita ya haɗo mata hollondia & honey ɗinta na gado  ya zuba mata maganin baccinta  ciki, yakawo mata .
da murna ta amsa  ta kafa kai ta shaye tas.

, fita yayi daga ɗakin ya shiga toilet yayi wanka, kafin ya fito har tayi nisa a bacci.
 kofin na   hannunta, tsayawa yayi a kanta ɗaure da towel iya kuguns  yana dariya ganin yadda ta riƙe kofin a hannunta gam, ta wani ɓata face sosai da gani bataso yin  baccin ba, towel ɗin dake jikinsa ya yar, dama da shi kaɗai ya fito daga toilet, yayi zindir, yana zuwa ya fara cire mata kayan jikinta  dan a matuƙar buƙace yake, zindir yayi mata itama ya Dan ,  tsaya tare da  tsurawa surar jikinta rikitattun idanunshi. 



Sosai yake kare mata kallon tsaf da mayun idanunshi   dogowa ce sosai Yar  siriya, sai dai ba fara bace kyal amma sune wanda ake kira da chocolate colour,   mai cikekken ƙirji, nonuwanta masu shegen kyau ɗas das  dasu sannan a tsaitsaye suke kyam , fatar jikinta  slick, ga laushi da santsi, har kwalli take.
fatar jikinta , irin ta Rihana, tana da faffaɗan ƙugu, gata da wadataccen hips, da ɗuwawu, tana da dogon hanci siriri, da manyan idanu  dara-dara,  kwayar idonta ruwan toka irinta Karishma Kapoor,sai ɗan ƙaramin bakinta, mai ɗauke da fararen haƙora masu wushirya, gata da dimples irin na pretty Zinta,  sai dogon gashin kai kwantacce, ga tsayi ga yawa idan ta sake shi yana kaiwa har wajen ɗuwawunta, tana bala'in kama da Nicki Minaj sosai sai dai tafi Nicki tsayi, amma idan suka tsaya bazaka taɓa tantance wacece Nicki din  ko Nablah ba.
, wata irin ajiyar zuciyar zuciya ya sauke, ya faɗa kan  gadon ya fara tsotsar bakinta kamar zai yi hauka, yana tsotsar bakin yana wasa da kan nononta, bakinsa ya cire daga cikin nata, ya mayar kan nononta sosai yake tsotsar nonon, yana wasa da kan ɗaya nonon, a hankali yayiyo ƙasa da bakinsa yana lasa har yazo cibiyarta tsostar cibiyar yayi, sannan ya mayar da bakin sa kan nononta idonta ta buɗe mai kama dana mashaya, hannu takai kan nononsa ta fara murza masa nipple's wata 'yar ƙara Deeni ya saki saboda wani mugun daɗi dayaji, sosai yake tsotsar nononta tana murza ɗayan a hanakli baka jin komai sai nishinsu, bakinsa na kan nononta ya gangara da hannunsa zuwa gabanta ya fara fingering ɗinta aiko ta ƙara gantsewa tayi ihun ɗadi, Deeni na shan nononta yana fingering ɗinta ɗayan hannun yana wasa da kan nononta, wani irin ihu Nablah keyi, a kunnensa ta rada masa " please suck me, cikin kwarewa ya zare bakinsa daga nononta yana yi mata tafiyar tsutsa a jikinta har yakai bakinsa ƙasanta jin wajen yayi a jiƙe sharkaf, harshensa  yasa yana yi mata wasa da saman ƙasanta, yanayi mata kamar tafiya tsotsa, hannunsa gaba ɗaya suna kan nononta yana murza mata kan nonon, sosai ihun Nablah ya ƙaru, a matuƙar galabaice ta birkice ta hau saman sa ta fara romancing ɗinsa tana zuba  sambatu iri  " please karka bari kaci gaba da jiyar dani wannan mugun daɗin, bakinta ta kai kan nipply din sa ta shiga tsotsa tana wasa da ɗayan nonon. 


Wani irin nishi Deeni ke saki a jere babu kyakkyauwa, Deeni bai ida zaucewa ba sai da yaji bakin ta akan jijiyar sa tana, tsotsar ta, yadda kasan dama can ta iya, sosai take sucking ɗin sa, tana wasa da kan nononta.
 baki Deeni ya buɗe ya shiga ihu, janyo ta yayi yace " please Nablah sex me, a hankali ya kama jijiyarsa ta danna ƙasanta ta haye samansa ta shiga sukuwa, tana cinsa tana wasa da kan nononsa, ihu Deeni yake yi sosai da iyakacin  ƙarfinsa, abinda bai taɓayi ba kenan a rayuwar sa, itama ihu take, taci game  da yin sama da ƙasa kan ruwan cikin Deeni, Deeni yace " wayyo daɗi wallahi ban taɓa cin mace mai daɗin ki ba.
, dama akwai mata irin ku a duniyar nan , wayyyyyoo ni Deeni nabar daɗi ashe .
, wayyohhhyyy wayyyyyoo Nablah please karki barni idan kika barni zan shiga halaka , arayuwata zatashiga garari , wayyohhhyyy mutuwa zanyi idan kika barni.
Wayyohhhyyy Allah  daɗi, daɗi, Nablah kina da daɗi ke ta dabance, wayyyo, ita ihu shi ihu, tun  7 pm  suke abu daya basu suka daina ba sai  10.pm shima badan ya ƙoshi ba, sai  dai kyale ta ne kawai, gyara mata jiki yayi ya shiga wanka, tunda Deeni yake arayuwar sa bai taɓa jin daɗin sex ba  irin na yau.
 shiyasa gabadaya ya kasance cikin farin ciki da fara'a, bayan ya fito daga wanka ya kimtsa, ya tada sallah, yana sallar ta farka, bata kawo komai a ranta ba, murmushi ɗauke a fuskarta, har Deeni ya idar ya kalle ta, a ransa yace " da alama itama taji abinda naji yau, a zahiri ya ɗan ɓata face yace " Malama ki tashi kiyi sallah mu tafi yau su Ummi zasu dawo, fa dammmmmm!!!!!!!  taji gabanta yayi muguwar faɗuwa nan da nan idonta suka canja daga farere zuwa ja, duk da Ac dake aiki a ɗakin hkn Bai hana gumi ya shiga tsatsafo mata ba.
 Shanyayyun idanunta ta zaro waje cikin sanyi tace " Please da gaske? 




Murmushi yayi ya tako har zuwa  gabanta ya sunkuyo yace " ba Deeni bane ya kamo da san Nablah ba.
, Nablah ce ta kamo da mugun  son Deeni sosai tashiga tafkin sonshi ta nitse . ji yadda lokaci ɗaya kika canja, kika zauce dan kinji Matata zata dawo.
, yasa hannushi  a saitin zuciyarta,yaji yadda take bugawa da sauri tamkar yadda tayi masa shima , "  ki yarda ko kar ki yarda wannan zuciyar ta kamu da mugun san Deeni, haɗi da mugun kishinsa, shiru tayi dan ta fahimci ramawa yayi, cikin mutuwar jiki ta miƙe ta shiga toilet, ya bita da wani irin  mayataccen kallo ba  har bai san lokacin daya furta *MAI DAƊI* tare  da  lumshe rikitattun idanunshi  yana haɗiyar wani mugun yawo.
, a toilet ma  kasa  komai tayi  sai aikin tunani, kardai, da gaske na kamu da san Deeni,ne kmr yadda yasha gaya min  aiko idan harda gaske ne zuciya ta bakiyi min adalci ba wlh .
, dan nasan na ashiga uku, na ɗebo ruwan dafa kaina da kaina .
 Ya zan yi  da Zeenart ?

 wannan muguwar matar tasa me shegen kishin maseefa ai sai ta kashe ni, to wai ma ni da nake wannan haukar  tunanin cewa akayi yana sona?

, ko zai aure ni,?

 nasan Deeni har abada yayi min nisa yafi ƙarfi,shi din ba ajina bane  bakin ƙofar toilet ɗin yazo yace " ko inzo inyi miki wanka ne.
, yana jin sanda ta sauke naunauyen ajiyar zuciya, yayi dariya yace " ana son  Deeni,,harda tunaninsa    amma anƙi yarda da ana sonshi.





MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO




~DEDICATED TO~
*HAUWA A USMAN*
     _JIDDARH_



Page 92



Wanka tayi Zuciyarta cike da tunaninsa  ...


Ta fito fuskarta a d'aure tana  ciccin magani, wanda kafin fitowarta oready deeni ya gama shirinsa tsab  ita kad'ai yake jira ..muryasa a sanyaye yace Kin hanzarta fa yau zamu koma gida domin jirginsu  first love Na gab da sauka.. 

 Take taji Gabanta Yayi mugun faduwa hankalinta ya tashi matuka da jin abinda yace ,ahankali km  zuciyarta tashiga harbawa da sauri da sauri .
cike da sanyi jiki tasoma Shiryawa itama  'cikin wata  doguwar rigar redymedy zuciyarta Na sake narkewa akan tausayin kanta .

Ta zauna  tare da  tsura masa shanyayyun idanunta .
dan murmushi ya sakar mata, tare da  kashe mata idonsa d'aya yace " lafiya Mrs Deeni naga duk Kin hargitse ?  
Rasa yadda zatayi ne yasa  cikin shagwab'a tace " ni yunwa nake ji, kitchen ya nufa ya had'o mata tea mai kauri, har ya dawo ya zauna a gefen ta, hannunsa rik'e da cup din tea amma bata sani ba,a kan bed site ya aje tea d'in .
 zuba mata lulu eyes d'inshi yayi had'e da hura mata iska a face dinta 


Naunauyen Ajiyar zuciya mai k'arfi ta sauke, bata ce masa komai ta zuba masa shanyayyun  idanunta, ganin ganin da suke yiwa juna yana neman sanya masa kasala ne ya sanshi kawar da kansa gefe, ya mik'e tsaye daga kan gadon zai fita tayi saurin rik'o hannushi juyowa Yayi da kanshi ya sake  tsareta da rikitattun idanunshi yana kallon fuskarta batare da yace mata komai ba .
 cike da sanyin jiki , muryata har d'an rawa tayi gurin cewa please let me stay  here ka barni anan na nacigaba da zama  tsoron komawa gidanka nike ....


Sort hannunta dake kan damtsen hannushi yabi da wani irin kallo batare da yace komai ba
", da sauri ta sakeshi ganin hannuta yake kallo  ta sunkuyar da kanta kasa a hankali ya koma ya zauna kusa da'ita sosai akan gado wani irin murmushi tayi wanda suka  bayyana fararen hak'oranta da wushiryarta saboda tunaninta zai barta anan din ne kamar yadda ta buk'ata, cikin wata irin murya mai karyawa namiji gab'ob'in jiki tace "  thank you so much Dear,  tsuntsun soyayya ...sai da numfashin sa yakusan d'aukewa saboda yadda tayi maganar...da kyar ya iya controlling d'in kanshi ya dukar da kanshi kawai yana gyara gaban rigarsa hakan nan taji tana 'cikin farin ciki da jin dad'i  cup d'in ta dauka batare da ta cire idanunta akanshi ba zata kurbi hot tea din daidai ya d'ago kanshi da sauri Ya rik'e cup d'in hannuta  yace"is so hot.. wani irin uncontrollable smile take masa tana kallon fuskarshi da sauri ya karb'i cup d'in daga hannuta yana juya tea d'in da wani cup saboda Yayi tsanyi ,yana tunanin a ranshi sunan data kirashi dashi ahankali ya furta sunan akasan ranshi tsuntsun soyayya.

To me wannan sunan yake nufi ?
,  yadda yake mata ne ya sata afkawa 'cikin duniyar  tunanin kodai deeni ya fara sonta ne da gaske kmr yadda take tunani ?

Take ta Kawar da wannan tunanin  ganin hkn ba me yiwuwa bane atsakaninsu .. ta d'an juyo ahankali 'cikin sanyin jiki  ta kalli fuskarshi shima  ita yake kallo ganin yadda ta rik'e kuncinta ta zuba masa shanyayyun idanunta da sauri Ya d'auke kanshi Ya cigaba da juya tea a hankali ya d'ebo a spoon ya Kai bakinshi yasha jin babu zafi,  Ya juyo yayi facing d'inta sosai ya debo a spoon yakai daidai  tsaitin bakinta wani irin murmushi tayi ta nuna kanta tare da cewa u won't to feed me Deeni ..?

Gyad'a mata kanshi Yayi kawai batare da ya iya ce mata komai ba .. wani irin  tattausanshen murmushi ya kufce mata  ya bayyana sosai akan fuskarta hannuta d'aya ta daura akan kafad'arsa domin son shagaltar dashi sai da numfashinsa ya kusan tsayawa lumshe rikitattun idanunshi Yayi sannan ya bud'e. murmushi tayi tare da turo masa dan  karamin tsukaken bakinta alamun yabata da kyar jikinsa a sanyaye yasamu Yayi controlling din kanshi ya Kai spoon d'in dake cike da tea bakinta yana mamakin yadda ta dawo masa ta kara sakin jikinta dashi hadiye tea tayi tare da lumshe idanunta dan ji tayi tamkar ba tea ta Sha ba ..

Ringing din  da wayarsa tayi ne yasa shi dawowa 'cikin  hanakalin shi,  'cikin damuwa ya ciro wayar yana kallon yadda take yanayinta  ya sauya a hankali yake kallon screen d'in wayarsa yana murmushi sannan ya d'au wayar yasa a kunnenshi Yayi shiru na kusan minti biyu sannan a hankali yace am sorry my sweet first love don't angry with me ganin nan zuwa ..kana Yayi shiru yana cigaba da kallon nablah dayaga hawaye sun cika mata idanunta ..
Muryarsa can kasa kasa km a sanyaye yace please ki bar damuwar nan I told you nothing will  happen, zan San yadda zanyi , hawayen idanunta suka karasa zubowa ..

Murya umminsa ta daki dodon kunnenshi son kayi sauri fa mun kusan hausa  Ok   first love ganinan zuwa,  ya Mikar  daita tsaye yana gyara mata hijab din dake sanye ajikinta Bai tsaya wani  karewa yanayin yadda take ba.
 ya sureta sai 'cikin motar.
Tare da yiwa  ' motar .key  suka bar gidan taba ganin sun doshi hanyar jakonde first get  ta fashe da wani irin matsanancin kuka me ban tausayi ..


Koda suka shiga estate din ma koina   shr baka jin motsin Komai .
kowa Na 'cikin part dinsa securities din bakin get suka mike tsaye suna  faman aikin  gaisheshi ..


Kai tsaye d'akinta ya kaita  ya kwantar yana rarrashita muryarta can kasa tace dee...Ni Ni tsoro nake ji nasan kwanan nan zan bar gidan nan , da zarar matarka taga 'cikin jikina takarasa fadar mgr tana rera kuka ahankali deeni Yayi salati ya zauna a gefenta tare da tattara duk wata natsuwarsa ya maida kanta  sannan yace ,wa yace miki hk ?
Girgiza masa  kanta  tayi da wani irin murya me cike da ban tausayi tace xuciyata ce ta sanar dani.
 dan girman Allah Na rokeka kada ka fasa taimaka min kmr yadda kayi Niyya tun farko  please  ta hada hannuwanta dukka..shr Yayi sbd Yadda take kukan har 'cikin zuciyarsa yake ji ..

A natse yakira sunanta nabeelah ..da kyar ta amsa tana kallon ciki. Idanunsa .
 " kinga oready yanzu  su ummi sun sauka ni kadai suke Jira please allow me to go and pick them please .. ban yi niyyar barinki ba har sai na isar da kudirina akanki  .
 dan hk Na rokeki ki kwantar min da hankalinki ta yadda zaki haifa min bby nah 'cikin koshin  lfy yana gama fadar hkn ya Mike tsaye tare da dan rutsunawa Yayi pink din goshinta ya bar gidan tare da securities dinsa  zuwa airport..

Tun daga nesa zeenat ta hango kyakkwan mijinta me cike da kyawu  da  haiba.
 ta lumshe idanunta tana jin wani irin farin ciki mara misaltuwa aciki zuciyata hakika tayi kewarsa fiyye da tunanin me karatu .
Sosai ta kura masa idanunta  har sanda yakaraso Inda suke 'cikin isa da kasaita  ya rungume umminsa yana murna da ganinta suna hada ido da zeenat kuwa ya kashe mata idonsa daya tare da furta mata I Miss you a saman lips dinsa ...
Lumshe idanunta tayi sbd ta fuskanci abinda yace ..ummi tayi murmushi ita kanta tayi farin ciki da ganin tilon Dan nata ....
Ya riko hannun umminsa yana mata sannu da zuwa   first love nayi missing din ki to the extended I can't explain it , .
"really my son ?
 "Off course my sweet first love sannan suka soma takowa ahankali  zuwa Inda jerin motocinsa ke jiran karasowarsu ....ummi tashi bayan wata hadaddeyar mota  range rober ta zauna yayinda deeni da madam dinsa suka shiga  byn wata motar daban ..dereba yaja .....

Zeenat na shiga 'cikin motar ta zube jikin deeni tana narke masa ,"my hrt I really miss you .... Like kilode Yayi murmushin me kara masa kya sannan yace  "missing you  too my wife hade da  manneta da jikinsa yana me kamo  tafin hannunta 'cikin nasa yasoma  murzawa yana kallonta  "you look so nice dear me umminki take baki ne acan India kika canza hk ?
Yakarasa fadar Hk yana  me hade fuskokinsu guri daya tayi murmushi my hrt kennan  ai Kai ne ma naga gaba d'aya  ka sauya ka kara kyau kayi fresh  tamkar bakayi missing dinta ba.
 ya kamo lips dinta yana tsotsa yana kallon 'cikin idanunta kana yace "Allah ko?
Ta d'age masa girarta d'aya Murmushi Yayi wanda a ranshi km yace bazaki gane sirrin abun ba zeenat, ai dole na canza tunda Ina samun abincina enough Ina ci ..gefe daya km Ga burin rayuwata da ake shirin haifar min .
 ta tsura masa idanunta sosai  tana kallonsa daidai sanda motarsu tayi parking a harabar compound din planums rows family estate.
 ya runtse idanushi yana kokarin fitowa Daga motar yayinda oready har Ummi ta fito yakarasa yana riko hannun Ummi suka karasa shiga 'cikin  gidan, a parloh suka zauna gaba d'ayan su cikin nutsuwa Nablah ta fito daga d'aki face d'in ta d'auke da murmushi, yayinda gabadaya hankalin  Ummi da idanunta na kan cikin jikinta , tana murmushi, durk'usawa Nablah tayi zata gaida Ummi, da sauri Ummi ta d'agota.
Tare da  rungumeta tace, "I miss you dota so much, cikin dariya Nablah tace " I miss you too Ummi.
, Ummi ta zaunar da Nablah a kusa da ita,  ta kalli inda Deeni ke zaune  tana  murmushi.
 dariya yayi ya kashewa ummi   ido d'aya.

,  tsaki Zeenart tayi tana jin wani irin mugun haushi dan gabadaya ita ta manta da halita da suka bari a gidan .. ahankali deeni mike tsaye  ya hau sama itama , Zeenart tabi bayan shi, Ummi tace wa Nablah " bari nayi Sallah, "to kawai nablah ta iya cewa ... 



Suna manne da juna har 'cikin dakinta hannuwansa duka zagaye da kugunta  sai shagwaba iri iri take zuba masa tare suka zube akan bed suna fidda numfashin tashige jikinsa tana narke masa shr Yayi hankalinsa gaba daya yana gurin nablah ..



Dan yasan tana can cikin damuwa, kuma ya tabbata bazata iya  cin abinci daya zame mata jiki ba duk dare.
Uwa uba ,  kewarta ke  damunshi ahalin yanzu , mik'ewa yayi yacewa Zeenart " yana son Yayi  wanka, aiko zambur itama ta  mik'e,tasoma cire masa   kayan jikinsa tana romancing din jikinshi ..tare suka shiga bathroom  byn itama ta cire nata, soap ta d'auko da shiga yi masa wankan cikin wani irin salo.
, aiko take  wutar dake yawo cikin kwalkwaluwarsa   ta d'auke, a hankali take goga masa sabulun a jikin sa, tana kallon yanayin face d'in shi, ganin ya lumshe ido ne ya tabbatar mata da sak'onta na isa gare shi, can km a hankali ta canja salon wankan.... 


Kan nipple's d'insa ta shiga murzawa, cikin wata irin murya tayi masa rad'a a kunne " are miss you me my hrt .
Did you miss me ?
Ya kashe mata idonsa daya .
Natsuwa da farincikina Bai dawo 'cikin gabobin jikina ba sai da Na dawo gareka Ina mugun sonka mijina ... yadda take maganar tana goga masa nononta a kirjinsa tana hura masa iska bakinta  a kunnene ya hana shi magana, daga kunnensa ta rink'a tafiya da bakinta har tazo saitin bakinsa, light kiss tayi masa tace " I miss your body Dear, hannunsa ta d'ago ta d'ora akan nononta, ta shiga tsotsar bakinsa a gigice.... 


Sosai Deeni ya rud'e dan da wani irin salo tazo masa, bakinsa ya cire daga nata yamayar kan nononta sosai yake tsotsar nonon, yana wasa da d'ayan nipple's d'inta, d'aya hannun yana k'asanta yana fingering,d inta  aiko kusan suma ne kawai  Zeenart batayi saboda wani irin  dad'i, sosai Deeni yake romancing d'inta duk sun gigice, Zeenart sai faman sambatu take " wayyyo Deeni zaka kashe ni da dad'inka, ina sanka my life bazan iya rayuwa babu kai, wayyyyyo dad'iiiiiiiiii, dammmm!!!!  Gaban Deeni ya fad'i dajin kalmar da Zeenart ta fad'a sai ta tuna masa daa Nablah, _wayyyyyo dad'iiiiiiiiii_ murmushi yayi na gefen baki, yace " I miss you my N..... 


Dan duk a tunaninsa da Nablah yake tare, sai a lokacin ya dawo haiyacinsa ya tuna da wacce yake tare, a hankali ya zame jikinsa daga na Zeenart, k'ara biyo shi tayi ta rik'o shi a gigice, " please my life karka daina, kallon yadda duk ta wani gigice yayi, tana k'ok'arin mayar da bakinta kan nasa yayi baya yace " ki bari muyi wanka muyi sallah muci abinci first ..... 



Mirgina masa kai tayi " Ni a'a please sex me,  cikin yanayin gajiya da maganar yace " yunwa nake ji, bai jira amsarta ba ya fara wanka, da kallon mamaki ta bishi, bakinta a bud'e take kallon sa, a ranta tace " ayya kuwa Deenin dana sani ne kuwa wannnan?

, Deeni dako kiss nayi mashi bai hak'ura zai gigice sai yaci  yake hakura  Deenin da kwata kwata baya  bada uziri akan sex, kuma ma how many months mukayi bama tare ?
Amman ace  baiyi missing d'ina ba?
, tana cikin wannan  tunani taji ya bud'e k'ofar toilet d'in ya fita, ya barta da sauri tayi wankan itama  tabi bayan sa...... 


shiryawa yayi cikin kayan bacci yace mata " ina zuwa, kiyi sallah ki shirya yanzu zan dawo, yana maganar yana tafiya,bata bashi amsa ba, ta shiga shafa lotion tana cigaba da nazarin mijin nata .... 


Direct to  bedroom d'inta ya nufa, ya iske bata nan, fitowa yayi yana neman ta, motsin mutum yaji a kitchen, dan haka ya nufi kitchen, tsaye ya iske ta tana  wanke hannu a sink, ta baya ya k'arasa ya rungumota, jikinshi  ya d'ora hab'afarsa akan kafad'arta, ya zagayo da hannayensa,duka saman  cikinta  yana shafawa yaNa lumshe idanunshi a tsorace  tace " waye?  


"Waye kuwa in banda ni, kema kin san kowaye, ai.
A hankali face d'inta d'auke da murmushi ta cire hannuwansa duka daga zagayenta dayayi ta jiyo, tana facing dinshi, shanyayyun idanunta suka  yi ja sosai, da gani taci kuka ta k'oshi, .
kasan kuma murmushin yak'e take, a hanakali ya kamo hannunta zuwa bedroom d'inta, a bakin gado ya zauna, ya zaunar daita akan cinyarsa, ya d'an b'ata face yace " kuka kikayi ko? 


Kai ta girgiza masa alamar a'a, yace " gashinan har wayan nan shanyayyun  idanun naki sun  kumbura, .

ko duk kishin nawa ne?

, da sauri ta d'ago red eyes d'inta ta kalle shi, yace " yes ya kashe mata ido d'aya, sunkuyar da kanta k'asa tayi, tace "ni dai a'a bawani kishi, " to naji me ya saki kuka, shiru tayi sai kuma can tace " ina aiki ne abu ya fad'amin a ido, " What!!!   aiki? Ya tmby a hargitse . 


"Uban wa yasaki aiki?  bana ce maki ki daina aiki ba, "a tsorace tace " please am sorry ta fad'a tana kama kunnenta, yayinda  face d'inta ke cike  alamar shagwab'a, dariya ta bashi sosai amma ya kanne baiyi ba, yace " to mai yasa baki jin magana..... 


"No ba haka bane, naga Ummi ta dawo kuma nasan tayi missing abincin Nigeria, musamman tuwo kasan Ummi dasan tuwo, da farfesun kayan ciki, shine fa nayi mata, dan in faranta mata, ina san ganinta cikin farin ciki da walwala, bak'aramin dad'i Deeni yaji ba, murmushi yayi sosai yace " Thank you so much, yanzu me kika dafa? 


"Tuwon shinkafa miyar Agushi da bushashshen kifi, da ganda, sai farfasun kayan ciki, da copee, " ok yace  yana had'e bakinsu waje d'aya, sosai yake shan bakinta,.
can km  yafara tsotsar nononta gaba d'ayan su sun gama fita haiyacinsu, cikin rawar jiki yace " please Nablah don't live me, sosai yake shan nononta, fingers dinsa  yakai k'asanta yana shirin fara fingering d'in ta, .
Tayi sauri ta ture shi,da karfi  ta koma gefe tana sauke ajiyar zuciya, rub da ciki ya kwanta yana mai da numfashi... 


Cikin wata irin murya tace " please ka fita a dakin nan  kar wani ya shigo ya same mu hk .
Ya Mike yana aiko mata da wani irin kallo Na bata isa ba ta sake marairaice fuska zatayi kuka please deeni ka taimaka kada kace a'a , ba musu ya Mike tsaye  ya fita, yana fita su kaci karo da Ummi, kallan tuhuma Ummi ta shiga yi masa, k'eyarsa ya shafa yace " Ummi Kina nan? 


A'a ina India, ta fad'a tana harararsa, kansa ya k'ara shafawa yayi murmushi yace " my first love, suna 'cikin  haka Zeenart ta sauko ta same su a falo, da fara'arta ta k'arasa kusa da Ummi ta zauna tace " Ummi yunwa, dariya Ummi tayi tace " mijinki zaki GAYAWA, kallon sa tayi taga hankalinsa gababaya baya wajensu, tace " Ummi naga kamar dianing  table a shirye yake ko? 


Kallon dining d'in Ummi tayi tace "eh kamar haka ne, Ummi ta kalli Deeni tace oya get off, kallonta yayi yace Ummi na k'oshi, ido kawai ta zuba masa, murmushi yayi yace " muje first love, gaba d'ayan su suka mik'e suka nufi dinning, Nablah ta fito, 


Fuskarta fayau, kallonta Ummi tayi tana murmushi tace " Yar albarka  ya zaman kad'aici, hope babu wani abu ko? 

Murmushi nablah tayi kawai sannan  tace " babu komai Ummi sai kewarki, ta fad'a tana langwab'ar da kanta, dariya Ummi tayi tace " nima nayi kewar ki sosai .
, Zeenart ko najin hk ta had'e rai kamar taga mutuwarta, hankalin Deeni yana kan Nablah da Ummi yana murmushi, tsaki Zeenart tayi ta kawar da face d'inta gefe, gaba d'aya suka kalle ta...... 


tab'e baki Deeni yayi, Ummi tace " me kika dafa mana Nablah,?

 murmushi tayi tace Ummi towan shinkafa da miyar aguahi nayi miki sai farfesun kayan ciki, " masha Allah Diyar albarka, Allah yayi miki albarka ya baki zuri'a nagari, Ubangiji ya albarkaci tsatsonki, Allah yasa zuri'arki ta kasance d'aya daga cikin wanda Annabi zaiyi alfahari da su ranar alkiya, "amin Ummi nagode, Oga Deeni bai san sanda yace " Amin Amin Ummi ba, harararsa Ummi tayi, tace " nablah  zuba mana abincin, "to tace ta fara service d'insu, tana bud'e food flask din abincin k'amshi ya gauraye wajen baki d'aya, lumshe ido Deeni yayi yana shak'ar kamshin abincin, sai lokacin wata mahaukaciyar yunwa ta taso masa, yawunsa ya tsinke, k'amshi ya bugi kowa, Ummi tace " masha Allah nablah akwai iya abinci ko a ina zanyi alfari dake akan girki, .
Oga a ransa yace " har a b'angaren karb'ar jijiya gwana ce, bayan ta gama zubawa kowa ne.
 ta juya  zata tafi ta manta bata zuba musu coffee ba.... 


Aiko cikin zafin rai Zeenart ta fisgota ta wanka mata mari tace " uban waye zai zuba mana coffee? 


Ta hankad'a ta, tafiya Nablah tayi taga-taga zata fad'i rubda ciki, aiko cikin zafin nama Deeni ya taro ta ta fad'a saman fadadden k'irjinsa hannu yasa ya rungumo ta jikinsa sosai,Ummi ta mik'e tsaye tace " wai ke me yasa baki da hankali Daga dawowar  .....ai Bata k'arasa ba taji tassssss,  wasu mahaukatan mari Deeni ya zubawa Zeenart, har alokacin yana rungume da Nablah akirjinsh............



MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
     💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO



      Dedicated to
*HAUWA A USMAN*
       (JIDDARH)





Page 93


Tare da aika mata  da wani irin kallo me cike da tsansar  jin haushin abinda ta aika .
ba zeenat dake tsaye  rike da kuncinta  ba hatta ummi hankalinta Yayi mugun tashi akan abinda deeni Yayi .
 " domin bata tunanin  deeni zai iya koda zagin zeenat bane akan nablah agabanta .
 ballanantana mari, ba daya ba har biyu ajire ..

wani irin kallo zeenat ke bin nablah dake kamale ajikin mijinta km wanda   tafi so fiyye  komai dake 'cikin duniyar nan .
Ahankali tasoma yin kasa kasa  'cikin slow motion ta zauna jagwab akan kujera datashi tana cigaba da kallonsu zuciyata Na mata wani irin zafi da radadi .
kishin mijinta ne kawai ke cin ranta da kirjinta take zuciyarta tashiga  harbawa da surin maseefa ..ta rantse idanunta gam dan bata kaunar sake daura idanunta kanshi dake like da juna tamkar wasu miji da mata .. 

Yayinda nablah dake jikin deeni  tasoma kokarin fexgewa Daga jikinsa Amman yaki sakinta sai kallon zeenat yake da rikitattun idanunshi. domin  ita kanta nablah  wani irin razananniyar  tsora ne yashigeta tashiga tunani kardai da abinda take tunani ke shirin faruwa ?
Kennan gaske ne deeni ya fada tarkon sonta ko yaya?
  Matarshi fa ya mara agabanta akan 'cikin jikinta wanda tasan bashine mutumin dayayi mata ba idan kuwa hk ta faru bata San yadda zatayi da rayuwarta ba nan wani kuka me karfi ya kufce mata ..

Ahankali deeni ya dauke idanunshi akan zeenat batare da ya kalli inda ummi ke tsaye tana aiko masa da kallon mamaki ba yayi hanyar step da nablah a barin jikinshi ..har suka wuce zeenat batasamu bude idanunta ba sai ma wasu Hawayen takaicin rayuwa suka samu nasarar biyo kuncinta gabadaya komai ya tsaya mata cak.

To me hkn yake nufi?

Me take shirin Gani km yau a gidanta Daga dawowarta ? 

Allah Allah ka duba min al'amarina ....
Ka tausayawa rayuwata kamin maganin maseefar dake shirin kusantoni da al'amarina gabadaya kada kabari wata maseefa tashiga tsakanina da mijina .Hk  ta dinga  fada  a 'cikin ranta ummi ta matso sosai kusa daita tana goge mata hawayen dake silalowa a kuncinta batare da tace mata  komai ba .
Domin  ita kanta taji mugun  zafin marin da deeni Yayi mata a gaban nablah,  amman tasan abinda zatayi ..

 Har sanda deeni yakaita dakinta  kuka nablah take Na fitar hankali sbd  gabadaya a tsorace take da ganin yanayin  zeenat da ummi.
  'cikin natsuwa  yakarasa ya  zaunar daita akan gadonta hade da janyo karamar stood din dake gefen bedside dinta ya zauna ya kamo hannuwanta dukka'cikin nashi yana murzawa ahankali ahankali tare da  tsurawa beauty face dinta rikitattun idanunshi yana kallonta.
 zuciyarsa Na masa  wani iri tsalle tamkar zata tarwatse ta fasa kirjinsa ta fito.
 muryarsa a sarke ya Kira sunanta ,ta dago shanyayyun idanunta ta zuba 'cikin nashi  kukan ya isa hk ....Ko wani guri Na miki ciwo ne?

Ta girgiza masa Kanta batare da tace komai ba.
Ok  ki natsu yanzu kibar kukan nan hk  kinsa bake kadai bace damuwarki zata iya shafar lafiyar bby nah .
 still shr tayi taki cewa komai yayinda km aranshi ya dinga jin zafin hasarar da zeenat taso yi masa.

 meyasa zeenat bata tausayin takala da rabarsa  ?

 Meyyasa take kyamar talaka da nisanta kanta Daga gareshi ?

Meyasa  girman Kai da kudi ke fusgarta da yawa.. har ta dinga manta kalar tarbiyar da umminsa tabata?
 shi yasan  Sam wannan ba kalar  tarbiyar umminsa bane sannan km ba halin mahaifiyarta  ta dauko ba mace me tsananin hakuri da son mutane . 
Shi ya rasa Ina tasoma wannan halin nata Na girman Kai da Kin talaka da nuna kowa bakomai bane  wanda ko acikin family itace lidar kowa . gabadaya zuwa  yanzu halayenta sun sake  canzawa fiyye da kowani lokacin  Wanda  can da Bai santa da hkn ba Amman yasan hakan ma  yana da nasara da sababbin kawayen datayi .
 Naunauyen ajiyar zuciya ya sauke da karfi yana jin a ranshi komai zai faru sai dai ya faru Amman wlh  kan 'cikin jikin  nablah sai dai   sirrin boye ya fito filli kowa yasan abinda ake ciki .
 ....Ya kamo fuskarta da hannuwashi duka yana kallon 'cikin kwayar idanunta ya dinga jin aranshi  da yana da iko akan kanshi, da dauketa kawai  zai yi gabadaya Daga kasar ,zuwa wata kasa daban su cigaba da rayuwarsu hankali kwance 'cikin natsuwa yashiga tunanin rayuwar da sukayi a sabon gidansa ,rayuwa me cike da jin dadi da natsuwa wanda wani lokaci har manta yake da matsalar komai ....
 bakinsa ya Kai daidai  kan lip's dinta zai tsotsa tayi saurin  kawar da fuskantar tana yatsinawa  tare da  zubawa plate din abincnta data dibo ajiye da niyar ci  idanunta ahankali ya maida idanunshi zuwa Inda take kallo din .
 ya tashi ya  dauko mata plate din  abincin  ya daura  kan tsood din daya tashi ya zauna a gefenta ,kici abinci please...Babu wani westing time  tasoma  ci dan  wani irin yunwa take ji tun tea data Sha agidan glass ne ke cikinta.

Deeni Bai bar dakin ba sai daya tabbatar da nablah taci abinci sosai tasha ruwa  sannan  ya sata tayi wanka dan taji dadin jikinta ya kwantar daita ya lullubeta da blanket ya duko sosai inda take ya tsotsi lips  dinta ya rage mata karfin AC dakin yaje ya kashe fitilar daki kana ya baro dakin tare da kulleta ciki dan gudun bala'i abinda zeenat zata iya mata .

Sosai hankalin ummi ya sake  tashi da ganin irin halin tashin hankali da diyar tashiga.
 ahankali muryar   ummi a sanyaye tasoma   rarrashin zeenat tana bata hkr akan abinda deeni Yayi mata  sannan ta nuna mata itama nata kuskure akan abinda tayi  Bai kamata ba mamana  abinda kikeyiwa  nablah domin  kowane dan Adam yanada nashi baiwar da Allah Yayi masa .
har sanda deeni ya dawo Dining din ummi Na zaune tana faman   aikin rarrashin zeenat dabata baki  Amman kwata kwata zeenat din bata San abinda ummi ke ce mata ba sbd gabadaya ta  dawo tamkar mutum mutumin tsabar mamaki da frigicin abinda deeni Yayi mata a gaban me aikinta.

 ganin tahowarsa  yasa ummi yin  shr da bakinta  ta hade ranta tamau tamkar wacce aka  aikowa  da mutuwa. shima ganin hk Yasa ya  hade nashi  ran sosai fiyye da tunanin me karantu idan baku manta ba daman kusan halin deeni da shan kamshi maseefa .


Gabadaya kuka zeenat take son yin Amman yaki zuwa mata  sbd tsoro da mamakin dake daskare akasan zuciyarta.
Wani irin zafi  kirjinta ke mata  tamkar ana zuba mata yaji .. gabadaya abun ya girmama tunaninta.
 to me hk yake nufi ?
Ta sake tmbyr kanta .

 Takasa kuka ta kasa hauka ta kasa komai sbd abin ya girmi momery dinta  zaune kawai take tana jin sautin  muryar ummi sama sama batare da tana  fahimci inda maganganunta suka dosa ba ..
yau Deeni mijinta ne  ya mareta akan wata watan ma me aikinta  kennan hkn Na nufin ya daina tsanar yarinya yanzu ko me ?
 Idan kuwa hk ta faru a 'cikin gidanta  da kuwa  ta shiga ukunta ..

Deeni Yayi tamkar babu abinda ya dameshi ya zuba tuwan da kanshi hankalinsa  kwance yasoma yaci batare da wata damuwa ba  yana zuba  santin tuwan acikin zuciyarsa .
 wani irin dadi tuwan yake ji Yayi masa
 ko kallon inda zeenat ke zaune bai yi ba ballanantana yasan damuwarta . 
 "yayinda hkn kuwa ya sake taba zuciyar ummi sosai  to me wannan salon nasa yake nufi?

 kardai gadar zaren  data shirya  diyarta ce  ke shirin ruftawa ciki ?
 

Jiki a sanyaye ummi ta Mike tsaye tare da duban Inda deeni yake wanda  oready tuni ita tagama tsakurar tuwanta .
muryata tamkar zata zubda kwala tace deeni muje Ina nemanka a daki.
 shi kanshi yadda yaji muryar umminsa da yadda  yake kallon yanayinta yasan ranta a bace yake matuka  akan abinda Yayiwa zeenat  yanzu dan hk shima  muryasa can kasa kasa yace Ok sannan ummi ta nufi daki..

Byn kmr minti Gona  sai gashi yashigo dakin yana ciccin magani sannan km fuskar nan tashi a daure still ya zauna a kujerar dake facing din umminsa .
 ummi har lokacin jikinta a sanyaye yake .sai data numfasa kana tace yanzu deeni Kai kana ganin abinda kayi ya dace kennan? A gabana deeni ka mari zeenat kan matarka dan tsabar ka rainani takarasa fadar hkn tana nuna kirjinta wlh kabani mamaki .km ka tsinka min zuciya .idan wani yace min a gabana zaka aikata hk wlh zance karya ne ..

Sosai ummi tashiga yi masa fada ta inda take shiga bata nan take fita ba.. kafin km  daga baya ta dawo yi masa  nasiha me ratsa jiki da zuciya.. yanzu abinda kayiwa zeenat  akan wannan yarinyar Yayi kennan ?
Nice fa  tamkar mahaifiya Ga zeenat.
Zeenat  bata da kowa acikin duniyar sama dani da mahaifinta sai Kai mijinta , Amman dan cin fuska agabana ka zage ka mararmin yarinya dan rashin mutunci.

kai kanka kasan banason aurenka da zeenat.
 duk duniya bbu abinda zancewa zeenat banaso Amman ta kafe ita taji tagani tana sonka km taji tagani    zata iya zama da baudaden hali irin naka.
ka tuna rayuwarku deeni ka tuna..bbu abinda banyi ba zeenat akan rashin son aurenku  ta rufe idanunta  tace ita Laila tana sonka.
 ka tuna abubuwan da tayiwa kannen mahaifinta agabanka deeni ka tuna wulakanci dakayiwa kakarta inna mahaifiyar mahainfinta  agabanta Amman ta Danni zuciyarta tacigaba da zama da kai, duk dan  sbd son da take maka.
 ka tuna irin dukan mutuwar da kayi mata. zeenat bata taba jin ta tsaneka ba ko tana kyamatar  Halinka ba.

 km duk tsiya dai zeenat uwar gidanka ce bata cancanci wannan wulakancin da kaskancin a gurinka ba.
 yakama maza Ku dinga daraja uwargidanku ,Ku mutuntasu  akan komai Na rayuwa ,domin kuwa sune wayanda suka fara bawa rayuwarku  farkon farincikin mara misaltuwa. Dan hk wlh azim yadda ka kuntata mata Daga dawowarta to ka tabbatar kaje kabata hakuri tare da sanyata 'cikin farinciki.
 gabadaya jikin deeni Yayi matsanancin tsanyin akan abinda ya'aikata muryarsa a kasalance yace first love kiyi hakuri Amman itama tayi kuskure abinda taso aikatawa  yarinya nan .
 yanzu idan wani abu ya  samu 'cikin jikinta mezamu ce ?
 yakarasa fadar mgn tamkar zai yi kuka Amman duk da hk nasan nayi kuskure nima kiyi hakuri  ..Ya tashi daga inda yake ya matso sosai kusa da ummi yana sake bata hkrn abinda Yayi ..bbu komai  amman ka tabbatar kabata hakuri naji first love zan bata ..Allah Yayi muku albarka ya amsa da  Ameen tare da Mikewa tsaye Yayi mata sallama ya bar dakin.

Ahankali yaji jikinsa Yayi masa sanyi sosai ya dinga jin har a 'cikin zuciyarsa Bai kyautawa zeenat ba sosai zuciyarsa tayi regretting din abinda Yayi mata . tabbas bbu karya 'cikin maganganu ummi zeenat tana tsantsar son shi da kaunarshi Bai kamata ya mareta agaban nablah ba.
 dan hk  Kai tsaye dakinta ya nufa..

Zaune  ya isketa  akan ters jingine da gadonta jikinta sanye da rigar baccin  gashin  kanta a watse bbu rebon  tana wani irin kukan  mutuwa me cin rai da taba zuciya ma'abocin sauraro sosai take resgar  kuka tamkar ranta zai fita yayinda zuciyarta ta hautsene  da tashin hankali mara iyaka .
 gabadaya ta gama fita haiyacinta sai sambatu take zubawa tazama tamkar wata mahaukaciya sabowar kamu '.
cikin sanyi jiki yakarasa zuwa Inda take zaune  zuciyarsa a dagule shi kanshi bai ji dadin yanayin dayaganta ba km hakika ya tabbatar da laifinshi me girma a gurinta tunda yaganta hk wani irin tausayinta ne ya ratsa zuciyarsa da gangar jikinsa domin yasan duk sbd shi take 'cikin wannan halin damuwar.
 duk fa sbd shi take wannan haukar kishi gsky shi kanshi yasan zeenat tana mugun sonshi yasan da wuya ya samu macce da take sonshi tsakani da Allah tamkar ta
 km yasan duk duniya bbu abinda tafi so sama dashi km duk abinda yace tayi zatayi akan irin son datake masa.
 hk ya dinga tuno abubuwa daki daki a game da irin son datake masa hk kawai yaji Hawayen tausayinta yashiga zubo masa Yasa ya dauke su da sauri batare da tagani ba  hannuwansa duka yasa ya  dagota tsaye  ya rungumeta ajikinshi yana sakin numafashi . tasoma kokarin fexgewa Daga jikinsa ya matseta gam yana sake fidda numfashi da ajiyar zuciya me karfi.
 sosai tacigaba da kukanta har da shesheka tana jin zafi da radadi wulakanci da Yayi mata duk akan kuskuren me aiki ...muryasa 'cikin kuka yace mata am sorry zeenat.. am really sorry zeenat for what I don  dan Allah kiyi hakuri ki yafe min abinda nayi miki ba nufina Na kuntata miki daga dawowarki ba.
 ni kaina bansa meyyesa Na aikata abinda nayi ba .
Banma San sanda Na aikata hkn  ba .. 
muryarta cike da kuka tace baka San sanda ka mareni akan yarinyar nan ba kennan sbd kana sonta ?
ahankali Ya sausauta rungumar da Yayi mata tare da tsura mata rikitattun idanunshi yana kallon 'cikin idanunta muryarsa a dake yace Allah Ya kiyaye zeenat Na so wata ya mace byn ke a duniya.
 idan ma soyayya zanyi sai  narasa inda zan ajiye soyayata sai a gurin  wannan yarinyar.
 karki manta kece mace ta farko da zuciyar deeni tasoma shan wahala akai  kafin umminta ta amince tabani aurenta ,
dan hk ki kwantar da hankalinki bbu komai a tsakanina da wannan yarinyar abinda kika Ga nayi ni kaina bansa Na aikata ba amma am sorry ya sake rungumeta tsam  ajikinshi.
'Cikin muryar kuka tace my hrt zuciyata na matsanancin sonka ,ni wace irin mace nakasance atare dakai takarasa mgnr tana kuka ?
Kin kasance tamkar  duniyatace , ke din daban kike a gurina .
 , zeenat ko bbu aure atsakaninmu mu din ruhi daya ne mafi kusancin  makusanta .to meyyasa Kai baka sona kmr yadda nake maka ?
Shiiiiii ya daura bakinsa akan lips dinta yana tsotsa ,  ahankali ya dinga  kwantar mata da hankali yana ruda mata jiki da salonsa yana gaya mata word masu dadi da kalamai masu  kashe zuciya .Ya nufi toilet daita da kanshi ya sake  yi mata wanka yana sake rarrashita da kwantar mata da hankali har taji zuciyarta tayi fess ta huce akanshi ta daina jin zafinsa da zafin  abinda Yayi mata .

  byn Yayi mata wanka ya rungumeta agefen jikinsa  suka fito tare ya goge mata jiki Ya  taje gashinta kanta hade da maida mata rebon din kanta  yaje ya hado mata coffee da tuwo yakawo mata har dakinta ya zauna yana bata abaki yana tausaya mata byn taci ya bata maganin zazzabi sbd jin yanayin yadda jikinta ya dauki zafi .
 sannan kafeta da rikitattun idanunshi yana kashe mata jiki dasu .
Ta dan yi murmushi dan son   kwantar masa da hankali .
ya koma tafin hannunta duka 'cikin nashi yana murzawa ahankali zuciyarsa Na masa sanyi akanta shima murmushi Yayi yana kashe mata idonsa daya sannan ya bude bakinsa da kyar well dazu kince  nayi sex dake to yanzu  I have a right to do it? 
tayi murmushi tana matse hannunshi dake 'cikin nata.
 ya lumshe rikitattun idanunshi ya sake budesu akan fuskarta sbd yasan oready ta rigada ta huce dashi  kasancewarta mara riko km bata iya dagon fushi akanshi 'cikin sanyi rai da natsuwa deeni ya zarce da romancing din zeenat itama tana maida mishi martani tun sanda ya kwantar daita a saman gadonta ya soma jefa mata kalamansa zafafa masu kashe mata duk wani gaba dake jikinta. zeenat ta dinga jin salonsa suna sauka 'cikin kunneta da ruhinta wani yanayi ne take jin yana bin duk wani lugu da sako na jikinta yasoma murza brest dinta yana shafasu 'cikin irin salonsa wanda yake rikita zeenat ya km zautar daita hankalinsa yasoma gushewa yayinda sha,awarta kawai ke cin ransa da wani irin tsananin tausayinta dayake jin yana ratsa masa gabobin jikinshi ahankali yake binta 'cikin natsuwa tare da samun hadin kanta bukatarsa ta biya har suka fada cikin duniyar ma'aurata..sosai suka gamsar da junansu da zuciyoyinsu da muradinsu wanda suka jima suna kewar juna  byn dan wani lokaci komai ya lafa atsakaninsu .
ya dauketa sukayi bathroom dinta daita wanka sukayi atare  zeenat najin wani irin  matsanancin son mijinta sosai tare suka fito suna manne da juna ta sauya wasu kayan shima ya tsaya shirya kanshi Amman da kyar ya kyaleta domin manne yake daita ajikinshi dan Sam yakasa barin tayi koda kwakwaran motsi ne ...


Washegari da sassafe ya tashi ya bar dakin zeenat ya nufi dakin nablah ya budeta.
 ya shiga ya dubata  bacci take sosai ya ya yaye bargon daya lulluba mata, tare dage rigar jikinta ya daura kunnenshi  saman 'cikin yana jin motsin cikinta.  lumshe rikitattun idanunshi Yayi yana jin sanyi har 'cikin zuciyarsa ' kiss Yayi cikinta da lip's dinta  sannan yabar dakin zuwa masjid .

'Cikin kwanaki nan ko office deeni yaje Allah Allah  yake ya dawo gida gurin zeenat  wata irin  kulawa ta musamman yashiga bawa zeenat din  tare da yi mata hidama sosai  da fada mata kalamai masu sanyaya rai da kashe zuciyar data dade 'cikin shaukin so. duk da nata ran zafi yake mata har lokacin  inda yagaya mata ta daina damuwa akan nablah shi bakomai bace agurinsa facce me aiki .. sannan yace tayi  hakuri kan duk  abinda Yayi mata yanzu yana son kwanciyar hankalinta da ganin  farincikinta.
 wani irin yanayi ta tsinci kanta ciki  mara misaltuwa gabadaya ya kashe mata  ilahirin jikinta da zantuttukansa masu birkita mata lissafi bbu abinda tafi so da kauna sama da farincikin mijinta dan hk ta sake rungumar mijinta da hannu biyu biyu tana zuba masa shagwaba iri iri ...

'Cikin wannan lokacin nablah taga abin mamaki me  tsoratar da zuciya.. domin tun dawowar matarsa taga deeni ya rage shishige mata  kmr lokacin da basu nan .
 hkn Yasa zuciyarta ta dinga kitsimata abubuwa dayawa akanshi har  ta yarda lallai namiji munafiki ne km  bashida alkibla .
,kwata kwata ya daina zuwa Inda take indai matarsa Na gida sai dare zai zo mata yaga lfyr jikinta ya dan mammatsata da romancing dinta .
 "sannan duk byn kwana biyu zai zo dakinta nan zai kwana har sai asuban faru tukun zai koma dakinsa ta kula kmr ya raba musu kwana Keenan atsakananinta da matarsa.
 duk  randa yake dakinta kuwa bata iya bacci kirki   takure jikinta take karshen gado Yayi Yayi ta saki jikinta dashi bbu abinda zai faru km bbu abinda zai mata amman taki yarda dashi .
dan ita gabadaya atsorace take da almarin. kada matarsa tasan halin da mijinta yake ciki akanta da km  'cikin jikinta ..



Tsaye take abakin wani dan karamin lugu tana wage wage tare da neman yaron dazata aika 'cikin gidan Nasu.
 can Allah Ya taimaketa ta hango tahowar wani karamin kaninsu wanda shine auta acikin gidan.. muryarta amatukar sanyaye tace abba ...

abba wanda ya kusan giftata ya dawo ahankali inda take tsaye yana karemata  kallo tsab  da son gano ko wacece ita sakamakon nikaf din dake manne da fuska.. can  km Yayi murmushi yace kai aunty Sal.....shiiiiii ta daura dan yatsanta a saman bakinsa tun Bai karasa ba .
"Baba Na 'cikin gida ne ?
Abba ya girgiza mata Kai baya gida yana gurin dauda me kanti gurinsa ma zani yanzu .
yauwa bari nashiga  Amman kada kafada masa naxo fa .. yace to aunty ta ciro naira hamsin acikin jakarta  ta mikasa tayi gaba abinta ...

Da sallama bisa harshenta tashiga gidan Nasu da yanzu yasamu sauyin yanayi rayuwa .ba kmr da ba ..shr taji koina bbu motsin kowa .
Muryarta a dan tsorace tace wai Ina mutane gidan nan suke ne ?

Atare mama da nuratu wacce nablah ke bi suka fito tsakar gidan suna gamu kabo kabo mama tace  tana murmushi, har yanzu  Salma bazaki rabaki kanki da sanya wannan abu ba a fuskarki ba  ?
Uhmmmm mama Ina zan iya da fadar baba tunda yace kada Na sake zuwan masa gida muddin ban dawo masa da nablah  ba .
kinga kuwa dole na kasance hk matukar Ina son zuwa ganinku inji cewar Salma dake kokarin zama kan cement  dake malale atsakar gidan Daga mama har nuratu dariya suke mata sannan sukace  sannu da hanya ta amsa tana gyara zaman nikaf din fuskarta da kyau ..Ni Banga amfani wannan fadan Na baba wlh , yarinya Na can tana achieve din rayuwarta zai damu kanshi da  mutane kmr an tsiyar daita.
 uhmmmm nuratu bana son jin  wannan mgnr Daga bakinki bashi kadai ba koni kaina yanzu Ina bukatar ganin yarinyata . wata takwas kennan fa rabon damu  sanyata 'cikin idanunmu ko Yar kaza kabayar dole kadu ballanantana mutun sukutun . ban da ma Muna  yin waya da hjyar ba , da tuni nasa Salma gaba na dauko yarinta ..suka kwashe da wata irin  dariya gabadayansu.
 kai jama'a tsakanin mama da baba narasan wanda yafi wani nacin nablah ba nuratu ta karasa fadar hkn tana tabe baki ..Ai duk son ya'ya dasu Daga baban har mama 
 Ina Muhammad da Kamal ne bangansu ba niji aunty Salma?

  Muhammad an sakashi koyon aiki kaniknci  Kamal km ya tafi gurin aikinsa Ok Allah Ya taimaka .
 nuratu taje ta kawowa aunty Salma ruwa me tsanyi da sauran abincin dayayi saura sannan suka shiga hirar duniya awa daya tayi a zaune kafin daga baya suka shige kuryar dakin mahaifiyarsu suna cigaba da zantawa duk  akan dawowar nablah gida da zarar ummi ta dawo ,wanda alokaci basu da masaniyar dawowar ummi din tunda bata Kira aunty Salma ta sanar mata ba ..'.

cikin hk suka jiyo  muryar mlm salisu yana doka  sallama yana kiran sunan nuratu ...nuratu gaban aunty Salma ya fadi wayyo Allah mama nashiga ukuna Ga baba nan ..
 wai nuratu  kina Ina ne hk nake ta faman kiranki ?
Nuratu  ta fito da gudu ta tsaya a 'bakin kofa Gani baba Na kokarin shigawa ciki , Ina singilotocin danace ki wanke min?

 shagwabe fuska tayi sannan tace shi nake son   wankewa yanzu  maza ki kokarta ki wanke min banida Na saka km  zuwa anjima Ina son shiga 'cikin  apapa .

 to aima baka bani kudin sabulo ba yasaka hannushi 'cikin aljihun gaban rigarsa ya ciro dari biyu ya Mika mata yana kokari sanya kanshi 'cikin dagon parlour gida yana kiran sunan mama itama ta fito 'cikin sanyi jiki  ta tsaya abakin dokin kofa dan kada yasamu damar shiga dakinta ungo wannan kisamu abinda kika dafamana daddare  ya mikamata odindin dubu daya sannan yakarasa dakinsa . wanda xuwa lokacin Salma dake daskare 'cikin dakin  mama kadan ya rage zuciyarta bata buga ba tsabar frigice. tana jin ya shiga dakinsa ta sauke naunauyen ajiyar zuciya tana goge gumin dake tsaftsafo mata .
mama ta zuba mata idanunta kema Salma ke maida hankali gurin dawowar yarinya nan .
nan kusa kindai San halin mahaifinku sarai bakara min aikinsa bane yabiki har gidanki ya tara miki jama'a.
 nima wlh abinda nake fargaba kennan mama shiyasa kullun nake addu'a .

Saratu  mlm salisu ya   kwallawa mama Kira ta sake fitowa suka cikaro dashi zai shigo dakin ya'akayi  ne baban Salma ?
Sai naji wata murya tamkar ta Salma a gidan nan  ..?
Salma km  a gidan nan ? yaushe rabon Salma da zuwa gidan tun zuwanta Na karshe dakayi mata korar kare ai bata sake zuwa ba .
bakuwa mukayi kawar nuratu ce tazo mlm salisu yayi Jim yana tunani da bin dakin da kallo shifa yasan muryar Salma fiyarsa ya  jiyo sama sama koda yashigo gidan ma yaji ,yace shikennan tare da juyawa jikinsa sanye Yayi tsakar gida  da babbar Riga ajikinsa   da alamun wanka zai shiga ya tsaya yana gyara sajen  fuskarsa .

Ki hanzarta barin gidan Salma  kafin ya fito Daga wanka ya tara miki mutane  to mama Salma ta Mike tsaye da hanzarta tana gyara zanin jikinta itama nuratu ta Mike tsaye  tare da fitowa tana Yan dube dubenta taga abinda baban Nasu yake .

yauwa nuratu miko min singlet guda biyu Na wanke yanzu kya wanke min  sauran Daga baya ,gaban nuratu ya fadi rassss dan tasan halin wanki babansu  dadewa yake Bai gama ba.
 ta juya da sauri jikinta Na rawa mama aunty Salma kinji wai wanki baba zai yi km yanzu ta fadi hk fuskarta tattare da damuwa gaban Salma yashiga dukan uku uku ta dafe kirjinta dan girma Allah ?
Wlh hk yace kinga shiryawarki kawai kiyi tafiyarki ba lallai bane ya Ganeki ,ince har safa kika saka inji cewar mama  ? Salma ta gyada mata kanta batare datace komai ba oya maza ki wuce abinki Kin dai San halin wankisa  bakarewa yake ba idan ma yaga dama zai iya cewa zai wankensu  duka yanzu ...

Sautin muryarsa suka ji Wanda ya sake hautsina zuciyar aunty Salma  wai Me kike yi ne har  yanzu nuratu ?
 Gani nan zuwa baba su nake son daukowa ta dauka da sauri ta bar dakin jikinta Na nuna alamun rashin gsky koda ta Mika masa kayan ma ta juya  bynta yabi da kallo sannan ya girgiza Kai ya  jika singlet din 'cikin ruwa, Yacigaba da abinda yake ..

Aunty Salmah tayi kmr zata fito ta sake komawa cikin dakin da sauri ganin inda mahaifinta ke facing. Wayyohhhyyy mama wlh tsoro nake ji bazan iya fita ba.
..Kai Kai Salma wlh kincika abin haushi sai kin bari babanku yagane halin da ake ciki wlh nima ki jawo min a tsamamin tsaraba  daman kullun  sai ya zageni cewar da hadin bakina akaje tsiyar masa da 'ya' idan baki bar rawar jikin nan ba fa zai iya  ganewa wlh  da kyar aunty Salma tayi karfin halin sake fitowa gabanta Na faduwa  nuratu Na gabanta tana dan janta da hira tamkar wata  kawata da gaske kirki damu zanzo miki dashi duk sanda zanzo gidanku, yayinda km   mama ke bayanta tana ce mata to  maimuna angode  kigaida gida muryar aunty Salma har rawa take gurin amsawa .
 ta gefta mahaifinta kadan taji Yayi gyaran murya ta tsaya cak jikinta Na wani irin kirrrrrrma nuratu ki siyo min hypo da kudin hannuki to baba inji nuratu  wani irin ajiyar zuciya aunty Salma ta sauke jin abinda yace suka karasa ficewa Daga tsakar gida gabadaya  har 'bakin kofar dagon zauren gidan   mama takaita sannan ta juyo 'cikin gidan  tana dauke plate din abincin da Aunty Salmah taci ..

Mlm salisu yaja numfashinsa yana duban mama wlh saratu yarinya nan  data fita yanzu  sak Salmata, gsky yanayinsu yaxo daya sosai  .
Mama tace uhmmmm ,kawai dai dan kasata a ranka ne shiyasa har kaga hk shr kawai Yayi  batare da ya sake cewa komai ba ita km ta dauki buta tashige bandaki tana jin jina hali irin Na mijinta..

Har 'bakin jection din gatankowa nuratu ta Kai aunty Salma suna hirar babansu suna dry  har sai dataga aunty Salma tashiga motar ishodi sannan ta kama hanyar komawa gida ...


 Rigingine  nablah ke zaune a dakinta hannuta a saman fuskarta tana tunani duniya yayinda jikinta ke sanye da riga da zani Na atamfa English me ABC  . Sosai tayi zurfi  har batasan  sanda bacci yayi nasarar dauketa ba . Zeenat dake zaune Kusa da ummi suna hira da kallo ta Kai idanunta kan agogon dake manne da jikin bangon parlour karfe biyar ta wuce.
 bataga alamun saukowar nablah daura musu abincin dare ba.
 ta Mike tsaye ahankali tana yatsina fuska ummi ta dubenta tana ya dai mamana ?
Murmushi ta sakarwa ummi bbu komai ummina zanje nakira yarinya nan ne tazo ta daura mana girkin dare  naga alamun bata niyar saukowa .
ummi tayi shr can km ta nunfasha kana tace kibari laraba tazo takirata man ,    bari kawai naje ummi.. akwai abinda zan dauko a dakina Na sama takarasa fadar hkn tana  juyawa ahankali tasoma tafiya tana girgiza jiki tana juyawa ummi tashiga addu'a acikin zuciyata Allah Yasa idanuta suGane mata abinda dade  take son kasancewarsa.

 Kai tsaye dakin nablah zeenat ta nufa tare da bude dakin 'cikin isa da takama ido hudu tayi da abin mamaki da ban tsoro   dan karamin 'cikin jikin nablah dayayi mata  dan kurcici dashi taci karo dashi .
 dasssssssss gaban ya yanke yashiga faduwa har yana duka uku uku .
da hanzarinta takarasa shigowa dakin sosai  tana sake bin 'cikin da wani irin kallo .
ciki take ganin a jikin yarinya nan  ko me ?
Tasa hannuta ta murza idanunta ta sake budesu fesss  still the same thing take  Gani ..

ta kwallara wata irin gigitacciyar kara wanda ya farkar da nablah daga naunauyen baccin dayayi nasarar dauketa tayi wall da shanyayyun  idanunta ta budesu tana kallon zeenat tsaye a gabanta tana zaro idanu.
 da sauri  tasoma kokarin   Mikewa tsaye tana  janyo hijab dinta domin  suturta jikinta .
da hannu zeenat ta dakatar daita alamun kada ta saka ..mamaki zeenat  tashiga yi da alajabi  ta rike bakinta takasa cewa komai da kyar ta iya bude bakinta gurin furta kalmar ..

Nashiga uku ni muzeenat .. mezangani hk ? 

inna lillahi wa inna ilaihi rajiun 'cikin tashin hankali  tashiga Kiran sunan ummi da karfi .ummi ta zabura ta Mike zaninta a hannu tayo habyar step da sauri .

a frigice zeenat tace wayyyyyoo   nashiga uku dama nasan za'a Rina  muryata cike da in ...inna..tace nab..lah.. 'cikin shige zaki haifar min acikin gida.
 lallai kuwa zan miki dukan mutuwa tare da  antayaki waje.
 kije can gurin wanda Yayi miki ciki.
 tayi kukan kura zata damkota wuyan nablah...




MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
 AUREN SIRRI
     💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO



            Dedicated to
     HAUWA A USMAN
            ( JIDDARH)



Page 95

Kanta ta dago ta kalleshi taga duk ya birkice ya fita haiyacinsa ta hadiye  abinda taji ya tasomata ya tsaya mata a kirji. sannan ta sauke naunauyen ajiyar zuciya tace eh gidansu nace direba yakaita taga iyayenta kmr yadda nayi mata alkwarin .Amman 
ummi Na dauka sai xuwa wani lokaci zata tafi  yasoma mgn muryasa  cike da zafin zuciya haba  first love yazaki bari yarinya ta tafi  wannan hargitsartsiyar unguwar  tasu  me cike da dowatsu alhalin  kinsa halin datake ciki yakarasa fadar mgr muryarsa kmr zaiyi kuka .
 Da kake wani fushin da daukar zabi akan yarinyar mutane .

diyata ce  nablah ko taka?

Yadda kake  tunanin kana son "dan" dazata haifa maka .
 itama hk iyayenta suke sonta km suke bukatar ganinta kusa dasu  dan hk kmr yadda nace maka  nasa direba ya ka ita gida .
 ahankali jikinsa Yayi mugun  sanyi zuciyarsa tashiga harbawa da sauri da sauri  ya runtse rikitattun idanunshi gam yana jin Babu dadi acikin ranshi ..
 tare da kamo lips dinsa na kasa yasoma cizawa da karfi can ya bude idanunshi ya zubawa ummi dake zaune bisa gado tana kallon yaninyasa da nazarinsa .
Muryarsa a sarke yace first love to meyasa kika.
 kwaso  kayanta ?

Nakwashe km nayi hakane domin Na tabbatar da abinda nake zarge akanka deeni .


Wai meyasa Ku maza bakwa iya dannar xuciyarku akan abinda kuke so?

 deeni tun ranar dana dawo daga india Na dira Daga airport Na tabbatar da ka kamu da matsanancin mugun son yarinyar nan nablah so km  bana wasa ba , sosai ka nitse 'cikin kogin sonta .
 " deeni kafi son  yarinyar nan fiyye da zeenat sannan km kana yiwa yarinyar nan wani irin mahaukacin so .

Da wani irin mugun sauri  ya dago  da rikitattun idanunsa ya zubawa ummi sosai  yana  mata wani irin kallo me tsoratarwa sannan  da mamakin mgnrta  saman fuskarshi .

Eh deeni bazakataba Gane hakan ba sai lokacin Yayi .
Amman ka rigada ka fada son yarinyar nan tunda har ka iya marin zeenat agabana akanta  batare ko shakkata ba .
 km ka  rungumi matarka agabana deeni  ka kwantar daita akan kirjinka hkn ya tabbatar min da bakaramin so kake yiwa nablah ba.

 ni dai koda zamanku zai daure daita  fatana  dan Allah dan annabi kayiwa diyata zeenat  adalci karkaga wannan itace uwar ya'yanka  itace me haihuwa sannan ka wulakanta min  zeenat ko byn raina banason ka wulakanta min ita .
 dan hk ka natsu ka kwantar da hankalinka da kyau  akan 'cikin jikin nablah Allah ne yabaka 'cikin jikinta km shine me tsare bayinsa .
 " inshallahu da kariyarsa nablah  zata haifamaka  abinda ke 'cikin ta.

 A hassale muryarsa Na rawa yace   ni duk ba wannan ba tunda nace kartaje  ba sai a hakura ba idan lokaci hk Yayi da kaina zan kaita uhmmmm sannu ubanta mlm salisu  ....... 

yau wata nawa rabon yarinyar nan  da iyayenta kada ka mata ita kanta nablah bazataso zama tare da iyayenta ba a  halin datake ciki . 
Km ma Muyi daita yau din nan  zata dawo .... zuciyarsa a hassale km muryarsa can kasa kasa yace first love nidai gsky banso tafiyarta ba. sannan km mgnr wai Ina son yarinyar nan  komai komai.... shima ba hk bane first love domin ni nasan zuciyata nasan abinda take so da wanda bata so . banasonta  yarinya idan har. Na afka sonta ta yaya bazan gane ba yakarasa fadar mgnr  tare da juyawa  fuuuuuu  yasoma tafiya ranshi abace ya bar gidan ummi tayi murmushi irin Nasu Na manya deeni kennan ne rikicin gangan Allah Yayi maka albarka tare da sanyaya maka zuciyarka ..


Hayaniyace ta kure 'cikin gidan mlm salisu da murna da kururuwar ganin nablah gabadaya duk wanda ya kalli fuskokin ahalin gidan  murna suke da farincikin ganinta ..

Mama tashiga nan nan  da diyarta kanneta zagaye daita kowannesu Na murna ganinta hatta aunty Salma tazo da murnata wace ummi ce tasanar mata da zuwan Nablah din . gabadayansu ,suka saka nablah a tsakiyar su .suna murna da jin dadi ganinta .
 nuratu ta kalli nablah  da kyau .
Kai Alhamdulilllahi yau dai zamu huta da shan zagi gurin baba.
Na aunty  Salma ta   tsiyar masa da "ya" nablah tayi  murmushi wanda ke karawa fuskarta kyau da annuri  tare da cewa  banana kennan.
 nayi kewarsa nima sosai  fiyye da tunaninku ..

uhm kalli  yadda kika dawo Nablah  kinyi kyau dake  kikayi fresh sosai gadabaya fatar jikinki ta sauya  wlh  gurin nan ya amsheki inji cewar nuratu  ..
Allah ko  nablah tace hk tana murmushi sannan tacigaba duk wannan kyawun  da fresh din danayi wlh nafi son gidanmu koda kuwa za'a kwana bamu ci  ba Amman dai  zan koma sbd wani dalili nawa .. aunty Salma tayi saurin cewa wlh bada hannuna ba 'cikin komawarki .
Ni dai tunda kin dawo Na auna arziki Na huta da fadan baba  wlh  har fargaba zuwa gidan nan nake .
Tun tafiyarki nake 'cikin tashin hankali boye miki kawai nakeyi sbd kwanciyar naki hankalin Amman mgnr gsky Na tsorata da al'amarin baba..  nan nuratu tashiga zaiyanewa  nablah labarin duk abinda ya faru da yadda aunty Salma ke shiri idan zatazo gida .
 aiko gabadayansu suka kwashe da wata mahaukaciyar dariya .

Maman da  tun sanda suka fara hirasu  da nuratu da Salma  ba tsoma musu baki  ba sai yanzu tace uhmmmm nablah bana jin babanki zai yarda ki sake barin gidan nan ballanantana har ki  koma wani  aiki.
 ni kaina wlh yanzu banaso komarwaki .
dan hk bbu inda zaki ki zauna kema 'cikin yan'uwanki zan fi samun kwanciyar hankali .
Aunty Salmah tace wlh zanceki  gaskiya ne mama  Amman kubari baban  yazo tukun nasan da zarar yasanar mata da  abinda ya zartar akanta zata natsu ... ko babu wannan dalilin bazata koma koina ba inji cewar mama .
 murmushi takaici nablah tayi tare da cewa Mama kennan Allah Ni dai zan koma wlh  Amman Na da wata uku  zan dawo gabadaya  gareku.
 mama dan Allah  kada kice a'a ta karasa mgnr tana marairaice muryar .
 uhmmmm mama ta sauke ajiyar zuciya to shikennan Amman kibari babanki yazo kiji me zaice.
 Take sukar bar zance suka shiga wata hirar daban .
karfe hudu daidai sai Ga  direban ummi ya dawo daukar nablah Amman nablah ta fita da kanta tace ba yau zata koma ba sai zuwa jibi ko gata. da zai wuce aunty Salma ta bishi Dan ya rage mata hanya .



Da daddare byn sallar isha'i mlm salisu yashigo gidan da sallama a bakinsa hannushi rike da wata  bakar leda yana shiga dogon parlour gidan.
  idanunshi suka sauka kan diyarsa nablah dake sanye da hijab ajikinta wanda tun safe datazo gidan  bataci re ba tana kwakume dashi abinda Yasa ma mama bata mata maganar ta cire  ba sbd tasan tun asali hk take mayar hijabi ce ita  ko bacci zatayi bata cirewa ..

Ahankali mlm salisu yakarasa shigowa ciki  tare da cewa wanake ganin hk kmr nablah agidan nan ?

Nuratu ta tashi da sauri  jikinta  a sanyaye  ta karbi ledar  hannushi ta ajiye a gefe  tana mishi sannu da zuwa .
Bai kulata ba sbd hankalinsa dake kan nablah ..tsam itama  nablah tayi da ranta tare da shan jinin jikinta sbd ganin irin kallon da mahaifin nata ke jifanta dashi .
 jikinta a matukar sanyaye ta bude bakinta da kyar gurin cewa sannu da zuwa baba ..

 uhmmmm yauwa Yan neman abun duniya da fatan dai kin samo masu yawa ?
Nablah tayi tsit  ta sake sha jinin jikinta ai nasan duk inda kika je zaki dawo , indai nine ubanki ba shegiya bace ke.....
yakarasa mgnr yana nunata da yatsa hannushi  haba haba  baban Salma tun...ke ...nasakaki cikin maganata ? Ya katse mama Yacigaba da mgnrsa .
Da "yata" nabeelah nake mgn ba da saratu ba .
dan hk banason jin bakinki cikin manta .
  ,ai duk da hadin bakinki yaran nan  suke yi duk isakanci da sukaga dama.
 basu dauke ni abakin komai ba km wlh duk lalacewata ni nan nine  ubansu dole km akirasu da sunana  sai dai mutun ya gudu bazan fasa mgn ba da cin uwar yarinya tsit kake jin gurin tamkar babu wasu halittu  acikin parlour  ..mlm salisu  yacigaba har ni ubanki zance miki banason abu kice sai kinyi dole .


Ni talakane me wadatar zuci  banida karfin daukar nauyin  karatunki  Amman kice dole sai kinyi .
 Yanzu Ina kudin da kika samo a yawon duniyar da kike je dan nasan ba aiki kikaje ba?
 duba Ga yanayin sauywar da jikinki Yayi   Amman bbu komai hkn ma daidai ne a gurina  kinyi son ranki  nima nayi son zuciyarta akanki yakarasa fadar Haka tare da shigewa 'cikin dakinsa Bai sake cewa komai ba.


 jikin mama Na rawa tace kungani ko.
Kunga irin  abinda nake gudar muku kennan Amman  bakwa jin magana..

Maza  maza ki tashi kibishi dakinsa  ki bashi hakuri ..

Jikin nablah a matukar sanyaya  ta Mike tsaye ta karasa 'bakin kofar dakinsa ta  dan yaye labulen dakin babanta.
 

Ta hangoshi zaune shr yasa  hannushi daya ya tallabe  habarsa dashi  tashigo ahankali ta durkusa da kyar tayi neldwon  'agabanshi muryarta Na rawa tace dan girman Allah babana kayi hakuri Allah bazan sake ba km wlh tsakani da Allah aiki naje baba ba yawon duniya ba .
Duk da  nasamu abinda Na fita  nema Amman banida natsuwar zuciya sakamakon bijirewa mgnrka danayi .
Amman kayi hakuri baba takarasa mgnrta hawaye Na bin kuncinta ..

Mlm salisu ya sauke naunauyen ajiyar zuciya yana duban nablah diyarsa wacce  yafi so da kauna duk a 'cikin ya'yansa komai nashi ta dauko basu da bambanci komai  sai dai kasacewarta macce muryara a sanyaye byn Yayi gyaran murya yace shikennan nablah  Allah kyauta km alhamdulilllahi tunda Allah Ya dawo min dake lfy bbu abinda ya sameki ai Na auna arziki.
 kukan nablah ya tsananta yayinda  a ranta km  tace wayyyyyoo babana akwai abinda yasameni har Yayi min nakasu a rayuwata ..

kibar kukan hk Na hakura km na yafe miki Allah Yayi miki albarka sai dai wani hanzari ba gudu ba nima nayi miki abinda bazaki ji dadinsa ba ..
Domin kuwa byn tafiyar ki bbu dadewa wani mutumin kirki yazo neman aurenki nan dai mlm salisu yayiwa nablah bayanin abinda ya faru  byn tafiyarta tun daga farko har karshe ..

Nablah Ta dago shanyayyun idanunta afrigice tana kallon mahaifinta dasu .
Shima ya dago yana nazarinta tare da   daga mata kanshi  alamun gaskiya ya sanar mata .
Ya numfasa kana yacigaba haushin abinda kika min da kaicinsa da km  kimar mutumin Yasa Na aikata Haka ..
 nablah wannan mutumin dana aura miki mutumin kirki ne me mutunci da girmama babba. bakiga yadda yake hidima damu ba ke kanki kinsan rayuwar gidan Na tausaya da al'amuran cikinsa gabadaya .
 yanzu Hk shine ya hanani wanki hular da nakeyi  ada ya samomin aiki me daraja acikin apapa.. 

bbu abinda zancewa  wannan mutumin sai Allah Yayi masa albarka km ya albarkaci aurenki dashi ..
yanzu tunda kin dawo zan nemeshi nasanar masa ya turo iyayensa gareni domin nasan nasabarsa da inda yake zaune  ..
sosai nablah ke resgar kukanta  har da shesheka tana jin wanin irin zafi 'cikin ranta meyasa abubuwa suke zuwa mata hk?
 daga wannan sai wannan tasan shikennan shirin karatunta ya rushe kennan har abada  tarasa burin zuciyarta da farincikin rayuwarta .
yau tazo mata da abubuwa iri iri  masu daci da muni.
 rasa karatunta 'cikin jikinta ...auren da babanta ya daura mata batare da amincewarta ba ..

 nabeelah mlm salisu yakira sunanta kinyi shr kina kuka  bakice min komai ba.
 ko zaki butulcewa  zabin dana miki ne?

Ta sinkuyar da kanta kasa sosai tana sake fashewa da wani sabon  kukan me cin rai da taba zuciya   tare da girgiza masa kanta ...

Kin amince da auren dana daura miki ?

Ta girgiza masa Kanta batare da tace komai ba alamun ta amince  yauwa diyar albarka nasan daman baki da  damuwa ta nan, ko wancen karo ma dakika bijeremin nasan sharrin Salma ne da makircinta Amman nasan ba halin diyata bane ..
sai da mlm salisu ya dasa aya sannan nablah tace  baba ... muryarta Na rawa rawa ..Ina neman alfarma guda daya agurinka  dan Allah kayi hakuri kabani nan da wata uku , Ina son nakoma gurin aikin nan nawa Dan   akwai abinda zan karasa musu wanda ya zama  lallai sai nice zanyi da zarar nagama inshallahu zan dawo sai natare....
 mlm salisu ya girgiza  Kai  yana mata wani irin duba kana yace Aa nabeela bazan iya sake barinki zuwa wani guri ba me kike son mutane suce akaina ..?
nazama uban banza kennan agareki koda bbu auren kowa akanki Nablah  bazan km  yarda da komawarki ba  ballanantana yanzu danasan da auren wani akanki .
Me kike tunani mijin naki zaice akai idan yaji labarin kinzo kin koma ?

Muryarta cike da kuka tace Baba tunda yasan banana km Bai San da dawowata ba  kawai kada kasanar masa Na dawo . 
Aa nabeela kiji mgnta sannan kiyi abinda nake so  ko al'amuran ki zasu daidaita arayuwa . gabadaya yanzu kin sauya halayenki dana sanki dasu  domin ada kin kasance me biyayya gareni sannan km  baki jayyaya ko yi min musu akan duk wani  abu danace  sabanin yanzu .

Sosai tashiga yiwa mlm salisu magiya da rokonshi tana kuka Amman yace sam Bai yarda ba.
  bbu abinda nablah bata fadawa mlm salisu ba akan yabarta ta koma .
bafa zan barki ba nabeelah  ki sake komawa ba.
 gara ma ki hakura kiyi zaman aurenki shiyafiyye miki alkhari akan wannan aikin .
  km inshallahu idan kika bi umarnina  zakiga  daidai arayuwarki .

Muryarta a shake sbd da kukan da tayi tace  shikennan baba Na hakura yayinda km acikin zuciyata ba Haka bane ta dai fadi Haka ne kawai . ta yaya ma zata zauna ta  haifi 'cikin shege a gidan ubanta.wazata tace Yayi mata ? 
 Kai ina...zamanta ma  bazai yuwa ba duk da tana son zama 'cikin alhalinta .

Alhamdulilllahi  kisoma shirinki daga wannan lokacin zuwa kowani lokacin zaki iya tarewa agidan mijinki....yana karasa fadar hk 
 ya Mike tsaye tsaye yasoma kokarin cire babbar Rigarsa ya rataye .


 Jikinta a sanyaye ta fito Daga dakin mahaifinta 


Byn fitarta mlm salisu ya dade zaune yana tunani akan lamarin nablah . gabadaya mlm salisu Yayi deciding akan abinda Yayi mata  ko zai amince da bukatar ta ko  bbu Nablah me biyayya ce agareshi.
 yashiga damuwar sosai akan  ganin yanayin diyarsa km abar kaunarsa ahankali ya dinga jin acikin tanaji  yanaji babu dadi .
Sannan kwata kwata Bai ji dadin ganinta 'cikin halin  damuwa ba. yakasa yin komai ko abincin da aka kawo masa tunani Bai barshi ya iya  ci ba ..


Daren ranar nablah Na kwance akan gadon mahaifiyarta juyi kawai takeyi tare da tuhumar kanta akan abinda take son aikatawa  kanta.
 batasan dalili ba .
Sannan batasan abinda yasa ba Amman ji kawai take zuciyarta Na ingizata ta gudu kawai ta bar gidan ta koma ta haifi abinda ke jikinta tunda tasamu wanda zai amsa km ya fita bukatar abinda ke cikinta . take km ta tsinci kanta 'cikin  wata  irin  faduwar gaba sakamakon tuno deeni da al'amuransa datayi .
Wani irin   kewarsa taji ta tsarga mata tare da mamaye zuciyata da gangar jikinta duk ta inda ta motsa sai taji hannushi Na yawo a tsantsar jikinta .sosai ta dinga sauyi atare daita agame dashi .
Ta dinga jinshi har   acikin jinin jikinta  da gangan jikinta  zuciyarta tashiga harbawa ahankali tana  aiyana mata  abubuwa masu tarin  ,yawa akansa.. da kyar nablah ta rentse shanyayyun idanunta tana saka da warwara a zuciyarta  akan zamanta gidansu da 'cikin wata bakwai da satinnai ..ajikinta.
 tasan muddin mahaifinta yasan da zaman 'cikin jikinta  kashinta ne kawai bazai yi ba da duka .akaron banza ma ,zance idan yakamaka kana sai Yayi matun mugun duka tana kallon yadda yake dukan nuratu akan tara samari Ina ga ita me dungurungun ......
Idanunta suka  bushe takasa runtsawa 'cikin Haka  nuratu  tashigo dakin  hannuta rike da waya tana chatting ta zauna agefen nablah. sanyayyiyar ajiye zuciya Nablah  ta sauke da karfi gaske har nuratu ta juyo 'cikin sanyi jiki  tana duban yanayinta kana tace  wai ke meke damunki ne duk kin wani takurawa kanki akan maganar baba?
 idan baki son auren dayayi miki  kigamasa man bawai ki zauna kina damun ruhinki da tunani banza ba  .
Itama  nablah  juyowa tayi sosai  tana kallon nuratu takasa ce mata  komai ..

Nablah ....nuratu takira sunanta .
muryata a sanyaye ta amsa da  Na'am. Ta amsa muryarta Na rawa .

meyasa. kike son komawa gidan aikin nan byn kinsamu abinda
 yakai ki ?

Kuma wani abu ne zai sake  maida ke ?

,aganina ki hakura kawai da duk ma abinda zakiyi  ki zauna acikin mu wlh lokacin da baki nan nasha mafarki dake  kina 'cikin wani halin tashin hankali shiyasa ni yanzu a gaskiya bana son ki sake yin nisa damu .
duk da jikinki ya nuna baki 'cikin damuwa da wahala  Amman wlh hankalina Bai kwanta da wannan aikin naki ba.

 , Nablah ta fara kwalla idanunta suka cicciko  taf da ruwan hawaye xuciyarta na sake karyewa .
 muryarta a sanyaye km cike da raunin hawaye tace aunty nuratu bazaki gane abinda zai maidani gurin aikin nan  ba kona gaya miki .
sannan km batun mafarkinki  gaskiya ne domin Ina 'cikin tashin hankali da garare rayuwa  wanda Yasa bana jin zan iya cigaba da zama a tsakaninku acikin wannan yanayi .
,dan hk Na yanke shawarar gobe zan yi tafiyata Amman dan Allah kada ma ki gayawa kowa dan bama  zan koma gidan aikin  ba . 
A frigice nuratu ta ajiye wayar hannuta tana fuskarta nablah dake kwance tana matso ruwan hawaye idanunta.
kina nufi duniya zaki shiga  ko me ?
 
Niidai kiyi min addu'a kawai domin rayuwata tana 'cikin tasko wanda bansa ranar dazan fita ciki ba Nablah takarasa mgnr hawaye nabin gefen idanunta.

Me Yayi zafi hk indai akan auren da baba ya daura miki ne Ai gara kiyi zamanki idan yaso kice masa
  baki so . 
Amman zance guduwa  ma kada ki farashi domin sunanki zaki bata .
Uhmmmm aunty nuratu wlh  ba a dalilin  auren da baba Yayi min bane .
Kawai dai akwai wani  sirri dake tattare dani ne.
Km shi  zai hanani zama tare daku a halin danake ciki .
 wani sirri ne wannan da har da bazaki iya  gaya min shi  ba Ina matsayin yaruwarki ? 

Nablah tayi shr zuciyarta Na wani irin bugawa km tana  son sanarwa yayarta zance cikin jikinta Amman bakinta Yayi mata nauyi takasa cewa mata komai.

Uhm Ina jinki nablah ki sanar min da abinda ke damunki ko zan iya taimaka miki idan km har abun   yafi karfina sai mu sanarwa da aunty Salma. still shr nablah tayi taki cewa komai duk yadda nuratu taso nablah ta sanar mata da damuwarta Amman taki. Dan hk nuratu ta hakura  tace shawarata takarshe da zan baki kada ki kuskura ki gudu kije koina ki zauna duk rintsi km komai Yayi tsananin sauki Na zuwa da izinin Allah .sannan 
Ta Mike ta fice Daga dakin ..

byn fitar nuratu nablah ta sake afkawa 'cikin duniyar tunani iri iri a game da rayuwarta shekarata, ta 'cikin  Sha takwas kennan Amman tension din dake idanunta Yayi mata yawa. zuciyarta banda zafi bbu abinda take mata  ,tana murna tazo gida gashi tazo ta tadda wani sabon  tashin hankali dayafi na 'cikin jikinta.
Wai  babanta ya daura mata aure da mutumin da ko shi kansa Bai San kowaye ba .abu kmr a film..
Yadda nablah batasamu runtsawa ba hk ce  takasance da deeni  shima.
Dan  kwata kwata ko kwanciya kasawa Yayi atsaye yake yana ta faman aikin zariyar a dakinsa .
 Da tunanin abinda zai biyo baya domin ake uku yayiwa Kule direban ummi zuwa unguwar su nablah ya daukota Amman taki biyo shi wai ba yanzu zata dawo ba har yakira ummi 'cikin tashin hankali  fisrt love kin Gani ko.
 kinga abinda yasa kikaji naki yarda da zuwan yarinyar nan ko... yanzu meyye solution ? 

 nifa zanje kai tsaye komai ma zai faru sai dai....naji Amman kabari zuwa gobe mugani ummi ta katse shi ta hanyar ce masa hk.
Ni San yarinyar nan bazata iya zaman gidansu. Da 'cikin jikinta ba .
Jin ummi kawai yake Amman gabadaya  hankalinsa a mutukar tashe yake.
  zariya yake sosai hannuwansa duka rungume da kirjinshi ...yana Allah Allah gari yawaye.



Washegari garin ranar mlm salisu ya iske Nablah kwance a dakin mama ta lullube jikinta da bargo duk tunani duniya  ya adabi ruhinta .tana ganin mahaifinta ne ta Mike Daga kwanciyar datayi ta zauna sosai kanta a sunkuye tana gaidashi ya amsa yana dubanta shi kansa yasan yana matukar sonta duk 'cikin yayansa km bayason damuwarta sannan ya zauna Yayi tunani sosai akanta Dan hk sbd jin dadin abinda tayi masa ahankali ya zauna abakin gadon ya kamo hannuta yana nazarinta muryarsa a kausashe mlm salisu yasoma mgn 'cikin natsuwa nabeelah duk 'cikin yayana bbu me mun biyayya kmr ki ba me son farincikina kmr ki  dole nima naso farincikinki tamkar yadda kike son farincikina a bisa biyayyar da kika min na auren dana miki baki min gardama ba ko nuna min kinki ko ki mutsa min ko kin kangare min ba  shiyasa  nima zanyi kokari  naga Na faranta miki.
 kije byn wata uku ki dawo ubangiji Allah Yayi miki albarka duniya da lahira ubangiji Allah Ya tsareki da tsarewarsa ubangiji ya kareki daga dukkanin wani sharri ko wani abin ki .
Allah yakaiki lfy ya dawo min  dake lfy sannan kitsare min mutunci ki da martabarki kin dai Ga yadda mahaifinki yake bakowa bane facce mlm salisu da Allah Ya rufa masa asiri yanzu  ..  nabeelah kimin alkwarin byn wata uku zaki dawo gareni kada kisani jin kunya ..tana kuka muryata rawa zuciyarta bugawa tace Nagode banana km inshallahu zan dawo kmr yadda kace ..kibar kukan nan hk  yanzu yaushe zaki koma can din ?
Inshallahu zuwa jibi to to shikennan Allah Ya nuna mana naga tsabar da hjyr tace akawo Masha Allah idan Kin koma kiyi mata godiya sosai ya Mike tsaye jikinshi a sanyaye ya fita Daga dakin ..


Nablah tasamu  natsuwa  ta kwantar da hankalinta tashiga 'cikin yan'uwanta anata shan shafta daita  ko yau din nan sai da Kule yazo Sau biyu  tace mishi ita batashirya ba sai gobe hk ya juya ya koma ya sanarwa ummi hankalinta Yayi matukar mugun tashi sosai ,ZUCIYAR deeni kuwa kadan ya rage ta buga , tun sanda ummi tasoma sanar masa da abinda Nablah tace yakasa mgn da kwakwaran motsin sai ma runtse idanunshi da Yayi.
 yana jin yadda kirjinshi kemasa zafi da radadi ya dinga aiyanawa aranshi Anya kuwa *AUREN SIRRI*  bazai tashi ba ya  dawo  AUREN BAYYANE  ba? Shiru kawai Yacigaba dayi batare da yace komai ba domin idan yace zai yi mgn komai zai tabarbare , umminsa ce zatashiga damuwa da tashin hankali  bashi ba    hatta uwar gayya zeenat  hankalinta atashe yake matuka  sai surutai take xubawa tana tsinewa Nablah a kasan  zuciyarta ganinta nablah kawai tana neman rusa masu shirinsu ne .
byn yanzu kowa yagama sanin ciki gareta ..

Washegari daga gurin aiki Kai tsaye unguwarsu nablah deeni  ya nufa yasamu guri nesa kadan da gidansu Yayi parking batare da ya fito Daga 'cikin  motar ba Yayi waning din glass din motarsa  yasamu wani matashin yaro da baifi shekara goma xuwa Sha biyu ba  ya aika 'cikin gidan  yaje yace  ana kiran nablah .
byn  kmr minti biyar yaron ya fito yasanar masa wai bata nan take yaji zuciyarsa ta buga da karfi gaske .

 A hargitse ya sake tura yaro jeka please ka tmby Inda taje muryarsa Na rawa .
yaro yashiga ya sake fitowa  wai ance  ba'a San inda take ba  .
gabansa ya km bugawa da matsanancin sauri ya rantse rikitattun idanushi ya budesu fesss akan yaro  yace wa yace maka hk?

 yayarta nuratu ce .
take deeni yagane amsar rainin hankali nuratu tabawa yaron  'cikin wannan halin  sai Ga abba autansu nablah ..yazo shigewa 

 deeni yace yauwa abba zo nan ya, ya futoshi da hannushi  dayake abba  yasanshi km sun dan saba dashi tunda yana zuwa gurin mlm salisu time to time da murna yakaraso yazo ya tsaya jikin motar deeni yana gaisheshi  deeni ya katse shi ta hanyar ce masa  duba min 'cikin gidanku nablah Na ciki.. abba Yayi murmushi har gibinsa ya bayyana yace la......wai aunty kake nema Ai yanzun ma  narakata jection  zata shiga motar ko ina ni ma  wlh  nama manta Sunan gurin   .

deeni ya zaro rikitattun idanunshi  waje.
 wasu zafa suka shiga karyo masa hankalinsa ya sake tashi yashiga jero addu'oi kala kala sannan  yasoma  yiwa motarsa key cike da hanzari ya tada motar Bai sake cewa abba komai ba Yayi gaba da mugun gudu .

 abba da wannan yaron suka bi byn motar da kallo kafin Daga bisani suka  kama gabansu ..

Abban nashiga gidan  yake gayawa nuratu wannan mutumin da baba yake cewa mijin aunty nablah ne.
 yazo yanzu yana tmbyr aunty nablah Amman nace masa yanzu narakata shiga mota.
  nuratu ta juyo da  wani irin mahaukaci sauri tana kallon Abba Dan Allah ? 
Wlh .daxo da zanshigo gida naganta da jaka  shine tace naraka . Yanzu km byn Na rakata km.... ubanka naji naji ba wannan dogon surunta naka nace kakaranto min ba, ai nasan da zance  tafiyarta ,shi dai mutumin dakace yazo nemanta ne nace   karya kakeyi .
 mutumin da Bai San da dawowar Nablah ba ta ya'ya zaice maka kakirata masa ita.
 Allah kuwa Aunty shine ya aiko musa sannan yace nima nakirata , ayya aiko wlh ban San  shi bane ,ta fadi Haka tare da  dafe goshinta har aika masa da bakar mgn nayi fa arashin sani .Na dauka wani ne wlh ....
Abba ya tabe bakinsa to ke aunty meyasa kike yin irin  hk ne ?
Komai fada fada da bakar mgn yakarasa fadar mgnrsa  tare da shigewa 'cikin dakin mama yana mata gunguni ta juya tabi bayansa da kallon tana mamakinsa  sannan yace Dan rainin hankali kawai ni kake fadawa hk taja tsaki tacigaba da aikin gabanta.  ,




Gudu sosai Deeni yake sulawa akan express din oshodi zuwa kan bridge din obalende gabadaya a rude yake addu'a kawai yakeyi  a bayyane Allah Yasa estate dinsu ta nufa ba wani guri ba ji yake tamkar ya fly yaganshi a gida km yaganta  wani irin tsalle zuciyarsa ke yi sakamakon rudanin daya shiga.
 " jikinsa Yayi mugun yin sanyi tamkar ana masa wanka da ruwan kankara da kyar yake iya hadeye miyo makoshinsa.
 dai dai 'bakin checking point din da zai Kai mutun zuwa  jakonde first get  ya hangota zaune gaban wata dalleliyar motar fuskarta dauke da murmushi har wushiryarta ta bayyana .da sauri ya runtse idanunshi tare da sa hannushi ya murzasu  .
ya sake budewa tabbas ita din dai yagani zaune gaban motar wani  shima mutumin ciki sai dariya yake bulbula mata yana shafa sumar kanshi da hannunshi.


Da sauri deeni ya bud'e murfin  motarsa yana shirin fitowa, kafin ya gama fitowa aka basu hannu da hanzari ya koma cikin motor tamkar wani zarar re yayi mata key, yabi bayan su, aguje sosai Deeni yake zabga uban  gudu akan titi, dan shi kanshi bai san gudun mutuwa yake ba. 


Ajiyar zuciya ya sauke ganin sun nufi titin estate d'in su, ci gaba yayi da binsu  baya , ahankali ahankali har suka k'arasa ko'far estate d'in daga can baya Deeni ya tsaya yana hangen su yana son yaga abinda zai faru a tsakaninsu .


Zuciyar sa ce ta buga da k'arfi gaske lokacin dayaga Nablah tana sake yiwa matuk'in motar murmushi, wanda har sai da dimple dinta  ta bayyana, sai da ta kusan wajen 15mnts da tsayawar motar sannan ta fito, har ta fara tafiya, mutumin ya k'ara yi mata magana ta juya ta rufe motar ta sunkuya ta window motar. 


Mutumin yace " dan Allah ki bani phone number ki mana idan babu damuwa,sbd idan zanzo gurinki  dariya tayi sosai  dimple  din ta ya sake  lotsawa, muryarta a sanyaye  tace " bani da waya wlh  a gidan mu ba'a bari na rik'e phone, nagode sosai da taimakon dakayi min, ya bude motarsa  ya fito ya tsaya agabanta yana gyara wuyar rigarsa tare da  karemata kallon tsab sannan yace Ok to ko zan iya samun card din  shiga estate din Ku .
Ta sake yin murmushi ai ba gidanmu bane aiki nake yi aciki ,can unguwar daka daukoni  to anan gidanmu yake. yashiga yi mata wani irin kallo yana  mamaki acikin ranshi yana maimaita  aiki aiki nake yi anan .....kennan duk wannan kyawun nata a geto take rayuwa  ? Take km 
Wata zuciyarsa tace masa  kada kayi mamaki daman  mata masu tsantsar kyau da hankali suna geto km ya'yan talakawa ne ..... we'll shikennan yace babu damuwa  koma dai  menene naji nagani  Ina sonki hk da fatan zaki karbeni ..... muryarta a shagwabe km a sanyaye tace uhm Nagode da soyayya ya dauko   iPhone x ya Mika mata ki karbi wannan wayar so that idan zanzo sai Na Kira ki .
Ta girgiza masa kanta alamun bataso wayyohhhyyy  kadan ya rage manager deeni Bai sume ba zaune 'cikin mota tsabar jarabar kishi mutumin Yayi ta karba taki karba sai daya matsa mata sosai  tukun ta karba   ta juya  tasoma bada steps din tafiyarta me kashiwa mutun jikinshi ta shiga estate din . 


Tunda Deeni yaga yadda Nablah keyiwa mutumin nan  murmushi da dariya har fararen  hak'onranta na bayyana, dimples d'inta suna lotsa, yaji kamar ya mutu, wani irin abu yaji ya tokare masa k'irjinsa, yana caccakar ruhinsa da tsokar jikinshi  take km  zuciyarsa ta shiga bugawa,  idonsa suka dena gani sosai sai dishi-dishi, wani irin mugun zafi gami da d'aci yaji yana taso masa daga zuciyar sa zuwa k'irjinsa, nan da nan bak'in ciki gami da zafin zuciyarsa suka k'aro, yana ganin Nablah ta shiga gida ya fito da hanzari, ko motar bai tsaya rufewa ba, wata irin tafiya yake, ya nufi mutum dake shirin shiga  motarsa . 


A kansa Deeni ya tsaya cak  yana k'are masa kallo tsana .
, iska ya furzar gameda yarfa hannunsa  yace " kai mlm wannan yarinyar daga ina ka d'auko ta?
, wani irin wulak'antaccen kallo mutumin yayiwa Deeni sannan  yace " malam lafiya dai?


Wata irin razananniyar Tsawa Deeni ya daka mishi yace " ban iskanci  ba tamabayar ka nake ba.
 cikin isa mutumin yace " daga gidan su, Deeni yace " meye tsakaninka da ita? 

" Santa nake kuma auren ta  zanyi mutumin ya bawa Deeni amsa kai tsaye, sai da Deeni ya dafe saitin zuciyarsa saboda wata muguwar bugawa da tayi da k'arfi, tana barazanar fasa k'irjinsa, hannunsa ya luma cikin sumar kansa, yana cizon leb'en sa da k'arfi, a harzuk'e yace " waye uban ka? 


Ido mutumin ya zaro, shima cikin zafin rai yace " dalla malam waye kai dazaka zo kaina ka tsaya kana min wasu surutai marasa kan gado? 


Deeni ya nuna kansa yace " ni......?  

sai kuma yayi guntun murmushi yace " dan uwarka uban waye ya baka izinin tsaya min da mata ta,?
 ido mutumin ya zaro yace " matar ka fa..? 


"Kwarai kuwa matata ce, baka da hankali ne da baka lura da cikin dake jikin ta ba? 


" dan girman Allah kayi hak'uri wallahi ban san matar aure bace, kuma Nablah bata gaya min tana da aure ba asalima yau nasoma ganinta har ma narage mata hanya . 


Jin mutumin ya kira sunanta yasa Deeni k'ara harzuk'a, nan yabar mutumin ya nufi gida, a parlor ya sami Ummi da Nablah suna hira, dayake ummi  tazo gidan maida kayan Nablah ...a fusace ya shigo parlor, hannunsa dafe da zuciyarsa, idonuwansa sunyi mugun yin nauyi , tafiya yake yana tangad'i tsabar jarabar kishi dake cin zuciyarsa..


" Subhanallahi  Ummi ta fad'a ta mik'e tsaye ta  nufe shi da sauri , dan bata tab'a ganin Deeni cikin mawuyacin hali,i Rin hk ba  kuma cikin tashin hankali irin na yau ba, da ganin baya cikin hayyacinsa, gadan-gadan kan Nablah ya nufa, itama tayi masifar tsorata da ganin yanayinsa da sauri ta mik'e tayi bayan Ummi da gudu. Wayyohhhyyy nashiga uku..


Ummi na tambaya lafiya? amma ina ita kawai yake san ya kama, itako ta b'oye a bayan Ummi, kwata-kwata ya manta da wani cikin jikin ta, idonsa ya rufe, cikin zafin rai ya fisgo ta daga bayan Ummi ya zuba mata lafiyayyun kuma kyawawan marika guda guda biyu , then  yana shirin rufeta da duka Ummi ta shiga tsakanin su tana rufeshi da maseefa ....



Nablah ta zube kasa  tana kuka kamar ranta zai fita, hannunta Ummi ta kama takai ta d'aki, a bakin gado ta zaunar da ita, fridge taje ta d'auko mata ruwan me sanyi ta bata, sai da tasha Ummi ta kalle ta tace " mai kika yi mishi? 


Cikin kuka Nablah tace " wallahi Ummi banyi mishi komai ba., 

"To naji yi shiru kinji, sosai Ummi ta lallashi Nablah sannan ta fita, a parlor ta iske shi, a tsaye yadda ta barshi, kallon sa Ummi tayi tace " me tayi maka son? 


Shiru yayi, tare da  furzar da iska,me zafi  yayi ruku'u, ya mik'e a galabaice cikin rawar murya yace " wai yarinyar nan dan iskanci da aure na a kanta take kula samari, harta hau gaban motar sa suna hira tanayi masa murmushi, shi kuma d'an iska na tambaye meye tsakanin su, yace min wai santa yake, auren ta zaiyi, babban abin haushin ma har sunan ta ta fad'a mishi da karbar waya a hannunshi ...


Murmushi Ummi tayi irin na manya ta kama hannunsa ta zaunar dashi ahankali a tsanake  take  kallonshi  tace"..........


MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO



    Dedicated to    
*HAUWA A usman*
       ( JIDDARH)



Page 96


Tace idan ance maka kana son yarinyar nan nablah  kace Sam  baka sonta.
" yanzu gashi nan tsabar kishi ji yadda gabadaya yanayinka yakoma.
  tunda Na haifeka deeni har zuwa yanzu ban taba ganin kamanninka sun sauya kazama wani irin mutun abun tsoro kmr irin  yau ba .
 "kama manta da cikar burinka wato 'cikin dake tare daita sbd tsabar kishi idanunka sun rufe kazo ka kwakwadawa yarinyar mutane mari.
 in banda ma Allah Yasa  Ina nan nashiga tsakani da sai kamata dukan dakayi asarar bby'n cikinta .
 "idan ance kana sonta kace Kai ba Haka ba yanzu meyye wannan kayi ?

 

Deeni Ga son yarinyar nan karara Ina Gani acikin kwayar idanunka tare da  zunzurutun kishinta .
Wanda Yasa har  zuciyarka ke bugawa da karfin.
 alokacin fa daka shigo dafe da tsaitin kirjinka kake sbd tsabar jarabar kishi da kunar da zuciyarka ke maka akanta  ...

Deeni kana son yarinyar nan ko ka yarda ko karka yarda.
 kanawa nabla wani irin  mahaukacin so ka duba yadda kishi Yasa zakawa yarinyar nan  nakaso.
 ka duba yadda kake huci kmr zaki , ka duba yadda ka kama Yar mutane zaka mata dukan mutuwa kana kokarin  son  illata musu 'ya deeni ..
 tunda ummi tasoma mgn deeni Yayi shr kawai yana sauraronta  batare da Yayi yunkurin cewa mata   komai ba.
 sai ma rikitattun idanunshi daya tsura mata yana mata wani irin kallo me cike jin tsoron furucinta ...
uhm kayi shr kana dubana  kaki cewa dani komai.
 sbd kana tunanin zance nah ba hk bane.. muryarsa a sarke km can kasa kasa yace first love ....sai km Yayi shr ..
  Deeni kennan karyata mgnta zakayi ko ?
  Ba wai karyatawa zanyi ba first love Amman ni bana jin hkn atare dani km  har cikin zuciyata da ruhin jikina bana jin wai sonta nake  ..Ni dai nasan Ina matukar kishin igiyoyin  aurena dake kanta yakarasa fadar Haka zuciyarsa Na tsananta bugawa da sauri da sauri....
Babu komai lokaci shi zai nuna  Haka .
can km ummi tayi kasa sosai da muryarta  nidai Dan girman Allah ka sausautawa kanka akan lamarin yarinyar nan..
Sannan km karage wannan mugun son dakake mata sbd gaba.. domin idan har yadda nake hango tsagwaron kaunarta 'cikin idanunka,idan  suka zarta hk akwai matsala wanda gaba   banida abinyi ....
Sannan ka tausayawa zeenat dina kada ta fuskanci wannan son dakake mata.
 " ka boye mata kada ruhinta Yayi baki wanda nasan sanadiyar hkn zata iya shiga 'cikin wani hali  ......hakika Ina tausayawa diyata ummi  takarasa mgnrta tamkar zata zubda hawayen tausayin zeenat.
 jikinsa a matukar  sanyaye ya kamo hannuwan ummi  dukka 'cikin nashi sannan ya Kira sunanta ... first love  ki daina ce min  hk sannan ki daina cewa Ina son yarinyar nan.
 kada bakinki ya kamani ..
"bawai bakina zai kamaka  bane deeni oready karigada kayi wannan saken...
Saken daka fada tarkon soyayyarta .
Ni farincikinka shine nawa ka nutsu kadaina takura kanka akanta dayawa  ....
a Dan zafafe ya Mike tsaye ta riko hannunshi dake 'cikin nata Ina zuwa km sbd nace ka daina takura kanka akanta ne kayi fushi  ..?
runtse rikitattun idanunshi Yayi sannan ya bude fess yana duban fuskar umminsa .. Sam wlh ba hk bane my first love zuwa zanyi nayi wannan yarinyar worning da kyau "
Dan wlh first love zan iya ilatata a duk sanda  Na sake ganinta da wani Kato ...
karka sake ka km taba lafiyar jikinta ..
'Cikin jin zafin abinda ummi tace Ya kamo lips dinsa na kasa yana  cizawa  yana zame hannunshi cikin nata tare da hawa step ...
yayinda duk wannan dramar da'ake madam zeenat Na can dakinta ta  manne kunneta da earpiece tana faman aikin  chatting..


Yana shigowa dakin ya isketa  zaune tana kuka sosai har da shesheka wani irin kallo wulakanci yajefo mata wanda Yasa kirjinta bugawa  da sauri ta yunkura ta Mike tsaye da Dan saurinta  jikinta Na kirma takoina .. a fusace deeni ya nuna Nablah dake tsaye da Yatsansa daya kana yace Daga Ina wannan mummunar mutumin ya daukoki ?

Tayi shr taki cewa komai sai hawaye ne ke silalowa.
 ya furzar da isaka ta bakinsa yana cigaba da mgn 'cikin bacin rai    Dan wulakanci km da tsabar iskanci Na tura Kule  har so ba adadi gidanku ya  daukoki Amman dayake ke Yar rainin sense ce  kikace bazaki xoba ko? sbd kinsa iskancin da kika shiryawa  kanki  ko ?
 Amman yanzu kin iya biyo wani katon banza har  kina washe masa baki .
....to dariyar uwar me kike masa ?
Tayi shr nan ma  taki  yin mgn sai wani  hawaye ne  sharrrrrrr ke sake fitowa Daga idanunta.
 shiiiiii ya daura yatsansa akan lips dinsa yi min shr munafuka kawai  kukan munafurci me zaki min byn ki bude baki ,ki amsa min questions dina .
 aiko take nablah  tasoma maida kukanta da sauri ...
 wai ke stupid har da wani  fari kike masa da  wayan nan banzayen  shanyayyun idanun naki  masu kama dana mayyu ko... ?
 'zo nan  zo nan ki kawo min wayar da wacen Dan iskan mutumin yabaki  me kama kwado .. tayi saurin girgiza masa kanta alamun bazata zo ba.
 Ok bazaki zo ba ?
 bari  ni nakaraso da kaina  yasoma     nufota ransa  abace.
 muryarta na rawa tace Dan girman Allah ka tsaya a nan karkaraso gareni tsoranka nake ji  km ni wlh .... Tambayoyinka sun min nauyi wlh  bazan iya amsa maka ba.
 Kinsa Allah sai kin amsa min km a yanzu 'cikin kuka tace wlh bazan iya ba.
Zaki iya ne  ya fada yana karasowa gabanta Daga inda yake yana jiyo  bugun zuciyarta da sauri kmr yadda yake jin nasa zuciyar Na tsananta bugawa da sauri tana ganin Yayi kusa daita sosai .
taja baya sannan ta tsura masa shanyayyun idanunta 'cikin nashi  wanda hkn yayi sanadiyar fitowar wasu abubuwa Daga idanunta suna shiga 'cikin nasa wani irin shock ya dinga ji ajikinsa .... muryarta a raunane km a shagwabe tace to..to..ka natsu ka daina fushin nan ka  zauna zangaya maka wlh  ... Nablah karki sake ki kawomin rainin hankali.
Wlh  kinyi kadan ki wulakanta deeni .. 
Sannan Ina son ki  sani ni ba lusarin namiji bane wanda Bai San ciwon kanshi ba da kimar nauyin dake kansa ba  .
 cikakken namiji ne Ni  wanda zai iya gwada kunjinsa a muhalinsa daya dace..
 "  gabadaya ta rude takasa fahimarta inda zancesa suka  dosa yakarasa fadar hk.  muryasa  'cikin da fada fada .
 gabadaya ta sake rudewa tarasa yadda zatayi dashi.
 domin bata son yanawa lamarinta shishigi da abinda yashafi rayuwarta .
Ganin yanayinsa Na sake birkicewa Yasa take wata idea tazo mata tayi saurin dafe gaban goshinta da hannuta tare da yin  kasa luuuuuuuu zata fadi   ..nan da nan deeni hankalinsa ya tashi karasa karasowa Yayi  gareta yana  kiran  sunanta tare da rungumata jikinshi taki  amsa kiran dayake mata .
Ke nablah .. nablah yana kiran sunanta ya girgiza fuskarta tana jinshi ta sake lafewa ajikinshi tana shakar daddaden kashin turaren jikinsa.
 ya Mike  tsaye daita ajikinshi ya kwantar daita a saman gado .
Da"" hanzari jikinsa Na rawa ya nufi  fridge  dauko ruwa ... nablah naganin hk ta Mike tsaye da sauri tayi hanyar waje da hanzarinta sai dai tana fita Daga dakin  taci karo da zeenat wacce ta fito yanzu  Daga bedroom dinta.
 da sauri nablah tace yi hkr Dan Allah aunty tana goge Hawayen fuskarta  ..

Me yabiyo hk Daga dakin ? Zeenat 
Ta fada tare da rike mata kafardata.
 muryar nablah  cike da matsananciyar tsoro tace shiiiiiiiii shine ...

Shine wa ?
 Daidai lokacin da deeni ya fito Daga dakin nablah  a frigice yana haki ganewa da Yayi wayo nablah tayi masa  yanaganinsu yaja birki  ya cuge  abakin kofa tare da rungume duka hannuwansa a fadadden kirjinshi yana dubansu.
 zeenat takai dubanta kan kofar taganshi tsaye kyam yana kallonsu da rikitattun idanunshi jawur sun koma kalar tashin hankali..

Ajiya zuciya zeenat ta sauke da karfi tare da tmbyr nablah mekika yi masa yashigo har dakinki ?

Nablah dake tsaye a gefen zeenat jikinta Na Dan kirma ta dubi deeni kadan sannan muryarta cike da in..inna.. tace wlh wlh.. aunty nima  bansani ba km daman ba sai Nayi  masa wani abu ba yake cin zalina. takarasa mgnr muryarta cike da shagwaba .. murmushin takaici  kawai zeenat tayi Dan wani irin abu taji ya caki tsakiyar zuciyarta. kirjinta  yashiga yi mata zafi da tafarfasa Amman ta danne.
 ta bude bakinta da kyar tace to daina wannan nishin da hakin dakikeyi  yanzu Ina zaki ?

Parlour zani gurin ummi to jeki abunki kinji ,sannan  ki saki ranki sosai sannan ki daina wannan tsalle tsallen dakike Kinsa bake kadai bace  nablah tayi jummmmmm da ranta  tare da matsawa Daga rikon da zeenat tayi mata tace tkns aunty zeenat am okay now ..
nan nablah ta wuce bata koma takan deeni dake tsaye yana kallonsu  tamkar wasu  picture ba ...takarasa sauka kasa .. zeenat tabita da kallo tana jin Ina ma itace da 'cikin jikin yarinyar nan .
Ina ma ajikinta yake ..Ina ma itace dauke dashi km na mijinta ne mafi soyuwa acikin zuciyata .. Allah mai iko akan komai .
Yabaka abu  km ya tafiyar dashi yadda yake so.
 kowa da yadda Allah yake son ganinsa dubi me yarinya tasamu ciki  sauki bbu laulayi komai ko amai ko wani abu daya danganci wahala da matsala.
wani lokacin idan taga nablah Na tsalle da 'cikin jikinta har kuka take abinda ita takasa jurewa kennan arayuwarki  gashi karamar yarinya ta jure duk da batasan wayye uban 'cikin ba ..


jikinta a mace ta sauke naunauyen ajiyar zuciya ta juyo  tana duban deeni dake tsaye har lokaci..

Ahankali zeenat ta maida hankalinta sosai kan mijinta mafi soyuwa a zuciyarta ...me nablah tayi maka  ka biyota irin hk alhalin kasan condition din datake ciki ?
Wani irin kallo rainin sense ya aiko mata dashi   sannan ya dubeta sama da kasa yace bbu ruwanki dani da km  abinda nayi mata gabadaya ya sake hargitsawa sbd jin haushin tmbyr da zeenat din  tayi masa ..
cool down my hrt tmby ce fa kawai .. just stay out of my way ya fada yana bin gefenta tare da shigewa dakinsa da kafa ya banko kofar da karfi ya fada kan makeken royal bed dinsa ..

Why why I care when someone else gets close wit her?
 ya jihowa kanshi wannan tmbyr yana me  runtse rikitattun idanunshi..


Zeenat ta Dan jima tsaye agurin byn barin deeni  tana wani irin tunani nadaban a zuciyarta tare  da nazarin yanayinsa. zuciyarta tasoma harbawa tana tsalle  can km zuciyarta tayi sanyi tayi saurin cire abinda ya darsu a ranta ..wanda take ganin da kamar  wuya faruwarsa ..


Bangaren deeni kuwa ahankali zuciyarsa tayi masa sanyi ko bbu komai ya godewa Allah dayasa ta dawo masa lfy da cikinsa .
 wanda ahalin yanzu Yake  tunanin bazai sake sakacin barinta zuwa koina ba ballanantana wannan hargitsatsiyar unguwar tasu .. sannu ahankali km zantuttukan umminsa ke dawo masa  daya byn daya akan wai son yarinyar yake .
ya girgiza kanshi kawai yana son karyata zance ,ai km ummi ita takawoshi duniya tasanshi tasan halinsa , yakamata ya amincewa kanshi da son yarinyar nan yake..Amman kwata kwata zuciyarsa taki yarda da hk .
 Ahankali tunaninsa yakai Ga Fk jikinsa a mace Ya janyo wayarsa Yayi dealing din number fk bugu daya biyu fk ya dauka da sallamarsa deeni ya amsa yana sakin numafashi da kyar.

 fk yace aboki ya'akayi ne ? 

Please kazo yanzu yanzu Ina son ganinka fk dake kishingide a parlour gidan sa yana kallon ball ya Mike zauna tare da da cewa lfy abokina ..
deeni ya furzar da isaka ta bakinsa yace Kai dai kazo kawai.
 fk ya Mike tsaye Ok Gani nan  zuwa ya fito Daga part dinsa yana cigaba da waya da deeni ..
Byn kmr minti goma sai Ga fk wanda zuwa lokacin gabadaya mutane gidan kowane yashige dakinsa ..



Kai tsaye dakin deeni fk ya nufa ya ganshi zaune a hargetse wani iri iri dashi  sai huro bakinsa yake da iska  yana sakewa.
  fk Yayi saurin karasowa gareshi yana aiko masa da tambayoyi iri iri da hannu deeni yayi masa nuni da gurin zama ..
byn fk ya zauna yana duban deeni.
Sai da deeni sauke numfashi ajire kmr Sau biyar da ajiyar zuciya sannan muryarsa a galabaice yace wasu Yan tambayoyi nake son zan maka please. Kataima min kasanar dani amsoshinsu  kada ka boye min komai idan har kasan amsar tambayoyin da zan maka .

fk yabashi gabadaya attention dinsa sosai yana jira Daga gareshi  . uhmmmm ina jinka .
Yauwa Kana ji ko akwai wata yarinya aduk sanda naganta  zuciyata ta dinga tsananta  yawan bugawa da faduwa kennan .
Sannan ko ganinta nayi da wani someone else zakaga  hankalina Yayi kololuwar  tashi tamkar zanyi hauka .
km idan bana kusa daita bana jin dadin rayuwa da zuciyata.
 matsuwa nake naganni Gani gata  . 
shine abun ya dameni nake son kasanarmin meke sa mutun tsintar kanshi'cikin wannan yanayin ?

 Wacece wannan yarinyar firstly ?

Wannan ba damuwarka bane  Fk da son sani kowace amsar tambayoyina kawai nake son ji  .Ok fk ya fadi Haka tare da dafa kafadarsa deeni da hannunshi daya sannan yace  da fari dai duk abinda kalissafa din nan  suna Daga 'cikin kadan Daga alamomin matsanancin so da kauna.....
 deeni ya zubaura ya Mike tsaye tare da dafe saitin zuciyarsa ,fk Yayi saurin me dashi inda ya tashi  cool dwon deeni .

koma wacece wannan yarinyar kayi nisa acikin tafkin sonta .
deeni ya dungule hannusa ya  buga akan  center table  yana jijiga kafarsa daya da kamo lips dinsa na kasa ya danne sosai da hakorinsa.
 nan dai fk yashiga yi masa bayanin dalla dalla da fahimta dashi abinda ke haifar da hk Dan yasan bashi da ilimin ta wannan fannin.
 kana yakarasa mgnrsa da cewa ko ita ce wannan yarinyar ta ranan nan?
Afrigice deeni ya dago rikitattun idanunshi ya zuba masa sannan ya girgiza masa kanshi alamun ba ita  bace.
To koma wacece kana matsanancin sonta km irin  sosai din nah .
Deeni yayi sororo yana tunani .

da fari nablah da kanta ta sanar masa sannan umminsa ta gayamishi hk .
yanzu km  Ga fk ya sake fahimtar dashi .. Amman duk da hk  yana ji azuciyarsa ba gsky bane ta ya'ya zai sota. 
take km  zuciyarsa tace masa  wakake son km ya sake  tabbatar maka da sonta kake ?
Zeenat ce ta fado masa ?
Yaji gabansa ya fadi rassss yacigaba da dukan uku uku .
  fk yabar zance yashiga janshi da hira ahankali ahankali har ya dawo dashi 'cikin natsuwarsa suka shiga hira Amman har lokaci zuciyar deeni cike take tap da  alhinin lamarin.
Shi sai yasan baya sonta Amman km bazai iya rabuwa daita ba.
 sai wajajen magriba sannan  fk yabar gidan .


Rashin jin duriyar  deeni a gidan tun rana Yasa abin duniya ya damu ZUCIYAR zeenat.
Byn tagama duk wani abinda take kafin bacci  ta nufi dakinsa  jikinta sanye da wani guntun  mini siket iya cinyarta da riga otanet.
 wacce ta bayyana brest dinta ta sama .
, kwance taganshi akan makeken gadonsa  yayi rigingine idanunshi Na kallon celling saman dakin da gani tunani yake mai zurfi,gaske.


 kan jikinsa ta fad'a tana narke masa cike da shagwaba iri iri tana tmbyrsa damuwarsa kayi hakuri idan sbd tmbyr dana maka dazu ne da abinda nace .
, kallonta yayi da rikitattun idanunshi yaga yadda duk tashiga damuwa akanshi .
  sai km tausayinta yakamashi Dan hk ya Dan  sakar mata murmushi tare da yi  mata mazauni a faffad'an k'irjinsa, hannunta ta cusa cikin k'irjinsa tana shafawa a hankali,  ido ya lumshe ya shak'i iska da k'arfi, ya fesar  ganin haka ne yasata had'e bakin su waje d'aya takai hannunta kan jijiyarsa tana shafawa, yayinda d'ayan hannunta yake kan nipply dinsa yana murzawa .



Birkita ta yayi, ya shiga romancing d'inta a gaggauce, gaba d'ayan suka  afka 'cikin  wata duniya ta daban,kusan 30mints suka dauka  suna romancing din junansu kafin Daga baya  ahankali ya samu nasarar shigarta. 


Sosai Deeni yake sex da Zeenart amma abin mamakin yadda ya kasa gamsuwa, daita.
 kwata-kwata yadda kasan ba aiki  yake ba , babu yadda Deeni bayyi ba dan ganin buk'atarsa ta biya yayinda ita tunin tayi release.
amma ina Shi  sam Bai yi .
, nan take Nablah ta fad'o,masa arai  ya tuna yadda yake jin dad'inta da yadda yake samun nutsuwa daita, duk da ba 'cikin haiyacinta take ba .
 wani irin shock yaji ajikinsa wanda har tsigar jikinshi suka Mike tsaye yrrrrrrrrrrrrr..... 


Zeenat kuwa sai faman kuka take tana raki, " wai har yanzu baka gamsu bane, ni gaskiya na fara  gajiya fa , wallahi bazan iya ba please ka d'agani, tsaki Deeni yayi ya d'aga Zeenat ko kallanta baiyi ba ya shige birthroom ya barta nan kwance tana ta faman juyi da kuka. 


_To k'alubale gare ku mata, idan kina yiwa mijin ki irin raki haka toki tabbata zai fad'a masifar neman mata, idan kuma yana da k'arfin imani ne zaiyi miki kishiya, idan mijinki yana sex dake kamata yayi koda baki jin dad'i kuma kin gaji ki daure, ki nuna masa kina masifar jin dad'i to bari muga ya oga Deeni zaiyi_da tarin sha,awarsa?



Yana shiga bathroom ya sakarwa kansa ruwa, ranshi  yayi masifar b'aci, a game da yadda zeenat keda raki wa tunaninsa inda sabo yakamata ace tasaba da yanayinsa zuwa yanzu.
..Amman kullun 'cikin raki take ..Ya ja tsaki  a ransa yace " wato ita kanta ta sani kenan, idan buk'atarta tabiya ni ko'oho, bata damu ba, koma yaya  zanyi inyi, .
idan ma zina zanyi ita baishafeta ba, hmmm Allah sarki Nablah, ashe ba k'aramar dauriyya take dani ba. 


Haka Deeni yayita sak'e2 aransa harya fito daga wanka, a kwance shame2 ya sameta tana ta faman haki, kallonta yayi ya kauda kansa gefe yace " get out of my room, a tsorace ta kalle shi tace " but why my  hrt ... 


Hannusa duka  yasa ya  d'agata  yace " am not ur hrt  idan har da gaske kina sona  d'in da kika ta faman fad'a, zaki iya jurewa buk'ata .
 ko shekara zanyi a kanki ina tunanin zaki iya jurewa bawai da zarar Na biya miki bukatarki ki dameni da kingaji ba . 
Inda nakasance mazinaci wlh da tuni kin nemeni kin rasa.


 ,tunda nasan akwai matan dayawa  zasu iya da lalurata Amman ko yanzu Alhamdulilllahi.. Nagodewa Allah daya tsareni daga afkawa 'cikin zina...

Cikin sanyi jiki tace " ina sanka kuma Allah ya sani.
Km Allah  shine  shaida nah akan irin son danake maka , amma  gaskiya duk  girman soyayyar danake maka baikai na iya jurewa buk'atarka, gabadaya ba.
 ,deeni zaka iya spend din the only night kana sex da mace batare da kagaji ba .
Banza iya da bukatarka ba deeni  tafi karfina  ... gaban sa yaji yayi wani irin  muguwar fad'uwa da sauri ya kalle ta yace " kenan jurewa namiji sex, ba soyayya bace? 


Kai ta girgiza masa alamar eh, tacigaba ba k'aramar soyayya bace, shiyasa nima nake iya k'ok'arina akan ka, yace " ok to jeki kwanta. 

Kallonsa tayi tace " please kabarni na kwana anan, "no yace mata. 

" Please my hrt , hannu ya d'aga mata yace " please don't let me shout at u, just go ya fad'a yana nuna mata hanyar waje, jikinta a sanyaye ta fita. 

_Wallahi kowanne namiji zai iyayin haka harma fiye da haka akan sex_

Zenat na fita ya fad'a gado, ya shiga duniyar tunani, " ashe bak'aramin so Nablah kemin ba kenan da har take iya jurewa buk'ata ta, Allah sarki gata yar yarinya k'arama,Amman take daukeni tsab .. 
zumbur ya mik'e tsaye ya   kunne CCTV kwance ya ganta daga ita sai yar yaloluwar rigar bacci bako pant balle bra ajikinta  Dan zuwa  yanzu ko sakasu tayi sai taji duk sun takurata  ajiki duk da bawani girma 'cikin nata Yayi ba..


Idonsa ya lumshe ya ciji leb'en sa ahankali  yana shafa sumar kansa, nan take yaji mazakutar sa ta motsa, a hankali ya mik'e tsaye  jikinsa a sanyaye ya zira jallabiyarsa  ya d'auko maganin baccin ta,ya nufi dakinta.
Yadda yaganta acikin CCTV hk ya sameta tana ganinsa tayi saurin janyo bargo tarufawa  jikinta  tana lumshe shanyayyun idanunta batare da tace masa komai ba.
 shima Bai wani damu da yanayin ko in kular datayi masa ba sbd hankalinsa dake kan Dan karamin cup din dayagani  ajiye a gefen beside dinta wanda ke dauke da malt aciki da milk  .
'Cikin dabara ya jefa kwayar magani  ciki sannan ya zauna yana karewa yanayinta kallo tsab tare da kai hannunshi kan kafafunta da suka Dan kumbura kadan yasoma mammatsa mata.
 ta sake lumshe idanunta tana budesu karaf idanunsu suka sarke 'cikin juna .. muryarsa a mace yace tunani me kikeyi ta girgiza masa kanta hade da daukar cup din malt ta Kai bakinta tana Sha ahankali ahankali har Tasha rabi ta ajiye sauran .

Ki daina yawan tunani domin yana saurin illata rayuwar mutun .
most special keda ke dauki da juna biyu. wannan karon idanunta ta runtse gam ..sbd dadin yadda yake massaging din kafafunta zuwa gwiwarta.
 ahankali tasoma jin bacci bacci tana ganin double ta zame kafafunta Daga 'cikin hannunshi muryata cike da mayyen bacci tace bacci ..ta fada tana zabga wata uwar hamma ..baice daita komai ba sai ma lip's dinsa daya kamo yana cizawa cike da shaukinta ya Mike tsaye ya lullubeta kmr gaske Yayi gaba  .. 



 Byn kmr awa daya daga shi sai towel a kugunsa ya sake nufi d'akinta ta b'arauniyar hanyarsa dayasa ba bi batare da sanin kowa ba .


A hanakali yakarasa yaje ya kulle ainihin kofar  shigowa  d'akin, .
cikin sand'a ya bude bargon datake lullube tana  baccin, aciki.
 ya shafa kwakkywar fuskanta me dauke da sihirtaccen kyau .
sannan  ya lallab'a yaje ya  kashe fitilar d'akin, a hankali ya hau gadon,bakinsu  ya hade guri daya  yashiga tsotsa yana  zuba mata miyon bakinsa ciki ta datse bakinsa da harshenta  yayi saurin  toshe mata hanci,ta hanyar daura nasa hancin kan nata dole tasa Nablah shaye miyonsa  don son  shak'ar lumfashi ta. 
, yana ganin ta shanye ya koma gefen Daga gefe  ya kunna dum light, 'cikin matsanancin bukatuwa daita yasoma romancing dinta 'cikin shauki yana ruda mata sansar jiki , aiko bayan wasu 'yan mintuna yaji ta fara maida masa da martani da  magana alamun tazo hannu sosai.
 Dan sai shafosa take tana nishi ahankali  . murmushi yayi, kawai tare da haye wa kanta yadda bazai danne mata ciki ba, a hankali yaji  tana sauke lumfashi, kuma tana tajera  sheshekar kuka wanda  daga ji kasan tun kukan da taci ne yammacin ranar . 


Fuskarta ya shafo a hankali sannan km cike da tausayinta yace " am so sorry dear, ba'a san raina na mare ki ba, ni kaina ban san dalili na nayin hakan ba, kamar tana jinshi ta turo masa Dan  k'aramin tsukaken bakin ta, dariya yayi yace " mara kunya, daga nan ya had'e bakin su,waje yana masa wani irin tsutsa Na fitar hankali tamkar wani mayuncin zaki .
aiko da sauri itama ta cafki bakin sa , cikin magagin bacci tace " shine ka daina zuwa gurina  kwana biyu ko? 

Nayi missing d'inka sosai, please ka daina dad'ewa baka zo inda nake ba, kana sani cikin wani hali.
 ina buk'atarka sosai, please yauma kajiyar dani dad'i,daka saba jiyar dani  tana kaiwa nan ta sake had'e  bakin su, ta cafki laulausar harshensa tashiga tsotsa, takai hannuta kan jijiyarsa ...


Wani irin mahaukacin shock Deeni yaji tun daga tafin k'afarsa har zuwa kwakwalwarsa, hannusa ya cika da nonuwanta ya shiga murza kan nipply dinta a hankali,yayinda  hannunsa d'aya km  ya kai 'cikin  k'asanta ya shiga yi mata fingering sannan km  bakinsu na manne  cikin na juna hunnan d'aya a kan nononta d'ayan a k'asanta, itama hannunta d'aya yana kan jijiyarsa d'ayan yana kan nipple's d'insa. 


Sosai Nablah ta zage take neman tsotsewa Deeni ruwan kansa, gaba d'aya ta gama rikita shi,da birkita masa tunani cikin Gigi bacci ta mik'e tsaye tare da hannuwanshi, ya zame mata k'amar d'an k'aramin yaro duk inda ta jashi nan yake yi, kallonsa tayi da shanyayyun idanunta, tace ka tsaya a tsaye yau ni zanyi maka komai. Ya zaro ido 'cikin shaukin


Yadda take maganar tana fad'awa jikinsa ne ya k'ara jefa Deeni cikin matsanancin hali, nelldown tayi ta kai bakin ta kan jijiyarsa tashiga sucking d'insa, hannuwanta ta mik'a tana daga tsukunnan tana murza masa nipply dinsa. 


Tab! Aiko suman tsaye ne  kawai Deeni bai yi ba,amman  gaba d'aya ya gama fita daga hayyacinsa fit,.
 yarinya k'arama ta neman  zautar da shi, saida ta gama tsotse jijiyarsa tas sannan ta mik'e tasa harshenta akan nipply dinsa tashiga tsostsar tana lasa.. 


Hannayenta kuma suna yawo a duk  sansar jikinsa, saida ta gama tsotse masa nipply s tas, sannan ta kwantar dashi ta saka masa nononta a bakinsa kamar baby aiko caraf ya cafka ya shiga tsosa breasts dinta, ita kuma tana shafa masa sumar kansa, sai da yasha mata brest dinta sosai sannan, ta kwantar dashi sosai ta kwanta a kansa, ta tura masa k'asanta a bakinsa aiko ya shiga aikin sucking,dinta yana gurnani awa zakin dayake fagen fama   yayin da itama take k'ara tsotsar jijiyarsa, sun d'auki lokaci sosai  a haka suna jiyar da kansu dadi  sannan ta sake  mik'ewa ta hau kansa, da kanta ta cafki jijiyarsa ta danna 'cikin  k'asanta, ta fara sama da kasa. Tamkar ba me ciki ba sannan km kmr cikin ba'a jikinta yake ba .


Aiko tsabar dadi Oga Deeni Bai San sanda  ya bud'e muryarsa da iya k'arfinsa ba ya shiga kwarara wani azababen ihu, dadi ba .
 Zeenat tana can duniyar  bacci,  amma Ummi kam da daman baccinta rabi da rabi ne sbd sallonlin dare datake yi .

 tajiyo sautin  ihun Deeni, da sauri a kuma tsorace ta tafito still tana sake jiyo ihunsa jikinta Na rawa  ta nufi inda take jiyo sautin ihun tilon Dan nata.
 , tabbas daga d'akin Nablah take jiyo ihun Deeni, a bakin k'ofar d'akin ta tsaya tana k'ok'arin bud'e k'ofar ne tajiyo sambatun su. 


 Oga Deeni yace "Please karki fita daga rayuwata Nablah, ke haske ce a duniyata, sai a kanki na kara  tabbatar da meye aure, na kuma  kara sanin  yadda dad'in mace yake, Nablah kina da dad'i ga ni'ima, ke din  ta dabance,wllh bazan iya rayuwa babu ke ba, ban san dad'in sex yakai hk ba sai a kanki, ban san haka mace keda ni'ima da dad'i ba sai a kanki, wllh bazan iya rabuwa dake ba,  idan kika barni zan fad'a halakar neman mata,wayyyyyo dad'iiiiiiii,  Ummi dake bakin k'ofa tayi saurin  toshe bakinta , tana kuma jiyo sautin ihun Deeni da gurnani tare da sambatunsa, iri iri .


Cikin mutuwar jiki Ummi ta juya da matsanancin sauri  ta koma d'aki, zuciyarta tamkar zata kama da wuta a bakin gado ta zauna ta saka kuka mai cin rai, a Fili take magana " na shiga uku ni da kaina nayiwa  Zeenat diyata kishiyar da bazata iya da ita,ba.
 lalle na had'awa 'yata *GADAR ZARE* da kaina  wanda ga dukkanin  alamu ni da ita ne zamu fad'a ciki. 


"Ga duk alamu Nablah irin matan nan ne masu ni'ima dad'i wanda su natural haka Allah ya halicce su, tunda tasan Nablah bata tab'a amfanin da maganin mata ba, .
to idan kuma Nablah ta waye ta fara amfanin da maganin mata fa?

, ta kuma San  meye aure fa? 


Kuka ta k'ara fashewa dashi "wayyo na shiga uku , ji yadda Deeni ke ihu yana sambatu akan yarinya k'arama.
 Yar cikinsa  kwata2 baya cikin hayyacinsa, to wai ina Zeenat take da har ya samu damar zuwa ga Nablah,?

 lalle Zeenat ta tabbata lusarar mace km shasha  wacce ta rako mata duniya, tunda harta bari yarinya k'arama kamar Nablah take neman shirin  kwace mata miji.


Gaban Ummi ne yayi muguwar fad'uwa data tuno da maganganun Deeni, a fili tace " wato Zeenat bata iya biyawa masa   buk'atarsa ko me yake nufi ? 

tayiwa kanta tambaya, ta tuno yadda yake ihu yana cewa bazai iya rayuwa ba .
Bbu Nablah, zai fad'a zina, to tabbas idan dai   Zeenat bata iya biyawa Deeni buk'atarsa, aiko indai haka ne laifinta ne.
 kuma ta tafka babban kuskure,a rayuwarta ita komai sai ta zamto raguwa  km koma baya.

 Amman zata San abinyi domin bazata zuba idanu ba tana ji tana Gani wata tazo tafi diyar komai agurin miji ba .
Shiyasa fa tace lallai sai kaskantacciyar km mara  galihu take son ya  aura. Amman km 
Gashi  abu  Na neman sauya salo .
Rashe Na neman juyewa.....  haka dai Ummi tayi ta sak'a da warwara ta yadda zata bullowa lamarin . 


Oga Deeni kuwa yana can yana kwasar gara da sukwati on the ground  bai samu nutsuwa ba sai da yayi gud 4rs akan Nablah, sannan ya samu gamsuwa kuma ko sau d'aya Nablah bata ce masa ta gaji ba, sai ma had'in kai datake  bashi 100%. 


Wasai Deeni yaji shi, cassssssssssss .
 cak ya d'auke ta yayi bathroom da ita bath d'in wanka ya cika da ruwa ya saka su ciki, sosai ya b'ata lokacinsa yana mammatsata kafin yayi mata  wanka ya fito daita rungume ajikinshi.
  sai da ya shirta tsaf sannan ya kwantar da ita ya tsotsi lips dinta sosai , yayiwa goshinta light kiss ya fita Daga dakin .




MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
     💖💖💖
💗💗💗💗💗






AYSHA A BAGUDO 






            Dedicated to
        *HAUWA A USMAN* 
              (JIDDARH)





Page  97





Bayan Deeni ya koma d'akinsa .
Da kuzari ajikinshi ya fad'a kan makeken royal bed d'insa zuciyarsa cike da farinciki Mara misaltuwa.
 shiru yayi kawai ya tsurawa cilling dakin idanunsa  yana tuna abubuwan  masu mahimmaci da dadi atattare da lamarin yarinyar.. 


Duk ta yadda  ya runtse idanunshi ita yake gani rungume ajikinshi tana aikin  sarrafashi . Da susuta masa jiki .
gaba daya abubuwan da suka faru a tsakaninsu yanzu  ya dinga tunawa daya bayan d'aya . Yana hadawa guri daya 
 sai murmushin dadi  yake  hade da lumshe rikitattun idanunshi .
da kyar ya samu barci ya d'aukeshi cike da mafarkaiya  masu dad'i da tunzura zuciya .


Washegarin ranar da wani sabon  kuzari Deeni ya tashi fuskarsa wasai  dauke da annuri babu wani alamar damuwa a tattare dashi ko bakinciki .
 sai dai kallo zaka masa kagane miskili Na bugawa ajarida domin duk wannan farinciki Bai bare sun bayyana ba .
miskilancinnan nasa Na nan  ba inda yaje.


Dakin Nablah   ya nufa Kai tsaye .
  tura kofar yayi ya shiga hade da sallama,
 jingine ya sameta a jikin gadonta  hannayenta dukka  a saman ruwan cikinta. 
tayi zurfi cikin tunanin abinda ke faruwa daita lokaci xuwa lokaci . 
A duk sanda deeni yayi sex daita tana ji ajikinta tunda ba'a zahirance take ganin hk ba .
 sai kawai  tafi daukar abin amatsayin mafarki ne irin wanda tasaba  .
  ko shigowar Deeni batajiba har sanda  ya  karaso gabanta .
 bata sani ba.
 zama yayi a Gefen gadon tare  da rungumeta  a faffadan kirjinsa.
yana kaiwa wunyata sumba. Ita kuwa nablah jin an rungumeta yasata dawowa Daga duniyar tunani data lula tare da sauke A jiyar zuciya  da karfi ta tsura masa shanyayyun idanunta tana narke fuska .

 Shima rikitattun idanunshi ya tsura mata yana kallon 'cikin kwayar idanunta masu narkar da zuciyarsa da gangar jikinshi .
ahankali yake fidda wani  numfashin sama sama tamkar wanda yayi gudun tsare .
wani irin feelings yake ji yana tasomasa marar misaltuwa a duk lokacin da yake tare da ita.

 
 sake lafewa tayi sosai  a jikinsa tana  sake sauke  ajiyar zuciya tana shakar daddad'an kamshinsa.
 sun d'auki tsawon lokaci a haka kowannensu da abinda zuciyarsa take saka masa ahankali ya d'agota daga jikinsa ya kafeta da rikitattun idanunsa, itama shi take kallo da shanyayyun idanunta.

 fuskarsa ya had'e da tata yayinda sukejin numfashin juna cikin maganarsa Me kamada  rad'a yace "tunanin me kikeyi ne haka?"

 Muryarta a raunane tace   babu  komai fa  tare da kauda fuskarta Daga gareshi.
 yace "koma meye yakamata ki rage wlh bason  tunaninnan da kike yi , kar yazo  yashafi lafiyar babyna"
 yafad'a yana kashe mata ido tareda shafo cikin nata cikin wani irin shauki yakarasa fadar hk.
Bakinshi yakai daidai tsaitin kunnenta yace ki  shirya  anjima dake zan wuce   asibiti aduba min  lafiyarku,ke bby nah
 shagwab'e fuska tayi sosai tana turo masa Dan karamin tsukaken bakinta kana  tace "uhm uhm gaskiya ni banason  xuwa hospital .
Km ko bashi bama  ni gani nake tamkar  za'aa gane  cikin dake  jikina.
Sai daya tsotsi lips dinta sannan  " yace "wayema zai  ganki a mota ta fa zaki shiga"
 tace "nidai a'a" shiiiiii yace "banason jin komai Daga bakinki .Yar rainin hankali kawai  Amman 
 ranar nan  dayake gidanku zakije bakiji kunyar fita da 'cikin ba, bananan ma kika yi tafiyarki ... sannan kina jin  tsoron xuwa hospital  sbd kada wani yaganki da ciki  ,kika iya shigowa motar wani jaki tundaga geto area din ku har zuwa nan ,bakiji komai ba sai yanzu ne zaki kawo wa mutane salo.
 ,  dan haka banason musu ko wani iyayi ki  shirya kawai kafin na gama breakfast  marar kunyar karya kawai .
Ya Mike tsaye yana kokari barin dakin .
 To dole ne  sai naje hospital din  ince 'cikin nawa ne .
 km lafiyata za'a duba . Ya Dan dawo dabaya da baya ya juyo yana kallonta .
 yess Haka ne fa ,Amman km dole kije yarinya kiga doctor .yana gama fadar hkn ya fice gabadaya.
"

Ahankali yake taka step har yakarasa saukowa zuwa dining area din  fuskasa cike da tsansar annuri da zati so fresh dashi ya zauna akan kujerar dinning wanda oready yake a shirye. ummi da zeenat ne zaune suna zaman  jiran fitowarsa .
,abinci zeenat ta hada masa da coffee dinsa Na gado  yasoma ci yana jin wani irin sanyi har 'cikin zuciyarsa 'cikin sanyi jiki yasoma cin abinci  sbd Yadda yaga umminsa tana kallonsa.
Sosai idanun ummi ke yawo a tsantsar jikinshi  ,km da zarar sun hada ido da ummi  sai yaga tana masa wani irin kallo kmr Na tunhuma kmr Na tambaya  wanda shi kwata kwata  Bai ganewa manufar hkn ba.
 kasancewar shi ba me son mgn bane  Yasa yashare ummi kawai Bai ce mata komai ba .
 bai km Bai tambayeta dalili ba Amman shi aranshi yana jin kmr an dauke masa wani dutse ne sbd yana jin kanshi so freshi da farinciki byn yakammala  da cin abincinsa  yake sanarwa ummi zance  zuwansa asibiti da nablah zai wuce .
domin  yana son ya  kaita  a duba masa lfyrta.
 tun kafin ummi tayi mgn zeenat tace Kai  gsky  kam my hrt yakamata wlh danni nima Na dade da yin tunani akan hk .
Km  tun jiya kayi mgn ai da tare zamu .
Me zai hana yanzu ma kibisu kuje taren ai zaifi tunda kinga ke mace .
Bakamar ba .

Girgiza kanta  kawai tayi bari suje kawai  ummi wani lokaci maje .
 koma Na kaita da kaina ..


Bayan sun isa asbiti aka  dubata da lafiyar bby  akace za'a yi mata scanning.
  fur Nablah taki yarda tasoma kuka  dole haka Deeni.
Yana ji yana Gani  ya hakura dan ya fuskanci rikici takeji dashi .
Daga hospital din Kai tsaye office dinsa ya wuce da .
 
Suna shiga ta Mike kan kushin dinsa me kama da bed tayi Kwanciya .
 shi km ya kulle office din yasoma abinda yakawoshi  ..

Ahankali bacci ya dauketa baita ta tashi ba sai gurin la'asar.
  kallonsa tayi kmr zatayi kuka tace  deeni kana tsoron Allah kuwa ?
Kalli  yadda  lokaci bautar Allah Ya wuceni baka tashe ba wai Kai wani irin mutu ne please ?

Murmushi yayi tare da girgiza mata kanshi alamun shima Bai sani ba .
harara ta cilla masa Daga inda take  cike da takaicin halinsa.
Sannan  mike ahankali zuwa toile din dake office din..


'Bayan ta idar da salolinta tayi addu'a ta shafa ta nike prayer mat din dayabata tayi salla dashi ta matsa ta daura masa saman table dinsa  ta koma ta zauna fuskarta a hade Dan jin haushinsa .

Xoki dauki abinci kici yace daita .

Azumi nake tabashi amsa adakile alhalin km  babu wani  azumin datakeyi .

Bai km mata magana ba Yacigaba da rubuce rubucesa har zuwa karfe shida saura tana zaune shr shi km yanata aikinsa kmr Bai san da mutun ba duk har 'cikin zuciyarsa yaji bbu dadin rashin cin abincin dabatayi ba ..

Ahankali yaga ta Mike tsaye  ta nufi kofar fita .

Taji sautin muryarsa 'cikin sanyi wani abu kike son akawo miki ?
yace daita batare daya dago Daga abinda yake ba .
 shanyayyun idanunta ta tsura masa wanda Yasa shi dagowa ahankali idanunsu suka sarke 'cikin juna ita tafara janye nata tayi kasa da kanta tana murza hannuwata 'cikin juna .

Sosai tabashi tausayi Dan ya hango gajiya da wunya attare daita .
Bataji motsinsa ba sai hucin numfashinsa taji daf daita a dan razane taja baya ya cilla mata wata uwar harara ,kauda Kai tayi tana mamakin yadda shi kwata kwata abun harara Bai yi masa wuya .

Mutafi ko kin gaji ?

Batare da ta amsa masa ba  tasoma tafiya  .
shi km  yana biye daita abaya.
 har suka  shiga lift suna fitowa ta barshi tayi gaba ta abinta  .
Tsaye ya sameta ajikin motarsa murmushi gefen baki yasakar mata sanda yakaraso Inda take.
Ta yamutsa fuskarta tare da turo masa Dan karamin tsukaken bakinta.
 dariya ya kyalkyale dashi sosai  yana nunata da key .

Bakinta ta bude Dan mamakin abinda yasakashi dariya har  hk .


Nas.. aliyu Muhammad khaliyal ashe rai kanga rai ?
wata matashiyar budurwar ce  fara Sol amman daganin ba tmby kasan ankara da cream din bleaching  ke cewa deeni hk .
yayinda take karasowa gurinsu bbu ko dar ta rungume deeni ajikinta  cike da dokin ganinsa tare da bashi sumba a kirjinsa .

Wayyohhhyyy zuciyar nablah tayi wani irin matsanancin harbawa da  karfi ,  sannan takoma ta dinga bugawa da sauri da sauri .
sai data saki kara a can kasan makoshinta wanda ita kadai taji sautin abinta .
Banda dokawa bbu abinda ZUCIYAR nablah keyi  Dan ganin wannan tashin hankali ganin matar nan taki raba jikinta danashi.
Taji wani irin tutukin haushi ya tsaya mata akirji .
 Yasa a fusace ta janyo matar tayi cilli daita gefe tare da dauketa da wasu mahaukan  mari . muryarta a sarke tace ke wacce irin jaka ce ki  dinga kula da jikin mazan mutane  .
 Dan gabadaya zaki iya fadawa tarkon sharia  ..tana nunata da yatsanta  . sororo deeni yayi yana aika mata da kallon mamaki .. 
Uhmmmm su nablah kennan .
ta juya ahankali  ta jingina da jikin motar .

Hannayeshi zube duka 'cikin aljihun wandonsa yabita da kallo fuskasa dauke da wani irin matsanancin murmushi farinciki .

Nas aliyu wacce wannan wawiyar yarinyar har ta iya taba lafiyar jikina agabanka kana kallo ? 
Wani irin mugun kallo ya sauke mata wanda Yasa tayi saurin ja da baya bashiri tafiya yasoma yi Dan isa idan take da hanzari Tasha gabansa yanzu  Nas aliyu kana kallo aka wulakantani Amman ka kasa daukar mataki alhalin rabonmu da ganin juna over 12 year kennan Ina ta nemanka sai yau Allah yabani sa'a gashi nazo taka Nas Dan Kai Amman da alamun ko murna haduwarmu da juna bakayi ba.
 haba Dan Allah  duk me yakawo hk ?

A kufuke ya Daga mata hannu kibarni naji da riginar da kika cazamin akan wanda nake ciki jidda  Dan  wulakanci ma ki rasa irin tarbar  dazaki min sai ta runguma 'cikin bayyanar jama'a .
Ai Ni wlh nablah tayi min daidai data dauke min ke da mari shasha kawai yasoma kokarin bude motarsa .kamoshi tayi cike da fitsari nablah dake tsaye still tana facing dinsu ta runtse idanunta gam.
 karar saukar  wasu irin mahaukatan  maruka  taji deeni ya sauke mata masu kyau d lfy . Ta sake runtse idanunta.
Banson shirme da shiriritanki Na iskanci leave me alone ..ya fada a fusace tun abaya banyi irin hk dake ba sai yanzu ne danake da lafiyayayun mata har guda biyu .....Ya nuna mata yatsunsa biyu 
take gabanta ya fadi tagane wacce yarinyar data mareta yanzu  matarsa ce  ..  wani irin  kallon rainin hankali nablah da bude idanunta ke masa jin ya ambaci mata biyu ..


Yana gama fadar hkn ya bude motarsa yace ke.....shiga muje.
Nablah  tayi masa banza taki motsawa ballanantana tashiga kmr yadda yabata umarni.
  Bai wani tsaya westing time ba sai ji tayi an dauke  ahankali byn ya  bude mota  side din baya   ya sakata  ya rufe shima yashiga.
Direbansa  ya tada motar .

'Bayan motarsa ta bi  da kallo cike da mamaki da takaicin tallabe da fuskanta .
Wato sai har yanzu  shi yana tamkar yadda tasanshi bai canzawa . atunani ganin yadda ya fito Daga cikin companies dinsa yana murmushi .
Ya canza Daga wance Nas  aliyu din data sani zuwa wani daban.
 tana kallonsa har sanda securities dinsa suka  saka motarsa a tsakiya suna kokari barin haravar ma'aikatan   sannan ta nufi motarta a guje ta fige motar tazo ta wuce shi .
Tabe bakinsa yayi yayinda azuciyarsa yace fitinanniyar banza kawai bbu abinda ta iya sai shashanci .
ban saurareki ba acan baya  sai yanxu .
shasha mara aji kawai  mtsssssss ya furta a bayyane ..

Har suka Kai gida bbu wanda Yayi dan'uwansa mgn Daga nablah har deeni .
sai da motar ta tsaya ne nablah ta yunkura  tana shirin fitowa taji .
 an janyota an maidota ahankali tare da juyo daita suna fuskantar junansu .
cikin kwayar idanunta yake kallo yana hango tsagwaron sonshi da  kishinsa tattare da  tashin hankali  iri iri a  'cikin su .
Muryarsa a kausashe yace as from today Karki kara yi min wannan stupid thing din da kikayi yau .
 Wato  marin wata akaina .Dan Banga abinda ya dameki dani ba ,da km rungumar datayi min .
Ko kina sona  dazaki haushi ?
Tayi shr tare da tsurawa 'cikin idanushi nata kwayar  idanun.
 Dan iskanci har dayi abu kmr wata matata ko zeenat datake matata bazata yi min abinda kikayi ba.
Muryarta cike da rauni tace  ..Amman ta ya'ya Dan tana Yar isaka zata rungumeka a.... shiiiiii gara ma nata akan Na wasu take tagane hannuka me sanda yayi mata idanunta suka cicciko zatayi kuka ..
muryarsa a sanyaye yacigaba da mgn  km wlh kinci darajar 'cikin jikinki ne  if not  ni kadai bansan abinda zan miki ba .wawiya kawai idan ance kina son mutun kice a'a .

dama kince kina  sona ko na dan  taimaka Na aureki ko Dan dararjar kyautar bby da kika min .

taja tsarki tare da bude kofar motar da karfi ta fice ta barshi nan  zaune . murmushi yayi kawai yana shafa sumar kanshi  ahankali ahankali yarinyar kin  makaro fa domin Na dinga kunna wutar kauna kennan acikin zuciyarki .

Wata irin  kulawa da tarairaya ta musamman Deeni yake bawa Nablah  ita kuwa saidai ta Bishi da shanyayyun idanunta akan duk abinda zai mata  domin kwata kwata batajin hidamarsa  gareta yana   birgeta.


Sannu ahankali rayuwa tayi ta tafiyar masu har zuwa  lokaci da watan   haihuwar  nablah tayi 'cikin ya   fito sosai yayi tsini har abun ya Daga hankalin deeni da ummi yayinda  gabadaya tunda watanta haiguwarta ya tsaya take 'cikin fargaba da tunani  kusa  zeenat da deeni har ma da ummi suke bata kulawa da nuna mata  tsansar  soyayya ..wanda kusan yanzu deeni da zeenat kullun suna dakin nablah suna kwantar mata da hankali akan ta kwantar da hankalinta  zata haihuwa lfy.
 wani lokaci ma har kwana suke a dakin su saka deeni a tsakiyarsu .wanda ita nablah sai dai taja gefe can tayi kwanciyarta tabarsu  tana mamakin yadda zeenat gabadaya ta sauya mata yanzu  ba kmr da ba .


Yau kmr koda kullun  deeni yashigo dakin ya iske tsaye a gaban mirrow tana duban yadda cikinta yayi girma sosai ahankali yakaraso Inda take tsaye yana dubanta tsunganawa yayi agabanta tare da manna kunnenshi kan cikinta a tare suka kalli junansu sakamakon motsin bby  suka ji .Ya dage mata gira yana nuna mata 'cikin da yatsansa lumshe shanyayyun idanunta tayi tana Daga kafafunta da kyar Dan son zuwa kan gado ya Mike tsaye jikinshi a sanyaye ya cimmata  tare da riko hannuta 'cikin nashi  ya    zaunar daita  akan gadon  km har lokacin  hannu nablah Na  rike 'cikin nashi yana aikin murzawa .
 ya tsura mata ido ahankali yana kallonta gabadaya ta sauya takoma wata kalar tausayi  Ya saki  hannunta .
 ya kamo  kafafunta ahankali ya maida bisa gado yashiga mammatsa mata sbd wani irin kumburi da sukayi .sosai take jin dadin yadda yake massaging din kafafunta ta Dan yatsuna fuska tana sake lumshe shanyayyun idanunta sorry please.. kiyi hakuri  inshallahu lfy zaki haifi abinda ke cikinki dukkanin mu Muna miki addu'ar kema kina ?
Me kike cewa tayi masa banza tamkar bada ita yake ba .jin motsin turo kofa Yasa ya saki ya zame hannunshi Daga abinda yake mata 
  zeenat ce tashigo tana sheki da daukar hankali ta zauna a gefenshi tana yiwa nablah sannu  .
Dan ita kanta yanzu takan tausayawa yarinyar da 'cikin jikinta  . Murmushi tayi  suka shiga  hirar 'cikin jikin nablah .
ita dai nablah shr tayi  bata ce dasu komai ba  sai dai tana  sauraransu ..wlh Allah nake naga yarinyar ta haihuwa kodan sbd mama ta abuja .
Deeni yana jinta yayi mata shr tacigaba kana ji ko my hrt idan yarinyar idan ta haifi mace fateeha za'a saka mata idan km namiji ne sunan fateehu za'a Sa .
 ya juya inda take zaune tana yauki ya  watsa mata wata uwar harara sbd yagane dalilinta . Nacewa hk Amman ya kanne Yace sbd me  zan saka wannan sunan duk da akwai shi  'cikin alqur'ani me girma?
 .Ni sunan first love dina zan saka idan macece idan km nmj ne sunan abbana zan saka .
  Ta Dan yatsuna fuska tana duban 'cikin jikin nablah kana tace  gsky Bai kamata kasawa  wannan 'cikin sunan iyayenmu ba.
   naga  bby din  ba daga tsatso me kyau suka fito ba ..tsaki yaja yana mata kallon tababbiya yayi  kwanta can kusa da nablah tare da juya mata  baya .
Kwanciya tayi itama abayansa ita dai nablah nata idanune kawai domin kusan tafi su matsuwa ta rabu da 'cikin jikinta .
km ko bbu komai tana jin dadi yadda suke bata kulawa sosai .fiyye da da .

Wata safiyar tafiya gaugawa  takama deeni zuwa abuja kwana biyu zai yi ya dawo Bai so tafiyar ba Amman takama sai shi dine zai je da zai tafi tamkar ya wuce da nablah hk yaji ,sai ummi ta nuna bacin ranta sannan ya wuce ..


'cikin bacci   nablah taji tamkar an tsunguleta ahankali km ta  dinga jin wani irin zazzabi ciwo mara iyaka abayanta da mararrta .
 ta bude idanunta wanda da kyar  tamkar jira ciwon  yake ta farka yace bismilla . Ta sauko Daga kan gado ahankali bata son tayi motsin mai karfi sbd ummi da zeenat su farka  .
Dan yanzu tare suke kwana  tashiga bayi sbd ji datayi kmr tana jin 'bayan gida 

' hk ta dinga shiga toilet yakai Sau goma tana tsugunawa Amman shr yaki fitowa  ta dawo ta kwanta tana jin ciwon yana ratsata ta sake jin cikinta ya cure guri tare da wata irin murdawa ta km  tashi da kyar takoma toilet Daga ba sai ciwo ya tsananta ba .
Ta sake fitowa ta kifa kanta da gado ta jujjuyawa da cicciza lips hannunta daya dafe da mararta 'cikin ummi ta farka da sauri tace nablah yaya ?
Muryarta da kyar tace ummi marata zan mutu ,ummi ta duro da mugun sauri tare da tashin zeenat itama a rude ta Mike tana duban nablah dake murkususu ciwo ummi ta dafa tare da cewa kiyi addu'a nablah inshallahu bazaki mutu ba abu fa kmr wasa ciwon nakuda yakama nablah yi take cicciza lips dinta tana buga kasa tana kiran mutuwa zanyi ummi ki taimakeni wlh mutuwa zanyi  ......





MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗



AYSHA A BAGUDO



    Dedicated to
HAUWA A USMAN
      JIDDARH



Kainuwa association



Page 98



Ki daina furta kalmar mutuwa nan nablah addu'a kawai shine mafuta .
zeenat wacce gabadaya tagama  rudewa sbd ganin halin da nablah take ciki tasoma zariya a dakin tana Kai kawo da  furta kalmar  inna lillahi wa inna ilaihi rajiun.
A rude ummi tace kamamin  ita zeenat mukaita dakin kasa .


Zeenat dake tsintitin acikin dakin takaraso da sauri .
Takai hannuta jikin nablah  ita da ummi zasu kamata.
 nablah tayi saurin  girgiza kanta tana dukan Tear's da tafin hannunta .
kibari akai ki dakin kasa nablah  zai fi sauki akan nan din. 

uhmmmm ummi uhmmmm takasa cewa komai sai uhmmmm da  murkususu ciwo .
take wani irin  gumi me zafi shiga  tsaftsafo mata  takoina jikinta.
  Jikinta ke wani irin  kirma Dan azabar radadin ciwo.
 ta dinga  cizan lip's dinta da karfi tsabar tashin hankali .
 kuka take da idanunta tana kokarin kamo hannu ummi 'aiko Allah yabata sa'a  ta damke hannun ummi  'cikin nata da karfi  tsiya .
nishi take hankali sbd numfashinta dake sizing yana dawo .
 zeenat dibo min  ruwa a cup kikawo nayi mata addu'a.

 hk zeenat ta fita jikinta Na rawa biyu biyu ta dinga taka step taje takawo  ummi ruwa acikin cup .

ummi takarba  tayi mata addu'a tabawa nablah tasha Amman still ciwon Bai ragu ba .
Sai abunda ya Karu Na naxaba  wani irin murdawa cikin nata yayi da karfi  aiko ta saki wata irin razananniyar kara wanda Yasa zeenat fashewa  da wani irin matsanancin kuka jikinta yacigaba da rawa .
Tana kuka tace  ummi Dan girma Allah mukai yarinyar nan  asibiti karfa Yar mutane ta mace mana mushiga uku Daga taimako ..

bazata mutu ba inshallahu .

Duk  wani taimakon da ummi tasan anayiwa me nakuda tayiwa nablah shi  Amman Sam bbu wata  alamun zuwan bby wanda hkn ya nuna ummi cewa doguwar nakuda gareta.
Daman km dayawa anasamun hk wani zaga alokacin rainon ciki basashan wahala sai gurin haihuwa wasu km tun gurin daukar 'cikin suke shan wahala har zuwa haihuwa wasu ma kwata kwata basu San da wannan matsalar ba zasuyi renon ciki lafiya Haka ma haihuwar 'cikin sauki zasuyi ta .

 kuka nablah keyi tana kiran mutuwa zatayi itama zeenat kuka take tana cewa ummi kinga abinda nake gudu da  jin tsoro ko........
 ummi kalli yadda yarinyar mutane ke shan wahala kalli yadda numfashinta keyi ni dai wlh tsoro nake ji wani abu yasameta 'cikin wani irin kuka zeenat takarashe  zancenta da wallahi ummi  bazan iya haihuwa ba ban zan iya ba wallahi Na hakura da haihuwar gabadaya .

'Cikin fushi ummi ta buga mata tsawa Dan Allah kiyiwa mutane shr duk kinbi kin cikawa mutane kunne ba'a haihuwa ke uwarki ta  haifeki.
 zakizo ki  ishi  mutane da surutan banza da wofi shasha kawai 'aiko kowace da yadda haihuwa take zuwa mata  kamamin ita ni mukaita kasa .. .

Haka suka  kama nablah zuwa  dakin kasa ummi ta kwantar daita tunda tun dazu a tsugunne take a sama har garin Allah yawaye ciwo yaki ci yaki cinyewa banda murkususu ciwo bbu abinda nablah keyi da ikin kiran sunan mamata da mutuwa zatayi .
Wani daren yashigo nablah Na kan  abu daya , tayi firifiri daita tayi mugun fita haiyacinta  iya jigatuwa tayi shi  har tasoma gajiya tana janyo numfashi da kyar tana fitawar da kyar km still  ummi da zeenat Na tsaye akanta  Amman haihuwa shr.
Gashi km  sosai nablah ke  jin wata irin azababen azaba har tasoma fezgar gashin kanta ....
 ta daina gane suwaye akanta ta dawo bbu karfin komai ajikinta bakinta ya bushe sannan Yayi fari fat..  idanunta suka bushe .
 hawayen dake idanunta suka kafe suka bar xuba  bakinta ne kawai ke motsin ahankali tana karanto duk wata addu'ar tada iya ji taje da zata iya data fizge 'cikin jikinta ta huta da radadin azabar ciwon datake ji ...

Daren ranar bbu shiri ummi ta da zeenat suka cucibi nablah tamkar wata Yar bby suka sakata  abayan mota batare da sanin kowa  ummi ta zauna baya tare da nablah  zeenat ta shiga gaban mota ta  tayiwa motar key sai wani asibiti kudi  me zaman kanshi da shegen kyau.

  suna xuwa hospital doctor yana  dubata yace haihuwa ce Amman km da saura Dan yanzu ma tasoma nakudar domin har lokacin jikin nablah Bai bude.
 ba jin Haka Yasa zeenat sadaukarwa da mutuwa zatayi duk wannan azabar data kwana tana Sha .
Ace km yanzu taka fara nukuda  ita kam tunda take arayuwarta   bata taba ganin irin ciwon nan ba.
 shi Yasa tasawa ranta ta nablah   takare ..


 Tun daren jiya jikin mahaifiyar nablah yake a tashe takasa runtsawa sakamakon gabanta  daketa aikin  faduwa tamkar ana buga mata guduma wanda batasan dalilin faruwar Hakan ba  Dan Haka ta Mike jikinta a sanyaye Daga kwanciyar datayi tazo ta dauki buta tayi alwala tashiga jero nafiloli da addu'oi neman tsari .


Shi can bangaren   deeni tun daren jiya jikinshi yabashi gidanshi bbu lafiya sbd mafarkin barkatai daya kwanayi   km duk akan nablah ne Dan Haka tun da asuba yashiga   neman layin zeenat dana ummi Amman shr bbu wanda ya dauka acikinsu ,Bai hakura ba Yacigaba da neman layin  Daga karshe ma daya Kira yaji wayar akashe .
 nan fa hankalin shi yayi mugun dagawa yakasa yin komai sannan Kuma rasa jin dadin zuciyarsa kawai yaga gara ya dawo gida  .batare da bata lokaci ba yabada Umarni siyan Tiket kawai  yana shirya jikinshi yana neman layin  ummi dana  zeenat Amman har lokaci shr swchoff ake ce masa . Wani tashin hankali ma sai jirginsu ya  sauka a Lagos gabansa ya tsananta faduwa zuciyarsa Na tsinkewa Allah Allah yake yaganshi agida kawai ..


Yana  shigowa 'cikin gidan da zeenat yasoma cin karo ya sauke ajiyar zuciya da karfi yana dubanta   tana sauri tana hada kayan  bby Na haihuwa Dan jiya daddare basu tafi da kayan haihuwa ba sbd a rude suke. 
 tana ganinsa duk ta dabirce tasoma kuka  muryasa Na rawa yace Ina nablah da ummi 'cikin sharar hawaye tace suna hospital prioucion s .
Tun jiya batada lfy amman doctor yace nakuda ce ....inna lillahi wa inna ilaihi rajiun yana tafiya yana furta hakan acikin zuciyarsa  atare suka shiga mota gabadayansu a rude suke  .

sanda ya iso asibiti nablah ta jigata iya jigatuwa bbu kowa agurinta  sai nurse nurse ne tare daita.
 deeni ko gaisawa bai tsaya yi  da ummi ba.

Hankalinsa a matukar tashe  yace Ina nablah  take  ?
Suka nuna mishi dakin haihuwa Kai tsaye yashige 'cikin labour' room din wata doctor ce tace please sir kayi hakuri ka Dan jiramu awaje hankalinsa a matukar tashe yace madam Dan girma Allah kiyi hakuri nima Ina son naga matata .
Ai yana dora idanunshi akanta Bai san sanda hawaye suka shiga siyayo masa .
ya mannata   ajikinshi ya rungumeta yana kuka da  aikin jero mata sannu bbu kaukautawa addu'a kawai yake mata yana zubda hawayen tausayinta ya dinga jin daana kar bar wa mutun nakuda daya karbarma ta huta tun daren jiya ake abu daya har yanzu .  tamkar shi nakudar take jira ta tashi zanga zanga  Amman haihuwa shr bbu labari .

Hankali likitoci Suma  yayi matukar  tashi sosai tun daren jiya suke tsaye akanta , zeenat kuwa a ranta tace tun dai shekaranjiya Dan dai bamu gaya muku gsky  bane .
.. likitoci suka tabbatarwa deeni zata haihu zuwa karfe goma shabiyu  ranar Amman gashi har yanzu shr Ga dai  'cikin Na motsa alamun bby 'cikin  Na raye.
Sosai  hankalin deeni yakai karshe gurin tashi tsigar jikinshi har tashi suke tsabar tausayin yarinyar .
ganin har  biyu  tayi ta wuce bbu sauki sai wahala datake Sha Yasa Shi  cewa doctors din suyi mata aiki su cire mata abinda yake 'cikin ta huta .
 tunda sauran karfinta yazamo yanzu ko nishin bata iyawa sai shanyayyun idanunta datake jujjuyawa wal wal dasu .

Hudu daidai aka yi mata shirin aiki sai addu'a ummi keyi ita ko zeenat kuka take sosai har da shesheka .


A dakin tiyata sabon ciwo yatashi 'cikin zafi zafi ta dinga jin bayanta tamkar ana Sara mata da ada jikinta wani irin  rawa  har gadon datake kwance akai  shima sheking yake .iya wahala nablah tasha sai dai Allah sauketa lafiya ..

Deeni  rike da hanuta yana kuka  yana mata addu'ar .Shi yanzu bata 'cikin jikinta yake ba ,ita din yafi bukata .domin duk yadda yakai da son haihuwa sai daya ji ta fita aranshi tausayinta da kaunarta ke zariya a gangar jikinshi.
   wani irin uban nishi tayi da karfi  sai Ga kan yaro ya fito fit .
Jim kadan wani kadan wani  yaron ya sake fitowa sororo deeni yayi yana kuka yana kallon ikon Allah Wani sabon kukan farinciki ya kufce masa ya rike hannuta gam yaki saki sai sumar kanta yake shafa ahankali yana mata sannu  can km  sai Ga wani  sabon ciwo  nakuda   take doctors din  suka gane Yan uku ne suka taimaka mata aka fiddota  agalabaice duk tafisu shan wahala Dan ko kuka batayi.
 nan suka fita da yaran duka uku Dan gyarasu ummi tayi matukar farinciki da saukarta lfy  an shirya yara ummi nata murna  .


Shi kam deeni bbu wanda yake son Gani kmr nablah doctors sukace masa kada ya damu ana kimtsa ta ne suka mata allurar bacci sannan suka kaita dakin hutu bacci take sosai Dan batasan irin hidimar da'akeyi daita ba .koda zeenat taga bbys sai kirjinta ya buga sbd tsabar kamanin da suke da deeni sak sak komai Nasu Na deeni har ma gara ta mace ta dauko kamanin uwarta sai sai farin Na deeni ta debo .'aiko take tasoma yiwa ummi mitar kamanin yaran .Kai zeenat wlh Kin fiyye matsala Wani kama yaran nan sukayi da deeni kawai idanunki ke ganin hk Amman ni Banga hk ba ..


Tun asibitin ummi ta dinga kiran dangi tana sheda musu zeenat ta haihu sauka lafiya tasamu yan uku .

Sannan ta tilasawa doctor kan sai ya sallamesu a ranar doctor yace a'a sbd uwar tana bukatar hutu .ummi tace bbu damuwa abar uwar anan zasu wace da yaran doctor yacika da mamaki Amman dayaga ai sune suka kawota yace shikennan .

Suna komawa gida nan dangi sukayi matuka murna da farinciki saukarta lfy kowa sai albarkaci bakinsa yake fada Kai Kai zeenat gsky kin iya haihuwa  tamkar bake ce kika haifi yaran nan ba. 
Kai Masha Allah Yara sak ubansu takoina deeni yaran nan  suka dauko  ita dai sai dai tayi murmushi  kawai tana duban yaran dake kwance masu  tsantsar kamanin da mijinta tun asibitin gabanta ke faduwa sbd tsabar kamanin da yaran ke yi da deeni ..

ita kam nablah tana can hospital batasan hidimar da'ake da bbys dinta a gida  ba.
 Dan  batama San yan uku ta haifa ba .


 Tana  farkawa idanunta suka sauka akan  deeni ya taso da sauri sannu nablah kin tashi ?
Kallonsa kurum tayi .
Ta kauda fuskarta gefe ya  wanke mata baki 'cikin wani dan karamin kwanan siliva tare da tayarda ita zaune yaje ya ajiye kwano ya hado mata tea me kwari yazo yana bata da kanshi ..idanunta  kawai ta tsura masa tana kallonsa tana tea din .
 ahankali ,shi kanshi yagane mgn take son yi .. 'cikin sanyi jiki  ta kauda bakinta Daga cup din . alamun takoshi .
Ya ajiye cup ya dawo gefenta ya zauna ya kamo tafin hannunta 'cikin nashi yana mammatsa mata  magana take son yi Amman bakinta Yayi mata nauyi ..

Ya kafe da rikitattun idanunshi gabadaya  tayi wata irin muguwar rama acikin kwana biyn din datayi tana nakuda muryarsa a sanyaye yace kina son wani abu ne akawo miki ?
Ta girgiza masa kanta. ahankali .

Ok kimin mgn mana  naji muryarki ko wani guri Na miki ciwo ne,?
Nan ma  ta girgiza masa kanta ..can  km muryarta a raunane tace Ina abinda Na haifa ?

 Gabansa yayi Wani irin tsalle Dan baiyi tunanin zata tambayi abinda ta haifa ba .take 
Zuciyarsa tashiga harbawa da sauri da sauri muryarsa can kasa kasa yace  Suna gida gurinsu ummi .
ta runtse shanyayyun idanunta da suka sake shanyewa tsabar wahala dataci .
 yabita da wani irin kallo tunhuma  Haka kawai yaji gabansa Nacigaba da dukan uku uku sautin muryarta ya sake ji nima Ina son zuwa gida .yace Ok bari nasamu doctor . Ya Mike tsaye ya sumbaci goshinta kana ya fice da sauri yana waigenta .


Byn deen  yasamu doctor yayi masa bayanin ko za'a iya sallamarsu bbu wata matsala doctor yace bbu komai ai zasu iya wucewa ..


Sai yamma liss suka shiga estate din ta kofar baya deeni yashiga daita sbd taron mutane dake 'cike da gidan.
 Yan taya murna  bai samu damar kaita dakinta ba .
 ya nufi dakinsa na kasa  daita zuwa lokacin da jama zasu tafi ..



 misalin karfe tara Na daren deeni  yaje gadon kwanciyar yaran ya dauko mace da namiji ya rungume yaran yana jin matukar son yaran nabin jiki da jinin jikinshi yana mamaye ruhinsa da zuciyarsa .. ummi ta dauko daya suka nufi dakin da nablah take .
Da sallama suka  shigo dakin nablah .
 suka zauna tare da saka nablah a tsakiyarsu  muryar deeni cike da farinciki yace nablah kinga arzikin da Allah Ya ...wani irin  kallo ummi tayi masa yakasa karasa abin zaice  take km yagane ashe  yaso ya kwabsa ne..kwantar da yaran sukayi akan bed .wayanda suka Sha wasu haddun kaya sanyi  masu shegen kyau da tsada da daukar hankalin farare tas tas dasu tamkar ya'yan turawa ,sosai ta tsurawa bbys din ido tana masu Wani irin.kallo kamanin yaran take kallo 'cikin tashin hankali taki dauke idanunta akansu yanzu itace ta haifi wayan nan kyawawan bbys din masu kyawun kyau hk ganin yadda yake kallon baby's din Yasa ummi tashi ta fice shima can deeni ya Mike tsaye yana amsa wayar Yan taya Shi murna ya bar dakin .

Dakin ya saura Daga nablah sai bbys dinta da suke kwance reras akan gado  abin sha'awa. kallon yaran tacigaba tana jin Wani irin sanyi Na bin jikinta  take km taji Wani irin mugun son yaran yashiga ranta tare da ratsa kowane shashi Na gangar jikinta tundaga tafin kafafunta har 'cikin kwalkwaluwarta nan take taji idan dukiya zata taru bazata iya rabuwa da yaranta ba ,daidai da daya Daga cikinsu bazata iya bayarwa ba ballanantana dukansu kawai ta fashe da wani irin matsanancin kuka tare da rungume yaranta tasoma sabatu , wallahi tallahi bazan iya rabuwa daku ba yarana  Ina  sonku ina kaunarku km zan rayu daku.
 koda kuwa duniya zatakini .
 ta zageni akanku Ina sonku takarasa fadar hkn tana sakin Wani irin kuka me cin rai ahankali take cigaba da kallon baby's dinta hawayenta Na tsaya ahankali  tasa hannuta ta goge tana sakin ajiyar zuciya 'ta daura mazan duka a saman cinyoyinta mace km ta daurata akafadarta tana jin Wani irin dadi mara misaltuwa aranta tare da jin duk abinda zai faru sai sai ya rafu Amman bazata rabuwa dasu ba ....



Uhmmmm nah wa oooooooooo 







MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO 


      Dedicated to
HAUWA A USMAN
        JIDDARH


Page 99



'Cikin wannan halin datake  ciki  deeni ya km shigowa dakin fasukarsa dauke da wani irin maganadisun murmushi .ta koina ka kalleshi kasan yana 'cikin tsantsar farinciki da murna samun wayan nan kyawawan bbys din masu matukar kyawun da daukar hankali .

Ahankali yakarasa inda take zaune rungume da ya'yanta duka .
 ya tsura mata rikitattun idanunshi yana kallonta  da jin Wani irin mugun sonta da yaran yana tasoma masa .
Yanayin daya ganta ciki  yasashi shan jinin jikinshi .
 zama yayi kusa daita sosai  har cinyoyinsu Na gugar juna ya amshi ta mace Daga hannuta  ya daurata saman cinyarsa yana kallonta yana kallon fuskarta nablah dayaga gabadaya ta canza ta dawo wata iri . muryarsa a sanyaye ya Kira sunanta nabeelah ....bata amsa masa  ba sai ma juyo da tayi inda yake zaune  tayi masa kallon second  2 kana ta dauke idanunta Daga kanshi.
 ta maidasu  kan yaranta dake cinyarta .
 ,sautin muryarsa taji a matukar sanyaye fiyye da farkon shigowarsa dakin  .. nablah kinga kyautar da Allah Yayi mana ko?

Adakike ta amsa masa da uhmmmm . gsky kin iya haihuwa.
 arayuwata bantaba ganin macce data iya haihuwa  kmr ki ba .
Gsky kinyi kokari sosai . nan ma  tayi masa banza ta sharesa gabadaya ma  taki cewa dashi  komai .
yanzu mekike bukata akawo miki ?
muryarta can kasa kasa tace babu tare da kamo lips dinta Na kasa tana cizawa ahankali ahankali tana Dan jijjiga kafarta daya akasa .

Gabadaya deeni ya rude yarasa abinda ke masa dadi tunda ta haihu yarasa gane kanta sai wani shashsharesa take tana basar dashi  da ciccin magani wanda yarasa dalilinta nayin hk . runtse rikitattun idanunshi Yayi sosai .
ciki Mutuwar jiki  sakamakon tuno da kyawawan bbys dinsu data haifar masa masu tsananin kamadashi  km  yake tare dasu ahalin yanzu.
To  me zai dameshi da duk abinda zatayi arayuwa tagama masa komai tunda tabashi abinda yafi so da kauna a rayuwarsa ta duniya . sumbar bby  girl din  yayi  yana jin wata irin natsuwa ta daban tana ratsa kowane shashi Na gangar jikinshi sosai yake son yaransa Amman yafi jin kaunar mace fiyye da sauran acikin zuciyarsa  .
Jikinasa cike da rauni soyayyarta  yakamo tafin hannuta  'cikin nashi  yasoma murzawa ahankali ahankali 'hade  da  shaukin kaunarta yace meke damunki nablah naga duk kinyi wani iri hk ?

Ki sanar da deeni  abinda ke damunki banason ganinki 'cikin wannan  damuwa da tashin hankalin  please ...
yanzu kin zama wata bangare Na rayuwata da farincikina gabadaya sbd wannan kyawawan  bbys din dakika bani ..

Kimin abinda wata matar  takasa jura ta min arayuwa  .
Kin bani kyautarsu alokacin danafi bukata . akan wayan nan yaran bbu abinda bazan iya miki Shi ba , matukar Bai shafi addanina ba .
ban ji  dadin yadda naganki ba yanzu.
 idan akwai wani abu dake damun zuciyarki ki fito ki sanar min.
 ni km nayi miki alkwarin zan yi miki maganinsa kowani iri ne .. yakarasa fadar hk yana matse laulausar tafin hannunta 'cikin nashi yana jin yadda sonta ke fizgar zuciyarsa gareta ..
 

So take tayi mgn Amman maganar taki fitowa sakamakon wani yanayi data tsinci kanta ciki ,ita fa bbu abinda ke damunta s halin yanzu wanda ya wuce son rabata da ya'ya za'a yi.
 ta lumshe shanyayyun idanunta kana ta budesu ahankali ta zubesu 'cikin nasa still takasa tabuka komai shima lumshe rikitattun idanunshi Yayi sannan yace Ok kingama ganin yaran zan maidasu kasa sbd masu zuwa ganin bby ..
take zuciyarta ta buga da matsanancin karfi har sai data taji zubowar  gudan jini Daga kasanta . afrigice ta zare hannuta 'cikin nashi tana kallonsa  a tsorace bakinta da alamun son yin mgn .
kanshi ya girgiza mata yana kokarin mikewa tsaye .
 

Muryarta cike da inn inna ta fizgo mgn da kyar  tace nifa.. nifa ..ban bada ya' yana.

 what ? Bai San sanda yakoma ya zauna ba .yana kallonta da matukar mamaki .

Wallahi wallahi deeni idan duniya zata taru akaina idan sama da kasa zata hade idan za'a yi ruwan jini deeni bazan iya bada ya'ya nan ba.
 kai ni daya Daga cikinsu ma bazan iya bayarwa ba ballanantana duka .
deeni koda duniya zata kini ciki  kuwa har da mahaifana dakai deeni koda zan dawo kwanan akan  bola Ina tsince tsince in ciyar da kaina da ya'ya Na ,bazan iya bada ya'yan nan ba wlh. duk da Allah yasani bansan waye mahaifinsu ba Amman Ina ji ajikina mahaifinsu ba wulakantacce mutun bane duba Ga yanayin ya'ya.
 take gaban deeni ya fadi rassss  rassss rassss yashiga bugawa da karfi karfi .zuciyarsa tashiga   tsalle da kururuwa neman dauki da agaji .

muryarta ahankali 'cikin sanyi jiki tacigaba da mgn tunda Na kalli fuskar ya'yan nan narasa meyasa naji Ina mugun kaunarsa wanda bansan dalili ba narasa meyasa tun sanda Na daura idanuna akansu kawai naji bazan iya rabuwa dasu ba .
takarasa mgnr tana fashe masa da wani irin matsanancin kuka me cin rai da Daga hankalin .

 Jikinta Na matsanancin rawa  ta kwantar da yaran daya byn daya akan gadon.
 da kyar  ta sauko Daga kan gadon datake   ta zube  masa a gabansa  ta dinga kuka Dan Allah deeni karku rabani da ya'yana Ina son su ko zan rasa raina bazan iya rayuwa bbu su ba.
Wallahi  bazan iya rabuwa da yarana ba   aduk yanayin da suke Wallahi azim bazan iya rayuwa bbu su ba ni Ina son su a Haka .
 kuka take sosai tana rokonsa akan kada surabata da yayanta .


Gabadaya jikin deeni yayi Wani irin mugun tsayi km  ilahirin jikinshi suka  mace murus yarasa abinda ke masa dadi a zuciyarsa .
 Ga koshi Ga kwana yunwa.
 hankalinsa ya Kai  kololuwar gurin tashi gabadaya yarasa abinda yakamata Yayi ahalin dayake ciki .
 kukan  farinciki zai yi ko haushinta zai ji Na sabon salon iskanci data tsiro  ...  sai kallon bbys din yake yana kallonta tsugunne agabansa tana risgar kuka  tana rokonsa . 
shima  ajiye bby' girl din  dake  hannunshi yayi .
ya tsura mata rikitattun  idanunshi da kyau  yana cigaba da kallonta hade da nazarinta wato dai da gaske mutuwar son yaran take kmr yadda shima yake matsanancin son su .
duk Shi a tunaninsa yafita son su da bukartasu arayuwarsa ..
a zuciyarsa yaji wani irin matsanancin sanyi ya ratsashi tundaga tafin kafafunshi zuwa kwanyarsa , kennan idan yace zai isar da sakon zuciyarsa gareta bazai Sha wata wahalar shawo kanta ba adalilin wayan nan yaran  ..

take  km burin  mahaifiyarsa ya fado masa  .
yaya zaiyi da ummi wace oready  tagama gaya duniya da shelar cewa  zeenat ta haihu ?
..yaya zata ji idan tasamu wannan mummunar labarin ?

 Kuka take Sosai ta rike kafafunshi gam deeni kayi hakuri nasan ban kyauta ba akan abinda nayi Amman  Ina son ya'yana  duk da  kasancewarsu shegu  wlh  ba zan iya kyauta dasu ba kmr yadda nayi maka.. shiiiiii Karki kara kiran ya'ya Na da  she.. shegu ni..Ni..ne ...sai km yayi shr ya datse harshensa da hakorinsa gam  jikinsa Na wani irin matsanancin  rawa idanunta dake cike da ruwan hawaye ta xuba masa tana kallon bakinsa .. zuciyarsa gabadaya gaskiya take son  fada mata Dan ta daina danganta ya' yansa da kalmar shegu   Amman yana jin matsanancin tsoron tashin hankali dazata shiga fiyye da wanda take ciki ahalin  yanzu.. Shi dai yasan  xuwa yanzu  ya Mika duk  rayuwarsa gareta  sbd kaunar dayake mata ita da yayanta ...

'Cikin wannan halin zeenat da ummi suka shigo dakin atare turus sukayi ganin nablah durkushe gaban deeni rike da kafafunsa  tana risgar  kuka da iyakacin karfinta .

Da sauri suka karasa garesu suna tmbyr deeni lafiya  meke faruwa ?

 'cikin rawar jiki nablah ta Mike tsaye ta nufi gurin ummi tana layi tana  kuka muryarta cike da kuka tace Dan girma Allah ummi ku  min rai wallahi bazan iya bada ya'yan nan ba  kumin abun alkhari nasani km Na gode da karamcinku gareni Amman kada Ku rabani da ya'yana .....

A zubure zeenat  ta dafe kirjinta tare da cewa what ke kina da hankali kuwa ?
 
Ke wace irin mahaukaciya  ce yaza'a yi kice bazaki iya bada ya'yan ba .....
take nablah ta fuskanceta sosai  a fusace tace gaki nan babbar mahaukacirya da  batasan abinda takeyi ba  da sanin ciwon Kanta  ba.
 ke kinsan zafin haihuwa ne?

 ko kinsa zafi ya'ya ke kinsa wahalar dana Sha akan wayan nan ya'ya?

 to nace bazan bayar ba km idan sama da kasa zata hade bazan bada ya'ya nan ba ke ni akan ya'yan nan banki duniya takini  ba ciki km har da iyayena wallahi wallahi dana bada ya'yan nan gara narasa rayuwata gabadaya.
 ke indai kika ga nabada ya'ya nan sai dai idan bana numfashi a doron kasa .

rassss rassss gaban ummi yayi wani irin matsanancin bugawa da karfi ..Hk ma deeni gabansa ya km bugawa  zuciyarsa tacigaba da rawar datake tun kafin shigiwarsu ummi ..

Zeenat tace Wallahi wallahi  baki isa ba nablah kinyi kadan km  sai kin bada yaran nan tunda tun farko ke kika  amince km kinyi alkawarin  zaki bada su  muryar zeenat  Na rawa takarasa fadar hk  .


Wani irin kallon tababbiya nablah tayi mata sannan muryarta Na rawa rawa  tace to..to.. yanzu nafasa badasu sbd nima  Ina son abuna dama can danayi kyautar su bansan zafinsu bane yanzu kuwa sai dai nabawa wasu labari .
Baki isa ba wallahi sai  dai kuwa ki rasa ran naki dakike ikirarin rasawa akansu Amman kmr kin bada ya'ya kingama ..  Ok zanga wanda ya isa dazai  rabani da ya'yana .. 

ke nifa nafiki zafin Kai da rashin mutunci akan yaran nan zan iya miki duk abinda yazo zuciyata inji cewa zeenat .

baki  nablah ta saki tana kallon zeenat da mamakinta  hakan yabawa zeenat damar cigaba da  maimaita kalmar dole abasu yara tunda tun farko an rigada anshirya hk  da surutai kala kala   tayi kan baby's   cike takama  zata dauka nablah tayi kuka kura ta dire gabanta cike da maseefa tace ubanwa  yabaki damar taba min yara ?

Ubanki  da km uban  Yayi miki ciki  a gidan nan .
a fusace ummi tashiga tsakaninsu tana jan zeenat baya.
 ummi ta dinga mamakin abinda nablah tayi duk da tasan Yar tatace da fadan rashin gsky Amman batayi tunani nablah zata  iyawa zeenat rashin kunya da tsiwa Haka ba  .


Ni zaki kawo danyen Kai da ranshi kunya ta fadi Haka tana nuna nablah da yatsan hannuta  Dan girma Allah ummi ki matsa Na canzawa wannan Yar iskar  yarinyar halitata dama Ina da ciki daita Ina takaici ta wlh.

 kallon kasa da sama nablah ke bin zeenat dashi ahankali wanda ke nuna alamun bata isa ba .

 Kina takaicina ai sai kixo ki kasheni ki huta  banda mijinki daya nace akan zai taimakamin  da tuni ban  san inda dare Yayi min .
zeenat tayi sororo tabi deeni da wani irin kallo tana jiran taji yakarya mgnr yarinyar .
 Amman taji Yayi shr yana binsu da idanu kawai .
  my hrt ummi kuna jin fa abinda yar iskar  yarinyar kecewa ko.
 ummi tace munji  ai zance nata duk shirme ne bakya ganin duk abinda take bata 'cikin haiyacinta tasoma jijjga zeenat din  kiyi shiru mu yanzu bawannan shirme bane agabanmu yadda yara zasu zama naki shi kawai  .kiyi shr ki  natsu asan abin yi .


nablah najin   Haka ta buga kafarta daya   a kasa ta nufi gurin da bbys dinta suke kwance  gadan gadan  tasa wani irin mahaukatan  kuka  tana cewa  wllahi tallahi ban bada ya'ya Na .
 ya'yan guda uku ta rungumesu ajikinta tana  sake sakin  wani irin matsanancin kuka  me ban tausayi da taba zuciyar ma aboci  saurare ..
 
Tashin hankali wanda ba'a saka masa ranar zuwa .
zaune kawai deeni yake yana kallon    sarautar Allah.
Yana mamakin  daman zafin kan yarinyar nan yakai hk Shi Bai sani ba ....abu kmr a film yarinya tana kokarin birkice musu da dagula musu lissafi.
  hatta ummi tsaye kawai take sake da baki tana kallon ikon Allah da yadda nablah ke nuna reaction dinta akan bby din da batasan taka maimain wanda yayi ma 'cikin su ba .
,to wannan  idan km tasan ya'yan deeni ne km  jikokinta   me zai faru ? Tayi wa kanta tmbyr tana cigaba da kallon nablah rungume da yara tana kuka . 
tamkar wata zautaucciya .
 Gabadaya Daga deeni har ummi kasa tabuka komai suka yi sai idanu  da suke bin nablah dashi ... 

Wani irin  tausayinta ne me gyaraye da tsansar soyayyarta   ke sake huda kirjinsa da  mamaye gangar jikinshi da zuciyarsa .
alahakikanin gaskiya Bai taba tunani yarinyar zata canza salo irin Haka  ba.bai dauka zata so ya'yan da ta dinga hauka akan acire mata su ba .
Wani irin  gumi ne me zafi ya shiga   tsaftsafo masa ta koina ajikinshi yazama tamkar wani mutun mutumi a zaune yana kallon nablah kwakwume da bbys ajikinta duk tayi firi firi tafita haiyacinta   .


Take zeenat ta dinga jin zuciyarta tamkar zata fashe ta tarwatse kan   takaicin nablah.
 ita kanta wani irin mugu mugun son bbys din ne yashiga ranta tun sanda suka zo duniya  ta daura idanunta akansu taji sun shiga ranta.
 duk da duk  sanda ta kallesu gabanta Na tsananta faduwa akan tsananin  kamanin da yaran keyi da mijinta.
 Dan ko mahaukaci ya kalli yaran yasan kamarsu daya da deeni babu wani bambanci launi ko sura  daidai da  yatsun kafafun yaran dana hannusu  irin na deeni  ne sak  .
bakinsu da  hanci komai Nasu  irin nasa ne .
 sosai take taji wani irin  mugun  son yara Na sake  ratsata  har 'cikin zuciyarta  tana jin bazata iya rayuwa bbu su ba ....


 Amman Ga tashin hankali da uwarsu tazo mata  dashi wanda take jin  bazata iya  jurawa ba .. Amman duk da Haka durkusawa wada ....
gabadayan ilahirin jikinta yayi mugun sanyi jikinta banda kirma bbu abinda yake tsabar tsoro da rudani .
Ga mamaki deeni da ummi har nablah.
 suka Ga zeenat ta zube a gaban nablah tana kuka tare da  rike kafafunta tana rokonta  Dan girma Allah nablah ki rufa min asiri kada ki min Haka  wannan   ita kadai ce damata da zata min katanga tare da yi min shingi da kishiya arayuwa ta.
  Dan girma  Allah kibar min yaran  wallahi nafiki bukatarsu  zan kular miki  dasu fiyye da tunaninki .
zan basu gatan  duk duniyar nan .
zan kaunace su fiyye da ke kanki da kika kawo su duniya ..
Dan Allah kibar min su Karki fasa kyautar mana dasu kmr yadda kikace  ummi Dan Allah kisa baki tabar min su .. my hrt kaima kayi shr kaki cewa komai please kuyi mata mgn kozataji  nafita bukatarsu takarasa mgnr tana fashewa da wani irin matsanancin kuka.

kuka zeenat take tana rokon nablah akan tabar mata  yaran ... ahankalin deeni ya Mike tsaye Daga zaune dayake yaje har gaban nablah ya mika mata  hannunwansa duka  alamun tabashi yaran Amman taki .

Yayi yayi tabashi yayan taki sai ma matsawa da tayi Daga kusa dashi tana jijiga yaran da zuwa yanzu hayaniyarsu tasoma tayar dasu .


da kyar  deeni ya shawo kanta ta hanyar ce mata bbu inda zanje da yaran nan  nablah  zan kwantar dasu ne kawai  ko bakiga yadda kika matsesu ba ajikinki ba kar wani abu yasamesu  .
sannan ta Mika masa mace da Na namiji zuciyarta cike da tsoro da fargaba yaje ya kwantar dasu .
ya dawo ya amshi dayan ma ya kwantar dashi kusa da yan'uwasa  kana ya janyo hannuta ciki sanyi jiki Ya zaunar daita akan gadonta ya tsura mata rikitattun idanunshi yana kare mata kallon  tsanake .
sannan  yasoma magana 'cikin sanyi rai da zuciya... 




MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO 


      Dedicated to
HAUWA A USMAN
      JIDDARH



Page 100



Nablah ki natsu ki dawo 'cikin haiyacinki muyi mgn 'cikin tsanake da fahimtar juna da farko kin amince da zaki bamu abinda zaki haifa wanda har muka sanyawa rayuwarmu son abinda ke cikinki.
 " to meyyasa yanzu kika canza ra'ayinki alhalin duniya tagama sannin wayan nan ya'yan ya'yanmu ne nida matata ?

Ilahirin jikinta da bakinta wara suke gurin cewa  nidai  kawai ji nake a halin yanzu bazan iya kyautar dasu ba.
. saboda kinsha wahala gurin haihuwarsu shiyasa bazaki iya badasu ko me ?
 Kai tsaye taji ya 'aiko mata da tmbyr datasa ta tsura masa shanyayyun idanunta da suke cike da ruwan hawaye taki ce masa komai sai kallonsa kawai  take ..
 "jikin deeni Yayi sanyi sosai sbd ganin yadda  yanayinta ya sauya . yarasa ta inda zai bullo mata.
 ta  kalleshi sosai Yayi matukar bata tausayi  Amman har 'cikin zuciyarta bata jin zata amince tabashi yayanta kyauta .
"  tacigaba da dubansa can km yace kina jina ko kiyi hakuri kibar mana yaran nan nida matata nayi miki alkwarin zan raba tarin dukiya biyu Na baki rabbi akansu kije kicigaba da rayuwarki .
Sosai ta sake  tsareshi da shanyayyun idanunta tamkar zata cinyeshi  tana mishi wani irin kallon rainin wayo.
 hakan Yasa gabansa cigaba  da faduwar dayake .
 shima kallonta yake yana jira Daga gareta tare da  mamakin canzawarta  a'cikin zuciyarsa .
 idan wani ya fada masa zata rikide ta dawo masa Haka wallahi zai rantse da Allah  yace karya ne ranta a matukar bace tace  Kai dukiya ta dama km take rudarka har kake jin Kai wani ne .
 Amman ni bbu abinda za'a bani a duniyar nan da zai Saka Na iya kyautar da ya'yana har UKu  ba daya ba.
 ko mahaikaciya ce Ni bazan soma yin wannan dayin aikin ba ballanantana Ina 'cikin haiyacina, yakarasa fadar hk tana nuna brain dinta da yatsan hannuta.
 kana tacigaba nidai Dan girma Allah Na rokeku daku barmin ya'ya Na Ina sansu nima a duk yadda suke.

 deeni ya runtse idanushi gam tare da furta ya Allah akasan zuciyarsa  ....yasoma cizan lips dinsa da karfi .
gabadaya komai Na 'cikin duniyar nan yasoma tsaya masa Bai taba tunani sanadiyar yarinyar zai taba  shiga  'cikin tashin hankali irin Haka ba.
   ya dauka rashin son 'cikin jikinta datake tun farko zai tsaya a Haka ne .
Amman a kalmomin bakinta na yanzu komai ya sauya agareshi yagane  shi din bakomai bane a duniya nan .
 sannan ya soma fahimtar Bai isa yace zai ma kaddarsa wayo ba .
Yau din nan tazo masa da tarin abubuwa da daya farinciki dake  tattare da tashin hankali mara misaltuwa .

Shin yanzu ya zaiyi da kaddarar data fada masa ?

Ya'yan da zai fara samu a duniya sunzo masa da wani irin salo  na daban .
yanzu mezai cewa danginsa da yan'uwa ?

Hakika Komai yagama dagule masa ahankali ya juya saitin da zeenat take tsaye surusuru tana aikin barin jiki da marairaice wa .
 yana aika mata da wani irin matsiyacin kallo me frigita zuciyar wanda akawa  sannan muryarsa a fusace  yace kinga ni ko ?
Kinga  irin abinda sakacinki  ya haifar mana   ko ?
Me kike tunani zai faru gaba  idan har taki amincewa tabada yaranta ?

Zeenat da jikinta ke mugun kirrrrrrma ta sake fashewa da wani irin matsanancin kuka tana yarfe hannuwa .
  yanzu dakin yi hakuri kin haifi wanda Allah yabaki da duk hk Bai faru ba.
 da km baki samu 'cikin tsaka me wuya ba. Amman bbu komai duk 'cikin wannan lamarin ni akafi cuta yakarasa mgnrsa yana jin kunar rai acikin zuciyarsa yayinda kirjinsa ke wani irin buguwa da karfi .
Shi kanshi  kuka yake son yi ko zai daina jin radadin azabar ciwon zuciyarsa keyi .

banda kuka bbu abinda zeenat keyi ita kanta tasan ta cuci kanta da kanta.
Ta  ruguza rayuwarsu sbd  sakacinta  da  son zuciyarta ta Mike Daga inda take  ahankali tana layi ta rungume ummi ajikinta  tana matsanancin kuka.
Ummi kiyi hakuri a rayuwa nasan Na cutar daku Amman ko daidai rana daya ummi baki taba kina ba .
Sai ma sabuwar kulawa da kike bani hakika ke uwace guda har da rabi samun irin Ku ahalin yanzu zai yi wuya  ummi kiyi hakuri abida nayi  ki ya femin Na cutar dake domin ba irin tarbiyya da kika bani ba kennan ta sake tsanata kukanta.
 ummi itama ta rungumeta sosai  tana zubda hawayen tausayin diyarta arayuwa ta tsani abinda zai saka zeenat dinta  zubd hawaye matukar tana da yadda zatayi.
 kasa cewa komai tayi Sai aikin  rarrashita datake tana shafa bayanta ..

Ahankali deeni ya dauke idanunsa akansu ya juyo sosai tare da gyaran zamansa yana fuskantar nablah da kyau ya kaskantar da kanshi da muryarsa agabanta yana nuna mata shin din bakomai bane facce me nema agurinta  .
a wannan fani har ya mance dako su waye  tsaye akansa.
 Domin Bai San sanda ya kamo tafin hannunta 'cikin sanyi jiki ba yana kallon 'cikin kwayar idanunta muryarsa cike da rauni zuciya tare  da mayyen sonta ya Kira sunanta.. nabeelah ...kiyiwa Allah ki mallaka mana bbys din nan.
 badanmu ba Sai saboda Allah  ki duba tashin hankali da zanshiga akan  yaran nan .
sannan ki duba halin da mahaifiyata da matata zasu shiga ki tausaya nablah ki duba yadda mahaifiyata tagama gayawa duniya akan nida matata muka haifi bbys din nan .Kinsa idan akaji sabanin hk zatashiga tashin hankali  da rudin rayuwa ..
 nablah nasan kina da saukin Kai  da sanyi hali hade da hakuri akan komai Na rayuwa .
Na rokeki da Allah kibarwa zeenat bbys din nan .
Allah zai duba lamarinki ya sake baki wasu da yardarsa ...
a fusace ta fizge hannuta 'cikin sauri Daga nashi tana jin takaicin mgnrsa .  ..

Kana ji har mara hankali matarka ta kirani dashi akan ya'yan dani kadai nasan  kalar wahalar dana Sha akansu tunda Daga cikinsu har zuwa haihuwarsu.
 idan har nabar mata yaran nan wallahi azim  Na tabbata mahaukaciyar gaske deeni .
 zeenat ta bar jikin ummi tamatso gareta sosai tana kuka tana rokon nablah. 

ZUCIYAR  deeni tasoma rawa yasoma jin Wani irin ajikinshi hakika ya tausayawa zeenat duk da yasan itace silar rugujewar rayuwarsu da yi musu katangar karfe da burin ransu km farincikinsu  Amman fur nablah taki amincewa tare da cewa aunty kiyi hakuri  wlh nima  Ina son ya'yana.
 idan nabaki su ni km yazamanto su kadai ne ya'ya da zan haifa a duniya   ni km Sai  nayi ya'ya ?

 Kiyi hakuri kawai kema Allah zai baki naki da yardarsa Amman zance nabar miki ma su  yanzu bbu shi .

 kibar min nawa nayi rayuwa dasu , sune duniyata  ayanzu bazan iya rayuwa bbu su ba .

deeni ya juyo a tsukwane ya kafe zeenat da idanushi yana kallon yadda ta dawo wata kala abar tausayi bbu wuya tashin hankali ya canza mata kammani .
Ummi takaraso ahankali itama  ta zauna kusa da nablah ta dinga bata hakuri da yima dabarunsu irin Na manya da siyasa iri iri Amman fur  nablah taki Sai ma fashe musu da sabon kuka datayi ni kibarni  Haka  Dan Allah Dame zanji .
 yanzu zan bar muku gidanku akan na bada yaran nan gara na komai
 kan bola Na rayu dasu 'cikin kulawata .

gabadaya deeni yasoma tsorata da yanayinta har yasoma aikawa kwalkwaluwarsa  tmbyr Anya kuwa wani abu Bai samu brain dinta ba kuwa gurin haihuwa ?

Sosai Ya xuba uban tagumi tare da jefa Dan  karamin yatsansa 'cikin  bakinsa yana cizawa da karfi yana kallonta  yana nazarin reaction dinta ..
sosai ya jima yana kallonta kafin Daga bisani yace first love barta kawai  akawo mata abinci  yaci da alamun tana jin yunwa tun da muka shigo gidan nayi nayi daita taci abinci taki ci a she rigima take ji shiyasa.
 jikin ummi a matukar sanyaye tace zeenat goge Hawayenki ki natsu  kada mutane su gane Muna 'cikin damuwa da matsala.
 muje maza  ki kawo mata abinci ni zan Dan tsaya saboda kauda idanun mutane akanmu.

Tare suka fita .
 ummi Na sake rarrashinta akan ta kwantar da hankalinta ..

Suna fita deeni ya juyo gareta ya hade da jikinshi ya rungumeta  zuciyarsa Na harbawa da sauri da sauri .
  tare sa sakin naunauyen ajiyar zuciya bakinsa yakai daidai saitin kunneta sosai.
Yace  Na yaba da jarumtarki Na yaba  miki da yadda kike son baby's dinmu .
 daman Haka yakamata duk wata uwa tayi akan yayanta .
 km hakan da kika yi ya sa naji kin  birgeni sosai. Sai dai me zai hana ki tausaya kibarwa zeenat dina baby's din please  zata kular miki dasu ..ki tuna sanda kike kuka kike rokona akan azubar da ciki Na hana batare da saninki ba .
ki tuna irin taimakon dana miki akan ni zan karbi 'cikin da bansan wanda Yayi miki ba domin gujewa kunyar  duniya 
Da karfina da dukiyata duk sa sadaukar akan Na inganta 'cikin jikinki da rayuwarki .
 Amman kirasa abinda zaki  sakayyar min dashi .
Sai  hanani bbyn dana gama wahala akansu.
Meyasa  zaki min hk ? Yakarasa mgnr da 
Ki bar mata sake of me please  nablah zanji dadi idan har zaki iya min hk .kina jin yadda zuciyarata ke bugawa da karfi  akanki .
,akanki zan iya yin komai ciki har da fallasa sirrin dake  boye wanda hakan bazaiwa first love dadi ba.
 please nablah sake of me jikinta Sai kirma yake tana zubda ruwan  hawayen tausayinsa muryarta a dashe tace nasani deeni kataimaka min a rayuwa km zan iya yi maka komai a rayuwa Amman bazan iya  kyautar yaran nan  Ga kowa ba ciki kuwa har da kai ..
Ni kaina Haka kawai Na tsinci zuciyata da matsanancin kaunarsu tunda Na daura idanuna akansu .kasa samun natsuwa .
Ya zanyi nabaku kennan ni zauna hk ?
Byn tarin wahalar dana Sha akansu .
 ahankali ya sausauta rungumar da Yayi mata ya ciro hanky Daga gaban aljihun rigarsa yashiga goge mata hawayen dake tsiyaya akan kuncinta .
bakinsa ya Kai kan lips dinta ya tsotsa yana kallon 'cikin idanunta .
Lumshe shanyayyun idanunta tayi tasoma kokari cire bakinta Daga nashi .
Jikinsa a sanyaye ya xuba mata rikitattun idanunshi kawai yana kallonta yana imagine dinta.
 har sanda zeenat ta dawo dakin hannuta rike da cool food flasks   da  flasks din ruwan zafi da plate ..

Deeni ya janyo wata Yar karamar stood tsakiyarsu  ya bude cool da  zeenat tashigo dashi.
 miyar dayafi tsana arayuwarsa  yasoma cin karo dashi wato miyar kuka wace Tasha  naman kaza da kayan kamshi makewa Yayi  ya ciro karamar ta sama ya ajiye yacigaba da bude cool yaga tuwan samiviter ne aciki Whit lailon ya ciro tuwon yasaka akan plate ita km zeenat jiki Na rawa ta hada mata tea me kauri ta mikowa deeni.
  " ya karba ya ajiye a gefen plet din.
 abin zeenat nabashi mamakin sannan km   yana jinjina girma al'amarin.
 lallai sanadin wayan nan baby's din  Yasa  zeenat dinsa tasoma sauya halinta wanda yajima yanasonta dashi .

Muryarsa a matukar sanyaye yace Bismillah nablah kici abinci .
taki ci ta xubawa masa  idanunta ya Mika mata cup din tea shima taki karba.
Yayi shr  ya tsura mata rikitattun idanunshi bazaki ci abinci ba ?
Ta girgiza masa kanta alamun eh saboda kina tunani zamuyi poison naki ko ?
Tayi saurin sake girgiza kanta to meyasa bazaki ci ba alhalin nasan kina jin yunwa ?

Muryarta a shagwabe tace nifa bance zakuyi min wani abu ba .. zeenat kawo min spoon. 
.
  Zeenat ta juya da sauri taje takawo masa spoon ta Mika masa .
 mamaki ne yakama zeenat Ganin deeni yasoma  tura  tuwon samiviter da miyar kuka  abakinsa the most abincin dayafi tsana kennan arayuwarsa ballanantana dai miyar kuka wanda ko sunan miyar akafada agabansa Sai ya yatsuna fuska tsabar baya sonta .
 Amman yau shine zaune yana ci hankali kwance dago rikitattun idanunshi Yayi masu tsantsar cike da tashin hankali  ya daura akan nablah dake zaune tamkar an dasata  tare da yi mata alama da spoon din hannunshi .
, zeenat tasoma itama  sosai ta tsoma hannuta sbd ganowa datayi lallai nablah bata yarda dasu ba.
 tasoma ci  Sai da nablah ta tabbatar dayaci sosai hk ma zeenat  sannan ta tsoma hannuta ciki tare da yin bismillah tasoma ci  ahankali aranta tace idan ma mutuwarce ba zan  mutu ni kadai  ba Sai dai abarwa ummi baby's din .
 ko tea din ma kin Sha tayi  Sai da zeenat Tasha deeni yasha sannan Tasha itama .
 deeni ya kalleta yana tabe baki girgiza Kai .
 sbd muraran km azahirance nablah ke nuna kuruciyarta a filli . Idan har wani abu zasuyi mata .
Ai tayi kadan ta kare kanta .


 number wayar ummi deeni  yakira .
Byn kmr minti goma Sai gata tashigo dakin   first love yakama ayiwa yarinyar wanka hk fa  da duk abinda yadace.
 ko bakace ba deeni duk za'a yi mata daman wannan tashin hankali ne Yasa nakasa samun natsuwa nayi mata ai nablah tamkar diyar cikina Na dauketa .

Da zai fita ya janyo hannu zeenat ya nufi dakinsa daita ya rungumeta tsam tsam  ajikinshi zeenat yakira  sunanta Ina so ki tattaro natsuwa ki sanyawa gangar jikinki sannan ki kwantar da hankalinki da sannu zan shawo kanta 'cikin sauki batare da wani hargitse ba har ta amince .
 domin wannan harbin iskar da kike da tashin hankalin   ba zai saka tabada ya'ya  'cikin sauki ba .
 as far as tasan wahalar daukar ciki da radadin haihuwa kema kinsa bazai yiwu a karbi yaran 'cikin sauki ba.
 ki dinga lallabata ta yadda taza yarda ta amince da ba cutar daita da yaranta zakiyi ba  ..

narkewa tayi sosai  ajikinshi , zanyi komai my hrt matukar yaran zasu zamo nawa Dan wlh wani irin mugu mugun  son yaran nake ji 'acikin zuciyarta .
Nima sun shiga raina zeenat  fiyye da ita kanta uwar data kawo su duniya.
 Amman duk da hk ba zai yiwu  muyi mata dole ba .
 tana bukatar rarrashi da caring  kema kinsa haihuwar nan  is not easy ballanantana irin nata datayi kwana biyu tana abu daya sosai deeni ya kwantarwa da zeenat hankali har ta Dan samu natsuwar zuciya tare da sake jin kaunar yaran daram acikin zuciyarta ..


Kowajen wanka ma kememe nablah taki yarda ummi ta rufe kofa toilet tayi.
  Dan kofar a bude aka barta tana hango wutsil wutsul din yaranta akan bed  Dan gabadaya atsorace take dasu ummu.
 yayinda  zuciyar ummi tashiga watsi watsi datashin hankali  anya kuwa ba wata maseefar ce ke shirin faruwa dasu ba.
 duba Ga yadda nablah ke nuna son yayanta mura mutane  da yin  kafa kafa dasu ...



Daren ranar  gabadayansu   Daga ummi har oga  deeni da zeenat adakin nablah suka  kwanna  sbd yaran a cewarsu .
 bbu wanda ya runtse acikinsu.
 yaran Sai kuka suke   nablah zaune tana feeding din mazan duka biyu  zeenat km tana tsaye tana hada abinci yara a fidda.
 shi km deeni yana tsaye rungume da bby girl dinsa yana jijigata sbd kukan datake ya saka mata lips dinsa abakinta yana Dan jijjigata har takoma bacci ya mannata ajikinshi  sannan ya koma ya zauna .
Ya jin yadda zeenat ke cigaba da rokon nablah Amman tayi mata banza taciga da feeding din yaranta tana jijiga kafa .zaune kawai deeni yake Dan  Bai San me zaice ba .
  ya kwantar daita zeenat ta karbi bby daya Daga hannu nablah  tashiga  bashi abincinsa.
 ita dai ummi zuru tayi tana aikin binsu da ido kawai.
 sbd al'amarin yarinyar ya daina bata mamakin ya dawo bata tsoro .
Haka 'cikin daren ummi da deeni sukayi ta mata naci da rarrashi akan yaran .
nablah kema tamkar diyata nake jinki 'cikin raina  sannan km bazan iya takuriki ba Amman  idan kinsa yadda  yaran nan  suke 'cikin zuciyarta dakin mallaka manasu  Kai tsaye bazan taba gajiya gurin rokonki  akan kibar mana  su ba .

 nablah tace uhmmmm azuciyarta , ummi kennan bazaki tabagane  value din yaran nan a raina ba  .
ni kaina bantabasani Haka yaya suke acikin zuciyar iyayensu ba Sai dayazo kaina .
 wayan nan yaran sune duniya ahalin yanzu .. zeenat ma  sake   saka baki ciki nablah zan kular miki dasu Dan girma Allah kiyi hakuri kibar minsu wlh nafiki bukatarsu sannan Ina rokon ki Dan Allah kibari a dinga sauka da baby's din nan kasa sbd Yan zuwa barka ..
Wani irin mugun kallo nablah tabi zeenat din dashi sannan tace nifa wlh bazan wani bayar da ya'yana ba .
 duk me son ganinsu yazo sama idan ya matsu  Amman wlh  idan kuka takurani zan ban bar muku gidanku Gobe goben nan , Dan  nima wlh atakure nake daku.

 gaban deeni  ya buga da karfi  ya tsurawa Dan karamin  tsukaken bakinta ido .
  Muryarsa   a sanyaye yace nablah  no  duk zance Bai kai hk ba .
Ba Sai kinje koina ba ke zeenat gobe kiyi zamanki anan dakin kawai  duk me son ganinki da bbys  yazo nan yasameki. jikinta a sanyaye tace to shikennan my hrt.



Washegari gidan yacika tap da dangi tana ji yadda kowa yake fadar irin  kyawun yaran Amman wai macce ce  kawai   bata biyo deeni  ba suko mazan tamkar an tsaga kara ne dashi  .
Ita ko  nablah tana kwance su ummi gabadayan sun rasa gane kanta domin ranta a matukar bace yake taki yarda tayi magana da ummi ballanantana wata zeenat.
 Barta   deeni ko kallo Bai isheta ba sbd magiyar dayake mata akan yaran aranta kuwa kwata kwata batason ta kara daidai da second daya agidan.
 tunanin kawai yadda zata gudu take da yaranta 'cikin sauki batare anganta ba ..



Tundaga ranar  duk yazo barka  ya nemi ganin baby's Sai  dai subada uzirin Doctor yace bbys din suna bukatar hutu yawan daukar da'ake musu yana saka su zazzabi dare wasu sun yarda da zance Sai dai wasu basu wani amince ba .
km suka dinga cewa iyayi ne kawai irin Na deeni Dan duk sunsa sharrinsa ne ...

 Sosai ummi ke bawa nablah kulawa ita da yaranta  .ta gasata  sosai da sosai duk da kasancewar  nabla  irin matan ne  masu tsukaken jiki wayan da da  zarar  anagama cinsu suke hadewa take Amman duk da ummi Na kula da kasanta .domin zuwa yanzu ta hade gam tamkar ba itace ta haifo Yan uku ba .sosai km take da nuna mata yadda zata kula da yaranta.
Itama nablah duk abinda ummi tasanar tana  kiyayewa sbd  daman ita can me kaunar yara ce nawasu ma  ta bauta musu ballanantana nata .ita kuwa zeenat gabadaya fargaba da tunani hade da  tashin hankali ya maidaita wata iri .
 tayi wujiga wujiga daita tayi wata irin rama tayi duhu  kallo daya zakayi  mata kasan tana 'cikin taskon rayuwa da  tsaka me wuya. Yayinda kullun kwana duniya take like da nablah tana yi mata naci da magiya akan tabar mata baby's din ta .ita km ta rufe idanunta taki wani lokacin idan abun ya isheta tasaka mata kuka .abu goma da ashirin Ga kewa gidansu datake Ga taushin hankali da fitinar zeenat.


Ta fanni deeni ma gabadaya ya susuce ya rame tsaye kawai yake da kafafunsa Amman zuciyarsa cike da rudani .
Tunda akayi haihuwar yagagara fita koina . abokansa sukayita zuwa taya Shi  murna  karuwar daya  samu .
 Yayinda ,gida da office takoina ka kalli fuskar jama'a  murna haihuwar  manager  suke .
 ,sadaka kuwa deeni Yayi shi  har bai San iyakacin abinda ya raba ba .hutu sati guda akabawa ma'aikata companies har sai byn suna .


Fk ma yazo ganin baby's da kyar deeni yasamu ya  karbi a gurin nablah yakai masa km har yakai su ya dawo dasu kuka take .tana ganin ya dawo mata da yaranta ta bar kuka datake  tana sakin numafashi da karfi da ajiyar zuciya 'cikin jikin nasa  yakaraso gareta  yana cizan lips dinsa yace yanzu har rashin yarda takai Haka nablah ?
Bazan cutar dasu domin nima sune duniyata kalli yadda kika dawo nablah akan yaran da nabaki ba .wata katuwar harara ta zabga masa sannan ta turo masa tsukaken bakinta gaba bangane yaran da  banawa ba? 
Kana ganin duk duniya akwai wanda ya isa Yayi claiming din yaran nan nashi ne ?

Ya Dan yi murmushin takaici ya zauna gabanta ya tsotse lips dinta cike da shaukinki kaunarta yace akwai ubansu km mahaifi ko ba dade zai bayyana kansa garesu Amman dai kafin zuwansa kiyi hakuri ki bar min su.

 
Ranar da bbys suka cika kwana hudu da haihuwa  tafiyar gaugauwa taka ma deeni zuwa abuja  tun safe deeni ya tafi abuja amman aranar zai dawo.
 ,tunda nablah taji zance tafiyar sa .
Ta kasa zaune ta kasa tsaye .
hankalinta Yayi matukar  mugun tashi .
Duk ta frigice ..
 taki sakarwa ruhinta salama  .



Karfe shida daidai 
 deeni yashigo gidan kai tsaye  dakin jikin nablah ya nufa yana bude kofar yayi turus  jikinsa  a sanyaye  sbd ganin da Yayi nablah tsaye rungume da yaranta biyu akirjinta ,sannan  km dayan na goye abayanta tana jijiga su tana kuka su ummi da zeenat tsaye akanta  sunyi cirkocirko suna dubanta .Dan gabadaya sun rasa yadda zasuyi daita tun barin deeni gidan take a Haka .
baby's din ma kuka suke sosai  tamkar sun San mamansu Na 'cikin tashin hankali.

 ahankali deeni yakarasa shigowa dakin sosai  yana bin su ummi da  kallo.
 kana jikinshi narawa da zuciyarsa gurin cewa lfy ummi naganku hk ?
Ina fa lfy  deeni tun safe daka bar gidan nan  nake fama daita taki cin taki Sha  har zuwa  yanzu.
Yanzu  km mun shigo dakin  munganta goye da ya'yan .
 da alamun shirin guduwa take ya runtse rikitattun idanushi dake cike da rudani  yana ambatar sunan Allah .
 ya kamota ya zauna daita ya karbi yaya duka  ya kwantar dasu ya riko hannuta'cikin nashi yana kallon ummi da zeenat tare da yi musu alamar su fita.

Byn sun fita gabadayansu  ya Mike yaje ya rufe dakin tare da yiwa kofar key yana dawowa ya rungumeta gam ajikinsa kusan minti goma shabiyar suka dauka haka batare da yace komai ba suna sauke naunauyen ajiyar zuciya da shakar numfashin junansu.cike da tausayinta ya zareta Daga jikinsa yaje ya hado mata tea me zafi yakawo mata ta kar Tasoma sha ahankali Dan yanzu tafi yarda dashi akan zeenat da ummi .
muryasa'cik e da fargaba yace nablah ta dago shanyayyun idanunta tana kallonsa batare da ta  amsa.
Meke damunki ?
Tayi shr taciga da kurbar tea .
Ko wani abu su ummi suka miki ?
Ta girgiza masa kanta .
Ya kamo tafin hannunta wanda yake empty yasoma murzawa ahankali ahankali  tare da tsareta da rikitattun idanunshi.
Muryarsa cike da laushi ya sanyaya ta sosai sannan yasoma mgn a tsanake  yace   ba ki min alkwarin zaki bani bby 
 ba?
Ba  gori ba  ki tuna abubuwan alkhari dana miki nablah akanki Na mari matata ta sunana akanki Na kewa mahaifiyarta gardama Ya'yanki ba'a San usilinsu ba.
 ba'a San tushensu ba Amman  naji nagani nace  karbi 'cikin jikinki domin Na rufa miki asiri sbd kar duniya ta zage ki .

,kin  tuna sanda kika yi 'cikin nan ban Kiki ba nayi rayuwa dake tamkar matata ,Na kula dake da abunda ke cikinki . please nablah kada ki canza ra'ayinki akan alkwarin dakika min akan zaki bani su . jikinsa Na rawa yacigaba da cewa wlh  idan kika yarda kika  amince kika bani baby's din nan  nayi miki alkwarin   zan mallaka miki gidan glass gabadayansa  zan mallaka miki  gidana  dake  ajawu estate zan maidake makaranta kicigaba da karantunki dakike buri .
 zan taimakawa iyayenki Na canza musu rayuwa  zan ingata rayuwarki data ahlinki gabadayansu .
 haka ya dinga kwadaita mata abubuwan alkhari  dazai mata .
nablah Ina son kisan wani abu ko matata ta sunnu bata taba zuwa sabon gidana Na glass ba Sai ke.
 bantaba yin rayuwa da wata mace a duniya irin yadda nayi rayuwa dake ba .
Narasa tantancewar kaina da zuciyata shin sonki nake ko  km tausayin ne ko km sabo ne Amman mutane da dama idan Na tmbyesu suna gaya min sonki nake.
 which's kema kinsha gaya min haka.
 Amman Ina karyata zuciyata nablah ki dubi Allah ki taimaka please ki bani yaran nan sake of me zuciyata tayi rauni dayawa gashi bata iya naci akan abu duk girma Amman yau tsawon kwana hudu Ina binki.
  sanadiyar wayan nan yaran bbu abinda bazan iya miki ba  arayuwa zan miki  komai Na rayuwar duniya r nan .
 jan jiyar dake dadin duniya zan saki daukaka acikin duniya.
 bazan taba barin ki wulakanta ba.
Duk abinda deeni ya mallaka naki ne hk  zuciyar deeni take ce please please nablah  ki taimaka please Haka ya dinga gaya mata Ward's masu dadi da sanyaya zuciya as ended.
 Ya zube kasa agabanta Yayi mata neildwon tamkar dai yadda zeenat tayi mata.
 ya daura kanshi a saman cinyarta sannan ya sakala hannushi ya rungumeta gam ta baya muryarsa a raunane yace mata.
 Dan girma Allah kiyi hakuri ki taimakeni ki rufa min asiri ni badan zeenat ba Dan ummi banason ki kunyata ummi sbd ta rigada tagama gayawa mutane zeenat haihu . Yanzu tunda abin yazama hk Kinfa sa kyautar mana da yaran shikennan   ki ba r  ya'ya kawai .
Amman Dan sbd dan kada mutane su farga su gane ba yaranmu bane .

Ki aro mana su  Amman agurin ki zasu dinga kwana a lallaba mutane har ayi suna inyaso byn suna Sai a gayawa duniya da  mutane abinda zeenat ta haifa sun mutu har an binnesu ke km kina iya tafiya da yaranki .
Gabanta ya fadi jikinta ya dauki  rawa tace to.. to. shikennan Na yarda da wannan .
zan muku alfarma har ta wata daya a gama rurumar suna da barka Sai dai fa wlh da ya'ya zan dinga kwana kmr yadda kace.
 zuciyarsa cike da farinciki samun nasara da Yayi yau  yace Na amince .
 to kira  ummi da zeenat ka maimaita agabansu gabadayansu suka shigo dakin byn kiran da deeni Yayi musu  ta waya.

Ahankali cike da natsuwa  ya maimaita yadda sukayi da nablah ummi zatayi mgn da zeenat Yayi saurin yiwa ummi sigina da idonsa  alamun kada suce komai take kuwa  suka yi shiru.
 suka hau  cewa shikennan mun yarda da wannan tsarin ... gabadayansu da ummi da zeenat har deeni suka tabbatar mata da sun  Yarda akan tsarin...




Uhmmmm to ko yazata kaya tsakanin deeni da zeenat har uwar gaya ummi 🤔🤔🤔🤔🤔🤔🤔Ku dai kucigaba da biyo Yar mutan bagudo 




MMN SUDAIS CE
