BAK’AR SHUKA…! NA HAUWA A USMAN JIDDARH Wattpad:HauwaAUsmanjiddarh ArewaBooks:HauwaAUsmanjiddarh Completed Book 1 Gudu-gudu sauri-sauri take tafiya tana waiwaye kamar zata hantsila, kallo d'aya zakayi mata ka fahimci bata cikin nutsuwarta, a mugun kid'eme take, ganin ta shigo cikin mutane yasata tsayawa had'i da durk'usawa tana fitar da nishin wahala, ajiyar zuciya ta sauke ta goge gumin data gaji da gogeshi, " sannu baiwar Allah, taji an furta daga bayanta, a matuk'ar tsorace ta kalli inda tajiyo sautin maganar ta fito, ganin yadda fuskasta ta bayyana tashin hankali yasashi cewa " lafiya kuwa!? Yayi maganar yana k'arewa jikinta dake rawa kamar mazari kallo, batayi mishi magana ba, ta taka k'afarta dakyar a galabaice zata bar wajen, saurin shan gabanta yayi yana fad'in " kada ki tafi ki zauna ki huta mana, yayi maganar cike da tausayawa, batayi mishi magana ba ta cigaba da tafiya, a zatonshi bataji abinda yace ba, dan haka ya sake shan gabanta cike da tausayawa yanayinta yace " baiwar Allah ki d'an zauna ki huta, ganin bata bashi amsa ba yayi zaton ko kurma ce, dan haka ya yarfa mata hannu irin yadda ake yiwa bebaye magana had'i da cewa " bakya jina? Kallan datayi mishi ne ya bashi tabbacin tuninshi ba gaskiya bane, bayyi niyyar k'ara yi mata magana ba amma abun *K'ADDARA* haka nan yaji baiji dadin yadda tayi mishi ba, " wulak'aci babu kyau musamman ga mutumin dayaso taimakawa rayuwarki, bada wata mammunar manufa nace ki huta ba, taimakonki nayi niyar yi amma tunda hankalinki bai kyauta ba shikenan, dummmm! hawaye na gangaro mata, batare data sani ba kalmomi biyu zuwa uku suka sub'uce daga bakinta, " kayi hak'ur.....! da wani irin sauri ta jiyo ta kalle shi tana girgiza kanta tare da ja baya cikin matsanancin tashin hankali, " na shiga uku magana nayi maka? "Na amsa maganarka? Binta yayi da kallo mai ma'anoni da dama ciki kuwa harda kallan mahauciya, cikin tsawa da masifa tace " meyasa ka matsani nayi maka magana? " Meyasa baka barni na tafi ba? Cikin rashin fahimta yace" me kike nufi? A tsorace tabar wajen da gudu-gudu, ta d'anyi nisa kad'an ta jiyo sautin ihuuu mutumin da k'arfi, cak ta tsaya, hawaye mai d'umi ya biyo kuncinta muryarta na rawa ta furta " *ALLAH YAJI K'ANKA, UBANGIJI YAYI MANA SAKAYYA,* *WATA SHARI'AR SAI A LAHIRA....,* duk da inda sabo yaci ace ta saba, amma ta kasa sabawa da jiyo ihuuun azabar fitar ran mutane da dama, wanda itace ta zama *SILAR MUTUWARSU,* babu irin mutuwar da bata gani ba, babu wani tashin hankali, tsoro, firgici da kid'imar da zasu gigitata, amma ya zatayi dole akwai tausayin rai, ta juya ta kalli gawar mutumin kwance cikin jini, tafiya ta cigaba dayi batare datasan inda take nufa ba, zuciyarta ta k'ek'ashe ta bushe babu d'igon tsoro a cikinta, tafiya tayi sosai kafin ta isa bakin titi, mutanen da suka santa suna ganinta suka fara guduwa suna ihuuu, siraran hawayen da suka biyo kuncinta ta goge tana cigaba da tafiyarta batare data tsaya ba, sai da tayi tafiya me nisa kana ta samu me napep,  ta tsaida ta hau, " ina zaki Hajiya? Wajen gari ta bashi amsa tana duk'ar da kanta k'asa, jin shiru bai tada mashin din ba yasata d'agowa tana fad'in "muje mana Mala....., sark'e mata maganar tayi a mak'ogwaro ganin mutumin a kwance kan sitiyarin napep din, idanuwanshi a waje kallo d'aya zakayi mishi kasan babu rai a jikinshi, wani irin ihuu ta saki had'i da dirowa daga napep din, kasa motsawa tayi balle tayi k'ok'arin guduwa, kuka takeyi sosai kamar ranta zai fita, " banyi mishi magana bafa, koda nayi mishi ma bai amsa min ba, meyasa bazaka barni haka ba? "Meyasa bazaka bar rayuwata ta huta ba, bayan iyayena, 'yan uwana da dangina *DAKA KASHE, HAKAN BAI ISHEKA BA, ACE DUK NAMIJIN DA YAYI MIN MAGANA, KO NAYI MISHI YA AMSA SAIKA KASHE SHI MEYASA....?* Wata irin mahaukaciyar dariya ta jiyo daga bayanta, bata motsa ba, balle ta juya ta kalleshi, ko ba'a fad'a mata ba tasan waye, tasan shine, dan ya zama inuwarta, ya zame mata damkar ruhi da gangar jikinta, bata ganinshi da idonta, amma duk inda ta sanya k'afa yana biye da ita, "wakike tambaya bayan kin san kece silar faruwar komai, * DEEYANAH* ke kika ja komai duk abinda ke faruwa da rayuwarki ke kika jawa kanki, yayi maganar yana zagayata, cikin kuka tace " na sani... nasan nice sila, shiyasa nake rok'onka nake kuma baka hak'uri akan ka fita daga rayuwata, da sauri ya durk'usa gabanta yana yi mata wani irin kallo, " hak'uri fa kikace *DEEYANAH* wannan wacce kalma ce mara dad'in ji da furtawa, kanshi ya d'aga yana kyalkyala mata dariya, " karya kike Deeyanah ba wannan maganar, har abada bazan barki ba, ni inuwarki ne, ko mutuwa tare zamu mutu, kuma a kabari d'aya za'a binne mu, ke ko mutuwa kikayi bazan tab'a barinki ki kwanta lafiya a kabarinki ba, haka idan ni na rigaki mutuwa fatalwata bazata barki ba Deeyanah , ta bud'e baki zatayi magana tajiyo hayaniyar mutane, kafin tayi wani yunk'uri sun k'araso inda take, saurin mayar da kallanta tayi inda yake taga bayanan, al'amarinshi har tsoro yake bata mutum kamar aljani ba'a ganinshi sai dai aikinshi, fincikota wani k'ato yayi ya d'agata sama ya buga da k'asa yana fad'in " tsinanniya annoba, wacce ta zama sanadiyyar mutuwar ahalinta da jama'ar da basu ji ba, basu gani ba, da ace ban san mutuwa hutu ce a gareki ba, da ni da kaina zan kasheki, inyaso nima a kashe ni, daga gefe wani ya amshe da cewa " aiko kasheta zamuyi yanzu bak'ar daga, taya zamu sakawa shegiya mu k'ona tsinanniya, " bazamu kasheta ba mu d'ibarwa kanmu sai dai mu nad'a mata dukan da saita kasa tashi, daga gefe wani yayi ihuu tare da d'ora hannu aka yace " ga gawar wani ta kashe shi, kukan kura mutanen sukayi suka afkawa Deeyanah da duka, saida suka had'a mata jini da majina, kafin suka d'auketa suka kaita daji suka yar, " idan muka k'ara ganinki a ariyar unguwar nan wallahi sai mun aiki inda kikayi sanadiyyar aika iyayenki, ya k'arashe maganar yana tofa mata yawu a fuska, sosai take kuka kamar ranta zai fita, mussamman da ake jifanta da kalmar tayi AJALIN AHALINTA, kalmar na mata ciwo a duk lokacin da aka jefeta da ita,, bataso sanya su cikin bala'i bane, data amsa musu maganarsu, tasan matuk'ar ta amsa d'ayansu bazai koma gida da rai ba duk yawansu, tasan sayya k'arar dasu tas, a hakan ma bata da tabbacin zai kyale su, tunda suka tab'a tafiyarta, ba ruwanshi da mata, idan kaga ya tab'a mace to matsawa Deeyanah tayi, kota shiga rayuwarta, amma namiji hmmmm ko kallanta kayi da wata manufa to sunanka *GAWA* musamman idan kayi mata magana ta amsa, bata damu da cikin bola take ba, ta cigaba da zama tana kuka, ta mik'e da niyyar barin wajen ta fara jiyo ihuuuun mutanen da suka daketa yanzu, ido ta runtse ta k'arfi hawaye na zubo mata, tun tana jiyo ihuuuun su harta ji shiru, alamar ya gama dasu, 'yar tafiya tayi kad'an ta samu waje ta zauna, kanta ta d'aga sama ta kalli sararin samaniya, a hankali komai ya soma dawo mata sabo kamar a lokacin yake faruwa. *WAIWAYE...* Family d'insu Deeyanah babbane a garin Kano, Malam Abduljalal shine mahaifinta, kusan gaba d'aya zuri'arsu suna zaune ne a Estate d'aya, a unguwar magajin rumfa sai danginsu na can nesa dake zaune a k'auyuka ko wani garin amma muddin kana cikin garin Kano to kana cikin Estate d'insu, duk k'ank'antar alakarku, suna da wayewar ilimin boko duk da basu bari iliminsu ya gurb'atasu ba, dan sun cud'anya ilimin bokon dana addini, haka ma yaransu a nutse suke sun samu tarbiyya dai-dai gwardado, tsaka-tsaki ne su, baza'a ce basu da tarbiyya ba, haka baza'a kira su da masu cikekkiyar tarbiyyar Islama ba, dan suna had'awa da boko, da wayewar zamani sai dai wayewar zamanin ba wai irin ta yaran nan fitsararru masu shaye-shaye da fidda tsiraici, marasa tarbiyya ba, yaransu a nutsu suke dai-dai gwargwado, Aina'u itace mahaifiyar Deeyanah, kuma ita kad'ai ce matar mahaifinta , yaransu hudu, mata uku namiji d'aya, Azan shine babba sai k'annanshi mata Azwah da Azrah, sai autarsu Deeyanah , Azrah da Azwah sunyi aure tuni, ya'yan wan mahaifinsu  suka aura, Abdulraheem da Abdulrasheed uwarsu d'aya ubansu d'aya, Abdulhakeem shine mahaifinsu, su biyar ne a wajen iyayensu, hudu maza sai autarsu mace Busainah, dukkaninsu suna nan zaune cikin Estate din, suna yiwa yaransu auren zumunci, koda wasa wata ko wani cikin zuri'arsu bai taba auren bare ba, Aina'u mahaifiyar Deeyanah , mace ce ta gari, ga hak'uri da kawaici, shiyasa duk yawancin yaran da suka taso a Estate d'in ita ta rik'esu, harta aurar dasu. DEEN... D'a ne ga Abdhulhakeem da Halimatu yana da yayye, maza biyu Abdhulrasheed da Abdulraheem, sai k'anwarsa Abeerah, yayyan Deen suke auran yayyan Deeyanah, Deen yana d'aya daga cikin yaran da Ammah (Aina'u ) ta rik'e, kuma har gobe yana gidan, sosai Ammah da Babah (Abdhul Jalal) ke ji dashi. Deen yaro ne kamili nutsutstse, mai hankali, shi mutum ne da yawan magana bai dameshi ba, yakance " sai mutum nada abin fada yake magana, shiko bai da abin fada, haka yawan magana da surutu yana sawa ayi karya, karya kuma tana kawo raini, shi kuma mutum ne da bai kaunar raini, duk yadda kuke dashi kace zaka rainashi yanzu zai kawo k'arshen alak'arku, ko yayyanshi da abokanshi suna girmamashi, bai cika yawan dariya ba dan ko yayi bata yi mishi kyau inji Deeyanah, haka ya cika takura mata musamman idan zata fita, tayi kwalliya kota yafa mayafi, kowa a gidan ya gane yana san Deeyanah, haka itama tana sanshi, k'ifad'i irin nashi ya hana ya sanar mata, koya nasarwa da iyayansu. Yana zaune a parlour saman sofa ya d'ora k'afa d'aya kan d'aya yana karanta jarida, saboda ta tsokaneshi ta ci kwalliya kamar zata gidan biki, ta yafa siririn mayafi, dan yadda yake nuna kishi a kanta yana burgeta sosai, tasha kiran mazan ajinsu suzo gidan tayi kamar tana zance, yadda yake fututtukewa yana fada yana bata sha'awa, 'yan gidan suyi tayi mishi dariya, ta gabanshi tazo zata wuce tana gyara mayafinta, had'i da satar kallanshi, baki ta turo ganin harta kai k'ofa amma baice mata komai ba, baima kalli inda take ba, jikinta a sanyaye zata fice, taji yace " ke!, cak ta tsaya had'i da yin murmushi " baki san mutuncin kanki bane zaki fita haka tsirara? Kamar gaske ta juya tana had'e fuska kamar yadda tashi take koyaushe, idonshi kan jaridar dayake karantawa, cikin yatsina fuska tace " tsirara fa kace? Bayyi mata magana ba, ta d'ora da cewa " kalli fa ka gani da kaya a jiki na, batare daya kalli inda take ba, yace " idan aka barki zaki iya fita haka? "Sosai kuwa, "jeki, yace a tak'aice, da sauri ta juya zata fice, tana k'ara taka takalmin k'afarta da k'arfi yana k'ara k'as-k'as, idonshi ya runtse ya bud'e, tare da aje jaridar, yana jin k'arar takun takalminta har cikin kanshi, ga turaren data fesa mai bala'in k'amshi, ya san halin mazan yanzu, zasu takurata kodan takunta mai d'aukar hankali, ko baka san tana zuwa ba k'amshinta da k'arar takunta zasu jawo hankalinka gareta, kamar yadda tun kafin ta k'araso k'amshinta ya ziyarceshi, takunta kuwa tare suke dokawa da zuciyarshi, ganin ta kusa fita yasashi saurin cewa " please mana Deeyanah!, saurin jiyowa tayi ta kafeshi da ido, yadda yayi magana yana huda zuciyarta kamar kifiya, kallan da tayi mishi yasashi ankarewa ya saki layi, fuska ya tsuke had'i da daka mata tsawa yana fad'in " ke! baki da hankali ne? " Dalla koma ki wanke fuskarki, ki saka hijab ki kuma canja takalmi, baki ta turo tana diddira k'afa tace " I'm 19yrs fa Yaya, ina jami'a in 100 level in saka hijab haba Yaya is on...... tsawar daya daka mata yasa bata k'arasa maganarta ba, tayi ciki da gudu, yabi bayanta da kallo yana murmushi had'i da shafa kanshi " wow! Wonder shall never end Son! yau kai ke murmushi da kanka? Kanshi ya shafa yana rusunawa yace " ina kwana Babah? " Lafiya lau, Alhamdulillah Romeo, murmushi yayi a karo na biyu yana shafa kanshi batare dayace komai ba, " hmmm yadai kamata ka magantu Son! wannan kame-kamen ba kai maka zayyi ba, ka fito ka sanar da ita kana santa, kar wani yayi maka kutse ayi maka shigar sauri, " Ah haba Babah waya isa? "Waya isa ya shiga tsanina da Manassah bayan had'in Allah ne mu, mutuwa kad'ai zata iya rabamu, murmushi Babah yayi yana rik'o Deen, " kadai fad'a mata saboda yanayin rayuwa da zuciya, " zan sanar da ita in sha Allah Babah, so nake saina tafi course d'innan America, " Allah ya tabbatar da alkhairi, " Amin ya Allah. Da yamma bayan sun tashi lectures k'awarta *RALEEYA* ta kawota har gida, fuskarta d'auke da murmushi ta fito daga motar, tana juyowa idanuwansu suka sark'e cikin na juna, yana tsaye ya hard'e hannuwanshi a k'irji, ya kafeta da ido, guntun murmushi tayi tana cije lips ta d'agawa Raleeya hannu had'i da kashe murya tace " bye my sai gobe I will miss you, tabi bayan motar da kallo tana murmushi, har motar ta b'ace tana d'aga mata hannu, kasancewar motar tit ce yasa Deen bai gane macece a motar ba, take idanuwanshi sukayi jajir, jijiyoyin kanshi suka fito, ganin yanayinshi yasata tsorata, ta rab'a zata wuce ta gefenshi, ya fincikota da iya k'arfinshi yana fad'in " uban waye ya kawo ki? Bakinta na rawa, dan tayi muguwar tsorata tace " Raleeya ce, a zafafe yace " karya kike yi, motar Raleeyan ce ban sani ba, " wallahi Yaya itace, " zaki fad'a min wanne shegen k'aton banzan ne ya kawoki ko kuwa? Yayi maganar yana girgizata da k'arfi, sosai inda ya rik'e yake yi mata zafi ji take tamkar yana b'alla mata k'asusuwa, kuka na k'ok'arin kwace mata tace " wallahi Yaya itace, " yaushe Raleeya ta canja mota? Ya fad'a ranshi na k'ara b'aci dan sosai ya tsani k'arya, " jij....ji....jiya, tayi maganar a rarrabe kamar me kayan magana, bayyi magana ba ya bud'e mota ya dannata ciki, ya zagaya ya shiga, yayiwa motar key ya fisgeta da gudu, " bani wayarki, hannunta na kerrrrma ta mik'a mishi, dukda da gaskiyarta ta had'a uban gumi, hausawa na cewa mara gaskiya ko a ruwa yayi jib'i yau ita da gaskiyarta take yin gumin, " idan har ba gaskiya bane sai ranki ya b'aci, ya k'arasa maganar yanayin parking a k'ofar gidansu Raleeya, sosai tayi mamakin yadda akayi yasan gidansu Raleeya, dukda tana da gaskiya bai hana cikinta murd'awa ba, motar ya bud'e ya zagaya ya bud'e mata ya rik'o hannunta, sau biyu ya buga get d'in me gadi ya bud'e 'yar k'aramar k'ofa da nufin tambayar waye, ganin Deeyanah yasashi washe baki yana fad'in " ah ah Deeyanah ce? Bata iya amsa mishi ba saboda halin da take ciki, fuskar Deen a tamke yacewa me gadin " yi man magana da Raleeya, " to to, amma da kun shigo daga ciki, ba musu ya jata suka shiga cikin dama neman damar shiga yake, suna shiga harabar gidan yaga motar, a fili ya sauke ajiyar zuciya tare da lumshe ido, dan harga Allah yayi zaton namiji ne, wato tana sani tayi hakan, tayi ne danta tsokane ni, bai jira me gadi da Raleeya sun fito ba, yaja hannunta suka fita, tafiya sukeyi shiru babu wanda yacewa wani k'ala, sai sheshshekar kukanta dake tashi, abin yayi mata ciwo, wai ita Deen ke zargi, why kake zargi na, why? Tayi maganar cikin ranta, abinda bata sani ba, maganar ta fito fili ya ji, " kiyi hak'uri, ya furta a hankali, kamar daga sama taji Deen yana bata hak'uri, cike da mamaki ta kalleshi, bata san sanda murmushi ya kufce mata ba, amma ta basar ta cigaba da matsar hawaye tana shashsheka, rolling daradaran idanuwanshi ya juya had'i da kafe ta dasu yace " nace kiyi hak'uri ko? Baki ta turo batare data ce mishi komai ba, yana yin parking ta bud'e motar ta fice ita a dole anyi mata laifi tana fushi, yabi bayanta da kallo yana murmushi. Dr Deen cikekken likitan kwakwalwa ne, yayi karatunshi a ABU Zaria, kafin daga baya ya tafi Germany yayi masters dinshi acan, nan da kwana biyar zai tafi America yin wani course, hankalinshi a tashe yake sosai na barin Deeyanah da zayyi, ga bai sanar mata yana santa ba, ya dai k'uduri niyyar da kafin ya dawo zai sanar da ita, yana da tabbacin bazai samu matsala da ita ba, da izinin Allah........... Kwanaki biyar d'in nan jinsu suke kamar seconds biyar dan basu tab'a ganin gudun lokacin irin wannan ba, dukkansu sun shiga cikin mawuyacin yanayi, duk Wanda ka kalla cikinsu kasan yana cikin damuwa, 'yan gidan sai dariya suke yi musu ciki-ciki ana tsokanarsu, lokaci ba wuya a wajen Allah, yauce ranar tafiyar Deen, yadda sukaga rana haka sukaga dare, ko gyangyadi cikinsu babu wanda yayi, ya tsaf ya fito yana janye da trolley, jinkinshi sanye da man material shara-shara, kayan sun karb'e shi, abinka da dogo fari me kyau, ganin gaba d'aya ahalinsu a harabar gidan yasashi k'ak'aro murmushin dole ya sanya a saman fuskarshi, amma kallo d'aya zakayi mishi kasan a iya saman leb'enshi murmushin ya tsaya bai kai zuciya ba, ido ya fara wulk'itawa yana neman ta inda zai ganota, amma ko alamarta babu, ta bayanshi yaji ance " Deeyanah! kake nema ne? " Tana ciki ta kulle kanta a d'aki tak'i fitowa ko abinci bata fito ta ci ba, da alama fa yadda ka kamu itama ta kamu, saurin juyawa yayi, Babah ne, kanshi ya shafa yana kallan Baban, kai Babah ya jinjina mishi danya gane kallan da Deen keyi mishi, ya d'ora da cewa " duk da baku furta ba, amma ina da tabbaci akan hakan, dan tun jiya data dawo makaranta ta shiga d'aki bata fito ba har yanzu, an buga mata k'ofa tak'i bud'ewa, zayyi magana Babah ya tareshi da cewa " ni dai ina baka shawara akan kayi mata magana kar lokaci ya k'ure maka, da kayi magana da yanzu da matarka zaka tafi, ina jiye maka abinda zaije ya dawo, ina jiya maka yanayin juyawar k'addarar dake raba masoya ta k'ulla sabuwar soyayya, cike da yak'ini Deen yace " hakan bata tab'a yiyuwa ba, Allah kad'ai zai rabani da Deeyanah, amma babu mahaluki abin halitta da ya isa ya shiga tsakanina da ita, k'uruciya, Babah yace cikin ranshi, a fili kuma yace " wannan duk yarda da kai ne? "A'a Babah ba yarda da kai bane, yak'ini da zuciya ne, murmushi Babah yayi ya rik'e hannun Deen yana fad'in " muje karka makara, bazai iya yiwa Babah musu ba amma yaso yaje k'ofar d'akinta ya jiyo koda fitar numfashinta ne, dole yabi bayan Babah idonshi kan k'ofar dakinta, basu wani jima a Airport ba jirginsu ya d'aga zuwa America, bata fito daga d'aki ba sai da akayi kiran sallar la'asar, kallo d'aya zakayi mata kasan tana cikin damuwa, Ammah na zaune saman sofa tabi bayanta da kallo batare datace komai ba, zatayi karya idan tace bataji babu dadi ba, bayan tafiyar Deen, sosai tayi kewarshi, sai da Raleeya ta sata gaba da tsokana tana cewa " da an san ana so aka tsaya jan aji, dole ta watsar ta shiga sabgar gabanta ta mayar da hankalinta gaba d'aya kan karatunta. *MAFARIN BAK'AR K'ADDARA...!!!* Da wuri ta shiga makarantar direct class ta nufa har tana tuntube kasancewar wayar da Raleeya tayi mata ta sanar da ita, yau me English ke had'a Assignment dinshi, tun farkon Semester Malamin ya bada Assignment din, ta rasa wanda zayyi mata, har caffe taje amma a banza, ga Malamin yayi gargadin kar mutum biyu suyi iri daya, muddin yaga iri d'aya zayyi musu cancel gaba daya, " kin san Allah haukana nayi mishi, tunda shi yace bai san copy copy ni na tab'a jin irin wannan kakalen, Cewar Raleeya tana bata fuska, rolling ido Deeyanah tayi tana fad'in " ni haukan ma na kasa yi wallahi, na rasa ta in da zan fara abin duniya duk ya isheni, shiru Raleeya tayi na d'an lokacin kafin ta sauke ajiyar zuciya tana fad'in " akwai mafita, cikin zakuwa Deeyanah tace " dan Allah? " Eh, naji yawancin 'yan ajinmu na cewa wani d'an level 400 ne yayi musu, an ce duk makarantar nan ba mai k'ok'arin shi, wai sau kusan biyar yana samun scholarship yana k'in tafiya, " me yasa? Deeyanah tayi maganar cike da mamaki, " eh to wai shine bai sha'awar fita waje yayi karatu, inda yana da ra'ayi daya fita dan babanshi me mugun kudi ne, naji ance shine sakataren governor fa, kuma shi kad'ai ya haifa, kuma mahaifinshi na mugun sonshi, kinga ra'ayin fita waje ne bayyi ba, kamar dai ke da baki da ra'ayin fita waje karatu, Raleeya ta fad'a tana kai mata dukan wasa, baki ta tab'e tana fad'in " wallahi nima dai banga amfanin karatu waje ba, sai b'ata tarbiyya da lalata d'abia a cirewa 'ya'ya mata kunya, su koma kamar tumakai, dariya Raleeya tayi tana fad'in " kedai kika sani, mudai samu ne da bamuyi ba, idan muka samu zamu, " ke dai ban san surutun banza rakani wajen... wama yake...., " AJLAAL , sunanshi Ajlal. " Ajlal...! ta maimaita sunan saman lips d'inta, jin yadda ta Deeyanah ta maimaita sunan so calm yasa Raleeya kallanta tana murmushi tace " yayi masifar had'uwa, ga kyau ga kudi, ga gayu da tsafta, ga Ilimi both boko da arabi ga kwakwalwa, gashi da aji wallahi, cike da k'osawa Deeyanah ta juya idonta tana fad'in " kai nidai naga ta kaina, kodai kodai... ta k'arasa maganar tana d'age mata gira d'aya, " wace ni kawata, wannan ai yafi k'arfin ajina, " tab wallahi ki daina fadar haka kika san me Allah zayyi, " hmmm banda dai anan, dan bakin wuta ba wajen wasan makaho bane, guntun murmushi Deeyanah tayi hadi da gyara tsaiwarta tace " Raleeya Rayuwa kamar kwai take bata da gaba ko baya balle wani yasan alkiblarta, ba kuma asan fuskarta ko keyarta ba, ba wanda yake da tabbacin dan tsako zai zama ko ko wainar kwai zai zama, duniya kamar mace mai ciki ce babu wanda yasan abinda zata haifa, Raleeya zata kuma magana Deeyanah tayi saurin cewa " dan Allah muje. *AJLAL....!* D'a d'aya tilo ga Alhaji Basaan da Hajiya Halimatu, Alhaji Basaan mutumin kirki ne ba laifi yana kwatantawa dai-dai gwargwado, yayinda Haliya Halimatu ta kasance bak'ar muguwa kuma azzalumar mace marar imani, shi kanshi Alhaji Basaan d'in ba dad'inta yake ji ba dan tafi k'arfinshi sai abinda tace kuma take so shi yake yi, tana iya kunyata shi gaban kowa, idan tana yi mishi fad'a da tsawa saika rantse d'anta ne, daga shi har ma'aikatan gidan mugun tsoranta suke ji, ta zama mijin ya zama matar, ko kallanshi tayi yasan abinda take nufi, a b'angaren jama'a kuwa mutuniyar kirki ce ga faram-faram da mutane, sai d'an abinda ba'a rasa ba, tana zaune da kowa lafiya amma a gida yadda kasan boss haka take, taita muzurai ita kad'ai, yayinda Ajlaal ya kasancewa mutum mai saurin fushi da bakar zuciya, idan ka b'ata mishi rai zayyi maka abinda shi da kanshi zai dawo yana nadama, babbar matsalarshi saurin hannu yanzu zai kai duka, kodan ya taso a sangarce a kuma shagwabe ne oho, tunda Ajlaal yake bai tab'a wayar gari ya nemi wani abu ya rasa a rayuwarshi ba, bayan wannan bashi da wani mugun hali, baya shaye-shaye, baya neman mata dan da d'an iska ne shi da an shiga uku yadda mata keyi mishi tururuwar kawo mishi tallar kansu, amma ko kallo basu isheshi ba yanzu zai dizgaki a gaban kowa, ya sha wulakanta mata wasu ma harda mari. Yauma kamar kullum tunda ya shigo makarantar mata ke kai mishi kokon bararsu akan soyayya, kusan mata uku ne suka tare shi suka sanar mishi suna sanshi, babu wacce ya amsawa a cikinsu sai dai ya wuce su yayi kamar bai ji su ba, amma deep down ya kawo iya wuya, ji yake kamar zayyi bindiga saboda takaici da bakin ciki, kwata-kwata baya san irin abun baya so, abun baya burgeshi, gani yake kamar rashin aji ne, rashin sanin darajar kai da karancin tarbiyya kesa mata su kawowa namiji tallar kansu. Yana tafe yana mita a zuciyarshi ya gama k'uluwa sosai, ya k'uduri niyyar duk yarinyar data sake k'ok'arin tsayar dashi ko tayi mishi magana, sayya kafa tarihi akanta wanda zai zamarwa wasu izzina, daga b'angare daya kaddara ta bud'e saban shafi a rayuwarsu ba tare da sun sani ba, " minti d'aya please Ajlaal zamuyi magana dakai, Raleeya ta fad'i suna k'arasawa inda yake, tsayawa yayi cak tare da runtse idonshi yana jin yadda tuk'ukin bakin ciki ke tasowa tun daga kasan zuciyarshi, "taimako nake nema daga gareka please ka taimaka man, Deeyanah ta fad'i cike da karaya, bayyi magana ba bare ya juyo, bata damu da yadda yayi musu ba, tunda ta samu labarin yana da girman kai, da yanga, abun bai wani dame ta ba, tunda ba alak'a take san k'ullawa dashi ba, assignment dinta kawai take san yayi mata, daga haka shikenan, k'ok'arin controlling kanshi yake san yi amma ya kasa, a tak'aice yace " a'a please, " dan Allah ka taimaka ka saurare ni, ba wani abu bane INA SAN KA KO.....!, loosing control yayi jin ta furta kalmar INA SANKA..., bai bari ta k'arasa fadar abinda take san fad'a ba ya d'auketa da marin daya sata kifawa, a fusace ya juyo tare da d'aga murya yace " enough ya isa please! Am tired from all your drama, stop it please, yadda yayi maganar cikin hargowa ya jawo hankalin dalibai, kan kace me an cika wajen makil, ya cigaba da cewa " bana sanku! ni kadai ne namiji a makarantar nan? "Ni kadai ne keda abinda kuke so? " Ni kadai ne nayi dai-dai da kalar namijin ra'ayinku? " Ya isa please! stop it right now, bana sanku bani da ra'ayin soyayya daku, haba abun ya isheni haka kowacce mace ni, kowacce mace tana so na, koma zanyi soyayya bada irin ku ba, balgaza, jaka mara sanin daraja da k'imar kanta, ya k'arasa maganar yana nuna su a wulakance, Raleeya dafe da kunci hawaye na gangaro mata ta kura mishi ido, bakin ciki ya hanata furta koda kalma daya, takaici ya hana ta yi mishi bayanin ba cewa zatayi tana sanshi ba, so take tace mishi INA SAN KA KOYA MIN ASSIGNMENT, amma ya datse maganarta ya tozartata ya wulakantata agaban dubban jama'a har da malamansu, cikin fushi Raleeya tace " kai! ba abinda muke nufi kenan ba, assign..... " quite, I said ya isa haka ban san sake jin koda kalma daya tak, yayi maganar yana nuna ta da yatsa while duk ilahirin jikinshi na kerrma, baya Deeyanah taja saboda yadda Ajlaal ya matso gaf da ita har suna iya juyo fitar numfashin juna, a hankali ta d'ago kanta ta kalli mutanen dake wajen, magana sukeyi sosai suna nunata harda masu zunbenta, da gudu ta juya tabar wajen had'i da fashewa da kuka, Raleeya ta nunashi da yatsa kamar zatayi magana sai kuma ta fasa tayi kwafa tabi bayan Deeyanah da sauri tana kwala mata kira, cike da halin ko in kula ya taka ya shige class babu damuwa balle nadamar abinda ya aikata a tattare dashi. Bata tsaya ba duk da kiran da Raleeya keyi mata, ta fad'a napep tana fad'in " muje...,! Napep din ya tada yana cewa " ina zan kaiki Hajiya? Bata d'ago kai ba ta bashi amsa cikin murya kuka, " Magajin Rumfa, bai kuma magana ba yaja suka tafi, Raleeya ta k'araso wajen tana fad'in " wait... wait ku tsaya, amma ina sun riga sun tafi, kanta ta tana sharb'ar kukan takaicin yau ita namiji ya disga a gaban mutane, har bakin get ya kaita, tun kafin ya ida tsayawa ta bashi 1000 ta sauko, me napep d'in na kwala mata kira kan ta amshi canji, amma ko takan canjin bata bi ba, da gudu ta shiga gida bata tsaya a parlour ba ta wuce bedroom dinta tare da rufe kofa ta fad'a saman bed ruf da cikin tare da saki saban kuka, saida tayi kwana uku bataje makaranta ba, sai a rana ta uku ne ta shirya ta tafi, tunda ta shiga makarantar kanta ke duk'e k'asa, koda wasa batayi gangancin d'agawa ta kalli kowa ba, duk inda ta wuce sai taga dalibai na nunata suna magana da dariya k'asa-k'asa, tafiya kawai take batare data san inda take jefa k'afarta ba, jinta take kamar tana tafiya a saman kayoyi duk ta tsargu, kamar daga sama taga gungun dalibai sun kai goma sun sha gabanta, cike da shakiyanci suna dariya guda daya daga cikinsu ya make murya yace " ina sanka.....! sauran suka had'a murya wajen cewa " aaahhh bana sanki, sai kace dole, suka dau ihuuuu gaba d'ayansu, batayi musu magana ba ta zagaye su ta raba ta wuce, suka bi bayanta suna ihuuuu, gabanta wani namiji yasha yana rangwada kamar mace ya yafa mayafi ya kalli wani dake gefenshi yace " ina sanka, fuska dayan ya bata had'i da yiwa dayan marin karya yace " bana sanki, banza ballagaza kawai, daya namijin mai mayafi ya durkusa yana yarfa hannu yace " bafa haka nake nufi ba, cewa zanyi ka koya man assignment, a tare sauran daliban suka dau ihuuu da shewa, batare da tayi musu magana ba ta wuce abinta ta shiga ta zauna a darare. Nasmah ta shigo da sauri ta zauna kusa da ita tana sauke ajiyar zuciya tace " ina ta nemanki a waya na rasa ki, takaitaccen murmushi Manassah tayi mata batare da tayi magana ba, Nasmah zatayi magana wani ya shigo yace " Manassah kizo inji HOD, kallan juna sukayi ita Nasmah kafin Nasmah ta kalli saurin tace " lafiya kuwa? " Ban sani ba, abinda na sani shine yace na kira ki, murmushin yake tayi tana fad'in ina zuwa, tayi maganar tana mik'ewa. Durkushe suke gaban HOD sai da ya dan dauki lokaci yana rubuce-rubuce a wasu file kafin ya rufe ya mayar da hankali kansu, ya dade yana kallansu tare da nazartar yanayinsu kafin ya cire farin glass din dake manne a fuskarshi wanda kallo zakayi mishi ka gane Medical ne, ajiyar zuciya ya sauke bayan ya gama kallansu yace " magana ta gaskiya kin bani mamaki Manassah, ban ji dadin abinda kika aikata ba, magana tabi ta cika makaranta kamar iska, me yakaiki da aikata wannan aiki? "Ba duka abinda muke so muke samu a rayuwarmu ba, abubuwa da dama muna hakura dasu saboda goben mu, saboda bamu san me gobe zata haifar ba, iya abinda ke rubuce a kaddarar rayuwarmu shine ya abinda zai same mu, masoyi ko makiya babu wanda ya isa iya sauya mana komai face abinda Ubangijin Sammai da Kassai ya zartar a rayuwarmu, kamar ke kinga kin b'ata goma daya bata gyaru ba, kin kai mishi tallar kanki baki samu biyan bukata ba sai wulakanci da cin mutunci, kodan darajar family ki da iyayenki bai kamata kiyi haka ba Manassah, hawayen da suka fara zubowa daga idonta tun daya magana ta goge tana fad'in " Malam kaima ka yarda zanyi hakan? "Ka yarda da abinda kowa ya yarda dashi? "Bayan babu wanda yake da tabbaci akan abinda ya faru, jita-jita da ji da jiyarwa ne irin ba mutanen wannan zamanin, wanda babu wani abu da suka iya ko suka kware akwai face yada alfasha da sharri, kage da abinda baka ji ba baka gani ba, sau da dama muna yin alkhairi da ayyukan kwarai amma ba'a fadarsu kadan kaddara zata sa kayi kuskure a soma yamadidi, wanda baiji ba, bai gani ba, baiga wanda yaji koya gani ba amma kaga ya zakalkale yana rantsuwa kamar agabanshi akayi, wallahi Malam ba abinda ya faru kenan ba, daga nan ta kwashe duk abinda ya faru ta sanar dashi, numfashi ya fitar yace " to yanzu idan ni na yarda na kuma san bazaki aikata hakan ba sauran mutane fa? Kanta ta dukar muryar na rawa tace " akwai Allah, sosai yayi musu nasiha mai ratsa jiki kana ya sallame su, tafiya kawai take batare data san inda take jefa k'afarta ba, ta bayanta wani ya rabo ya d'aga murya yace " ashe bamu bane kadai 'yan iskan ba? "Duk wanda ya samu dama zai dama, wani yayi caraf ya amshi " ah namu ne ya fito fili kuma gwara mu maza ne duk abinda zamuyi ado ne, wata mace tace " muma da muke matan bamu taba kai tallar kanmu an dizgamu ba, wanda yace yanayi damu dashi muke yi, " ana ganinsu kamammu na Allah ashe duk zamuce ta tadda muje mu, taku kawai aka fimu iyawa, da gudu tayi waje tana tare kukan daya ci k'arfinta da tafukan hannayenta, anan tabar jakarta da sauran kayanta Nasmah ta nuna su da yatsa tare da cije lebenta na kasa tayi kwafa, tace " kuji tsoron Allah ku tuna akwai ranar da zakuyi bayani a bisa ayyukanku. Napep ta shiga tare da bashi umarnin ya tafi, Nasmah ta k'araso wajen da sauri ta shiga cikin napep, sosai Manassah ke kuka wiwi tana fad'in, " na hak'ura da karatun na hak'ura da makarantar nan, daga yau bazan sake zuwa ba, na bar makarantar har abada, Nasmah da ke girgiza kanta tunda Manassah ta soma magana tayi saurin cewa " a'a karkiyi haka please, K'uduri yafi rayuwa mahimmanci, Idan har wancan kudirin alkhairi ne ga alumma to lalle zai zama ukuba ga masu neman tauyeki, rayuwa zata iya canja miki a cikin mintuna kalilan abinda kika Saba dashi zai iya sauyawa zuwa Wanda baki taba tunani ba, bakin ciki ko farin ciki, rashi ko samu, Allah yana jarabtar bawa ta kowanne fanni, ajiyar zuciya Manassah ta sauke tana cigaba da tsiyayar hawaye, Nasmah ta cigaba " akwai mafita idan har zakiyi, sai dai nasan ba lalle ki iya yi ba, da sauri Manassah ta kalle ta tana fad'in " wacce irin mafita ce? Kallan me napep din Nasmah tayi kana ta kalli Manassah tace " ki bari zanzo gida nayi miki bayani, sai dai akwai yiyuwar ba lalle ne ki iya aikatawa ba, hakan kuma shi kad'ai ne mafita, then ina tsoron na bud'e miki SIRRIN RAYUWATA, ki k'i yi, daga karshe ma ki guje min ko ki rinka man wani mugun kallan, har suka isa gida babu wanda yayi magana cikinsu, kowannensu da abinda yake sakawa cikin ranshi, ita Manassah tana mamakin kalaman Nasmah, cikin ranta tace " wacece Namsah? " meye sirrin rayuwarta da take tsoron bayyana min? Batare da tayi magana ba ta sauka daga napep din na shige gida Nasmah nayi mata magana bata juyo ba......! *Cigaban Labari....* Bata damu da yadda hawaye ya jik'a mata fuska ba, ta mik'e dakyar tana d'ingishi tabar cikin bolar, hanjin cikinta ya fara juyawa alamar yunwa take ji, yadda kasan mahaukaciya haka Deeyanah ke tafiya ba takalmi, kafarta duk faso ta tsatstsage jini na bin k'afar, kayan jikinta sunyi fata-fata sun yage, da bak'ar leda tayi dan kwali ta rufe gashin kanta, koda wasa batayi gangancin bi ta inda gawar mutanen daya kashe suke ba, danta tabbatar zuwa yanzu mutane sun cika wajen, ta baya ta zagaye tayi ta tafiya ga yunwa da k'ishirwa na azalzalarta, tayi tafiya takai ta awa biyu kafin takai bakin titi, jikinta na b'ari ta galabaita sosai harta manta da wacece ita, ta isa gaban wani shago muryarta sark'ewa tace " ru....ruwa Bakinshi a sake yake binta da kallo tun daga sama har k'asa, tunanin daya fara zuwa ranshi ko mahaukaciya ce, bayyi magana ba ya mika mata pure water, jikinta na rawa ta wafta a hannunshi cikin abinda bai wuce dakika biyu zuwa uku ba ta zuke ruwan tas ta yadda ledar, ta kara zuba mishi ido a karo na biyu, " baki k'oshi ba? Da sauri ta daga mishi kanta alamar eh, bayyi magana ba ya mika mata wani ruwan, ta amsa ta shanye duka, cike da tausayawa yace " kin koshi? "Kai ta daga mishi tana fad'in " Alhamdulillah, da sauri ya juyo ya kalleta yana mamaki dan har lokacin yayi tsammanin bata da hankali, " nagode tace tana barin wajen, yabi bayanta da kallo cikin ranshi yana mamaki mace har mace amma ta zata kamar tababbiya saboda yanayin rayuwa, tsaye tayi gaban mai saida doya da kwai, ta k'urawa doyar ido bata ko kiftawa, jikinta har rawa yake saboda matsananciyar yunwar dake azalzalarta, kallanta mai doyar yayi cike da k'ama yace " bar wajen nan, da ido kawai Deeyanah ta bishi batare dayi abinda yace ba, a tsawace yace " nace ki bar nan ko? Deeyanah bata motsa ba ta cigaba da kallan doyar, zayyi magana wani dake zaune yana cin soyayyar doya da kwai yace bata ta biyu, jin ace a bata yasata ta kalli Wanda yace abatan hawaye na gangaro mata tace " nagode sosai Bawan Allah, Ubangiji ya biyaka, ya amsa da Amin, me doyar ya d'ago kanshi ya kalleta yana fad'in " dama ba mahaukaciya bace ke? Cikin sanyinta ta d'aga mishi kanta, faranti ya cika da doyar ya hada mata da soyayyar kwai da k'undu ya mik'a mata, jikinta na rawa ta fisga ya kalleta cike da tausayawa, yadda take ci hannu baka hannu kwarya duk ilahirin jikinta na tsuma ya kara karya mishi zuciya, tas ta cinye ta mik'e mishi faranti bakinta cike da doyar tace " nagode, ya amshi faranti tare da mika mata ruwa, ta amsa ta tabi, titi tabi taita tafiya saida ta fita daga cikin mutane sosai sannan ta samu gindin bishiya ta zauna, ta sani duk rintsin da zata shiga bazata tab'a rasa mataimaka ba, saboda addu'ar da  mahaifiyata tasha yi mata, ta fashe da kuka data tuna yadda rayuwarta take a  baya, yadda ta taso cikin babban dangi da suke santa, ta taso cikin gata da kulawar 'yan uwanta, balle uwa uba  MIJINTA mai santa saboda Allah, wanda baya san ganin bacin ranta kona dakika daya, amma taci amanarshi tayi mishi butulci, duniyar tunani ta tsunduma tana tuno rayuwarta ta baya mai kunshi da haske da farin ciki. *WAIWAYE.....*Cikowar mutane Raleeya ta gani makil a harabar makarantar wanda yawancinsu d'alibai ne, kallo d'aya zakayiwa dayawa daga cikinsu ka fahimci suna cike da tsantsar mamaki, kutsawa ta farayi cikin mutanen dan ganewa idonta abinda ke faruwa wanda ya tara d'alibai har da Malamai haka, idonta ta zaro cike da mamaki gami da zallar tashin hankali, ganin AJLAAL BASAAN durk'ushe gaban DEEYANAH bisa gwiwowinshi, idanuwanshi cike da hawaye yana fad'in " KECE RAYUWATA DEEYANAH, KE KAD'AI NAKE SO, KI YARDA DANI, zan baki kulawar da wata mace bata tab'a samu daga wajen d'a namiji ba, zan soki sanda ba'a tab'a yiwa wata d'iya mace ba, zan tarayrayeki zan baki kulawa nayi miki alk'awarin bazan tab'a barinki cikin k'unci ba balle harta kai ga d'igon hawayenki ya zuba, wallahi tallahi billahil azim da Allah yayi umarni wani yayiwa wani SUJJADA dake zan fara yiwa SUJJADA, da ace bautawa wanin Allah ba laifi bane dake zan mayar abin bautata, saboda tsantsar soyayyar danake miki, da kisan kai ba babban laifin bane dana tsaga k'irjina na ciro miki zuciyata na d'ora ta a tafin k'afarki kin taka, naji labaran soyayya da dama, wad'anda suka faru a jinsi daban-daban a jin Larabawa akwai Lailah Majnun, a turawa akwai Romeo & Juliet, a indiya akwai Ram da Sita, amma duk cikinsu bana jin akwai wanda yakaini san abar sona, inaga mune zamu kafa namu tarihin a namu jinsin Deeyanah dan Allah ki taimakeni ki amshi k'ok'on barana karkice a'a, idan kika k'i karb'ata a matsayin masoyinki ina mai tabbatar miki anan take zan mutu, ya k'arashe maganar hawaye na zubo mishi, idonta ta juya had'i da yamutsa fuska ta nuna kanta tana fad'in " ni? "Ni Deeyanah kake so? "Ni Deeyanah daka gama tozartawa kaci mutuncinta ka wulak'antata a gaban mutane? Murmushi tayi tana cije lips d'inta had'i da cewa " da alama baka san me kake yi ba, baka san me kake fad'a ba, idan ma ka sani hala ka manta da wacce kake magana, idonta ya ciko da hawaye yana k'ok'arin zubowa juyawa tayi da nufin barin wajen, yayi saurin rik'e k'afarta gami da fashewa da kuka wiwi, " ki taimake ni dan Allah, ki tuna Allah yana san mutane masu yafiya, na sani na b'ata miki ban kyauta ba amma zan iya hukunta kaina a bisa laifin danayi miki, kanshi ya soma duka da duka hannayenshi da iya k'arfinshi had'i da buga kanshi a k'asa cikin k'ank'anin lokaci bakinshi da kanshi ya fashe, jini ya b'ata mishi jiki, cak ta tsaya tare da goge hawayen idonta ta taka zuwa gabanshi, ido ta kafeshi dashi na d'an lokaci kafin tace " ko zaka mutu, ko zaka kashe kanka bazan tab'a sanka ba, tsayawa cak yayi zuciyarshi na dokawa da tsananin k'arfin dake neman tarwatsa k'irjinshi baki ya bud'e da nufin yin magana ya kasa, harshenshi yayi nauyi, jikinshi a mace ya zube k'asa idanuwanshi suka soma rufewa da bud'ewa, dakyar yayi k'arfin halin kiran sunanta amma bata tsaya ba, ta cigaba da tafiya tana goge hawaye, duk kiran da yake mata bata saurareshi ba. Ido Raleeya ta murza ta bud'e ta kalli abinda ke faruwa danta tabbatarwa kanta gaskiya ne ko mafarki ne, baki bud'e mutane ke kallan abinda ke faruwa, Raleeya na kallan Deeyanah na tafiya amma saboda tsabar mamaki ta kasa abinta. Yau kam mamaki neman kashe kowa yake, bakin su duk ya mutu duk anyi tsit, dakyar Raleeya ta iya jan k'afarta tabar harabar makarantar, ta shiga motarta tayi gidansu Deeyanah. A harabar gidansu Deeyanah tayi parking ta fito da sauri ta shiga main gidan, a tsaitsaye ta gaida Ammi dan Allah Allah take taji yadda akayi, tana san ta tabbatar da abinda ta gani, Deeyanah na Sallah Raleeya ta shigo, ganin Deeyanah na sallah ya tuna mata batayi sallah ba, san jin kwakwaf ya mantar da ita, tana jin Deeyanah tace " Assalamu Alaikum tace " kawata ya akayi haka ta faru? Murmushi Deeyanah tayi tana cewa " Rayuwa idan babu k'alubale to babu nasara, idan kuwa akwai K'alubale to lalle akwai Nasara, a haka Allah ya tsara rayuwar, Cikin rashin fahimta Raleeya tace " kamar yaya ban gane ba? "Kina mamaki da ikon Allah ne? " Ko kina tunanin tashin dare da nake ina tsayawa bisa tafukana ina kai kukana wajen Ubangijina akan ya saka man zai tafi a banza? "Yaushe abin ya soma da har yayi nisa haka ban sani ba? Baki Deeyanah ta tab'e tana mik'ewa tace " tun last week ya fara bibiyata sama-sama abun bayyi tsamari irin this week ba, ajiyar zuciya Raleeya ta sauke tana rafka tagumi tace " to yanzu meye abinyi? "Me kuwa? Cikin zaro ido Raleeya tace " mak'iyinki ne fa? " Dan mak'iyina ne sai akayi yaya? "Masoyi da mak'iyi ina alfahari da kowanne daga cikinsu saboda kowanne akwai ranarsa haka yana da amfanin dazai yi min Makiyin? Amfani fa kika ce? "Hmmmm, Deeyanah tace gami da sauke ajiyar zuciya kafin tace " kwarai kuwa dan zan iya cewa amfanin makiyi yafi na masoyi, Cike da mamaki Raleeya kebin Deeyanah da kallo batare datace komai ba, " eh mana, saboda shi makiyi a koda yaushe kokarinshi yaga kuskurenka yayi ta yadawa danya aibataka a wajen mutanen da suke ganin k'imarka, batare dayasan yana gyara maka dabi'u da kurakuren rayuwarka ba, muddin kayi kuskure kaji an fada ka kuma gane kuskure ne bazaka kara maimaitashi ba, haka munafuki burinshi yayi abinda zai burgeka danka bashi yarda da amana, ya kara samun kusanci dakai shiyasa zayyi tayin abinda zai burgeka, babban amfaninshi zai rinka rage maka zunubi, ya kwashe daga kanka ya d'ibarwa kanshi, kinga duk mutumin da zai rage maka zunubi yayiwa kanshi kyautarshi shine masoyi, Masoyi na gaskiya kuma har abada ana tareshi dashi ba yardarka ko bashi amanarka yake bukata danya cutar dakai ba, haka bazai baka lu'u-lu'u, gwal, azurfa, gida ko mota da kudi ba, zuciyarshi da rayuwarshi zai baka, tashi gaskiyar da amanar, hadi da yardarshi zai baka. Raleeya zatayi magana Deeyanah tayi saurin barin d'akin tana fad'in " ke ni yunwa nake ji, dan tasan idan bata bar d'akin ba suna iya kwana Raleeya na damunta da tambayoyi kamar 'yar jarida. Bayan Deeyanah tabi tana fad'in dan Allah zo ki k'arasa labarta min labari kin sanni da san jin zance, suna zaune a dining suna cin abinci minti d'aya minti biyu sai Raleeya tace "unhunn namiji kenan ba kunya. *WACECE RALEEYA?* Iyayenta masu rufin asirin Allah ne, mahaifinta tsohon Malamin makaranta ne wanda yayi riyata shekaru 20 baya, sai 'yar sana'ar hannu da yake tab'awa, tunda Nasmah ta taso Allah yayita da son rayuwar k'arya da fafa, taso ace iyayenta masu kud'i ne amma kash, tasha tambayar kanta meyasa tazo a 'yar talakawa, shiyasa ta raina iyayen ba wani sosai take ganin mutuncinsu ba, idan suka saka ta abu saitaga dama zatayi kozasu kasheta bazatayi abinda bata so ba, da haka ta taso tana girma halayenta na k'ara girma while burinkanta na bunk'asa, cikin k'awayenta kaf ba 'yar talakawa duk 'ya'yan manyan masu kud'i ne, da bala'i ta saka kanta a private school dan tayi manyan k'awaye, acewarta wata k'ila ta samu d'aya daga cikin yayyan k'awayenta ya aureta ta shiga babban gida, aikatau ta samu take yi take biyan kud'in makarantar duk da iyayenta sunso hanata k'arfinsu datafi yasa suka zuba mata ido dole, had'i dayi mata addu'ar shiriya, sosai take jin kunyar ta nuna gidansu da iyayenta ga k'awayenta tana ganin k'ask'anci da ci baya ne, akwai wata 'yar uwarsu wacce da kakanta da kakan Babanta suke uba d'aya, tana auren babban mai kud'i idan k'awayenta zasu zo gidansu can take kaisu, kafin a hankali a hankali ta koma gidan Auntyn tata da zama gaba d'aya, itama Auntyn dayake 'yar abi yarima asha kid'a ce bata matsa mata ba, sai Raleeya tayi shekara 2 bata ga iyayenta ba amma babu abinda ya dameta ko'a jikinta, Auntyn Raleeya 'yar I don't care ce, ita ko 'ya'yanta na cikinta bata fiya sanin me suke ciki ba, abu d'aya ta mayar da hankali a kai shine MAGANIN MATA, wannan fa ko a China yake taje ta karb'o, ko a k'afa zata taka, ko mak'iyinta ya bata ganin mata zatayi mafani dashi, ta yadda da maganin mata sosai, ta d'auki dukkan yarda da yak'inin duniya ta d'ora akanshi gani take idan bashi ba rayuwa babu abinda zayyu idan babu shi, acewarta wai maza zuma ne sai da wuta k'asan mace shine martabarta mazan wannan zamanin babu abinda suka d'auka da daraja kamar jima'i gaban ki shine k'imarki a wajen mijinki dan sunfi san sex fiye dake, sunfi d'aukarshi da mahimmanci fiye da komai a aure, duk inda ta zauna maganarta kenan, bata da aiki sai had'a wancan gwamutsa wancan tasha, shiyasa tasu tazo d'aya da Raleeya dan duk inda taji me maganin mata zata siya ko nawa ne ta kawo mata, haka duk inda zata shiga ta nemo mata zata shiga duk had'arin dake wajen, duk da wad'annan halayen na Raleeya bata zina bata Lez. Raleeya na kitchen na dafawa Aunty Jamila tsumi, ta shiga hannunta rik'e da kofi tana sha, " me aka samu kuma yau? Raleeya ta fad'a tana juya tsumin, " kin san yau ba zama fa, yau zai daga abuja, shine kafin tsumin ya kammala na had'a kwakwa da dabino da kankana na markad'a na zuba zuma da madarar ruwa nake sha, dariya Raleeya tayi tace " Allah yasa dai yadda kike fama wajen k'ok'arin faranta mishi haka shima yake yi, dariya Aunty Jamila tayi batare datace komai ba, Raleeya tace " wai tsaya ma Abbah yana kai miki geji kuwa? Wani irin shu'umin murmushi tayi had'i da cewa " ke idan kika gammu a turaka saiki rantse da Allah kafuran farko ne wad'anda basu san Allah ba, dan zagewa mukeyi muyi duk wani kalar iskanci da kika san anayi a shinfid'a wani lokacin ma muna kallan BF muna yi. Kwashewa da dariya Raleeya tayi harda buga k'afa tana fad'in " ah kice wata rana zan lab'e nasha kallo, sukayi dariya suka tafa Aunty Jamila tace " aiko zaki ganowa kanki abinda ya girmi kanki. Sosai Ajlaal ya matsawa Deeyanah da rok'o akan ta kulashi ta taimaka ta so shi, duk inda tasa k'afa yana biye da ita ya zama tamkar inuwarta, ya susuce ya zare, gaban uban kowa durk'usawa yake yi a gabanta yana had'a ta da Allah, yadda kasan mahaukaci haka Ajlaal ya koma, saida takai ga ta daina zuwa makaranta ita abimma har tsoro yake bata har gaban malamansu bai jin kunya balle tsoro kuka kam yayi shi har ya gaji, saboda Deeyanah yak'i zana jarabawarshi ta k'arshe wacce daga ita shikenan ya gama jami'a, lokacin da labari ya iske Deeyanah sosai tayi mamakin abun, zuciyarta tayi rauni sosai, ta fara tausaya mishi, yayinda iyayenshi da Malamai sukayi tayi mishi fad'a, amma ina wanda yayi nisa baya jin kira Ajlaal kam yayi nisan da bai jin kira, ko cikin bacci bashi da abin kira sai Deeyanah abun kamar hauka hauka ko wanda aka jefa haka ya koma, tana zaune a cafeteria gaba d'aya hankalinta ya gama tafiya ga kallan wasu fararan tsuntsaye dake gabanta d'aya na bawa d'aya abinci ta bakinshi, firgigit tayi ta tsorata jin an rik'e k'afafuwanta, " yi hak'uri na tsorataki ko? Batayi mishi magana ba, sai k'ok'arin kwace k'afarta data shiga yi, gam ya rik'e k'afar da iya k'arfinshi yana rusa kuka tamkar wanda aka cewa uwarshi da ubanshi sun mutu, abinka da makaranta kan kace me wajen ya cika makil Ajlaal kwance rub da ciki ya rik'e k'afafuwan Deeyanah, wasu daga cikin d'aliban suka ciro waya suna d'aukar abinda ke faruwa, da ido Deeyanah tayi mishi alamar ya tashi amma yak'i, " bazaki sani abu nak'i yi ba wannan ma dan dole ne, kiyi hak'uri bazan tashi ba har sai kin bani amsa ta, Malamai da dama sukayi mishi magana yak'i tashi, akayi yin duniya yak'i tashi ya kafe sai Deeyanah ta bashi amsa zai tashi inba haka ba sai dai su kwana anan, Raleeya ta matsa kusa da Deeyanah tayi mata rad'a a kunne " ki amsa mishi kawai, da sauri Deeyanah ta kalle ta tana zaro ido, k'asa Raleeya ta sakeyi da murya tace " wallahi baki da wata mafita wacce ta wuce wannan, ki lallab'ashi ku rabu idan Allah ya had'aka da mahaukacin masoyi sai hak'uri, dakyar Raleeya ta shawo kan Deeyanah ta amince zata lallab'a Ajlaal, kallanshi tayi fuskarta d'auke da murmushi tace " tashi mu tafi, ganin karon farko tayi mishi murmushi yasashi saurin mik'ewa, " daga yau ka zama aboki na, kai ya girgiza yana fad'in " ba aboki nake san zama a wajenki ba, fiye da haka nake san zama, murmushinta ta k'ara fad'ad'awa tace " kayi hak'uri ka kwantar min da hankalinka, duk wata soyayyar dakaga ta kafa tarihi a duniya daga abota ta samo asali, kayi hak'uri mubi komai a sannu daga abotar sai kayi k'ok'arin siye zuciya ta, kaji ko? Tayi maganar cikin taushi cike da tausayawa, kamar k'aramin yaro ya mik'e yana d'aga mata kai, tun daga wannan rana Ajlaal da Deeyanah suka d'inke suka zama manyan abokanai, tamkar gum haka ya zame mata, bacci kad'ai ke rabasu yayinda k'arfi da yaji Ajlaal ya dawo da kanshi level 1, tun abun na bawa mutane mamaki har ya dawo bawa kowa tsoro, baijin maganar kowa sai tata, a hankali tausayin Ajlaal da Deeyanah keyi ya rikid'e ya fara zama SO, lokacin da mahaifinshi ya samu labari ba k'aramin tashi hankalinshi yayi ba, musamman da yaga videon Ajlaal durk'ushe gaban mace yana rok'on soyayyarta tamkar almajiri abin ba k'aramin b'ata ranshi yayi ba, fisgo Ajlaal yayi cikin zafin rai ya yarfa mishi zafafan marika biyu, da sauri Mama (mahaifiyarshi) ta mik'e bakinta bud'e cike da mamaki kasancewar wannan ne karo na farko da hakan ya faru a iya tsayin rayuwarta, "lafiya Alhaji...? Batare daya kalleta ba ya nuna mata yatsa, yana fad'in " karki soma tsumo bakinki cikin maganar nan, 'yan aikin tsaye sukayi suna kallan ikon Allah, yau Alhaji Basaan ne da tab'uka abun arziki a gidanshi haka, mutumin dako kara Hajiya Halimatu ta aje baya iya k'etarawa yadda kasan k'aramin yaro haka yake a wajenta labari ya cika unguwa da duk mutanen da suka sansu cewar ta mallakeshi, danko magana zayyi mata cikin girmamawa kanshi a duk'e yake mata, cikin hargowa Alhaji Basaan yace " kana da hankali kuwa Ajlaal ? "Kasan me kakeyi? "Kasan meka aikata kuwa? Ajlaal dake rik'e da kuncinshi yace " kayi hak'uri Abba wallahi ina santa itace rayuwata, yayi maganar hawaye na gangaro mishi, cikin rashin fahimta Hajiya Halimatu tace " wai me ke faruwa ne Alhaji? Wayar ya mik'a mata yana fad'in " kalli kiga abinda yayi kuma wannan bashi ne karo na farko ba, haka yarinyar tayi ta janshi a k'asa yana biye da ita kamar kare, babban abin takaicinma wai ya koma level 1 saboda ita, saurin d'ago kanta tayi ta kalli Alhaji kana ta mayar da kallanta ga Ajlaal tana yi mishi kallan tuhuma, kanshi ya sunyar k'asa hakan dayayi ya bata tabbacin abinda Alhaji ya fad'a gaskiya ne, hannun Alhaji ta kama ta zaunar dashi saman sofa, "inaga mafita d'aya kawai muke da ita akan abun nan, " wacce mafita? Cewar Alhaji Basaan yana binta da kallo, " a aura mishi ita, shiru Alhaji Basaan yayi na d'an wani lokaci kamar zai iya tab'uka wani abun kirki, " ya sunanta? Ajlaal dake tsaye kamar an dasashi ya kasa motsawa saboda wani irin mugun dad'in da yake ji tun daga takun k'afarshi har tsakiyar kanshi, ya rungume Hajiya Halimatu yana fad'in " nagode Mama nagode sosai, "sunanta Deeyanah d'iyar Malam Abduljalal ce, da sauri Alhaji ya mik'e yana fad'in " wanne Abduljalal d'in? A zabure Abba yace "Kar dai kace min Nakowa? "Shi Abba cewar Ajlaal , "to ikon Allah wannan ba sai anyi wani bincike ko b'ata lokaci ba, zan nemi mutane sai muje, murmushi Ajlaal yayi yana shafa kanshi yace " nagode sosai amma dan Allah aje da wuri, " zamuje da wuri amma sai kayi min alk'awarin zaka koma kamar da zaka koma Ajlaal Basaan d'in dana sani zaka koma level 4 d'inka, " in sha Allah Abba, har Ajlaal yakai bakin k'ofa Alhaji Basaan ya kira sunanshi cikin taushin murya "Ajlaal..!, jin yadda ya kira sunanshi yasashi juyawa cikin nutsuwa, " Lokaci da rayuwa suna da matuk'ar mahimmanci dan idan daya daga cikinsu ya kufce maka bazai taba dawo maka ba, kayi kokari ka amfanesu, ba shekara ba, ba wata ba, ba sati ba, ba kwana ko yini ba, ba awa ko minti ba dai-dai da dakika daya idan ta wuce daga rayuwarka bazata kara dawowa ba harka koma ga Allah, dan haka kasan me kayi a kowacce rana ta rayuwarka da zai amfane ka Duniya da Lahira, fata, buri da mafarki duk abu d'aya ne, kuma kowa yana da nasa, yawan burikanka yawan jajircewarka, karka bari shirme da shiririta su cinye kaso mafi yawa a rayuwarka, ya kamata kayi abinda zaka amfana kuma al'umma zasu amfaneshi, wanda zaka ci moyarshi duniya da lahira, murmushi Ajlaal yayi tare da jinjina kanshi yace " nagode sosai Abba in sha Allah zanyi amfani da abinda ka fad'a min. Daya shigo makaranta farkon abinda yake fara yi shine nemanta, in banda ma tayi mishi gargad'i da fad'in " karka soma gangancin zuwa gidan mu duk ranar daka sake kaje gidanmu nasan daga ranar bazaka sake ganina a rayuwarka ba dan cire ni za'ayi daga makaranta ayi min aure. Murmushi yayi yace mata " dako saina addabi ahalinki da mijin daya aureki, da kice mace ta farko a duniyar musulunci da zata fara kasancewa matar maza biyu dan kuwa ko kinyi aure ke tawa ce ni kad'ai Deeyanah, tana d'aukar kalamanshi da wasa dan haka bata tab'a basu mahimmanci ba. Yauma yana shigowa department d'insu ya wuce tana zaune cikin aji ana yi musu lecture's yayi sa'a tana dai-dai window dan haka yaje jikin windon ya tsaya yana kallanta, cikin sa'a ta d'ago ta kalli windon suka had'a ido, tayi mishi murmushi shima ya mayar mata da martanin murmushi, a hankali cikin rad'a-rad'a yace " yaushe zaku fito? Itama cikin rad'a-rad'ar ta bashi amsa da " nan da minti 30, dayake dama ya saba idan zata kwana tana lectures sayya jirata duk dad'ewar da zatayi baya damuwa, ya koma gefe ya zauna yana jiranta. "Deeyanah me nace? Malaminsu ya tambaye ta saboda ya lura da abinda take yi, " na'am Malam! Ni? "Eh! Ke me nake cewa yanzu? Kame-kame ta soma yi, "fito nan, Malamin ya fad'a yana kafe ta da ido, cikin sanyin jiki ta fito gaban allo,  alli ya mik'a mata yace " ungo maza k'arasa mana bayanin tunda naga kamar kin riga kin sani, bata karb'i allin dayake mik'o bata ba tace " kayi hak'uri dan Allah Malam. "Dama soyayya da kula-kulan maza iyayanki suka turo ki yi makaranta? "Arahar taki har takai haka? "Gaskiya banyi zaton kina da sauk'in samu haka ba wall...... Tasssss! Tassssss! Ajlaal ya d'auke shi da gigitattun marika masu k'arfi, ya shak'i wuyanshi yana huci ya d'aga shi sama " idan mahaifiyarka ko matarka da 'yarka ta cikinka da k'anwarka aka fad'awa ya zaka ji? " Suma fa 'ya'yan wasu ne, k'annan wasu sannan wata rana zasu zama matan wasu har su kai ga zama iyayen wasu, ya buga shi da k'asa zai rufe shi da duka Deeyanah tayi saurin shiga tsakiya tana zubar da hawaye tace " ka kyale shi dan Allah. Hannunshi ya dunk'ule had'i da nausar iska kana ya rik'o hannunta suka fice daga ajin, ko ba'a fad'a mata ba tasan Ajlaal akwai bak'ar zuciya ji yadda jijiyoyin kanshi sukayi rad'o rad'o idanuwanshi sukayi jajir kamar gauta, bayyi mata magana ba ya bud'e mata gaban motar ba musu ta shiga ya mayar ya rufe ya zagaya ya shiga, ya figi motar da k'arfi ya tada k'ura. A bak'in get d'in Estate d'insu yayi parking bayyi mata magana ba ya bud'e ya fita ya zagaya ya bud'e mata, cikin sanyi jiki ta fito, tayi tsaye tana kallanshi kamar zatayi magana sai kuma ta fasa tasa kai zata shige ciki "kiyi hak'uri please! ya fad'a cikin sanyin murya, cike da mamakin hak'urin da yake bata na miye ta juyo, murmushi ya sakar mata yaja motar ya tafi batare da yayi mata magana ba, tabi bayan motar da kallo tana murmushi tace " rigimamme!. Washe gari kusan a tare suka shiga makaranta, suna wajen me siyar da gurasa ita da Raleeya ya k'araso wajen, kallo d'aya tayi mishi ta kawar da kanta tana fad'in " zaka ci gurasa band'ashe? "Kin cika baki kina yi man tayin rowa wai zaka ci, to ban ci, dariya tayi gami da kallan me siyar da gurasar tace " ka had'a mishi special. Ya soma cin gurasar kenan aka aiko kiransu shida Deeyanah, kallan juna sukayi kana ya mayar da kallanshi ga wanda aka turo yace " kace muna zuwa, hankalinshi kwance yadda kasan babu me jiranshi ya gama cin gurasar, "muje mana, a nutse ya mik'e suka jera har office d'in, Malamai suka gani birjik da gani meeting suke yi, da sallama a bakunansu suka shiga, ganin yadda Malaman suka tsatstsare su da ido yasa Ajlaal murtuke fuska murtuk kamar wanda akayiwa sammacin mutuwa, sai da ta d'an rusuna kana ta gaida Malaman suka amsa ba yabo ba fallasa, while shi yana daga tsaye yace " ina yini? Daga haka bai k'ara ba, kad'an daga cikinsu ne suka amsa, HOD su yayi gyaran murya had'i da cewa " wai meke faruwa daku ne? "Meke damunku? "Meke yawo cikin kanku? "Fisabilillahi abinda kayi ka kyauta kenan? Cike da gwarin yace " me nayi Malam? Cikin zafin rai ganin yana neman rena musu hankali d'aya daga cikin Malam yace " kai ka shiga taitayinka  duk cikin mu nan babu sa'anka balle ka rena mana hankali, ido ya zubawa Malamin ya tsare shi da ido yana yi mishi kallan ka shiga hankalinka. "Kasan wannan? HOD ya fad'a yana nuna mishi Malamin su Deeyanah daya mara, "eh! yace kai tsaye cikin rashin tsoro. "Meya had'aka dashi? Tsayyuwarshi ya gyara  kana cikin isa yace "Abun rashin kyautawa yayi ni kuma na gyara mishi, ya fad'awa 'yar wani, k'anwar wani, matar wani kuma mahaifiyar wani maganar da bata dace ba wacce idan aka fad'awa mahaifiyar shi ko k'anwarshi ko matarshi da 'yar shi sai inda k'arfinshi ya k'are, shiyasa nima na nuna mishi rashin dacewar hakan a aikace bada baki ba. Kwafa d'aya daga cikin malaman yayi had'i da girgiza kanshi, Ajlaal yayi mishi kallan iyakacin nan amma bazan daku ba. HOD yace " fad'a min abinda ya faru in details, tun daga farko har k'arshe ya komai ya fad'awa su HOD babu abinda ya b'oye har dukan da yayiwa Malamin sai da ya fad'a. A zafafe d'aya daga cikin Malaman yace " kai ina ruwanka a cikin maganar? "Meka had'a da ita k'anwarka kome? A rene ya kalli Malamin yace " matata ce ko kai akwai wanda zayyi b'atanci ga matarka a gaban idonka kayi shiru? "Lusarin namiji shashasha wanda bai san mutunci da k'imar kanshi ba shine wanda za'a ciwa matarshi mutunci a gaban idonshi tsoro yasa yayi shiru saboda tsabar rashin sanin ciwon kai...... Dakatar dashi HOD yayi ta hanyar d'aga mishi hannu kana yace " ka bashi hak'uri shikenan komai ya wuce dan kyautawa bai kyauta ba shima. " In bashi hak'uri akan me? "Me nayi na rashin dacewa da zan bashi hak'uri, shiya kamata ma ace ya bata hak'uri agaban mutunen daya muzanta ta, a d'an hasale HOD yace " nace ka bashi hak'uri ko? "Kayi hak'uri Malaman ina ganin mutuncinka sosai amma gaskiya bazan iya bashi hak'uri ba, babu juyin duniyar da ba'ayi da Ajlaal ya bawa Malamin nan hak'uri ba amma ya lashi k'asa ya dire ya k'i fur. "To shikenan tunda bazaka bashi hak'uri ba, kayi taurin kai kuma ka kafe duk da bamu ce saika koma cikin class gaban d'aliban daka mareshi a gabansu ba amma shine ka turje kak'i bin umarnin mu duk da munso muyi masalaha cikin salama dan haka mun yanke mu dakatar dakai har lokacin daka yanke ka bashi hak'uri, cikin tafasar zuciya ya bud'e baki zayyi magana tayi saurin rik'e hannunshi. Hannunshi data rik'e ya kalla yana jin yadda bugun zuciyarshi ya k'aru da kaso 70 ido ya zuba mata batare daya iya furta komai ba, a hankali ta girgiza mishi kanta alamar a'a kana ta motsa labb'anta cikin sanyi tace " ka bashi hak'urin please. Ido ya runtse da k'arfi, bashi da yadda zayyi bazai iya yi mata musu ba amma banda ita da idan duniya zata tashi bazai bashi hak'urin ba, idonshi a runtse yace " kayi hak'uri. Ido ya k'ifta gami da cewa " eye! banji me kace ba fa, hannunshi dake cikin nata ta k'ara damk'ewa tana rad'a mishi please a kunne, idanuwanshi ya bud'e ya sauke su akansu sai da gabanta ya fad'i ganin yadda suka canja launi zuwa asalin jajaye, " kayi hak'uri. "Nifa bana jinka, in zakayi magana kayi da sigar rok'o ba kana magana kamar kana bani umarni ba, kayi magiya Malam, ka rok’e ni, idonshi ya sake runtsewa da tsananin k'arfi kana ya d'an d'aga murya yace " kayi dan Allah, sai a lokacin Malamin ya sauke ajiyar zuciya kana ya d'ora da " bakomai dama ni ban k'ulla ce ka ba, HOD yayi musu 'yar nasiha akan rayuwa, tayi mishi godiya dan shi ko kalma d'aya bai tsinta ba cikin nasihar saboda tsabar zafin zuciya. Suna fitowa su HOD suka rufarwa wannan Malamin da fad'a dan bayyi dai-dai ba. Har bakin get ya kaita ta shige gida, shi kuma ya wuce bai nemeta sai dare ya kira wayarta tana zaune kan sallaya wayarta ta soma ringing bata amsa kiran ba sai ta shafa addu'ar, "an huce kenan? "Au da fushi nayi? "Sosai ma kuwa, wai dama haka kake da bak’ar zuciya? “Anya zakayi saurin yafiya kuwa!? Kwashewa yayi da dariya sosai yace “ me kike nufi? “Ai gani nayi cikin d’an lokaci ka canja har kalar idonka ma saida ta canja kala anya da a zamanin su fir’auna da Abu Jahil kazo zaka karb’i musulunci kuwa? Dariya ya kuma yi sosai har da buga k’afa had’i da cewa “ ai zuciyar bata kai nan ba, waya sukayi sosai kana sukayi sallama. *America....* Kwance yake saman kujera idanuwanshi lumshe dukda kasancewar ba bacci yake ba, abin duniya ya isheshi, tunda ya taho ko a waya baiji Deeyanah ko sau d'aya ba, baiji halin da take ciki ba, muskutawa yayi ya gyara kwanciyarshi yana fad'in " gaskiya nayi k'ok'ari wata shida kenan fa ban ganta ba banji daga gareta ba, k'arar shigowar sak'o dayaji a wayarshi yasashi jan d'an guntun tsaki yana d'aukar wayar, a Arewa Youth's Achievers group yaga alamar an turo sak'on, group d'in daya had'a manyan matasan Arewa da suka zama wani abu a rayuwarsu, Ajlaal ne kad'ai wanda baya aiki, kuma d'alibi a group d'in, shima dan ana saka ran gobenshi mai kyau ce, shiyasa aka saka shi, gashi da kwakwalwa da hazak'a gami da nacin karatu, kuma yana bada gudunmawa sosai a group d'in dan sau da dama za'a bawa masu yin master Assignment su kasa sai Ajlaal ne zai koya musu, sak'on da aka turo Deen ya karanta _" d'aya daga cikin Member d'inmu na wannan group Ajlaal Basaan wanda ba b'oyayye bane anan, kowa ya sanshi,_ _ya fad'a soyayya da wata yarinya, a makarantarsu bayan ya ci mutuncinta ya ci zarafinta ya muzantata ya tozartata ya wulakantata,_ _daga k'arshe Allah ya jarrabeshi da matsananciyar soyayyarta,_ kamar ya share sai kuma yayi playing videon da aka turo, baki ya tab'e had'i da cewa " sharmeee zambur ya mik'e tsaye kamar an tsikare shi, bakinshi bud'e cike da mamaki gami da tsoro ganin Deeyanah ce........Take jikinshi ya d'auki rawa da kerrrma yana tsuma, komawa yayi ya sake duba rubutun da akayi a k'asan videon, "meke faruwa ne? "Meya had'a Ajlaal da Deeyanah? "Me tayi mishi daya wulakantata yaci zarafinta? "Ya akayi ni duk ban San wannan na faruwa ba? "Ina nan ina zaton bani da matsala da ita, ina tunanin ina da yak'ini akanta, yayi maganar yana dafe da kanshi, kanshi ya d'aga alamar tunani ya dad'e a haka kafin ya sauke ajiyar zuciya a karo na ba adadi, mik'ewa yayi ya shiga bedroom d'inshi da sauri, kayanshi ya shiga had'awa cikin gaggawa a trolley, ko wanka bayyi ba ya saka kayanshi ya jawo trolley, ma'aikatan gidan yabarwa sallahun zaije ganin gida bazai dad'e ba zai dawo, su kula da gidan, direct airport ya nufa, yasha wuya sosai kafin su bashi ticket, sai da yayi musu k'aryar mutuwa akayi mishi, k'arfe 12:30 na dare ya sauka a Nigeria, jirgin sama ya hau daga Abuja zuwa Kano, bai shiga gida ba sai 5:00 na safe, babu wanda ya gayawa yana tafe dan haka babu wanda yasan da zuwanshi, d'akinshi ya wuce saboda damuwar dayake ciki bai ko cire kayan jikinshi ba ya kwanta, Allah Allah yake gari ya k'arasa wayewa. Da sauri ta fito tana duba agogon hannunta, bata kula ba saiji tayi, tayi karo da abu, da sauri ta d'ago kanta tana ja baya cike da tsoro, ganin Imran ba k'aramin mamaki ya bata ba, wanda ta kasa b'oye mamakinta ya fito ya bayyana k'arara saman fuskarta, " mamakin na meye? Ya fad'a yana k'are mata kallo, hannuwanshi sark'e a k'irjinshi, murmushinta ta fad'ad'a wanda ya bayyanar da kyawawan hak'oranta, " laaaa! Yaya yaushe kazo? Tsaiwarshi ya gyara had'i da jefa idonshi cikin nata ya dad'e yana kallan kwayar idonta kafin ta sunkuyar da kanta k'asa, dan bazata iya jurewa kallan kwayar idonshi ba, kamar daga sama taji yace " waye Ajlaal? "Meye alak'arku dashi? Da sauri ta d'ago kanta ta kalle shi cike da tsoro da zallar tashin hankali, idonshi kanta ya tsuke fuska babu alamun wasa ko dariya yace " ya akayi? "Kina mamakin yadda akayi na sani ne Deeyanah ? Kanta ta duk'ar cikin sanyi dukta dabarbarce ta rasa abinda zatace mishi, saboda yadda ya kafe ta da ido " fad'a min abinda yake tsakaninku? Kanta k'asa ta kwashe komai ta fad'a mishi tun daga farkon zuwa k'arshe, Deeyanah bata tab'a sanin Deen yana da bak'ar zuciya ba, sai yau, jikinshi har rawa yake, jijiyoyin kanshi sukayi rad'o-rad'o idonshi yayi jajir kamar gauta, " saboda ya mayar dake teddy kuma 'yar tsana wacce zai juya yadda yake so, wacce zai d'auka sanda yaga dama ya aje lokacin dayaga dama bayan ya tozartaki cikin mutane sannan ya dawo yana miki kukan munafurci wai yana sanki saboda yafi kowa iya game? " Ko an fad'a mishi kowa irinshi ne? "An fad'a mishi kowa sakarai ne? Yayi maganar a zafafe cikin b'acin rai, " wallahi saina nuna mishi yayi kuskure saina nuna mishi nafishi zafin kai, ya k'arasa maganar yana rik'o hannunta yana tafiya, ganin yana nufar mota da ita yasata kalleshi tana fad'in " ina zamuje Yaya? Maimakon ya bata amsa sayya bud'e gaban mota yace " shiga!, taso tayi mishi musu amma ta kasa saboda yanayin fuskarshi ya tsoratata, yadda ya figi motar kad'ai ya isa ya tabbatar maka yana cikin b'acin rai, hannunta ta d'ora saman nashi cike da tsoro tace " Yaya ka kai gudun motar k'arshe fa, ko kallanta bayyi ba ya cigaba da mugun gudu da motar, sosai gabanta ke fad'uwa, tashin hankali da fargaba ne suka shigeta lokaci d'aya dataga ya shiga get d'in makarantarsu, sai yanzu ta fahimci abinda yake shirin yi, tasan halin Ajlaal sosai kamar yunwar cikinta haka tasan halin Deen, tasan ba k'aramar b'acacciya za'ayi ba muddin suka had'u, a tsorace ta fara girgiza kanta kwalla na taruwa a idonta tana fad'in " a'a Yaya, dan Allah karkayi haka wallahi Ajlaal yana da bak'ar zuciya shima, idan kaje komai yana iya faruwa, birki ya taka k'uuuuuu, in banda dokawa babu abinda k'irjinshi keyi, ita kanta dake kusa dashi tana iya ganin yadda k'irjinshi ke sama da k'asa, cike da tsoro ta d'ora hannunta saman nashi tace " please Yaya, kujera ya kwantar ya kwanta tare da lumshe idonshi, tunda motar Deen ta faka a kan idon Ajlaal bai damu da yasan wanda ke cikin motar ba dan halinshi na shareya yana nan, " kina sanshi ko? Deen yayiwa Deeyanah tambayar, idonta dake cike da hawaye ta bud'e tarr ta kalleshi, yadda kasan bashi yayi maganar ba, Ajlaal dake zaune ya mik'e ya nufi class da nufin dubawa ko Deeyanah ta k'araso, dan ya kirata yafi so ba adadi ba'a d'auka, yana tafiya yana dialing number, bugun da zuciyarshi keyi da k'arfi ya tabbatar mishi Deeyanah na kusa, dafe k'irjinshi saitin zuciyarshi yayi, yana murmushi had'i da kara wayar a kunne, dai-dai lokacin da zai wuce ta kusa da motar da Deeyanah ke ciki, wayarta ta soma ruri, harya gota motar ya tsara cak danko a mafarki yaji k'anshinta da ringing wayarta zai gane, a hankali Deen ya bud'e idonshi ya zuba mata su, wayar dake faman rori ya kalla kana yace " pick it, kanta ta girza mishi hawayen dake idonta suka samu damar gangarowa saman kuncinta, "nace ki d'aga ko.....? "Ko saina...! knocking window da akayi ya katse mishi maganarshi, yasan Ajlaal Basaan sama-sama a group d'insu, shiyasa bayyi wani wahalar ganeshi ba, yadda yake kallan Deeyanah yana murmushi tana mayar mishi da martanin murmushi yasa wani k'ululun abu tokare mishi mak'ogwaronshi, idanuwanshi suka sake rinewa ya rasa abinda keyi masa dad'i a duniya, can k'asan mak'oshinshi yace " nayi sake, da yalwataccen murmushi a saman fuskarta ta kalli Deen tana fad'in " Yaya ga Ajlaal, bayyi niyyar fita ba amma yadda Deeyanah tayi mishi da yadda Ajlaal ke buga masa glass d'in mota suka k'ara hasala shi, bayyi magana ba ya bud'e motar ya fita, ya zagaya inda Ajlaal ke tsaye had'i da hard'e hannuwanshi a k'irji, yana k'are mishi kallo from head to toe yace " yadai Malam kake bugawa mutane mota? Murmushi Ajlaal yayi yana mik'awa Deen hannu yace " ina yini? "Alhamdulillah, cewar Deen batare daya mik'awa Ajlaal hannun ba, kallan Deeyanah yayi yana murmushi had'i da cewa " fito man...., bai k'arasa maganar ba ganin hawaye a idonta da sauri ya zagaye Deen ya fara k'ok'arin bud'e motar, Deen na daga inda yake ya dannawa motar key, ya tsaya yana kallan Ajlaal , " please ka bud'e ta kuka fa take, bai motsa ba balle yayi magana, cikin hargowa Ajlaal ya nufi Deen yana fad'in " nace ka bud'eta ko baka ji abinda nace ba? Still shiru Deen yayi yana bin Ajlaal da ido, cikin matsanancin b'acin rai Ajlaal yaci kwalar Deen had'i da dunk'ule hannu zai kai mishi naushi, " no! Ajlaal Yaya na ne, Deeyanah ta fad'a hankalinta a matuk'ar tashe, motar ya daka da k'arfi, har yaji ciwo, juyawa yayi yana shafa kanshi kafin ya dawo ya had'e hannunshi alamar rok'o yana fad'in " dan Allah!, rigarshi ya gyara inda ya ci kwalarshi fuskarshi d'auke da murmushi yace " bata fad'a maka a kaf zuri'armu bamu auren bare ba? " Sai dai idan Allah bai bawa mutum ba, amma idan Allah ya bashi babu mahaluk'in daya isa ya hana, hannu Deen ya d'aga mishi gami da cewa " ya isa, ni bana ja da hukuncin Allah, bawai mace tana buk'atar namijin dazai mutu dominta bane kad'ai, a'a tana buk'atar namijin dazai rayu dominta ne, wanda zai k'arfafi musuluncinta da imaninta wanda zai jagoranceta izuwa Aljanna cikin Aminci da yardar Allah, haka mafi girman arziki mutum ya dace da abokin rayuwa, wanda ya damu da kyautatawa rayuwarshi na duniya da lahira, ka sani kasa a ranka cewa nine mijin Deeyanah da izinin Allah, in sha Allah bata da mijin daya wuce ni Deen, kuma yau-yau d'innan ba sai gobe ba, za'a d'aura mana aure, ta zama mallakina halaliyata, bai jira abinda zai ce ba ya wuce yabarshi nan tsaye, da ido Ajlaal yabi Deen maganganunshi nayi mishi yawo aka, kafin Deen ya k'arasa ga motar Ajlaal ya rigashi hannunshi dake zubar jini wanda ya bugi motar dashi, dashi ya naushi window'n glass d'in motar, ya rik'o Deeyanah, cak Deen ya tsaya yana bin hannun Ajlaal inda daya rik'e Deeyanah da kallo, zuciya ta kawoshi har wuya kamar namijin zaki haka yayiyo kan Ajlaal, cikin matsanancin kuka Deeyanah tace " a'a dan girman Allah karka tab'a shi please, ido ya runtse da k'arfi kana ya bud'e su a lokaci zuciyarshi kamar zata tsage gida biyu, ji yake kamar ya cinnawa duniya wuta kowa ya huta, Ajlaal ya zagaye yq bud'e motar ya shiga had'i da figar motar yabar harabar makarantar, Ajlaal yabi bayan motar da mugun gudu kamar zararre yana kiran sunanta, baya ya dawo da gudu ya nufi inda yayi parking motarshi ya shiga ya figeta ya rufa musu baya. Ta window ta hango Ajlaal na binsu, jikinta ya d'auki rawa dan duk abinda ke faruwa tsakaninta da Ajlaal babu wanda ya sani a gida, hannunta saman na Deen ta rik'eshi gam, cikin muryar kuka tace " karka kashe mu Yaya ka tafi a hankali please, kawar da kanshi yayi gefe aiko idonshi ya sauka akan wata mota dake biye dasu da gudu kamar hauka, ko ba'a fad'a mishi ba yasan Ajlaal ne, low yayi da motar sosai ya soma k'ok'arin gangarawa gefen titi, kuka ta saka mishi tana rok'onshi karya tsaya, yaso ya tsaya amma yadda ta take rok'onshi yasashi ya taka motar, bai sausauta motar ba saida suka isa gida, mai gadinsu yayiwa kashedi da fad'in " karka sake ka bud'ewa kowa get duk wanda yazo karka sake ka barshi ya shiga matuk'ar ba d'an family bane, cike da mamakin kashedin da Deen keyi mishi ya d'aga kanshi dan hakan bai tab'a faruwa a tsakaninsu ba, sama da shekaru 20 yana yi musu aikin gadi, tsakanin Deen da ma'aikatan gidan sai kyautata da sam barka shi bai ma shiga harkar da bata tashi ba, ko a danginshi ne, parking yayi a inda aka tanada dan aje motoci, ya kifa kanshi saman sitiyari yana sauke ajiyar zuciya, a sanyaye tace " kayi hak'uri please Yaya, kanshi ya d'ago ya zuba mata ido na tsayin lokaci, " kayi hak'uri..... da sauri ya katseta da cewa ki rik'e hak'urinki bana so Deeyanah, Tunda aka haife ki, kika bud'e ido kika ganni a rayuwarki Deeyanah, baki san yaushe ne ba, baki san ya akayi ba, kedai kawai kin bud'e idonki a duniya kin ganmu tare, amma ban tab'a, tab'a koda d'an yatsanki bane balle jikinki ba, saboda bashi ne a gabana ba, ked'in ke kad'ai nake so Deeyanah, saurin d'ago kanta tayi ta kalleshi yanayin kallan dayake yi mata yasata saurin duk'ar da kanta k'asa cike da kunya had'i da mamaki, " eh Deeyanah ina sanki iya tsayin rayuwata na rayu ne da sanki, ban fad'a miki bane saboda ina tunanin bani da matsala da hakan, cikin sanyi ya rik'o duka tafukan hannayenta cikin nashi tare da tausasa muryarshi yace " kece rayuwata, ina da tabbacin babu wani haluk'in da zai miki irin san danake miki, a shekarunki bazaki tantance so, k'auna, soyayya ko sha'awa ba, wad'annan k'ananan samarin da kike gani duk ba aure ne a gabansu ba, yaudara da lalata 'ya'yan mutane ne a ransu, idan kin bani dama a yau a yanzu zan aureki, a yau zaki zama mallakina Deeyanah, amma idan baki yarda ba shikenan duk k'ok'arina ban isa na wuce iyakar abinda Allah ya rubuta zan samu ba, hannunta ya saki ya juya da nufin fita daga cikin motar da sauri tace " dan Allah Yaya karka fad'i abinda ke faruwa a gida, guntun murmushi yayi tare da k'arasa ficewa, wajen 11:30 na safe abun ya faru, dan haka yasan gaba d'aya iyayensu na gida, babban parlour'n gidan ya wuce, ya tarar da kowa a ciki harda kakanninsu, cikin girmamawa ya duk'a ya gaidasu, cike da mamaki suka amsa mishi Babah ya d'ora da cewa " saukar yaushe Son? Kanshi k'asa yace " yau Babah, " lafiya dai ko irin wannan zuwan bazata haka? Murmushi yayi had'i da shafa kanshi yace " dama maganar auren mu ce ta taso, kafin Babah yayi magana mahaifinshi yayi saurin cewa " aurenku kuma? " Kai dawa? Cike da kunya kanshi k'asa yace " dama na dawo ne ayi auren sai mu koma tare, " wai kai da wa? D'an shiru yayi yana sosa k'eyarshi, " wai da wa? Abbi ya fad'a yana kallanshi, cikin in ina yace " Dee....ya...nah yana k'ara duk'ar da kanshi k'asa, " Deeyanah? "To kun dai-daita kanku ne koyaya? "Eh! Abbi, mun gama magana, da so muke a d'aura auren yau, sai mu tafi gobe ko jibi, " kasan me kake cewa kuwa Deen? "An fad'a maka maganar aure maganar yanzu-yanza ce? " Ko an fad'a maka ana yiwa aure gaggawa? " Sabo.....! shigowar Deeyanah yasa Abbi yin shiru, da kallo duk suka bita, ko ince kallan tuhuma dan kallo d'aya zakayi mata ka fuskanci taci kuka, ga jikinta dake rawa hakan yasa suka fahimci akwai wani abu a k'asa kuma akwai rashin gaskiya a tattare da ita, yadda kowa ke jifanta da kallan tuhuma yasa tayi saurin kallan Deen tsoronta na bayyana a saman fuskarta tsammaninta ko Deen ya fad'a musu abinda ya faru tsakaninta da Ajlaal, a d'arare ta raba kusa da Deen  ta zauna had'i da b'oyewa a bayanshi, " hakan da kikayi kina ganin ya fiye miki? Abbi ya fad'a yana samun tabbacin akwai abinda ke faruwa, kuka ta saka tana fad'in " dan Allah Abbi kuyi hak'uri wallahi sharrin shaid'a....., saurin d'ora hannunshi yayi saman nata tare zare mata ido yana girgiza mata kai, alamar bai fad'a musu abinda take tunani ba, ajiyar zuciya ta sauke da k'arfi, duk abinda ya faru akan idon iyayensu, Babah ya kalli Abbi da iyayensu wato kakaninsu Deen, kowa yasan akwai wani abu, akwai abinda ya faru, musamman da Deeyanah tace " sharrin shaid'an ne, Abbi zayyi magana suka jiyo kamar hayaniya a harabar gidan, da sauri duk suka mik'e suka fita, a harabar gidan suka iske ana kokowa haik'an da Ajlaal da ma'aikatan gidan, wani irin mugun tsoro da rikici ne suka shigeta sauran kad'an fitsari ya kwace mata, " lafiya? Babah ya buk'ata yana bin Ajlaal da kallo, gashi dai tsaf bashi da wata alama ta hauka ko motsuwar kai, " k'aramin me gida ne yace karmu bari kowa ya shigo muddin ba d'an family bane, da wannan abokin Deeyanah yazo na hanashi shine yasa mun k'arfi ya shigo, ina k'ok'arin rik'eshi, yana kwacewa zai shiga cikin gidan, a fili Abbi yace " abokin Deeyanah kuma? Idon Ajlaal na sauka akan Deeyanah yayiyo kanta gadan-gadan zai rungume ta, fitsarin datake iyakar k'ok'arin wajen ta matse shi ya kwace mata saboda rud'ewa da tashin hankali, yana gaf da isa gareta Deen ya shiga tsakiyarsu, kallan kallo suka fara yi a tsakaninsu kafin Ajlaal ya cukumi wuyan rigar Deen, cikin matsanancin zafin zuciya Abbi ya kifawa Ajlaal lafiyayyan mari, ya d'ora da fad'in, " kana da hankali kuwa? "Kazo har cikin gidanmu zaka rungume 'ya ta akan idona saboda fitsara, da rashin tarbiyya, rikitaccen kuka Ajlaal ya saka had'i da durk'usawa gaban Abbi yana fad'in, " nayi kuskure, dan Allah kuyi min hak'uri, karku rabani da ita, itace rayuwata, itace farin ciki na da duniyata, dan girman Allah karku rabani da ita please yayi maganar yana rik'e k'afafuwan Abbi, " wallahi aurenta nake san yi, nayi muku alk'awarin zan bata duk wani farin cikin dake cikin duniya, " fice daga gidan nan, cewar Abbi a hasale yana nuna mishi get, ko motsawa Ajlaal bayyi ba, ya had'e hannuwanshi yana rok'onsu kan su taimaka karsu rabashi da Deeyanah, ihunnn da Deeyanah ta saka ya jawo hankalin sauran mutanen gidan mata duk suka fito, wani irin mugun duka Babah keyi mata da iya k'arfinshi, take duk ilahirin jikinshi ya d'auki kerrrrma idanuwanshi suka rufe ruf baya ganin komai sai duhu, a haukace Ajlaal yayi kan Babah ya rik'e kwalarshi ya d'aga hannu zai nausheshi, jini nabin bakinta ta d'aga murya da k'arfi tace " Baba na ne mahaifi Ajlaal, hannunshi ya dunk'ule had'i da dukan iskan bayan ya saki Babah, Babah da sauran jama'ar dake wajen suman tsaye sukayi cike da mamaki, gaba d'aya 'ya'ya mazan Family d'in sukayi kan Ajlaal suna dukanshi kamar zasu kashe shi, Babah da har lokacin yana tsaye kamar an dasa shi yayi k'arfin halin cewa " ku daina dukanshi, ba laifinshi bane laifin 'yar mu, ku kyale shi bashi da laifin komai, Abbi yace " ku fitar mana shi daga gidanmu, cali-cali sukayi da Ajlaal suka fitar dashi waje, bai damu da yadda jikinshi yayi jina-jina ba ya mik'e da sauri ya shiga mota, ikon Allah ne yakaishi gidansu, daga yadda yayi parking iyayenshi suka san ba lafiya, a tare Hajiya Halimatu da Alhaji Basaan suka fito, ganinshi haka a birkice kamar wanda ya kwato daga bakin kura yayi masifar d'aga musu hankali dan duk duniya babu abinda suke so sama da Ajlaal, " Abba nace kaje tunda wuri ka nemar min auren Deeyanah kak'i, idan na rasata mutuwa zanyi Abbah, wallahi mutuwa zanyi, yayi maganar yana dafe saitin zuciyarshi, jikinsu na rawa suka tallafeshi suna tambayarshi " lafiya Ajlaal? "Meke faruwa ne? "Ba lokacin doguwar magana Abbah inba haka ba lokaci zai k'ure zan rasata rasawa ta har abada, kazo muje gidansu Deeyanah yanzu ka nema min aurenta dan Allah Abbah, Alhaji Basaan zayyi magana Hajiya Halimatu ta daka mishi tsawar datasashi rud'ewa " dalla Malam karka tsaya b'ata lokaci d'ana ya mutu, wallahi idan Ajlaal ya mutu kaima saika bishi lusari kawai ka tsaya kana shirme rayuwar d'anka na neman salwanta kan ya rasa abinda yake so, a dururuce Alhaji Basaan ya mik'e yana fad'in" to to tashi muje Ajlaal , " kai kad'ai zan bari kaje neman auren kaje kayi hauka ka lalata komai? "Tsaya nazo muje tare, tayi maganar tana komawa cikin gida. Abbi da Deen suka tallafe Babah suka shigar dashi babban parlour'n gidan, duk akabi bayansu har matan, parlour'n yayi shiru ba mai magana, babu abinda ke tashi sai sautin kukan Deeyanah, tsawa Azan ya daka mata yana fad'in " dalla yiwa mutane shiru mutuniyar banza kawai, Hannu Babah yasa a aljihu ya ciro kud'in da baisan adadinsu ba, ya mik'awa Abb muryarshi na rawa can k'asa yace " ga sadakin d'ana Deen nan ina nemar mishi auren 'yarka Deeyanah.........!Duk da halin da take ciki bai hana ta shiga mummunan tashin hankali ba, gabanta yayi mummunar fad'uwa, a razane ta d'ago kanta ta kalli Deen suka had'a ido, in banda hawaye babu abinda ke rige-rigen sauka saman kuncinta, kanshi ya langwab'ar gefe yana kallan kwayar idonta, Abbi ya kalli Babah cike da neman tabbacin abinda ya fad'a, gane irin kallan da Abbin keyi masa yasa Babah gyad'a kanshi tare dayin murmushin k'arfin hali, dan bazai iya fad'ar koda kalma d'aya bace, " me kake san ce min Abduljalal? "Karka yanke hukunci cikin fushi da b'acin rai, kar muyi abinda daga baya zai raba kanmu, ya kawo rugujewar zumuncinmu, farin cikinmu da kwanciyar hankalinmu, kar muyi abinda zai tarwatsa kanmu ya kawo lalacewar komai, dakyar Babah ya iya bud'e baki da fad'in " babu komai sai Alkhairi in sha Allah, Abbi ya bud'e baki zayyi magana cikin sanyi yana danne abinda ke taso mishi  ya katse shi da fad'in " dan Allah Yaya....! ni dai alfarma nake nema a wajenka ta aurawa d'ana 'yarka in kuma....! shiru Babah yayi ya kasa k'arasa abinda yayi niyyar fad'a, Abbi ya mayar da kallanshi ga Deeyanah da Deen, kan Deen duk'e, fuskarshi fayau cike da annuri, while Deeyanah nata faman kuka kamar ranta zai fita, " dan Allah Yaya please! Babah ya kuma fad'i har zuwa lokacin yana mik'a mishi sadakin, jikin Abbi a sanyaye ya karb'a, anan take a gaban kowa, aka d'aura auran Deen da Deeyanah, ana shafa fatiha Babah ya sauke numfashin da bai san yana rik'e dashi ba, yace " Allah ya sani dai-dai nayi, Ubangiji yasa hakan ya zama Alkhairi, Na yafe muku duniya da lahira, Allah ya baku zaman lafiya da zuri'a ta gari, ya d'ora da " yaushe zaku tafi? Yayi maganar yana kallan Deen, kanshi ya k'ara duk'arwa k'asa cike da matsananciyar kunyar Babah data saukar mishi a lokaci d'aya yace " cikin satin nan in sha Allah, " Allah ya kaimu, Babah ya fad'a yana mik'ewa ya fice, Abbi ya kalli Deeyanah cike da tausayawa dan yaga kamar bata san Deen d'in, bayasan yak'i yarda da hukuncin da Babah ya zartar ne dankar ya zargi wani abu musamman da Deen ya kasance d'anshi, " Allah baku zaman lafiya, Abbi ya fad'a yana mik'ewa, gaba d'aya suka mik'e suka fice daga parlour'n, a harabar gidan suka iske Babah da Alhaji Basaan da Hajiya Halimatu tsaye, mamaki shinfid'e a saman fuskar Abbi ya k'arasa wajen tare da mik'awa Alhaji Basaan hannu suka gaisa, Deen da Deeyanah da sauran 'yan gidan sunyi tsaye suna kallansu, "Mu shiga daga ciki, muyi magana, ba musu suka koma parlour'n gaba d'ayansu har su Deeyanah, bayan kowa ya zauna Abbi ya tsaida kallanshi akan Alhaji Basaan cike da san jin meke tafe dasu, sai da Alhaji Basaan yayi gyaran murya had'i da satar kallan Hajiya Halimatu kana ya soma magana, " munji abinda Ajlaal yayi tabbas bai kyauta ba, muna baku hak'uri a bisa abinda yayi, ya d'anyi shiru kafin ya d'ora da " tun a kwanakin baya ya sameni da maganar inzo na nemar mishi auren Deeyanah a wajenku to sai aka samu d'an akasi Allah yasa ban zo ba, murmushi Babah yayi yana fad'in " ayya sai dai kun makara dan yanzu-yanza aka d'aurawa Deeyanah aure da d'an uwanta Deen, cikin kid'ima Ajlaal ya mik'e tsaye kanshi ya shiga sarawa, ya kalli Deeyanah da Deen, murmushin da Deen ya sakar mishi ya bashi tabbaci akan maganar Babah, " kaga sadakinta a hannuna, cewar Abbi yana nuna musu sanadin Deeyanah...... ihunnnn da Ajlaal ya saki yasa Abbi yin shiru, " nooo! A'a hakan bazata tab'a faruwa ba, Deeyanah tawa ce ni kad'ai, danni kad'ai aka halicceta, yayi maganar kamar zararre, Gabanta yaje ya durk'usa ya k'ura mata ido, " kina so na Deeyanah na sani, ina sanki kin sani, karki bari a rabamu please yayi maganar yana k'ok'arin rik'o hannunta, cikin zafin rai Deen ya had'ashi baya, " are you mad? " Kasan me kake k'ok'arin yi kuwa? "Matar tawa zaka tab'a a gaba na dan iskanci? Jin Deen ya kira Deeyanah da matarshi yasa Ajlaal durk'ushewa k'asa ya kifa kanshi yana wani irin kuka mai gunji, Deen ya rik'o hannun Deeyanah suka bar parlour'n, Abbi da Babah da kowa suka fita suka bar Ajlaal , Alhaji Basaan da Hajiya Halimatu zaune. " Saika tashi mu tafi asararre lusari wanda ya kasa nemarwa tilon d'ansa aure, dan mutuwar zuciya ka kasa cika masa buri da muradinshi, zungwi-zungwi sumi-sumi ya mik'e ya fita. ***************************************** Zaune suke a gaban iyayensu anayi musu nasiha kasancewar yaune ranar tafiyarsu, Abbi yayi gyaran murya ya soma magana, " magana ta farko kuyi rik'o dan Allah da Ma'aiki da addininku, kuji tsoron Allah a bisa dukkan mu'amulolinku, Ubangijinmu me tausayi ne, idan kaga Allah yana hana maka jin dadin duniya, yana waita maka k'unci da bala'i to ka sani hakika kana da girma a wajen Allah kuma makusanci ne a gareshi, kuma zai share maka hanya irin ta bayinsa cikakku, Allah baya kyautar duniya ga Annabawansa, ku sani babu wanda yake tausayin bawa sama da Ubangiji, babu wanda yafi sanin bak'in cikin da kake ciki sama da Ubangijinka, kuma babu wanda yake da ikon yaye maka duk abinda ya dameka face Ubangiji, dan haka mu koma gareshi mu kasance masu neman taimako daga wajenshi a koyaushe, ku kasance masu yafiya dan zuciyar data kasance mai yafiya mai ita zai kasance cikin salama, sai hak'uri, hak'uri da juriya sune jigo kuma katangar da take tokare da igiyoyin aure, duk wanda yace bazayyi hak'uri a cikin zamantakewa ba yana tare da babban kalubalen rayuwa, masu hak'uri kadai ake cikawa sakamakonsu ba tare da hisabi ba, hak'uri da Iyali kauna ce, hakuri da mak'ota dattaku ne, hakuri da jama'a mutunta kai ne, hak'uri da bin dokokin Allah dace imani ne, duk mutumin daya rungumi d'abi'ar hak'uri to bazai tab'a rabuwa da samun nasara a rayuwa ba, duk da yake nasarar tana iya d'aukar lokaci, idan kayi hakuri a rayuwa wata rana zaka zama madaukaki akan wadanda suka cutar dakai, ita duniya gidan hak'uri ce, rayuwa kuma gidan juriya ne, haka duk girman bakin ciki baya tarwatsa zuciyar da akwai Allah a cikinta, kyawawan dabi'u sune hak'ik'anin kyau ba kyawun fuska ba, kowanne mutum yana da mabud'ai guda biyu a hannunshi na alkhairi dana sharri, shike zab'awa kanshi k'ofar dazai bud'e da mabud'inshi, A wajen 'ya mace ba kudi ko tarin abin duniya ne arziki ba, sa'a da miji na gari shine babban arziki, sosai akayi musu nasiha me ratsa jiki, in banda kuka babu abinda Deeyanah keyi, yayinda Deen kejin kukanta har k'ark'ashin zuciyarshi, har Airport 'yan gidansu suka raka su, dakyar Deeyanah ta rabu da 'yan uwanta. A daddafe Ajlaal ya shiga gida ya kulle kanshi a d'aki yana rusgar kuka riris kamar mace, kwana biyu yayi a d'aki baci basha, baya magana da kowa, Tsaye Alhaji Basaan yayi a k'ofar d'akin Ajlaal, sai da ya tattaro gaba d'aya k'arfin gwiwarshi kana yayi knocking, tare da kiran sunanshi yana fad'in " Ajlaal ka bud'e min k'ofa in har na isa dakai, umarni na baka, sai da akayi minti d'aya kana Alhaji Basaan yaji sautin key alamar an cire key, amma bai bud'e k'ofar ba, a hankali Alhaji Basaan ya tura k'ofar ya shiga, halin dayaga Ajlaal a ciki yayi masifar d'aga mishi hankali ya kuma bashi mamaki, dan bayyi zaton yana san yarinyar har haka ba, fita yayi ya had'owa Ajlaal tea ya dawo ya zauna kusa dashi tare da mik'a mishi kofin, baya san magana dan haka ya karb'a ba musu, a hankali Alhaji Basaan ya dafashi yana fad'in " kana da hankali kuwa Ajlaal? "Kana neman kashe kanka a banza a wofi akan mace, macen da tana can tare da mijinta........ bai k'arasa maganar ba yaji tasssssssss glass cup d'in hannun Ajlaal ya fashe, saurin kallan  hannun Ajlaal yayi yanata faman zubar da jini, " please Abba please, kayi shiru...' ya fad'a a galabaice, Murmushin k'arfin hali Alhaji Basaan yayi yana kallan Ajwaad yace " Idan zuciya ta shiga cikin damuwa da bak'in ciki babu wani abu da zai zame mata nutsuwa da kwanciyar hankali face ambaton Allah Dole muji babu dadi idan wanda muke so ya rabu damu, amma ba akan wanda ya yaudare mu ba, rasa abinda muke so nuni ne na cewa rabonmu yana ta can wani wajen yana nemanmu, dan mun fad'i a soyayyar wani ba wai mun rasa soyayya ta har abada bane, Ba asara bane danka rasa wanda kake so, arasa shine ka rasa kanka wajen kaunar wanda kai a wajensa ba komai bane, sauk'i yana tare da tsanani, mai hak'uri yana cimma dad'i, mai kyauta baya rasawa, kowa yaji tsoron Allah, Ubangiji zayyi masa mafita, manta da damuwa ka fuskanci rayuwa, kowa ka gani a duniya akwai abinda ya dame shi, duk abinda ka rasa a rayuwa ba naka bane kuma ba alkhairinka bane, rabonka baya tab'a wuce ka. idan Allah ya k'addara Deeyanah matarka ce ba aure tayi ba, ko mutuwa tayi saika aure ta, wani baya auren matar wani, kamar yadda wani baya haihuwar d'an wani, sosai Alhaji Basaan yayi mishi nasiha ya kawo mishi misalai da dama, ya bashi shawara ya dage ya cimma muradanshi saboda bai san me gaba zata haifar ba. *********************************** Tana ta faman sheshshekar kuka bacci ya d'auke ta bata sani, sanyin AC jirgin ya sata shigewa cikin jikinshi batare data sani ba, ta k'ank'ame shi sosai sai faman sauke ajiyar zuciya take yi, fuskarshi d'auke da siririn murmushi ya manna mata light kiss a goshi had'i da k'ara matseta a jikinshi. K'arfe uku da kwata na dare na k'asar America jirginsu ya sauka a  babban birninsu Washington, yaso ya sauko rungume da ita a jikinshi amma ganin ba fuska yasashi hak'ura, yana tafe tana biye dashi har suka fice daga airport, jerin gwanon taxi d'in dake gabansu yabi da kallo kafin ya zab'i d'aya cikinsu ya bud'e mata baya ta shiga kana shima ya shiga bayan me taxi driver ya saka musu kayansu a boot. Gida ne d'an madaidaici me d'auke da d'akuna biyu kowanne da ban d'aki a cikinshi, sai babban falo da kitchen gidan ya tsaru sosai ga yasha home decor ga flowers kun dai san tsarin gidan turawa, tsaye tayi tana bin gidan da kallo har cikin ranta gidan ya burgeta gashi dai d'an k'arami d'an kijifjif gwanin ban sha'awa, babu abinda yafi d'aukar hankalinta sai barandar waje, d'aya daga cikin bedroom d'in ya nuna mata yana fad'in " ki d'auki wancan bedroom d'in, ni ga nawa can, batayi mishi magana ba ta shige bedroom d'in, d'akin a gyare tsaf kamar da wanda ke zaune gidan, hand bag d'inta ta aje saman wood bed ta zauna tana sauke ajiyar zuciya. Cikin mutuwar jiki ta mik'e ta rage kayan jikinta ta fad'a ban d'aki, wanka tayi gami da d'auro alwala ta fito d'aure da towel d'in data gani aje a ban d'akin a wanke tsaf, k'ank'antar towel d'in tasa ko mazaunanta bai gama rufewa, gashi baima rutsa ta sosai ba, sai zamewa yake yi, d'an guntun tsaki taja had'i da rolling idanuwanta data tuno bata d'auko kayanta ba, juyawa tayi da nufin fita ya turo k'ofar ya shigo kai tsaye, idanuwanshi suka sauka akanta, yarrr yaji har cikin kanshi, yaso ya d'auke idonshi daga kanta amma ya kasa, itama  duk tabi ta rikice tashin hankali bayyane saman fuskarta, sai kokawa take da towel yana zamewa, garin ta kaiwa hijab wawura towel d'in ya zame, naked body d'inta ya bayyana, ido ya runtse da k'arfi had'i da furta "ya Allah, sai da yayi da gaske kafin ya iya saita kanshi, jajayen idanuwanshi da suka rine cikin k'ank'anin lokaci ya bud'e ya sauke mata su a jikinta, wata irin tsuma jikinta ya d'auka saboda tsabar tsoratar da tayi na ganin yadda idanuwanshi suka canja kala, a hankali ya sunkuya ya d'auki towel d'in ya mik'a mata had'i da ficewa daga d'akin. Bayan ta gama shiryawa, tayi sallah ta jera kayanta cikin wardrobe ta shirya gaban mudubinta ta saita komai, sai da ta samu nutsuwa kana taji yunwa, ga kewa da kad'aici gidansu babban gida ne, mai mutane da yawa nan ko daga ita sai shi, saita jita kamar cikin keji, bak'i ciki yasata fashewa da kuka. Yana fita daga d'akin ya wuce bedroom d'inshi ya fad'a bathroom ya sakarwa kanshi shower ya dad'e ruwan na sauka kanshi sai faman sauke ajiyar zuciya yake yi, Deen ya kasancewa d'aya daga cikin maza masu matsananciyar sha'awa abu kad'an ke motsa mishi sha'awar shi, sai da d'auki lokaci cikin ban d'akin kana yayi wanka ya fito d'aure da towel a k'ugunshi, har lokacin yana cikin yanayi bawai sha'awar ta lafa bane, wondo ya saka 3 quarter dark blue da rigarshi ya fashe jikinshi da jerin turarurrukan dake  kan mudubin shi wanda a k'alla sunyi goma kuma da gani designers ne, fitowa yayi daga bedroom d'in zuwa falo ya kishingid'a saman sofa yana mayar da numfashi, sautin kukanta ya soma jiyowa kad'an-kad'an daga bedroom d'inta, cikin nutsuwa ya mik'e ya nufi bedroom d'in nata, har ya d'ora hannunshi akan handle d'in k'ofar sai kuma ya fasa shiga ya juya zuwa kitchen bai d'auki lokaci me tsayi ba ya had'a mata shayi me kauri, ya fito hannunshi d'auke da tea cup ya shiga d'akinta. Tana zaune bakin gado tana ta faman kuka kamar ranta zai fita, ya mik'a mata kofin shayi, hannunshi daya mik'o mata kofin tabi da kallo, had'i da kawar da kanta gefe tana cigaba da kukanta, akan bedside ya zauna bayan ya ajeyi kofin a gefe, ya rik'o hannayenta cikin nashi had'i da zuba mata ido, ya dad'e yana kallanta kana ya sauke ajiyar zuciya yana fad'in " dama bakya so na Deeyanah? " Wannan kuka duk na an aure miki ni ne? Yayi maganar so calm, share shi tayi ta cigaba da kukanta, " nayi zaton kina so na ashe wani na kike so can daban, nayi zaton danni kad'ai zuciyarki ke bugawa, ashe ba haka bane, nayi tsammanin ni kike so Deeyanah, wallahi dana san bakya so na, babu abinda zaisa na yarda a d'aura mana aure, amma yanzumma bata b'aci ba, zanyi yadda kike so, zanyi abinda zai sanyi ki rayu cikin farin ciki, zan sauwak'e igiyoyin aure na dake kanki kije ki aure Ajla..., kasa k'arasa sunanshi yayi, ya runtse idonshi cikin k'unar rai yace " ki aure wanda kike so, wanda kike san kasancewa tare dashi, karki damu zanyi k'ok'arin fahimtar da iyayenmu, zan kuma wuce miki gaba wajen cimma muradinki, yayi maganar yana mik'ewa had'i da k'ok'arin barin d'akin, tayi saurin rik'o hannunshi tare da sassauta kukanta tace " kayi hak'uri Yaya, ba haka ne nufi na ba, "to meye nufin naki bayan gashi nan na gani da ido na? Shiru tayi ta sunkuyar da kanta k'asa, ganin haka ya sashi dawowa ya zauna kusa da ita, yayi k'asa can da muryarshi yace " kina so na? Yadda yayi maganar a kasalance ya kashe mata jiki, ta kuma duk'ar da kanta k'asa cike da kunya tana wasa da 'yan yatsunta, " please say it! do you love me? Cikin nutsuwa ta d'ago kanta idanuwansu suka sark'e cikin na juna, " ban tab'a had'a soyayyarka data wani ba Yaya, kai kad'ai zuciyata take so, bayan kai ban tab'a jin san wani dai-dai dana second d'aya ba, dan kai zuciyata ke harbawa, dan kai nake rayuwa Yaya, ban san yaushe bane, san a ina bane, ban san lokacin ba Yaya na taso na tsinci kaina da sanka, abu d'aya na sani ina sanka, ina jin tausayinshi ne kawai, ina jin ban kyauta mishi ba, ina ji a jikina wani abu mai munin gaske zai far...... dakatar da ita yayi ta hanyar rufe mata baki da hannunshi, " babu abinda zai faru sai alkhairi da izinin Allah, I love you, I love you more & more most, ke kad'ai nake gani a matsayin mace, yayi maganar yana k'ara rungumeta sosai a k'irjinshi. Bayanta ya shiga bubbugawa had'i shafa kanta, a hankali ya zame hular kanta da reborn d'in data d'aure gashin kanta dashi, ya cusa hannunshi cikin gashin kanta ya soma massaging fatar kanta, zatayi k'arya idan tace bata ji dad'in abinda yake yi mata, idanuwanta ta lumshe tare da sake yin luf a k'irjinshi, ganin haka ya bashi damar soma goga kumatunshi a nata kumatun, idanuwanshi lumshe dan ya soma loosing control, ba zato sai ji tayi zura harshenshi cikin kunnenta, a fili ta sauke ajiyar zuciya, a hankali ya k'asa da harshenshi ya soma lasar wuyanta, a hankali ta soma fitar da nishi, gashin kanta ya damk'a ya d'ago kanta ya kalli cikin kwayar idanuwanta da suka soma canjawa, kai tsaye ya had'e bakinsu soma tsotsar harshenta da lips d'inta while yana tura mata nashi, da dabara ya zagaya da hannunshi bayanta ya zage zip d'in rigarta fatar bayanta ta bayyana, cikin salon d'aukar hankali ya zura hannunshi ya fara shafa bayan yana yi mata tafiyar tsutsa a kwarmin bayanta, bata sanda ta gantsare ba had'i da sakin nishi. Ta cikin rigar ya b'alle mata Bra ya zagayo hannunshi ya soma matsa boobs d'inta had'i da murza nipples d'inta, ai yana soma murza nipples d'inta ya ida rikicewa ya fice daga hayyacinshi, jikinshi na kerrrrma ya zame mata doguwar rigar jikinta blue black d'inta pant & fararen boobs d'inta dake tsaye cak suka bayyana, wohoho 'yan maza aka zabura damin jijiya ya mik'e, rigingine ya kwanta da ya zame rigar jikinshi farar fatar jikinshi sai kyalli take, rumfa yayi mata ya kafa bakinshi saman boobs d'inta yana tsatsarsu tare da d'an ciza nipples, while d'aya hannun yana aikin murza d'ayan. Bakin Deeyana ya mutu murus in banda nishi da k'ara turo mishi k'irjinta babu abinda take, yayinda hannunta ke cikin suman kanshi tana wasa gashin kanshi had'i da k'ara kanshi, cikin salon narkar da zuciya da k'ara rikitata yayi k'asa da harshenshi yana lasar silk skin d'inta har ya isa cibiyarta yasa harshe cikin cibiyarta, jinta take kamar ba a duniyar ba, ta manta komai da kowa, babu abinda take iya tunawa sai dad'in Deen d'inta. Duk da bata cikin hayyacinta bai hanata fahimtar inda ya dosa ba, da sauri ta yunk'ura zata tashi zaune, yayi saurin mayar da ita, " A'a Yaya! please ya isa haka. Tayi maganar a rarrabe kamar me koyon magana, sake k'ok'arin tashi tayi had'i da k'ok'arin ture shi, ai ji yayi kamar zata rabashi da ranshi, gaba d'aya nauyinshi ya sakar mata ya danneta yadda bazata iya tashi ba, kuka ta saka mishi had'i rok'onshi tana yi mishi magiyar ya kyale ta, kasancewar baya jinta dan baya cikin duniyar gaba d'aya yasa bai sarara mata ba, ga dukkanin alamu yau kam babu d'aga dan tasan babu me kwatar ta a hannunshi. A wannan dare suka zama abu d'aya, suka kasance ciki farin cikin da ma'aurata ke kasancewa. Bai sarara mata ba sai da ya biya buk'atarshi nutsuwa ta lullub'e shi, ya zame gefe ya kwanta yana mayar da numfashi, ta shigata sosai, dan ta zubar da jini sosai, amma bata zauna ba, ta daddafa ta shige bathroom ta gyara kanta had'i da kasa jikinta sosai tayi wanka ta dawo ta kwanta gefenshi, yana so ya tashi yayi wanka amma baya jin zai iya, ko sallar asuba bayyi ba, dan jikinshi ya mutu sosai. Wata irin soyayya sukewa junansu me shiga rai had'i da laab'a juna da farantawa juna rai, da kanshi yake koyar da ita matsananciyar soyayyarshi me shiga rai da zama a zuciya, ko girki tare suke yin abunsu, wata biyu da zuwansu ya nemar mata makaranta. Tana zaune a falo daga ita sai wani wondo me kama da pant da half best a jikinta tana cin cop corn ya shigo, da gudu ta fad'a jikinshi tana dariya tare fad'in " oyoyo dad'ina! Dariya yayi gami da lakace mata hanci yace " kamar gaske yanzu da zan ce muje ki karb'i dad'in da guduwa zakiyi, k'irjinta ta turo mishi had'i da kashe mishi ido d'aya tace " wa zaik'i dad'i, tayi maganar tana dariya, dariya yayi gami da ja mata hanci yana fad'in " wa kuwa zaik'i dad'i, bedroom d'inta suka wuce ta shiga bathroom ta had'a mishi ruwan wanka, daga shi sai towel d'aure a k'ugunshi ya shigo bathroom d'in, ta baya ya rungume tare da d'ora hab'arshi saman kafad'arta ya lumshe ido, " ina sanki Deeyanah! ina sanki fiye da so, dan Allah karki barni, cikin nutsuwa ta juyo suka fuskanci juna takai hannunta kan hancinshi taja hancin tana dariya tace " na sani K'aunata, kayi wanka kazo muci abinci, tayi maganar tana barin jikinshi zata, rik'o ta yayi ya dawo da ita jikinshi yana rausaya yace " ina kuma zaki? "Ai tare zamuyi wankan kefa kika ce wa zaik'i dad'i, kafin tayi magana yayi sama da ita sai cikin kwamin wanka, a shagwab'e tace " kai K'auna ta! Sai da suka b'ata lokaci suka murzar juna cikin kwamin wanka kana sukayi wankan. Tana zaune saman cinyarshi tana bashi abinci a baki, sai zuba mishi kissa take, duk tabi ta hana shi zama sakat, shi kam duk abinda tayi biye mata yake, bayan sun gama cin abincin sun nutsu yace " rufe idonki! Wani irin kallo tayi mishi daya ratsa ruhinshi, " surprise ne ko? Dakyar yace " kedai rufe mana, "tom! tace tana rufe idon, takarda ya dank'a mata a hannunta kana yace " bud'e! cikin rashin fahimta tabi takardar da kallo, da ido yayi mata alamar duba, a nutse ta soma karanta takardar, ihuuu tayi ta rungume shi, kiss ta shiga jera mishi ta ko'ina a fuskarshi, " nagode! nagode! nagode K'auna ta, thank you so much Dee!, ina sanka, I love you, cikin basarwa yace " na sani! tana dariya tace " bakomai yau kam bazanji haushi ba, na sani ramawa kayi. "Deeyanah! ya kira sunanta a hankali, jin yadda ya kira sunanta yasata nutsuwa, zaki fara karatu a k'asar da addininmu da al'adarmu suka sha bam-bam, muna bambamce-bambamce mai tarin yawa tsakaninmu dasu, ina da kishi Deeyanah, ina da matsanancin kishin da zan iyayin komai akanki, ina iya bada rayuwata akanki, ki kula kada kija abinda zai haifar mana da matsala a tsakaninmu, " in sha Allah zan kiyaye Yaya, kanshi ya d'aga mata tare da cewa Allah ya bada sa'a, ta amsa da " Amin ya Allah!. " To a bani tukwicina! ture shi tayi tana murmushi tace " wai kai yaya baka gajiya da sex ne? "Kai da ayi ta abu d'aya, kwashe yayi da dariya sosai sai da yayi me isarshi kana yace " aiko bazan tab'a gajiya dake ba har abada, bama na fatan Allah ya kawo ranar da zan gaji dake, kedai kiyi ta bani ina kwasa kawai idan banyi sex ba me zanyi? "Daga shi sai sallah sune suka zame min dole. Idonta kanshi tace " Dee! ni ko me zanyi maka ka tsane ni, kai tsaye yace " cin amana Deeyanah, daga ranar dana san kina cin amanata da wani daga ranar kar ki raba d'aya biyu zan tsaneki tsana ta har abada, zanyi miki nisan nisa, nisa na har abada, daga ranar nayi miki alk'awarin bazaki sake gani na ba har abada... "Dakata duk me ya kawo haka? "Ina kishi Deeyanah, ina matsanancin kishin da nake jin zan iya kashe koma waye a kanki. "Kwantar da hankalinka hakan ma bazata tab'a faruwa ba har abada ni taka ce kai kad'ai har rai da mutuwa in sha Allah. Ranar da zata fara zuwa makaranta shigar musulunci tayi, doguwar riga ta saka marar shape da d'an madaidaicin hijabinta, sai da ya biya ya aje ta a makaranta, har zata shige aji yace " Deeyanah ina sanki, kada ki manta ina da kishi ki kula sosai, murmushi tayi mishi had'i dayi mishi kiss. Gaskiya Deen dayace akwai banbanci mai tsayin gaske a tsakaninmu damu dan kuwa taga abinda ya girmi kanta, dan haka taji gargad'in Deen ta kuma yiwa kashedinshi guri cikin kanta ya zauna daram ta kame kanta sosai, musamman kullum idan zai kawo ta makaranta sayya fad'a mata yana da kishi. Tana zaune saman sofa while yana zaune k'asan carpet yana yanke mata farce, " Dee! ni ko zan so naga kishin nan naka da ake tayi min gargad'i kanshi, ido ya zuba mata na tsayin lokaci kana yayi murmushi had'i da girgiza kanshi batare dayace komai, " wata rana zan tsokano kishi nan dai na ganshi da ido, " kada ki soma! karma kiyi fatan ganin haka, zatayi magana amai ya taso mata, da gudu ta mik'e ta shige bedroom d'inshi ta fad'a toilet daga tsaye ta soma kelaya amai, yana tsaye kanta yana jera mata sannu, wanka yayi mata kana ya wanke bathroom d'in, tana kwance saman 3 sitter ya k'araso kanta. " Sannu! Kanta ta d'aga mishi, " dama baki da lafiya ne? Ganin yadda duk ya d'aga hankalinshi yasata mik'a mishi hannu tana murmushi ya zauna kusa da ita ta shige jikinshi, cikin sanyin murya tace " bakomai fa inaga wani abu naci ya lalata min ciki, kanta ya shiga shafa yana jera mata sannu, abu kamar wasa Deeyanah taita sintirin amai, tun tana aman har ya zama sai dai tayi ta yunkurin aman amma babu komai, kasa daurewa yayi ya d'auketa zuwa asibiti, ba a sha wahalar gano d'an k'aramin cikin da take d'auke dashi ba, murna da farin ciki wajensu ba'a magana, sosai cikin ke wahalar da ita, laulayin cikin me tsurfa ne ga yawan amai ga yawu, dole ta daina zuwa makaranta sai da cikinta yakai watanni bakwai, duk da ba laulayin ta dena ba, kulawa kam babu irin wacce Deen baya bata, komai shike yi mata baya barinta tayi komai, wani lokacin ma abun mamaki yake bata ace duk taurin kan nan nashi babu ya sauke, ashe dama fahimtar shi da mutane basuyi ba shiyasa ake yi mishi kallan miskili. Ta fito daga class sanye da zumbulelen hijab tana tura cikinta wani d'an ajinsu ya tare ta yana tambayarta " lafiya kwana biyu banga kinzo makaranta ba? Murmushi tayi mishi tare da cewa bani da lafiya, " ayya sannu! ya fad'a cike da tausayawa yana kai hannunshi goshinta, baya taja da sauri tana k'ok'arin barin wajen sai ji tayi an wafci baturen yaron an d'aga shi sama an buga shi da k'asa, ta ko'ina Deen ya shiga dukan yaron yana naushinshi ba jini ba gani, ganin yana neman illata yaron yasata rik'e shi had'i ta fasa kuka, yana juyowa ya d'auke ta da wani irin mari da saura kad'an k'arfin marin ya kada ita, idanuwanshi sunyi jajir, yayinda jijiyoyin kanshi sukayi rad'o-rad'o, take duk ilahirin jikinta ya d'auki rawa da kerrrrma tsoro ya kamata bata san sanda ta saki fitsari a jikinta ba, kafin wani lokaci har 'yan sanda sunzo, suka tisa k'eyar Deen da yaron, tabi su da gudu, motarshi ta shiga ta bi baya su da gudu dan karsu b'ace mata, sai da Deen yayi kwana uku a hannunsu kana suka sake shi, a haka ma dan yana da 'yar gaskiya ne kuma basa so abin ya girmama, gudun kar a juya abun ya zama religion war, tunda matarshi ya tab'a mishi a gaban mutane. Dakyar ta shawo kanshi suka shirya, dan yakai sati baya kallan inda take, "kayi hak'uri dan Allah wallahi ba laifi bane. "Har murmushin da kikayi mishi duk ba laifinki bane? "Ka gane dama suna yiwa musulmai wani irin kallo shiyasa, ta k'arasa maganar tana fashewa da kuka had'i da fad'awa jikinshi, " kayi hak'uri dan Allah k'aunata, idanuwanshi ya lumshe yana k'ara matseta a jikinshi yace " ya wuce, ina sanki Deeyanah bana san ko namijin k'uda ya rab'eki, ina kishin ki, bana na kamaki da rashin gaskiya ko cin amana a zamantakewar mu dan daga ranar na rabu dake har abada, daga ranar duk wata alak'ar dake tsakaninmu zan datse ta, saurin d'agowa tayi daga jikinshi ta kalle shi, tabbas da gaske yake dan yanayinshi ya nuna har cikin ranshi yayi maganar, cikin sanyi tace " Allah tsare ni dacin amanar aure, Ubangiji yayi min tsari da wannan mummunar k'addarar, ta fad'a had'i da mik'ewa zata bar wajen, mayar da ita yayi ta zauna saman cinyarshi, "kiyi hak'uri da marin da nayi miki duk da bakiyin min k'orafin shi ba, fuskarta a d'an tsuke tace " ba damuwa, ta sake yunk'urawa zata tashi, mayar da ita ya sake yi yana fad'in " ina kuma zaki? "Kin san fa na dad'e ban gaisa da Baby na, yayi maganar gami da zura hannunshi cikin rigarta ya ciro boobs d'inta yana mammatsawa, sake tsuke fuska tayi, ya kai harshenshi kansu ya soma lasa while idonshi na kanta, tun tana basarwa har ta bada kai bori ya hau, suka d'inke suka koma normal kamar wani abu bai tab'a faruwa a tsakaninsu ba. Cikinta ya shiga watan haihuwa babu yadda su Ammu da Ammi basuyi a dawo da ita gida ta haihu ba amma fur Deen yak'i yace duk wata kulawa da zasu bata shima zai iya bata, iyayen basu ja ba, sukayi musu fatan alkhairi. Bayan kwana biyu da safe tana wanka shi kuma yana tsaye gaban mudubin ban d'aki yana brush yana ta zuba mata surutu, jin tayi shiru bata bashi amsa, yasashi juyowa halin da take ciki ba k'aramin tsorata shi ba yayi, a gaggauce ya d'auraye mata jikinta ya zira mata doguwar riga bai ma tsaya bi takan kayan Baby ba yayi waje da ita sai asibiti, bata fi awa biyu ba ta haifo santalelen d'anta fari fat me kama da ubanshi sak, dayake da yana cikin Labour Room d'in dashi akayi haihuwar ya k'ame a tsaye sai bin Babyn yake da kallo yana murmushi, Doctor ya mik'a mishi d'an ya karb'a ya rungume yana ta maimaita " Alhamdulillah Alhamdulillah Allah nagode maka ya rabbi!, gefen gadon da take kwance yaje ya mik'a mata yaron yana fad'in " kinga kyautar da Allah yayi mana ko? "Nagode sosai Deeyanah ke alkhairi ce agare ni. Raleeya na tuk'i taci kwalliya, tazo junction danja ta tsaida su, taga maza nata kallanta, tayi dariya had'i da dukan sitiyarin motar tace " ya Allah ka bawa mata kud'i suyi soyayya da wanda ransu ke so su juya maza a tafin hannunsu yadda sukaga dama, saboda da yawa gada cikin mata suna soyayya da jahilai kuma dabbobi ne saboda kud'i, wani tsoho mai tallan carbi yayi murmushi jin abinda tace, ya kalleta sosai yana fad'in " duniya kamar maciji ce, ga kyau ga laushi amma dafin cikinta yafi guba zafi da illa, ta kalli tsohon da nufin yin magana danja ta basu hannu. *CIGABAN LABARI* A matuk'ar tsorace ta mik'e tsaye duk ilahirin jikinta na rawa da tsuma, sakamakon ganin gawar me doya da kwai, dame shagon daya bata ruwa, da mutumin daya sai mata doya, duk da zuciyarta ta gama k'ek'ashewa bai hana hawayenta zuba ba, hankalinta ya kai k'oluwar tashi, rasa abinda zatayi yasa ta d'ora hannu aka ta durk'ushe k'asa, tayi shiru, ta kasa kukan fili saina zuciya, sautin dariyarshi ta daki dodon kunnenta, " bakiga komai ba yarinya, bazaki aikata alkhairi ki lalace ba saboda alkhairi dank'o ne baya fad'uwa k'asa banza, haka kuma bazaki k'ulla sharri ki gama lafiya ba, saboda sharri d'an aike ne duk nisan da yayi sayya dawowa meshi, kin cuceni kin lalata min rayuwa, kin rabani da duk wani farin ciki da jin dad'i na, busassun idanuwata da suka dad'e da bushewa ta d'ago ta kalleshi ido cikin ido, duk da bata k'aunar ganin koda sawayenshi ne, " na sani na kuma yarda ni me laifi ce ko awajen Allah, shi Ubangiji gafurur Rahim ne, shi mai yafiya ne, inata Istigfari da neman yafiyarshi, sai kaine baka yafiya? "Meyasa bazaka manta da abinda ya faru a baya mu fuskanci gaba ba? "Meyasa bazaka yafe min ba, bayan na tuba, na karb'i kuskure na, na baka hak'uri na nemi yafiyarka? Hannayenta ta had'e waje d'aya tana rok'onshi tare da bashi hak'uri, amma a banza sai dariyar dayake kyalkyalata mata, ganin bashi da niyyar hak'ura yasata mik'ewa taja k'afarta tayi gaba ta barshi anan, hannunta rik'e da zaninta dake neman fad'uwa, duk wata gajiya da yunwar da take ji sun tafi, tana d'angyashi tayi tafiya me nisan gaske, kana ta samu waje ta zauna ta zubawa k'asa ido tana hawaye had'i da tuno *D'ANTA*, a fili ta furta sunanshi " *DEEDEE* yaron dayaci sunan Babah, suka had'a sunansu waje d'aya ya bada *DEEDEE* * Deeyanah & Deen* *WAIWAYE....* Deedee ya taso cikin gata da kulawa, kowa cikin dangi na sanshi, ga Deedee da shiga rai, suna zuwa hutu jefi-jefi, saboda acan Deen yake aiki bayan ya gama abinda ya kaishi suka rik'e shi saboda kwazonshi, shekarun Deedee uku Deeyanah ta sake samun ciki, lokacin sun kusa shekara biyar da aure, watan ciki Deeyanah hud'u suka zo gida hutu, Murna wajen dangi da 'yan uwa ba'a magana, cikin dare matsanancin ciwon mara ya tasarwa Deeyanah , ta kasa bacci, sai juye-juye take ta kasa kuka, ta kasa tashin Deen ta fad'a mishi, saboda tasan yana da meeting me matuk'ar mahimmanci gobe, tana cikin wannan hali sai faman nishi take ya farka, a tsorace ya diro daga kan gadon, jikinshi na rawa ya k'arasa inda take, ya d'agota had'i da fad'in " lafiya? "Meke damunki? Da hannunta ta nuna mishi mararta while tana jujjuya kanta saboda azaba, jallabiya ya zira da sauri, ya sunkuya da nufin d'aukarta, da hannu tayi mishi alamar a'a, " please ki bari mu tafi asibiti, agogo ta kalla 2:30am na dare, shima agogon ya kalla danya gane nufinta, " na sani dare yayi, amma bakomai, dakyar tayi k'arfin halin cewa " ka bari ya lafa, zanyi bacci gobe maje, " kin tabbatar LOML! kanta ta d'aga mishi alamar eh, tallafe ta yayi ya kwantar da ita akan gado yaja mata bargo ya rufeta, cikin ikon Allah bacci me nauyi yayi gaba da ita, da wuri ya tashi ya had'a mata ruwan wanka, ya dafa mata tea, dama Deedee yana part dinsu Babah, da salati a bakinta ta tashi, idonta ya sauka akanshi, suka sakarwa juna k'ayataccen murmushi, " harka tashi? Tayi maganar tana murza ido, " ba dole na tashi da wuri na shirya zuwa asibiti ba, " asibiti kuma? Kallan da yayi mata yasata yin dariya tace " au ashe fa bani da lafiya ko? Ta fad'a cike da tsokana, " au ashe ne ma ko? " Kodan bake ke jin zafin ciwon ba? " Oh! haka ne fa ko? "Zafin a jikinka yake shiyasa bana ji, hancinta yaja yana dariya yace " tashi kiyi wanka muje kiga likita, " meeting d'inka fa? Kanshi ya dafe yana koikwayon muryarta yace " au ashe fa ina da meeting ko? Sosai ya bata dariya danta gane ramawa yayi, " Allah naji sauk'i kayi tafiyarka ba damuwa, " kinga tashi ki shirya mu tafi, yayi maganar yana d'agota, cikin shagwab'a tace " Allah na samu sauk'i, kayi tafiyarka, turata yayi cikin ban d'aki yana dariya, ta gama shiryawa tsaf, cikin shirinshi ya kalleta ya lumshe ido had'i da rausayar da kanshi, cikin sanyin murya yace " masha Allah, Ubangiji yayi halitta a wajen nan, ta cikin mudubi ta kalleshi a nutse tace " Yaya kayi tafiyarka meeting d'inka wallahi jikina da sauk'i, idan ka matsa sai naje da kaina kai kayi tafiyarka, ido ya zaro yana takowa gareta yace " na barki kiyi me? "Allah Dee! da gaske nake, damma ka matsa ne zani, amma badan haka ba, da babu inda zani, dakyar ta shawo kanshi ya yarda zaje meeting ta tafi asibitin da kanta, har bakin mota ta rakoshi tana d'auke da briefcase d'inshi, ya shiga ya zauna a mazaunin driver ya kalleta yana murmushi yace " kodai zakije ki d'auko hijab na kaiki da kaina inyaso saiki dawo, motar ta rufe mishi tana dariya ta juya da gudu zata koma gida danta san idan ta biye mishi saisu kwana anan, bayanta yabi da kallo yana murmushi, kanshi ya girgiza tare da yiwa motar key, harya kai bakin get zai fita ya tsaya had'i da kwala mata kira, " Deeyanah!, ta juyo tana dariya, ya d'aga mata hannu yana murmushi yace " ki kula da kanki please, an na baki amanar kanki, dan haka nan yaji jikinshi wani iri shiyasa hankalinshi yak'i kwanciya, tana dariya ta shige part d'insu. Hijab ta saka ta zari handbag da key d'in mota ta fice, part d'in iyayensu ta shiga ta gaidasu, ta sanar dasu zata asibiti bata jin dad'i, ganinta da Hijab yasa Deedee sanya kuka yana fad'in " Momy zan biki, kanshi ta shafa tana murmushi ta kasa cewa yazo su tafi tare, saboda kunyar iyayensu, ganin basu ce ta tafi dashi ba, gashi yana kuka yasata zama, ta kasa tafiyar, " kikace asibiti zaki? Cewar Babah, Ammi data gane meyasa tak'i tafiya tayi murmushi tana cewa " barta fasawa tayi saboda d'anta yana kuka bazata iya tafiya ta barshi ba, da sauri ta mik'e ta fice tana dariya cike da kunya, suma dariyar suke mata, Babah yace " rabu da ita zo ki d'auki d'anki, tana cigaba da tafiya tace " a'a  nifa ba haka nake nufi ba, ta k'arasa maganar tana shigewa mota, ta fice, tunda ta hau titi gabanta ke faman fad'uwa, a fili ta furta " innalillahi wa'inna ilaihir raji'un , " K'iiiiiiii motarta ta tsaya, tayi yin duniya amma tak'i tashi, ta fito daga cikin motar tana jan tsoki, jakarta ta bud'e ta fito da waya zata kira, Yana tuk'i cikin kwanciyar hankali, wanda a zahiri hankalinshi ba'a kwancen yake ba, tun bayan rabuwarshi da ita ya rasa sukuni da walwala, Shekaru biyar kenan rabunshi da ita, jin shekaru biyar d'inan yake kamar shekaru dubu biyar, yana rayuwa ne a tsaye amma ta ciki mutuwa yake yi a kowacce dak'ik'a, wayarshi dake ta faman ruri ya kalla kafin yaja d'an gajeren tsaki d'aga idon da zayyi idonshi ya sauka a kanta, kamar daga sama ya hangota tsaye jikin mota tana latsa waya, wucewa yayi had'i da girgiza kanshi dan idan da sabo ya saba da ganin gizonta, idanuwanshi sun dad'e da ribatuwa da ita, mudubi ya kalla yaga still tana tsaye, "kodai da gaske itan ce? Ya tambayi kanshi, bai san sanda ya taka mahaukacin burki k'ukk'uuuuuuuuu ba saida gabanta yayi mummunar fad'uwa dataji k'arar burkin, jikinshi na rawa ya fito, bakinshi na rawa ya furta " Dee.....ya...nah!, yayi maganar a rarrabe kamar me koyan magana, wata irin mahaukaciyar fad'uwa gabanta yayi, cikin kid'ima da tashin hankali taja baya tana fad'in " Aj....lal, kyakkyawan murmushinshi ya sakar mata yana fad'in " ashe zaki gane ni? Cikin murmushin yak'e muryarta na rawa tace " so..sai ma, kawar da idonshi yayi daga kanta, dan jin wani irin mugun sonta da sha'awarta na taso mishi, take yaji tamkar bai tab'a santa a duniya ba sai a wannan lokacin, wutar santa data lafa mishi ta taso mishi, saboda ita yak'i aure, dan kullum gani yake zata dawo gare shi, ko sau d'aya bai tab'a cire rai da samunta ba, akanta yake kallan matan duniya tamkar maza ba mata ba, motarta ya kalla yana fad'in " lafiya meya samu motar? Yak'e ta kuma yi tace " tsayawa tayi, hannu ya mik'a mata yana fad'in " bani key d'in, ba musu ta bashi, dan kallo d'aya zakayi mata kasan a tsorace take, yayi yin duniya motar tak'i tashi, ya fito yace " tak'i tashi ina zaki? "Asibiti... Sai a lokacin ya kula da cikin jikinta, wani abu yaji ya tokare mishi mak'oshi saboda bak'in ciki, murmushin dole ya k'ak'aro yace " muje na aje ki, " a'a ka barshi zanyiwa k'aunata waya yazo yakaini, ido ya runtse da k'arfi kana ya bud'e yana fad'in " ki tambaye shi idan ya yarda saina kaiki, tab! tashin hankali wanda ba'a saka maka rana, Deen zatayiwa maganar Ajlaal, bayan tasan yafi san mutuwarshi akan Ajlaal, "A'a zan hau napep kawai, yin duniya tahau ya kaita tak'i hawa, tsakiyar titi ya koma yayi zaman cin abinci ya tankwashe k'afafuwanshi, cikin mamaki ta kalleshi kana ta mayar da kallanta kan uban go slow d'in daya had'a, mutane sai zagi suke yi, " ka tashi please, maimakon ya tashi sai yayi kneel down a gabanta, yana fad'in " dan Allah ki hau na kaiki, yayi maganar hannunshi had'e alamar rok'o, batare daya damu da yadda mutane ke kallanshi ba, tasan halinshi da mugun taurin kan tsiya, idan ya kafe akan abu ko za'a mutu bazai yanje ba, ganin mutane sun fara cire waya zasuyi musu video yasata cewa " tashi muje, da sauri ya mik'e duk ilahirin jikinshi na tsuma, ya bud'e mata gaban mota, tak'i hawa ta bud'e baya ta shiga, mudubi ya saita yana kallanta, yana fad'in " shekaru biyar, watanni 60, sati 260, kwanaki 1800, awanni 43,200 ban ganki ba Deeyanah, cikin matsanancin mamaki ta d'ago kanta dake duk'e ta kalleshi, "kina mamaki ko? Guntun murmushi yayi yace " yau da gobe taba canja komai Deeyanah sai dai tana nuna mata hak'ik'anin mutane, shekaru, watanni, satittika basa iya canja hak'ik'anin abinda ke cikin zuciyar masoyi na gaskiya, " niko kaga na dad'e da mantawa da rufe babinka a rayuwata, dan baka zame min dole saina rayu dakai a tunani ba, kamar yadda ban zame maka dole saika rayu dani a rayuwarka da zuciyarka ba, ko dani ko bani, ko da kai ko ba kai kowa zai iya gudanar da rayuwarshi, danya kawar da maganar yace " yaranki nawa? Banza tayi kamar bazatayi magana ba kafin tace " 1 DeeDee, " DeeDee! Ya maimaita sunan kafin yace " Dee yana nufin Deeyanah ko? Sosai yake bata mamaki amma data tuna yadda yake da kwakwalwa saita daina, murmushi tayi tace "eh! while d'aya Dee d'in kuma na nufin Deen, kai fa kana da aure? "Hmmmmm ina ni ina aure bayan kina raye kina taka doran k'asa, koda bakya raye bazan tab'a yin aure ba, muddin bake ce matar ba, yayi maganar cikin ranshi, a zahiri kuma yace " eh nayi aure harda yara biyu, Deeyanah da Ajlaal , sunan yarana, dayake 'yan biyu shine na saka musu sunan mu, idan tace bataji tausayin shi ba k'arya take take yi, "wannan wacce irin soyayya ce? Ta fad'a cikin ranta, cikin sanyi tace " Allah ya raya su, ya amsa da " Amin ya Allah, kanta ta mayar kan wayarta ta cigaba da abinda take yi bata k'ara yi mishi magana ba. ************************************* Farkawa tayi ta ganta a gidanta mijinta Deen zaune kusa da ita yana yi mata sannu, sosai kanta ya kulle bazata iya tuna komai ba, daga lokacin da take zaune a motar Ajlaal yana fad'a mata sunan yaranshi, kanta ta dafe tana san tuna wani abu amma ta kasa tuna komai, jikinta tabi da kallo taga babu abinda ya canja, ta kalli Deen tace " Dee! ya akayi nazo nan? "Waya akayi min, aka sanar dani nazo na d'aukeki an tsince ki cikin motarki a sume, ajiyar zuciya ta sauke still tana san tuna wani abu ta kasa, kanta take tambaya da " meya faru dani? "Ya akayi haka ta faru? "Ina Ajlaal? "Meke faruwa ne? Ta jerawa kanta da kanta tambayoyin, tayi nisa cikin duniyar tunani ya katse mata tunani da fad'in " dama saida nace miki ki bari na kaiki kikace a'a, cikin mutuwar jiki ta kwantar da kanta saman k'irjinshi tana fad'in kayi hak'uri, ya shafa kanta yana murmushi, shiya taimaka mata tayi wanka ya shirya ta, hannunta cikin nashi suka fito falo ya zaunar da ita tare da bata abinci a baki, sukuku take Allah kad'ai yasan meke faruwa cikin ranta, haka nan hankalinta yak'i kwanciya, wani irin mugun tsoro da fargaba suka shige ta, in banda fad'uwa babu abinda gabanta keyi, tana san ta fad'awa Deen gaskiyar abinda ya faru tana jin tsoro. Bayan kwana biyu Deeyanah zaune a falo tana kallon SunnaTv, ta shagala sosai da kallan saboda tarihin Sayyadina Umar ake yi, film d'in ya tafi da ita, shigowar sak'o cikin wayarta yasata d'auke idonta daga kan TV ta mayar kan wayarta, sharewa tayi ta cigaba da kallanta, jim kad'an wayarta ta soma rori, saida taja tsoki saboda an katse mata kallanta kana tayi picking wayar batare data duba number ba, " Assalamu Alaikum, Amin wa'alaikissalam, jin muryar Ajlaal yasata zaro ido sosai a tsorace, " lafiya? "Ina ka samu number ta? Cikin isa da tak'ama yace " zan turo miki address d'in gida na kizo yanzu ina san ganinki, wayar ta cire daga kunnenta ta duba a karo na biyu, kana ta mayar da wayar kunnenta tana fad'in " ka san wacce ka kira kuwa? " Inaga baka san da wacce kake magana ba, dariya ya sanya sosai yana fad'in " da Mrs Deeyanah Deen nake magana na sani, tsaki taja had'i da cewa " inaga dai ka samu tab'in hankali Ajlaal, tana k'ok'arin kashe wayar yayi saurin cewa " a'a kul karki soma kashe min waya, ga sak'o nan na turo miki ta WhatsApp ki duba saiki yanke hukuncin zaki zo ko a'a, yana gama magana ya kashe wayar, jikinta na rawa ta duba WhatsApp d'in, video ta gani ya turo mata hannunta har rawa yake, tayi playing videon, itace kwance tsirara haihuwar uwarta da ubanta, tana kwance wani namiji yazo shima jikinshi ba kaya amma ya rufe fuskarshi da mask, ita da kanta ta jawoshi jikinta ya fad'a kanta, suka shiga aiwatar da masha'a. Bata san sanda ta buga wayar da bango ta tarwatse ba, kanta ya shiga juyawa ta soma ganin komai bibbiyu, k'ara tayi ta sulale k'asa a sume.Bata farka ba sai cikin dare, bakinta d'auke da salati ta dafe kanta tare da yamutsa fuskarta, a hankali ta bud'e idanuwanta da sukayi mata nauyi ta fara ganin komai dishi-dishi kafin a hankali idanta ya washe tarr, k'ok'arin mik'ewa zaune ta soma hannunta dafe da kanta, " yi a hankali, taji an furta daga gefenta, idonta ta sake warewa sosai tana bin inda take da kallo, sai a lokacin ta kula da a asibiti take, hannunta jone da cannula ana k'ara mata ruwa. "Sannu..! Deen! yace yana tallafe ta, juyawa tayi ta kalleshi, tana d'ora idonta akanshi komai ya shiga dawowa mata, tunaninta ya dawo, wata irin mahaukaciyar k'ara tayi tare da tushe kunnuwanta da hannayenta ta saki rikitaccen kuka tana fad'in. "Na shiga uku!... na shiga uku na lalace. "Subhanallah me yayi zafi haka Deeyanah? Deen ya fad'a yana rik'e ta. Ammi tace " kul karna sake jin kince kin shiga uku kinji ko? A haukace kamar zararriya ta kalli Ammin tana girgiza kanta while tana kukan tace " idan da abinda yafi shiga uku ma na shiga, na shiga dubu ma ba uku ba, ina cikin bala'i da musiba Ammi, wannan wacce irin bak'ar k'addara ce Allah ya d'ora min? "Me yasa saini? Rik'e mata hannu Ammi tayi tana fad'in " kowacce dak'ik'a data harba a agogo tana harbawa ne da rubutun wata k'addara a rayuwarmu, K'addarar da zatana iya zama shafi cikin littafin rayuwarmu, fatanmu Allah ya gina mana katangar karfe da mummunar k'addara. Cikin kuka Deeyanah tace " amma meyasa saini? "Meyasa akaina kawai zata fad’a? Idon Deen kanta yace " Deeyanah ki manta da abinda ya cutar dake amma karki sake ki manta da darasin daya koyar dake, zatayi magana Deen yace " wai mema ya firgitaki haka? D'an jimm tayi tana tunanin ta fad'a musu ko karta fad'a musu, "kiyi addu'a koma meye yazo miki da sauki saboda taka tsantsan baya hana afkuwar masifa, amma addu'a tana tasiri akan masifar data sauka dama wacce bata sauka ba, Masifa takan sakko sai addu'a ta tareta, suyita fafatawa har ranar tashin alkiyama, kinga masifar bazata cimma ma'abocin addu'a ba, cikin mutuwar jiki tasa hannu ta goge hawayen dake ta faman zubowa saman fuskarta, " Ammi ki tayani addu'a mummunar k'addara ta afkawa min. Kallon juna Ammi da Deen sukayi kafin suka mayar da kallonsu ga Deeyanah cikin rashin fahimta Ammi tace " kamar ya ban gane inda maganarki ta dosa ba!? "Bazaki gane ba Ammi. "Duk irin bayanin da zanyi miki bazaki fahimci komai cikin zance na ba, ni kaina na kasa fahimtar komai, ko kalma d'aya na kasa fahimta Ammi. "Ki nutsu kiyi ki kwantar da hankalinki, kyayi mana bayani daga baya, Deen ya fad'a yana k'ok'arin had'a Ido da ita tak'i bashi dama, wani iri take ji cikin jikinta wai itace tayi video tsiraici na batsa? Itace irin wannan bak'ar k'addarar ta fad'awa, komawa tayi ta kwanta had'i da lumshe idanuwanta hawaye na gangarowa ta gefen idanuwanta. Ba bacci takeyi ba, tana jin hirar da Ammi da Deen keyi amma bata fahimci ko kalma d'aya cikin maganganun da sukeyi ba, hankalinta baya jikinta, k'ofar d'akin aka bud'e DeeDee ya shigo da gudu yana fad'in Momy, wani abu babba taji ya tokare mata mak'ogwaro ya soki Zuciyarta. "Momy! Deedee ya fad'a yana fad'awa jikinta. A fili ta sauke nannauyan ajiyar zuciya kafin ta d'agoshi tana k'ak'aro murmushin k'arfin hali ta lullub'awa fuskarta. "Ki daina bari yana fad'a miki kinga ba ke kad'ai bace kar wani abu ya samu d'an cikinki, Ammi ta fad'a tana kallan yanayin Deeyanah, murmushi tayi batare da tace komai ba, su Babah suka shigo bakinsu d'auke da sallama, "au wai dama tare kuke dashi? Eh! Mana ya gudo wajen iyayenshi yabarmu ba. "Sannu Deeyanah ya jikin naki? Cikin sanyin jiki da muryarta da bata fita sosai tace " da sauki? "Wai meke damunta ne? "Ince dai ba bari tayi ba ko? Abbi yayi maganar a lokacin d'aya yana kallan Deen. "Ga cikin ya d'an soma fitowa ma ba wani b'ari lafiyar cikin lau. Cewar Ammi tana kallan cikin jikin Deeyanah. Deen ya sauke ajiyar zuciya yace " nima dai ban san meke damunta ba Ina shiga gidan na ganta kwance k'asa a sume. Ammi tace " To wai fad'uwa kikayi ne ko kokuwa dai wani abunne ya faru? Deeyanah najinsu amma batayi magana ba. "Deeyanah dake fa ake magana kinyi shiru kina jin mu, batare data d'ago kanta ba tace " bakomai Ammi,  "to Allah ya kyauta. Gaba d'ayansu suka amsa da "Amin. Kwanakin Deeyanah uku a asibiti aka sallameta kowa ya fahimci akwai abinda ke damunta dan kallo d'aya zakayi mata kasan tana tattare da tarin damuwa. Tun bayan komawarsu gida komai nata dana gidan ya canja ta zama wata sukuku ta daina magana sosai sai jefi-jefi ta koma shiru-shirun dole, duk suturun Deeyanah da faram-faram d'inta duk sun zamana babu duk lokacin dazaka ganta sai dai ka ganta zaune ta rafka uban tagumi hannu bibbiyu, dama wayar ta lalace layinta a kashe yake. Tana zaune bakin gado ta rufe kanta a d'aki tana rusgar kuka wiki kamar ranta zai fita, idanuwanta har sun kumbura tana fad'in, " wayyo Allah! na shiga uku! " Ni Deeyanah na shiga uku rayuwata ta lalace tashin duniyata yazo, na jefa kaina da rayuwata a cikin masifa da babban k'alubalen da babu mai fitar dani sai Allah. Zamewa tayi daga saman gadon ta durk'usa k'asa saman gwiwowinta ta d'aga hannayenta sama a fili ta soma addu'a. "Ya Ubangijin Al'arshe ya Ubangijin sammai da k'assai ya gagara buwayi majib'ancin al amura me tausayi mai jin k'ai me yaye damuwa, ya Allah ya ka kawo min mafita, ka jib'anci ramura na, kayi min mafita ka kareni daga sharrin wannan bawa naka kayi min tsari daga kaidinshi, ta zame takai sujjada bata damu da cewar ko hijabi babu a jikinta ba while tana cigaba da rusa kuka. Tsaye yayi cak yana kallanta cike matsanancin mamaki ya kasa fahimtar komai amma yaji komai, sai dai babu abinda ya iya ganewa kanshi ya juye a fili ya furta. " Ka kareni daga sharrin wannan bawa naka, kayi min tsari daga kaidinshi? "Waye wannan d'in da Deeyanah ke magana akanshi? Yayi maganar kamar me koyan magana, cikin rashin gwarin jiki ya jawo k'afarshi ya k'araso kanta yayi tsaye yadda take rusa kuka sosai yake tab'a mishi zuciya. " Deeyanah! Ya kira sunanta a hankali cikin nutsuwa, bata shigowarshi ba balle motsinshi sai muryarshi dataji a kanta, da sauri ta d'ago daga sujjadar yana d'ora idonshi a kanta gabanshi ya fad'i saboda gaba d'aya kamaninta sun canja yadda kasan ba itace Deeyanah ba. Itama a mugun tsorace take dan tana gudun koya fahinci maganganunta, a hankali yasa hannayenshi ya d'agota ya zaunar a gefen gado ya fita, bai dad'e ba ya dawo hannunshi d'auke da ruwa ya mik'a bata ta karb'a tashanye tas ta mik'a mishi kofin tana sauke ajiyar zuciya. Ido ya zuba mata batare dayace mata komai ba har tsayin lokaci kafin yayi gyaran murya yace " meke faruwa dake ne Deeyanah? Bata d'ago kai ta kallaeshi ba balle tayi magana. " Ina tunannin duk duniya babu wanda kike da kusanci dashi sama da ni a halin yanzu, nafi kowa damar sanin damuwa da matsalarki Deeyanah, ni nafi kowa cancanta dana share miki hawayenki dake zuba, dani ya kamata ki raba damuwarki, ki daure ki fad'a min abinda yake damunki dan mu tari matsalar tunda wuri, karki bari sai abun ya girmama ya wuce mu tare shi, koma meye ki sanar dani dan ina da tabbacin ya shafeni, kina da matsayin dako aure bai shiga tsakaninmu ba zan tsaya miki tsayin daka akan matsololinki balle kina matsayin matata kuma uwar 'yayana, dan Allah mu raba k'uncinmu, damuwarmu, bak'in cikinmu da kuma kukanmu tare, ki sanar dani dan girman Allah ni kuma nayi miki alk'awarin ko abinda na mallaka zai k'are kuma ko zan rasa rai na zanyi miki maganinshi please. Yayi magamar so calm. Tasan duk abinda ya fad'a gaskiya ne, amma tayaya zata kallanshi ta sanar dashi ta hau matar Ajlaal har ya kaita gidanshi yayi zina da ita? Ta yaya zata sanar dashi tayi zina da Ajlaal da aurenshi a kanta? Bayan tasan kishin Deen a kanta, tasan yadda yake bala'in kishinta, tasan duk duniya babu wanda ya tsana sama da Ajlaal, jifa yadda ya nemi yin hauka a baya da bama soyayya suke yi ba, balle yanzu da suka had'a jiki tasan mutuwa Deen zayyi idan yaji wannan maganar. Yadda tayi shiru tana tunani ya k'ara tabbatar mishi da lalle akwai wani abu, ya bud'e baki zayyi magana tayi saurin cewa " bakomai! Cike da mamaki ya kalli kwayar idonta tayi saurin sunkuyar da kanta k'asa " bakomai fa kikace? Cikin sanyin jiki tace " bakomai Abban Deedee babu abinda yake damu na, kamar zayyi magana sai kuma ya fasa, ya mik'a mata kwalin sabuwar waya yana fad'in " gashi wancan bazata gyaru ba layinki yana ciki. Yadda kasan ya mik'o mata wuta taja baya da sauri had'i da girgiza kanta tace " A'a Yaya ka barta a wajenka letter zan karb'a. Abun kuma ya fara bashi tsoro yadda Deeyanah ke san waya amma itace yau ke rejecting waya, sun sha yin fad'a da ita akan waya dan ta bawa waya mahimmanci sosai a rayuwarta, danya tabbatar da abinda yake zargi ya sake tura mata wayar ta zabura taja baya muryarta na sark'ewa tace " no please Yaya ka barta zan karb'a, harta fice idonshi nakanta cike da matsanancin mamaki fal ranshi ya kasa magana. Cikin bacci sama-sama taji kamar ana shafa mata fuska, a hankali ta bud'e idanuwanta da dama ba wani baccin kirkine a cikinsu ba karaf idanuwanta suka sark'e cikin na Ajlaal saurin mayar da idanuwanta tayi da runtse da k'arfi tana fad'in " A'uzubillahi minashshaid'anir rajim! Allahumma ajirni fi musibati! Dan a tunanin ta mafarki ne ko kuma tayi mummunan gamo! Dariya yayi sosai had'i da shan yaji shhhh kafin yace " nine shaid'anin da kike neman tsari daga ni? Saurin bud'e idanuwanta tayi dan jin muryarshi ta daki dodon kunnenta idanuwanshi ya lumshe had'i da turo bakinshi ya jefa mata kiss, saurin kallan gefen da Deen ke kwance tayi taga wayam baya nan. " Wa kike nema 'yan matana!? So take tayi magana amma bakinta yayi nauyi sai leb'enta dake motsi kamar an d'ora musu garwashin wuta. Fuskarshi d'auke da shu'umin murmushi yace " fad'i! Shiru d'akin yayi, babu abinda jikinta keyi sai rawa gami da kerrrrma " fad'i abinda kike san fad'a mana! Yayi maganar idonshi kan wuyanta, still kasa magama Deeyanah tayi ya matso gaf da ita tare da cusa kanshi wuyanshi yana shinshinar k'amshin jikinta, sai a lokacin taji wani irin k'arfi yazo mata, tasa hannayenta duka biyun ta hankad'a shi baya, yayi dariya tare da mik'ewa tsaye, itama tayi saurin dirowa daga kan gadon ta mik'e cikin dakewa ta nunashi da yatsa ta bud'e baki zatayi magana ya rik'e yatsan data nunashi dashi ya jefashi cikin bakinshi ya soma tsotsa yana lasa kamar ya samu alawa. Tayi saurin fisge hannunta tana jefa mishi wani irin kallo ya fisgota ya manneta da bango kafin ya matseta jikin bangon ya lumshe ido yana shinshinar gashin kanta yace " karki tambayeni abinda ya kawo ni ko ta ina na shigo ko ya akayi na shigo dan ina da hanyoyin shigowa da yawa ke ko kark'ashin k'asa kika shiga saina nemoki duk inda zaki shiga a duniya saina bincikoki Deeyanah, abinda kuma ya kawo ni shine na fad'a miki ki karb'i wayar da kwartanki ya kawo miki dan mu rink'a magana Inba haka ba wallahi kullum saina zo gidan nan, ido ta zaro cike da mamakin yadda akayi yasan Deen ya bata waya tak'i karb'a. Dariya yayi yace " kina mamakin yadda akayi na sani? "Nasan kinki karb'ar wayar ne saboda ni, dan zaton k'aramar kwakwalwarki idan baki da waya bani da wata hanya da zan same ko? Cikin tsoro ta kalleshi dan kuwa haka ta aiyana cikin ranta to ya akayi Ajlaal yasan abinda ta yanke cikin ranta. Yayi murmushi yace " ai nayi zaton daya tambayeki abinda yake damunki zaki sanar dashi gaskiya, ita kam yanzu abun nashi ya soma bata tsoro anya Ajlaal ba Aljani bane? Kallan d'akin ta soma cike da tsoro da matsananciyar fargaba, bakinta ya tsotsa sosai kafin yace " ki karb'a, idan baki karb’a ba hakan yana nufin kina san kullum na dinga zuwa, yana kaiwa nan ya juya ya fice batare data iya furta koda kalma d'aya ba. Tana jikin bangon Deen ya shigo, ta kalli agogon bangon dake dak'in taga k'arfe 3:40am na dare ajiyar zuciya ta sauke a hankali tasan sallahr dare yayi, ya kalle ta kamar zayyi magana sai kuma ya fasa. "Ina wayar nan? Da mamaki k'arara a fuskarshi ya kalleta magana yayi niyyar yi sai kuma ya fasa ya fita ya d'auko mata ya dawo ya mik'a mata ya koma ya kwanta saman gadon, tana tsaye ta bud'e wayar IPhone 14pro ta junata a caji tana saka ta a caji ta kunna kanta, second 10 da kunna wayar sak'on Ajlaal ya shigo. "Zab'i me kyau. D'an d'agowa yayi daga kwancen yace " idan kin gama ki kashe mana fitilar, 'yar razana tayi ta tsorata ganin yadda ta tsorata yasa shi cewa "kina lafiya kuwa? Ya tambayeta "bakomai, tace tana kwanciya saman gadon, wani sak'on ya sake shigowa. "Au gado d'aya ma zaku kwana? Wayar ta saka a do not disturb ta juya tayi kwanciyarta amma ko kad’an baccin bayyi gigin rab'arta ba. Sai bayan sallar asuba bacci ya d’auke ta, bata farka ba sai wajen sha d'aya na safe ganin gari tarr yasata saurin wartsakewa ta mik'e ta fad'a band'aki ta d'auro alwala a gurguje tayi sallahr walaha kana ta shirya ta fita, tama manta da batun wata waya. Kitchen ta nufa ta had'a tea me kauri ta fito tana kurb'a bata nemi Deeedee ba, dan tasan yana part d'in Ammi, a nutse ta gama shan shayin kana ta mik'e ta mayar da cup d'in kitchen ta aje direct bedroom d'insu ta koma danta gyara fulallukan ta fara kwashewa ta bankad'a zanin gadon aiko wayar ta gangaro wata irin muguwar fad'uwa gabanta yayi a d'an tsorace ta mik'a hannu ta d'auki wayar, hannunta har rawa yake while gabanta na tsananta fad'uwa. 50 missed call d'in Ajlaal ta gani duk da batayi saving number shi ba amma tasan shine dan tasan shine zayyi mata wannan kiran haukan. Ta cire wayar daga do not disturb message kam 30 ta gani, jikinta ba kwari ta zame ta zauna bakin gadon. "Kizo gida na Ina san ganinki! Text d'in farko kenan na biyu kuma cewa yayi. "I want fuck your fucking pussy right now, so come an meet me at my home! Sai d'ayan kuma cewa yayi. " Ina da video nan still in my phone ki duba WhatsApp d'inki na sake tura miki wallahi idan baki zo ba I will send it to your Husband right now. "Are you kidding me! Oh! You are testing me, you are tasting my patient? Tana cikin duba sak'onin wani sakon ya shigo "On my way to your home so get ready for me, an lastly zan nunawa kowa videon. Da sauri ta mik'e tsaye hannunta na wani irin rawa ta danna mishi call, bugu d'aya yayi picking ya tuntsure da wata irin dariya, a hankali ta runtse idanuwanta hawaye na gangarowa saman kumcinta tace " dan girman Allah Ajlaal ka kyale ni, ka rufawa rayuwata asiri ka fita daga duniya ta, shin menayi maka da zafi haka? "Wanne laifin na aikata maka da kake san tarwatsa min rayuwata? Dariya yayi sosai kafin yace " zaki zo ku kuma na shigo? Sai da ta runtse idonta da k'arfi kana tace " za.....n .... Z....o " Better! yace had'i da kashe wayar. Jikinta na wata irin rawa ta mik'e ta zumbula hijab ta suri wayarta ta fice daga gidan, text tayiwa Deen da " na fita please! Bazata iya gane gidan ba dan ba'a cikin hayyacinta take ba, haka zuwanta d'aya gidan shima bana dad'i ba, ko unguwar ma bata sani ba balle gidan, k'ara shigowar text taji dan haka ta duba, ki duba WhatsApp na turo miki location dan naga kamar bazaki iya kawo kanki ba. Batayi mishi reply ba tabi location d'in daya turo mata ya kaita har k'ofar gidan, baya tayi da motar sosai tayi parking nesa da gidan ta tako a hankali tana waige-waige kamar munafuka. Sake jin shigowar text tayi ya shigo wayarta ta duba " feel free my Bobo! ki daina sand'a kina waige-waige ki taho kanki tsaye kawai. Ajiyar zuciya ta sauke a fili ta isa bakin get d'in tayi tsaye ta kasa shiga gidan in banda dukan uku-uku babu abinda k'irjinta keyi. " Ki shigo get d'in a bud'e yake, ta karanta text d'in daya sake turo mata, sai da ta sake d'aukar lokaci kana ta tura ta shiga gidan. Gidan babbane sosai sama da k'asa ya tsaru an kashe kud'i sosai wajen ginin gidan, irin ginin turawa ga motoci nan zube a parking space bazata iya k'iyasta adadin kud'in da aka zuba wajen ginan gidan ba ga garden da swimming pool, k'ofar shiga cikin gidan ta nufa kanta tsaye ta d'ora hannunta a saman handle ta murd'a ta bud'e wani irin mahaukacin bugu zuciyarta keyi yadda kasan zata tsaga k'irjinta ta fito. Tsaye tayi tana bin ko'ina na falon da kallo, wayar hannunta ta d'auki k'ara sai da tad'an zabura saboda tsoron da take ciki, ajiyar zuciya ta sauke kana ta goge gumin dake tsatstsafo mata a fuska ta d'aga wayar ta kara a kunnenta. " ki hawo sama. Zata kashe wayar yayi saurin cewa " don't drop my call, tana rik'e da wayar yana fad'a mata inda zatabi har ta isa tsakiyar wani babban falo, kamar daga sama taji an d'aga ta sama ya shiga juyi da ita cikin falon. " I missed you my love! "Tun d'azu na k'agu na ganki fa, yana k'ok'arin had'e bakinsu tayi wuf ta gartsa mishi cizo a lips d'inshi, da iya k'arfinta ta gatsa leb'en nashi, har sai da ya kusa yar da ita, siririyar k'ara ya saki tare da runtse idanunshi da k'arfi, ta sauri ta dire saman k'afafunta taja baya, shi kuma yayi ruku'u saboda azaba, idanuwanta sun k'ek'ashe cikin rashin tsoro da bushewar zuciya ta nunashi da yatsa cike da zallar masifa da hargowa soma magana. "Kai! K'aramin shaid'ani, fasik'i!, fajiri, mak'iyin Allah wallahi karya kakeyi ka lalata min rayuwata, kayi kad'an ka wargaza min duniyata da rayuwa, ni ba lalatacciya bace irinka, banza d'an hau! Marar tarbiya, jahili wanda bai san Allah ba, wallahi idan baka tuba ba wuta zaka, ka rink'a neman matar aure. Cikin nutsuwa ya d'ago fuskarshi d'auke da shu'umin murmushi mai d'auke da ma'anoni da dama kawata-kwata babu alamun fushi ko b'acin rai da fusata a tattare dashi, tsayawa yayi sosai had'i da zuba hannayenshi cikin aljihun wondonshi yana kallanta. "Nace maka ka fita daga rayuwata! Ka barni nayi rayuwata cikin salama a duniyata tare da ahalina, ka daina bibiyata kana addabata kana barazana ga walwala da farin ciki na, ta k'arashe maganar had'i da had'e hannayenta waje guda alamar rok'o, ido cikin ido yake kallanta har zuwa lokacin fuskarshi d'auke da murmushi bayyi magana ba. Ta juya ta taka zata fita daga falon ya gyara tsaiwarshi sosai had'i da hard'e hannayenshi a k'irjinshi. " Deeyanah!. Ya kira a wahalce. " Wallahi idan k'afarki ta sake tako d'aya daga inda kike saina saki videon nan ga duniya ki zama macen Bahaushiya musulma 'yar arewa cin Nigeria ta farko da zata fara yin videon iskanci, saina d'orashi a duk wata kafar sada zumunta da kika sani wahil azim. A fusace ta juyo tace " sake shin wa duniya mana sai me ai kaima kana cikin video kaga kai kuma saika zama namijin Bahaushe musulmi d'an arewa cin Nigeria na farko da zai fara yin videon iskanci. Dariya yayi sosai harda rik'e ciki yace " da alama baki kalli videon sosai ba, ai fuskata bata fito ba kwata-kwata sai da na saka protection na rufe fuskata tsaf, takowa tayi gabanshi gaf da gaf har suna iya jiyo numfashin juna tace " idan fuskarka bata fito ba ai tsiraicinka ya fito. Kafad'a ya d'age had'i da d'age gira d'aya yace " sai me dan tsiraici na ya fito? " Idan zaki bi duniya rataye da Al-Qur'ani kina cewa nine babu me yadda saboda babu wanda yasan tsiraici na, k'asa-k'asa yayi da murya yakai bakinshi saitin kunnenta yace " sai ke kad'ai kika san tsiraici na ke kikayi disvirgin d'ina, ya k'areshe maganar had'i da kashe mata ido d'aya. "Idan na fito na k'aryataki Ina da damar da zanyi shari'a dake nace kin b'ata min suna akan wannan kina iya zuwa gidan yari tunda baki da wata hujjar da zata tabbatarwa da duniya cewar ni d'in ne da gaske, yayi maganar yana zagayata. Durkushewa tayi a k'asa had'i da fashewa da wani irin rikitaccen kuka tana fad’in " wannan wacce irin bak'ar k'addara ce? " Meyasa sai ni ta fad'awa? " Me nayi, wanne laifin na aikata? " Allah na tuba ka yafe min, Astagfirullah Astagfirullah na wa'itubi alaik, na tuba ya Ubangiji ka yafe min idan wani laifin na aikata. Kneel down tayi ta durk'usa bisa gwiwowinta ta had'e hannunta tana fad'in " kayi hak'uri dan zatin Allah kabarni, kayi min hak'uri idan nayi maka wani laifi bisa rashin sani. Baki ya tab'e yace " kidaina wahalar da kanki wajen bani hak'uri dan idan duniya zata tashi idan sama da k'asa zasu had'u babu mai rabani dake a wannan lokacin a wancan lokacin dai an rabani dake but not now Deeyanah babu mahaluk'in daya isa ya rabani dake a wannan karon, ke tawace ni kad'ai Deeyanah. Cikin matsanancin kuka tace " me nayi maka Ajlaal? "Meyasa kake azabatar dani ta wannan hanyar why Ajlaal? " Love! "It's Love Deeyanah. "Ina sanki fiye da kowa da komai, zan iya kashe duk wanda yace zai shigo gabana akanki, kamar yadda kika ji nace zan iya kashe kowa akanki Ina nufin kowa ban cire miki kowa ba, a yadda nake ji akanki zan iya yak'ar duniya da abinda ke cikinta akanki, Ina sanki fiye da kaina zan iya bada raina akanki. "So hauka ne Ajlaal!? "Dan kana so na saika tarwatsa min gobe na? "Ko haka ka gani ana soyayya a duniya? " Ni kalar tawa soyayyar kenan Deeyanah. " Dan Allah ka tausaya min ka barni na rayu da yarana da mijina, ni matar wani ce, kuma uwar wasu. Zubewa yayi a gabanta, ya durk'usa saman gwiwowinshi yana fitar da wani irin nishi " nima ki tausaya min sanki na neman zauta ni, ki tausaya min ki rayu dani ki haifa min yara kamar yadda kika haifawa Deen Please!? "Mijin nawa da d'an nawa zan bari na dawo maka ko me kake nufi? "Ka ga fa Ajlaal ciki ke gare ni, Ina d'auke da wani d’an nashi fa. "Mijinki!, D'anki!, da kuma cikinki su kad'ai ne damuwar!? Kanta ta sunkuyar batare data bashi amsa ba. Idanuwanshi waje kamar zasu fad'o k'asa yace " to idan suka mutu fa!? " Shikenan zaki dawo gareni? A zabure ta mik'e tsaye tana ja baya had'i da girgiza kanta tana fad'in " a'a Ajlaal a'a no please basu ne damuwar ba karkayi musu komai!? " To ki aure ni! ya fad'a a haukace!, “ saboda ke nake zaune har yanzu banyi aure ba, saboda bana kallan kowacce mace a matsayi mace, duk tsayin shekarun nan kullum kwanan duniya zaman jiranki nake yi, kuma kullum Ina jin zaki dawo gare ni, wallahi Deeyanah ban tab'a sanin wata 'ya mace ba saike, kece mace farko dana fara had'a jikina da nata, ki daure ki hak'ura da Deen kije ya sakeki yabar min ke na aure ki shikenan komai ya wuce. "Iyayena bazasu tab'a bari in aureka ba, Babah bazai tab'a amincewa aurenmu ba, bazasu bari Deen ya sake ni ba. A haukace yace " idan kuma duk suka mutu fa zaki aure ni? A rikice tace " A'a karsu mutu please. "To ki aure ni idan baki san su mutu, ki fanshi rayuwarsu ta hanyar aure na. Bakinta na rawa kamar mazari tace " miji na da..... slicing glass door d'in ya daka da k'arfi k'ofar ta fashe glass d'in ya yanki hannunshi jini ya fara d’iga daga hannun, "Mijinki! Mijinki!  ya fad'a ya sake dukan bango. Sosai tsoro ya sake kama Deeyanah jikinta ya d'auki rawa da kerrrma  ya juya ya nufota gadan-gadan da baya da baya take tafiya yana biyota har suka kai bango idanuwanshi da suka gama rinewa zuwa asalin jajaye ya zuba mata. "Zab'i ya rage naki, ko ki fito na aureki kona cigaba da nemanki a haka kina haifa min 'yaya idan kuma kikak'i zab'ar ko d'aya daga cikin zab'in nan dana baki zan saki videon wa duniya sannan na k'arar da gaba d’aya ahalinki. In banda kakkarwa da tsuma babu abin jikinta keyi, ya gama cika mata ciki taf da tsoro bata jin zata iya furta koda kalma d'aya saboda yadda kasan dodo ko wani mutum da yazo daga wata duniyar ta daban haka take kallanshi, ya canja mata, gaba d'aya kamaninshi sun rikid'e yadda kasan bashi ne Ajlaal d'in data sani ba. Maganarshi ta katse mata tunaninta " yanzu bazan barki ki tafi haka ba saina kashe wutar data ke cina, yayi maganar fuskarshi d'auke da murmushi yadda kasan bashi ne yanzu ya koma mata kamar dodo ba, cikin ranta take fad'in " Anya lafiyar Ajlaal lau kuwa? "Kodai shaye-shaye ya fara yi bayan rabuwarsu, kanta ta girgiza a zahiri cikin ranta tace " kai wannan canja salon da yake yi cikin 'yan sakanni yafi k'arfin shaye-shaye sai dai idan cult ya fara dan taji ance 'yan cult ne suke iya canja yanayinsu in seconds. Jikinshi ya cusa cikin jikinta had'i da lumshe idanunshi yana gogo fuskarshi a saman tata fuskar a hankali ya zame hijabin jikinta yayi jifa dashi gefe, ya zame d'an kwallin kanta ya fad'i k'asa ya sanya hannu ya baza kwantaccen gashin kanta ya zuba gadon bayanta yakai hancinshi ya shak'i k'amshin gashin kanta dana wuyanta da k'arfi ya lumshe idanunshi. A hankali yakai hannu ya shafo cikinta jin cikin jikinta ya sashi jan tsoki had'i dayin kwafa yace " ta kanka zan fara you are my first target zatayi magana ya had'e bakinsu ya soma rikita mata lissafi da zallar soyayyarshi cikin salo yake tsotsar lips d'inta da harshenta, sosai Deeyanah ta soma kokawa da kiciniyar kwacewa tare da sakin kukan mutuwa. Shi ko Ajlaal ya dage sai tsotsar bakinta yana tura harshenshi cikin bakinta, bai wani damu da kukan da takeyi ba, a haukace ta sanya hannunta tana dukan k'irjinshi da iya k'arfinta, hannayenta da take dukanshi dasu ya rik'e gam had'i da d'agowa ya sakar mata shu'umin murmushi. " Dan Allah please Ajlaal please karkayi min haka, kaji tsoron Allah karka keta min haddi Ina da igiyoyin auren wani a kaina, ta fad'a cikin kuka muryarta na shak'ewa. Bakinshi ya sake mayarwa cikin nata tare da surarta cak wutsil-wutsil ta soma yi zata kwace amma Ina wane ita, saman sofa 3 sitter ya direta ya bita ya danne cikin salo ya cire mata gaba d'aya kayan jikinta silky naked body d'inta ya bayya hannayenta ta sanya ta kare jikinta while tana cigaba da kukan had'i da rok'onshi. K'ok'arin tashi daga kan kujerar ta soma yi amma wane ita maza bisa kanta Ajlaal dake cin k'arfe, gaba d'aya nauyinshi ya sakar mata ya danne ta, ya soma rikita mata jikinta, babu inda baya shafawa a jikinta, musamman hips da breast d'inta, jikinshi ya d'auki wata irin muguwar rawa da kerrrma ya rikice ya fita daga hayyacinshi a haukace ya rink'a romancing d'inta, duk ihuu da rok'on da Deeyanah keyi mishi akan ya kyaleta bai sarara mata ba sai da hak'onshi ya cimma ruwa. Sakwaf jikinshi ya saki ya zube kanta yana mayar da numfashi deep down kuma yana jin wata irin nutsuwa na lullub'eshi, murginashi tayi k'asa ya zube kan Turkish Carpet dake malale a tsakiyar falon, tayi saurin mik'ewa jikinta na rawa ta mayar da kayan jikinta saboda rud'ewa ma nan tabar hand bag d'inta da mukullin motar zube a k'asa tana gaf da ficewa daga falon ta jiyo muryarshi na cewa " dad'in ne ya saki manta jakarki da mukullin motar? " Da alama nafi Deen iya hak'on rijiya. Yayi maganar cike da shak'iyanci, dawowa tayi ta d'auka, tana k'ok'arin sake ficewa tajiyo shi yana fad'in " na baki nan da 24hrs kuje kiyi tunani ki zab'i d'aya cikin zab'in dana baki in ba haka ba, ya cije lips d'inshi na k'asa had'i da lumshe idonshi. Bata tsaya bashi amsa ba ta fice saboda tsabar yadda jikinta ke rawa saura kad'an ta kifa a steps d'in bene, da d'an gudu ta fice daga gidan tana shiga motar ta kifa kanta kan sitiyarin motar ta saki kuka me k'una, ta dad'e tana kukan, taji shigowar text cikin wayarta tasan shine, kamar bazata duba ba sai kuma ta d'ago kanta had'i da goge hawayenta ta bud'a text d'in. "Idan kin gama zaman kukan ki dawo ki k'ara bani mara ban k'oshi ba! a fili taja tsaki kafin tayiwa motar key ta fige ta tabar wajen. Bata zame ko'ina ba sai gidansu, tana yin parking ta fito ko d'an mukullin motar bata tsaya cirewa ba, tun a falo tayi cilli ta hand bag da hijabinta ta fad'a bedroom, directly ta wuce bathroom, a k'asan ban d'akin ta cire kayan jikinta ta zubar, duk da muku-mukun sanyin da ake bai hanata sakarwa kanta ruwan sanyi ba, ita bama ta jin sanyin wani irin zafi take ji a duk wata k'ofar gashi dake jikinta. Da iya k'arfinta take dirzar fatar jikinta tamkar zata b'are ta daga jikinta, sai da ta gaji dan kanta kana tayi zaman dirshen a k'asan tiles d'in ban d'akin ta saki rikitaccen kuka tana fad'in " innalillahi wa'inna ilaihir raji'un yau ni Deeyanah ke yin zina da aure na? " Na shiga uku! Na cuci kaina da rayuwata! na lalata duniyata da lahira ta, Allah na tuba ka yafe min, ta k'arashe maganar tana k'ara sautin kukanta. " Deeyanah afiyarki kuwa!? Deen ya fad'a yana daga bakin k'ofar bathroom d'in had'i da d'an kwankwasawa kad'an, firgigit tayi a razane ta mik'e tana goge hawayenta tace " lafiya lau wanka nake yi, tayi maganar tana k'ok'arin saita kanta. " kuma shine kike kuka? "Kuka kuma Abban Deedee? "Babu wani kuka wanka nake yi fa. "Ok, bari na shigo muyi tare, kafin tayi magana ya shigo, kallanta ya tsaya yi, tayi muguwar rama tayi fayau da ita, hasken ta ya k'ara fitowa, ga idonta yayi ja sosai ya kumbura da alama ta dad'e tana kukan. "Meke damun Deeyanah haka? " Me take b'oye mishi? "Kika ce ba kuka kikeyi ba? Murmushin yak'e ta k'ak'aro dole ta shinfid'awa fuskarta, tace " abu ne ya fad'a min a ido na. Kamar zayyi magana sai kuma ya fasa, kayanshi ya cire ya k'arasa inda take, yana ganin canje-canje da dama a tattare da ita, da da ne da kanta zata kamo shi in saxy way suyi wankan tare, bayyi k'orafi ba ya rungumota a fili ya sauke ajiyar zuciya ,saurin sakinta yayi yaja baya " lafiyarki kuwa!? Kallanshi tayi batare data ce mishi komai ba," ana wannan mugun sanyin kike wanka da ruwan sanyi? Sake kallanshi tayi bata ce komai ba, dawowa yayi ya kunna hitar ruwan zafi, ruwan yayi d'an zafi, salaf sukayi wankan ya tuna lokutan da idan suna wanka tare suyi ta watse-watsan ruwa suna romancing juna daga nan sai sex, is so hardly suyi wanka tare basuyi sex ba. Dole ta fito daga bathroom d'in batare da tayi wankan janaba ba (wankan tsarki) dan bazatayi a gabanshi ba, towel ya d'auko ya nufo ta dashi zai goge mata jikinta, tayi saurin barin jikin madubin ta nufi wardrobe, ta bud'a ta d'auko simple doguwar riga, ya nufo wardrobe d'in nan ma tayi saurin barin wajen, tsaye yayi rik'e da towel a hannunshi ya zuba mata ido, tasan kallanta yake yi dan haka tak'i kallanshi dan karsu had'a ido. " Deeyanah! ya kira sunanta in a deeper voice. Batare data kalleshi ba ta amsa, " na'am! "Dan girman Allah dan zatin Allah ki daure ki sanar dani abinda yake damunki please. Still bata kalleshi ba dan bata san su had'a ido tace " bakomai Yaya! "Ko ban cancanci nasan damuwarki bane!? Shiru tayi bata ce mishi komai ba, jin tayi shiru yasashi fara takowa yana nufarta, tana jin takun shi yana nufota tayi saurin juyawa zata bar wajen, yayi wuf ya rik'o ta ya d'aga ta sama ya zaunar da ita kan mirror yasa hannunshi a hab'arta ya d'ago kanta ya kira sunanta. "Deeyanah! Bata iya amsawa ba saboda yadda zuciyarta ke mugun bugu da k'arfi. " Deeyanah! d'ago ki kalli cikin kwayar idona zaki ga tsantsar soyayyar danake yi miki, wallahi duk duniya nafi kowa sanki, nafi kowa sanin ciwonki da zafinki, nafi kowa kare miki mutuncinki, martabarki da k'imarki ke wallahi nafi Ammah da Babah sanki, dan haka ki fad'a min damuwarki please. Cikin sanyin jikin daya fara zamar mata jiki cikin 'yan kwanakin nan ta d'ago aiko karaf idanuwansu suka sark'e cikin na juna, tayi saurin mayar da kanta k'asa. "Please mana ki sanar dani, nayi miki alkawarin zan yak'i komeye koda zan rasa rayuwata kinji. Cikin sanyin murya tace " bakomai! Cikin b'acin rai da tafasar da zuciyarshi keyi ya daki mirror d'in bayanta da wani irin k'arfi mirror d'in ya tarwatse, wata irin muguwar tsorata tayi saura kad'an ta fad'o daga kan mirror d'in ta sanya hannunta ta toshe kunnuwanta, ya sake nausar mirror d'in a karo na biyu. "Bakomai! Bakomai! abinda kike ta fad'a min kenan, baya ya juya mata had'i da cusa hannunshi cikin kwantacciyar suman kanshi while hannunshi na zubar da jini, ta durk'ushe a k'asa had'i sakin rikitaccen kuka, juyawa yayi ya nufota saboda tsabar tashin hankali babu inda baya rawa a jikinta, ya sanya hannunshi ya d'agota ya matseta a jikinshi gam, idanuwanshi sunyi mugun ja kamar garwashi jijiyoyin kanshi sunyi rad'o-rad'o. " Bakomai ko!? " Ke da kanki kika ce min bakomai! ni kuma nayi miki alk'awarin har a tashi duniya bazan sake tambayarki damuwarki ba, ya saketa ya nufi k'ofa ya bud'e ya fice ya bango mata k'ofar d'akin da mugun k'arfi har sai da d'akin ya girgiza, ya fice daga shi sai towel d'aure a k'ugunshi, ta durk'ushe ta cigaba da kukanta, k'arar shigowar text taji ya shigo wayarta bata kula wayar ba ta mik'e ta koma bathroom tayi wankan tsarki ta fito, ko mai bata shafa ba ta zira doguwar riga ta tada sallah, ta dad'e zaune kan sallaya tana karatun Al-Quran kafin tayi addu'a ta shafa ta mik'e, tana ninke sallaya wayarta ta soma rori, wata irin muguwar fad'uwa gabanta yayi kamar munafuka ta isa gaban wayar cikin tashin hankali ta furta " shine!. "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! ta sake furtawa cikin tsoro har wayar ta tsinke bata d'aga ba tana tsaye tana kallanta sake kiran wayar akayi a karo na biyu, cikin fargaba ta mik'a hannunta dake faman rawa ta d'auki wayar ta amsa tare da karawa a kunnenta. "K'arya yake yi Deeyanah! Wallahi nafi kowa sanki bai kai ni sanki ba, ko rabin sanda nake yi miki bayayi miki shi, munafurci ne danya lallab'aki ki sanar dashi damuwarki ne, yayi maganar cikin hargowa. "Wait tsaya Ajlaal wai ya akayi kasan duk wani motsina na gida dana waje!? "Ya akayi kasan munyi wannan maganar da Deen!? "Badai bi diddigi (tricker) ka saka min ba ko!? Cikin dariya yace " har wankan da kukayi tare dashi na sani, ai na riga na fad'a miki duk inda kika shiga a fad'in duniya saina nemo ki Deeyanah, nayi sake kin kufce min a baya amma a wannan karon in duniya zata tashi babu wanda ya isa ya rabani dake duk wanda ya shiga gaba na zan kawar dashi a hanyata. Cikin masifa tace " wai bi diddigi da d'au sauti ka saka min Ajlaal? Wata irin dariya ya saki kana yace " fiya da nan yarinya! na fad'a miki zan iya yin komai akanki kamar yadda kikaji nace komai to Ina nufin komai, zatayi magana ya tari numfashinta da fad'in " idan kika sake kika sanar da Deen gaskiyar abinda ke faruwa tsakani na dake to ki tabbatar kin yankar mishi tikitin mutuwa, bai bari tayi magana ba ya kashe wayar. Zama tayi bakin gado jiki ba kwari wani iri take ji a jikinta, tayi-tayi hawayenta su zubo amma sunk'i zubowa, cikin sanyin jiki ta kashe wayarta gaba d'aya ta jefa ta saman wardrobe ta fice daga d'akin, dayake bata iya cin komai sai ruwan tea yanzu kitchen ta shiga ta had'o ruwan black tea ta dawo Falo ta zauna tana kurb'a. Bayan Kwana Biyu...... Tun da Deeyanah ta kashe wayarta bata sake kallan inda wayar take ba balle ta kunna ta, Ajlaal ya neme ta yafi a irga amma switch off, yau ma kamar kullum yana zaune a d'aya daga cikin falokanshi na k'asa, yana sanye da riga armless da wondo 3 quarter ya kishingid'a bayanshi da jikin kujerar da yake zaune k'afuwanshi na kan glass center table wayarshi d'aya da American chips nakan center table d'in, while d'aya wayarshi na rik'e a hannunshi sai faman latsa ta yake, fuskarshi kawai zaka kalla kasan yana cikin b'acin rai, dan fuskar a had'e take murtuk ba alamar annuri. Makekiyar Tv data kusa cika bangon d'akin nata aiki amma hankalinshi baya kan tv. Wayar ya aje a gefe tare dayin murmushin gefen bakin irin na cikakkun 'yan duniya nan a fili yace " yaro bai san wuta ba sayya taka ta. "Kina wasa da wuta Deeyanah! kina tunannin duk abubuwan dana ce miki zan aiki bazan iya aikatawa bane? Yayiwa kanshi da kanshi tambayar, " sanda nake yi miki bazai hana na gigita duniyarki na kuma tarwatsa rayuwarki ba muddin naga zan rasa ki sai dai muyi biyu babu kowa ya rasa a tsakaninmu. Bai d'auki komai ba sai d'aya daga cikin mukullan motocinshi ya fita, duk da dare yayi sosai dan k'arfe 2:30am na dare hakan bai dame shi ba. Tana kwance kan bed tana bacci hancinta ya shak'o mata k'amshin dako a gigin mutuwa taji shi zata gane kona waye, saurin bud'e idonta tayi aiko idonta ya sauka cikin nashi sosai yayi gaf da ita har numfashinshi na shiga cikin hancinta. Cikin tashin hankali ta mik'e zaune shima zaunen ya tashi had'e da matsowa daf da ita ya zura hannunshi ta gefen wuyanta zuwa k'eyarta cikin gashin kanta ya matso da fuskarta dai-dai tashi ya goga hancinshi a kuncinta ya shak'i k'amshinta, hannayenta ta sanya a k'irjinshi ta hankad'ashi da k'arfi ta juya ta mik'e tsaye, wani irin kallo yayi mata tun daga sama har k'asa bakinshi bud'e yace. "Wow! Wato irin wannan sexy night gown d'in ake saka mishi kenan? "Amma idan za'a d'an b'alla min sai nayi ta fama, to wallahi gobe idan zaki zo ki taho min da wannan rigar baccin. "Hannayen ta had'e tana jin wani malolo daya tokare mata mak'oshi, " dan Allah ka fita Deen yana toilet karya fito ya ganka. "To ya gannin mana, in ya ganni sai me? Muryarta na sark'ewa tace " ka fita please idan ya ganka anan komai yana iya faruwa!? Komawa yayi ya zauna saman gadon had'i da tankware k'afarshi yace " ai nafi san koman ya faru. Jin motsin Deen cikin toilet d'in ya sata saurin kallan k'ofar toilet, ganin kamar ana tab'a k'ofar ai bata san sanda ta rik'o Ajlaal ba, yayi wani layi irin na 'yan duniya yana dariya yace " calm down Beb! " Zuwa nayi naji dalilin daya saki rufe wayarki tun bayan kwana biyu. Tana turashi zuwa k'ofa tace " kaje zan kunna yanzu, bud'e k'ofar Deen yayi dai-dai da d'auke wuta, kissaing Deeyanah Ajlaal yayi a kumatu kana ya rad'a mata " ki tabbatar kin kunna wayar nan yanzu in ba haka ba na dawo, bata bashi amsa ba ta hankad'a shi waje, ido ta lumshe tare da sauke ajiyar zuciya a fili. " D'auke wuta yau kuma a Estate d'in nan!? A dururuce tace " gaskiya da mamaki kam! Zai sake yin magana wutar ta dawo, kallo d'aya yayi mata ya gane a dabarbarce take ga gumi dake ta faman tsatstsafo mata!. Bayyi mata magana ba ya nufi bed d'an tsayawa yayi ya shak'i iska kafin yace “ new scent wannan saban k'amshin fa daga ina kuma? Yadda kasan saukar aradu haka k'irjinta ya buga da mugun k'arfin cikin kame-kame tace " na'am magana kake!? "Naji wani saban k'amshi ne, kamar kwanaki ma na tab'a jin irinshi a d'akin nan. Saboda tsabar rud'ewa ji tayi k'afafunta na neman kasa d'aukarta. "Eye! tace a figice, kallan yadda duk ta rud'e yayi kamar zayyi magana sayya fasa, ya kwanta saman bed ya barta nan tsaye k'afuwanta na kerrrma, cikin sanyi taja jikinta zuwa bed d'inta harta kwanta ta tuna da batun kunna waya, tayi saurin mik'ewa taje ta d'auko wayar ta kunna, tana kunna wayar sak'onshi ya shigo. " Harya fahimci saban k'amshi a d'akin kenan? ai da kin gaya mishi nina kawo miki ziyara. Ita yanzu al'amarin Ajlaal ya daina bata mamaki tsoro yake bata ace mutum kamar Aljani yasan duk wani motsinsu, a b'angaren Deen ma ba bacci yake yi ba yana jinta tana ta juye-juye har asuba, sai bayan sunyi sallar asuba bacci ya d'auketa. K'arfe goma sha d'aya na safe k'arar wayarta ya farkar da ita daga baccin da wani irin mugun tsoro, yanzu sosai take tsoron sautin wayarta duk wani ringing ko k'arar shigowar sak'o sai ta tsorata gabanta ya fad'i, duk tabi ta zabure ta koma firgitacciya gaba d'aya bata cikin nutsuwarta, jikinta na rawa ta amsa wayar ta kara a kunnenta danta riga ma tasan sauran zancen. "Ki tashi haka k'arfe sha d'aya fa. Shiru tayi batace komai ba, ya d'ora da " kizo yanzu ina jiranki, yauwa karki manta ki taho da rigar baccin nan karki manta. "Dan girman Allah Ajlaal kayi hak'uri ka barni na... bai bari ta k'arasa ba ya kashe wayarshi, yana dropping wayar ya tura mata text da. "Wallahi idan baki zo tamm! Ina da videon nan. Dole ta tashi ta shirya ta fita, yau kam ta k'uduri niyyar zasuyi uwar watsi sai dai duk abinda zai faru ya faru, kanta tsaye ta shiga gidan, saboda tsabar bala'in dayake cinta bibbiyu take taka step d'in benen. Kwance ta sameshi d'ai-d'ai saman bed daga shi sai pant yana bin wak'ar Ali Jita dake tashi a d'akin. Cikin masifa da tsiwa tace " wai kai wanne irin kare ne? "Fasik'i! wanda baya tsoran Allah, Ajlaal kasan bala'in dake cikin zina kuwa!? " Balle zina da matar aure, kasan cikin masifar daka jefa mu kuwa!? "To bari kaji idan baka sani ba yau idan muka mutu wuta zamu shiga, babu abinda zai hana mu shiga wuta sai mutuwa. Cikin isa ya mik'e ya isa gareta yace " ke kika San muyi zinar Deeyanah, ke da kanki kika zab'a mana zina, na baki zab'i amma kink'i d'aukar ko d'aya. "Na gaji Ajlaal! Idan san da kake ikirarin kana yi min gaskiya ne meyasa bazaka barni na huta ba? " Idan soyayyarka gaskiya ce a gare ni meyasa bazaka yi sadaukarwa ba!? "Meyasa bazaka barni na rayu cikin nutsuwa da kwanciyar hankali ba? "Sadaukarwa fa!? "Wacce irin sadaukarwa!? "Kina nufin irin wacce nayi a baya na barwa Deen ke!? "No! No! bazan iya ba, nima Ina buk'atarki a kusa dani yanzu. So take tayi kuka kota samu sassauci da k'unar da zuciyarta keyi, amma ina hawayenta sun dad'e da k'afewa, ji take yi kamar ba ita ba, " na tsane ka da duka zuciyata Ajlaal, wallahi na tsane ka fiye da kowa da komai a duniya, bank'i ace min kayi mushe yanzu ba, bana san ganinka mugu azzulumi bak'in kumurci, yadda kayi Allah yayi maka, in banda nasan hukuncin wanda ya kashe wani wallahi dani zanyi ajalinka na ragewa duniya mugun iri. Ya tsuntsure da dariya yayi me isarshi kana yace " zaki so ni nan gaba kad'an dana rikitaki da soyayyata zaki manta da kowa, nasan zaki kashe ni amma da soyayyarki, ya k'arashe maganar had'i da kashe mata ido d'aya, ji take yi tamkar zuciyarta zata tsaga k'irjinta ta fito, wani irin yaji-yaji take ji a duk wata k'ofar gashi dake jikinta, lokaci d'aya duk ilahirin jikinta ya d'auki mugun k'aik'ayi, bata sanda ta kifa mishi gigitaccen mari ba, ta rik'e kwalar rigarshi had'i ta tofa mishi yawu a fuska, ta kalli cikin kwayar idonshi tace " na tsane ka! Ajlaal, banza wanda bai san darajar kanshi ba, sakarai, wawa mahaukaci marar tarbiyya, iyayenka sunyi asara da suka kasa baka tarbiyya, kodan naji ance ubanka lusari ne uwarka ta gama dashi ita ke juya gidan kaga kuwa d'an mace bazayyi tarbiyya ba. Sosai Ajlaal yaji zafi da k'unar maganganun ta har cikin ranshi, saboda tsabar tafasar da zuciyarshi keyi jikinshi har rawa yake yi, amma dayake shegen duniya ne sayya saki murmushi had'i da saka yatsa ya kwashe yawun data tofa mishi yasa harshe ya lashe yadda yake wasa da harshenshi akan yatsan ko k'aramin yaro yasa da akwai abinda yake nufi. “Ki aure ni kinga kema sai ki mayar dani lusari. Kanta ta kawar gefe had'i da cewa " turrr, zatayi magana ya damk'o gashin kanta da k'arfi ya cilla ta kan gado ya bita ya danne, cike da mugunta yasa k'arfi ya durza mata boobs d'inta, yadda yake sucking bakinta ya tabbatar mata da b'acin ranshi, Deeyanah ta azubtu sosai a hannunshi in banda bata da hawayen kuka yau kam datayi kuka harta gaji, duk da haka sai da tayi kukan zuci, in banda zuk'i da rad'ad'i babu abinda k'asanta da boobs da bakinta keyi mata, jikinta kam yadda kasan ana kakkarya mata gab'ob'in jikinta. Dakyar ta mik'e ta mayar da kayan jikinta tana shirin fita yace " ince dai babu inda zaki biya ko? "Dan nayi amfani da abortion cream a jikin penis d'ina a koyaushe wannan abun na jikinki yana iya fita dan bazan iya jurewa sex dake da cikin wani a jikinki ba, bata kula maganarshi ba dan bata yarda ba, tasa kai zata fice ta dawo tace " alfarma d'aya nake nema a wajenka please. Da Ido yayi mata alamar ta fad'a yana jinta, " dan Allah ka daina zuwa gidanmu ko kira na a waya direct, ka rink'a yi min message kawai zan duba. "Ok as you say, but idan baki san na rink'a zuwa gidanku karki k'ara kashe wayarki, cikin sanyin jiki ta d'aga mishi kanta alamar to, " kira kuma ya danganta, " dan Allah karka k'ara kira text me kawai please. "Ok amma idan nayi miki text ki rink'a saurin responding in ba haka ba zan kira gaskiya. " In sha Allah zanyi responding. "Better!, yace a tak'aice, sosai canjin daya gani daga gareta ya bashi mamaki, har zata fita yace " Deeyanah ki kula idan kika ce zakiyi wasa dani wallahi sai na k'arar da gaba d'aya zuri'arku kaf, batayi magana ba tasa kai ta fice. Tun a hanya ta soma jin mararta na kartawa sama-sama amma bata wani damu ba, koda ta isa gida bathroom ta fad'a tayi wanka ta fito, sallah tayi niyyar tayarwa mararta tayi wani irin mugun kartawa, anan ta durk'ushe tana mayar da numfashi, cikin k'ank'anin lokaci ta fita daga hayyacinta dishi-dishi taga Deen ya shigo daga nan bata sake sanin inda kanta yake ba. Bata farka ba sai wajen k'arfe biyu na dare sosai kanta yayi mata mugun nauyi, a wahalce ta yunk'ura zata tashi zaune, saurin tallafe ta Ammi tayi tana fad'in "sannu Deeyanah, dakyar ta iya d'aga idonta da yayi mata nauyi ta kalli Ammi, da taimakon Ammi ta tashi zaune, sai a lokacin ta fahimci a asibiti take, shiru tayi tana k'ok'arin tuna abinda ya faru, tasan dai mararta ta rik'e. "Ince dai babu inda zaki biya ko? "Dan nayi amfani da abortion cream a jikin penis d'ina a koyaushe wannan abun na jikinki yana iya fita dan bazan iya jurewa sex dake da cikin wani a jikinki ba. Maganganun Ajlaal suka dawo mata saurin shafa cikinta tayi taji wayau babu alamun komai, kanta ne ya kulle ta kasa fahimtar komai dan haka ta bud'e baki dakyar tace " Ammi meya kawo ni asibiti? Ammi tsaye gaban fridge tana had'a mata tea ta juyo ta nufo ta d'auke da kofin tea a hannunta ta mik'a mata tana fad'in " b'ari kikayi mun rasa babyn cikinki. Ido ta runtse da k’arfi hawaye na gangarowa saman kuncinta, koda yace mata ya shafa abortion cream bata yarda ba, “dama rashin imanin “ Ajlaal har ya kai haka? "Dama da gaske zai iya aikata duk abinda yake fad'ar zai aikata? Bata tab'a yarda zai iya aikata abubuwan rashin imanin dayake fad'ar zai aikata ba, wani irin mugun tsoronshi taji ya shigeta lokaci d'aya, yadda kasan wacce ake kad'awa gangi haka jikinta ya d'auki rawa da kerrrrma kaf! Kaf! Kaf! Kamar me farfad'iya. Kenan dayake cewa zai kashe iyayenta da Deen dama gaba d'aya zuri'arsu da gaske yake!? A fili ta furta "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un na shiga uku. "Kai Deeyanah sai kace ba musulma ba miye dan kin rasa d'an da baki haifa ba kike kin shiga uku!? "Da kin san zaki samu Allah ya baki? Bama tasan abinda Ammi ke fad'a ba tadai ga Ammi tsaye kanta bakinta na motsi, amma duk fad'an da takeyi babu abinda ta iya fahimta. Tana cikin wannan halin wayarta tayi vibrating alamar shigowar text dan tuni ta mayar da wayarta vibrate ko kiranta akayi sai dai tayi Vibrating kawai, hannunta na rawa saboda saban tsoranshi d'aya shigeta ta d'auki wayar ta duba sak'on. "Congratulations to me! For winning karki damu kinji Baby dakin warke zan bani wani cikin I love you my life. Wata irin juyawa taji kanta yanayi ta zame ta kwanta, ita tama rasa tunanin da zatayi ta rasa mafita, to kodai ta kashe auren Deen inyaso taje ta auri Ajlaal d’in? Sai dai kuma tasan muddin tayi haka ba ita ba iyayenta har a tashi duniya, haka idan iyayenta suka k'i amincewa aurenta da Ajlaal tasan zai iya kashe su, to idan kuma bata aure shi ba haka zata k'arar da rayuwarta cikin tsoro da fargaba suna aikata zinace-zinace? Idan ta bijire tak'i aurenshi kota k'i bashi kanta tasan videon nan zai saki, mutuncin iyayenta, mutuncin gidansu, sunanta dana ahalinta zai b'aci har abada, haka zalika idan tace zata fad'awa ahalinta halin da ake ciki yayi rantsuwa sayya saki videon kuma ya k'arar da gaba d'aya zuri'arsu, wannan shi ake kira gaba kura baya zaki, ganin ta kasa cimma matsaya ga kanta na barazanar tarwatsewa yasata komawa ta kwanta lamo. Kwananta biyu a asibiti aka sallamota bayan tasha gwagwarmaya da Ajlaal kan sayya zo dubata sai da tayi alk'awarin ana sallamota zata zo kana ya hak'ura ya fasa zuwa. Kwana d'aya da sallamota suna zaune akan dining a part d’in Ammuh, Ammi da Ammu na zaune da Deedee sai Deeyanah da Deen kowa yana cin abinci ana hira amma banda Deeyanah datayi shiru tana tunani da kofin shayi a gabanta. " Deeyanah! Ammu ta kira sunanta a hankali, cikin sanyi ta d'ago kanta ta kalle ta, Ammu ta zuba mata ido na tsayin lokaci hakan yasa Deeyanah sunkuyar da kanta. "Lafiyarki kuwa Deeyanah, duba kiga yadda kika koma fa, kin rame, kin bushe kin k'ek'ashe duk wannan gayun da kwalliyar nan taki duk babu, duk kin sukurkurce kin lalace meke damunki ne!? Ido Deen ya zubawa Deeyanah yana jiran yaji amsar da zata bayar duk da yasan bazai wuce tace musu bakomai ba, amma watak'ila su tad'an basu wata kafa da zasu iya fahimtar abinda ke damunta. Cikin sanyin murya tace " bakomai!, tsaki yayi had'i da mik'ewa yabar wajen, duk suka bi bayanshi da kallo, Ammi tayi k'asa da murya tace " ko keda shi ne? Saurin girgiza kanta tayi tace " A'a Ammi, sosai suka sakata gaba da tambayar abinda ke damunta amma amsarta d'aya bakomai, dole tasa su hak'ura, had'i dayi mata nasihar koma meke damunta tayi addu'a. Deen na fita ta zargawa karenta igiya sai gidan Ajlaal dan yayi mata rantsuwar muddin bata zo ba shi zai zo kuma ba ruwanshi da wai yanzu rana ne ido na ganin ido. Tun daga wajen gidan ta rink'a ganin romantic decoration kanta bai gama kumcewa saida ta shiga cikin gidan anyiwa ko'ina decorating kamar na auren India, an zuzzuba flowers a ko'ina da saxy candle an kukkuna k'amshi na tashi yadda kasan an wanke gidan da turare, gidan ba haske sosai sai dumb light sosai decor d'in yayi mata kyau ya birgeta amma dayake ba cikin kwanciyar hankali take ba abun ma haushi ya bata. "Welcome home my love! Ya fad'a cikin taushin murya had'i da rungumo ta ta baya, cikin dabara da d'an tsoro ta zame jikinta daga cikin nashi ta d'an ja baya a d'arare, tana murmushin yak'e, fuskarshi d'auke da murmushi kamar kullum ya mik'o mata jar night gown me siririn hannu yace " saka min wannan yau love kawai zamu sha not sex, jikinta ba kwari ta amshi rigar ta shiga d'aya daga cikin bedrooms d'in gidan ta saka, rigar iya cinya ta tsaya mata, dakyar ta iya fitowa daga d'akin tana sand'a kamar b'arauniya. Hannuwanshi ya tafa tare da cewa " wow! So masha Allah! Ke kinganki kuwa!? " Tab! ai bazanyi sake a kwace min ke ba, sosai yanzu Deeyanah take tsoranshi tunda ya zubar mata ciki tasan zai iya aikata duk abinda yake fad'ar zai aikata yanzu ko gardama bata iya yi mishi, hannunta ya rik'o had'i da sak'alo k'ugunta ya soma taka rawa a hankali yana janta har zuwa dining table, tulin abincin dake kan dinning d'in ta kalla taga yawancinsu duk irin abinciccikan data fi so ne, babu wani abinci da take so a duniya da babu shi akan dinning d'in. Zaunar da ita yayi akan d'aya daga cikin kujerun dinning d'in ya d'auki hular kuku ya saka a kanshi had'i da d'an rusunawa yace "me kike buk'atar ci ranki ya dad'e? Kari na farko da tun bayan sake had'uwarsu da tayi murmushi, ita kanta bata san tayi murmushin ba da alama kwace mata yayi. "Murmushi kikayi!? "Wa ni!? "A'a ko d'aya, ta k'ara tsuke fuskarta. Hannayenshi ya taga had'i dayin juyi yayi d'an siririn ihuuu yace " finally! Yau kinyi murmushi, Alhamdulillah dama na fad'a miki da sannu zaki fara sona. "Har abada bazan tab'a sanka ba Ajlaal, bayan duk wad'annan abubuwan dakayi min!? "Bayan rayuwata daka tarwatsa min zan so ka!? "Aiko da bazan tab'a yafewa zuciyata ba, kuma da harna mutu ina tsinewa kaina. "Zaki so ni Deeyanah, zaki so ni komai daren da d'ewa, lokaci kawai kike buk'ata amma idan ina jik'a miki zuciyarki da soyayyata bama kisan sanda zaki sonin ba. Zatayi magana ya d'an rusuna yace " what can I offer you? Bata bashi amsa ba illa ido data zuba mishi deep down tana k'ara jin mugun tsoronshi na ratsa ta, tuwon shinkafa da miyar wake data ji kifi , ya tsiyaya mata sob'on dayasha had'i da tacaccen ruwan fruit, a cokali ya d'ebo ya nufi bakinta dashi yana fad'in " take it my Queen, ba musu ta bud'e bakin ya bata, da kanshi ya rink'a bata harta k'oshi. "Yaushe rabanki da cin abincin kullum sai dai black tea kamar buzuwa!? "Wai ya akayi yake sanin komai game da ni wanda ko Deen bai sani ba? Ta fad'a cikin ranta ba tare datasan maganar ta fito fili ba. "Saboda na fishi sanki, na fishi sanin zafi da ciwonki shiyasa nake sane da duk wani motsinki? Yayi maganar cikin salo da kwantar da kai. Ido ta d'an zuba mishi tana karantar yanayinshi kafin tace " ya akayi ranar nan ya samu controlling wutar estate d'in mu gaba d'aya? Batare daya kalle ta ba yace " ba iya controlling light d'inku kad'ai ke hannu ba, komai da komai naku yana hannu na Ina daga nan wallahi Allah zan iya kashe kowa dake cikin estate d'inku. Yadda yayi maganar ya tabbatar mata da gaske yake dan ko bai fad'a ba tasan hakan saboda duk wani motsinta na gidan a tafin hannunshi yake. Sosai taji mugun tsoronshi ya sake shigar ta fiye da koyaushe. "Daga yau idan muna sex I want to you to perform, kiyi min duk abinda zanji dad'i, ya k'arashe maganar yana kallan kwayar idonta, tayi saurin d'aga mishi kanta alamar "to!, "good girl, yace yana shafa kanta. In bridal way ya d'auke cak sai kan sofa 3 sitter ya kwantar da ita plate cikin salo ya cire mata kayan jikinta tsaf ya rage daga ita sai pant da bra. "Kace fa yau ba sex!, ta fad'a jikinta na mugun rawa. Yatsanshi ya d'ora saman lips d'inshi gami da cewa " shhhhhhh relax an watch! Red rose (jar fulawa) ya d'auko ya tsumata cikin ruwan zuma kana ya soma shafe  jikinta da ita cikin salo, sai da ya gama shafe ko'ina na jikinta da ruwan zumar kana ya mik'e ya cire rigarshi ya rige daga shi sai wondo 3 Quater, ya raba k'afuwanta ya shiga tsakiya, yasa harshenshi yana lashe zumar dake jikinta, a fili ta sauke ajiyar zuciya me k'arfi had'i da lumshe idonta. Wani irin salo yakewa Deeyanah wanda bata tab'a sanin da akwai irinshi a fad'in duniya ba, ba Deeyanah ba duk macen da ake yiwa irin wannan rikitaccen salo dole ta d'imauci, bata san sanda ta soma gantsarewa tana sake tura mishi jikinta ba, ta cusa hannunta cikin sumar gashin kanshi tana wasa da sumar had'i da sake danna kanshi, da kanta ta kamo hannunshi ta d'ora saman boobs d'inta. D'agowa yayi had'i dayi mata shu'umin kallo fuskarshi d'auke da yaudararren murmushi cikin ranshi ya furta " ta samu. Cigaba yayi da rud'a mata jiki yana sandarar mata da jijiyoyi had'i da duk wata magudanar jini dake jikinta, ya tsutse mata ruwanta, bai gama goge mata haddarta tas ba sai taji bakinshi k'asanta yana zira harshenshi cikin HQ d'inta, wani irin siririn ihuu ta sake tana fad'in " suck me! Oya continue please, don't stop tana maganar tana jan sautin ashhhhh!. Da kanta ta kamo joy stick d'inshi tana massaging nata, ai take shima ya ida rikicewa ya d'imauce ya fice fit daga hayyacinshi, duk abinda kasan d'a namiji zayyiwa mace danta ji dad'i ya kuma gamsar da ita Ajlaal yayiwa Deeyanah, dan saida ya mantar da ita kowa da komai a duniya, saida ta manta da ita kanta wacece ita, basu sararawa juna ba sai suka samu nutsuwa dukkansu, ranar kam Deeyanah ta kwashi dad'i dan tunda take a duniya bata tab'a jin dad'i da gamsuwar sex ba irin yau, idan tace bata ji dad'in abinda Ajlaal yayi mata ba k'arya take. Koda suka dawo cikin hayyacinsu bata wani damu da abinda ya faru tsakaninsu ba, ta daiji 'yar kunya kad'an, dan suna gamawa ta juya mishi baya, a hankali ya rungumota ta bayan had'i da d'ora hab'arshi kan kafad'arta yana goga sajenshi a kumatunta, cikin kasalalliyar murya yace " thank you for making my day shining my Queen!, yayi maganar yana d'an danna joy stick d'inshi a saman mazaunanta tare da d'an mammatsa mata jikinta, a fili ta sauke ajiyar zuciya batare datace komai ba. "Zanyi wanka!. Ta furta a wahalce tana danne abinda ke taso mata, ta kasawa ranta daga yau  duk sanda sukayi sex da Ajlaal a gidanshi zata rink'a yin wanka ta gaji da d’aukar k'azantar janabar zina takai gidan aurenta, gidan da iyayanta suka gina da gumin halak d'insu, idan tayi haka bata yi musu adalci ba. "Your wish is my command my Queen, yayi maganar yana d'an risinar da kanshi k'asa, yana daga kan gadon ya d'auko remote ya danta, take labulayen wajen suka yaye transferent bathroom ya bayyana da kanshi ya d'auke ta cak sai cikin kwamin wankan dake aje me kama da kwai a tsakiyar bathroom d'in, yana niyyar sunkuyowa ya soma watsa mata ruwa tayi saurin cewa " ka barshi zanyi da kaina. Murmushi ya sakar mata had'i da kissing goshinta kana ya mik'e ya fita, cikin nutsuwa tayi wankanta tsaf ta fito sanye da rigar wankan daya aje mata, bata tsaya b'ata lokaci ba ta sanya kayanta ta fice, sai da ya rakata har jikin motarta. Koda ta koma gida yau ba kamar kullum  da take rufe kanta cikin d'aki taita kuka ba, ko taita k'unci ba, yau da d'an sauk'i danta saki ranta ba yabo ba fallasa, jakarta ta aje tayi sallah ta mik'e ta shiga kitchen da niyyar d'ora abinci danta manta rabanta da tayi girki, brown rice tayi niyyar yi da meat paper sauce, a d'an gaggauce ta bud'e freezer ta fiddo abubuwan da take buk'ata ta soma aikin. Awa d'aya da rabi zuwa awa biyu ta kammala komai ta jere saman dining, bedroom ta koma ta cire kayanta ta fad'a wanka, cikin 'yan mintuna ta shirya cikin atamfa riga da siket kayan sun zauna d'as a jikinta, bata cika fuskarta da kwalliya ba d'an heavy make up tayi ta fito. Da mamaki tayi saurin k'arasawa dinning d'in dan alamu sun nuna wani ya ci abinci, ga sauran rice & pepper meat sauce d'in sai drinks da aka fasa aka sha aka rage."Deen ne ko Deedee!? "No ba Deedee bane dan tsayinshi bazai kai ba, and yadda aka zuba abincin a nutse aka ci a nutse ba'a zuzzubar ba badai yaro ba sai dai babba. " Deen ne. ta fad'a cike da fargabar da bata san dalilin yinta ba, bata gama yanke hukunci ba Deen ya rigo kwallanshi tayi tsaf daga sama har k'asa kana tace " yanzu ka shigo ne!? "Eh! yace yana binta da kallan mamakin canjin daya gani tattare da ita, raban daya ganta wasai haka harya manta, sosai fargabarta ta k'aru zuciyarta ta shiga rawa, hasken da wayarta tayi ne ya bata tabbacin sak'o ya shigo da saurin ta duba sak'on " so tasty! kin manta baki bani abinci ba dana baki, kikayi girkin ma dan rowa bakiyi min tayi ba, but I feed my self, next time a baki zaki bani, truly you know how to cook, kina da komai, kin iya komai dana ke buk'ata a mace luv you. "Mu karanta tare? taji muryar Deen gaf da ita, sai da wayar ta kusa b'ucewa daga hannunta saboda tsabar tsoro da tashin hankali, " yadai!? Yace yana kallan yadda tashin hankali ya fito k'arara ya bayan a saman fuskarta, murmushin yak'e tayi tare da cewa " bakomai! Idonshi ya runtse da k'arfi, idan da abinda ya tsana a rayuwarshi bai wuce yaji kalmar bakomai ta fito daga bakin Deeyanah ba. "Wai ke baki da wata kalma ne sai bakomai? Murmushi tayi a karo na biyu tana fad'in " Abban Deedee muje kayi wanka kazo kaci abinci, yau da kaina nayi maka girki, ta k'arasa maganar tana rik'o hannunshi ba musu ya bita, har cikin bathroom takaishi ta cire mishi kaya kana ta juya zata fita yayi saurin rik'o hannunta ya fisgota ta fad'a jikinshi ya zagayo da hannunshi ta k'ugunta yace " muyi tare mana, idonshi kawai ta kalla ta hango jarabar dake cinshi, ta d'an marairaice tace " yanzu fa nayi wankan, zayyi magana tayi saurin manna mishi kiss a kumatu ta fice. Sosai al'amarin Deeyanah ke bashi mamaki da a baya ne idan zatayi wanka ta shirya sau goma a rana idan ya buk'aci hakan zatayi ba sanyi ba komai ake yi, saurin kawar da abinda yazo ranshi yayi had'i da sakarwa kanshi shower. Daga shi sai jallabiya ya fito ya isketa zaune a falo tana kallan tv, yana fitowa ta mik'e, abincin ta zuba mishi ta tura mishi gabanshi, 'yar hararar wasa ya watsa mata yace " ya zaki turo min ke fa? "Ba kaga plate ba? "Yanzu na gama cin nawa abincin. "Tab! aiko wallahi baki isa ba tare zamu ci ki bani a baki na baki a baki, batayi mishi musu ba dan bata san ya soma zargin wani abu, tana bashi yana bata har suka k'oshi, tun suna cin abincin ya soma nuna mata kwad'ayinshi akanta da tarin sha'awarta dake damunshi, ya sanya k'afarshi yana gogar tata k'afar, kasa hak'uri yayi dan haka ya mik'e ya d'auketa cak ya d'orata saman dinning table d'in ya zame d'an kwalin kanta kallan dayake yi mata kad'ai da idanuwanshi da suka gama rinewa ya isa ya tabbatar mata yau ba sauk'i. Bakinsu ya had'e ya soma bata deep Spanish kiss, duk da bata cikin yanayi na sha'awa amma sai da taji tsikar jikinta na tashi, tasan yayi kewarta sosai, kuma yayi hak'uri dan rabansu da sex an kai wajen wata biyu zuwa uku, dole badan tana so ba ta soma biye shi, haske wayarta ta somayi alamar shigowar text amma tayi biris da wayar, cikin abinda baifi mintuna biyar ba sak'onnin Ajlaal 20 sun shigo wayar, dayaga ma text bazayyi mishi ba kira ya soma yi, tana sane da abinda ke faruwa amma tayi biris dashi, kayan jikinta ya cire mata tass ko pant bai barta dashi ba, da taimakonta ya zare jallabiyar jikinshi while bakinsu na had'e, ya d'auki lokaci yana yamutsa ta kafin ya soma k'ok'arin shigarta. "No please! the door is open kowa yana iya shigowa, ba musu ya saketa ya tafi rufe k'ofar, saurin d'aukar wayar tayi, " 50 missed call? Ta fad'a tana duba text d'in farko. "Karki soma! karki fara bashi kanki Deeyanah idan ba haka ba wallahi saina kashe shi. Na biyu kuma. "Mutuwarshi kike jawo mishi, muddin kika bari ya kusance ki wallahi saina huda mishi k'irjinshi. A fili ta sauke ajiyar zuciya tana k'ok'arin bud'e sak'o na uku kiranshi ya shigo, a haukace kamar zai fasa mata dodon kunne yace " kina wasa da rayuwar Deen, wallahil azim kika bari ya kunce ki sai nayi ajalinshi, batayi magana ba ta zare wayar daga kunnenta had'i da kashe wayar gaba d'aya, yana dawo daga rufe k'ofar abubuwa suka sake d'aukar zafi, yadda jikin Deen ke rawa yasa har ya bata tausayi batayi k'ok'arin hanashi kanta ba, duk da ba wani dad'i take ji sosai ba, cikin kwanciyar hankali ya jefa kwallanshi a raga ya soma kashe arna. A haukace ya kaiwa tvn dake jikin bango raruma ya d'agata ya buga da k'asa, wani irin ihuu yake yana bin duk wani abu na glass yana bugawa da k'asa, duk yaji ciwo a jikinshi hannunshi ya farfashe jini na zuba, komawa yayi ya zauna saman sofa yana dafe da kanshi had'i da fad'in "no! no! no! Deeyanah tawa ce ni kad'ai, ke d'in tawa ce, zambur ya mik'e kamar an tsikare shi yayi waje. Anan kan dinning d'in sukayi sex, bayan sun gama ya d'auke ta cak sai bedroom har lokacin bakinshi yana cikin nata suna tsotsar harshen junansu, bathroom ya wuce d'auke da ita ya sakar musu shower, sun dad'e suna wasan ruwa kafin sukayi wankan suka fito d'aure da towel d'aya a jikinsu, bayan sun shirya ta haye gado zata kwanta, idonshi kanta yace " badai bacci ba ko? A shagwab'e tace " bacci mana wallahi na gaji. "Ke dai da raki kike, me akayi? "Abinda ba wani dad'ewa akayi ana kashe arnan ba, murmushi tayi me zurfi wanda yasa side dimples d'inta lotsawa, tace " hmmm. "Hmmmm me!? "Kiyi maganarki kai tsaye za'a baki amsa karki damu. "Babu wata magana, kissing d'inta yayi a kumatu ya mik'e zai fice, tayi saurin cewa " fita zakayi? "Abinci zanje na ci. "Abinci kuma, ta fad'a cikin mamaki. "Eh abincin mana, wanda naci duk kin zuk'eshi yanzu, ga wannan uban aiki dana sha ai dole naci abinci. Murmushi kawai tayi batare da tace mishi komai ba ya fita, ta gyara kwanciyarta had'i da jan bargo zata rafa, salatin Deen tajiyo a falo da k'arfi, wata irin razananniyar fad'uwa gabanta yayi, da tsalle ta wuntsilo daga kan gado ta diro k'asa, yadda kasan ana hankad'a ta haka take tafiya, bata san yadda akayi ba sai ganinta tayi a falon. Yana zaune ya d'ora k'afa d'aya kan d'aya hannunshi rik'e da 'yar k'aramar siririyar wuk'a da jini ya b'atata faca-face, bakinta na rawa ta furta " Aj...l....a..al!? Da farko bata lura da akan me k'afarshi take ba sai daga baya ta fahimci k'afarshi akan Deen take, "De....en, ta fad'a kamar me koyan magana. Idanuwan Deen rufe baya motsi ga jini yana zuba daga k'irjinshi saitin zuciyarshi inda aka caka mishi wuk'a. Wani irin shuuuuuu taji cikin kunnenta, take komai ya d'auke mata duniyar ta tsaya mata cak ta daina fahimtar komai, sakwaf ta zauna k'asan tile idanuwanta kan Deen dake kwance cikin jini, ji tayi bugun zuciyarta ya tsaya mata cak, wani abu taji me tsananin azaba yana bud'ewa a k'irjinta, d'is-d'is hawaye suka soma zubawa daga idonta kafin hawayenta su b'alle yadda kasan an b'alle magudanar teku. "Bai mutu ba, ban kai ga kashe shi ba tunna, wannan jan kunne ne na farko, 'yar k'aramar huda nayi mishi a zuciyarshi wanda bazai wuce inci d'aya ba, idan kikayi gaggawar kaishi asibiti nan da mintuna goma sha biyar ana iya ceton rayuwarshi. A rud'e ta zabura tayi kan Deen d'in tana k'ok'arin d'agashi. "A'a! bada sauri haka ba, kafin nan ki fara yi min alk'awarin bazaki sake bashi kanki ba, shiru tayi sai kukan da take yi tamkar ranta zai fita, "muddin kina san ya cigaba da rayuwa dole ki koyi yadda zaki nesanta kanki dashi, dole zaki rink'a yin abinda nace, kiyi min alk'awarin duk abinda nake so kuma nace kiyi shi zakiyi. Kanta ta d'ago ta kalleshi cike zallar tsana da k'iyayya tace " na tsaneka Ajlaal fiye da yadda na tsani mutuwa ta, kasa a ranka komai daren dad'ewa ni Deeyanah ce ajalinka, ina ji a jikina mutuwarka na hannuna, an zana taswirar ajalinka a tafin hannuna Ajlaal. Kafad'a ya d'age yana fad'in " you're out of time, 10 minutes remaining, wata irin muguwar rawa jikin Deen ya d'auka, k'ara ta saki tana k'ank'ame Deen d'in tace " please ka d'aga shi na kaishi asibiti dan Allah, sake take shi yayi da k'afarshi yace " damar na hannunki. Cikin kuka tace " naji na yarda na amince da dukkan sharad'inka, kamar zayyi magana sai kuma ya fasa ya d'auke k'afarshi daga kan Deen, babu yadda Deeyanah batayi ta d'aga Deen ba amma ta kasa kasancewar jikinshi ya saki, Ajlaal na zaune kame yana kallanta, da gudu ta nufi k'ofar falon amma abun mamaki ta jita a rufe, tun rufewar da Deen yayi mata da zasuyi sex, ta ina kenan Ajlaal ya shigo, bata tsaya b'atawa kanta lokacin tambayarshi ba ta fice. Da wani irin ihuuu ta fita tana fad'in " ku taimaka min dan Allah, Abbi da Babah dake tsaye bakin mota da alama d'aya ne ya rako d'aya, su ta nufa da gudu tana fad'in " Abbi Deen! Kallan juna Abbi da Babah sukayi kafin suka mayar da kallansu gare ta Babah yace " Ina Deen d'in yake meya same shi, tana haki take nuna musu part d'in su tana fad'in " Abbi Deen! Deen Abbi! abinda take iya fad'a kenan, da gudu Abbi da Babah suka nufi part d'in nasu dan sun fahimci ba lafiya, da taimakon su Abbi aka kai Deen asibiti. Tana ta sintiri k'ofar Emergency room d'in tana kaiwa da komowa duk wata dak'ik'a dake bugawa da bugun zuciyarta suke bugawa tare, an d'auki wajen awanni uku kafin Allah ya bawa likitoci ikon cito rayuwar Deen. "Alhamdulillah mun samu narasar cetoshi baya cikin had'ari kuna iya shiga ku ganshi, idanuwanta ta lumshe hawaye na zuba ta sauke ajiyar zuciya a fili. Bai farfad'o ba sai washe gari da yamma dukkansu kowa da kowa yana cikin d'akin, yana zaune saman bed while tana zaune kusa dashi tana bashi ruwan tea Abbi yace " ni fa na kasa fahimtar komai, kaina ya kulle gaba d'aya, ace duk tarin masu gadin dake gidan har wani ya samu damar shigowa ya cutar damu? Babah yace " abin dai da d'aure kai yake na duba gaba  d'aya CCTV Cameras amma babu komai, d'an shiru sukayi kafin Abbi ya kalli Deen yace " kuma bakaga wanda ya soke ka da wuk'ar ba? Cikin sanyin jiki ya girgiza kanshi kafin yace " ban gani ba, ina tafiya zuwa dinning naji an rik'e ni ta baya gam, kafin nayi wani motsi an cika min wuk'ar. "Ikon Allah! Babah ya fad'a cikin jimami kafin ya d'ora da " kuma babu wanda kake zargi!? "A'a!, yace yana girgiza kanshi, Abbi yace " Doctor yace min koma waye yana da mugun sani akan zubin halittar d'an Adam, dan yayi abun cikin kwarewa, kuma ko waye ba san kashe shi yake yi ba. "Allah dai ya kyauta. Satinsu biyu a asibitin aka sallamesu dan ya warke sarai sosai, koda suka koma gida bai kwanta ba cigaba yayi da harkokinshi, ranar da suka koma gida Ajlaal ya nemi ganin Deeyanah dole badan taso ba taje, dan yanzu tsoranshi ya gama cika mata jinin jikinta, da ace ba musulma bace ita da tuni ta kashe kanta, sai dai ta riga tasan hukuncin yin hakan a addininta, amma dai ta gwammaci mutuwarta sau dubu da wannan rayuwar tsoron da rashin kwanciyar hankalin da take yi. Bayan Wata Uku.... Sannu a hankali Deeyanah ta fara sakin jikin da Ajlaal tun bata jin dad'in sex da romance d'inshi har ta fara ji, da farko-farko bata nunawa nannok'ewa take yi tana basarwa kafin daga baya ta saki jiki suke aiwatar da masha'arsu. Tun daga falon k'asa na fara cin arba da pant & bra gami sauran kayan sawa na maza dana mata, kayan nabi da kallo ina mamaki, wani irin gurnani na soma jiyowa daga wani lungu cikin sand'a nabi inda sautin ke fitowa. Abinda na gani ba k'aramin girgiza ni  da dakar min zuciya yayi ba, Deeyanah durk'ushe saman gwiwowinta tana yiwa Ajlaal sucking, idanuwana na murza na sake kallan abinda ke faruwa, a yadda na fuskanta babu alamun tsoro ko tilastawa a tattare da ita, sai dad'in da take ji. " Kai kad'ai ke iya gamsar dani naji na gamsu, kai kad'ai ke korar k'ishir ruwa na ta d'a namiji. "Ka Iya sex Ajlaal ! ka iya sarrafa mace a shinfid'a, dama haka sex keda dad'i amma ban sani ba!? "Gaskiya na cuci kai na dana tsaya ina fulako da fari. "Thank you! Nagode sosai. Ido ya lumshe yana jin wani sanyin dad'in da kalamanta ke saukar mishi, gashin kanta ya rik'o yana sake danna kanta yace " I love you, zan iya yak'ai duniya akanki Deeyanah, akanki zan iya karb'ar mutuwa sau dubu, ya k'arashe maganar yana d'agota, da kanta ta had'e bakinsu ta soma tsotsar harshenshi had'i da tura mishi nata yana tsotsa, hannunshi ta rik'o cikin nata takaishi saman bed ta kwantar plate kana ta haye ruwan cikinshi da kanta ta saita joy stick d'inshi ta danna a k'asanta gami da soma pumping. Wasu irin kalamai Deeyanah ke fad'awa mishi da suka saka k'afafuna kasa d'auka ta, tsaf suka gama biyawa juna buk'atarsu tayi kwance saman k'irjinshi tama wasa da gashin dake kewayen nipple d'inshi. "Kin gaji ko My Angel!? "Sannu Annurin rai na, yayi maganar yana shafa mata kanta, banza tayi dashi, yakai hannu ya d'an muntsini boobs d'inta, ta buge  hannunshi tana fad'in " Allah bana so, tayi maganar cikin shagwab'a, yayi dariya sosai yace " ni kuma ina so. Mik'ewa yayi da ita a jikinshi ya shiga bathroom ya cika musu kwamin wanka da ruwa suka shiga, sai da suka b'ata lokaci sosai wajen tab'e-tab'e da latse-latsen juna gami da watse-watsen ruwa sannan yayi mata wankan tas ya sillota a towel ya fito d'auke da ita a hannunshi kamar jaririya. Har ya gama shirya ta tana zuba mishi sangarta da shagwab'a, ya saka mata takalmi suka fita, Amala delight suka nufa acan d'imma da kanshi ya bata abincin a baki, kafin suka nufi wani k'aton mall dake kan zaria road ta jibgi k'anan kayan sawa sosai da duk abinda zata buk'ata, ya biya suka dawo gida, bedroom guda ya ware mata nata na kanta a cikin gidan, tare suka shirya kayan a cikin wardrobe. " Bacci nake ji, ta fad'a cikin salon d'aukar hankali. Yayi murmushi had'i da mik'ewa ya d'auke ta sai kan bed yana fad'in " bacci kodai abun ne ke motsi yana buk'atar a d'an, ya k'arashe maganar had'i da kashe mata ido d'aya, " sai kace wata harija, yanzu fa muka gama ai sai nace ba lafiya ba. "Kinga imma shine ki fito kiyi bayani kar ki cuci kanki ni dai kin San bana gajiya namijin gaske ne. "In shi d'inne me zai hana ni fad'a!? "Kaga ni kashe min light, light d'in ya kashe ya dawo zai kwanta ta kalle shi tace " kazo ka hanani bacci ko? "Nop wane ni, baccin dai nima zanyi, " tam naji amma banda 'yan tab'e-tab'e, "okay Ma'am, yace had'i da rungumo ta jikinshi tsam kamar wani zai kwace mishi ita, suka tsunduma duniyar baccinsu cikin kwanciyar hankali. Basu tashi ba sai 5:30pm na rana a gurguje ta mik'e ta shirya ta fice ko sallah bata tsaya tayi ba, har bakin motarta ya rakata yayi mata kiss a goshi, yana tsaye harta fita, dayake get d'in me control da remote ne, da remote ya rufe, ya koma ciki. A harabar Estate ta hangoshi yana niyyar shiga mota, ganin ta shigo ya sashi d'an dakatawa ya fasa shiga motar, ya zuba mata ido yana yi maka kallan tuhuma yace " daga ina kike? Tana k'ok'arin had'a nutsuwarta tace " saloon! Ido ya tsareta dashi yana karantar yanayinta, kanta ta sunkuyar dan kallan da yake yi mata yana neman rikitata ta fad'i abinda ba shi kenan ba, kanshi ya kawar had'i da shiga motar yana maimaita a'uzubiyya cikin ranshi saboda abinda shaid'ai ke bijiro mishi dashi. D'an siririn tsaki taja tana watsawa motar dayake ciki harara ta wuce gidan, "Momy kina ina tun d'azu nake nemanki. Murmushi tayi tare da shafa kanshi tace " d'an Ammi kasuwa naje, " kacuwa! To Momy ina chocolate d'ina, hannu ta sanya cikin jakarta ta d'auko chocolate harta mik'a mishi sai wani tunani yazo ranta. "Gashi ki kaiwa Deedee!. Maganar Ajlaal ta dawo mata, tasan Ajlaal baya k'aunar ahalinta kaf musamman Deen, d'aukar Deedee tayi ta isa bakin fridge ta bud'e ta d'auko Chocolate ta bashi, ya amsa tare da cewa "thank you Mom!, ya soma k'ok'arin sakkowa ta direshi tana dariya tace " an samu abinda ake so za'a gudu wajen Ammu. Wayar hannunta ta soma haske tayi murmushi had'i dayin picking tace " Noor Hayati ya akayi!? Ajlaal yace " meyasa kika fasa bashi chocolate d'in dana siya mishi? 'Yar dariya tayi kana tace " haka nan kawai, "hmmm kedai kika sani, "bari nayi sallah zan kira ka, "ok, had'i da kashe wayar. *********************************** Silifas d'in k'afarshi ya cire ya hawo gadon, tayi lamo kamar me bacci dan yau ta kula da take-takenshi shiyasa ma ta baro shi a dinning dan bata san k'aryarda zatayi mishi yau ba, hannunshi ya mik'a ya jawota jikinshi yana fad'in " badai har kinyi bacci ba? "Au ko tashi ma zakiyi dan bazan iya hak'uri ba yau, harshenshi ya tura cikin bakinta tare da zira hannunshi cikin rigar jikinta ya soma wasa da boobs d'inta yana murza nipples d'inta, still shiru Deeyanah tayi yadda kasan bata san abinda yake yi ba, sosai ya birkice yana shafa duk inda yaci karo dashi a jikinta, a k'agauce ya cire rigar baccin jikinta da pant d'inta ya zubar a k'asa dama jikinta ba bra, wani irin nishi ya soma saki yana lasar boobs d'inta while hannunshi yana k'asanta, yayinda d'aya hannun ke aikin murza sassan jikinta, duk yadda d'a namiji yakai da buk'atuwar mace to yau Deen yakai dan rabanshi da sex kimanin watanni uku kenan. Jin yana k'ok'arin shigarta yasata saurin mik'ewa had'i da kunna fitilar d'akin. "Au wai kin tashi ai na d'auka baccin kike yi, irin wannan bacci haka? Ya fad'a da sigar tsokana, yana sake shigewa jikinta, idanuwanta ta lumshe tana tuno kashedin Ajlaal dake fad'in " muddin kika sake bashi kanki kin jawo mishi mutuwarshi. Ta tabbatar da zai iya kashe Deen tunda ya tab'a attempting hakan, tasan yanzu haka ma yana kallansu, zame jikinta tayi tana k'ok'arin saita kanta tace " Papa! bani da lafiya fa. Muryarshi can k'asan mak'ogwaro yace " I'm very sorry but yau kam bazan iya d'aga miki k'afa ba gaskiya, ya k'arasa maganar yana sake had'e bakinsu. Bakinta ta zame tana marairace fuska tace " please kayi hak'uri bazan iya ba. A matuk'ar wahalce muryarshi na sark'ewa yace " please ki barni nayi ko kad'an ne, ganin tana k'ok'arin tashi yasa Deen saka mata k'arfi ya jawota ya jefa saman gadon ya danneta da iya k'arfinshi, ya soma k'ok'arin shigarta, dan a yadda yake ji yau idan bai kusanci mace ba komai yana iya faruwa dashi, k'ara ta saki had'i da tura shi baya da iya k'arfinta ta mirgina ta sauka daga kan gadon. Bakinshi bud'e yana binta da kallan data kasa fassara shi. "Nace maka bana so ana dole ne Deen? Tar ya bud'e idonshi dake cike da sha'awa ya zuba su a kanta, a fili ya maimaita " Deen! " Deeyanah ni kike fad'awa haka!? "Ni mijinki!? "To nace maka I'm not in the mood but you still insist bana so ana dole ne? "Ana dole mana tunda ke matata ce, halila na ce, ina da hakk'i akanki. "Kai kasan wannan! ta fad'a cike da rashin kunya. Sai da ya d'anyi mata kallan 'yan dak'ik'u kana yace " idan ba manta lissafin nayi ba yau kusan wata uku da kwanaki baki bani hakk'i na ba, tunda nayi rashin lafiya, nabiki nabiki harna gaji koyaushe da uzurin da zaki kawo min, nasan wasu lokutan k'arya kike yi min ina kyale ki ne kawai saboda yau da gobe sai Allah, tunda muka dawo k'asar nan na kasa gane kanki, na kasa gane abinda kike nufi, idan da akwai wani abu a ranki ki fito kiyi min bayani. Kanta ta kawar dan bazata iya jurewa irin kallan dayake yi mata ba. Tsaye yayi da idonshi cak akanta ya kasa cewa komai tun asalinshi shi ba mutum bane me san yawan magana ba balle fad'a, ko akan meye idan yaja aka ja saki yake yi. "Nasanki ciki da bai Deeyanah nasanki tun kafin ke kanki kisan kanki, nasan halaye da d'abi'unki kaf, dan haka nake hana kaina zarginki so da dama kina yin abubuwan daban yarda dasu ba, kina yin abubuwan daya kamata na tuhume ki na bincike ki amma banayi dan bana so ko kusa na zargeki sai na sawa raina bari nayi miki uzuri, lokuta da dama shaid'an yana ainayana min abubuwa akanki amma Ina k'i dan bana san na lalata aurenmu, bana san bud'e k'ofar zargi da rashin jituwa a tsakaninmu, amma ke duk baki ga wannan ba. "Nasan yanayin sha'awarki Deeyanah, nasan yadda kike, na yarda dake d'ari bisa d'ari dan Allah kada ki bawa zuciyata damar soma rawa da zargi akanki, bazan tambaye ki dalilinki nayin hakan ba, haka bazan sake tambayarki hakk'ina ba, kamar yadda nayi alk'awarin bazan sake tambayarki damuwarki ba. Har ya juya zai kwanta ya sake kallan kwayar idonta yace " Allah ya sani ban tab'a cin amanarki ba, Allah shaida ne akan irin san da nake yi miki, ina sanki fiye da komai da kowa, zan iya yafe miki duk girman laifin da zakiyi min amma bazan tab'a yafe miki laifin cin amanata ba, babu dalilin da zai saka na k'i ki kona gujeki, amma zan tsaneki tsana ta har abada muddin kika ci amanata, zanyi nisan nisa dake, zan nisanta kaina daga gare ki, muddin kika ci min amana ta Deeyanah, Destiny can only be delayed but can not be denied. Ji tayi tamkar an d'auke ta anyi cilli da ita gefe, tamkar akan saharar k'ank'ara take tsaye haka take ji, wani irin abu take ji yana fita daga jikinta, k'arara tsoro da tashin hankali suka bayyana a tattare da ita, yawun bakinta ya bushe, jiri-jiri yana d'ibarta saboda tashin hankali da tsoro, jin tana neman zubewa k'asata yasata zamewa ta tsugunna had'i da fashewa da kuka marar sauti. Yaso ya fita yabar mata d'akin amma ya daure ya kwanta, ya tabbatarwa kanshi akwai abinda Deeyanah ke b'oye mishi, dukkanninsu babu wanda ya runtsa. (DESTINY CAN ONLY BE DELAYED BUT CAN NOT BE DENIED) Da sassafe ya shirya ya fita saboda karb'o musu renewal d'in passport sai dai shi Deedee sabo akayi mishi, tana jinshi har ya fita bata d'ago ta kalleshi ba, yana fita ta sauke ajiyar zuciya a fili ta mik'e, ta shiga toilet, cikin rashin sa'a tana d'ora k'afarta santsin tile da tsantsin ruwan wankan Deen suka d'ebeta tayi tangal-tangal zata kifa, da sauri ya d'agota ya mannata ta jikinshi ta sauke ajiyar zuciya da k'arfi tare da kwantar da kanta a k'irjinshi. "Kin gani ba, ai na fad'a miki duk sanda kika shiga matsala ni zan kawo miki d'auki, haka duk sanda kike buk'atar taimako zan bayyana a duk inda kike, Ajlaal ya fad'a yana shafa kanta. "Meyasa kazo gida? Bata bari ya bata amsa ba ta d'ora da kafa yi min alk'awarin bazaka sake zuwa gida ba,  ta fad'a tana shafa k'irjinshi. "Zuwa nayi na d'ebe miki kewa na mantar dake damuwar da yasaka ki kika kwana cikin bak'in ciki, murmushi tayi had'i da cewa " muyi wanka ko!? "Wanne wanka zamuyi babu dalili!? "Ai gwara muyi me dalilin ko? Ya k'arashe maganar had'i da kashe mata ido, hannunta ta sanya cikin sumar kanshi ta kifo da kanshi ta had'e bakinsu cikin salo ta kai hannunta kan joy stick ta soma shafa ta gami da murzatawa, while shima yana mayar mata da martani, cikin k'ak'anin lokaci suka mantar da junansu komai da kowa, basu sararawa juna ba sai da suka samu nutsuwa kana sukayi wanka suka fito. Jallabiyar Deen ta d'auko mishi ya galla mata harara yana fad'in " God forbid! na saka kayanshi, tayi dariya sosai kana ta mayar ta aje ta shirya shi ya mayar da kayan daya cire ita kuma ta sanya wasu, ta nufi k'ofa zata fita "ina kuma zaki? "Abinci zan nemo mana! "Bari na taso nazo na tayaki mu dafa, idanuwa ta zaro kamar zasu fad'o k'asa tace " rufa min asiri. Ya d'an harare yace " oh! yanzu ba, amma dayake d'ibarki za'ayi baki ce na rufa miki asiri ba, zatayi magana yace " karki damu everything is under my control so feel comfortable, tasan da gaske yake tunda har ya iya shigowa ido na ganin ido duk tarin masu gadi da ma'aikatan da suke gidan, tare sukayi girkinsu cikin soyayya, bayan sun gama suka zubo a plate d'aya tana bashi yana bata har suka k'oshi, yaso ya kwanta yayi bacci amma ta hanashi saboda tana jin tsoro dole ya hak'ura ya tafi, bayan sun gama 'yan tsotse-tsotsensu. ***************************** Tsaye take bakin mirror tana taje gashin kanta ya shigo hannunshi rik'e da takardu batare daya kalli inda take ba yace " ki shirya next week zamu wuce ana nema na a wajen aiki. A firgice ta juyo ta kalleshi had'i da cewa " tafiya!? Yana cire kayan jikinshi yace " eh! "Wai America zamu tafi!? Tsaida idonshi yayi a kanta batare dayace komai ba. Juyawa tayi ta fice da sauri had'i da d'aukar wayarta , can cikin lambun Estate d'in ta shiga hannunta na rawa tayi dialing number Ajlaal, yana d'agawa ta soma magana da fad'in " kaji wannan d'an rainin hankalin ko!? Sai da ya fitar da nannauyan numfashi a cikin kunnenta kana yace " to ke me kika yanke? "Kamar ya mena yanke? "Uhunnn fad'i mana bana san nayi magana kice na fiye san kai na ne, amma ki sani wallahi muddin kikayi kuskuran binshi kafin jirginku yakai inda zai kai kun samu labarin rugujewar ahalinku da mutuwarsu kaf dan bazan tab'a barin d'ayansu da rai a doron k'asa ba, kuma na saki video na watsa cewa sanadin video batsarki ne yayi sanadiyyar ajalinsu, suka kashe kansu saboda kunyar duniya, zab'i ya rage naki tsakanin ran ahalinki da mutuncinki da kuma k'iimar zuri'arku kaf da kuma binshi America wanne ya fiye miki mahimmanci. "Kaima kasan idan duniya zata tashi bazan bishi konan da k'ofar takashi ba, murmushin samun nasara akanta yayi kana yace " good Dear. Tun ranar dayayi mata maganar komawarsu bai sake yi mata magana ba, sai yau da yake shirin fita siyayyar tafiya, " ki shirya mu fita siyayyar tafiya, sarai ta jishi amma tayi kamar ma bata san yayi maganar ba. " Deeyanah, ya kira sunanta had'i da zuba mata ido, "unn! ta amsa batare data kalleshi ba, "nace ki shirya mu fita siyayyar tafiya ko? "Tafiya zakayi ne? Ta fad'a duk da tasan abinda yake nufi, while tana cigaba da shafa jan bakinta, cak ya tsayar da abinda yake had'i da zuba mata ido cike da mamaki, kamar bazayyi magana ba sai kuma yace " ban gane tafiya zanyi ba, dama na tab'a yin wata tafiya ne batare dake ba tunda mukayi aure? "Ops! Ashe tare zamuyi tafiyar ma! kenan? Tayi maganar tana k'ok'arin barin wajen, a zuciye ya fisgota cike da k'ufula renin wayon da take san yi mishi, ya jefa ta saman bed had'i da nuna ta da d'an yatsa yace " stop it! Ya isa haka Deeyanah bana san renin wayo. Harara ta watsa mishi tana fad'in " karya ni kake san yi? Zayyi magana tayi saurin cewa " kaga bari ma na fad'a maka gaskiya ni fa babu inda zani bazani wata America ba. Kafad'arta ya damk'a da k'arfi har saida ta runtse ido ta saki 'yar k'ara, " me kike nufi Deeyanah? "Abin da kaji wallahi bazan bika ko'ina ba, ta fad'a cike da tsiwa, k'ara damk'e k'afad'ar tata yayi da k'arfi ya d'an risino dai-dai fuskarta ya kalli cikin kwayar idonta yace " wallahi baki isa ba, muddin kina matsayin matata kina k'ark'ashin iko na baki isa nace ga abinda nake san kiyi ki k'i yi ba. Sai da ta d'an turo baki kana tace " to sai ka janye auren naka, ka warware k'ullin dayayi mana zabari a tsakaninmu. Sakinta yayi had'i da d'agowa cike da mamakinta dan ya tabbatar da abinda ta fad'a yace " me!? "Me kika fad'a yanzu? "Maimaita abinda kika fad'a. Baki ta d'an sake turowa batare data ce mishi komai ba. "Ok, yayi kyau amma ki sani sai dai ki zab'a zama anan ko kuma aurena dan muddin kina matsayin matata bazan barki anan ba, bai jira tayi magana ba ya juya ya fice dan zuciyarshi na gaf da tarwatsewa. Baki ta murgud'a mishi had'i da cewa mugu kawai. Sosai al'amarin Deeyanah ya soma bashi tsoro dan abubuwan nata sun wuce su bashi mamaki, kanshi ya kulle ya rasa tunanin da zayyi, ya rasa wazai fad'awa maganar koya samu sauk'in rad'ad'in da zuciyarshi keyi mishi," anya kanta d'aya kuwa!? "Kodai Aljanu ne suka shige ta? Ya fad'a yana gyara kwanciyarshi, har asuba ya rasa abinda yake yi mishi dad'i ya rasa tunanin abinda zayyi. Ita kam tana d'akinta dan yau bataje bedroom d'inshi ba, da kanta ta kira Ajlaal yazo suka kwana tare suna murzar juna, shi kanshi har mamakinta yake yi, yasha zargin kodai wani abu take shirya mishi dan wasu lokutan tana zo mai da iskancin daya girmi nashi, idan suna sex tasha yi mishi abinda sai kwakwalwarshi ta tsaya cak, sosai take zagewa susha madarar iskancinsu, tasha tsotsewa Ajlaal ruwan kai a bed. Haka suna kwana suna ligwi-gwita junansu sai da ta had'a mishi breakfast ta bashi a baki kana ya tafi. Tana kwance gashin kanta duk ya yamutse ya shigo kallo d'aya yayi mata ya gabanshi yayi mummunar fad'uwa, ya santa farin sani, matarshi ce ita d'in, ya san yadda take komawa idan sukayi sex, saurin d'auke kanshi yayi daga dubanta yana a'uzubiyya a cikin ranshi, d'an sake kallanta yayi  kafin ya mayar da kallanshi d'akin da saman bed d'in komai ba'a dai-dai yake ba, ji yayi gabanshi ya sake muguwar fad'uwa, ya sake saurin kawar da idonshi daga kanta yace " wanne hukunci kika yanke? Sai da ta d'auki lokaci kamar bazata bashi amsa ba kana tace " na zab'i zama anan!. "Kin san me hakan ke nufi kuwa? Ya fad'a yana tsare ta da idanuwanshi, cikin k'osawa tace " na sani mana, ba cewa kayi na zab'a tsakanin aure da zama anan ba!? Sai da mamakinta ya kusa sawa zuciyarshi ta tsaya a hasale ya damk'ota yana fad'in " me kike nufi!? "Kaga bafa a dole a auratayya. Hannu ya d'aga zai kifa mata mari sai kuma ya fasa, cilli yayi da ita ya fice, tunda abubuwan suka fara faruwa bai tab'a fad'awa kowa ba, amma yau kam dole iyaye su shiga dan a yadda yake jin zuciyarshi yana iya yanke hukuncin da bazai yiwa kowa dad'in ba, Babah ya samu a falon k'asa ya durk'usa gabanshi batare dayace komai ba, idonshi kad'ai Babah yana kallanshi yasan ba lafiya ba, yasan halin Deen da bak'ar zuciya, bayyi mishi magana ba ya mik'e ya isa fridge ya d'auko mishi ruwan sanyi a roba ya mik'a mishi, duk ilahirin jikinshi na rawa ya amsa da sauri kamar dama jira yake, tunda ya kafa robar a bakinshi bai cire ba sai da shanye ruwan tass, " in k'aro maka wani ne!? Kai ya girgizawa Babah batare da yayi magana ba, yasan halin kayanshi dan haka ya koma ya zauna ya cigaba da kallan labaranshi yasan idan zuciyar ta lafa da kanshi zayyi mishi bayanin komai, ba'afi mintuna biyar fa ya d'ago yace " Babah!. Babah yayi murmushi tare da juyowa dan yasan ya sakko yanzu zasuyi magana, " Babah ina san Deeyanah amma tana neman kashe ni. "Subhanallahi ita Deeyanan ke neman kashe ka!? "Meya faru? Sai da ya sauke ajiyar zuciya kana ya fad'awa Babah duk yadda sukayi tun daga ranar daya soma yi mata maganar tafiyarsu har yadda sukayi yau, bai fad'awa Babah maganar zamantakewarsu ba, da yadda ta hanashi kanta har yau, wannan ya barwa cikinshi. "Kamar ya bazata bika ba? "Ban fahimta ba fa Deen. "To nima dai ban fahimta, shiyasa nace bari na fad'a maka kokai zaka fahimta, ran Babah in yayi dubu yayi mugun b'aci a hasale ya ciro wayarshi a aljihu ya kirata, tana ganin kiran Babah tak'i tad'awa danta san can Deen yakaita k'ara kuma bayanshi Babah zai bi, kiran na tsinkewa tayi saurin kiran Abbi. Wayar Babah yabi da kallo kana ya kalli Deen suka had'a ido, sake kiran wayar yayi yaji busy sau uku yana kiran wayar amma busy hakan ba k'aramin hasala ran Babah yayi ba, wayar Ammu ya kira tana d'agawa yace " jeki taho min da Deeyanah, bai jira jin abinda zatace ba ya kashe wayar. Abbi na d'agawa ta fasa kukan kissa wiwi, " subhanallah lafiya Deeyanah? Cikin kuka da marairaicewa tace " Abbi Deen ne ya kai k'arata gun Babah kan nace bazan bishi America ba saboda tarbiyyar Deedee, " to! ikon Allah, yanzu Ina Babah da Deen d'in? "Suna falon Babah, " ki taho falon nima bari naje can na same su, cikin zumud'i ta amsa da "to dan tasan duk wacce za'ayi Abbi bazai tab'a bari ayi mata dole ba, tana kashe wayar Abbi ta kira wayar Babah, amma harta tsinke bai d'aga ba, zata sake kiranshi Ammu ta shigo, a d'an tsorace ta mik'e tana gaida Ammu kafin tayi shiru tana jiran taji abinda zatace mata dan tasan ta ba wasa, " wani laifin kika yiwa Babanki ne!? Da saurinta ta girgiza kanta gami da cewa " a'a! " hmmm kedai kika sani, yace kije falonshi yana san ganinki, jikinta na rawa tabi bayan Ammu, hanyar part d'insu Ammu ta nufa Deeyanah tayi saurin cewa " Ammu ke bazaki wajen kiran ba? "Akan me zani? "Ni 'yar aike ce a tsakaninku mahaifi ne yace na kira mishi 'yarshi na kuma isar da sak'o na meye nawa da zanyi katsalandan a ciki!? A fili ta sauke ajiyar zuciya cikin ranta take godewa Allah kan k'in zuwan da Ammu tayi, da Ammi ce ma da d'an sauk'i-sauk'i dan tasan idan aka cirza bayanta zata bi, " Wai bazaki tafi bane kika tsaya kika tsare ni da ido kina mimi da baki!? Saurin barin wajen tayi kafin Ammun tace zata biyota, tana kaiwa k'ofar zata shiga Abbi na kawo kai, a hankali ta fitar da sassanyan numfashi had'i dayin hamdala cikin ranta, sai da ta baari Abbi ya wuce gaba kafin ta bi bayanshi bakinta d'auke da sallama, daga Babah har Deen babu wanda ya amsa mata sallamar sai ma harara da Babah ya galla mata yana fad'in" wato sai da kika biya kika taho da Abbanku saboda kin san baki da gaskiya ko? Kanta ta sunkuyar had'i da nemar guri ta zauna kana ta d'an rusuna tace " Ina yini Babah? Batare daya amsa gaisuwar tata ba yace " kije ki fara shiri jibi zaku wuce in sha Allahu, sai da ta k'ara yin k'asa da kanta kana tace " Babah dama bance bazan bishi babu wani dalili ba, kallan banza Babah ya watsa mata yana fad'in " ki rik'i dalilin naki. "A'a fa Abduljalal karkayi gaggawar yanke hukunci batare daka ji ta bakinta ba itama, "ai dama nasan dan haka ta sako ka a gaba. Dariya Abbi yayi kafin yace " ta sako ni a gaba kuma? "Eh mana, danka shigar mata ba, Abbi yayi murmushi kafin ya kalli Deen yana fad'in " meke faruwa ne!? Cikin girmamawa ya kwashe yadda sukayi kan komawarsu America ya sake fad'awa Abbi, a fili Abbi ya sauke ajiyar zuciya had'i da jinjina kanshi. "Kaji fa fisabilillahi in ba shirme ba har mijinki yace ki shirya ku koma ki tsaya kina wani b'ata lokaci dan samun waje. Ita kam ido ta zubawa Deen tana k'ara ganin girma da k'imarshi kan rashin fad'awa su Babah hanashi hakk'inshi da take yi, wani mugun tausayinshi taji yayi bala'in kamata, hawayen tausayinsu dake shirin zubo mata take ta k'ok'arin mayarwa, ji take yi tamkar ta bishi amma wane ita fad'an yafi k'arfinta, dan idan ta sake tayi kuskuran binshi komai yana iya faruwa. Abbi ya mayar da dubanshi ga Deeyanah yana fad'in " uhunn yi mana bayanin dalilinki nak'in bin mijinki,  d'an jimm tayi kalaman Ajlaal na sake dawowa cikin kanta " wallahi muddin kikayi kuskuran binshi kafin jirginku yakai inda zai kai kun samu labarin rugujewar ahalinku da mutuwarsu kaf dan bazan tab'a barin d'ayansu da rai a doron k'asa ba, kuma na saki video na watsa cewa sanadin video batsarki ne yayi sanadiyyar ajalinsu, suka kashe kansu saboda kunyar duniya, zab'i ya rage naki tsakanin ran ahalinki da mutuncinki da kuma k'iimar zuri'arku kaf da kuma binshi America wanne ya fiye miki mahimmanci. Kanta ta sake sunkuyarwa dan gudun karsu fahimci yadda take kokawa da nutsuwarta, hawayen da take ta dannewa tana k'ok'arin mayar dasu ne, suka kwace mata kafin kace me sun wanke mata fuska. A hasale cikin fushi Babah yace " wai bada ke ake magana bane kinyi shiru in baki da abin cewa mu tashi mu baki waje. Wahalallan munfashi ta fitar had'i da lumshe idonta hawayen suka sake tsiyayowa dan harga Allah tana jin d'acin rabuwa da zatayi dashi da kuma nesa da juna da zasuyi, dakyar ta saita kanta ta bud'i baki tace " Abbi dama saboda tarbiyyar Deedee ne, duk da yadda tayi k'ok'ari wajen saita kanta sai da muryarta tayi rawa. Babah zayyi Magana Abbi yace " ka tsaya a bita a hankali mana, ya mayar da kallanshi gare ta yace " sai ki barshi anan wajen Ammu da Ammi, tunda yanzu ma ba'a hannunki yake ba, muryarta na rawa kamar zatayi kuka tace " Abbi ni dai bana san binshi, da sauri Deen ya d'ago ya kalleta, bata bari sun had'a ido ba tayi saurin sunkuyar da kanta k'asa, a zafafe Babah yace " ke d'in banza kice bazaki biki mijinki ba, idan kin zauna anan d'in wata uwar zakiyi mana? "Shashasha sakarya mara wayo kawai, " kayi hak'uri muji dalilinta mana, Abbi ya sake mayar da kallanshi kanta yace " meyasa baki san binshi Deeyanah? Kanta k'asa tana danne abinda ke taso mata tace " bakomai Abbi. Da k'arfi ya runtse idonshi had'i da cije lips d'inshi, " wani abun yake yi miki acan na zalunci ko na rashin adalci da kyautatawa? "A'a ta sake cewa kanta k'asa. "Wasu abubuwan yake yi wad'anda basu kyautu a addininmu da al'adarmu ba acan? "A'a, ta sake cewa kanta k'asa hawaye nabin fuskarta. "To meyesa baki san bin mijinki inda Allah ya k'adarta muku zama? Shiru tayi dan bata da abin fad'a, "ba tambayarki ake yi ba kin yiwa mututa ne banza dan sakarcin banza? "Bakomai, haka nan kawai bana san binshi, jin tana ta maimaita bata san binshi yayi bala'in dugunzuma Deen, kun san halin kayanku da bak'ar zuciya take yaji ranshi yayi bala'in b'aci, zuciyarshi tayi bak'ikk'irin yadda kasan gawayi, jijiyoyin kanshi sukayi rad'o-rad'o kamar an zana su, saboda tsabar zuciya har wani yaji-yaji yake ji cikin idonshi, ji yayi ko idan bai tafi da ita ba hakan na nufin ajalinshi ya hak'ura, ko duniya zata tashi bata binshi America, har abada ya gama tafiya da ita ko'ina a duniya, Abbi zayyi magana yayi saurin cewa " shikenan bakomai ta zauna d'in Abbi. Nan fa Babah yayi tsalle ya dire ya shiga bambami " ke d'in banza ke d'in wofi Deeyanah har kin isa ni mahaifinki da mijinki da kike a k'ark'ashin mu muce ga abinda zakiyi kice ba haka ba, wallahi baki isa ba, ai bake kika haifi kanki ba, ba kuma ke kike auran kanki ba, bake kika haife mu ba, kamar yadda bake kike auranshi ba, muddin kina neman kwanciyar hankali ki shirya kibi mijinki. Sanin halin bak'ar zuciyar Deen da tun yana yaro in yace yabar abu ya barshi har abada ko za'a kashe shi yasa Abbi saurin cewa " a'a ka tsaya abi komai a hankali cikin lumana da dad'in rai, kar ayi abinda zai zo bayyiwa wani dad'i ba, adalci da fahimtar juna shine farkon abinda ake so a auratayya, yau da gobe sai Allah kamata yayi a karb'i uzurinta a duba mata itama, bawai a tirsasa mata ba. "Karka d'aure mata gindi, wannan ai maganar banza ce daga bakin mutanen banza ka tab'a jin inda kana wata duniya matarka na wata nahiya fisabilillahi? "Kai namiji ne, ni namiji ne daga ni har kai mun san yanayin in dai ba kuma so ake ajefa shi a halaka ba, a sashi ya fara neme-neman matan banza ba, Babah ya fad'a yana kallan Abbi. Abbi zayyi magana Babah yayi saurin cewa " wallahi ko zata mutu acan saita bishi. Jin Babah ya runtse yasa Abbi cewa " Allah ya kyauta, Babah ya amsa da Amin. Duk da hukuncin da Babah ya yanke ko kad'an Deen bai ji a ranshi cewar zai tafi da Deeyanah ba, a yadda yake ji a ranshi idan aka matsa yana iya sauke mata igiyoyin aurenshi kowa ya huta. Shi kad'ai yake ta shirya-shiryen tafiyarshi bai sake bi takanta ba, bai kuma sake yi mata maganar tafiyar ba, itama batayi mishi maganar ba, bai gayawa kowa shi kad'ai zai tafi ba har ranar tafiyar tazo yana janye da trolley ya fito daga bedroom d'inshi dan tuni suka raba d'akin kwana, da sauri ta mik'e tana binshi da kallan mamaki, gaba d'aya tama kasa magana ta zama speechless, take gabanta ya shiga fad'uwa yana dukan uku-uku, tsoro da tsakanin fargaba suka shigeta lokaci d'aya, cikin ranta ta soma maimaita " Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un badai tafiya zayyi ya barni ni kad'ai cikin wannan babban bala'in ba? "Bazan iya ba, bazan iya d'auka ni kad'ai ba, ganinka kawai da nake yi a kusa dani yana sakamun nutsuwa da kwanciyar hankalin cewa koba komai ina da mai tayani yak'ar Ajlaal wata rana, Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un na shiga uku ina zan kai wannan mummunar k'addarar? Ta fad'a cikin ranta, kamar bazayyi mata magana ba sai kuma ya dawo ya kalli idonta dake cike tab da ruwan hawaye yace " zan tafi, na aje miki kud'i, idan sun k'are ko kina buk'atar wani abu muyi magana. Wani irin kuka ne mai nauyi da k'unci  ya kwace mata, bata san sanda ta fad'a jikinshi tana fad'in " karka tafi ka barni ni kad'ai ba, bazan iya jurewa k'addarori biyu a lokaci d'aya ba, na gwammaci mutuwa ta sau dubu yaya da irin rayuwar da nake yi, sai da yayi da gaske ya iya mayar da abinda ke taso mishi, a hankali ya rabata da jikinshi dan baiga dalilin yin kukanta yanzu ba, duk wata dama ya bata, ya tambayeta idan tana cikin matsala ta fad'a mishi su raba matsalar tare, amma tak'i bashi damar data cancance shi, ta hanashi hakk'inshi dake kanta wanda Allah ya halarta mishi. Hannunshi ta rik'e gam cikin nata hawaye nabin fuskarta tace " da nace ina sanka a karon farko nasan ka jini, na fad'a na sake maimaitawa badan ina da shakku kan yardarka ba, sai dan ranakun da kalamai zasuyi min k'aranci, dan ranakun da yanayin k'addara zasu iya yi min katanga da fad'ar, dan ranakun da bani da tambacin samun damar fad'ar, na so ka jiya, ina sanka yau, babu kuma abinda zai canja gobe, Deen zuciyata taka ce kai kad'ai, koda k'addara ta gifta a tsakaninmu ka sani nayi abinda nayi ne danku. Juyowa yayi ya kalli cikin kwayar idonta yace " ina sanki jiya ina sanki yau, cin amana ne kad'ai zai canja gobe, Deeyanah ina sanki da komai nawa, numfashi na bai tab'a fita batare dana tunaki ba, amma ki sani muddin cin amana ya shigo tsakaninmu nayi miki alk'awarin zan tsane ki fiye da komai har izuwa k'arshen rayuwata, kuma wallahi har ki mutu bazaki sake gani na a duniyarki ba, murmushin yak'e tayi tana shafa fuskarshi amma deep down yadda kasan ana tsikarawa zuciyarta alluran da suka shekara a wuta haka take ji, tana kallanshi har ya fice ta kasa cewa komai balle ta bishi, abinda take ji yau ya girmi bak'in ciki, kalamanshi sun saukar mata tsoro da fargaba. "Karki bishi Deeyanah, karki sake kiyi gigi da gangancin binshi, dan binshi tamkar kin sallama kowa cikin ahalinki ne ciki kuwa har da tilon d'anki, sannan shima saina sashi ya tsaneki fiye da mutuwarshi dan saina saki videon nan, kuma bazaki tab'a b'ace min a duniya ba, duk inda kika shiga saina nemomi a duniya. Kalaman Ajlaal daya fad'a mata bayan sun dawo daga wajensu Abbi da Babah suka dawo mata, tana nan tsaye inda ya barta kamar wacce aka dasa hawaye nabin fuskarta, taji an hura mata iska a fuska, ajiyar ta sauke a fili ta kalleshi batare datace komai ba. Allah ya taimaka su Abbi basa gida lokacin da Deen zai tafiya danshi a zatonshi da Deeyanah zai tafiya, jiya da daddare daje yi musu sallah nasihar dayayi mishi ta shafi ta zamansu acan, sama-sama ya biya yayiwa su Ammu sallama ya wuce yana juya kalamanta cikin kanshi. Light kiss yayi mata a gefen fuskarta yana fad'in " kin samu freedom ko? "Hararshi tayi tana d'oye damuwarta tace " ka dai samu freedom, tuntsurewa yayi da dariya sosai yana cewa " tab! sannunki, ai ni dama can a freedom d'ina nake kece dai a kulle kamar dabba, bataji dad'in maganarshi ba, amma ta basar, "zamuje can ne ko anan zamu soye, yayi maganar had'i da kashe mata ido d'aya ya cije leb'enshi na k'asa, ai yadda yayi mata take taji wani yarrrr a jikinta wutar ta ta kawo bata san, sanda ta had'e bakinsu tana k'ok'arin nemarwa kanta sauk'i da sassauci kan halin da take ciki ba. Martani ya shiga mayar mata cikin salon gusar da hankali, ya d'auketa cak ta zagayo da k'afarta ta bayanshi suna daga tsaye suke mahaukacin romance, bakinshi cikin nata yana sucking lips d'inta while hannayenshi na bayanta yana shafa duk inda ya ci karo dashi, a haka ya rink'a tafiya har ya isa bango ya had'a bayanta da bango ya gyara tsaiyuwarshi sosai yadda zaiji dad'i, ya soma murza boobs d'inta, a hankali ya cire bakinshi daga nata ya mayar kan boobs d'inta ya shiga basu kyakkyawan sucking had'i da lasar kan nipples d'inta, sai da suka gama birkita juna da haukata junansu kafin daga tsaye a haka sukayi sex. Bayan Shekara D'aya.... Haka rayuwa tayi ta tafiya lokaci na k'urewa amma babu abinda ya canja tsakanin Deeyanah da Ajlaal sai ma abinda yayi gaba, dan yanzu wata irin muguwar shak'uwa ce ta shiga tsakaninsu, tare suke aiwatar da kusan gaba d'aya rayuwarsu, tuni Ajlaal ya dawo da kwana nan gidansu Deeyanah, amma babu wanda yaga wani alamu balle ayi zargin wani abu, tun farko idan baku manta ba na fad'a muku irin kwakwalwar Ajlaal da k'ok'arin dayake dashi a makaranta, so yana shirya komai ne da kwakwalwa cikin kwarewa, da zurfaffan tunani, dan bayayin abu cikin sauri sai yayi tunani me zurfi akanshi, a b'angaren Deen kuwa har yanzu bai dawo ba tunda ya tafi kun san mutuminku da bak'ar zuciya, ko tunanin waiwayar Nigeria bayayi, haka a tsakaninshi da Deeyanah babu wata jituwa sai sama-sama bama ta fiya kiran nashi ba, shima kuma bai wani damu da hakan ba balle ya dameshi, yakance kowanne mutum ya kan buk'aci hutu da sarari idan aka k'i bashi ko aka matsa mishi ana iya samun matsala. Sanye take da rigarshi armless a jikinta da gajeren wondo gashin kanta d'aure da ribon tana kallanshi d'aure da towel a k'ugunshi yana yankan albasa, Deeyanah tayi dariya tana kallan yadda idon Ajlaal ke zubar da kwalla tace " kaji yadda ake ji ko? "Ni babu wani abinda naji, kudai mata kun fiya raki wallahi, ta kwashe da dariya har da rik'e ciki tace " kalli fa yadda idonka ke ruwa amma dan fad'in ran tsiya kak'i yarda ka fad'i dama ance gajerun mutane fad'in ran tsiya ne dasu. Dakatawa yayi da yankan albasar ya kalleta yace " wait wai dani kike? "Nine gajeren kowa? Ya fad'a yana nuna kanshi cike da mamaki, ya kalli tazarar tsayin dake tsakaninsu da iyakacinta k'irjinshi amma take ce mishi gajere. "A'a! Bada kai nake ba da wancan fridge d'in nake, " hmmm, yace tare da d'aukar albasar daya gama yankawa zai zuba a tukunya tayi saurin cewa " karka zuba ba haka ake yi ba, sororo yayi rik'e da albasar a hannunshi yana binta da kallo, baya taja tana dariya gami da nuna mishi yatsa tace " kaga na kama ka ta tabbata abincin jiya suyowa kayi bakai ka dafa ba. "Eh! Naji na yarda siyowar nayi amma dai kin san ai na iya girki ko? "Kuma sanin kanki ne ba fina iyawa kikayi ba. "Shiyasa jiya ka dama mana kunu da sunan d'an wake, yayi kanta da gudu ta zame tayi waje ya bita sukayi ta zagaye falon suna jefe-jefen pillows, yayi caraf ya kamata ya d'agata sama suna dariya. "Wana kama!? Tayi dariya tace " Wanda ya fad'i gaskiyar ka dama kunu da sunan d'an wake. Kissing d'inta yayi had'i da zaunar da ita akan durowar kitchen yana fad'in " zauna kiyi kallan Chef Ajlaal na Deeyanah yana girki, ta kwab'e fuska kamar zatayi kuka tace " ni dai please a'a muyi order kawai, idan naci wannan girkin naka kwana zanyi ina sintirin zuwa toilet, d'an dukan wasa ya kawo mata ta goge tana dariya yace " sai fa kin ci. Da taimakonta ya dafa musu fried spaghetti da hanta, yana bata tana bashi har suka k'oshi, ta d'ane bayanshi tana dariya sukayi bathroom,  sai da suka gama lalacewar su da wasan ruwa kana sukayi wanka tare. Haka suke aiwatar da rayuwarsu ko yaushe cikin farin ciki da kulawa, sai dai bata fiya zuwa gidanshi ba saboda mugun idon da Babah ya saka mata, sai dai shi kullum yana gidan 24/7 suna tare, idan kaga sun rabu sai dai idan wani babban dalili ne, kullum koyaushe suna cikin yin sex sai kace engine. Tuni Deeyanah ta falle, idonta ya bud'e ta shiga harkar neme-nemen magungunan mata wanda a da can batayi, a cewarta fruit kad'ai is okey but not now, dan yanzu duk inda sukaji maganin mata sai sun siya daga ita harshi, tun yana siyo mata ya tsareta ta shanye tas a gabanshi har yakai dakanta take siyan kayanta. Ta jajje neman Aunty Jamilan Raleeya bata samunta dan taji labarinta wajen Raleeya kan bala'in bid'ar magungunan mata, a online ta had'u da wata gogar mata 'yar duniya ta bugawa a jarida shafin farko, taso ta rink'a had'a Deeyanah da wasu mazan amma tak'i iyakar alak'arta da matar siyan magungunan mata a hannunta. Tana kwance saman faffad'an k'irjinshi hannunta na aikin shafa kwantaccen gashin dake kwance luf-luf a k'irjinshi, yayinda hannunshi ke shafa gashin kanta ta d'ago ta kalleshi tace " Noor yaushe zamu je gidan Aunty Sa'a ne, tayi min waya an kawo sabbabin kayan harka daga Niger da Sokoto fa. Wayar hannunshi da yake dubawa ya aje yana kallanta yace " wai da gaske? "Da gaske mana jiya take fad'a min. "Ta kawo harda na maza in siya nima. D'agowa tayi da sauri ta kalleshi tace " Wa zaka shawa maganin amma badai ni ba ko? A hakan ma yana k'are da jarabarka balle kasha wani abu? "Kai kullum joy stick d'inka a mik'e take ko gajiya ma batayi. Dariya yayi sosai ya kamo hannunta ya d'ora saman Bananarshi yana fad'in " kinji ta yanzu ma a mik'en take. Ido ta d'an zaro waje tace " yanzu muka gama sex and kayi over 30 minutes akaina daga kan romance zuwa sex amma still kana neman k'ari? "Ai dai gata nan kin ji ta, ba wani ne ya fad'a miki ba. "Wai ni kam dan Allah baka gajiya da sex ne? "Tsaya dama can haka kake ko kuwa yanzu samun waje ne? Dariya ya saka yana juyewa ya mayar da ita k'asanshi ya haye samanta yana fad'in " samun waje ko, bari kiga tabbacin na samu waje, dariya ta sanya sosai tace " wallahi baka isa ba, tab! na biyeka cikin 'yan shekaru zaka kwak'uleni ka mayar dani tsohuwar k'arfi da yaji, kai baka gajiya da abu d'aya, bayyi magana ba ya had'e bakinsu, ya tsoma tsotsar leb'enta da harshenta, while hannunshi yana yawo a jikinta, sosai ya soma rikitata, dan Ajlaal namijin gaske ne, ya kai mak'ura wajen iya sarrafa mace akan bed, wani irin gurnani ne ya soma tashi had'i da fad'awa junansu kalamai masu dad'i. Kasancewar gidansu Deeyanah estate ne kowa da part d'inshi, ba kasafai suka fiye shiga part d'in juna ba, gwara ma yaran idan safiya tayi suna shiga su gaida iyayensu, sun had'a uban gumi harka ta d'auki zafi ya soma pushing a kanta suka ji yo bugun k'ofa, sama-sama ta rink'a jin bugun kafin bugun ya yawaita ta jiyo shi sosai cikin kwanta, da sauri ta soma k'ok'arin zame jikinta daga nashi amma sayya k'ara sakar mata nauyinshi ya danneta sosai yadda bazata iya kwacewa ba, muryarta na sark'ewa tace" Aj....lal ana bu....gun...k'o....far...fa, tayi maganar a rarrabe kamar me koyon magana. Babu abinda yayi illa cigaba ma da yayi da pumping akan ruwan cikinta, batayi zato ba taji ana bugun k'ofar bedroom d'in da suke, wai tashin hankali wanda ba'a saka maka rana take jikin Deeyanah ya d'auki wani irin mugun rawa da kerrrma, hankalinta yakai k'ololuwar tashi, ta sanya hannu d'aya ta rufe bakin Ajlaal dake faman ihuuun dad'i, d'aya hannun kuma ta soma tureshi da iya k'arfinta, jin ko gezau ba yayi yasata fara kuka k'asa tana rok'onshi amma ina bama yajin abinda take cewa, dan kwata-kwata baya cikin hayyacinshi baima san a wacce duniyar yake ba, duk abinda take yi da bugun k'ofar da ake ta famanyi ba jinsu yake ba, yana can k'ololuwar sama yana yawo. K'irjinshi ta soma duka da iya k'arfinta had'i da cizonshi da yakushi amma a banza yadda kasan dutse take yiwa. " Deeyanah ko bacci kike yi ne? Ta jiyo muryar Ammu daga bakin k'ofar d'akin, "Momy! ci bute mana, Deedee ya fad'a shima yana bugun k'ofar. Bata tab'a sanin k'aryar iskanci ba sai yau, tunda suka fara nema ita da Ajlaal bata tab'a shiga tashin hankali da firgici irin na yau ba, da aurenta kwarto yana sex da ita a gidansu, a d'akin aurenta akan gadon mijinta, ga mahaifiyarta da d'anta na cikinta na tsaye a bakin k'ofar d'akin da take aikata zina, bayan da auren mahaifinshi akanta, tasan yara bakomai suke iya sani ko su fahimta ba, amma tasan muddin yau asirinta ya tono har abada hoton abun bazai tab'a gogewa daga kwakwalwar Deedee ba. "Wayyo Allah na shiga uku! ta furta batare data sani ba, karaf kalmar ta sauka akan kunnen Ammu data juya zata bar bakin k'ofar dan tayi zaton bacci take yi, saurin dawowa tayi cikin tashin hankali ta d'an bugi k'ofar kad'an tana fad'in " lafiya Deeyanah? "Meya same ki? "Kina jina? Sautin kuka da gurnani Ammu ta soma jiyowa k'asa-k'asa hakan ba k'aramin d'aga hankalinta yayi ba jikinta ya d'auki rawa dan a tunaninta wani abu ne ya samu Deeyanah, bugun k'ofar ta shiga yi sosai tana k'iran sunanta, jin shiru yasa Ammu fita da gudu dan kiransu Babah, da ma'aikatan gidan azo a b'alle k'ofar. Bata dad'e ba suka dawo tare da Abbi da Babah da kuma Ammi da kusan mutum goma har da yayyan Deeyanah, Azaan da Azwah, suma bugun k'ofar suka shiga yi suna kiran sunanta, amma shiru, "ga fara daga jikin k'ofar. Abbi ya fad'a yana tattare wondon shaddar dake jikinshi, ganin abinda yake shirin aikatawa yasa Azaan saurin tarar Abbi ya bugi k'ofar da iya k'arfinshi amma ko gezau k'ofar batayi ba. Wayyo Allah ai Deeyanah tana jin an fara bugun k'ofar jikinta ya d'auki kerrrma da tsuma kamar ana buga mata ganki ko me cutar farfad'iya, tayi iya k'ok'arinta ta tura Ajlaal daga kanta amma yadda kasan k'ara mishi k'arfin danneta take yi, yau kam tana shirin ganin tunon asiri wata k'illa tashin alk'iyamarta ne yazo, duk addu'ar da tazo bakinta ita take yi, har wani kashi-kashi take ji yana danno ta, in banda dukan uku babu abinda k'irjinta keyi, saboda tsananin yadda k'irjinta ke bugawa da k'arfi idan ka tsaya kusa da ita zaka iya juyo sautin bugun da k'irjinta keyi. Wani irin nauyi zuciyarta tayi mata, nauyin da bazata iya d'auka ba, idanuwanta ta lumshe hawaye na gangaro mata, ta riga ta sadak'ar yau me aukuwa zata auku, tasan komai zata fad'a musu dan kare kanta bazasu tab'a yarda da ita ba, balle har su fahimce ta, tasan ta riga tayiwa kanta da rayuwarta illar da har a tashi duniya bazata tab'a gyaruwa ba. Baya Azaan da Azwah suka ja kafin suka dawo suka daki k'ofar da k'arfi aiko bugun da sukayiwa k'ofar a tare lokaci d'aya yasa k'ofar bud'ewa, lokaci d'aya suka danna kai cikin d'akin, kwance suka isketa saman gadon kamar matacciya, jikin Ammi na rawa ta hau saman gadon ta d'agota tana jijjiga ta had'i da kiran sunanta " Deeyanah? Amma shiru babu alamun motsi " Alhaji a sume fa take, bargon data rufe jikinta dashi Azaan ya yaye bayyi magana ba ya sungume ta cak yayi waje da ita, Ammi ta bishi rik'e da d'an kwallin doguwar rigar dake jikin Deeyanah a hannunta, duk aka fita banda Ammu dake bin d'akin da kallo, haka nan kawai take jin ranta babu dad'i game da d'akin, takai minti d'aya tana bin d'akin da kallo kana ta fice, Ajlaal dake lab'e cikin wardrobe ya fito tsirara yana mayar da numfashi. Bai damu dan an shigo an gansu suna sex ba, yasan babu abinda suka isa suyi mishi yadai b'uya ne saboda ita da kuma farin cikinta, tuno yadda ta rink'a marinshi tayi tana fad'in " Ajlaal ka rufa min asiri ka d'aga ni, matuk'ar son da kake yi min gaskiya ne zaka so kare min mutunci na, zaka rufa min asiri na dan kar na kunyata na muzanta a idon ahalina, bata daina marinshi tana rok'onshi ba har saida Allah ya taimake ta ya dawo cikin hayyacinshi ya ji abinda take fad'a da abinda ke faruwa, da sauri ya d'agata, ta mayar da part da bra d'inta a gaggauce, ta zira doguwar rigar atampa ta tattare gashin kanta ta saka ribon, ta danna shi cikin wardrobe ta b'uye, da sauri ta dawo ta kwanta, tana kwanciya suna b'alle k'ofar. Murmushi yayi gami da shafa kwantacciyar sumar kanshi ya fad'a bathroom yana wankan yana mitar yau an d'auke Deeyanah an barshi yana wanka shi kad'ai, hankalinshi a kwance kamar yana gidan ubanshi yayi wankan ya fito ya shirya kana ya sulale yabi ta k'ofar baya ya fice. Jikin Azaan na rawa ya shinfid'e Deeyanah a bayan mota, da hanzarinshi ya zagaya zai zauna a mazaunin driver, d'aya daga cikin drivers d'in gidan yayi saurin shiga ya zauna, Azaan ya bud'e gaban motar ya shiga driver yaja motar suka fice daga harabar gidan, dan gani Azaan yake matsalar tafi k'arfin asibitin cikin Estate. A wata motar su Ammi suka bi bayansu, sai da suka fito kana Ammi ta kira Azaan " wanne asibiti kuka nufa? "Sahal, ya bata amsa a tak'aice. Ana zuwa aka shigar da ita Emergency likita mace ta shiga da sauri, tana shiga ta iske Deeyanah a zaune kan gadon dangwargwar cikin mamaki ta nunata tana fad'in " ba kece marar lafiyar da aka kawo yanzu Unconscious ba. Murmushi Deeyanah tayi daya k'ara jefa likitan cikin mamaki tace " wai ina mara lafiyar ne? "Ni ce nan mara lafiyar da aka kawo, kuma lafiya ta k'alau, abinda nake so dake ki fita ki sanar dasu ba wani abu ne yake damuna sosai ba, wani abu naci ya b'ata min ciki, hannuwa likitan ta hard'e a k'irji tana kallan Deeyanah tace " meyasa zanyi hakan? Hannu Deeyanah ta saka a k'ugunta ta zaro bandir d'in 'yan dubu-dubu guda uku data soke dan hakan, ta mik'a mata su, tana fad'in " idan sunyi miki kad'an ki bani account number ki yanzu zan saka a tura miki 700k su cike 1m, jikin likitan na rawa tayi caraf ta amshi tana fad'in " ai babu mai mayar da alkhairi sai Shaid'an, bari na baki account number tawa. Murmushi Deeyanah tayi mai kamar dariya had'i da rolling sexy eyes d'inta tace " naira kenan me maganin d'an ganta, me mayar da talaka ya koma sarki, me mayar da tsoho yaro, me wanke bak'in ciki da damuwa, " bari na baki number da zaki tura a saka miki kud'in, ta karanto mata number Ajlaal, ta tura mishi account number, dama ya riga ya san zancen batayi minti biyu da tura mishi account number ba kud'in suka shigo. Idanuwa ta zaro tana fad'in " sun shigo fa, Deeyanah tayi 'yar siririyar dariya, likita ta saka kud'in a jakarta tana fad'in kwanta, tana kwanciya nurses na shigowa, likitan ta cire safar hannunta tana fad'in " na gama dubata ku kaita d'akin hutu ku juna mata drip.Cikin girmamawa suka amsa da " to, bata k'ara magana ba ta fice ta iske Familyn Deeyanah tsaiysaye bakin k'ofa, suna ganin ta fito duk sukayo kanta da tamabayar ya Deeyanah, 'yar gyaran murya tayi tace " Alhamdulillah ba wani babban abun damuwa bane, inaga wani abun taci ya b'ata mata ciki, ko kuma tana da allergy da abun bata sani ba, a godewa Allah da abun ya tsaya iya haka, tana d'akin hutu zaku iya shiga ku ganta, ta k'arasa maganar tana bin fuskokinsu da kallo tana hango tsatsar damuwar da suka shiga, cikin ranta take tunanin meyasa tayiwa iyayenta wannan k'aryar? Gaba d'ayansu suka d'unguma zuwa d'akin hutun da aka kaita, tana kwance kamar me bacci hannunta manne da drip, kowa ka gani fuskarshi babu walwala duk sunyi wani jugum-jugum kalar tausayi, tana kwance saman gadon marasa lafiya sai sauke numfashi take kamar gaske, idon Ammu tsaye k'em akan Deeyanah, ta rasa meke mata dad'i, tana jin wani nauyi a k'asan zuciyarta, ta rasa dalilin da yasa take jin kamar komai ba'a dai-dai yake ba, sai da aka d'auki kusan awa d'aya da rabi kafin ta yamutsa fuskarta a hankali ta bud'e idonta, cikin dauriya da k'arfin hali ta soma k'ok'arin tashi daga kwancen, " sannu! Ammi ta fad'a tana rik'e ta, sai da ta kwab'e fuskarta kamar zatayi kuka ta amsa da " yauwa. "Me kika ci ne da har ya b'ata miki ciki haka? "Dakyar tace " jiya cikin dare naji yunwa shine fa d'an dafa Indomie naci na kwanta, " sai kace wata k'aramar yarinyar da bata san ba'a cin abinci a kwanta ba, ke ma me fad'awa wani ce fa Deeyanah. "Wallahi Ammi ji nayi yunwar na neman illata ni shiyasa naci abincin, kuma ina gama ci bacci ya d'auke ni, " Allah kyauta, Ammu tace tana danna wayar dake hannunta. "Allah ya kyauta kuma? "A'a to me zance? "Allah ya bata lafiya ya kamata kice ai, " to Allah bata lafiya. Taso tunda sukayi kwana d'aya su koma gida amma Ammu tace " wani abu kika aje a gidanne da kika matsu akanshi har haka, bata kuma maganar sallamar ba, fuskarta d'auke da murmushi hannunta rik'e da wayarta tana chart da Ajlaal, "wai sai yaushe za'a sallame ki? "Wallahi nima ban sani ba, nayi zaton yau za'a sallame ni, dan har magana ma nayi Ammu ta mayar min da bak'ar maganar data sani yin shiru dole, "Wallahi a matse nake ne, emoji's d'in dariya da gwalo ta tura mishi, yayi murmushi had'i da gyara kwanciyarshi ya tura mata " to kodai inzo ne kawai muyi anan? Emojin zaro ido ta tura mishi had'i da cewa " kai! rufa min asiri Ammu na nan fa, "to dan tana nan sai me? "Yadda kake ihuuun nan ai ji zatayi, ta tura mishi fuskarta d'auke da bayyanan murmushi, "ku dai yaran nan bakwa gajiya baki da lafiyan ma kina kwance a asibiti Deen bazai sarara miki ba? Saurin kifa wayar tayi dan a zatonta Ammi tayi bacci tuni, "lah Ammi bafa haka bane, "idan ba haka bane to yaya ne? Murmushi tayi had'i da cewa " Ammi gaya mishi nayi bani da lafiya shine yace zai taho nace mishi a'a ya bari sai anyi hutu, " hmmm kudai kuka sani kuma, shiru sukayi daga ita har Ammin kafin Deeyanah ta kira sunanta, " Ammi!, "na'am Ammi ta amsa tana kallan Deeyanah, sai da ta sauke ajiyar zuciya kafin ta sake kiran sunanta " Ammi!, d'an shiru tayi batare datace komai ba, tashi zaune Ammi tayi daga kwancen da take tana kallan Deeyanah tace "uhunn ina jinki. A fili ta sauke ajiyar zuciya tana san tayi magana da wani amma tana tsoro, tana san ta fad'awa wani damuwarta koba komai zata samu sauk'i da sassauci amma ta rasa ta yadda zatayi ta fad'a, " kin kira ni kuma kinyi shiru, muryarta k'asa-k'asa kamar me rad'a tace " bakomai  Ammi, yadda tayi maganar ya tabbatarwa Ammi da wani abu, "kiyi maganarki bakomai kinji, murmushin k'arfin hali tayi tace " bafa wani abu bane dama cewa zanyi gobe za'a iya sallamarmu? Daga yanayin yadda tayi maganar ya tambatarwa Ammi cewa " ba maganar dake k'ark'ashin zuciyarta kenan ba, d'an murmushi Ammi tayi irin nasu na manya cikin ranta tana fad'in " wata k'ila, tayi niyyar tayi mata magana  mai mahimmanci amma saita fasa, komawa Ammi tayi ta kwanta, Deeyanah ta d'auki wayarta tana duba chart d'in Ajlaal, " ki shigo ban d'aki, ido ta zaro had'i da kallan Ammi, taga ta juya mata baya da alama batayi bacci ba, sake karanta chart d'in tayi taga tun kusan mintuna biyar baya yayi maganar, " wai da gaske? A tak'ace ya mayar mata amsa da " shigo ki gani mana, wayar ta kifa tana jan numfashi da k'arfi, a hankali ta zuro k'afafuwanta k'asa ta mik'e Ammi najin motsinta amma batayi magana ba ta san wata k'ila ban d'aki zata shiga, cikin sand'a take takawa harta isa bakin k'ofar ban d'akin ta sanya hannu ta bud'e a hankali ta shiga, yana zaune kan masan zama yana daddana waya, da sauri ta k'arasa shigowa ta mayar da k'ofar ta rufe, " kana da hankali kuwa Ajlaal har nan ka biyo ni? Ta fad'a cikin tashin hankali idanuwanta kamar zasu fad'o k'asa, yatsanshi ya d'ora saman lips d'inshi yace " shhhhhh, had'i da nuna mata k'ofa da ido, ta d'an daki kafad'arshi tare da cewa " idan aka kama mu fa? "Dai-dai kenan kinga sai su bar ki na aura shikenan kowa ya huta, dukanshi ta sake yi a kafad'a ya shafa wajen yana fad'in " ouch da zafi, ya mik'a hannunshi ya jawo ta ya zaunar da ita saman cinyarshi ya shafa bayanta yace " I missed you so much, tana dariya taja hancinshi tare da cewa " nima haka, murmushi yayi wanda yasa zuciyarta tsayawa cak, Ajlaal yana da wani irin sihirtaccen kyau shiyasa mata dayawa suka mutu kan sanshi, duk abinda ake nema a wajen d'a namiji yana dashi, dariya ya sake mata a karo na ba adadi ya hura mata iskar bakinshi a fuskarta tare cewa " wannan kallon fa? Kanta tayi saurin kawar gefe tana jin yadda zuciyarta ke tsananta bugawa, sake juyowa tayi ta sauke idonta akan kyakkyawan leb'enshi pink color ta zubawa leb'en ido bata ko k'iftawa, mak'ogwaronta ya kalla yaga yadda take had'iyar yawu da sauri da sauri,  zayyi magana tayi saurin fisgoshi ta had'e bakinsu, had'i da luma yatsunta cikin kwanciyar sumar kanshi, hannunshi ya zagayo ta bayanta ya matso da ita sosai ya soma tsotsar lips d'inta, kafin kace me sun gama rikicewa sun birkice sun fice fit daga hayyacinsu wani irin American hot romance suke yiwa juna, hannunshi d'aya kan boobs d'inta while d'aya hannun yana cikin pant d'inta, gantsarewa ta somayi tana turo mishi k'irjinta yayinda d'aya hannunta yake kan hannunshi dake cikin k'asanta tana  k'ara danna hannun cikin k'asan nata, in banda nishi da gurnani babu abinda suke fitarwa, sun gama tsundumawa wata duniya ta daban, knocking k'ofar ban d'akin Ammi ta soma tana fad'in " lafiya Deeyanah, da farko bata jiyo maganar Ammi ba sai daga baya, dakyar ta iya bud'e bakinta tace " Ammi nishin kashi nake yi, ta fad'a a rarrabe kamar me koyan magana, " to Allah ya sauwak'e Ammi tace tana barin bakin k'ofar. Sun d'auki lokaci suna jiyar da junansu dad'in juna kafin suka sassautawa juna, tana nishi ta sanya hannu ta mayar da gashin kanta baya tace " ka tafi ni zan koma kar Ammi taga na dad'e, " to, kawai ya iya cewa ya dira ta window, sai da ta wanke fuskarta ta d'an saita kanta kana ta fita, lokacin har bacci ya d'auke Ammi, a fili ta sauke ajiyar zuciya ta kwanta rigingine tana kallan rufin d'akin while tana mayar da numfashi, a hankali ta rufe idonta tana jin wani irin yanayi me wuyar fassarawa, kwanakinsu biyar a asibitin aka sallamesu, bayan duk dare sai Ajlaal yazo ya kwashi ganima. Suna zaune a babban falon gidan ana kallon tsohon film d'in Marigayi Rabilu Musa d'an Ibro mai suna Namamajo su Abbi sai dariya suke yi, Deeyanah na zaune kan dinning tana shan tea while wayarta na hannunta tana chart Deedee ya rugo da gudu wajen " Momy dan ta, murmushi tayi mishi had'i da cewa " da zafi sosai, " to Momy bani wayanki nayi game, sai da gabanta ya fad'i dan chart take yi Ajlaal, tayi murmushin yak'e tace " a'a bazan baka wayata ba jeka wajen Abbi ko Ammi su baka tasu dama da ita ka saba yin game d'in, "Momy ni taki nake so, ya fad'a yana kwab'e fuska zayyi kuka, " wayata babu game ko d'aya Deedee kaje Ammu ta baka tata kayi, kuka ya saka harda buga k'ofa irin na shagwabb'un yaran masu kud'i yace " ni dai taki nake so, yayi maganar hannunshi kan wayarta, bata san sanda ta d'auke shi da mari ba, had'i da tura shi baya ya fad'i ba, dai-dai akan idon Ammi. Tasowa tayi cikin b'acin rai tace " me yayi da zaki dake shi? Yaran da tsakaninki dashi haihuwa ce kawai, sai dai ki kalleshi da ido bayan nan wata tsiyar kike tsinana mishi? " Ammu damu na yayi nace mishi ya bari yak'i bari, cikin kuka Deedee yace " waya nace ta bani nayi game fa, cikin masifa da bambami Ammi tace " wata tsiyar ce a cikin wayar taki da kike b'oyewa har haka? "Daga yace ki bashi waya yayi game sai duka dan zalunci? " Ya Isa haka dan Allah, Abbi ya fad'a idonshi kan Tv, "Alhaji na lura kwata-kwata baku kula da canjawar da yarinyar nan tayi ba, abubuwa take yi a nannad'e kamar munafuka, duk suffofin munafurci da rashin gaskiya sun bayyana a tattare da ita. "Subhanallahi! Haba  Aina'u meke damunki haka? " 'Yarki ce fa ta cikinki kike fad'ar abinda ko wani kikaji zai fad'a akanta sai inda k'arfinki ya k'are, Babah ya fad'a ranshi a matuk'ar b'ace, zata sake yin magana ya d'aga hannu tare cewa " ki fad'i alkhairi ko kiyi shiru, bata sake magana ba ta watsawa Deeyanah harara had'i da d'aukar Deedee tabar wajen gaba d'aya. Deeyanah ta mik'e hannunta rik'e da kofi zata mayar kitchen taji wayar Ammi ta d'auki sowa, bata kula ba tasa kai zata wuce kitchen tana gaf da shiga kitchen d'in ta jiyo Ammi na fad'in " lafiya k'alau Deeni ya nan wajen naku? Bata san amsar daya bata ba ta shige kitchen d'in dan ita har mantawa take yi dashi idan ba irin haka ta kama ba, ko dalili yasa ta tunoshi, ta aje kofin tana shirin fitowa ta jiyo muryar Ammi na fad'in " ai har an sallamomu daga asibitin ma, duk da bata ji abinda yace mata ba amma ta fuskanta dan ko ba'a fad'a mata tasan cewa yayi waye bai da lafiya, mamaki k'arara a fuskar Ammi tace " ban gane waye bashi da lafiya ba? Daga d'aya b'angaren kuwa mik'ewa yayi daga kwancen da yake yana fad'in " wallahi Ammi ban san wanda bashi da lafiya ba, bakinta bud'e tana kallan Deeyanah dake fitowa daga kitchen tace " matarka aka kwantar a asibiti har kwana biyar. Cikin Mamaki yace " Deeyanah? "Kana da wata matar ne bayan ita? Ido Deeyanah ta runtse da k'arfi had'i da cije leb'enta na k'asa tace " wayyo Allah, dan ta tuno ranar da take chart a asibiti da Ammi tayi mata magana tace mata Deen take fad'awa bata da lafiya, kanta ta dafe tana tunanin k'aryar da zata yiwa Ammin dan gusar da hankalinta daga zargin wani abun na daban kamar yadda Ammu ke yi. "A'a! Ammi kawai dai ina mamakin meya hanata sanar dani ne, itama Ammi tunowa tayi da Deeyanah tace mata ta fad'awa Deen, kamar zatayi magana sai kuma ta fasa tace " Allah ya rufa asiri to, ya amsa da " Amin ya Allah, suka kashe wayar, idon Ammi kanta tana jefawa Deeyanah kallan tuhuma tace " zo nan! Yadda kasan tana tafiya akan iska haka ta nufo inda Ammi while gabanta na wata irin muguwar fad'uwa k'afuwanta har  'yar rawa suke yi mata, tana zuwa ta zube gaban Ammi,  kunnenta ta rik'o ta murd'e sosai har dai da Deeyanah tayi k'ara ta runtse idanuwanta saboda zafin data ji, " fad'a kuka sake yi ko? Ammi ta tambaye, " wash kunne na. Ta fad'a kamar zatayi kuka, sassauta rik'on da tayiwa kunnen tayi tare da cewa " tambayarki nake yi baki bani amsa ba, "me kika ce Ammi ai banji ba, " nace fad'a kukayi? Murmushi Deeyanah tayi danta samu hanyar renawa Ammi hankali, idan bata nunawa Ammi fad'an sukayi ba da matsala gwara ta fad'a mata sunyi fad'a zaifi, " Ammi to ai lefinshi ne, "kinga koma meye ya had'aku ba saina ji ba, bana kuma san kowa yaji balle har wani ya samu damar shiga tsakaninku, duk duniya babu wanda ya kaiku kusanci da juna, nina haifi Deen amma koni ban kaiki kusanci dashi ba, dan yanzu kin fini saninshi, kin san abinda ni ban isa in sani ba, kece mace kece zakifi saurin bada k'ofa da b'arakar da wani zai shiga tsakaninku dan haka kiyaye shi aure d'an hak'uri ne sai a cuce ka amma dole kana ji kana gani kayi kamar baka sani ba, muma nan da kika gammu duk hak'uri muke yi ana b'ata mana muna shanyewa ke mace kullum kece a k'asa, cikin sanyi ta d'agawa Ammi kai tare da cewa " in sha Allahu zan kiyaye, Ammi tayi murmushi had'i da sakin kunnen. Duk abinda ke faruwa Ajlaal yana jinsu ta ware less earpiece d'in da Deeyanah ta sanya a kunnenta, dan matuk'ar basa tare da juna to suna manne da Bluetooth a kunnenta koyaushe suna aikin waya, " kaga dai Ammu ta fara zargin wani abu dole mud'an canja taku, dan ma Allah ya taimaka Ammi nada fahimta ai da abun ya k'ara cab'ewa, " kin ga kawai mu fito muyi musu bayani dama nina fara gajiya da wannan rayuwar b'oye-b'oyen da muke fa, idanuwanta waje ta zazzaro su tace " me zamu fad'a musu d'in? Kamar baya san yin magana yace " muna san junanmu mana, kina so na, kuma ke kanki shaida ce akan irin san da nake yi, so why not bazamu fito da soyayyarmu fili dan muci ribarta ba, meye amfanin soyayya idan babu aure? "Gaskiya ni dai a'a, a nutse kamar yana kallanta yace " meye a'a d'in Deeyanah? "Bakya so na ne, ko bazaki iya aure na ba? "Tab tashin hankali, ta fad'a tana fitar da numfashi kafin ta d'ora da "Ka rufa min asiri karma ka soma tunanin fito da maganar nan yanzu. "Hmmm naji to!, tace " yauwa, tana sauke numfashi, sai da ya gyara zama yace " yaushe zamuje gidan Aunty me kayan mata mu siyo ne, d'an shiru tayi kafin tace " ka bari sai nan da next week dan yanzu ma idan nace zan fita baza'a barni ba cewa za'ayi daga dawowata daga asibiti zan fara fita, " ok ba damuwa Allah ya kaimu. Shi ko Deen da tunani Ammi ta barshi, ya rasa meyake damun Deeyanah ya rasa dalilin sauyawarta da yawa haka, wasu lokutan yasha tambayar kanshi ko shine ya sauya ba ita ba, ko shine keda matsalar data sanya ta sauyawa dole, yasha bincikar kanshi ta fannoni da dama, yasha tambayar kanshi menene gazawarshi a matsayin miji ko uba amma ya rasa yana san ya sameta suyi magana face to face ta fahimta amma tak'i bashi dama balle lokaci, so da dama yana fahimtar idan ya kirata a waya tana amsa mishi a dak'ile kamar ma ya matsa mata shiyasa ya daina sai lokaci zuwa lokaci, Families sun sha tambayarshi yaushe zai dawo har ta kai ga sun fara matsa mishi kan ya dawo kusan kullum sai sunyi mishi maganar dawowa dai-dai da Deedee duk sanda zasuyi magana dashi sayya cewa " Daddy ka dawo Ina san ganinka I missed you, amma banda Deeyanah ko sau d'aya bata tab'a cewa ya dawo ba, bata tab'a nemanshi ba, bata tab'a cewa tayi kewarshi ko kewar wani abu nashi ba, ai ko irin maganganun sex da irin yadda tayi kewar sex da sauran su tayi mishi amma shiru, ganin tunanin bazai kai mishi ba ya sashi mik'ewa ya shiga bathroom ya d'auro alwala ya tada sallar mafila kasancewar su can tsakar dare ne. **************************************** Ajlaal da Deeyanah kam likkafa taci gaba dan har cikin Niger suke shiga neman maganin mata, sune Sokota, Zamfara, Katsina kai har Neja k'asar nufawa suke tsallakawa sai dai duk inda zasu je a jirgi suke zuwa dan basa kwana ranar suke zuwa su dawo ranar, babu abinda suka aje sai sex su dai ayi sex kawai aji dad'i, kullum suna manne da juna kamar cingam, sun yiwa junansu mummunan sabo da juna ta yadda ko bacci basa iyawa sai rungume da juna. Wannan kenan..... Cigaban Labari..... Ihuuun yara da taji akanta suna fad'in " mahaukaciya 'yar macukule! mahaukaciya 'yar macukule!! ya dawo da ita cikin hayyacinta tayi firgigit ta dawo daga duniyar tunanin rayuwarta ta baya data tsunduma, kafin tayi wani yunk'uri dutsen da d'aya daga cikin yaran ya jeho ya sauka a saman goshinta, take goshin ya fashe jini ya soma zuba, ta sanya hannu ta dafe wajen had'i da mik'ewa ta soma tafiya danta bar wajen, ta yanki daji danta nisanta kanta daga duniyar mutane, gwara ta shiga daji wani naman dajin ya cinye ta data rink'a ganin wulak'anci da kyama wajen mutane bil Adama 'yan uwanta, babu irin tozarci da wulak'anci gami da cin mutuncin da bata gani ba a rayuwarta ta duniya ba, ana cewa Wata Shari'ar sai a lahira ita kam taga tata sakamakon shari'ar tun a duniya, yau ita Deeyanah Abduljalal ce ta k'are haka, lalle rayuwa tayi mata gwatson kenwa, duniya tayi mata atishawar tsaki, tasan har yau bata gama girbar bak'ar shuka data tayi ba, tasan da sauranta dan baici ace ta gama girbar abinda ta shuka ba. Ta zama BAK'AR SHUKA... me fidda bak'in tsiro, bak'ar shuka d'an itaciyarta baya ciyuwa dan d'aci da bauri koka tauta saika furzar, ta zama bak'ar shuka da babu mahaluk'in da zai rab'e ta balle ya zauna a inuwarta, bak'ar shuka da babu me amfanarta, bak'ar shuka babu wanda zayyi marmarin irinta belle ya shuka.... Yuuuuu yaran suka bita suna yi mata ihuuun mahaukaciya 'yar macule wasu na jefanta da duwatsu wasu na d'ibar k'asa suna watsa mata, kwalla ta goge tana d'an gudu danta nisanta kanta da yaran, wani mutum dake tahowa ta hanyar data biyo ya k'araso wajen da hanzarinshi ya d'auki d'an icce ya kora yaran suka watse suna ihuuu, ya dawo inda take yace " sannu baiwar Allah, yayi maganar yana d'an ja baya cike da tsoron ko mahaukaciyar ce da gaske, yadda yayi yasata yin murmushi batare datace mishi komai ba ta wuce, wata irin dariya taji da gaba d'aya dajin sai da ya amsa kana aka ce " kin jawo mishi mutuwarshi Deeyanah, da sauri ta juyo sauke idon da zatayi taga mutum kwance shame-shame cikin jini,  ta d'an ja baya hawaye na zubo mata tace " banyi mishi magana ba, murmushi kawai nayi mishi. Dariyar aka sake yi a karo na biyu had'i cewa " murmushi fa kika ce Deeyanah? "Ai gwamma kiyi mishi magana sau dubu da kiyi mishi murmushi, ki ta jawa mutane mutuwa ni kuma nayi miki alk'awarin zanta kashe su kamar kiyashi, bazan tab'a gajiya da kashe su ba, hawayenta ta goge tana fad'in " ka cigaba da tsinke numfashin bayin Allah, Ubangiji yana madakata yana jiranka, shikenan ace mutum ko taimako na yayi saika ga bayanshi? "Ba dama a taimake ni ko a nuna tausayawa a gare ni? "Ai baki cancanci taimakon  kowa  da tausayawa daga wajen kowa ba Deeyanah, gwara ki azabtu kamar yadda kika azabtar da wasu bayin Allah, gwara kema ki d'and'ani abinda suka d'and'ana, muguwa, azzaluma, macuciya, mayaudariya Allah ya isa tsakanina dake kan lalata min rayuwar da kikayi, kin tarwatsa gobe na, kin lalata duniya da lahira ta, tayaya kike tsammanin zan barki ki rayu cikin salama da kwanciyar hankali? "Cikin matsanancin kuka tamkar ranta zai fita tace " naji nayi duk abinda ka fad'a, na aminta duk abinda ka fad'a gaskiya ne ban k'aryata ka ba, amma na baka hak'uri ai, na nemi yafiyarka, kuma kaima ai ka rama duk abinda nayi maka ka rama har ma ci riba sosai, dariya yayi yace " da saura dai yarinya ki jira duka-duka me akayi da maza? Zatayi magana ya juya mata baya yabar wajen tana kallanshi har ya b'ace, yau kwananta biyu kenan ko ruwa bata sha ba, yunwa ta gama kwak'uleta takai k'arshe ta yadda dakyar take iya jan k'afarta ta galabaita sosai, fasa shiga dajin tayi danta san idan ta shiga babu inda zata samu abinci, ta biyo titi tana tafiya tana had'a hanya kamar wacce tasha kwaya, a haka ta isa shagon me siyar da abinci, ta d'an tsaya nesa da rumfar me abincin tasan idan ta matsa korota zasuyi saboda tsananin warin da take yi, mutane maak'il da wajen amma babu wanda ya kula dasu ita da tarin al'majiran data iske a wajen, tana nan tsaye wani yaci abincin ya rage fiye da rabi, da gudu suka zuba ita al'majiren suna rige-rigen d'auka Allah ya bata sa'a ta d'auka, ta dumama hannu ta cika bakinta fall ta k'ara cika hannu ta tura, ta shak'e sosai amma ba halin ta tsaya dan idan ta sake ta tsaya wawashewa zasuyi su barta, haushin ta wawashe abincin yasa wani almajiri kwana mata robarshi aka, sauran almajirin suka saka wawa, daga ita harsu duk wawar suke, dakyar ta samu tayi loma uku, dayake almajirai ne basu damu da warin da take yi ba, itama bata damu da k'arzuwar dake jikinsu ba. Bata bar wajen ba sai dare aiko ta cika cikinta fall tasha ruwa ta juya zata bar wajen almajiran suka zagaye ta, dukkansu babu wanda ya haura shekaru goma sha uku zuwa sha hud'u, d'aya daga cikinsu ya d'aga robarshi ya sake kwad'a mata aka da k'arfi ya d'ora da " daga yau idan muka sake ganinki anan sai jikinki ya gaya miki, shegiya 'yar iska fice ki bamu waje kin zo duk kin wawashe mana abinci, ba musu ta juya tabar wajen batare data ce musu komai ba. Cikin makarantar Primary ta lallab'a ta shiga batare dame gadin makarantar ya ganta ba, cikin sand'a ta isa bakin famfo, ta zagaya ta samu tsohun bokiti duk ya fashe sai data karkata shi gefe kana ta samu ruwa ya zauna ciki, waigawa gaba da bayanta tayi taga babu kowa dan haka ta cire kayanta ta diddirzasu haka babu sabulu ta wankesu, ta sake tarar ruwan ta watsawa jikinta, ta wanke bakin, tayi walwala ta d'an jira kayan suka bushe ta mayar jikinta, d'aya daga cikin ajujuwan makarantar ta shiga tayi sallah ta kwanta, bata dad'e ba wahalallan bacci yayi awon gaba da ita, sai firgita take yi cikin baccin tana sauke ajiyar zuciya. Bata farka ba har garin Allah ya waye Allah ya taimaketa yau asabar da d'alibai sun cimmata, famfon ta koma tayi walwala tayi sallah kana ta sad'ad'a ta fice, hanya ta sake bi d'od'ar bata san inda take nufa ba, har azahar tayi, ta isa gefen wata me siyar da awara da dankalin hausa ta zauna daga d'an gefenta, har yamma tana zaune gefen me soya awarar, tausayinta ya kama yarinyar ta zuba awara biyar dankalin hausa biyar a leda da yaji da kabeji ta mik'a mata, jikin Deeyanah na rawa da tsuma ta mik'e ta amsa ta koma ta zauna ta cinye tas yarinyar ta sake mik'a mata ruwan sanyi ta amsa ta shanye ta yar da ledar tabar wajen tana tsoran tayi mata godiya ya kashe ta, yarinyar tabi bayanta da kallo cike da tausayawa, ganin yamma tayi kuma bata da wani wajen kwana yasa Deeyanah juyawa ta koma makarantar data kwana jiya. Yau ma tayi sa'a harta shiga tayi sallah ta kwanta babu wanda ya ganta, da safe bayan tayi sallah ta fito ta shiga neman abinci, dayake bata fiya shiga cikin gari sosai ba, tafi yin wajen gari, ta gangare daga kan titi tayi ta tafiya, tana cikin tafiya ta isa wani k'aton kango, wasu samari 'yan shaye-shaye  sun kai bakwai zaune kan bulalluka suna busa hayak'in wiwi. "Kai Goga kaga wata 'yar shila? "Tana ina? D'ayan ya tambaya, " duba ka gani ko idona ne ke gaya min k'arya, " ko kuma kasha da yawa tayi ma karo take gaya maka k'arya ba, wanda aka kira Goga ya fad'a ya k'ara ware idonshi yana kallan hanya, " kai banza ba nan ba, can zaka kalla, Goga ya fad'a yana juyar da kan Bahbah. " Kutuwar dumadu wallahi da gaske ne, kaga rabo na Minallahi tsuntsu daga sama gashashshe, dira sukayi daga kan bulan suka nufeta gaba d'ayansu, suka sanya ta a tsakiyarsu, tsaiwar ma na neman gagararsu dan sai faman layi suke yi su kad'ai, Bahbah yace " ke mutum ko Aljan? Banza tayi dasu dan babu d'igon tsoro a tattare da ita kwata-kwata, " ke daga ina zuwa ina? Goga ya fad'a yana layi kamar zai fad'i, banza ta sake yi dasu tare da rab'awa zata wuce ta gefensu, "ah! kai kaga wata cikekkiyar 'yar zarah, wai mu zata nunawa tsaiwar ido, d'auko mana ita taji nauyinmu Caku, wanda aka kira da Caku, ya nufeta dakyar yana had'a hanya idanuwanshi suna bud'ewa suna rufewa, yana isa gabanta ya durk'usa yana wawure-wawuren iska wai zai d'auko ta, ita abumma dariya ya bata, yadda taga yana tada k'ura wai zai d'auketa, " kai kaga shege fa, idan ance mishi ya rink'a shan abu dai-dai da kanshi yace kanshi yana ja zai iya d'aukar komai, ya k'arasa maganar yana isa gaban Deeyanah yana zuwa ya sab'eta yabar Bahbah anan yana tada k'ura. Ihuuu ta soma yi da k'arfi tana wutsil-wutsil da k'afarta, amma ko'a jikinsu suka shigar da ita cikin kangon ya kwantar da ita saman buhu ya raba k'afa akanta ya soma k'ok'arin cire wondonshi, " hau ka sauka ka bani, Bahbah ya fad'a yana k'arasowa wajen, "mu kuma duk muna nan muna kallanku ko? "Sai dai muyi mata rufdugu gaba d'ayanmu, d'aya cikinsu ya fad'a, zindir Gogo yayi had'i da rankwafuwa kanta yana niyyar saka mata jijiyarshi a jikinta, ihuuuun ta rink'a yi da k'arfi tana kai musu duka hannu bibbiyu, nan fa ta haukace musu da duka da ihuuu ta rink'a rarumar duwatse da k'asa tana watsa musu tana daga kwancen, " kai kutumar dumadu kaga yarinya da k'arfin hali, ke dan tsakiyar tsohonki ba taimaka miki zamuyi ba? "Naga ai bamu kad'ai ne zamu ji dad'in ba har dake kaga shegiya, kai ku turmushe min ita, gaba d'ayansu sukayi kanta, wani ya rufe mata baki sauran suka rink'e k'afarta da hannayenta, duk da hakan bata bari ba ta cigaba da motsi da jikinta tana d'ago mazaunanta, ganin hakan ba kai mata zayyi ba yasa ta gantsarawa wanda ya rufe mata baki cizo da k'arfin tsiya, ya janye hannunshi da sauri tare dayin k'ara, cikin azaba ya shiga yarfa hannun, "bura uba cizo, batayi tsammani ba sai jin saukar marika tayi a fuskarta, kafin ta gama dawowa hayyacinta ya saka k'afa ya take mata ciki da k'arfi cikin mugunta harda cije leb'enshi. Yadda kasan walk'iya haka k'afar tashi daya d'ora saman cikinta ta fita, daga shi da aka sarewa k'afar har sauran tsayawa sukayi suna kallan k'afar kafin daga baya ya saki mahaukacin ihuuun da duk ilahirin dajin sai da ya amsa, tsaye yayi kanshi duk'e rik'e da sharb'eb'iyar adda jini na d'aga, duk da a buge suke mankas sai da suka tsorata batare da sunyi magana ba suka juya zasu gudu, ya bisu da gudu, d'aya bayan d'aya sai da ya kashe su tasss suna ihuuun neman ceto amma a banza, sai da ya k'arar dasu tas, ya juya ya koma inda take kwance ta kasa tashi. Da hannu d'aya ya d'agota ya sab'ata a bayanshi, a wahalce tace " ka sauke ni please bazan bika ba, wutsil-wutsil ta soma tayi tana san ta dare while tana ihuuu, ganin haka yasashi sanya hannu a gefen wuyanta ya d'ana d'as, cikin abinda baifi seconds biyu zuwa uku ba jikinta ya saki sakwaf alamar ta suma, ya bud'e bayan motarshi ya kwantar da ita kana ya cire mask d'in da daya rufe fuskarshi da bak'ar rigar jikinshi da safar hannun ya watsa su a bayan motar, ya bud'e butt d'in motar ya saka addar a ciki kana ya shiga yaja motar yabar wajen. Bata farka ba sai da duhun dare yayi sosai da sauri ta mik'e ta ganta tsaye ita d'aya tal a tsakiyar daji ba gida gaba ba gida ba, cikin tashin hankali ta dafe kanta had'i da juyawa baya tana k'arewa inda take kallo, k'afa taja ta soma tafiya tana d'an gudu-gudu, sai da taci uwar tafiya takai ta kilo meter 30 kana ta isa makarantar da take kwana, cikin sand'a ta lallab'a ta shiga, alwala ta fara yi tayi sallah, yau ko addu'ar da take yi bata tsaya tayi ba bacci me nauyi yayi awon gaba da ita. Sama-sama cikin baccin ta rink'a jin ihunn yara, a hankali ta bud'e idonta, yara d'alibai ta gani cunkus a kanta, da sauri ta mik'e tana bud'e idonta tar baya d'aliban suka soma ja cikin tsoro suna ihuuu, hakan ya jawo hankalin Malaman makarantar sukayo wajen, duk cikinsu babu wanda yayi gigin k'arasawa inda take dan a zatonsu mahaukaciya ce, d'aya daga cikin Malaman ya kwalawa me gadi kira da k'arfi, ya k'araso wajen da gudu hannunshi rik'e da zabgegiyar dorina, cikin fad'a da masifa Head Master makarantar yace " kana can kana sakarcin banza ka bar mahaukaciya ta shigo mana makaranta, k'asa yayi da kanshi cikin girmamawa yace " ayi hak'uri wallahi ban sani ba, "dama ta yaya za'ayi ka sani? "Dalla fitar mana da ita, kafin ya k'arasa rufe bakinshi ya shinfid'awa Deeyanah dorina a gadon baya, zafin dukanne yasata firgicewa ta fita daga hayyacinta, k'ara zuba mata yayi da k'arfi, har sai da tayi ihuuu sosai, ta fita da gudu ya bita yana duka yara suka rufa musu baya suna ihuuu. Suna b'acewa mutane ya bayyana a gaban me gadin, cikin matsanancin kuka soma girgiza kanta tana fad'in " a'a please! ka kyale shi, dan Allah karka yi mishi komai please dan...., bata k'arasa fad'ar abinda tayi niyya ba ya cakawa mutumin wuk'a a mak'ogwaro ya tsarga wuyanshi biyu, me gadin ya fad'i k'asa timmm, durk'ushewa tayi k'asa had'i da fasa rikitaccen kuka tana fad'in " na shiga uku, wayyo ni kaina wayyo ni Allah, kaico na, meye amfanin irin wannan rayuwar tawa? "Meye amfanin haihuwa ta da iyaye na sukayi? "Na zama bala'i a doron k'asa na zama silar mutuwar mutane bayin Allah da bazasu irgu ba, na zama masifa kuma annoba a cikin al umma, mik'ewa ta sake yi tsaye fuskarta cike taf da hawaye ta had'e hannayenta biyu waje d'aya tace " dan girman Allah, dan zatin Allah, dan darajar fiyayyan halitta ka kashe ni nima na huta please. Sai da yayi gajeriyar dariya kana yace " in mutuwar kike so ke meyasa bazaki kashe kanki ba ko sai ni kike san na kashe ki? "Ai kin fini sanin hanyoyin da zaki bi in mutuwar kike so da gaske, aina fad'a miki sai kin gwammaci mutuwa sau dubu Deeyanah, na fad'a miki saina lalata rayuwarki, zatayi magana ya d'aga mata hannu had'i da cewa " kije ki mutun mana waya hana ki? Hawayenta ta goge da bayan hannunta ta soma tafiya tabarshi nan tsaye batare data sake cewa komai ba, gefen wani kango ta samu ta zauna a k'asa, saurin kallan kanta tayi cikin mamaki, bakinta bud'e tace " kodai bani bace an canja ni? Ta fad'a tana bin kayan jikinta da kallo, an canja mata kayan jikinta ba wad'anda take sanye dasu bane, yanzu doguwar riga ce bak'a a jikinta an d'aura mata mayafin doguwar rigar a kanta, an yanke mata farcenta duka na k'afa dana hannu, saurin janye d'an kwallin kanta tayi ta shafa gashin kanta, shima an wanke mata shi tas an taje mata shi an gyara yaji man gashi, sai lokacin ta tuno jiya da zatayi alwala dataje tsarki taji wajen sub'ul wato har shaving aka yi mata, tashin hankali da rashin nutsuwar data ke ciki ne ya hana ta fahimtar komai har canjin kayan jikinta, wato jiya daya d'auketa abinda yayi mata kenan. Dariya ta saka harda tafa hannu tana fad'in " habawa bani bace, dama nasan bani ce Deeyanah dana sani ba, tana dariyar ta fashe da kuka mai cin rai, ta dad'e nan zaune tana kukan kafin ta rarrashi kanta da kanta ta bawa kanta hak'uri ta goge hawayenta, ta d'an kishingid'a, rayuwarta ta baya ta shiga tunanowa da irin abubuwan da suka faru da ita. Waiwaye..... Siririn bak'in gilashin dake kan kyakkyawar fuskarshi ya cire, ya d'aga kanshi ya kalli sararin samaniya had'i da shak'ar iska da d'an k'arfi, a hankali cikin nutsuwa ya soma taka matattakalar jirgin yana sauka k'asa, cikin ranshi yana jin sanyin dad'i na ratsashi, daga wani b'angare na zuciyarshi tsoro na baibayeshi, bai san dalilin jin tsoron ba, amma yasan bazan wuce akan sab'anin da suka samu da Deeyanah ba daren jiya ba, yana fita daga harabar Airport d'in ya hangi su Azaan tsaye suna jiranshi, fuskarshi d'auke da bayyanan nan murmushi ya nufe su, caraf yaji an rik'e shi " Daddy sannu da zuwa, Deedee ya fad'a yana dariya, fad'ad'a fara'ar fuskarshi yayi ya sunkuya ya d'auke shi gami da jefa shi sama ya cab'e yana dariya. "Nayi farin cikin ganinka My Son, Deedee yayiwa Deen kiss a kumatu yana dariya yace " meka kawo min Daddy? "Da wuri haka? "Aika bari na isa gida na huta ko? Yayi mamakin rashin zuwan Deeyanah tararshi Airport har ya kasa hak'uri yace " Deeyanah bata zo bane? "Inaga aiki take yi, danayi mata magana cewa tayi muje kawai, shiru kawai yayi bayyi magana ba dan bashi da abin cewa, Har suka isa gida Deedee yana rungume jikin Deen yana zuba mishi surutu wasu ya gane ya bashi amsa wasu kuma sai da ya bishi da un! u'u, yana d'auke dashi ya fito daga motar, ya nufi inda su Abbi da Babah suke tsaitsaye suna ta murmushi, cikin girmamawa ya durk'usa ya gaidasu suka amsa cike da fara, Abbi ya d'ora da " an dawo lafiya? "Alhamdulillah yace yana dariya, cikin zolaya Babah yace " irin wannan dogon yaji haka? "Bamu mukayi laifi ba amma harda mu a karb'ar hukunci, cike da jin kunya ya shafa kanshi, wajen su Ammu da Ammi ya shiga gaidasu, kana ya shiga part d'inshi, tasha kwalliya duk da bamai yawa bace, simple make up tayi, jikinta sanye da doguwar rigar bubu ta leshi, ta kashe d'aurin d'an kwalli, fuskarta d'auke da yalwataccen murmushi ta mik'e ta tare shi, " sannu da zuwa me gida ran gida, 'yar hararar wasa ya jefa mata yana mik'a mata jakar hannunshi yace " ai kece me gidan yanzu dan kin zama hukuma sai rarrashi, " wace ni ranka ya dad'e, ta fad'a tana shigar da jikinta cikin jikinshi, hannunshi ya saka ya rungume ta tsam yana mayar da numfashi, a wahalce yace " nayi kewarki sosai k'aunata. Dariya tayi ta d'an zame jikinta daga nashi, yayi saurin mayar da ita jikinshi yana fad'in " ki barni a haka na samu nutsuwar dana gaza samu tsayin lokaci, murmushi tayi me zurfi dayasa side dimples d'inta lotsawa ta zame jikinta daga nashi a hankali tana fad'in " kayi wanka kaci abinci ka huta tukunna, ta k'arasa maganar tana barin wajen, yayi saurin bin bayanta, a tsakiyar d'akin ya cimma ta, ya mik'a hannu ya jawota jikinshi ya mannata da k'irjinshi had'i da jan dogon siririn hancinta ya jefa idonshi cikin nata yana kallanta eyeball to eyeball, wani irin shu'umin kallo da murmushi ta jefa mishi mai narkar da mutum, " Ya Allah! Yace yana lumshe idonshi, ya bud'e idon ya sake kallanta, irin kallan nan nan k'asan ido yace " kina neman zauta ni Deeyanah. Dariya ta sanya harda rufe baki tace " ko kuma mu zauta juna ba, zayyi magana ta sanya hannunta a k'irjinshi ta tura shi baya in a romantic way har ta kaishi cikin bathroom tace " Yallab'ai ka fara yin wanka, ta juya zata bar wajen ya rik'o k'ugunta, ya dawo da ita suka fuskanci juna yace " ki bari nayi wankan me dalili mana, ya k'arasa maganar had'i da kashe mata ido d'aya, sai da k'irjinta ya kusa fad'owa saboda tsabar tsoratar da tayi danta gane abinda yake nufi, tasan dama dole sai haka ta faru tun da shi ba k'arfe bane, da ranshi da lafiyarshi dole zai buk'aci mace a tsayin lokacin nan, kashe din Ajlaal ya fad'o mata. "Ba Deen kad'ai ba Deeyanah, wallahi zan iya k'arar da duniya akanki, ba Ina nufin iya ahalinki kad'ai ba, ina nufin kowa dake cikin duniya, kinga har da nawa iyayen da ahalin duk suna ciki, ki kula sosai in ba haka ba zaki jawo yak'in duniya na k'arshe, dan a yadda nake jina nafi hitila bala'i, daga ranar da kika sallamawa Deen kanki kika bashi kanki wallahi kowa ya tsaya mishi bai k'ara kwana duniya. Cikin kuka tace " haha Ajlaal shifa mijina ne, sadaki na ya biya fa, ai da tausayin rai duk wannan lokacin bai kusanci matarshi ta sunna ba ina kake san yakai buk'atarshi? "Ina kake san yaje ya zazzage wutar sha'awar dake addabarshi? "Ko so kake yi shima ya fad'a halaka kamar yadda muka fad'a? Kafad'a ya d'age irin ko'a jikinshi d'in nan yace " shi yasan inda zai kai ta, kuma da kike cewa mijinki ne, sadaki ya biya, ni so nawa nace miki ki bani dama na zama mijin naki na biya sadakin naki amma kika k'i? "Wai ka hauka ce ne Ajlaal? "Hauka kake yi kome da kake cewa na aure ka, ina ka tab'a ganin anyi aure akan aure? " Eh! Ina hauka Deeyanah, na hauka ce akanki sanki, ya fad'a cikin hargowa ya d'ora da " idan kin haramta abinda Allah ya halatta a tsakaninmu ai gashi nan kin halatta mana abinda Allah ya haramta mana, cikin mamaki hawaye nabin fuskarta tace " mena halatta mana d'in? "Zina Deeyanah, kin hana muyi aure amma gashi kin bari munata zina, " duk abinda zaka ce kaje kace amma saina bawa Deen kaina, a haukace ya damk'o gashin kanta, idanunshi duk sun firfito waje saboda bala'i, bakinshi har kumfa yake yace " kije ki bashi kan naki, amma wallahi ki sani kafin alfijir ya keto na k'arar da duk mahaluk'in dake cikin estate d'in nan, " so kake ya fara zargin akwai wani abu? "Ko so kake yi ya fara zargina? "Idan ban bashi kaina ba dole zayyi zargin wani abu dole zai saka ayoyin tambaya a kaina. "Ya dad'e bai zarge kin ba, k'ark'ari dai yace zai sake ki, to ni Ina maraba da haka dan abinda na dad'e ina jira ne, kuma yaje duk uwar da zayyi yayi. Iska Deen ya hura mata a fuska had'i da d'an girgiza kafad'unta yace " hello where are you? "Ina kika tafi ne? Yawu ta had'iya ba shiri, ta kalleshi had'i da goge gumin daya soma tsatstsafo mata a goshi ta k'ak'aro murmushin yak'e tace " am am dama girki, na d'ora ne, ta fad'a kamar me koyon magana, kafin yayi magana ta juya ta fice da sauri, zama tayi akan kujera tana mayar da numfashi, hannunta na rawa ta d'auki rogowar ruwan data aje tasha kad'an ta mayar ta aje, numfashi ta sake fitarwa da k'arfi had'i da dafe goshinta tana tunanin ta ina zata b'ullowa wannan al'amarin, tana nan zaune tana shawarwari ya fito d'aure da towel a k'ugunshi, saurin mik'ewa tayi bakinta na rawa muryarta na hard'ewa tace " am.....am...am, ido ya kafe ta dashi batare datace komai ba. Ganin maganar tak'i fitowa yasata saurin barin wajen ta shiga kitchen babu abinda zata d'auka a cikin fridge amma ta bud'e fridge d'in, tana jin takunshi na nufo ta ta runtse idonta da k'arfi, sai da ya kusa k'arasowa gaf da ita tayi saurin barin wajen ta fice gaba d'aya daga cikin kitchen d'in, sake bin bayanta yayi tana tsaye jikin dinning while deep down duk ilahirin jikinta kerrrrma yake yi, yadda kasan ta fasa ihuu haka take ji, cikin nutsuwa ya k'araso inda take tsaye, ya d'ora hannunshi saman kafad'arta ta runtse idonta da k'arfi, a hankali ya zaunar da ita kan kujerar dinning d'in kana ya d'auki ragowar ruwan data aje ya mik'a mata, ba musu ta amshi ruwan ta shanye tas ta aje kofin, sai da ya bari tad'an nutsu kana yace " muje ki bani kaya in saka. Ba musu ta mik'e tayi gaba ya bita a baya, jallabiya ta d'auko mishi ta fesheta da turare, kana ta mik'e mishi, kin karb'a yayi ya fara d'aukar steps zai had'e tazarar dake tsakaninsu, a shab'e yace " baki shafa min mai ba, jikinta na tsuma saboda yadda ya matseta da jikinshi sosai ta juya zata d'auko lotion d'in Nivea na maza yayi caraf ya rik'e hannunta, tsallen da zuciyarta tayi ne ya haifar mata da kwarewa, ya k'ara matseta sosai yana shinshinar wuyanta cikin raunananniyar murya yace " I missed you. Hannunshi ya sanya ya zame d'an kwallin kanta had'i da tura hannunshi cikin kwantaccen gashin kanta ya soma yamutsawa ya d'ago kanta zai had'e bakinsu tayi saurin zame jikinta tabar wajen ta barshi nan tsaye, " sallar magriba ta kusa muci abinci muyi sallah tukunna, batayi zaton ya biyo ta ba, sai jin bakinshi tayi cikin kunnenta yana fad'in " zamuyi sallar daga baya amma mu fara kawar da k'ishirwar mu, ya k'arasa maganar yana sauke mata numfashi cikin kunne, a hankali ya zura harshenshi cikin kunnenta gami da zagayo da hannunshi zai damk'i boobs d'inta, cikin firgici ta durk'usa k'asa tana k'ak'aro dariyar dole tace " tab wallahi yunwa nake ji, ya nufo ta tayi saurin ficewa daga d'akin tana fad'in " ka saka rigar ka fito muci abinci please, tun safe babu abinda nake na tsaya jiranka, bayanta yabi da kallo yana murmushi tare da cije lips d'inshi na k'asa. Da sauri da sauri take fitar da numfashi kamar wacce tayi gasar tseran gudu, in banda gumi babu abinda ke tsatstsafo mata, hawaye ne suka soma zubo mata wasu na bin wasu, duk inda ake kaiwa wajen shiga tashin hankali ta shiga yau, ga abin gudu ba wajen zuwa, kanta da dafe da duka hannayenta tana maimaita Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un cikin ranta, jin motsi yasata saurin mik'ewa zunbur ta soma bubbud'a food warmers d'in, saboda tsabar tashin hankali ta manta ma abincin yana kan wuta bata kwashe ba, da sauri ta shiga kitchen d'in ta kwashe farar shinkafar dataji kayan lambu a kula harma ta soma kamawa, zaune ta iske shi akan dinning yana tsiyaya sob'o a glass cup yabi ta da kallan sha'awa yana fad'in " na fito a daina jira na. Murmushi tayi batare data ce komai ba, ta zuba musu shinkafar a plate ta zuba musu coleslaw a gefe ta bud'e kular miyar nan fa k'amshi ya cika ko'ina, duk wani nau'in halaltaccen nama akwaishi a miyar, naman rago, gandar saniya, tumbi, kaza ga miyar ta soyu gwanin ban sha'awa, ta zuba musu miyar kana ta sake tsiyaya musu had'in sob'on da akayi babu d'igon ruwa saina kankana da abarba, sosai ya zage yaci abincin yana ta zuba santi, ita ko tsoro da fargaba sun hanata ci sosai, wani d'aci-d'aci ma taji abincin yana yi mata a baki, haka taita jan lokaci har aka kira sallar magriba, a fili ta sauke ajiyar zuciya dan tasan inya fita bazai dawo ba sai anyi sallar ishaa, yadda ta sauke ajiyar zuciyar yasashi kallanta tare cewa " yadai? "Bakomai, tace tana danne abin da ke taso mata, ta mik'e zata bar wajen yace " duk ikirarin yunwar da ake ta cewa ana ji iyakarta kenan? Bata tsaya ba tana cigaba da tafiya tace " sallah zanyi na dawo na cigaba da d'iba, bayyi magana ba ya mik'e bai bita d'akinta ba ya wuce d'akinshi da hanzari ya k'arasa alwalar ya fita dan yaji har liman ya shiga, tana jin fitarshi ta sauke ajiyar zuciya zuciya had'i da fad'awa kan gado ta saki kuka, tana jin wayarta na motsi amma tayi banza da wayar danta san ko waye, sai da tayi me isarta kana ta mik'e ta shiga ban d'aki ta d'auro alwala ta fito ta tada, bata tashi daga kan sallayar ba tana lazimi har aka kira sallar ishaa, ta mik'e tayi sallar bata tsaya yin addu'a ba tayi saurin ficewa daga part d'in su dan kar dawo ya same ta, part d'in Ammi ta shige ta iske ta zaune kan sallah tana jan carbi, ganin Deeyanah yasata tak'aita addu'ar, suna hira har tara sai ga Deen ya shigo, tana ganinshi ta soma gyangyad'in k'arya, zama shima yayi suka d'an tab'a hirar da Ammi har goma tayi, ganin irin kallan da yake yiwa Deeyanah suna hirar amma gaba d'aya hankalinshi na kanta, sai zungurinta yake yi ta k'asa da k'afa yasa Ammi cewa " tashi kuje sai da safe. Dole badan taso ba ta mik'e yayi saurin ficewa tabi bayanshi, Ammi tabi bayansu da kallo tana murmushi, tsayawa yayi wajen Azrah daya gani tsaye, tayi saurin shigewa gidan tayi amfani da wannan damar tana zuwa ta baje saman bed, kafin yazo ta hau baccin k'arya, daya dawo yayi mata tashin duniya amma tak'i tashi wai ita tayi bacci, "yanzu fa kika shiga ko minti biyar ba'ayi ba amma har kinyi nisa a bacci kuma a sanin danayi miki ai baki da nauyin bacci haka? Ganin bata da niyyar tashi yasa shi d'ago ta yana fad'in " haba kusan shekara biyu bamuyi sex ba amma bakya ko d'okina? "Ke in zaki iya jurewa ni nakai k'arshen mak'ura ya fad'a yana had'e bakinsu, da iya k'arfinta ta rufe bakin tak'i bashi damar da zai sha bakinta, murmushi yayi had'i da kwantar da ita batare daya sake yin yunk'urin wani abu ba ya fice daga d'akin, dakyar ya iya kai kanshi d'akin shi saboda wata irin muguwar sha'awa dake cinshi, yana shiga bedroom d'inshi ya wuce bathroom had'i da sakarwa kanshi shower ya dad'e ruwan na sauka kanshi kafin ya samu wutar dake ruruwa a jikinshi ta mutu, dakyar ya rarrafa ya cire kayanshi ya zube saman bed. Ita ko yana fita ta mik'e zata dannawa k'ofar key Ajlaal ya turo k'ofar ya shigo rolling idanuwanta tayi had'i da cewa " me kazo yi kuma? "Raya sunna, ya rad'a mata a kunnenta yana dariya, dariyar itama tayi ta juya ta koma kan gadon, ya bita yana cewa " ah irin wannan kwalliya haka da akayi mishi? Dariya tayi sosai gami da cewa " sarkin kishi, ya zauna kusa da ita had'i da sanya hannu ya d'ago hab'arta ya zuba mata ido yana kallan kwayar idonta, sun d'auki lokaci a haka sannan ya had'e bakinsu suka soma aikawa juna deep kiss had'i da tsotsar lips d'in junansu, cikin salon gwarewa da iya sarrafa mace ya zame rigar jikinta k'asa ya soma sarrafa ta yana rud'a mata jikinta da sak'unanshi masu wuyar mantawa, a rikice ta soma mayar mishi da martani ta fara rikita mishi lissafi had'i da mantar dashi zahirin duniyar da yake, cikin k'ank'anin lokaci suka gama rikita junansu, suka birkita komai dake kan gadon duk wani pillow sai da aka wullo shi k'asa abu ya d'auki zafi iya zafi kana komai ya wakana basu sararawa juna ba sai wajen asuba, suka zube saman gadon suna mayar da numfashi, shi kam Deen kwana yayi cur bai runtsa ba yana ta faman murk'ususu yana juyi saboda sha'awa, ya mik'e zaije d'akinta yafi sau goma amma bai san meke hanashi zuwan ba, sai wajejen asuba wahalallan bacci yayi awon gaba dana shi. Bai farka ba sai wajejen sha d'aya na safe wani masifaffen ciwon ciki ya farkar dashi a daddafe ya fito daga d'akin daga shi sai bedsheet d'in daya rufa ya jawo ya d'aura ya fito dashi, tana tsaye daga ita sai rigar bacci iya gwiwa ko d'an kwalli babu akanta ta tufke gashin kanta da ribon, tana jera abinci a dinning Deedee na zaune yana ta faman zuba mata surutu Deen ya fito, bai ma kula da Deedee ba, bai san yadda akayi ba sai ganinshi yayi kusa da ita, tun da take dashi a iya tsayin rayuwar da sukayi tare bata tab'a ganinshi cikin irin wannan yanayin ba, wani irin mugun tsoro ne ya kamata ta saki kofin glass d'in hannunta, kafin tayi wani yunk'uri ya damk'eta ya had'e bakinsu, wani irin kiss yake yi mata da k'arfi har zafi-zafi take ji, bazai iya tsayawa long romance ba, dan haka ya sab'ule hannun rigar jikinta ta fad'i k'asa, dakyar ta iya had'a kalmomin bakinta tace " Deedee..!, ido ya soma rabawa yana duba inda yaron yake, zaune ya ganshi kan kujera ya saki baki yana kallan ikon Allah. A tsawace cikin hargowa Deen ya daka mishi tsawa " tashi ka fita, jikin yaran na rawa ya mik'e ya fice saboda tsoratar da yayi a bud'e yabar k'ofar da gudu ya shiga part d'in Ammu, tare da Ammi ya same su tsaye a kitchen suna aiki, " Ammi ga Daddy can yana cirewa Momy kaya, shima ya cire kayan jikinshi shine ya koro ni, kallan juna sukayi ita da Ammi, Ammu taja tsaki tana fad'in " yaran yanzu sai a barsu, koma wanne uzurin ne ya kamasu su kasa hak'uri a gaban d'ansu fisabilillahi? Ammi tayi murmushi tare da durk'usawa ga Deedee tace " laifi tayi mishi shine zai zane ta, kaima idan ka sake ka fad'awa wani abinda ya faru irin abinda yayiwa Momynka shi zayyi maka, a tsorace ya girgiza kanshi yana cewa " babu wanda zan gayawa, " yauwa good boy, Ammi ta fad'a tana shafa kanshi, Ammu ta sake jan dogon tsaki a karo na biyu cikin jin haushi tayi kwafa batare data ce komai ba, Ammi tayi dariya tana fad'in " ke karki matsawa yara na, barsu suyi lokacinsu ne, ke meye bakuyi ba a lokacinku, Ammu tayi dariya batare datace komai ba. Deedee na fita ya sake had'e bakinsu har wani sake danno kanta yake yi ta baya da hannunshi, ya zagayo da hannunshi kan boobs d'inta ya soma mammatsa su, cak ya d'auke ta ya rabata da k'asa ya dawo cikin falo da ita ya jefa ta saman sofa 3 sitter ya bita ya danne, a gaggauce ya cigaba da romancing d'inta, ita kam in banda bugu babu abinda k'irjinta keyi, a hankali ta soma k'ok'arin janye jikinta daga nashi, ai yadda kasan zata rabashi da ranshi, ya sanya k'irjinshi ya danne ta sosai ta yadda ko kwakkwaran motsi bazata iya ba, tayi-tayi ta kwace kanta amma ta kasa, idonta ta runtse da k'arfi had'i da tattaro daga d'aya k'arfinta ta tura shi, tayi saurin tashi zaune tare da kifa kanta kan tafin hannayenta tana mayar da numfashi. Da sauri ya tashi ya kuma nufarta tayi saurin mik'ewa had'i da dakatar dashi ta hanyar d'aga mishi hannu tana hakki tace " ba....ba...bana... sallah, ina period ne, d'an dakawa yayi gami da tsare ta da shanyayyun idanuwanshi da suka rikid'e suka koma kamar na mashaya, sai da ya furzar da iska daga bakinshi kana yace " da idan kina period haka kike yi min idan ina cikin mood? "Naga kin san duk hanyar da zaki bi ki saka ni na samu nutsuwa, yayi magana yana tsareta da ido yayinda acan k'asan zuciyarshi kokawa yake da zuciyar dan karta sak'a mishi mugun abun da take san sak'a mishi akanta, leb'enta na k'asa ta d'an lasa gami da sanya hannu ta mayar da gashin kanta daya bazo mata, tana san tayi magana amma idonshi dake kanta ya hanata bata damar yin maganar. Cikin suyar k'irji yace " haka kika yi tayi min wan can karon har na gaji nayi zuciya na barki da abunki, yanzu ma gashi kin kuma, anya Deeyanah babu wani abu da kike b'oyewa, shekara kusan biyu fa bamuyi sex ba, and shekara d'aya da rabi bama tare baki ganni ba ban ganki ba, bakiji d'umin jikina ba ban ji d'umin jikinki ba, amma ace dana dawo ko marmarima da d'orina bakiyi? "Dana tafi America ko sau d'aya tak baki tab'a kira na kince min sha'awa na damunki ko you're in the mood ba, baki tab'a kira na video call ba, ke bama ki bani time & attention d'inki ba, babu wata kula da kika bani har naje na dawo a matsayi na mijinki, dana dawo maimakon ma ace kece ke rushing in to sex amma kece ke denied, why Deeyanah? "Ina sha'awarki take tafiya? "Wake gusar miki da ita Deeyanah? "Anya bakya neman maza da aure na akanki!? "Wad'annan sune tambayoyin da ke san na rink'a yiwa kaina har zarginki ya shiga raina auren mu ya haramta? "Ko ko kin d'auki aure abin wasa da sai lokacin da kike da buk'atar koma meye za'ayi? "Bana san na zarge ki, please karki tilastawa zuciya ta zarginki dan hakan bazai tab'a haifar mana d'a me ido ba, dan Allah karki tursasa ni na shiga zarginki, daga ni har ke bazamu ji dad'in abun ba, gwara tun wuri ki nemarwa kanki mafita, imma wasu k'awayen kikayi suke neman hure miki kunne gwara ma tun wuri tun kan dare yayi miki ki canja tunani, har ya juya zai bar wajen ya juyo ya sake jefa idonshi cikin nata yana kallan kwayar idonta ya nuna mata d'an yatsa yace " duk abinda zakiyi kije kiyi ta yinshi zan iya jurewa, amma middin kika sake kika ci amanata, ya cije lips d'inshi na k'asa. "Dan bai yiwa ni ina d'a namiji da duk kalar iskancin da zanyi dan iya yinshi ba aure ne akaina ba ko duniyar ce akaina zan iya aikata koma meye amma na kame kai na, ke da kike mace a k'ark'ashin ikona sannan ke keyin abinda kike so, wallahi Wallahi tallahi na rantse miki da girman Allah kika sake na kamaki da cin amanata saina barki har abada koda kece autar matan duniya, koda hakan yana nufin bazan k'ara aure ba har a nad'e k'asa, k'asa-k'asa yayi da muryarshi yace " wallahi koda hakan yana nufin mutuwa ta, kuma zan tsane ki tsana ta har abada, Deeyanah bazaki sake gani na ba a iya tsayin rayuwar da zamuyi a duniya, yana kaiwa nan ya juya ya barta nan tsaye. In banda rawa babu abinda jikinta keyi, duk da sanyin ac dake d'akin bai hanata yin gumi ba, mak'ogwaronta ya bushe har wani d'aci-d'aci yake mata yayinda da zuciyarta da k'irjinta ke luguden bugu, ji take yi kamar ana d'agata sama ana bugawa da k'asa, idonta yaji yake yi mata sosai saboda tsantsar tashin hankali, jikinta a sanyaye ta zame ta zauna kan kujerar dake bayanta had'i da cusa yatsunta duka goman cikin gashin kanta, bata san sanda ta saki kuka me k'una da soya zuciya ba, kukan dake fitowa daga can k'asan zuciyarta, ta rasa yadda zatayi, ta rasa mafita gaba d'aya kanta ya gama kullewa b'am, wannan wacce irin bak'ar rayuwa ce? In banda na shiga uku, babu abinda take fad'a, ta durk'ushe nan wajen taita rusa kuka wiwi. Shi kam a b'angaren shi yana shiga bedroom d'inshi ya zube saman bed rigingine idonshi kan roping, tunanin daya fara zuwa kanshi shine koyaje ya sanar da iyaynsu halin da ake ciki? Kanshi ya girgiza had'i da furta " ni! nakai k'arar mace saboda sex Allah ya kiyaye? Har yamma tayi yana nan kwance yama rasa tunanin da zayyi, ko sallar azahar bayyi ba, " kodai wani ta samu wanda ya fini iya sex? Ya furta a hankali, da sauri yace " Astagfirullah, ya yana k'ok'arin cire zargin daga ranshi amma sai me daram zargin ya zauna mishi, yayi-yayi ya kawar da tunanin cikin kanshi amma ya kasa, " to idan ba wani ta samu ba ya akayi take iya controlling feelings d'inta? "Me yasa tunda na tafi har na dawo bata neme ni ba? "Meyasa bata yi min dirty talks kamar a baya when he's not at home? Duk yadda Deen yaso kar ya zargi Deeyanah amma abun ya gagareshi, yayi iya yinshi yayi kokowa da zuciyarshi da tunaninshi amma abun yafi k'arfinshi, dole ya yarda ya amince da cewar akwai wani a rayuwar Deeyanah bayanshi, zambur ya mik'e zaune had'i da dafe kanshi dake barazanar tarwatsewa, a jikinshi yake jin duk wani noti dake jikinshi yana kuncewa, wani abu yaji yana fita daga zuciyarshi da wani irin k'arfi, take yaji ya fara tsanarta tsananin kyankyaminta na shigarshi, a hankali ya fara d'an marin kanshi yana fad'in " a'a Deen wannan tunanin banza ne da aikin shaid'an la'anannen Allah, wani irin k'aramin hoto zuciyarshi ta hango mishi na Deeyanah da wani, ai bai san sanda ya mik'e tsaye ba, kawai sai tsintar kanshi yayi yana tafiya. "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, ya shiga maimaitawa deep down yana jin wani mugun tsoro na shigarshi, " dole na sakawa Deeyanah ido, dole na binciko abinda take b'oyewa, dole na rink'a bin diddiginta kodan karta kai ni wuta, ya fad'a a zahiri yana rik'e k'ugunshi, duk yadda yayi iya yinshi dan kar ya zargeta abun ya ci tura sai da zargin Deeyanah ya shiga ranshi. ************************************* Yana zaune a falo ta fito hannunta rik'e da hand bag d'inta while kunnenta manne da bluetooth, tunda abun ya faru bata sake bari sun had'u da juna ba, bata san meyasa take mugun jin tsoranshi da kuma kunyarshi yanzu ba, ko ido bata san su had'a, kanta k'asa tace " ina kwana, an tashi lafiya? "Sai da ya d'auki lokaci kamar bazai amsa ba, kana ya amsa da " Alhamdulillah, tana kallan gefe dan bata san su had'a ido tace " dama saloon zani. "Da da kika shirya zaki tafi kin tambaye ni ? “ba gaban kanki kikayi ba? "Ko kuma da can da kike fita yawonki da izini na kike fita? "Ko sai yanzu dan kin ganni a zaune shine kika tambaye ni? Kanta k'asa cikin sanyin murya tace " ba haka bane dama niya nayi idan na fito sai na tambayeka, da har zaice ta koma sai kuma wani tunani yazo kanshi, " sai kin dawo, ya fad'a tak'aice, kamar wacce aka hankad'a, tayi wuf tabar wajen. "Kai gaskiya kina fama, dama har yanzu halin miskilancin Deen yana nan? Ajlaal dake kan waya ya fad'a, " hmmmm haka yake har yanzu babu abinda ya canja ga bak'ar zuciya kamar ta fir'auna, wallahi zuciyar Deen da a kafiri yazo ban jin bai karb'i musulunci, ta fad'a tana yiwa motar key ta fice daga gidan, sosai Ajlal ya saka dariya har da neman gwarewa, " uhmmmm wato an tab'o maka inda yake maka ciwo an kushe mak'iyinka ko? Yana k'ok'arin tsaida dariyar yace " a'a ba haka bane, gani nayi keda kanki kika fad'a, "yanzu dai duk ba wannan ba, meye first sex ko abinci ? “Dan yunwa nake ji ban karya ba. " Sex ne farko amma tunda kina jin yunwa bari na saka kuku ya dafa miki wani abun ko nayi miki order, dan idan kina jin yunwa bazan samu biyan buk'ata ba gwara na fara ciyar dake kici kiyi fam kafin a soma harka zaki fi bani joy ma. Murmushi tayi me kama da dariya ta bud'e baki zatayi magana ya zabura had'i da cewa " what? “Menene? Ta tambaye shi, k’ara ware idonshi yayi sosai tare da cewa. "Kin san me kuwa? Hankalinta kwance tace "a'a, " wallahi Deen yana binki a baya, wani irin mahaukacin birki ta taka a tsakiyar titi k'uuuuuu saura kad'an ta had'a mummunan had'ari " me kace? "Deen na bina ko me kace? Tayi maganar cikin tashin hankali. "Wallahi yana binki gashi nan a bayanki yana bin motarki, in slowly ta lek'a ta windo, aiko ta hangoshi ya samu waje nesa da ita yayi parking saboda ta tsaya, wata irin muguwar tsuma jikinta ya d'auka har hak'oranta na had'uwa kafkafkaf, " na shiga uku Ajlaal, shikenan Deen ya fara zargina, ta fad'a out of control, sai a lokacin ta fahimci maganar daya fad'a mata yanzu da zata fito " da can da kike fita yawonki da izini na kike fita, wato yawon dayake nufi tana fita shine yawon banza na zuwa wajen maza, kukan bak'in ciki ne ya kufce mata. "Kin ga ki nutsu yanzu kina yin wani motsi zai gane kin san yana binki, ki cigaba da tuk'inki kamar baki san yana binki ba, jikinta na rawa tayiwa motar key ta taka motar a hankali, " yauwa ina kika ce mishi zaki? Bakinta na rawa tace "saloon, " to yi can d'in, tafi wajen saloon d'in, jikinta ba b’ari ta tuk'a motar bata zame ko'ina ba sai wajen saloon d'in, shiko Deen dake biye da ita ya samu waje yayi parking yana jiran fitowarta. "Shit! wallahi yau naci burin samunki dan har zak'ami nasha zan moreki amma wannan jakin banzan ya b'ata min target, aiko ya faro wasan da bazai iya k'arashe shi ba, muddin yace duk inda zakije zai biki wallahi saina wahalar dashi, da daddare kuma naje gidanshi, d'akinshi kan gadonshi na mayar da mahaifa, na zazzagewa matarshi kwayena, dariya tayi tace " ni wallahi abun ma mamaki ya bani, bak'in munafuki dana barshi a gida kamar ba komai a ranshi, ashe shima nan wai yana da wayo, a haka kamar mutumin kirki ashe tsohon banza ne.Dariya Ajlaal yayi harda dukan table d'in dake gabanshi yace " ke dai kika fad'a ni ba ruwa na, baki na da goro, dogon tsoki mstwwwwww taja had'i da cewa " Allah kuwa sumi-sumi dashi kamar na Allah ashe mutumin banza ne d'an cikiyar sharri, inba cikiyar sharri ba meye nabin bayana fisabilillahi? "Yanzu ya jawo min zuwa saloon d'in da banyi niyya ba, zayyi magana ta tsaya cak had'i da cewa " wai tsaya ma tayaya akayi kasan Deen yana bi na a baya? "Wait! Wait! Karka ce min yadda kake bibiyata shima haka kake bibiyarshi? Cikin basarwa yace " koma dai meye ba gashi yayi miki amfani ba, "ashe ma ni yayiwa amfani? "Ah to wa yayiwa? "Ni dai kin san babu uban da nake jin tsoro ko a gabanshi kika d'aga min cinya zan shiga wallahi, ido ta waro kamar tana gabanshi tace " a gabanshi fa. "Wallahi am telling you, shi d'in banza ma, tun yi yana da sauk'i zan kwasheki tsaf, tab! ina ruwa na? Ajiyar zuciya ta sauke had'i da cewa " ah lalle! suna waya har aka wanke mata k'afa da hannu aka gyara mata gashin kanta, yayinda har lokacin Deen na zaune cikin mota yana jiranta, bata bar wajen ba sai yamma lik'is. Zaune ta iske shi saman sofa tayi mishi kallan gefen ido had'i da jan tsaki cikin ranta, ta wuce yabi bayanta da kallo. Bayan sati d'aya, sosai rigima ta b'arke tsakanin Ajlaal da Deeyanah dan ya fututtuke idan bata zo ba shi zai zo dole, hannunta rik'e da tea cup ta fito daga kitchen "haba mana Ajlaal kana ganin fa halin da ake ciki, ko so kake a samu matsala asirinmu ya tonu? "Asirin mu ya tonu ko kuma asirinki ya tonu? "Naji koma meye ni dai kayi hak'uri ka d'an bari a alafa, " a lafi me? "Wallahi hak'uri na ya k'are bazan iya ba, sati d'aya kenan fa bamuyi sex ba, zatayi magana ya katse ta da fad'in " kinga idan zaki zo ki zo idan kuma bazaki zo ba zaki ganni a gidan wallahi, bai bari tayi magana ba ya kashe wayar, wayar tabi da kallo cikin ranta tana tunanin mafita. Dole ba yadda zatayi ta shirya ta fita dan bata san Ajlaal yazo gidan gudun wata rana kar a samu akasi, sai da ta tabbatar ya fita kana ta fito itama, tana gaf da isa gidan ya kirata a waya, " kai ka fiya gajen hak'uri wallahi gani nan gaf da gidan fa. "Ba wannan ba, Deen yana biye dake a baya, zata taka birki yayi saurin cewa " karki tsaya ki cigaba da tafiya, zamu wahalar dashi, suna waya tana tuk'i while Deen na biye da ita a baya, idan tabi tanan sai ta b'ille can, haka taita wahalar dashi kusan awa uku, wata irin shammata tayi mishi ta b'ace mishi b'at a cikin motoci, ya nemeta sama ko k'asa ya rasa, ranshi a matuk'ar b'ace ya juya ya koma gida, ko mukullan motar bai cire daga jikin motar ba ya fito, yana cika yana batsewa yadda kasan zai fashe ya shiga part d'in su, ba k'aramin mamakin ganin zaune a falo tana kallo yayi ba. Sosai kanshi yayi masifar kullewa, yama rasa ta ina zai fara, kamar zayyi magana sai kuma ya fasa ya shige ciki ya barta, tabi bayanshi da kallo tana dariya k'asa. "Gobe ki sake fitowa zamu sake raina mishi hankali, tunda haka ya zab'a zamuyi ta wahalar dashi muna tamola dashi a titi, ni ne fa, nine Ajlaal har ya isa ya gwara kai na, wane shi maza bisa kanshi wallahi, waya suka cigaba dayi har dare kafin suka kashe. Washe gari da safe wajen k'arfe 11:30am ta shirya cikin riga da siket na lace ta d'ora hijab akai, sai da ta tabbatar yana falo kana ta fito, yayinda kunnenta ke manne da bluetooth wireless, fuskarta wasai d'auke da fara'a tace " ina kwana yaya, dakyar ya bud'i baki ya amsa da " lafiya, ga breakfast d'inka can akan dinning na gama, "ok, kawai yace a tak'aice, tana kanne dariya ta fice, bai tambaye ta inda zata ba, hakan ya bata tabbacin zai biyo bayanta, d'aya daga cikin motocin gidan ta shiga Elantra dayake basa ware motoci kowa hawan kowacce yake yi, duk wacce yiwa mutum kawai hawa zayyi. Tana kallanshi ta mirror yana biye da ita, tayi dariya had'i da buga sitiyari tace " iska tana wahalar dame kayan kara, kai kaga yadda yake bina a hankali kamar me shirin kama wani abu? "Wani abun yake san kamawa mana, "au haka ne fa ko? Ta fad'a tana kwashewa da dariya, " wallahi idan kaga yadda na barshi a falo kamar dolo kai baka ce yasan wani abu me makammancin haka ba, sosai Ajlaal yayi dariya jin tacewa Deen dolo, wasu irin surk'uk'in lunguna masu cab'i ta rink'a shiga dashi, yana biye da ita yana jan tsaki deep down kuma yana tambayar kanshi abinda ya kawo ta irin wannan unguwar, yau kam har inda k'afarshi bata tab'a takawa cikin garin Kano ba ta taka, duk irin rintsi da cunkosan da ake cewa Nigeria nadashi bai tab'a tabbatarwa ba sai yau, shi bai ma tab'a tunanin akwai irin wad'annan unguyoyin ba, yana tafe yana tsinewa 'yan siyasar Nigeria cikin ranshi, yana auno cikin bala'i da masifar da zasu shiga ranar lahira, wasu guraren ko dabbobi akace su rayu a wajen an cutar dasu balle mutane bil Adam. Bai san yadda akayi ba, sai ganin motar yayi fake a gabanshi, yayi parking shima daga nesa inda zai rink'a hango motar, a k'alla an d'auki wajen mintuna talatin babu wanda ya fito daga motar koya shiga, shiru-shiru har akayi awa d'aya da rabi amma babu kowa, agogon Rolex dake d'aure a hannunshi ya duba yana jan tsaki a fili, wata irin d'aukewa nefarshi tayi da tunanin kodai suna cikin motar yazo cikin kanshi, bai tsaya yin shawara da zuciyarshi ba ya bud'e motar ya fita, saboda rawar da jikinshi keyi yayi tuntub'e saura kad'an ya fad'a cikin kwata, bai tsaya dubawa ba ya cigaba da nufar motar zuciyarshi na wani irin mugun bugu da k'arfi. Bisa mamakinshi motar babu kowa ciki, da sauri ya kama hannun motar zai bud'e yaji ta a rufe, sosai mamakinshi ya bayyana k'arara saman fuskarshi, "ya akayi ta kufce min? "Ya akayi ta b'ace min ta bani k'afa har haka? Ya fad'a hannunshi kan k'eyarshi, take kanshi ya juye, tunaninshi ya kulle yama rasa tunanin da zayyi, abinka da me zuciya, ji yayi tamkar ya shak'e kanshi ya mutu, saboda tsananin zuciya har juwa-juwa ya rink'a ji, a daddafe ya koma motarshi ya shiga ya fige ta trillion baima damu da ramukan unguwar ba, ko faci baya tsoron yayi. Ita kam tana shan kwanar lungun kafin ya shawo kwanar tayi sauri ta fice ta dannawa motar luck, wani siririn lungu ta samu ta rab'e ciki tana lek'enshi, hannunta saman bakinta tana rufe bakin dan kar yaji sautin dariyar da take yi, numfashi Ajlaal ya sauke had'i da cewa " kiyi sauri kizo kafin ya gane bakya cikin motar munyi abinda zamuyi, sai da ta sake kallan Deen tayi murmushi kana ta juya tabar wajen tana fad'in " wahalalle kai kaga dare wallahi. Mai adai-daita sahu ta tare ta shige tabarshi nan yana zaman jiran gawon shanu, tana shiga get d'in gidan taga Ajlaal tsaye daga shi sai pant, gira tsaya ta d'age tare da cewa " na gudu kona tsaya? Dariya yayi yace " imma kin gudun zaki dawo ne, tana k'arasowa inda yake tace " oh! matsuwar har ta kai haka? Shu'umin kallo yayi mata na cikin kwayar ido yana lasar leb'enshi yace " fiye da haka ma, k'irjinshi ta shafa had'i da d'an murza kan nipples d'inshi ta kashe mishi ido d'aya tace " bazan tabbatar ba sai na jika a kain.... Kafin ta k'arasa ya had'e bakinsu yana lasar lips d'inta, deep kiss ya shiga yi mata sosai a haukace yadda kasan zai cire mata bakinta daga jikinta, jin tsaiwar na neman gagararsu yasashi d'aukarta batare daya raba bakinsu ba, bai tsaya a falo ba ya huce bedroom yana zuwa ya jefa ta kan mamaken Turkish Bed d'in dake d'akin, ta gyara kwanciyarta had'i da fizgo shi ya fad'a kanta, yadda kasan mayunwacin zakin daya shekara baici komai ba haka ya far mata, sautinsu ya soma tashi a d'akin, sai da ya sha bakinta sosai iya shan shi kana ya cire bakinshi daga cikin nata a gaggauce ya cire mata kayan jikinta kaf bai barta da komai ba, ya sake fad'awa kanta yayi mata rumfa yadda kasan mayu haka suke lashe-lashe da tand'e-tand'en juna, cikin k'ank'anin lokaci suka gama rikita juna, suka fice fit daga cikin hayyacinsu, in banda ihuuu da gurnaninsu baka jin komai na tashi cikin d'akin, an kai awa d'aya suna abu d'aya kafin suka sararawa juna. Samanta ya zube yana mayar da wahalallen numfashi bayan ya samu nutsuwa, ba tare daya d'aga ta ba baccin samun nutsuwa yayi awon gaba dashi, jin ya sakar mata gaba d'aya nauyinshi yasata ture shi ya fad'a saman gadon, a hankali ya bud'e idonshi da har lokacin basu gama dawowa dai-dai ba, ajiyar zuciya ta sauke me nauyi tana kallan kwayar idonshi tace " bari nayi sauri nayi wanka na tafi, kasan yana gane bana cikin motar gida zai nufa, iska ya furzar daga bakinshi batare da yace komai ba ya mik'e tare da ita a jikinshi ya shiga bathroom, sai da suka gama lalacewa a bathroom d'in kafin sukayo wankan suka fito, tana tsaye ya goge mata jikinta tsaf da towel kana ya mayar mata da kayan jikinta, har bakin get ya rako ta yana zuba mata rigimar shi bai k'oshi ba, " wannan fa d'and'ani haukaci kikayi min. Dariya tayi gami da cewa " ina laifi asa a baka ai yafi a rataya, " ni dai wallahi bazan iya sake d'aukar wannan tsayin lokaci ba gaskiya, ki dawo gobe ko jibi, danta lallab'a shi su rabu lafiya tace mishi to taji, ta fice. Allah ya taimake ta harta koma gidan bai dawo ba, dan daga gidan Ajlaal direct gida ta wuce bata bi ta kan motar ba, balle ta koma inda motar take, jakarta da hijabinta kawai ta aje a bedroom ta fito ta shiga kitchen ta d'ora tuwon shinkafa, fiki sukunbiya da markad'add'un kayan miya ta fiddo daga freezer, ta d'auko non stick ta zuba mai ta d'ora saman gas, dayake kifin a yayyanke yake kuma a wanke yake tas yasata d'ora man, tunda tasan ba wani lokaci zata b'ata ba, cikin ruwan zafi ta saka kifin ya saki, ta sake d'auraye shi ta zuba mishi gishiri ta zuba cikin man tare da yanka albasa me d'an yawa ta zuba cikin dan kar k'arnin kifin ya cika mata gida, ranshi a mugun dugunzume ya shigo gidan, yadda kasan yayi bindiga ya fashe haka yake ji. Saman sofa ya zube ya kishingid'a da fari bai ji motsinta ba sai daga baya, d'an shiru yayi tare da yin kasak'e da kunne danya tabbatar, sake jin motsinta yayi a kitchen, kamar mara gaskiya ya mik'e ya nufi kitchen d'in, tana ta faman aikin hankalinta kwance yadda kasan babu wani abu, tun shigowarshi tasan ya shigo haka yanzu ma dayake tsaye jikin fridge tana sane dashi, amma yadda kasan bata san Allah yayi ruwan halittarshi a wajen ba, har ya juya zai fita sai kuma ya dawo ya kalle ta sosai yace " kin fita yau ne? D'an firgigit tayi wai ta tsorota, har da dafe k'irji tace " kai! Yaya ka tsorata ni, bai kula da maganar da tayi ba, ya d'aure fuska babu alamun wasa kwata-kwata a tattare dashi yace " nace kin fita yau ne? Kai tsaye tace " ba'a gabanka na fita ba koka manta ne? Sai lokacin ya tuna yana zaune a falo ta fita, sake tsuke fuska yayi yace " da kika fita ina kika je? "Gidan kunshi naje, kallan da yayiwa hannunta da k'afarta ne yasata dafe goshinta tana murmushi tace " ops ban k'arasa gidan ba nayi faci motar ma acan na barta, kai kaga unguwar Yaya? "Wai ina 'yan siyasar mu zasu kai hakk'in talakawa ne? "Wallahi d'ai-d'ai daga cikin 'yan siyar Nigeria ne bazasu ci wuta ba, kallan sosai yayi mata, kamar bazayyi magana ba sai kuma yace " ya akayi kika dawo gida, sai da ta juya idanuwanta kana tace " Napep nahau mana, " wannan lokacin da kika d'auka anan kawai kika tsaya? Wata irin mummunar fad'uwa gabanta yayi, k'irjinta ya doka da tsananin k'arfi, ta tsaya cak tabar abinda take yi, a hankali ta juyo ta kalli cikin kwayar idonshi, shima tar yake kallan idonta, ganin irin kallan da yake yi mata yasata yin rau-rau da ido zatayi kuka tace " me kake nufi da wannan maganar taka Yaya? Sosai take k'ok'arin k'ak'aro kuka tace " Yaya zargi na kake yi? Tsoki ja mtswwww yace "idan ma zargi nake yi laifi ne? "Ko ba kece kika jawa kanki zargin ba? Ya fad'a idonshi tar cikin nata, abinda ta hango cikin kwayar idonshi ba k'aramin firgita ta yayi ba, wanda har ya hanata magana, tana kallanshi har ya fice bata iya furta koda kalma d'aya ba, ta dad'e tsaye nan inda ya barta a matuk'ar tsorace da abinda ta gani tattare dashi, cikin sanyin jiki ta juya ta cigaba da aikinta, kafin Magriba ta gama tuwon shinkafa da miyar Ogun leaf dayasha kifi sukunbiya da bushashshen kifi d'an Maiduguri, ga ganda da kwalla, ta zubawa Ammi nata a kula haka ma Ammu, da kanta ta mik'a musu, sama-sama ta tsaya suka gaisa saboda bata cikin nutsuwarta, taso ma tayi sob'o ko coconut drink amma ta kasa tuwon ma danta riga ta d'ora ne. Bazata iya fassara abinda ta gani cikin idonshi ba amma koma meye abun tayi masifar tsorata dashi, har tayi wanka tayi sallah a firgice take, sai da tayi waya da Ajlaal kana yad'an kwantar mata da hankali. Tana zaune kan sallaya bayan ta idar da sallar isha tana waya da Ajlaal kasancewar bluetooth d'inta babu caji yasata kara wayar a kunnenta fuskarta d'auke da murmushi, bata ji motsin shi ba sai kawai jin banko k'ofar bedroom d'inta taji, tayi saurin kifa wayar, tashin hankali, tsoro da firgici k'arara bayyane saman fuskarta, ga rashin gaskiya nan k'uru-k'uru yana gani a tattare da ita, yaso yayi magana amma ya fasa ya juya ya fice, yama fasa yin abinda ya kawo shi d'akin gaba d'aya dama raban daya shigo d'akinta har ya manta. Jikinta na rawa ta kashe wayar batare da sunyi sallama ba ta mik'e tabi bayanshi duk ilahirin jikinta na tsuma, yana zaune saman dinning table yana daddana waya da alama ita yake jira ta bashi abinci, hakan ba k'aramin kwantar mata da hankali yayi ba dan tasan daya ji wayar da take yi da bai zauna zaman cin abinci ba, idanuwanta ta lumshe had'i da sauke ajiyar zuciya a hankali, duk abinda takeyi yana sane, ta k'araso ta zuba mishi abincin, ta d'auko mishi lemon Chiivita a fridge ta kawo mishi had'e da glass cup, itama ta zuba ta zauna tana ci sama-sama, gaba d'aya hankalinta yana kan wayarta, tana chart fuskarta d'auke da murmushi, duk wani motsinta yana sane dashi, shima murmushin yayi na gefen baki yana danne abinda ke taso mishi, tare dakai lomar tuwan, saboda b'acin rai ji yayi tamkar ya saka mad'aci a bakinshi, sai da yayi da gaske kafin ya iya daurewa ya had'iye tuwan bakinshi, kallanta ya sake yi yaga still she's on her phone, ya buga uban tsaki had'i da kwab'ar da plate d'in tuwan da k'arfi ya mik'e, firgigit tayi ta dawo cikin hayyacinta, ta kalleshi dai-dai lokacin da yake shigewa bedroom d'inshi kana ta dawo da kallanta kan tuwon, baki ta tab'e had'i da zagewa taci tuwon san ranta kana ta mik'e ta shige bedroom ta fad'a saman bed suka cigaba da wayarsu tana yi tana juyi cike da annashuwa. Tayi nisa cikin wayar tana ta mirgine-mirgine ya shigo, tayi saurin tashi zaune saboda tsananin tsoro yadda kasan idanuwanta zaro fad'o, ido ya kafe ta dashi na tsayin lokaci, ta sunkuyar da kanta k'asa dan bazata iya jurewa irin kallan da yake yi mata ba, kamar daga sama taji yace " dawa kike waya? A kid'ime ta d'ago ta kalle shi, kun san mutane masu manyan idanuwa basa iya b'uye tsoro, firgici da tashin hankali dan haka a idanuwanta ya hango zallar tashin hankalin data shiga, k'afarshi d'aya ya d'ora saman gadon yayinda d'aya k'afar tashi take taka k'asa, ya matso da fuskarshi gaf da tata ta yadda iskar numfashinshi take sauka cikin hancinta, ranshi a matuk'ar b'ace yace " dawa kike waya? Yawu ta had'iye kwat ba shiri, take gumi ya soma tsatsafo mata a saman goshinta, in banda rawa babu abinda bakin keyi, bata ma da nutsuwar had'a kalamai balle ta iya yi mishi k'arya, " nace dawa kike waya? Ya fad'a a tsawace, wata irin muguwar rawa da tsuma duk ilahirin jikinta ya d'auka lokaci d'aya ga matsanancin tsoronshi daya shigeta, idonshi dake kanta ya kai kan wayar, itama wayar ta kalla, ya kai hannu zai d'auki wayar tayi saurin d'auke wayar, wani irin kallo ya bita dashi me wuyar fassarawa, wani irin tuk'uk'i yaji yana taso mishi daga can k'asan k'irjinshi, idonshi yayi wani irin mugun ja, jijiyoyin kanshi sukayi rad'o-rad'o yadda kasan an zana su, da k'arfi ya finciko ta ya warb'ar da ita a k'asa, saboda tsabar soyar da zuciyarshi keyi mishi har bibbiyu yake gani, abinka dama dame zuciya, sake damk'o ta yayi ya d'agata sama, ya had'a ta da jikin bango ya mak'ure ta, ya shak'e mata wuya da iya k'arfinshi. Tsabar azaba tasa idanuwanta yin jajir kamar gauta, duk sunyo waje k'uru-k'uru yadda kasan zasu fad'o k'asa, sosai ta soma kokawa da numfashinta dake neman kwace mata, d'aya hannun yakai ya d'auki wayar dake yashe a k'asa ya shiga dubawa, duk inda ya kamata ya duba ya duba amma baiga komai ba, har Chart d'inta ya duba, da Gallery, Message, Phonebook, received call, Missed called amma babu wani abu daya gani na zargi, hakan ya sashi sakinta ta zube k'asa tana tari da faman mayar da numfashi. " Deeyanah karki bari na kama ki da wani abu daya danganci cin amana, butulci da yaudara, idan kika sake kika ci amanata zanyi nisa dake da duniyarki, zan yiwa rayuwarki nisan da har ki mutu bazaki sake gani na. Yana gama fad'a ya nufi k'ofa zai fice har yakai bakin k'ofar ya juya ya kalle ta sosai yace " daga yau ni zan rink'a kaiki duk inda zaki, ban yarda ki fita ke kad'ai ba, bai jira amsarta ba ya fice, tabi bayanshi da kallo, har lokacin tana rik'e da wuyanta hawayen azaba nabin kuncinta, " Allah ya isa na mugu azzalumi kawai, ta fad'a a wahalce, dakyar ta mik'e ta d'auki wayarta ta koma saman gadon tana dialing number Ajlaal, number busy aka ce mata, tana niyyar sake kira wayarshi ta shigo. Ranshi a matuk'ar b'ace yace " Deeyanah ki bari na kashe Deen please, wallahi badan ina tsoron b'acin ranki ba da yau bazai kwana duniya ba, " a tsawace tace " karka fara tunanin kashe min miji, shi d'in mijina ne, shine katangar dake tokare da bayana, ka kula, tsaki yayi had'i da kashe wayar ya jefata saman kujera, yana danasanin datsar wayar da yayi ya goge komai, " dama banyi hacking wayar nayi formatting ba, dana bari yaga abinda ya kamata ya gani komai yazo k'arshe, ya k'arashe maganar had'i da jan dogon tsaki. Idanuwanshi ya lumshe had'i da tallafe kanshi yana jin zafin shak'ar da Deen yayiwa Deeyanah, wayarshi da tayi ringing yasa shi jan dogon tsaki mtswww had'i da bud'e idonshi ya d'auki wayar, batare daya duba sunan wanda ke jikin wayar ba ya kara a kunne yana fad'in " ki kyale ni please. "Wacece zata kyale ka? Jin muryar Mamanshi yasashi yin murmushi yana gyara zamanshi yace " Deeya.....!, saurin ankarewa yayi dan haka yace " wata ce, zatayi magana Abba ya warce wayar daga hannunta yana fad'in " kai yanzu Ajlaal kayi mana adalci kenan fisabilillahi? Idanuwanshi ya lumshe ya sake bud'ewa a nutse dan ya riga yasan laifinshi, " akan mace ka sallama mu, tun daga ranar daka rasa Deeyanah shikenan muma ka yafe mu, ace muna gari d'aya amma sai muyi wata bamu saka ka a idonmu ba Ajlaal? "Kayi hak'uri Abba in sha Allahu zan zo gobe. Mama ta amshi wayar tana fad'in " me zaka ci na saka a dafa maka? "Komai ma Mama! " kafa zo d'in please, mik'ewa yayi yana fad'in " zan zo in sha Allah Mama, wayar ya kashe ya saka a aljihun wondonshi ya zari key d'in mota ya fice. Washe gari yana tashi yayi wanka ya shirya ya fice, minti 18 ne ya sada shi da gidansu, suna jin tsayawar mota suka fito harabar gidan, Mama nata rawar jikin ganinshi bakinta yak'i rufuwa, yayinda Abbah ke tsaye ya zuba mishi ido ganin yadda yayi wani fresh dashi, Mama na rik'e dashi har falo, kallanshi Abbah yayi sosai ya fitar da numfashi yace " Ajlaal!, yadda ya kira sunanshi ba k'aramin karya mishi zuciya yayi ba, a hankali ya d'ago ido ya zubawa Abbah ido. "Ka sani babu da wani d'an sai kai, kai kad'ai Allah ya bamu balle idan babu kai muce akwai wani Wanda zai d'ebe mana kewa, gashi girma ya kamamu mu duka, lokacin da muka fi buk'atar ka a kusa damu, lokacin da muke buk'atar taimakonka, lokacin daya kamata ace ka karb'i ragamar dukiyata amma a lokacin ne zakayi nesa damu kayi watsi da al'amuranmu akan mace? Kanshi k'asa yace " wallahi Abbah ba haka bane, " to yaya ne Ajlaal, ai ko babu amfanin da zakayi mana zamu so ganinka kusa damu. " Kayi hak'uri in sha Allah zan gyara. " Aikin kenan ayi hak'uri kullum abinda kake fad'a kenan. " Wannan karon nayi maka alk'awarin zan rink'a zuwa kullum ina ganinku, " to mai zai hana ka dawo kusa damu gaba d'aya? Kafin Ajlaal yayi magana Mama ta watsa mishi uwar harara tana fad'in " dan Allah karka dameshi, karka matsawa yaron nan ka barshi yaji dad'in lokacinshi ya morewa rayuwarshi haba, tsit Abbah yayi bai sake cewa komai ba, kallanta ta mayar ga Ajlaal cikin zak'uwa tace mishi " wacece yarinyar da kayi maganarta? Cikin mamakin da Abbah ya kasa danneshi yace " unbelievable Ajlaal ne ke maganar mace? "Wannan wace me sa'ar ce? Kallanshi Mama tayi ta watsar irin ba'a saka bakinka ba d'innan ta mayar da kallanta ga Ajlaal tace " ya sunanta? A shagwab'e yace " Mama! "Eh! Wallahi a matse nake kayi aure naga 'yan jikokina, " ki bari tukunna da d'an sauran lokaci kad'an. "Wanne lokaci ne ya rage? "Kaga a bari ya huce shike kawo raban wani, da zafifi kan bugi k'arfe. "Karki damu Mama wannan bazai huce ba balle ya kawo raban wanin, ita d'in tawace ni kad'ai, an riga an rubuta ni kad'ai ne mamallakinta, wannan karon bazan tab'a bari wani ya sake shiga tsakanina da soyayya ta ba, dariya Mama tayi tare da cewa " kayi komai danka mallaketa yak'i a soyayya ai halak ne, Abbah nasan yayi magana amma wani nauyi na hanashi. Gidan ya yini bai bar gidan ba sai dare, sun sha hira, yana fitowa daga gidan yayi dialing number ta, bugu d'aya ta d'aga wayar tare da kara wayar a kunnenta batare datace mishi komai ba, yasan fishi take yi dashi dan haka tak'i yi mishi magana, idanuwanshi ya lumshe, had'i da sauke ajiyar zuciya a hankali, cikin taushin murya yace " kiyi hak'uri, soyayyarki ce tasa ni aikata duk abinda na aikata Deeyanah. Cikin kunnenshi ta fitar da numfashi kana tace " ya wuce, murmushi yayi kamar tana ganinshi yace " yaushe zamu had'u na sake bada hak'uri sosai? Kafin tayi magana yace " au na manta ashe fa Boss yace shi zai rink'a kaiwa unguwa da kanshi duk inda za'a aje ko? Murmushi tayi me sauti dan tasan akwai abinda yake nufi, " fad'i kawai ina jinka! ta fad'a tana dariya, " tunda haka ya zab'a ya zamuyi? "Tunda shiya zab'i ya zame mana driver ai hikenan, ya fad'a yana dariya, itama dariyar tayi tace " kaga a matse nake fa kwana biyu bamu had'u ba yaushe zanzo a d'an sosa min? Dariya yayi sosai harda dukan sitiyari yace " kamar ko kin san nima a matsen nake, idan zai yiwo gobe kizo mana mu d'an gwangwaje, " to shikenan ba damuwa, Allah ya kaimu, tana k'ok'arin kashe wayar yace " ki cewa saban driver mu yabi min ke a hankali fa, dariya tayi gami da kashe wayar batare data ce komai ba. Text ta tura mishi kamar haka " gobe ina san ka kaini gidan Raleeya da safe please tace tana san gani na, bata jima da tura mishi sak'on ba ya dawo mata da amsar " Allah ya kaimu. Yana zaune cikin mota yana jiranta ta fito, kallo d'aya yayi mata ya d'auke kanshi, ta bud'e ta shigo ta zaune a kujerar gaba, " ina kwana, an tashi lafiya? Yana yiwa motar key ya amsa da " Alhamdulillah, babu wanda ya sake cewa komai har suka hau titi batare daya kalleta ba yace " ina ne? Tana yi mishi kwatance har suka k'arasa k'ofar gidan Ajlaal, yabi gidan da kallo kamar zayyi magana sai kuma ya fasa ta bud'e motar ta fita tana fad'in " zaka je ka dawo ne? "Ina nan ina jiranki ki gama ki fito mu tafi, batayi magana ba ta shige gidan, shi kuma ya gyara parking had'i da kwantar da kujera ya kishingid'a yana zaman jiranta. Ta window suke lek'en Deen, a tare suka kwashe da dariya had'i da tafawa, " ashe dai da Hausawa ke cewa maso kayanka ya fika dabara da gaske ne? "Shi da kanshi ya kawo matarshi inda za'a d'ebe mata albarkatun jiki ya zauna yana zaman jira a gama ya mayar da ita gida, lalle wata shari'ar sai a lahira, labulen window ta saki ta jingina bayanta da jikin window tace " shi yaga zai iya ai, bamu muka tilasta mishi ba, zab'in shi ne hakan, glass cup d'in hannunshi ya aje saman bedside ya tako gareta fuskarshi d'auke da shu'umin murmushi ya matseta sosai gami da sake kallan motar Deen yace " so pity, karka damu kad'an zan d'an tsakureta, ya k'arashe maganar tare da had'e bakinsu. Caraf ta amshe bakinshi ta soma tsotsar bakin tana lasa kamar ta samu ice cream, cikin salo ya d'auketa cak ya zaunar da ita saman k'ugunshi while bayanta na jingine jikin bango ya zame d'ankwalin kanta ya fad'i k'asa yasa hannunshi cikin kwantaccen gashin kanta daya sha gyara ya fara yamutsawa, sosai suka zage suka jiyar da junansu dad'i, ranar kam anyi gogen fata da gaske, cikin kwanciyar hankali sukayi suka gama yadda kasan babu wanda ke jiransu a waje, har wanka sukayi tare. Tana saka kayanta yace " shanyar can fa da kikayi ta shanyu da kyau harta bushe, kanta ta dafe gami da d'an zaro ido tace "ops kasan na manta dashi? "Ah! Ba dole ki manta dashi ba tunda kin karb'i damen jijiya harta kai miki karo, pillow ta jefa mishi tana dariya, har bakin get ya taka ta ya d'an tsotsi bakinta yana fad'in " ni dai ban k'oshi ba azo a k'ara min, ta tura shi baya tana dariya, sai da ta saita kanta sosai kana ta fita, bacci ta same shi yana yi cikin mota, har cikin ranta bata ji dad'in yadda ta same shi ba, sosai taji tausayinshi na ratsa ta, a hankali tayi knocking glass d'in window motar, cikin nutsuwa ya farka, motar ya bud'e mata ta shiga ta zauna, " kayi hak'uri na dad'e ko? Bayyi magana ba yayiwa motar key suka bar wajen, Ajlaal dake tsaye jikin window yana kallansu yayi murmushi gami da kai glass cup d'in bakinshi. Tun daga wannan rana ya zama cewa Deen ke kai Deeyanah gidan Ajlaal koyaushe, kuma ya jirata ta gama abinda take yi ya d'auko ta har tsayin watanni uku. Deen na zaune saman dinning table yana cin abinci ta fito daga bedroom hannunta rik'e da waya tana lallatsawa, bai d'aga kai ya kalleta ba balle yayi mata magana, ta zauna saman sofa tana cigaba da abinda take yi itama batayi mishi maganar ba, a nutse ya gama abinda yake yi ya mik'e yabar wajen, kwance yake saman makeken gadonshi k'irar Turkish sai juyi yake yi ya rasa abinda yake yi mishi dad'i gaba d'aya duniyar tayi mishi bak'ikk'irin k'irjinshi yayi mishi nauyi, haushin kowa yake ji, duniyar tayi mishi duhu, abin duniya sun taru sunyi mishi yawa, duk iya bin diddigin Deen da bincikenshi ya kasa gano komai, babu abinda ya iya ganowa, dan duk wani takun da zayyi na Ajlaal na gaba da nashi, idan baku manta ba na fad'a muku Ajlaal nada kwakwalwa da masifaffan k'ok'ari irinsu ne ake kira da genius ko gifted, duk inda kuke tsammanin shegen mugun mai matuk'ar wayo da kwanya Ajlaal yakai, shiyasa Deen ya kasa gano komai duk iya bincikenshi. Yana kwance ya tsunduma duniyar tunani saurin mik'ewa yayi tare da cewa " wait! tuno lokacin da suke hira da Deeyanah tace mishi ta nemi Raleeya ta rasa, bata sake jin labarinta ba tun bayan aurensu yayi, ya sake tuno tunda suke zuwa gidan Raleeya bata tab'a rako Deeyanah ba, bata tab'a cewa ya shiga su gaisa ko ta fito su gaisa ba, " da wani abu! lalle da akwai wani abu a wannan gidan ya fad'a a fili, bai tsaya yin shawarar komai ba ya mik'e, d'akinta ya shiga kamar an hankad'ashi ciki ya fad'a d'akin, ta fito daga wanka daga ita sai towel, " shirya mu fita, cike da mamaki ta kalleshi had'i da kallan agogon bango tace " unguwa kuma? "Wacce irin unguwa cikin daren nan? "Eh! nace ki shirya koma ina ne idan munje zaki gani, batayi tsammanin wani abu ba tace " to bani minti biyar na gama shiryawa, " shirya ina jiranki, yace yana zama saman gado, batayi magana ba ta soma shiryawa bata d'auki lokaci ba ta gama, ta zira hijab tare da d'aukar wayarta ta kalleshi tace " muje ko? "Bani wayarki, yace yana mik'a mata hannu, cikin matsanancin mamakin dake bayyane saman fuskarta tace " wayata kuma? "Eh ita, mik’a mishi wayar tayi tana kallanshi sosai, ya sata gaba yana binta a baya suka fice, " wai ina zamu ne? Ta tambaya ganin ya hau babban titi, bai bata amsa ba illa mayar da hankali da yayi kan tuk'inshi, ganin suna d'aukar hanyar gidan Ajlaal yasa hantar cikinta kad'awa, cikinta ya juya da k'arfi, murmushin yak'e ta k'ak'aro tare da dakewa tace " idan ka gama da waya ta ka bani, hankalinshi nakan tuk'in da yake yi yace " ban gama ba, yayi maganar a tak'aice, wani irin mugun bugu k'irjinta ya shiga yi, zuciyarta na tsalle kamar zata tsaga k'irjinta ta fito, jinta take yi tamkar a saman ruwan k'ank'ara take zaune, hannuwanta take ta faman kwantala saboda tsabar tashin hankali batare data sani ba, batayi aune ba sai gani tayi yayi parking a k'ofar gidan Ajlaal, wata irin muguwar tsuma da kerrrrma jikinta ya d'auka lokaci d'aya. A hannunta take jiyo sautin tsinkewar jijiyoyin kanta, duk wata k'ofar gashin dake jikinta ta soma tsatsafo da gumi, ko mala'ikan mutuwa ta gani akanta iyakacin abinda zata ji kenan, saurin kallanshi tayi cikin matsananciyar kad'uwa da firgita tana goge gumin kumatunta tace " me kuma muka zo yi anan? "Ina san magana da Raleeya ne yau, ya k'arashe maganar had'i da sakin murmushin da bata isa ta iya fassarawa ba, yawun daya wuce mata ba shiri yasata kwarewa, sosai take tari while idonta kanshi tana kallanshi da idanuwanta da suka firfito kamar zasu fad'o k'asa, da k'arfi tsiya ta tsaida tarin, muryarta na shak'ewa tace " bari na shiga na kira ta, fuskarshi d'auke da murmushin har zuwa lokacin ya kafe ta da idanuwanshi dake k'ara firgita ta yace " nop! karki damu ba sai kin shiga ba, bari na samu yaro mu turo yayi yo mana sallama da mijinta in yazo shi sai yayi mana iso zuwa wajenta, " babu wanda fa ke shigar musu gida saboda tsaro, suna ma da k'attin k'arnuka, ta fad'a kamar me koyon magana, bai bi takanta ba ya bud'e motar ya fito, jikinta na rawa ta bud'e motar ta fito itama tana fad'in " ba saika aika yaro ba ka barni na shiga nayi mata magana mana. Almajirin daya zo zai gifta shi ya kira tare da cewa " dan Allah shiga gidan nan kayi mana sallama dame gidan kome gadin gidan, Almajirin ya amsa da "to!, had'i da nufar gidan. 2 Hannuwanta ta dunk'ule waje d'aya had'i da d'aga kanta sama tana fad'in " Allah kada ka tozarta ni, Ubangiji kaji tausayi na kaji k'aina ka rufe min asiri nayau kad'ai, ta fad'a jikinta na wata irin muguwar kerrrrma, tare da wani kamilin mutum Almajirin ya fito, mutumin ya mik'awa Deen hannu suka gaisa fuskarshi d'auke da murmushi yace " bawan Allah ban gane ka ba? Martanin murmushin shi Deen ya mayar mishi kana yace nine mijin Deeyanah, ya k'arashe maganar yana kallan Deeyanah, murmushin yak'e ta k'ak'aro ta shinfid'awa fuskarta, " ah Deeyanah ce wai, ni bamma kula dake ba ai, shine zaku tsaya anan, meyasa bazaku shiga ba? Mamakin mutumin dabata tab'a ganinshi a duniya ba ya cika da yadda yake mata magana tamkar tsofaffin abokan da suka san juna sama da shekaru, " ina ya sanni? "Ya akayi ya san sunana? Kashe mata tunani yayi ta hanyar cewa " bakuyi waya da ita bane? A dururuce cikin kame-kame duk ta gama rikicewa ta had'a uban gumi tace " wa? Fakaitar idon Deen mutumin yayi ka kashewa Deeyanah ido d'aya, a fili ta sauke ajiyar zuciya had'i da sanya gefen mayafinta ta goge gumin dake tsatsafo mata, tasan wannan bakomai bane sai aikin Ajlaal, tana k'ok'arin saita kanta tace " anya bamuyi waya da ita ba, halan bata nan ta fita? "Wallahi ta fita tun yamma bata dawo ba amma nasan yanzu zaku ganta, ku shiga ku jira ta, ido ta zaro had'i da cije leb'enta tana kallan mutumin ido ya lumshe mata tare da nuna mata hannu alamar bakomai ta kwantar da hankalinta, duk wata dak'ik'a ta duniya tare take bugawa da zuciyarta ta kafe Deen da ido tana jiran taji amsar da zai bayar yadda kasan k'irjinta zai fad'o k'asa haka take ji, " a'a bakomai ba sai mun jira ta ba, ma dawo wata rana, nannauyan numfashi ta fitar a fili gami da lumshe idanuwanta, Deen ya yiwa mutumin sallama ya shige mota dan gudun kar Deen ya zargi wani abu yasa tayi saurin bin bayanshi. Tuk'in kawai yake yi amma hankalinshi baya jikinshi, motar tayi tsit sai sautin kukan Deeyanah dake tashi tana shashsheka, while tana d'an satar kallanshi, sai da sukayi d'an nisa kana ta d'ago ta kalleshi sosai tace " abun har ya kai haka Yaya? "Har ya kai daka fara zargina kana kokwanto akan gaskiya da amanata? "Ina dukkan yardar da kayi min? "Ina tarin alk'awarirrikan da mukayiwa junan..... Kallan daya jefa mata ne yasata had'iye sauran maganar, harya bud'e baki zayyi magana sai ya  fasa, kuka ta fashe dashi wiwi kamar k'aramar yarinya, bayyi mata magana ba ya gangara gefen titi yayi parking, idanuwanshi ya runtse da k'arfi yana jin yadda kanshi ke barazanar tarwatsewa, a hankali ya bud'e idonshi da suka gama rinewa ya sauke su akanta, wani irin haushin ta yaji yana fisgarshi kamar ya rufe ta da duka, kwantar da kujerar motar yayi ya kwanta batare daya furta koda kalma d'aya ba. Cike da mamaki ta kalleshi ta tuna a baya idan tanayi mishi kukan wasa danta tsokane shi kusan haukace mata yake yi, yayi ta rarrashinta yana lallab'a ta kamar kwai, amma yau itace take kuka a gabanshi ko kallo bata ishe shi ba, bak'in ciki yasata watsa mishi harara tare da goge hawayenta tace " ka kaini gida, ba musu ya d'ago had'i da yiwa motar key ya fad'a saman titi, har suka isa gida babu wanda ya sake yiwa wani magana a tsakaninsu, yana yin parking motar ya bud'e ya fice ya barta cikin motar tana bin bayanshi da kallo, cikin sanyin jiki da wani irin mugun tsoronshi ta mik'a hannu ta d'auki wayarta daya bar mata anan ta bud'e motar ta fita, koda ta shiga falon babu ko alamunshi cikin falon, kamar wacce kwai ya fashewa a ciki taja k'afa ta shige bedroom d'inta. Tana shiga wayar hannunta ta soma haske alamar shigowar kira, sai da ta ja tsaki mtswwww kana tayi picking wayar, bata bari yayi magana ba tace " wai ya akayi kake sanin duk abinda zai faru ne tun kafin ya farun? "Ya akayi ka san muna zuwa gidanka har kayi duk wannan shirin? Dariya yayi sosai kana yace " shiyasa nace miki babu inda zaki shiga a duniya ki gujewa ganina da jina, bazaki tab'a iya b'oye min ba Deeyanah, duk inda kike ina tare dake, idanuwanta ta juya tace " kai ka sani, wannan mutumin waye shi? "Ina zan san waye shi My Angel, idanuwanta waje tace " badai baka sanshi ba? "Eh! ban sanshi ba, kanta ta dafe gami da runtse idanuwanta tace " ya Salam! "Ya akayi ne? Yace yana kai cokalin abinci bakinshi, " okay wato kai bama ka damu ba ko? "Kaje ka d'auko mutumin da bamu sanshi ba ka saka shi cikin sabgar mu, baka tsoron wani abu ya biyo baya? "Baka tsoron ya tona mana asiri? "Rashin sanin nashi da bamuyi ba shiyasa babu abinda zai biyo baya, kuma shiyasa bazai tab'a tona mana asiri ba, dana ji kuna magana da Deen na tsaya tsai na fahimci nan gidan zaku zo, shine na fita waje can wata unguwa wacce kwata-kwata bata da had'aka da nan area na samo mutumin da zayyi presenting mijin Raleeya, bai san mu ba, bai san komai akan mu ba, bashi da wata makamar da zai tuna mana asiri tunda bai ma san asirin namu ba balle ya tone shi. Sassanyan murmushi tayi me kyau ta kwanta kan gado cikin ranta tana jijjinawa kaifin kwakwalwa da basirar da Allah yayiwa Ajlaal, " naji kinyi murmushi, murmushin ta sake yi a karo na biyu, " yauwa kin sake yin wani, suka saka dariya a tare, " gobe zani wankin k'afa in sha Allahu, wata k'illa ma nayi jan lalle, "dan Allah kiyi min jan lalle yana bala'in yi miki kyau sosai, " in sha Allah zanyi maka, yana k'ok'arin kashe wayar tace " dama da maganar da nake sanyi dakai please. "Okey Ina jinki! Sai da tayi gyaran murya kana tace " kaga saboda rashin bawa Deen kaina da banayi ya fara zargin da akwai wani abu, kuma yana bala'in saka min ido yanzu sosai, d'an shiru tayi yace " uhunnn ina jinki cigaba da managarki, dan ya riga yasan k'arshen maganar, cikin in i na da rawar murya tace " shine dama nace idan ka bani izini ka yarda ka amince ka barni na rink'a bashi kaina ko sau d'aya a sati ne dan Allah, bayyi mata magana ba ya kashe wayarshi, wayar ya jefa saman gado had'i da jan tsoki "mstwwwww banza butulu kawai duk abinda nake yi mata, duk iya k'ok'arin da nake yi akanta amma a banza hankalinta yana kan mijinta sakarya mara wayo kawai. A b'angaren ta kam wayar ta cire daga kunnenta tare da zubawa wayar ido, ta dad'e tana tunani, ta sak'a wancan ta kunce wancan har dare. Da sassafe ta tashi ta gama duk abinda zatayi da wuri, tayi wanka ta shirya tsaf ta zauna tana zaman jiran fitowarshi a falon, ganin lokaci yana neman k'ure mata gashi tana san tayi har jan lallen yasata mik'ewa ta nufi hanyar bedroom d'inshi da raban data bi har ta manta, cikin d'an tsoro-tsoro tayi knocking, sai da ta d'auki lokaci tana kwankwasa k'ofar d'akin kana cikin isa ya bud'e baki dakyar kamar baya so yace " waye? "D'an wulak'anci, in banda wulak'anci wa yake tsammanin zai buga mishi k'ofar d'aki? Ta fad'a cikin ranta, a zahiri kuma cewa tayi " nice, a dak'ile yace " meye? "Saloon nake san zuwa wankin k'afa da k'unshi, sai da ya d'auki lokaci bayyi magana ba, harta fidda rai daga samun amsar shi ta juya zata bar wajen taji yace " kije kawai, ina da abubuwan da zanyi masu mahimmaci, bata bashi amsa ba tabar wajen, jakarta da wayarta ta d'auka ta fice bayan ta zira hijab, bata jin zata iya tuk'i dan haka bata d'auki mukullin mota ba ta fice daga get d'in gidan, tana tafiya a k'afa yana biye da ita a baya a mota har ta fita bakin titi ta tare me Napep ta hau, yana biye da ita har shagon saloon d'in, me Napep d'in ya aje ta a wajen ta bud'e jakarta ta d'auko kud'i ta biyashi ta shige, nesa da wajen yayi parking yana jiran fitowarta, kanta da k'afarta aka fara wanke mata kana aka zana mata jan lalle me kyau yadda kasan d'orashi akayi a k'afar. Bayan ta biya ta fito kunenta lik'e da waya tana murmushi tace " kaima kasan saika fara gani kafin shi, idan ma ya gani ai iyakacinshi ganin kawai, gani kuma ai ba tab'awa ba, ba ci ba, yana dariya sosai yace " nace ki bari nazo na d'aukeki amma kin k'i ko? "Karka damu gani nan ai, ta fad'a tana tsayar dame Napep, ta fad'a mishi inda zai kaita ta hau, Deen yayi saurin bin bayanta tare da kallan number jikin Napep d'in 37 ya maimaita a zahiri, tana ta waya da Ajlaal hankalinta kwance har suka hau babban titi, Ajlaal yace “ idan kun sha Round kicewa me Napep d'in yayi hagu. "Hagu kuma? Ta fad'a cikin mamaki, kana ta d'ora da"  meyasa? "Kedai kiyi abinda nace miki please? Wayar na manne a kunnenta tacewa me Napep d'in " Malam idan mun sha Round muyi hagu please, " to Hajiya ba damuwa, suna shan round suka ga masu Napep sunfi  guda 500 iri d'aya sak da wacce take ciki kowacce d’auke da number d’aya 37, ba Deen kad'ai ba har Deeyanah da me Napep d'in sai da kansu ya kulle,  wani irin mugun burki Deen ya taka yana bin Napep's d'in da kallo cike da mamaki da tsoro, bakinshi bud'e, yama rasa abinyi, a tare gaba d'aya Napep d'in suka sha round kana suka rabu kashi 5, d'ari-d'ari suka bi titina, " Ajlaal yace " yanzu kuna iya bin hanya normal ku taho, sitiyari Deen ya doka da k'arfi cike da takaici, kana ya juya kan motar ya koma gida. "Deen ya biyo ni ko? "Eh! " wato shiyasa kayi duk wannan shirin danka bashi k'afa? "Uhunnn! Yace yana kurb'ar lemo, idanuwanta ta juya cike da fargaba. Har k'ofar gida me Napep d'in ya kaita ta zaro kud'inshi ta biyashi kana ta shige cikin gidan, kanta tsaye kamar gidanta ta danna kai cikin gidan, ko'ina tsaf a gyare sai kamshi ke tashi, sosai tsaftar Ajlaal ke burgeta, ganin baya falo yasata wucewa bedroom d'in da yafi zama, tana shiga yana fitowa daga wanka d'aure da towel a k'ugunshi, " tab aiko baka isa ba, kasan ina tafe shine kayi wanka kai kad'ai baka jira ni ba ko? Kyakkyawan murmushi yayi tare da janyo ta jikinshi ya rungume ta ta baya, mazaunanta na saitin mararshi, idonshi ya lumshe had'i da sauke ajiyar zuciya, muryarshi can k'asan mak'oshi yace " I missed you Dee!. Juyowa tayi ta fuskance shi sosai tana murmushi tace " ban yarda ba sai ka koma mun sake yin wanka tare, yana goga kumatun shi a fuskarta while idanuwanshi lumshe yace " naji amma mu fara kashe wutar dake cin mu in yaso sai muyi wankan me dalili, ya fad'a muryarshi bata fita sosai, ta bud'e baki zatayi magana ya saka mata harshenshi cikin bakinta, a nutse suka soma kissing junansu suna sucking lips d'insu, cikin salo ta zame towel d'in dake jikinshi tayar dashi a k'asa, tasa hannu tana shafa cibiyarshi zuwa mararshi, wani irin nishi ya fitar da k'arfi, tayi k'asa da hannunta ta cafki joy stick d'inshi ta soma murzata a hankali tana shafa ta cikin salo, har lokacin bakinsu na cikin na juna. Zame jikinta tayi daga cikin nashi yana k'ok'arin sake manna jikinshi da nata ta sanya hannunta a k'irjinshi tana d'an turashi baya har suka isa bakin gado, ta sanya hannu ta hankad'ashi saman gadon ya fad'a, ta bishi ta danne, ta hau saman ruwan cikinshi ta zauna dangwargwar tare da mayar da bakinta cikin nashi, hannu ya sanya ya kifa kanta yadda zaiji dad'in shan bakinta sosai, da hannunshi d'aya ya zame mata rigar jikinta yayi cilli da ita, yasa hannu ya b'alle mata bra, standard boobs d'inta suka bayyana, bakinta ta cire daga cikin nashi,, idonta cikin nashi tayi k'asa ta damk'i joy stick ta saka a bakinta da k'arfi ya saki ihuuuu, gami da k'ank'ame ta sosai ya cigaba da sakin ihuuun da iya k'arfinshi, sosai suka rikita junansu da dad'i tare da mantar da kansu komai da kowa suka tsunduma cikin tsakiyar duniyar dad'i, da kanshi ya d'ago ta ya d'orata saman joy stick d'inshi ta zauna kanta tana pumping, yayinda shi kuma duka hannunshi ke kan boobs d'inta yana aikin murza su da mammatsa su, kifo da ita yayi kanshi ya saka boobs d'inta a bakinshi ya soma tsotsar su yana lasar kan nipples d'inta, aiko itama ta soma ihuuun while tana cigaba da sukuwa akan ruwan cikinshi, basu sassautawa juna, sun sarara ba sai da suka samu biyan buk'atarsu kowannensu ya samu cikekkiyar gamsuwa kana suka lafa. Kwance tayi samanshi tana mayar da numfashi, ya sanya hannunshi ya matse ta da jikinshi sosai, shima yana sauke ajiyar zuciya, sun jima a haka kana ta zame ta kwanta saman gadon tare da zubawa kyakkyawar fuskarshi ido tana mamakin tsananin kyanshi, kwata-kwata Ajlaal baya kama da Hausawa Fulani yafi kama da buzaye 'yan Niger ko Larabawa da Indiyawa, iskar bakinshi ya hura mata a fuskarta yana cewa " lafiya irin wannan kallo haka? Murmushi tayi had'i da kai hannunta saman fuskarshi ta shafa fuskarshi tace " ina mamakin kyan ka ne, baka kama da Abba da Mamanka, kai bama ka kama da 'yan Nigeria wallahi, dariya yayi sosai kana yace " haka ake ce min tun ina yaro, mutane da yawa na fad'ar haka wai bana kama da kowa,  zatayi magana yaja siririn dogon hancinta yace " ai kema haka bakya kama da 'yan k'asar nan, ji fa yadda farinki ke d'aukar ido saboda fari har jijiyoyinki ana gani fa, 'yar guntuwar dariya tayi kana tace " ai kakanninmu na wajen uba Larawaban Algeria ne, shiyasa zaka ga muna kama da Yaya Deen. Tsuke fuska yayi sosai, taja hancinshi tana fashewa da dariya tace " sarkin kishi kawai, idan Deen yasan abinda mukeyi shi rataye kanshi zayyi kenan? Baki ya tab'e yace " oho mishi, shiya sani. "Yauwa dama ina san mu k'arasa magana akanshi...... Dakatar da ita yayi ta hanyar d'aga mata hannu yace " please karki soma zo min da abinda bazai yiyu ba, zatayi magana yayi saurin cewa " kina san ganin gawarshi kenan? Ido kawai ta zuba mishi batare data bashi amsa ba, ta mik'e tana jan zanin gadon ta rufe jikinta ta fad'a bathroom, " ba kince tare zamuyi wankan ba? Batare data juyo ba tace " ka bari kawai, murmushi yayi me kama da dariya ya mik'e yabi bayanta, ta baya ya rungume ta yana bata hak'uri, " kiyi hak'uri please ki gane irin girman san da nake yi miki Deeyanah, wallahi daki bashi kanki gwara na mutu, bai barta ba, sai da ya lallab'a ta ya bata hak'uri har tayi dariya kana suka shiga wankan, da kanshi yayi mata wankan. ************************************** Bai shigar da motarshi cikin get ba, a k'ofar Estate d'insu yayi parking ya fito da d'an saurinshi ya shiga gidan, me gadinsu yana alwala, ya d'an tsaya ya kalli me gadin tare cewa " Baba dan Allah..... fasa tambayarshi yayi Deeyanah ta dawo gida dan ganin rashin cancantar hakan, dan bai shefe shi ba, tambayar yana iya zubar mata da mutunci a idanun masu gadin gidan, wucewa main part d'insu ya duba babu alamar ma an shigo, duk da haka ya dudduba ko'ina danya tabbatar, ganin bata nan ya sashi fitowa daga part d'in nasu ya shiga na Ammu, sama-sama suka gaisa ya tambayeta idan Deeyanah ta shigo, Ammu ta bashi amsa da " bata shigo ba ka duba part d'in Ammi wata k'ila tana can, bayyi magana ba ya fice, camma daya shiga bata can, d'aya bayan d'aya ya rink'a shiga part - part yana neman Deeyanah amma babu ita babu dalilinta. Fita yayi ya shiga mota yayi mata key ya nufi gidan Raleeya, daga gefen get  yayi parking ya fito ya taka da k'afarshi zuwa k'ofar gidan, a hankali ya mik'a  hannu da nufin ya kwankwasa get d'in, yana d'ora hannunshi da nufin kwankwasawa k'ofar jikin get d'in ta bud'e mamaki fal fuskarshi ya tura k'ofar zai shiga, dai-dai lokacin Deeyanah ta sako k'afarta wajen get d'in sukayi kacib'us yayi saurin yin baya, baya tayi ta baje a k'asa ta fad'i sosai k'afarta ta bugu taji azaba da rad'ad'i sosai amma ganin wanda ke tsaye kanta yasata saurin mik'ewa tsaye tare da had'iye yawu kwat bayanta ta juya tana kallan inda tabar Ajlaal tsaye taga baya nan, ido ta runtse da k'arfi had'i had'iye yawu a karo na biyu ganin yana k'ok'arin shigowa gidan yasata fitowa tare da jan k'ofar ta rufe ta da sauri, yayinda duk ilahirin jikinta ke mugun b'ari da kerrrma, firgici k'arara kwance saman fuskarta, bakinta na rawa tace " m....u......j....e ko....? Ta fad'a a rarrabe kamar me koyan magana, kallan tsanaki yayi mata batare da yayi magana ba ya nuna mata hanya da hannunshi alamar muje, tana gaba yana binta a baya, sai faman guge gumi take yi, handkerchief ya mik'a mata bayan sun zauna yace " naga kamar gumi ya dame ki ko? Hannunta na rawa ta karb'i handkerchief had'i da yin gajeren murmushin yak'e ta goge goshinta, mik'a mishi handkerchief d'in tayi ya kalle ta yana murmushi yace " da dai kin barshi a hannunki zaifi yi miki amfani fiye dani, ya k'arashe maganar tare da kanne mata ido d'aya, wata irin razananniyar fad'uwa gabanta yayi yadda kasan k'irjinta zai rabe biyu, ta sanshi, tasan waye shi, tasan halinshi ciki da bai ta tabbata akwai wani abu bunne a k'asan zuciyarshi, wai ma yaushe rabanta dataga murmushin shi, balle ya kalle ta fuskarshi shinfid'e da murmushi kamar haka, tasan akwai wani abu. Hannunta ta rink'a murzawa da k'arfi har tana karcewa da farcenta, duk abinda takeyi idonshi na kanta, har suka k'arasa gida babu wanda yace ko k'ala, bayan sun isa gida kowa ya nufi bedroom d'inshi babu wanda yace kowa komai. Bayan sati d'aya.... Tun ranar da dataje gidan Ajlaal bata sake fita ko nan da can ba dan tasan tunda yayi mata wannan murmushin akwai abinda yake shiryawa cikin ranshi, dan haka ta tattaro gaba d'aya nutsuwarta ta sanyawa kanta gudun kar a samu matsala, tana zaune a falo tana kallan Indian Hausa me suna Gawa Tafe na Algaita a tashar Tauraruwa Tv ya zo ya wuce ta gabanta, bayyi mata magana ba, itama batayi mishi ba, ya fice yana sauri. Wajen wasu bak’inshi yaje da suka zo daga America bai dawo ba sai yamma, ta wajen gidan Raleeya ya biyo, duk yadda yake k'ok'ari da zuciyarshi kan karya biya gidan Raleeya amma abun yaci tura sai da zuciyarshi ta rinjaye shi, bai san yadda akayi ba sai ganin kanshi yayi, yayi parking a k'ofar gidan, sai da ya d'an tsaya kana ya fito daga motar zuciyarshi na tsalle kamar zata tsaga k'irjinshi ta fito, kwankwasa k'ofar gidan yayi sau biyu zuwa uku, shiru babu alamar za'a bud'e har ya juya zai bar wajen yaji ana bud'e get, juyowa yayi tare da zubawa get d'in ido, wata tsohuwar dattijuwar mata ce ta fito, bayan sun gaisa ta d'ora da cewa " aiko masu gidan basa nan sun fita, nima fitowar nan da kaga nayi gida zani na gama aiki na, daga kalaman matar ya fahimci 'yar aiki ce, murmushi yayi ba tare daya ce komai ba ya juya yabar wajen. Labulen window Ajlaal ya saki yana dariya yace " kayi iya yinka me 'yar k'aramar kwakwalwa da gajeren tunani amma bazaka tab'a cimma sawaye na ba balle takuna, na riga nayi gaba tunani na ya girmewa saninka Deen, duk abinda zakayi bazaka tab'a samun koda 'yar k'aramar makama ba balle hujja. Shi kam Deen motarshi ya shiga yayi mata key yabar wajen, kunnenta manne da Bluetooth tana waya da Ajlaal yana bata labarin zuwan Deen ya shigo ya wuce ta, tabi bayanshi da kallo tana kanne dariyar dake cinta, yana shigewa d'akinshi ta bushe da dariya harda buga k'afa tace " munafukin banza Allah ya fika ja'iri. Bayan wata biyu.... Haka rayuwarsu ta cigaba da tafiya babu dad'i tsakanin Deen da Deeyanah sai dai d'an abinda ba'a rasa ba, yayinda suke cigaba da more rayuwarsu tsakaninta da Ajlaal suna cin duniyarsu da tsinke babu abinda ya dame su, duk yadda zayyi yayi, yayi bincike da bin kwakkwafi amma a banza dan bai iya gano komai ba, dan haka ya tattara komai ya watsar ya cigaba da harkokin rayuwarshi ya manta da ita, sai dai har zuwa lokacin shike kaita unguwa, idan ya kaita gidan Ajlaal suyi ta lek'enshi ta window suna yi mishi shak'iyanci, wai shi da kanshi ya kawo matarshi inda za'ayi amfani da ita ya zauna ya jira a gama ya d'auko ta, suyi ta lek'enshi suna dariya. Tun yawan zuwanta gidan Raleeya da rashin zuwan Raleeya nasu gidan yana damunshi har ya daina damunshi, yauma shi da kanshi ya d'auko ta ya kawo ta gidan Raleeya da zata fita daga motar ya kalle yace " karki dad'e please sauri nake yi, murmushi tayi mishi tace " tom in sha Allah bazan dad'e ba, bayyi mata magana ba ya cigaba da yin abinda yake yi. Yana zaune a falo ta shigo ya mik'e ya tare ta yana murmushi tare da wara mata hannu aiko ta fad'a jikinshi tana sauke ajiyar zuciya, ya mayar da hannunshi ya rungume ta tsaf a jikinshi yana fad'in " wannan driver naki baya aikinshi yadda ya kamata ina ganin sai mun canja shi, dariya tayi gami da d'an dukan k'irjinshi tace " ka fara ko!? "Eh mana! baya sauri kwata-kwata tun d'azu nake ta faman jira amma shiru, " inaga bashi da energy ne kasan fa ya tara tsatsa a mararshi kuma ka kafa ka tsare balle a taimaka mishi a yashe mai ita, " au haka ne fa, ya fad'a yana rik'e baki suka saka dariya su dukkansu. "yau so nake nayi sex dake while idona na kanshi ina yi mishi gwalo, " everything's is yours, duk yadda kake so haka za'ayi, dariya yayi yana shinshina wuyanta yace " ina san k'amshinki abar k'aunata, ya fad'a yana had'a ta da jikin window kafin ya had'e bakinshi ya soma aika mata France kiss me gusar da tunani. idonsu kanshi suna kallanshi suna yi mishi gwalo while suna sex har suka gama, tayi wanka ta fito, ta iske shi tsaye jikin motar yana waya, yana hangota tana tahowa ya shige mota ta shiga yaja suka tafi yana cigaba da wayarshi. **************************************** Hankalinta kwance take tuk'in tana bin wak'ar Ranar Aure na ta mawak'i Umar me Sanyi da gidan radio suka saka, takai hannu ta k'ara volume, tana rausaya kanta alamar tana bala'in jin dad'in wak'ar, ana gama wak'ar gidan Radio suka sak'o wa'azin Malam Ibrahim Daurawa me taken ILLAR ZINA, wata irin muguwar fad'uwa gabanta yayi, Malamin yayi gyaran murya yayi sallama kana ya fara magana " in Allah ya yarda yau zamuyi magana akan illolin zina, zamu tab'o har b'angaren matan auren dake ZINA DA AURENSU, dammmm! dammmm! dammmm! gabanta ya shiga dokawa da tsananin k'arfi. " Tsira da amincin ALLAH sutabbata ga ANNABIN dababu wani bayanshi Salati da tsira da amincin Allah su tabbata bisa Jagoran Annabawa da Manzanni, Shugabanmu Annabi Muhammadu (ﷺ)tare da iyalan gidansa tsarkaka da Sahabbansa Maɗukaka. ILoLin zina da kuma Hukuncinta Ya tabbata a cikin hadisi an tambayi Annabi (ﷺ) a kan wane zunubi ne ya fi girma, sai Manzon Allah (ﷺ) ya ce, "Shirka da Allah, Alhali shine ya halicce ka, " Sai aka ce sai wanne? Sai ya ce "Sannan kashe ɗanka don kada ya ci tare da kai." Sai aka ce "sannan sai  wanne ? " Sai ya ce "Ka yi zina da matar makwabcinka,  (Bukhari) yadda ruwaito. Allah Maɗaukakin sarki ya sanya hukuncin wanda duk ya yi zina kuma ya taɓa aure ko yana da aure a jefe shi, namiji ko mace, idan kuwa bai taɓa aure ba, sai a yi masa bulala ɗari, sannan a baquntar da shi a wani gari daban tsawon shekara guda. Duk wanda ya kalli hukuncin zina, zai ga Allah Ya keɓance shi da wasu abubuwa masu yawa, saboda munin zina, ga kad'an daga cikin abubuwan da hukuncin ya kunsa. 1. Kausasawa wajen ukubar mazinaci, ta hanyar jefewa, ko kuma bulala da bakuntarwa shekara guda. 2. Hana jin tausayin mazinaci ko mazinaciya yayin da ake musu ukuba Allah yace :- ٱلزَّانِيَةُ وَٱلزَّانِى فَٱجْلِدُوا۟ كُلَّ وَٰحِدٍ مِّنْهُمَا مِا۟ئَةَ جَلْدَةٍ ۖ وَلَا تَأْخُذْكُم بِهِمَا رَأْفَةٌ فِى دِينِ ٱللَّهِ إِن كُنتُمْ تُؤْمِنُونَ بِٱللَّهِ وَٱلْيَوْمِ ٱلْءَاخِرِ ۖ وَلْيَشْهَدْ عَذَابَهُمَا طَآئِفَةٌ مِّنَ ٱلْمُؤْمِنِين "Mazinaciya da mazinaci to ku yi bulala d'ari ga kowanne ɗaya daga gare su, kuma kada tausayi ya kama ku game da su a cikin addinin Allah idan kun kasance kuna yin imani da Allah da ranar lahira, sannan wani yankin jama'a daga muminai su halarci azabarsu.  (Annur : 2). . Ayi musu ukuba a gaban mutane ba'a yarda a yi musu a boye ba. Imamul Bukhari ya kawo a cikin ingantaccen littafinsa daga Maimun Al-audiy ya ce, "A lokacin jahiliyya na taɓa ganin wani biri da ya yi zina da wata biranya, sai sauran biran suka taru suka jefe su. Mafi munin zina ita ce wadda mutum zai yi da mahaifiyarsa, sai da muharramarsa, sai wadda zai yi da matar makwabcinsa, Allah ya kare mu. ILLoLin Zina: Babu shakka duk mai hankali ya san cewa zina tana tattare da illoli masu yawa, waɗanda suke shafar mazinacin ko mazinaciya, ko su shafi al'umma gaba daya. 1. Zubar da mutunci da jawo wa kai k'ask'anci, Duk matar da ta yi zina to ta jawo wa kanta da danginta da mijinta ƙasƙanci, ta kuma zubar musu da mutunci a idon duniya, Idan har ta sami ciki ta haihu, sannan ta kashe ɗan, to ta haɗa laifi biyu, laifin zina da laifin kisan kai, In kuma ta bar shi, to kuma ta shigar wa mijinta ko danginta, wanda ba ya cikinsu, Idan kuwa mai zinar namiji ne to ya lalata mace, ya jawo mata lalacewa da taɓewa, wanda hakan lalata duniya ne gaba daya. 2. Zina ta haɗa dukkan sharri gaba ɗaya, saboda a cikin zina akwai rashin tsoron Allah, rashin kunya, rashin tsantseni, rashin cika alk'awarin, ƙarya da butulci da sauransu, Duk kuwa waɗannan munanan halaye ne a Musulunci. Manzon Allah (ﷺ) yace Allah ya la'anci mai sake al'aura da mai kallon al'auran wani. Baihaqi ya ruwaitoshi An karɓo daga mu'azu ɗan jabal (r.a) ya karɓo daga manzon ALLAH (ﷺ) sai yace " ranar alk'iyama ranar hasara ce da nadama Allah zai ta da al'umma daga ƙabarburansu siffa goma sha biyu (12). Siffa na biyar daga ciki. Za'a tashe su daga cikin ƙabarinsu suna wari kamar dunge mai kira yayi kira da fuskar Ubangiji waɗannan sune masu zina sun mutu batare da sun tuba ba, basuji kunyar Allah maɗaukaki ba wannan shine sakamakonsu makomar su zuwa ga wuta. (Faɗin ALLAH maɗaukakin sarki) ﻳَﺴْﺘَﺨْﻔُﻮﻥَ ﻣِﻦَ ﺍﻟﻨَّﺎﺱِ ﻭَﻟَﺎ ﻳَﺴْﺘَﺨْﻔُﻮﻥَ ﻣِﻦَ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﻭَﻫُﻮَ ﻣَﻌَﻬُﻢْ ( ﺍﻟﻨﺴﺎﺀ – ﺍﻵﻳﺔ108 ) Suna neman ɓoyewa daga mutane kuma ba su neman ɓoyewa daga Allah, alhali kuwa shi yana tare da su. Siffa na takwas Za'a tashesu daga cikin kabarinsu wani ruwa mai yauk'i (na bala'i) yana fita daga farjinsu mai kira yayi kira da fuskar Ubangiji " waɗannan sune masu zina sun mutu batare da sun tuba ba wannan shine sakamakon su makomar su zuwa ga wuta. (Faɗin ALLAH maɗaukakin sarki) ﻭَﻟَﺎ ﺗَﻘْﺮَﺑُﻮﺍ ﺍﻟﺰِّﻧَﺎ ۖ ﺇِﻧَّﻪُ ﻛَﺎﻥَ ﻓَﺎﺣِﺸَﺔً ﻭَﺳَﺎﺀَ ﺳَﺒِﻴﻠًﺎ ‏(ﺍﻹﺳﺮﺍﺀ 32- ) Kuma kada ku kusanci zina, lalle ne ita ta kasance alfasha ce kuma ta munana ga zama hanya. Duk matar auren da tayi zina ba zata sadu da mijin ta ba har sai tayi istibra'i..! Annabi SAW yayi hani da cin wannan kudin da aka bata na wannan zinan, Zina dai wani aiki ne da Allah ya hana muslmi ko musulma aikatawa, kai ba ma aikata zinan ba, hatta kusantar ta ma Allah mad'aukakin sarki ya hana Allah ya  gargad'e mu a cikin Alkur'ni mai tsarki cewa 'kada ku kusanci zina ( wala ta k'arabuzzina). Zina dai tana cikin manyan zunubbai, wato ALKABA'IRA, sannan kuma manzon Allah SAW yace " mutum baya aikata Zina sai an cire mishi imaninshi gaba d'aya idan kuma ya gama aka za'a mayar mishi, ba'a mayar mishi da gaba d'aya imanin nashi, ashe ke nan da mazinaci zai mutu a wannan halin ya mutu a mara imani." Babu abinda mutum yake samu a zina banda taɓewa da nadama da yake biyo baya, zina babu wani alheri dake tare da ita banda ƙasƙan ci da wulakanci da mutum yake tsintar kansa akai tun daga nan duniya kafin aje lahira. Zina tana jawo masifu da bala'i wanda duk mai hankali idan yayi tunani bai kamata ya kai kansa cikin ta ba koda babu Shari'ar da zata hana yin taba. Illar da zina take jawowa yafi dukkan yadda mutum zayyi tunani. Shiyasa cikin hikima da Buwaya irin ta Ubangiji yace kada a kusance tama balle a aikata ta saboda irin illar da take jawowa dan Adam. Zina tana jawo fushin Ubangiji ya sauka ga bawa komai yaki da dadi, tana jawo tawayar arziki da rashin sanin manufa a rayuwa, tana saka kuncin zuciya da munana zato ga mutane, tana tafiyar da kwarjini da ƙima a idan mutane, illar zina yana shafar har zuria ta kuma jawo musu ƙasƙan ci, tana tafiyar da imani da kunya ga mutum, tana sa mutum ya rayu cikin nadama da wulakanci. Illar zina da munin ta yafi karfin a rubuta su, ku nisan ci zina domin babu wani alheri dake tare da ita. Allah ya tsare mu ya kare mu. Aameen!. Sosai Malamin ya zage yayi wa'azi akan zina ya fad'i azabobin da Allah ya tanadarwa masu aikata ta, da irin bak'ar masifar da zasu tsinta tun daga zarar ransu zuwa kwanciyar kabarinsu. Rawar da jikinta keyi ce ta haifarwa da motar yin tangal- tangal a saman titi tana yawo daga wannan hannun zuwa wannan hannun dakyar ta samu ta iya tsaida motar a tsakiyar titi masu mashina da motoci da Napep sai zaginta suke amma bama tasan suna yi ba, jin babu iskar da zata shak'a kwata-kwata yasata bud'e motar da sauri jikinta na wani irin b'ari da kyarma, yadda kasan wacce ke shirin hawa iska, ko motar bata tsaya rufewa ba ta durk'ushe a k'asa tsakiyar titi tana mayar da numfashi kamar me Asthma, sosai take hakki while hannunta dafe da k'irjinta, wani abu take ji me zafi da k'arfi yana fita daga k'irjinta, yayinda da zuciyarta ke bud'ewa tana tarwatse, gaba d'aya tsikar jikinta a tashe take saboda tsabar tashin hankali, idanuwanta sukayi jajir kamar gauta, har wani yaji take ji kamar wacce aka shak'awa tiyagas. Baki take san bud'ewa ta furta Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un amma abun ya gagara ko kalma d'aya ta gagara fitowa daga bakinta, a jikinta take jin yadda jijiyoyin jikinta ke tsinkewa jinin jikinta na tafasa, babu bata gab'a ta jikinta da bata karye ba, in banda rawa da kerrrrma babu abinda jikinta keyi, so take tayi kuka amma ta kasa, sosai take kokawa da numfashi, tayi iya bakin k'ok'arinta dan ta samu sassauci da sauk'i amma babu sauk'in. Dakyar ta yunk'ura zata mik'e aiko sai amai ta shiga kelaya amai sosai, cikin aman ta durk'ushe ta saki wani irin mahaukacin kuka me rikitarwa yadda kasan ranta ake zarewa, kallo d'aya zakayi mata kasan da duka zuciyarta take kukan, cikin ihuuuu da hargowa take fad'in " Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un 'yar wuta ce ni. "Wuta zan shiga! 'yar wuta ce, in na mutu a haka wallahi wuta zan shiga, na shiga uku! idan ban tuba ba wuta zan shiga, zanyi mummunan k'arshe, na shiga uku na lalace na cuci kaina da rayuwa ta, nayiwa kaina da kaina babbar illa, illar da har abada bazata dawo dai-dai ba, na tarwatsa komai, tarwatsawar da bazata tab'a dawowa dai-dai ba, na shiga uku, na jawowa kaina abin kunya, na jawowa iyaye na da ahalina abun fad'a, Allah ka yafe min, ta k'arasa maganar had'i da d'iban k'asa tana zubawa kanta tare da dukan kanta da hannu bibbiyu. Kuka takeyi sosai dake fitowa daga can k'ark'ashin zuciyarta, tana ihuuu tana d'iban k'asa tana zubawa jikinta, in banda Allah ya taimake ta unguwar babu mutane da an taru ana kallanta, har masu yi mata video ma da an samu, ta dad'e cikin wannan mummunan yanayi kafin ta mik'e fuska kace-kace da majina da hawaye, dakyar take iya tuk'in tana tafe hawaye na zuba danta kasa tsaida hawayenta, bama tayi k'ok'arin tsayar dasu ba, dan ita zubar ma da sukeyi sauk'i ne a gare ta. A bakin get tayi parking motar ta fito ko rufe motar batayi ba ta tura k'ofar shiga gidan wacce ba get ba ta shige, yadda take tafiya tana had'a hanya ga k'afarta babu takalmi yasa ma'aikatan kallanta baki bud'e, tana tafe tana tangad'i while hawaye na d'iga ta mik'awa d'aya daga cikin drivers d'in gidan key d'in motar batare data ce komai ba, hannu na rawa ya amsa, ta shige gida, dama can cikin motar tabar takalmin da jakarta da wayoyinta, duk abinda ke faruwa Ajlaal na jinta, shu'umin murmushi ya saki had'i da d'ora k'afa d'aya kan d'aya yace " kin makara Deeyanah, kin riga kin makara, wallahi baki isa ki raba kanki dani ba, dan zan iya yak'ar duniya na k'arar da kowa da komai daga doran k'asa, duk wanda yace zai shiga gaba na akanta ni kuma nayi alwashin kawar dashi daga hanya ta, zanyi komai danna mallakeki, ya k'arashe maganar yana fashewa da mahaukaciyar dariya. Direct bedroom d'inta ta wuce ta shiga bathroom ta sakarwa kanta shower batare data cire kayan jikinta ba, har lokacin jikinta b'ari yake, ta dafa bango tana cigaba da kukan, takai awanni biyu ruwan shower na sauka kanta kana ta mik'e tsaye daga zaman dirshan d'in da tayi a k'asa, kayan jikinta ta cire tsaf ta zuba su a shara gaba d'aya kyankyamin kanta da jikinta da komai ma take yi, har kayan jikinta da bathroom d'in da gaba d'aya bata san ganin komai, dan duk abinda ta kalla hotan irin abinda sukayi da Ajlaal ke dawo mata cikin kanta, ido ta runtse da k'arfi hawaye na zubo mata, cikin zafin rai ta bud'e idanuwanta da suka gama rinewa zuwa ja, da wani irin zafin rai ta nufi inda take aje soson k'arfen wanke masai tasa hannu ta damk'e shi, da wani irin k'arfi ta soma dirzawa jikinta da iya k'arfinta. Tana kuka tamkar ranta zai fita tana dirzar fatar jikinta jini na zuba da fushi take dirzar fatar kamar zata b'aye fatar jikinta, duk tabi taji ciwo amma hakan bai dame ta ba, ta dad'e tana wankan kana ta sulele tana kuka, tayi wankan tsarki yafi sau 20 gani take har zuwa lokacin daud'ar zina bata bar jikinta ba, gani take duk yawan wankan tsarkin da zatayi bazata tab'a samun tsarkin jiki dana ruhi ba, sai da ta gaji dan kanta kana ta hak'ura ta fito daga wankan, tana d'ora idonta akan gadon dake d'akin, ta ganta kwance Ajlaal na saman ruwan cikinta suna aikata zina, ido ta runtse da k'arfi had'i da kawar da kanta gefe tace " turrrr dani, kaico na, tun yanzu tun kan aje ko'ina mugun abinda na aikata ya fara farautar rayuwata, ya fara barazana ga farin ciki na. Durk'ushewa tayi tana kuka wiwi tare da dukan k'irjinta tana fad'in " na tarwatsa gidana, na tarwatsa ahalina, na fasa gidana, na wargaza farin cikin mijina dana d'ana, na b'ata aure na, na b'ata sunan zuri'armu gaba d'aya, Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un na shiga uku na lalace, Allah na tuba ka yafe min, Astagfirullah Astagfirullah Astagfirullah, ta k'arashe maganar da wani irin kuka. Ji tayi ta tsani gaba d'aya gidan komai ya fice mata a ranta ta tsani kanta, duk wata kusurwa ta gidan data kalla hoton ta da Ajlaal take gani suna aikata masha'a, har aka kira magriba tana nan zaune ta had'a kai da gwiwa tana ta faman risgar kuka wiwi tun muryarta na fita har yakai ya kawo muryarta ta dishashe idanuwanta sun kumbura suntum, dakyar ta rarrafa ta shiga ban d'aki ta d'auro alwala, ta fito ta shinfid'a sallaya ta zira doguwar riga ta tada sallah, tana tada sallar saban kuka ya kwace mata, dan sai yanzu taji tana jin kunyar Ubangiji, ta tayar da sallah yakai sau biyar kuka yana sata sallamewa sai haka ta hak'ura tayi sallar hawaye na zuba, da takai sujjada me memakon karatun sujjada sai Allah na tuba ka yafe min take maimaitawa. D'ogowa tayi ta sake sabuwar sallah amma tana kai goshinta k'asa kuka ya kwace mata, dole tayi control kukan tayi sallar, data sallame sallar sake komawa tayi sujjada takai goshinta k'asa ta soma addu'a " Ya ALLAH! kasanya mu cikin bayinka tsarkaka masu dace da ni'imar ka, gafarar ka, rahamar ka, bud'i da wadatar zuci, da tsarkin zucciya, da shiriyar mu baki d'aya, ya Ubangijin talik'ai ya majib'ancin lamura, kai ne Afuwu me afuwa, kai ne Rahamanu me Rahama, kai ne mad'aukakin sarki wanda ba'a haifa ba kuma bai haifa ba, Allah ka yafe min, ka tsarkaken zuciya ta, kayi min afuwa da sassauci, kayiwa ruhina salama, ina jin kunyarka ya Ubangiji, ina jin kunyar girman laifi na, ina jin kunyar neman afuwa agare ka, Astagfirullah Astagfirullah! Astagfirullahna wa'atubi ilaik, ta k'arashe da wani irin kuka. Ranar kam cur Deeyanah ta kwana saman sallaya tana neman yafiya da afuwar Ubangijinta, ko gyangyad'i batayi ba, duk iya satar bacci da ake fad'a yau kam ko kusa da ita bai zo ba balle ya sace ta, bayan ta idar da sallar asuba cigaba da zama tayi akan sallayar tana jan La'ilaha Illa antassubahanaka innikuntu minal zalimin har garin Allah ya waye. Tana zaune kan sallayar taji ana kwankwasa k'ofar part d'insu agogon bango ta kalla taga k'arfe takwas da rabi, a fili ta sauke ajiyar zuciya kana ta mik'e ta fita hannunta rik'e da carbi, sai da ya rusuna kana ya gaida ita, bata iya amsawa kamar yadda ta saba ba, ya mik'a mata jakarta da takalmin da wayarta yace " jiya nazo har sau uku in kawo miki amma baki bud'e ba, da har zan sanar dasu Abba sai kuma na tuna Bature yana ciki ai, (Bature sunan da suke kiran Deen dashi kenan) murmushin yak'e tayi mishi ta karb'i kayan batare datayi magana ba ta juya ta koma cikin gidan, d'akinta ta sake komawa ta aje kayan tana shirin shiga ban d'aki wayarta ta soma rori, babu alamun tsoro ko firgici tattare da ita duk da ta riga tasan waye me kiran. Bata kula wayar ba ta shige toilet, har ta fito daga toilet ba'a daina kiran wayar ba, amma ko'a jikinta yadda kasan ba wayarta ake kira ba, tana jan carbi ta isa inda wayar take ta d'auka da nufin kashe ta gaba d'aya, " 150 missed call, ta fad'a a zahiri cikin ranta tana jinjina daga jiya zuwa yau kawai yayi mata miss call d'ari da hamsin yaya kenan idan akayi sati, tana k'ok'arin kashe wayar kiranshi ya sake shigowa, wayar ta rik'e a hannunta tana jujjuyata tana tunanin ta d'aga ko karta d'aga " ki d'aga kiyi mishi kashedin karya sake kiranki, wata zuciyar ta bata amsa, yayinda wata zuciyar ke gargad'inta da " karki d'aga yana iya sake yaudararki. Murmushi ta saki me ciwo tana furta " wallahi ko dad'in bakin duka mayaudaran mazan duniya za'a had'a mishi bazasu yi tasiri akaina ba wannan karon, cike da yak'ini ta d'aga wayar ta kara a kunnenta, cikin kunnenta ya sauke kasalalliyar ajiyar zuciya ya d'ora da fad'in. "Karki fara Deeyanah, karki faro fad'an da bazaki iya kai k'arshen shi ba, karki d'aukowa kanki dala ba gammo, wallahi Deeyanah nafi hitila bala'i, dafin dake jikina yafi na bak'in maciji bazaki gaskata hakan ba sai lokacin da kikayi min taurin kai, idan kikace zaki bijirewa umarni na..... Cikin masifa da taurin rai tace " umarninka umarnin Allah ne da idan nak'i binshi wani bala'in zai fad'a min? "Waye kai Ajlaal? "D'an iskan k'arshen zamani da sai da iskanci ya k'are babu komai sai kale kake yin naka? "Banza wulak'anctacce tab'abbe halakkke d'an wuta, waye kai a duniyar iskanci da sunanka har yanzu ko unguwar da kake bai zagaye ba? "Ina kaje ina aka sanka a duniyar shagalallu tab'abb'u da har yanzu babu wanda ya sanka a duniya? "Duk iskancin ka ka kai Fir'auna? "Ka kai d'an k'aruna? "Ka kai Abu Jahil? "Ka kai Barau kwallon Shege? "Ko ka kai Musailamatus Kazzaba? "Ko ka kai Abdullahi d'an Ubayyu d'an Salul? "Ka kai Uddaru? "Ka kai Lamaduru? Kai da duk iskancinka baka kai Hamana ba, ko ka kai shaid'an da yayi fito na fito da Allah? "Shi kanshi Hitilan da kake ikirarin kafi shi bala'i ko sawunshi baka taka ba. Shiru yayi yana saurarenta har ta dasa aya kana yace " na baki na da kwana d'aya kizo idan baki zo ba..... "Me zakayi idan ban zo d'in ba? "Wallahi Tallahi Ajlaal ko shekara zaka bani bazan tab'a zuwa inda kake ba, an riga an gama, komai ya k'are Ajlaal an riga an buga kid'an tashi, zayyi magana ta kashe wayar had'i da jefa ta kan gado, rasa abinda zatayi yasata sulalewa k'asa had'i da sakin kuka. Bayan sati d'aya... Duk yadda kake zaton mutum zai shiga damuwa Deeyanah ta shiga fiye da haka, bata da aiki sai kuka, ko fita bata yi kullum tana d'aki tana aikin kuka da Istigfari, koyaushe tana kan sallaya dare da rana tana neman yafiyar Allah da karatun Al Qur'ani tana karatun hawaye na zuba, ko abinci bata iya ci iyaka ci tasha shayi, kasancewar ita da Deen tuni kusancin su ya tarwatse kowa rayuwarshi yake gudanarwa batare da d'an uwanshi ba, shiyasa Deen bai damu da rashin ganinta da bayayi kwana biyu ba, dan dama ba wani magana suke yi sosai ba sai idan ta kama. Duk yadda Ajwaad ke tsammanin abun ya wuce nan dan shi a zatonshi da fari wasa take yi, sannu a hankali al amarin ya fara girmewa tunaninshi, duk sanda ya kira number ta bata shiga da alama ma a rufe wayar take ko kuma tayi blocking d'inshi dan ko text ya tura mata baya tafiya, iska ya kaiwa naushi tare da fad'in " shit!, me yarinyar nan ke nufi ne? "Me take shirin aiwatarwa? D'an shiru yayi yana tunani kana yace " wow! wai tana nufin the game is over? "Kinyi kad'an Deeyanah, kinyi tsararo yarinya wallahi duk duniya babu wanda ya isa ya raba ni da ke, ko ke da kanki baki isa ki raba ni da kanki ba, zan iyayin komai zan iya kawar da kowa akanki, ya k'arashe maganar had'i da bushewa da mahaukaciyar dariya. A b'angaren Deeyanah kuwa abun babu sauk'i sai azabtar da kanta da ruhinta take yi, agogo ta kalla k'arfe uku da minti 40, kanta dake barazanar tarwatsewa saboda azababban ciwon da yake yi mata ta dafe, saboda tsanin ciwon da kanta keyi har jiri ke d'ibarta, bango ta dafe da d'aya hannunta while d'aya hannun ta dafe kanta dashi, ta sunkuya zata kwanta a gado aka fisgota ta baya, sama aka d'aga ta da hannu d'aya kana aka matse ta da bango. Wuyanta da aka shak'e ta soma kiciniyar kwacewa amma ta kasa, soma dukan hannun da aka shak'etan tayi amma a banza, sai da ya gaji dan kanshi kana ya sake ta, ta fad'i k'asa da rarrafe ta kama gado ta kifa tana tari, ta dad'e tana tarin hawaye da majina na zuba kana ta d'ago ta zuba mishi jajayen idanuwanta da hawaye ke zubawa dakyar muryarta bata fita sosai tace " kayi hauka ne? "Ko kana so ka kashe ni ne? Hannunshi ya sanya cikin wondon 3 quarter dayake sanye dashi. "Me kike nufi Deeyanah? Mik'ewa tayi ta nufi inda hijabinta ke aje ta d'auka ta saka cikin nutsuwa ta kallanshi ta nuna mishi k'ofa tace " fita! "Wow! yace yana tafa hannu had'i da jijjiga kanshi, tun daga k'afarta ya d'auko kallo har izuwa fuskarta ya kwashe da dariya har da rik'e ciki yace " abun mamaki wonder shall never end! "Ni! wai kike sakawa hijabi yau? Ya fad'a still yana dariyar, zagaya ta ya soma yi tare da sanya hannu ya rik'e hijabin jikinta, " me yayi saura Deeyanah? "Meye ban gani ba meye kuma ban tab'a ba, meye bak'ona a jikinki? Ido ta runtse da k'arfi hawaye na gangarowa saman kuncinta, sai da ta cije lips d'inta kana ta bud'e idonta gami da nuna mishi k'ofa tace " fita! Hijabin nata ya saki yaja baya yana kallanta yace " kuma fa sai naga kin k'ara kyau, kinyi fess dake kamar sabuwar budurwa dad'i na dake bakya tsufa ga kuma dad'i a gado, ya k'arashe maganar had'i da kashe mata ido d'aya, " ashhhhh yace yana mik'a, " dan Allah muje ki d'an lugwigwita ni a gado kamar yadda kika saba, kin gane ai, ido ta sake runtsewa da k'arfi kana ta bud'e su cikin d'an d'aga murya tace " nace ka fita ko? Ta fad'a tana nuna mishi k'ofa, shu'umin murmushi ya saki yana d'aukar steps zuwa gare ta, hannunshi ya sanya ya zagayo da ita ta baya ya rik'o k'ugunta had'i da matso da ita daf dashi ta yadda suna iya jiyo fitar numfashin juna, ya sanya yatsunshi biyu yana shafa gefen kumatunta, muryarshi can k'asan mak'ogwaro yace " zan iyayin komai akan soyayya ta, ina sanki sama da komai da kowa Deeyan.... Hannayenta ta saka ta hankad'a shi baya da k'arfi ya sake yowa kanta zai rungume ta, kafin ya k'araso ta kifa mishi mari da iya k'arfinta ji kake tassss!, ta nuna shi da yatsa cikin bushewar zuciya da k'ek'ashewar rai, kallo d'aya zakayi mata kasan ta gama kaiwa k'arshe ta jefa idonta cikin nashi tana kallan cikin kwayar idonshi babu d'igon tsoranshi a cikin ranta, saboda tsabar b'acin rai jijiyoyin kanta sun fito sunyi rad'o-rad'o while duk ilahirin jikinta na tsuma. "Karka kuskura ka sake matsowa kusa dani, ko taku d'aya ka k'ara sai na shayar dakai giyar mamaki Ajlaal, banza k'azami, wulak'antacce k'ask'antacce tab'abbe, wanda idan baka tuba ba sai kayi irin mutuwar karnuka, babu abinda ke damunka sai duhun jahilci na rashin ilimin addini, Basaan da Halimatu sun cuce ka da basu baka ingantacciyar tarbiyyar addinin Islama ba, na tsane ka Ajlaal na tsane ka fiye da mutuwa ta, idan da mutumin da nake san ganin mutuwarshi to kai ne, ban k'i naga gawarka kwance a gaba na ba, duk da zan so ace sai ka wulak'anta irin wulak'antar dako kafiri mak'iyin Allah yayi ta sai an tausaya mishi, ka cuce ni Ajlaal, ka lalata min gobe na, ka tarwatsa duniya ta da komai nawa, ka jefa ni cikin k'uncin da har in mutu haske bazai tab'a gauraye duhun ba, har in mutu bazan tab'a yafewa kaina ba, ni da farin ciki da walwala har izuwa fitar numfashi na na k'arshe. "Allah ya isa Ajlaal, Allah ya isa na, Ubangiji ya saka min, sakayya cikin gaggawa, durk'ushewa tayi a k'asa had'i da sakin rikitaccen kuka tana fad'in " ka lalata min komai, babu abinda yayi saura komai ya lalace, Allah ya isa tsakani na dakai, Ubangiji yayi min sakayya. "Ni kika mara Deeyanah? Damk'o ta yayi ya d'ago ta sama cikin matsanancin b'acin rai ya kalle ta da jajayen idanuwanshi yana fad'in " ni kika mara? Kakin majina tayi ta tofa mashi a fuskarshi ta d'ora da " an mare ka waye kai? " Har yanzu da alama baki san waye ni ba. "Kai ne a jikin dubu d'aya ko d'ari biyar da ya zama dole saina sanka. Sakin ta yayi ta fad'a saman gado yasa yatsa ya dankwalo majinar data tofa mishi, ya kalli yatsan gami da yin murmushin gefen baki, sai kuma ya had'e fuskarshi yadda kasan bai tab'a yin dariya ba, ya durk'usa dai-dai fuskarta ya nuna mata yatsa yadda kasan zai tsone mata ido cikin matsanancin b'acin rai ya soma magana " baki isa ba Deeyanah, zan baki zab'i biyu kad'ai imma dai ki kashe aurenki kizo muyi aure mu rayu mu biyu a cikin duniyarmu daga mu sai 'ya'yanmu, ko kuma kizo mu cigaba da d'orawa daga inda muka tsaya, ina nufin kizo muci gaba da more rayuwarmu kamar yadda muke yi ko kuma..... ya cije leb'enshi. Hankad'a shi baya tayi ta mik'e a haukace tace " ko kuma me? "Ko kuma zan kashe Deen, ko kuma zan kashe gaba d'aya ahalinki, ko kuma zan k'arar da gaba d'aya danginki ko kuma na kashe tilon d'anki ko kuma zan saki videon ki ta fad'a a haukace, duk tabi ta haukace masa, " su kenan iya abinda kake tak'ama dasu? " Shikenan iya barazanar taka kenan ko? "Sune abubuwan da kake amfani dasu wajen tsora ta ni kayi yadda kaso dani ko? "Ko ba su ba ne? "Idan sune na riga na sansu har ma na haddace su idan da wasu sabbabi ka fad'e su inji ina jira. Hak'oranshi ya taune da k'arfi ya juya mata baya had'i da nausar bango da k'arfi ya tako ya dawo gabanta ya kalli cikin kwayar idonta yace " kina wasa da wuta yarinya, kina wasa da rayuwar ahalinki, tsaki taja had'i da jijjiga kanta tace " nace maka na riga na san wad'an nan ka samo wasu sababbi, cikin hargowa yace " baki san da wanda kike san yin wasan mutuwa ba, " waye kai? "Ina san na san waye kai Ajlaal, uhunnn fad'a min ina jinka, " zan kashe kowa Deeyanah ina fad'a miki kina ganin kamar wasa ne ko? Cikin masifa da hargowa tace " je ka! je ka kashe su d'in, maza jeka kashe su, ta fad'a tana yarfa mishi hannu, yatsa ya nuna ta dashi ya bud'e baki zayyi magana ta daka mishi tsawar da gaba d'aya d'akin sai da ya amsa " nace maka kaje ka kashe su, tunda rai da rayuwa a hannunka suke kana da iko da su, waye kai da kake tunk'aron datse numfashin wani? "Kai d'igon maniyyi ne wanda aka halicce shi daga yunb'u (tab'o) wulak'antaccen bawa, wanda shi kanshi bashi da iko akan rayuwarshi balle ta wani, amma kana k'ababar zaka kashe, zaka kashe, to jeka kashe idan kana da iko da rayuwarsu, in banda kai sakarai ne shashasha har ana tunk'aho da kisan kai ne? "Yadda kake yin tak'amar nan yana bani mamaki nakan ji kamar ka haukace a wasu lokutan, mutumin da bashi da tabbaci akan second d'aya na rayuwarshi, mutumin da bashi da tabbaci akan rayuwarshi, mutumin da bai san yaushe zai mutu ba, bai san a inane zai mutu ba, mutumin da idan Allah mai komai da kowa, wanda ke da ikon akan kowa da komai yaso yanzu anan take kana iya mutuwa amma shinke tak'amar kawo k'arshen rayuwar wasu, Ajlaal Basaan na k'alubance ka idan rai da rayuwar ahalina a hannunta take ina san ka kawo k'arshenta anan take yanzu-yanzu, haka idan rayuwar mijina tana k'ark'ashin ikonka da sarrafawarka ina san akawo min gawarshi yau d'in nan ba sai gobe ba, idan kana da iko da gobe da duniyar gaba d'aya ina san ka fad'a min abinda zai faru nan da awa d'aya a gaba. Shiru sukayi gaba d'ayansu idanuwansu cikin na juna na wani d'an lokaci, murmushi tayi had'i da hard'e hannuwanta a k'irji tace " bazaka iya ba ko? " Saboda baka sani ba? "Bazaka iya ba, saboda baka da iko akan komai da kowa, kai kanka ikon rayuwarka da lafiyarka ake yi, a yanzu idan aka so ana iya kawo k'arshen su, oh! na tuna ashe fa baka da masaniya akan haka, ayya bashi da ilimin addini shiyasa, am pity you, banza wawa dabba d'an akuya fasik'i mazinaci wanda zai iyayin zina da mahaifiyarshi, zaka iya yin goho mahaifinka ya nemeka ta bayanka Ajlaal, tun da kake yin irin wad'annan mugayen kalaman zaka iyayin komai, zaka iya aikata duk wani sab'an Allah dake doron k'asa, banza jahili fajiri, gaka a tsaye haka kamar me hankali ashe banko ne, ina jiranka kaje ka kashe kowan kamar yadda kace Malam Me Rayuwa. Matsowa yayi daf da ita ya nuna ta da yatsa zayyi magana tayi saurin tarar numfashi, ta nuna mishi yatsa har yana gogar fatar idonshi, idanuwanta sun firfito waje kamar zasu fad'o k'asa tana cije hak'ora ta soma magana cikin zafin rai " zuciya, gangar jiki na da ruhi na sun k'ek'ashe sun bushe k'ayau ta yadda babu wata firgitarwa, tsoratarwa da muzantawar ka da zasuyi tasiri akai na, ka sani duk abinda zakayi komeye shi wallahi tallahi bazai tab'a sawa na waiwayi gurb'atacciyar rayuwar da mukayi a baya ba, babu wani abu da zayyi tasiri akaina Ajlaal babu shi, koda duniya da abinda ke cikinta zaka cinnawa wuta kowa ya mutu. " Kinyi ganganci Deeyanah, kin tafka babban kuskuren yin jayayya dani, cikin hargowa da d'aga murya tace " fita! yatsa ya nuna mata zayyi magana ta runtse idonta tare cewa " out! da k'arfi sai da d'akin ya amsa, yatsa ya k'ada mata a fuska gami da cije leb'enshi na k'asa yayi kwafa ya juya, har ya kai bakin k'ofa zai fice ya juyo tare da fad'in " na baki nan da kwana biyu zan jira jin abinda kika yanke, bai jira jin abinda zata ce ba ya fice. Durk'ushewa tayi a k'asa hannunta d'aya saman gado ta saki rikitaccen kuka. Yana ficewa daga d'akin ya haura katanga ya fice daga estate d'in gaba d'aya batare da wani ya ganshi ba, sai da yayi 'yar tafiya kana ya k'arasa inda ya aje motarshi, ya bud'e mazaunin driver ya shiga ya zauna, ajiyar zuciya ya sauke a fili tare da shafo kanshi tun daga k'eyarshi zuwa fuskarshi, tana neman saka mishi ciwon kai, ya rasa dalilin sauyawarta har haka, ya rasa meyasa take da taurin kai da kafiya, ya rasa me ya haifar da hakan, a yanayin yadda ya karance ta idan kashe ta zayyi ta hanyar yankar naman jikinta bazata tab'a yarda ta dawo mishi ba, daga maganganun bakinta ya samu tabbacin komai ya k'are ya san idan bai dage yayi da gaske ba yana iya rasata ma. Sitiyari ya nausa da k'arfi har ya danne horn, horn d'in ya cika unguwar, tsaki yaja a fili tare da tallafe kanshi, ya dad'e a haka kafin yaja motar ya bar wajen. Tana zaune a falo tana kallan wa'azin Sheik Isah Ali Pantami a sunna Tv kujerar dake gefe ya zauna Tv ya kalla ya d'an tab'e baki had'i da cewa " ba sauraron ba Allah yasa ayi aiki dashi, juyowa tayi ta d'an kalle shi kana ta mayar da idonta kan Tv, duk da bai san abinda ya faru ba amma wata irin muguwar kunyar shi da nauyinshi take ji, ko alamun shi taji sai gabanta ya yanke ya fad'i balle kuma ta ganshi, yanzu ma tunda ya zauna gabanta ke lugudan fad'uwa, idonta nakan TV amma bata iya fahimtar komai, batare daya kalle ta ba yace " idan kina da buk'atar wani abu kiyi min list idan kuma kud'in zan tura miki to!, shiru yayi yana jiran amsarta na wani d'an lokaci, jin batayi magana ba yasa shi mik'ewa yabar wajen tabi bayanshi da kallo kwalla na zuba. "Haka na cuci kaina na lalata rayuwar gida na da ahalina? "Haka na mayar da gidan aure na tamkar gidan zaman makoki? "Ni da mijin aure na mun zama tamkar bak'in juna, kamar wad'anda akayiwa auren dole, sai kace ba auren soyayya mukayi ba, yana so na ina sanshi, sai kace wad'anda sukayi auren k'iyayya, na shiga uku, wayyo ni kaina na lalata komai, babu abinda zai gyaru, ta k'arashe maganar da firgitaccen kuka mai razana zuciya. Ranar komai sabo ya dawo mata fil haka ta kwana cur saman sallaya tana sharb'ar kuka kamar wacce ake zarewa rai, ta manta yaushe raban da taga dariya da murmushi akan fuskar Deen, raban data ganshi cikin walwala da fara'a har ta manta, bazata iya tuna ranar k'arshe da sukayi hira cikin so irin na ma'aura ta ba, ta san yayi mata mugun hak'uri, yayi mata kara da kawaici, yayi juriya da kawar da kai, duk wani hak'uri da miji zayyiwa matarshi tasan yayi mata, duk uzurin daya kamata miji yayiwa matarshi yayi mata. "Yayi k'ok'ari ma, yayi min duk abinda miji zayyiwa matarshi, yayi min abinda wa zai yiwa k'anwarshi kai har abinda ya kamata uba yayiwa 'yarshi Deen yayi min, ya rufa min asiri bai tab'a fad'awa iyayenmu halin da ake ciki ba, shekararmu biyu zuwa uku bama sex wanda shine gundarin auren, babu wata alak'a dake alak'anta ma'aura ta dake shiga tsakaninmu har tsayin kusan shekaru uku, amma duk da haka bai tab'a kai k'ara ta wajen iyayenmu ba, babu wanda zai so ni kamar ka, babu wata soyayya da zan samu dake saman taka a fad'in duniya, kai cikekken masoyi ne na gaskiya abin tunk'aho, kai miji nagari ne burin samun kowacce d'iya mace, ka cika masoyi, bani da abinda zan biyaka dashi bani da abinda zan saka maka dashi. "Nayi maka butulci Deen, nayi maka muguwar sakayya, na cuce ka, naci amanarka har a gidanka a d'akinka akan gadonka na aure na kawo wani k'ato da bai biya sadaki na ba ya kwanta dani, na cuci rayuwa ta, nayiwa kai na babbar illa, idan baka yafe min ba hakk'inka zai ta bibiyata yana wahalar dani har zuwa k'arshen rayuwata, alhakinka ba bazai daina farautar farin ciki da walwala ta har izuwa fitar numfashi na na k'arshe ba, ka yafe min Deen, ka taimaka ka yafe min in baka yafe min ba nasan mummunan k'arshe zanyi da zai zamewa wasu Izzina, wani irin kuka take yi me gunji wanda ya cika gaba d'aya d'akin. Kofin tangaran d'in hannunshi ya d'aga ya buga a window ji kake tasssss sun rotse gaba d'ayansu, baya yin shaye-shaye bai tab'a shan d'igon wani abu na maye ma, amma idan ka ganshi sai ka rantse babu abinda bai sha ba a halin da yake ciki ba, ya birkici ya haukace yadda kasan wanda ya gudo daga asibitin mahaukata, nishi yake yana haki kamar wanda ya kwana yana aikin k'arfi, wani iri yake ji a jikinshi zuciyarshi kam tamkar an zazzaga mata fetur an kesta ashana, gaba d'aya duniyar tayi mishi zafi, komai ya fice mishi a rai, haushin kowa yake ji, ji yake kamar ya zazzaga fetur ya k'ona kanshi ya huta da azabar da zuciyarshi keyi mishi, Bluetooth d'in dake kunnenshi ya zare yayi wurgi dashi, yaji duk abinta tace kaf. "Ni ne k'aton banzan? Ya fad'a kamar yana magana da wani, "ni Deeyanah ke jefa da wad'annan maganganun akan Deen? "Wato yama fini sanki? "Soyayyarshi itace abin kambamawa ba tawa ba, tawa ta zama ta banza? "Soyayyarshi itace ta gaskiya tawa ta k'arya? "Zan tabbatar miki da duk duniya nafi kowa sanki Deeyanah, zan tabbatar miki baki da masoyi kamar ni. "Zan d'auki duk abinda zakiyi min, zan jure duk wani zagi da cin mutuncin da zakiyi min amma bazan tab'a jure ki fifita wani gardi akaina ba, bazan jure jin tausasan kalamai akan Deen yayinda ni kuma kike kausasa min furuci ba, bazan lamunci wulak'anta min soyayya ta a gare ki kina kurara tashi ba, bazai yiyu ba Deeyanah, fad'awa saman sofa yayi yana dariya da iya k'arfinshi kamar zararre. ************************************ Nan kan sallayar wahalallan bacci ya kwashe ta tana kuka, sai sauke ajiyar zuciya take yi cikin bacci, sama-sama kamar a mafarki taji ana knocking k'ofar bedroom d'inta, sake bugun da akayi ya farkar da ita firgigit a d'an tsorace tana salati, idanuwanta ta lumshe had'i da goge gumin goshinta ta fitar da nannauyan numfashi, sake buga k'ofar d'akin akayi a karo na uku, hammar da take yi ta katse gami da cewa " shigo k'ofar a bud'e take, cikin nutsuwa ya nuro k'ofar ya shigo, daga tsaye ya tsaya kanta yana binta da kallan mamaki dan yaga alamar anan ta kwana, idanta da yayi ja kuma fuskarta a kumbure da alamar kuka ya kalla tare da fad'in " kina lafiya? Ya fad'a cikin kulawa, kanta ta d'aga mishi alamar eh, kana cikin sanyin murya tace " ina kwana? "Alhamdulillah, Ammu tace ta turo miki list zakiyi mata siyayya ko? Kanta ta dafe tana rufe bakinta saboda hamma, d'an juyawa tayi ta kalli drawer dan ta dad'e da mantawa da wata waya, raban da tayi amfani da waya harta manta, mik'ewa tayi tana cewa " wallahi ban sani ba bari na duba, " idan kin shirya kiyi min magana na kaiki, idan kuma zakije da kanki to, ya fad'a idonshi kanta yana jiran amsarta, da sauri tace " a'a bari na shirya sai muje!, juyawa yayi ya fice batare daya ce komai ba, dayace idan zataje ta tafi har cikin zuciyarshi yayi maganar dan tuni ya tattara komai ya watsar ya samawa kanshi lafiya a cewarshi kowa yayi na gari dan kanshi, haka kowa ya gyara ya sani, bin diddigin da yayi mata da bai kamata da laifin komai ba ya k'ara mishi yak'ini da yarda akanta sosai, harga Allah yaji ya samu kwanciyar hankali fiye da baya, yakan ce " yasan Deeyanan shi bazata tab'a aikata abinda bai dace ba, yasan duk abinda zatayi akwai dalilinta nayin hakan, wata k'ila wani laifin yayi mata bisa rashin sani da yasata ta k'auce masa. Wayar ta d'auko daga cikin drawer ta kunna, kamar jira yake yi ta kunna kiranshi ya shigo, tsaki taja ta zauna gefen gado tana jira kiran nashi ya katse ta duba sak'on Ammun, takai mintuna zaune tana san duba sak'on amma kiranshi dake shigowa akai akai ya hanata dubawa, a do not disturb ta saka wayar kana ta samu ta duba sak'on, sakonshi 453 ne suka shigo wayar, duk da IPhone bata hukin ranar sai da tata tayi, jira tayi wayar ta dawo dai-dai kana ta goge gaba d'aya sak'unan cikin wayar ta danna mishi blocking ta jefa wayar saman gado ta mik'e ta fad'a bathroom. A d'an gaggauce tayi wanka ta fito ta shirya cikin kayan data san yafi san ya ga ta sanya, heavy make-up tayi tayi kyau sosai damma muguwar ramar da tayi ta rage mata kyau ga kumburin da fuskart tayi saboda kuka, kallan kanta tayi a mudubi tayi d'anyi gajeran murmushi ta fice hannunta rik'e da waya, dai-dai ya fito daga bedroom d'inshi yana d'aura agogo, tsayawa sukayi suna kallan juna shi ya fara d'auke idonshi daga kanta ya wuce, tabi bayanshi sumi-sumi kanta a k'asa. Yana tuk'in a nutse tana ta faman janshi da hira, ya d'an yi mamaki duk da ya san dama tana da shegen surutu, jefa-jefi yakan bata amsa idan ta kama, a babban shagon siyayyar Sahad Store sukayi parking da sauri ta bud'e motar ta fito dan su jera amma yayi saurin yin gaba dan ya gane manufar ta, bata ji komai a ranta ba tabi bayanshi, tana duba list d'in tana d'ibar kayan harta gama, ta tura kwandon da kayan ke ciki gabanshi tana cewa " fara biyan wannan bari na duba abubuwan gida, bayyi magana ba ya karb'i keken kwandon ya tura zuwan wajen biya. " Deeyanah! ya kira sunanta cike da kwarin gwiwa, saurin juyowa tayi ta zuba idanuwanta akanshi, yana tsaye hard'e da hannu a k'irjinshi fuskarshi d'auke da murmushi a d'an tsorace ta juya bayanta ta kalli Deen, ajiyar zuciya ta ganin yabar wajen tayi, murmushi yayi me kama da dariya yace " karki damu yabar wajen bazai tab'a sanin meke tsakaninmu ba sai idan kin so hakan. Shiru tayi tana kallanshi batare datace komai ba, ya jijjiga kanshi had'i da cewa " eh sai inkin so zai sani, abinda nake nufi da sai kin so, sai idan kinyi taurin kai da kafiya kink'i dawo min, sai idan kin bujirewa umarni na, to anan fa zai san komai zai san duk abinda ke tsakaninmu kamar yadda kikaji nace komai to ina nufi zan sanar dashi duk wata badak'alar da mukayi zan tura mishi videon blue film d'in mu, ya k'ara shi maganar had'i da kashe mata ido d'aya, batayi magana ba ta girgiza kanta gami da juyawa zata bar wajen. (Ku gane bambamcin dake tsakanin jijjiga kai da girgiza kai, jijjiga kai yana nufin d'aga kai sama da k'asa while girgiza kai daga b'arin hagu zuwa b'arin dama) Fisgota yayi da k'arfi ta fad'a jikinshi ta bud'e baki zatayi magana ya yasa hannunshi ya rufe mata bakinta yasa k'arfi yaja ta, ta k'ofar baya, tana ta dukan shi amma a banza mota ya dannata ya zagaya ya shiga motar tana ta dukan glass tana ihuuu amma dayake motar tint ce babu wanda ya ganta, sai da yayi tafiya me nisa da ita kana yayi parking ya fito, ya zagaya b'arin da take ya bud'e ya finciko ta waje, baya ya juya tare da dafe kanshi, ihuuu yayi da k'arfi had'i da naushin iska ya juyo gareta yana kallanta sosai yace " ya kamata ki gane irin girman son da nake yi miki, ina sanki Deeyanah ina sanki fiye da so, ina sanki da duka zuciya ta, ya sunkuya inda take yade a k'asa yace " please ki so ni nima, ki soni koda kwatankwacin son da nake yi miki ne, ki kashe aurenki kizo muyi aure dan Allah. "I love you try to understand my feelings please. "I hate you Ajlaal, na tsane ka bana k'aunar ganinka ta fad'a cikin zafin rai had'i da tofa mishi yawo a fuska, a matuk'ar hasale ya damk'o gashin kanta ya kalli cikin kwayar idonta da idanuwanshi dake waje sunyi jajir yace " aiko kin taro fad'in da bazaki iya k'arasa shi ba, akan ki zan iya yiwa kowa komai Deeyanah, dana rayu babu ke gwara na mutu sau dubu. "K'arya kake yi Ajlaal ba so na kake yi ba akwai dai abinda ke ranka game dani, dan idan har soyayyar da kake min gaskiya ce zaka so na rayu cikin farin ciki, zaka barni nayi rayuwata yadda naso, zakayi sadaukarwa irin sadaukarwa da jaruman masoyan farko sukeyi, ai akwai sadaukarwa a soyayya, zaka barni nayi rayuwa da wanda na zab'arwa kai na, zaka barni kuma kayi nesa dani nayi rayuwa tare da mijina da d'ana bawai kace na rabu dasu ba, wallahi tallahi Ajlaal ba soyayya bace abinda kake ikirarin kana yi min, a haukace yace " idan ba soyayya bace menene? "Hauka, Hauka ne Ajlaal, abinda kake yi hauka ne amma ba soyayya ba, dan idan soyayya ce zaka barni nayi rayuwa ta cikin farin ciki koda hakan na nufin mutuwarka, kana da san kanka, san kanka yayi yawa Ajlaal har ya rufe maka ido kana neman halakar damu ka kaimu wuta, muzo duniya a banza mu koma a wofi. " Danna so kaina laifi ne Deeyanah? Hannunta ta had'e waje d'aya alamar rok'o tana kuka wiwi kamar ranta zai fita tace " dan Allah dan zatin Allah dan girman iyayenka ka fita daga cikin rayuwata ka barni nayi rayuwa cikin salama please. "Bazan iya ba wallahi bazan iya ba Deeyanah, " to shikenan tunda bazaka iya ba kaje kayi duk abinda zakayi. "Kina da sauran dama tun kan lokaci ya k'ure miki ki dawo min in ba haka ba zan lalata komai, " baka ji me nace ba kenan? "Ai nace maka kaje kayi duk abinda zakayi. "A'a fa karki kizo kina danasani da danama. "Danasani da danama ai na gama yinsu koma ince cikin yinsu nake, nayi danasanin had'uwa dakai a rayuwata nayi danasanin saninka a rayuwata, kai bama saninka kad'ai ba harta jami'ar dana shiga na sanka sai da nayi danasanin karatun boko da tsanarshi gaba d'aya. Dariya yayi sosai yace " shikenan tunda haka kika zab'arwa kanki amma ki sani baki fara danasani ba har yanzu zadai ki fara ranar tana nan zuwa ki shirya tarbarta, cikin matsanancin kuka ta d'aga hannayenta sama tana kallan sararin samaniya ta soma magana " Allah ya isa Ajlaal Allah ya isa na, Allah ya isar min, Ubangiji yayi min sakayya me tsanani a tsakani na da wannan bawa naka, Allah ya tsare ni daga sharrinka, Allah ya tsare ni daga mugayen alkaba'inka duk irin bala'i da masifar da kake nema na dasu ina rok'on Allah ya mayar maka abinka kanka. Mik'ewa tayi ta juya zata bar wajen har tayi taku biyu zuwa uku ta juya ta kalli kwayar idonshi tace " kana yi min barazanar zaka sanar da Deen komai, murmushi tayi me ciwo had'i da cewa nayi maka alk'awarin kafin ka sanar dashi ni da kaina zan sanar dashi abinda ke tsakaninmu so ka kwantar da hankalinka ka kuma saka ranka a inuwa, na riga nakai matakin k'arshe nakai matakin da baka isa ka rikito dani k'asa ka dawo dani baya ba, kaima ina yi maka fatan shiriya idan kuma bazaka shiryu ba Allah yasan yanda zayyi dakai, ta juya tayi tafiyarta tana sharar kwalla da tunanin abinda zata cewa Deen. Tsaye ta iske shi a harabar gida da sauran family duk anyi cirko-cirko ana tunnin sace ta akayi, tana shiga duk ayo kanta tana wani irin kuka ta fad'a jikin Ammi, " lafiya meya faru? "Meya same ki? "Ammi.....! ta fad'a da wani irin kuka me k'arfi dake fitowa daga can k'ark'ashin zuciyarta so take tayi magana amma kuka ya hanata, duk sunyi tsaye kanta cikin damuwa da tashin hankali, "kaita gida mayi magana daga baya, Abbi ya fad'a yana kallan Deen, kanshi ya d'aga alamar to kana ya sunkuya ya d'auke ta cak yabar wajen da ita, in banda kallanshi da kuka babu abinda take yi, saman gado ya shinfid'eta yaja mata bargo ya rufe ta zuwa k'irjinta ya juya zai fita caraf tayi ta rik'e hannunshi cikin sheshsheka tace " d....a...n A.....ll...ah kar...ka tafi.....ka zau....na dani na.....wa....ni, d'an....lo...ka...ci, guntun murmushi yayi mata tare da zame hannunshi daga cikin nata kana ya zauna saman sofar dake d'akin yana danna waya, idanuwanta kanshi ta kasa d'auke ido daga kanshi, yana sane da kallan da take yi mishi while yana jiyo sautin kukanta dake fita a hankali a haka bacci ya kashe shi, ita kam bata runtsa ba kwana tayi tana tunanin irin soyayyar da ahalinta keyi mata amma ta saka musu da bak'in batulci. Wasa-wasa abu ya wace sekanni, awanni, satittika har aka kai wata d'aya, duk yadda Ajlaal ke tunanin abun ya wuce nan dan babu yadda bayyi da ita ba amma tak'i sake yarda dashi, ya rasa yadda zayyi da ita abun duniya ya tattaru yayi mishi yawa. A b'angaren Deeyanah kuwa ta koma kamar tsohuwar data gaji da duniya, bata iya cin komai sai ruwan tea da drinks shima ba sosai ba, ta rame ta k'ek'ashe bata da aiki sai kuka, tun babu wanda ya sani har kowa ya sani, babu irin tambayar duniyar da ba'ayi mata ba akan meke damunta kullum amsarta d'aya ce babu komai, duk gida an tattara an zuba mata ido, ga bp d'inta da yayi mugun hawa. Tana kwance saman gado, aka kira sallar la'asar ta mik'e da d'an hanzari jiri ya d'ebeta tayi baya ta fad'a saman gadon d'an shuuuuu taji cikin kanta da kunnenta, zama tayi saman gadon tana ganin komai bibbiyu yana juya mata, bango ta dafe ta mik'e tana bin bangon tana tafiya while tana gani dishi-dishi jiri na d'ibarta har takai k'ofar shiga bathroom d'in ta d'aga k'afarta zata shiga bathroom d'in jirin ya d'ebe ta, ta fad'i daga nan bata sake sanin inda kanta yake ba, babu wanda ya shigo har magariba, Deedee ne ya shigo wajenta, ganinta a kwance k'ofar bathroom yasa shi k'arasawa wajenta ya durk'usa gabanta yana girgizata tare da kiran sunanta, jin shiru yasa shi fita da gudu, d'akin Deen ya shiga yana haki, " Daddy kazo Momy ta fad'i tak'i tashi. Jikinshi na rawa ya fito da d'an gudu, " Deeyanah ! ya fad'a yana jijjiga ta amma shiru, sai jini daya fara fitowa daga hancinta kad'an-kad'an, jikinshi na b'ari ya sumgume ta sai asibitin dake nan cikin estate d'insu, anyi mata gwaje-gwaje da aune-aune inda aka gano zuciyarta ta soma kumbura. Gumi likitin ya goge kana ya soma magana yana kallan Abbi da Babah sa Deen da yayyan Deeyanah yace " wai meke damun yarinyar nan ne? "Gaskiya ya kamata ku bincika kusan damuwarta da kuma matsalarta dan abun ya fara girma gaskiya, yarinya k'arama da k'ananun shekaru amma ace tana tattare da irin wannan damuwar dake neman haifar mata da bugawar zuciya, a zahirin gaskiya abun yafi k'arfi shekarunta dan haka ya kamata kusa ido akan wasu abubuwa fa, da fari bawan jini yanzu kuma kumburin zuciya? Kallan da Abbi yayi mishi ne ya fahimtar dashi shi ake zargi akan damuwarta, dakyar ya iya had'iye yawun daya tsaya mishi tsakanin baki da mak'ogwaro, likitin ya d'ora da " a halin yanzu takai matakin da dole sai mun d'orata akan magani ta fara shan maganin, kuma koda ta fara shan maganin dole fa sai an saka ido kuma anyi mata maganin damuwarta in ba haka ba komai yana iya faruwa at any movement so take note please. Ajiyar zuciya Abbi ya sauke a b'oye kana cikin nutsuwa yace " Allah ya tsare, in sha Allah zamu bincika da yardar Allah zamuyi maganin koma meye. Tana kwance saman gadon luf tayi lamo yadda kasan babu rai a jikinta, fuskar nan tata tayi fayau sai uban haske, saboda kana ganin k'asusuwan fuskarta, jijiyoyin jikinta kam yadda kasan zana su akayi gasu nan rad'o-rad'o sun fito, hannunta dake june da ruwa ya kalla had'i da zuba mata ido yana mamaki abinda ke damunta da girma har haka, tunaninshi ya d'auko tun daga farko shekaru kusan uku baya, ta fara canjawa ne tun daga lokacin data suma ya kaita asibiti, a wancan lokacin ma haka ta shiga matsananciyar damuwa yayi juyin duniya ta fad'a mishi abinda ke damunta tak'i sanar dashi, tun daga lokacin bai sake gane kanta ba har yau. "What is going on? "Meke faruwa ne? " Meke damunta? "Meye damuwarta? Yayiwa kanshi tambayar, kanshi ya kulle ya kasa gane ko fahimtar komai, ya rasa a ma'aunin da zai sanya abun, tunanin nika da yawa suka rink'a zuwa kanshi, ya sak'a wancan ya k'ulla wannan, " bakomai idan ta warke in sha Allah zan sake tambayar ta damuwarta duk da nayi alk'awarin bazan sake tambayar ta damuwarta ba, Babah ya dafa kafad'arshi tare da d'an matsa kafad'ar yana fad'in " karka ayi biyu, kabar tunanin nan, wani abu ya had'iye ya sake danne abun cikin ranshi, ya dad'e yana san ya tattauna matsalar dake tsakaninsu kodan asama musu masalaha, yana san yayi maganar da wani koba komai za'a bashi shawarar da zata kaisu da samun mafita, yana san yayi maganar da Babah tunda shi bashi da aboki balle suyi maganar to amma Babah mahaifinta ne, idan ya sanar dashi yana iya zama sanadiyyar samun matsala tsakaninta da iyayenta, dole babu yadda ya iya ya hak'ura ya danne komai cikin ranshi, shima abun na damunshi, shima yana cikin damuwar, shima da za'a gwada shi ya tabbatar sai an samu matsalar data fi tata a jikinshi. "Badai zaka bar tunanin ba kenan? Murmushin k'arfin hali yayi yana b'oye damuwarshi batare daya ce komai ba, kwananta hud'u a asibiti aka sallame ta, gata kam babu irin wanda bata gani ba, idan tace tana san abu kaza kafin ta gama rufe bakinta an kawo mata shi, kowa sai lallab'a yake yi kamar kwai, shima a fannin gogan babu yabo babu fallasa yana bata kulawa dai-dai iyawarshi, Ammi taso ta wuce part d'inta da ita amma Deeyanah tak'i binta dole Ammi ta hak'ura aka mayar da Deeyanah part d'insu, kwananta biyu da sallamota Abbi ya kira su ita da Deen a babban falonshi, Babah na gefe zaune suka shigo, bayan sun zauna a k'asan carpet suka gaida iyayen nasu, Abbi yayi gyaran murya kana ya soma magana. " Deeyanah ya jikin naki? "Alhamdulillah da sauk'i Abbi. "Madalla haka ake so, an miki bayanin abinda yake damunki? Sake sunkuyar da kanta tayi k'asa kana tace " eh! "Kin san dalilan dake kawo irin wannan ciwon ko? "Eh!, ta sake cewa cikin girmamawa, " kin san illolin ciwon? "Eh! Abbi. "To meyasa Deeyanah? "Meyasa kika haifarwa kanki tunani da damuwar da zata iya zama silar rayuwarki? "Kinyi tunanin halin da zamu shiga idan hakan ta faru? "Ko sau d'aya kin duba mijinki da d'anki da zasuyi maraici? Kanta k'asa hawaye ya soma d'iga daga idonta, " meke damunki? "Meye damuwarki? D'an shiru ne ya biyo baya sai sautin kukanta dake tashi k'asa-k'asa, "mu muka fi kowa cancanta damu san damuwarki, mu ya kamata mu san matsalarki dan mune iyayenki mu zamuyi miki maganinta, ko bamu da maganinta zamu baki shawara ta gaskiya tsakani da Allah wacce bazata cutar dake ba, kuma zamu tayaki da addu'a, ina tunanin kin san k'arfin da addu'ar iyaye take da ita ga d'ansu, dan Allah kiyi mana adalci ki yiwa kanki adalci, ki taimake mu ki taimaki kanki ki fad'a mana damuwarki tun kan ta girma tafi k'arfin mu. Wannan karon sosai sautin kukan nata ya fito ya gauraye falon, bata so yin kukan gabansu ba, bata so ta basu alamar da zata basu tabbacin tana cikin matsala ba. " Kodan matsalar daga gidan aurenki take? "Kodai matsalar tana tattare da mijin aurenki? "Dan muddin kaga mace cikin irin wannan mummunar matsala da tarin damuwa to imma daga mijinta ko 'ya'yanta ko kuma dai dangin mijinta da iyayen mijin, na tabbatar ke baki da matsalar 'ya'ya, dangin miji data iyayen miji sai dai kota mijin, ya k'arashe maganar idonshi kan Deen daya d'ago ya kalle shi. "A'a, ba lalle matsalar daga gare shi take ba, Babah da tunda aka fara magana bai ce komai ba sai yanzu ya fad'a. Cikin fad'a-fad'a Abbi yace " ai dama kai ka saba kare shi, duk abinda Deeni yayi kai a wajenka ba laifi bane, ya zaka ce matsalar ba daga shi bace idan ba daga wajen shi take ba daga ita take? " Ya za'ayi ace yarinya kamar Deeyanah tana cikin irin wannan halin ace babu saka hannun mijinta kwata-kwata fisabilillahi? Cikin sanyin murya Babah yace " kada kayi saurin yanke hukunci ka tsaya dai ayi bincike sosai, kallan mamakin anya kuwa kaika haife ta Abbi yayi mishi, kamar zayyi mishi magana sai kuma ya fasa, ya sake mayar da kallanshi gare su yace " kiyi mana bayani Deeyanah muji idan da cutarwa a zamantakewar taku sai mu duba masalahar kowa, idan ta kama ma dole sai a raba auren tunda aure ba wajibu bane Sunnah ce ba Farillah ba idan da cutarwa sai a hak'ura ba lalle ba dole. "A raba auren fa kace? Cewar Babah yana kallan Abbi cike da mamaki, shiru yayi baibi takan maganar Babah ba. Saurin d'ago kanta tayi tana fitar da sautin kukanta sosai duk tabi ta rikice tana girgiza kanta tace " a'a Abbi dan Allah kar'a raba mu muna san junanmu, bashi da laifin komai, duk laifi na ne, nice na lalata komai Abbi, nice nake cutar dashi, dan Allah ku yafe min Abbi, ku taimaka ku yafe min, shima ku bashi hak'uri ya yafe min, tayi maganar cikin rikitaccen kuka tamkar ranta zai fita. Cikin rashin fahimtar inda zancenta ya dosa gaba d'ayansu suke kallanta, " me kike nufi Deeyanah? Babah ya fad'a yana kallan Abbi daya kasa magana, magana take san yi amma kuka yaci k'arfinta ta yadda ta kasa furta koda kalma d'aya, illa kallansu da take yi da jajayen idanuwanta da suka rine, " ni fa na kasa fahimtar komai ko kai ka fahimci wani abu? Abbi ya tambayi Babah idonshi kansu, "yi shiru ki nutsu sai kiyi mana bayani yadda zamu gane, Deen bayyi magana ba ya mik'e ya nufi fridge ya bud'e ya d'auko mata robar ruwan Faro ya dawo ya zauna kusa da ita ya zauna ya bar 'yar tazara kad'an a tsakanin su, ya bud'e rofar ya mik'a mata, hannunta na rawa ta amsa tasha sosai, so take ta tsaida kukanta amma ta kasa, tana ta k'ok'arin yin shiru amma kukan yak'i tsayawa, tana shashsheka ta kalli Abbi tace " kada ku zargi Deen wallahi babu ruwanshi shima yayi iya bakin k'ok'arin shi akaina, kuyi hak'uri karku raba mu dan Allah muna san junan mu, tayi maganar muryarta na shak'ewa. "To munji babu ruwanshi, fad'a mana meke damunki daya haddasa miki wannan mummunan ciwon? "Babu komai Abbi ta fad'a tana girgiza kanta, babu irin tambayar da ba'ayi mata ba amma amsarta d'aya babu komai, dole tasa Abbi ya sallame su badan ya yarda ba, sai dan kar ya matsa mata, har sun kai bakin k'ofa zasu fita Babah ya kira sunanta cikin sanyin murya, "Deeyanah!. Jikinta a sanyaye ta juya ta kalle shi had'i da amsawa. "Deeyanah yaye wata babbar garkuwa ce ga mutum duk girmanshi, iyaye sune katangar da mutum yake jingina da ita a kowanne irin yanayi wala farin ciki ko sab'anin haka, iyaye ginshik'i ne na kowanne mutum, zaki ga ko dabba tana k'ok'arin bayar da kariya ga d'anta, duk wani bala'i ko masifar daya tasowa d'a iyaye sukan shiga gaba dansu tarewa d'an wannan masifar data tunkaro shi koda hakan yana nufin mutuwarsu, koda ace bamu da k'arfin tare miki bala'in daya tunkaro ki, koda ace bamu da ikon yaye miki damuwarki ai zamu raba damuwar tare, kuma koba komai zamu tayaki da addu'a, kuma addu'ar iyaye tana da matuk'ar tasiri ga rayuwar d'a, ko kin sanar damu ko baki sanar damu ba zamu tayaki addu'a da duka k'arfin mu, murmushi kawai tayi mishi batare data ce komai ba, deep down tana jin sanyin dad'in dace da sa'ar iyaye nagari da tayi da ahali masu matuk'ar son ta. Har cikin d'aki ya raka ta, ta zauna saman gado, ya jawo dorowar gefen gado, ya ciro ledar magungunan ta ya b'allar mata ya mik'a mata had'e da ruwa ba musu ta amsa had'i da runtse idonta da k'arfi saboda bata san shan magani, ta afa maganin ta kora da ruwa, " ki kwanta ki huta, ya fad'a tare da ja mata bargo, bai sake magana ba ya fice, tabi bayanshi da kallo tana tuno a baya idan bata da lafiya yadda yake lallab'a ta yana tarairayarta kamar kwai, musamman idan akazo fannin shan magani daya san bata so, sai ansha daga da gwagwarmaya ta zuba sangarta da shagwab'a san ranta kafin tasha maganin, amma yau ita dashi tamkar bak'in da basu tab'a ganin juna ba. "Ubangiji kayi min sassauci, kayi min afuwa ka yafe min ka dai-daita tsakani na da mijina ya Rabbi, tayi addu'ar tana zubar da kwalla har lokacin idaonta na kan k'ofar. A hankali bacci ya soma fisgarta, tana lumshe ido tana bud'ewa bacci na d'aukarta ta ganshi tsaye kanta, da fari ta d'auka gizo yake yi mata ko kuma idonta ne, sai da ta bud'e idon ta ganshi tarrr a gabanta, a firgice ta mik'e zaune tana k'ok'arin sake bud'e idanuwanta da sukayi mata nauyi saboda cikin magungunan akwai me sa bacci, ta zuba su akanshi gami da cewa " me.....me...ya...kawo...ka? Ta fad'a bakinta na rawa, " me kazo yi gidan aure na Ajlaal? "Ka dai rantse saika k'arasa wargaza min rayuwata ka lalata duniya ta meyasa Ajlaal? "Meyasa baka jin rok'o da magiya? "Yanzu bazaka barni na rayu cikin salama da guntun farin cikin da nake k'ok'arin samarwa kaina ba? "Wai me yayi saura Ajlaal bayan komai ya k'are ka riga ka gama tarwatsa komai? Hannunta ta had'e waje d'aya kukan bak'in ciki na kufce mata tace " dan Allah, dan girman Allah ka barni Ajlaal, ka barni haka, dan zatin Allah, ta fad'a cikin rikitaccen kuka. Bisa mamakinta sai taga ya zube gabanta gami da rusa kuka wiwi shima ya kifa kanshi kan k'afafuwanta, yadda kasan wuta ya zuba mata kan cinyoyinta tayi saurin zame su kanshi ya bugi katakon gado, duk da haka bai damu ba, ya tallafe kanshi da duka hannayenshi yana rusa kuka wiwi kamar mahaukacin daya gudo daga gidan mahaukata, a tsorace take binshi da kallo kamar kace mata arrrrr ta ruga. "Ina sanki Deeyanah, bazan rayuwa babu ke ba, dan Allah ki taimaka min ki dawo gare ni idan ba haka ba mutuwa zanyi, tunda kika barni rayuwata ta shiga tangard'a, mutuwa zanyi muddin kika barni Deeyanah, dan Allah ki taimaki rayuwata karki barni, karki barni ina sanki, kece duniya ta, kece hasken rayuwata please...! "Ni kuma bana sanka Ajlaal idan dakai a cikin rayuwata komai nawa lalacewa zayyi dan Allah ka barni. "A'a Deeyanah ba haka bane, kizo muyi aure mu haifi 'ya'yanmu mu rayu cikin salama da farin ciki, zan baki dukkan farin ciki da jin dad'in duniya da kowacce mace ke burin samu a wajen d'a namiji, zan mayar dake macen tafi kowacce mace a fad'in duniya, zan mantar dake kowa da komai babu abinda zaki rink'a tunawa sai ni da yaranmu da zamu haifa, nayi miki alk'awarin zan shinfid'a miki rayuwata a k'asan k'afarki, nayi miki alk'awarin zan yi miki biyayya bazan tab'a sab'a umarnin ki ba har izuwa fitar da numfashi na k'arshe, nidai fata na kada ki barni, ki zauna tare da ni please, yayi maganar yana durk'ushe gabanta while yana rusa kuka. "Kai tamkar wani gajimare ne daya wanzu a rayuwata kuma ya washe, kai ba komai bane face mummunan mafarki dana tab'ayi dakai da babu duk d'aya ne a ryuwata, danni a waje na babun ma ta fiye min dan baka da amfanin komai a wajena sai tarin rashin amfani. " Deeyanah an halicce mu ne dan junan mu, nine mijinki, nine wanda zaki rayu dashi. "A'a ya isa dan Allah ya isa haka, bani da wani miji a duniya da lahira bayan Deen, shine mijina duniya da lahira, ina fata ya zama mijina har a aljanna, shine uban ya'yana dashi ne zan haihu, shi kad'ai zan haifawa 'ya'ya, danshi aka halicce ni, danni aka halicce shi, bana sanka Ajlal, Deen nake so, danshi zuciyata ke dokawa, shine zab'in rai na, kuma shine zab'in iyaye na, dashi kad'ai zan rayu nayi farin ciki. " Yanwa anzo wajen dama nasan shi d'in ba zab'in ki bane, kina tare dashi ne saboda shine zab'in iyayenki amma a bad'iri nine zab'inki, dan Allah kada ki azabatar da zuciyoyin mu ta hanyar nesanta mu da juna hakan kan haifar da rugujewar rayuwar mu. " Ya isa! Ta fad'a cikin tsawa, zayyi magana ta nuna mishi k'ofa tace " fice min daga gani daga yau kada ka sake nuna min wannan bak'ar fuskar taka, me mugun nufi, bak'in azzalumi, shaid'an mai san raba sunnar Ma'aiki, ka fice min bana fatan sake ganinka a rayuwata. " Dan Allah Deeyanah kada kiyi min haka please, mik'ewa tayi had'i da fincikar gaban rigarshi ta hankad'a shi waje, ta karkad'a mishi yatsa a fuska tace " karka sake zuwar min gidan aure in ba haka ba.... ta cije leb'enta na k'asa da k'arfi. Hawayenshi yasa d'an yatsa ya goge yana murmushi ya kalli cikin kwayar idonta yace " kisa a ranki ke tawa ce ni kad'ai kuma zan tabbatar miki da hakan, nayi miki alk'awarin babu wani d'a namiji daya isa ya rab'eki a fad'in duniya duk wanda ya kuskura yayi gangancin rab'arki ya cije leb'enshi na k'asa yana murmushi ya juya yabar wajen. Bata damu ta furucin da yayi ba ta koma cikin d'akinta ta fad'a saman gado had'i da sakin rikitaccen kuka me cin rai tana fad'in " na cuce kaina na jefa rayuwata cikin masifar da bazan iya fitar da kaina ba, wayyo Allah kaico na kaicon rayuwata. Yana kwance d'akinshi ya jiyo sautin kukanta kad'an-kad'an d'an sararawa yayi danya tabbatar, tabbas kunnenshi bayyi mishi k'arya ba da gaske kukan nata ne, " wai me yake damun yarinyar nan ne? Ya fad'a yana mik'ewa silifas d'in dake gefen gadonshi ya sanya ya fita yana d'aure igiyar rigar baccin jikinshi, zaune ya iske ta gefen gado tana rusgar kuka, har ya shigo ya tsaya kanta bata sani ba, ya d'an dad'e tsaye kanta yana kallanta, sai da ya sauke ajiyar zuciya kana ya zauna kusa da ita ya dafa k'afarta had'i da kiran sunanta " Deeyanah! Firgigit tayi a tsorace dan bata san shigowar shi ba, murmushi yayi mata da suka had'a ido cikin dakewa yace " komai yayi tsanani maganinshi Allah, Ubangiji ya dank'a mana maganin damuwar mu a tafin hannunmu tunda yayi mu a musulmai masu imani, ya bamu Alkur'ani da addu'o'i, koma wacce irin matsala kike ciki idan kika dage da addu'a kina kaiwa Allah kukanki da sannu zai yaye miki dukkan matsalarki, kiyi hak'uri ki dangana ki mik'awa Allah komai, kiyi imani akan zayyi miki maganin dukkan damuwa da matsalarki. Hawayen ta goge ta d'aga idonta ta kalleshi cike da girmamawa tace " bazaka tambaye ni komai ba Yaya? Kyakkyawan murmushi yayi yace " bazan matsa miki kamar wancan karon ba, idan kin so kinga na cancanci nasan damuwarki, keda kanki zaki sanar dani komai, bana san sake haifar miki da wata damuwar bayan wacce kike ciki. Wani abu dake neman huda k'irjinta ta danne tace " kayi hak'uri Yaya, na jefa rayuwarmu cikin matsala, na mayar da gidan mu tamkar gidan zaman makoki, na gurb'ata kyakkyawar alak'ar dake tsakanin mu, na wargaza farin cikinmu, na lalata komai, kana da matarka ta aure ta sunna na mayar dakai tamkar gwauro duk da nasan kana da yawan buk'atar mace amma saboda san zuciya ta na rufe idona, nak'i tausaya maka, na danne maka duk wani hakk'inka dake kaina, na tauye maka damarka da Allah ya baka a kaina, amma duk da haka kayi hak'uri dani, ka jure duk wata musgunawa ta, na jefa rayuwar mu cikin bak'in bala'in da babu me fitar damu sai Allah, ka yafe min dan Allah, ta k'arasa maganar cikin matsanancin kukan dake huda zuciyarshi."Kiyi addu'a in sha Allah komai zaizo mana da sauk'i, da yardar Allah komai zai gyaru. "Kayya kayya Yaya, adayyi shiru kawai amma har abada babu abinda zai gyaru. "Subhanallahi haba sai kace ba musulma ba, sai kin yiwa kanki bak'in bakin da zai biki, babu abinda zai gagari Allah kedai kiyi addu'a. Murmushi ya sake yi mata ya mik'e yaja mata bargo ya rufe ta yana fad'in " ki kwanta sai da safe. Tana san tace ya tsaya ya taya ta kwana amma tana jin kunyar fad'ar hakan, tana ji tana gani ya fice bayan ya kashe mata fitilar d'akin, ta sauke nannauyan numfashi had'i da rufe idonta tunaninka kala-kala na zuwa kanta, har bacci yayi awon gaba da ita. ************************************* " Ajlaal wai meke damunka ne? "Duk kabi kayi wani zuru-zuru dakai kamar mahaukaci saban kamo, Abbanshi ya fad'a yana kallan shi. A fili Mama ta sauke ajiyar zuciya had'i da cewa " jibi yadda ya lalace ya rame ya jeme, ka fad'a mana abinda ke damunka matuk'ar baifi k'arfin mu ba zamuyi maka maganinshi da izinin Allah. "Ina santa! Itace rayuwata, ita kad'ai ce macen da nake so, dan ita numfashi na ke fita, dan ita zuciya ta ke bugawa idan na sake rasata a karo na biyu bazan iya jurewa ba, mutuwa zanyi, dan Allah ku taimaka min ina santa da duka zuciya ta. Kallan juna Mama da Abbah sukayi cikin mamakin dake bayyane saman fuskarsu k'arara, mayar da kallanshi Abbah yayi kan Ajlaal yace " bamu fahimce ka ba? "Kayi mana k'arin bayanin inda kalamanka suka dosa wacece kake son? A wahalce muryarshi na rawa yace " Deeyanah! Abbah Deeyanah ce ina matuk'ar santa akanta zan iya aikata komai, please ku taimaka min karku rasa ni. Sake kallan juna Mama da Abba sukayi a karo na biyu  sai dai wannan karon ba mamaki bane bayyane saman fuskarsu ba, tsoro ne, tsoron kodai tilon d'ansu ya haukace ne, dan su a iya saninsu Deeyanah ta dad'e dayin aure, bama zasu iya tuna adadin shekarun ba, a k'iyasi dai sun san yanzu tayi yara hud'u, amma ita yake magana yanzu? "Meyasa kake magana akan matar wani? "Meyasa kake magana akan Deeyanah bayan kafi kowa sanin tana da aure harda yara? "Meyasa bazaka hak'ura da ita ka nemi wata ka aura ba? "Ita dai Abbah, Deeyanah daka sani ita. "Kodai ka fara shaye-shaye ne Ajlaal bamu sani ba? Abbah yayi maganar yana kallan Ajlaal d'in cikin tashin hankali. "Ban fara ba amma ina gaf da farawa a kowanne lokaci. "Wata k'ila ma ta dad'e da mantawa dakai a rayuwarta tana can tana rayuwarta cikin farin ciki ka tsaya kana azabtar da kanka a banza, please ka sawa ranka hak'uri da salama ka dangana ba komai muke so muke samu ba a rayuwa, sau da yawa zaka ga abinda muka so bashi ne yake zama rabon mu ba, haka ba shine alkhairin mu ba. " Rasa wanda muke so nuni ne na cewa raban mu yana ta can wani wajen yana neman mu, dan mun fad'i a soyayyar wani ba yana nufin mun rasa soyayya ta har abada bane, ba asara bane danka rasa wanda kake so, asara shine ka rasa kanka wajen k'aunar wanda kai a wajenshi ba komai bane, sauk'i yana tare da tsanani, mai hak'uri yana cimma dad'i, mai kyauta baya tab'a rasawa, duk wanda yaji tsoron Allah Ubangiji zayyi mishi mafita, manta da damuwa ka fuskanci rayuwa, kowa ka gani a duniya da akwai abinda ya dame shi. " Fadadawa rayuwa ce, tsukakewa mutuwa ce, rayuwa itace yiwa kowa fatan alkhairi, san wawashe komai wa kanka ba komai cikinsa face halaka, a kowacce mu'amula ka zama mai gaskiya da rik'on amana saboda baka san yaushe ne, a wanne lokaci a ina ne cutar dakai zata farauci rayuwarka, duniyarka da farin cikinka ba........ " Kai dalla can dakata shashasha sauna asararran banza kawai ba wa'azi yazo yace kayi mishi ba ka cika mutane da surutun banza duk kabi ka tofe mu da yawu, haka ka tsaya shirme a wancan lokacin na baya har ya rasata, Mama ta fad'a cikin masifa tana galla mishi harara kamar idanuwanta zasu fad'o k'asa, lakwas Abbah yayi duk da yana san ya sake yin magana amma tsoronta dake danne shi ya hana. Kallanta ta mayar ga Ajlaal tana huci kamar wacce tayi tseren gudu tace " kaima kai ka tsaya kana b'atawa kanka lokaci wannan gantallen daka d'auka a matsayin uba wacce uwar zai iya yi maka? "Ka fita kaje ka nemi soyayyarka ta kowanne hali, kada ka sake ka dawo min gida batare da suruka ta abar k'aunarka Deeyanah ba, kayi koma meye danka mallake ta. Cikin sanyi cike da fargaba Abbah yace " koma meye kika ce f..... kallan data watsa mishi yasashi had'iye sauran maganar dole. ********************************* Tana zaune saman sallaya ta d'aga hannayenta tana tsiyayar da hawaye me k'una da take jinsu tamkar soyayyan mai, addu'a take yi sosai ta neman yafiya. "Ya Ubangijin al'arshe ya Ubangijin sammai da k'assai, kaji k'aina ka yafe min zunubaina, Kai mai rahama ne, mai tausayi ne, mai yafiya da afuwa ne, ya Allah na sani ni mai tarin zunubai da manyan laifuka ne wad'anda suke rinjaya ta, ya Allah ka....... Banko k'ofar da akayi yasata saurin d'agowa ta kalli k'ofar, ya fad'o d'akin tamkar an jeho shi, yayi tsaye k'erere kanta, daga k'amshin turaren jikinshi ta gane shine batare data d'ago kanta ta kalle shi ba. A galabaice ya kira sunanta " Deeyanah!. Yadda kasan ba sunanta ya kira ba ta cigaba da addu'arta. "Ina sanki Deeyanah dan Allah karki barni, karki juya min baya a sanda nafi buk'atarki, wallahi nafi Deen sanki, ki yarda dani, kizo mu gudu muyi ta can wani b'angaren duniya, muyi rayuwa daga ni saike sai yaranmu. Addu'ar ta shafa kana ta mik'e ta ninke sallayar ta aje, ta nufi gado ta kwanta yadda kasan bata san da mutum ba, jikinshi na wata irin rawa kamar mazari ya isa gareta yasa hannu ya d'ago ta ya mannata da k'irjinshi, a fili ya sauke ajiyar zuciya yana fad'in " a wajenki kad'ai nake samun irin wannan nutsuwar dan Allah karki guje ni..... A zuciye ta fisge jikinta daga nashi tana jin turirin azabar da fatar jikinta ke fitarwa tamkar ya watsa mata wuta, cikin matsanancin b'acin rai ta yarfa mishi mari a saman kuncin shi, zayyi magana ta dakatar dashi da hannunta tace. "Kamar ban tab'a fad'a maka bana bana san kana tab'a min jikina ba? "Sau nawa kake san na sanar dakai illa da bak'ar masifar dake tattare da hakan? "Sanki ne ke neman haukata ni. "K'arya kake baka so na Ajlaal, wallahi da kana so na daka so min kyakkyawan k'arshe da gamawa da duniya lafiya, da kayi min sha'awar rayuwa mai kyau, daka yi min fatan kusanci da Allah da samun rabauta duniya da lahira, da kayi min addu'ar shiga Aljanna, da kayi min addu'ar neman tsari da wuta, da kayi min fatan rahamar Allah, amma kai da kake ikirarin kafi kowa so na, kaine zaka kama hannuna ka shigar dani wuta. "Kana tak'amar kana so na d'inne zaka nisanta ni da mahaliccina? "Kana so na zaka nisanta ni da samun rahamar Ubangiji? "Kana so na zaka rabani da dukkanin farin ciki na? "Kana so..... " Dakata Deeyanah! Ya fad'a yanayinshi yana canjawa! " Wallahi idan duniya zata tashi, babu mahaluk'in daya isa ya rabani dake koda kuwa keda kanki ne, koda hakan yana nufin kawo yak'in duniya na k'arshe, ban damu da adadin mutanen da zasu rasa rayukansu ba, dan haka ki dawo cikin hayyacinki, a baya na baki zab'i biyu kink'i d'aukar ko d'aya, to yanzu ma zan sake baki wani zab'in imma ki dawo mu d'ora daga inda muka tsaya ko kuma ki kashe aurenki kizo muyi aure ko kuma in turawa mijinki video dan yana nan a wayata har yanzu, kinga ai dole ya sake ki ki dawo min. Ta bud'e baki zatayi magana ya d'ora yatsanshi saman lips d'inta yana zagaya bakinta had'e da cije lips d'inshi ya lumshe idanuwanshi yana shafa k'irjinshi yace " ina san bakin nan naki, yana da dad'in tsotsa, ya k'arashe maganar had'e da rankwafowa zai sha bakinta, ta hannayenta ta hankad'ashi baya da iya k'arfinta gami da nunashi da yatsa tace " Allah yayi min tsari dakai la'ananne mai mugun nufi, yayi dariya yana cewa " karki manta lissafin kwanakin fa sati d'aya yana nufin kwanaki bakwai, bai jira tayi magana ba ya fice, rasa abinda zatayi ne yasata durk'ushewa a k'asa ta fasa rikitaccen kuka. Anan k'asa tana kuka bacci yayi awon gaba da ita, sha biyu dai-dai na dare ringing d'in wayarta ya cika dak'in ta farka firgigit cikin rashin nutsuwa, da sauri ta kaiwa wayar raruma hannunta ya danna wajen amsa kira batare data sani ba, "irin wannan bacci haka kamar ina kusa dake, yayi maganar sautin dariyarshi na ratsa cikin kanta, " tik tok tik tok lokacinki yana tafiya fa yau saura kwanaki shida, batayi mishi magana ba ta datse kiran had'i da kashe wayar tayi jefa da ita gefe. Tun daga wannan rana kullum Ajlaal sayya kira layinta ya tuna mata lissafin kwanaki, yauma tana tsaye a kitchen tana yankan albasa wayarta ta soma vibrating ko inda wayar take bata kalla ba ta cigaba da aikin gabanta, kira akayi tayi akai-akai, ta wawuri wayar a zuciye zata kashe ta, ganin ba number shi bace yasata sauke ajiyar zuciya a fili had'i da d'aga wayar, " ahhhhh! k'aunata yankan albasar ne ya hanaki d'aga wayata? Wayar ta raba da kunnenta da niyyar kashe wayar yayi saurin fad'in " saura awanni 72 bi ma'ana kwanaki uku suka rage miki, na rantse miki da girmin Allah idan har baki yanke hukunci kafin wad'annan kwanakin ba saina sanar da mijinki duk abinda ke tsakaninmu na kuma bashi tabbaci ta hanyar tura mishi video..... "Idan kuma ni na fad'a mishi da bakina fa? D'auke wuta yayi d'if dan jin maganar yayi a bazata, d'auka yayi baiji abinda ta fad'a sosai ba, dan haka yace " eh! "Eh!, nace idan kuma na riga ka na fad'a mishi komai da kaina fa shikenan barazana ta k'are? Dariya yayi sosai me isar shi, dan dakyar ya iya tsayar da dariyar yace " wasa kake! wai irin ki bani mamakin nan, ko giya kike sha kya soma tunkarar Deen da wannan maganar? "Zancen banza ma kenan, murmushi tayi me ciwo had'i da fitar da numfashi ta kashe wayar batare datace komai ba, gas d'in da take girkin ta kashe ta koma falo ta shiga safa da marwa tana tunani. " Gwara kawai na fad'a mishi koba komai na huta da barazanar Ajlaal, kuma zan ji sauk'in nina fara fad'a mishi akan ace Ajlaal d'in ne ya fara sanar dashi, d'aki ta koma ta zauna saman gado, kamar an tsikare ta ta mik'e zambur ta shiga bathroom, babu abinda tayi a bathroom d'in ta fito ta sake komawa falo, ji tayi gaba d'aya gidan yayi mata zafi, tabbas da ba musulma bace ita da kirat d'in giya zata siyo ta shiga d'aki ta rufe kanta tayi tsirara ta sha giyar tayi mankas, wata k'ila idan ta bugu zata d'an manta damuwarta koda ta wucin dagi ce. **********Idonta kan makekiyar tv bango tana kallan tashar sunna inda Malam Argugun yake wa'azi akan zaman takewar auratayya ji take tamkar sunanta yake kira yana wa'azin dan kusan gaba d'aya wa'azin ya shafi rayuwarta, da zamantakewar aurenta, wani hawayen bak'in ciki masu ciwo ne suka zubo mata, cikin kukan dake cinta tana danne shi tace " in sha Allah yau za'ayita ta k'are, bazan dauwamar da rayuwata cikin tsoro da firgicin tunuwar asirina ba, gwamma kawai na fad'a duk abinda zai faru ya faru. Ta mik'e zata fita ya shigo sanye da jallabiya yatsanshi na latsa carbin tally counter, dakyar cikin dakewar zuciya ta runtse idonta da k'arfi muryarta na sark'ewa tace " in....ina....san....maga...na dakai, ta fad'a a rarrabe kamar me koyan magana. "Nooooooo! Ajlaal yace da k'arfi had'i da wawurar computer gabanshi ya bugata da k'asa idanuwanshi sukayi jajir kamar wuta " a'a Deeyanah karkiyi min haka please, data ce zata fad'a mishi bai tab'a d'auka da gaske zata iya sanar dashi ba, bai d'auka tana da irin wannan k'arfin halin da dakewar zuciyar ba, yayi zaton shaci fad'i ne kawai ta fad'a ne danya kyale ta, dayasan da gaske take da yayi mata barazanar kashe shi idan ta sake ta fad'a mishi. Ba musu ya k'araso ya zauna kan d'aya daga cikin kujerun har lokacin tana tsaye bata zauna ba, "ina jinki, yace yana bin jikinta dake rawa kamar mazari da kallo, kasa magana tayi ta kuma kasa zama, yakai mintuna goma a zaune yana jiranta, jin batace komai ba yasashi mik'ewa zai bar wajen, tayi saurin zubewa gabanshi had'i da rik'e k'afarshi gam ta saki rikitaccen kuka wiwi kamar wacce ake zarewa ranta. Komawa yayi ya zauna ya zuba mata ido yana nazartar ta, an sake d'aukar lokaci batayi magana ba, bata kuma da niyyar yin magana, "Lafiya Deeyanah? Ya fad'a a nutse, jajayen idanuwanta ta d'ago ta zuba mishi ta kalli cikin kwayar idanuwanshi, " bari na kalle ka Yaya wata k'ila bazan sake samun damar kallanka ina matsayin matarka ba, cikin rashin fahimta yace " ban gane ba? Sake fashewa tayi da kuka tare da sake rik'e k'afafuwanshi gam, " na lalata komai Yaya, na wargaza komai, na cuci kaina, na lalata rayuwata nayiwa kaina babbar illa, na sari kaina da bak'in dafi, nayi BAK'AR SHUKAR da har in mutu bazata daina yad'o ba, Yaya BAK'AR SHUKAR danayi ce ta fara fidda bak'ak'en 'ya'ya, ka yafe idan zai yiyu Yaya. "Wai meke faruwa ne? Ya fad'a gabanshi na tsananta fad'uwa, sai da ta runtse idanuwanta da k'arfi dakyar ta motsa bakinta ta had'a kalaman " NA CUCE KA, NACI AMARKA Yaya, daga nan ta kwashe komai tasss tun daga farko har k'arshe ta fad'a mishi. Ji yayi an fisgeshi an d'aga shi sama an buga shi da k'asa da k'arfi, kamar zararre ya kwashe da dariya yace " Deeyanah kenan a sani na baki da k'awaye balle ince sune suke zagaki ki rabu dani, idan har rabuwa kike san yi dani basai kin biyo ta wannan hanyar ba, dakin sanar dani da zan sawwak'e miki kuma na d'orawa kaina laifin idan ma iyayenmu kike ji, bazan bari kiyi laifi ba zan wanke ki a idonsu, cikin kuka ta kama kafad'unshi ta girgizashi tana fad'in " da gaske nake Yaya wallahil azim babu k'arya a magana ta. Murmushi ya sake yi a karo na biyu yace " kice dai kawai kin daina so na Deeyanah ko kuma dama tun farko bani kike so ba matsa miki akayi batare da an tambaye ki ra'ayinki ba, zatayi magana ya dakatar da ita ta hanyar d'aga mata hannu ya mik'e yana fad'in " a gida d'aya aka haife mu muka girma, a d'aki d'aya aka rene mu, mutane d'aya ne sukayi mana tarbiyya Deeyanah idan har ke mace zaki iya aikata wad'annan abubuwan a tarbiyyar da aka bamu to ni namiji da yanzu ba'a san inda nake ba, ki rink'a tunani kafin ki zartar da abu ki tuna da mutuncin iyayenmu dana ahalimu dana gidanmu, koda ace kina san rabuwa dani bai kamata kiyiwa kanki irin wannan mummunan sharrin ba, zan baki kwanaki biyu kiyi tunani idan kinga kina san rabuwa dani shikenan, amma ki sani ina sanki, ina matuk'ar k'aunarki. Tana gunjin kuka tana fad'in " na rantse maka da girman Allah da gaske nake, amma baiko juyo ba ya fice. Bayanshi tabi da kallo cikin ranta tana jinjina girman yarda da amintar da yayi da ita, tabbas miji ne nagari, ya yarda da ita fiye da yadda ya yarda da kanshi, da kanta da bakinta ta sanar dashi komai amma duk da haka yak'i yarda ina kuma ga ace wani ne ya fad'a mishi, lalle Deen ya cika cikekken masoyin da za'ayi alfahari dashi a ko'ina a gaban kowa. Tabbas yana zarginta amma ko kusa tunaninshi bai tab'a kaishi nan wajen ba, bai tab'a kai zarginshi ko kusa da nan ba, shi bama Deeyanah daya sani tun tana jaririya ba ko wata macen baya zaton zata aikata irin haka cikin hayyacinta sai dai idan an gusar mata da hankalinta, ya k'arashe tunanin yana gyara kwanciyarshi. Kanshi ya d'aga sama yana kyalkyala dariya kamar kafuran farko, " duk da kin sanar dashi babu abinda zai canja yanzu ma aka fara wasan Deeyanah. Yadda taga dare haka taga rana komai ya dawo mata sabo fil saboda kuka har muryarta ta dishe dakyar ta mik'e da lalube ta shiga bathroom dan bata gani sosai saboda kumburin da idanuwanta sukayi, turus tayi ganinshi zaune saman WC yana ganinta ya mik'e yana dariya " dama ke nake ta jira tun d'azu, hannuwanshi ya hard'e a k'irjinshi ya jingina bayanshi da bango, idonshi cikin nata fuskarshi d'auke da shu'umin murmushi. "Malama Deeyanah kenan, kina ta cika bakin zaki fad'awa mijinki ki huta da barazana ta, banyi tsammanin da gaske zaki iya fad'a mishin ba, dan banyi tunanin kina da k'arfin hali har haka ba, amma bakomai tunda fad'a mishin bayyi amfanin komai ba, yak'i saurararki saima gwaleki da yayi yama d'auki maganar taki shirme, kuma shaci fad'i! ya k'arasa maganar had'i da tab'e baki ya d'aga gira d'aya irin I don't care d'innan, a hankali ya taka gabanta ya d'an sunkuya kad'an kasancewar ya fita tsayi, yakai bakinshi saitin kunnenta yace " karki damu har yanzu kina da sauran lokaci kuma ina nan ina jiranki, you're highly welcome k'ofa a bud'e take, ya k'arashe maganar had'i da hura mata iska a kunne ya kashe mata ido d'aya, ya rab'a ta gefenta zai wuce fuskarshi d'auke da murmushin cin nasara. Har yakai bakin k'ofa zai fita ya jiyo muryarta tana fad'in " Yarda! aminta, yak'ini! Juyowa tayi ta fuskance shi had'i da sakin hannunta data hard'e a k'irjinta ta furzar da iska daga bakinta tace " mema kace? "Shirme! shaci fad'i! ya gwale ni, bai saurare ni ba ko? Idonta ta bud'e tar cikin nashi tana kallanshi eyeball to eyeball tare da fad'in " duk ba su bane, Yarda! Amincewa da yak'ini ne, ya yarda dani fiye da yadda ya yarda da kowa da komai har da kanshi, ya aminta dani ya bani amana fiye da kowa, zuciyarshi nada yak'ini akaina shiyasa yak'i yarda da maganar duk da kasancewar ni da kaina da bakina na fad'a mishi, sai kayi tunani idan da wani ne ya fad'a mishi fa? "Kwakwalwarka bazata iya hasaso abinda zai faru ba, so ka sani ba gwashale ni yayi ba, yarda dani da yayi yasa, bai zai tab'a tunanin irin wannan muguwar sakayyar daga gare ni ba. Baki ya tab'e had'e da d'age gira d'aya irin bai dame ni ba, " duk da wannan tarin yarda da yayi dake kike san na wargazata ta hanyar nuna mishi videon blue film d'inki? " Gaskiya bai kamata kiyi mishi wannan BAK'AR SHUKAR a zuciyarshi ba, dan bazata tab'a barin zuciyarshi ba, ina baki shawarar kibi shawarar daya baki ta sakinki kike son yayi, kice mishi eh kawai kinga asirinki bai tonu ba, ki dawo min mu dasa. " Turrrr dakai da wannan k'azamin tunanin naka, wallahi dana dawo maka na gwammaci mutuwa sau dubu, na gwammaci duniya da abinda ke cikinta su gujeni su kyamace ni, na gwammaci kwanan bola. "Un'un'un me yayi zafi haka Malama Deeyanah Allah ya bada hak'uri? "But you're out of time, lokacinki yana tafiya dan sauranki 55hrs, kwanaki biyu da wasu 'yan a wanni, I hope you're ready for the fight, duk wata dak'ik'ar agogo dake bugawa tana tafiya ne da komai naki, tik tok tik tok get ready, ya fad'a yana barin wajen, tabi bayanshi da kallo batare datace komai ba. ***********A hankali ta tura k'ofar d'akin ta shiga cikin sand'a kamar b'auniya, yana zaune saman sallaya bacci na fisgarshi jin an tab'a k'ofa yasashi ware idanuwanshi akan k'ofar yana jiran me shigowa, ganin itace ya sashi lumshe idonshi had'i da sake bud'e su akanta, raban daya tsaya ya k'are mata kallo har ya manta, ta rame sosai ta fige tayi bak'i, duk tayi wani sukuku da ita yadda kasan mareniya, gabanshi ta zube ta d'ora hannayenta akan k'afarshi yayinda data kifa fuskarta akan cinyarshi, ta fashe da kukan k'unci. "Yaya ka tsaya ka saurare ni, lokaci yana k'ure mana a kowanne lokaci komai yana iya faruwa, ka tsaya muyi shawarar ta inda zamu b'ullowa al amarin tun kafin dare yayi mana, Ajlaal bashi da imani babu abinda bazai iya aiwatarwa.... Turare ta yayi daga jikinshi ya mik'e tsaye had'i da nuna mata k'ofa yace " fita! Cikin mamaki ta kalleshi tace " bazaka tsaya ka saurare ni ba Yaya? "Me yasa kak'i yarda da duk abinda zan fad'a maka ne? "Ni fa ba k'aramar yarinya bace, ina da hankali da tunani na bazan yiwa kaina irin wannan mummunan sharrin ba, dan Allah ka tsaya ka fahimce ni. Idonshi kanta yace " in banda nayi miki farin sanin dako kaina banyiwa shi ba, da saina ce ko shaye-shaye kika fara, to idan kuwa bakya shaye-shaye to tabbas ciwon hauka ne ya sameki ko kuma kwakwalwarki ta samu matsala. Kamar tab'abb'iya ta soma girgiza kanta tana fad'in " a'a babu ko d'aya, ka yarda dani wallahi gaskiya nake fad'a maka, idonshi ya runtse da k'arfi yace " nace ki fice min daga d'aki ko? Ta bud'e baki zatayi magana yace " out! a tsawace sai da d'akin ya amsa, rushewa tayi da rikitaccen kuka tana fad'in " wallahi tallahi Yaya da gaske nake naci amanarka da Ajlaal, nayi zina da aurenka, kuma yayi video lokacin da muke aikata zinar yana yi min barazanar muddin ban koma muka cigaba ba zai sakarwa duniya video, ka yarda dani dan Allah Yaya, cikin b'acin ran da kalamanta suka haifar mishi ya damk'e ta yaja ta zuwa wajen d'ak'in, tana turjewa tana ta kiciniyar kwacewa while tana ihuuun kuka tana rok'onshi ya yarda da ita. " Yaya zakayi danasanin k'in yarda dani d'in da kayi, zakayi nadamar rashin sauraro na da rashin d'aukar magana ta da muhimmanci, jefa ta yayi waje ya mayar da k'ofar d'akinshi ya rufe, bata bar k'ofar d'akin ba saima bugun k'ofar d'akin data farayi tana kuka tamkar ranta zai fita tana fad'in " ka yarda dani dan Allah Yaya. Ya rasa abinyi ya rasa abin kamawa, kanshi ya gama kullewa gaba d'aya, wani iri yake ji cikin kanshi, bathroom ya shiga ya d'auro alwala ya tada sallah ko zai samu nutsuwa. Tun daga wannan lokacin Deen ya ida fita a sabgar Deeyanah d'an abincin da idan ta dafa da yake ci yanzu ya daina ci, duk wani abu da zai had'ashi alak'a da ita ya daina yi, ko magana bayayi mata, yayinda babu irin nacin da rok'onshi da Deeo batayi ba akan ya tsaya ya fahimce ta suyi magana, dan lokacin su na k'urewa amma yak'i sauraronta dan a tunaninshi zuga ta akeyi ta rabu dashi. Cigaban Labari........ Saukar ruwan tsarin data ji a jikinta ne ya dawo da ita cikin hayyacinta, lokaci d'aya amai ya taso mata sakamakon dukan hancinta da warin ruwan yayi, bata gama dawowa cikin hayyacinta ba yaji muryar wani figigin mutum ramamme kamar a hureshi ya fad'i yana sanye da riga 'yar shara yana fad'in. " Yawwa Alhamdulillah yau nayi kamu dama na dad'e ina kwantan b'auna a wajen nan ina san na kama tsinannun dake bin duhun dare suna yi mana iskanci a cikin kangon nan, tur daku munafukai duk kunbi kun addabi yaran unguwa da tumaki, ku baga mutane ba ku baga dabbobi ba, cikin sanyinta tace " wallahi ba... bayan hannunshi ya saka ya gwab'e mata baki ya d'ora da " bak'ar annamimiya rufe mana baki, imma kwastamominki kike jira to wallahi tun da sauran rab'a a zuciya ta ki tashi kibar wajen nan inba haka ba na nad'a miki na jaki, na zage iya k'arfina nayi miki mugun duka, ya k'arashe maganar had'i da tofa mata wawwaran yawonshi a fuska me d'oyi kamar rub'abb'iyar jab'a, gefen bakinta dake zubar da jini tasa hannunta ta goge, ta kalle shi sosai kana ta mik'e tabar wajen, har ta d'anyi nisa tana jiyo bambamin bala'in mutumin. Duhun daren bai bata tsoro ba taita tafiya harta fita daga dajin ta isa titi, babu kowa gari yayi tsit baka jin komai sai sautin kukan tsuntsaye, tana cikin tafiya wata bak'ar mota hayis ta faka a gabanta wasu k'attin maza suka fito, basuyi wata-wata ba suka damk'e ta nan fa dambe ya b'arke tsakaninsu, ihuuuun neman taimako ta somayi da iya k'arfinta. "Wayyo Allah jama'a a taimake ni zasu sace ni, ban san su ba!. Tsaye yayi gefensu hannunshi na dama rik'e da sharb'ebiyar adda while d'aya hannun yana rik'e da wani abu da duhu ya hana su gane kome nene, idonshi kanta yana kallanta yace " a karo na farko a rayuwarki ki nemi taimako na, ni kuma nayi miki alk'awarin d'ayansu bazai bar nan a raye ba, d'aya daga cikin mutanen ya tunkaro shi yana fad'in " kai har waye da kake cewa d'ayanmu bazai bar nan a raye ba? "Kalli yawan mu fa! Mu bakwai kai kuma kai d'aya ne, ya fad'a yana hankad'a shi baya, bai kula mutumin ba yace " ki nemi taimako na, ya fad'a idonshi kanta. " Wallahi dana nemi taimakonka na gwammaci ni da kaina da k'afafuwa na na bisu duk da kasancewar ban sansu ba ban tab'a ganinsu ba amma ina da yak'in sun fika tausayi da imani, a hasale yayi magana da k'arfi cikin zafin rai " nace ki rok'e ni ko? Kallanta ta mayar ga k'attin mazan tace " muje ko!, ta fad'a tana wucewa gaba zata shiga motar, yasan halin Deeyanah da shegen taurin kan tsiya kamar na kafiran farko, ya tabbatar data rok'i taimakonshi gwara ta bisun, idanuwanshi ya runtse da k'arfi ya bud'e a lokaci d'aya suka canja launi zuwa asalin jajaye, cike da matsanancin mamakinta k'attan maza suka bi bayanta zasu shige motar, yadda kasan k'iftawar ido ya sare kan uku daga cikinsu. Kallan gangar jikin matattun dake zube k'asa babu kawuka suka yi kana suka mayar da kallansu gare shi, d'ayan na k'ok'arin ciro bindiga ya sare kanshi shida na bayanshi, ihuuu sauran biyun suka saki had'i da yankar daji a guje dan ceton rayuwarsu. "Ni kad'ai ne a duniya nake da ikon cutar dake, ni kad'ai ne nake da ikon saka hawayenki zuba, ni ke da iko akanki, ni ke da ikon yi miki komai bayan ni babu wani mahaluk'i daya isa ko inuwarki ya cutar, bai jira amsarta ba ya juya bar wajen. Kallan gawarwakin tayi babu d'igon tsoro a tattare da ita, ta dad'e tana kallansu kana tasa k'afa ta tsallake su tayi nata waje. Sai da tayi nisa da wajen sosai kana ta samu gindin bishiyar darbejiya ta zauna bata yi bacci ba har aka kira sallar asuba, kasancewar babu ruwan yin alwala yasata yin taimama, mayafin data d'aura a kanta ta warware ta yafashi sosai a jikinta ta tada sallar, haka kan k'asa babu abun shinfid'awa tayi sallar, bayan ta idar ta d'aga hannayenta sama ta soma yin addu'a while hawaye na bin kuncinta, ta dad'e tana addu'ar har garin Allah ya waye kana ta shafa, ta kakkab'e jikinta sannan tabi hanya dan yunwar data ke ji bazata kyale ta ba. Ta dad'e tana kartar k'asa da k'afufuwanta dako takalmi babu ga zafin rana, ta k'arasa gari, gaban wata me siyar da koko da k'osai tayi tsaye tana kallan k'osan tana had'iyar yawu kamar mayya, batare dame k'osan tace mata komai ba ta zuba mata a cikin faranti ta mik'a mata, saura kad'an ta afka cikin man toya k'osan saboda yadda jikinta ke muguwar tsuma da kerrrrma. "Bi a hankali mana, me k'osan ta fad'a tana kallanta, " zaki sha koko? Da sauri ta d'aga mata kai, alamar eh, batayi mata magana ba ta d'auki robar siyar da kokon ta zuba mata ta saka mata siga da ludayi ta mik'a mata, da hanzari ta karb'a bakinta cike da k'osan data cunkusa a bakinta tace " nagode! Mai k'osan bata ce mata komai ba illa satar kallanta da takeyi harta gama shan koko da k'osan, ta mik'a mata robar da farantin tana fad'in " nagode sosai Allah ya saka miki da mafificin alkhairinshi yadda kika taimakeni Ubangijin Rahama ya taimakeki, fuska cike da murmushi ta amsa mata da " Amin ya Allah nagode nima. Maimakon tabi titi saita sake yankar daji ta natsa taitai tafiya, sai da ta fice daga cikin gari kana tasamu gindin bishiya tayi kwanciyar dama ciki ya d'auka dakyar ta kawo kanta wajen saboda baccin da take ji, bacci ya soma d'aukarta taji an jeho mata k'urgumemen abu jikinta firgigit tayi ta bud'e idanuwanta dake cike da bacci, ganinka ba alheri bane ta gani tsaye kanta, (sunan da take kiranshi dashi) yasata saurin bud'e idanuwanta a kanshi. Wani abu ya wulla mata a cikin kwali, kwalin na fad'uwa ya rabe biyu kan mutum ya mirgino zuwa gabanta kallan abun tayi taga kan wannan mutumin ne daya zuba mata ruwan tsami a jiki ya kuma tofa mata yawu, ko gezau Deeyanah batayi ba balle tsoro ko firgici ya bayyana a tattare da ita, kallan kan mutumin tayi had'i dayin tsaki tasa k'afa tayi ball da kan ta juya ta gyara kwanciyarta tana fad'in " ni ai yanzu naci dubu sai ceto babu wata gawar da zata razana ni, ta rufe idonta da nufin yin bacci amma sai me? Ranar da komai ya k'are mata a rayuwarta, duniyarta ta tarwatse, farin ciki da walwala suka yanke mata ta shiga dawo mata cikin kwayar idanuwanta. Waiwaye.... Wayar ta data dame ta da ringing ta d'aga kamar jira yake ta d'aga ya kwashe da mahaukaciyar dariya yana fad'in " tik tok tik tok rana bata k'arya sai dai uwar d'iya taji kunya, yau ne adadin kwanakin dana baki zasu cika cif-cif ina fatan kin shiryawa komai, kin shiryawa tarbar aradu daka? Zatayi magana yayi saurin cewa har yanzu kina da sauran 10 second, so mu irga tare, amma ki sani idan har sakanni goman nan suka cika batare da kin d'auki zab'in daya danace ba har ki mutu kina danasani, so mu fara irgawa 10,9,8,7,6,5,4,3,2,1,0 ....., sai kawai ji tayi ya kashe wayar, wayar ta zame daga kunnenta ta zubawa ido kamar tana jiran wani abu ya fito ta cikin wayar. Yana tsaye gaban mudubi ya fito daga wanka k'ugunshi d'aure da towel ya matsi lotion zai shafa a fuskarshi wayarshi ta d'an yi k'ara alamar shigowar sak'o kallan wayar yayi haka nan yaji gabanshi yayi muguwar fad'uwa, d'auke idonshi yayi daga kan wayar ya cigaba da abinda yake yi, har ya gama shiryawa bai sake bi takan wayar ba danshi yama manta da shigowar sak'on, jallabiya ya zira, har ya kai bakin k'ofa zai fita wayarshi ta sake yin k'ara a karo na biyu, sai lokacin ya tuna da wayar, komawa yayi ya d'auki wayar yana nufar k'ofar fita daga bedroom d'in yana duba sak'on daya shigo, video aka turo mishi ta WhatsApp da wata new number, video ya danna yayi playing, videon ya bud'e dai-dai lokacin daya d'ora hannunshi akan handle d'in k'ofa. Tun daga kan k'afafuwanta aka soma hasko ta, hakan ya sashi tsayawa cak batare daya fita ba, macece kwance tsirara sanb'al akan gado, " subhanallah! yace yana kawar da idonshi, yana yawan jin labarin irin mutanan nan masu turawa mutane blue film ta WhatsApp bai tab'a yarda ba sai yau daya faru a kanshi, tsaki yaja yana fad'in " Allah ya kyauta, idonshi ya sauke akan wayar dai-dai sanda aka hasko fuskar Deeyanah kwance shame-shame tsirara haihuwar uwarta. Wani irin mugun shock yaji tun daga kan babban d'an yatsanshi zuwa tsakiyar kanshi, ji yake kamar ana tsistsinka mishi jijiyoyin jikinshi, wayar yake so ya saki amma yadda kasan an saka gam an lik'e ta da jikinshi, kokawa ya shigayi da numfashin shi dake neman kwace mishi, batare daya sani ba wayar ta sub'uce daga hannunshi ta fad'i k'asa, baya yaja a mugun tsorace, idanuwanshi sunyi k'uru-k'uru tamkar wanda akayiwa turaren barkono, duk da wayar ta fad'i k'asa videon bai tsaya ba ya cigaba da yi, take komai nashi ya tsaya mishi cak, babu abinda ke aiki a jikinshi, bai san yadda akayi ba sai tsintar kanshi yayi zube k'asa wanwar a tsakiyar d'akin, saboda tsabar rud'ewa yana zaune a wajen amman ji yake kamar ruhin shi ya fita daga jikinshi shine ya koma gefe suna kallon videon tare. Deeyanan shi matarshi ta sunna wacce ke d'auke da igiyoyin aurenshi itace wani k'ato da bai biya sadakinta ba yake sassak'a, tamkar wanda aka kafe idonshi akai, dakyar ya iya d'auke idonshi daga kan video, kaf-kaf jikinshi ya d'auki muguwar rawa kamar mazari, wani irin sanyi yake ji aduk wata k'ofar gashi dake jikinshi, tamkar yadda tangaran yake tarwatse haka wani abu me nauyin gaske ya tarwatse a zuciyarshi wanda yake da yak'inin har abada bazai tab'a dawowa dai-dai ba, ta cikin kunnenshi yake jiyo sautin tsistsinkewar jijiyoyin kanshi, kanshi dake barazanar tarwatsewa ya dafe da duka hannayenshi ya kurma firgitaccen ihuuu, jikinshi a sake ya mik'e sakaka, yadda kasan me koyan tafiya haka yake taka k'afufuwan ya isa gaban mudubi ta cikin mudubin yake kallan kanshi tamkar hannunshi ba'a jikinshi yake ba ya d'aga tare da nuna kanshi ta cikin mudubin muryarshi na sark'ewa yace " nine Deen kuwa? " Anya nine dai? Ya fad'a kamar zararre, hannunshi ya cusa cikin gashin kanshi ya runtse idanuwanshi da k'arfi ya shiga kurma ihuuun mutuwa, glass center table d'in dake tsakiyar d'akin ya d'auka ya jifi mudubi dashi gaba d'ayansu suka tarwatse, yana cigaba da kurrma ihuuu ya rink'a dukan mirror'n jikin wardrobe, duk da ciwon dayaji a hannunshi hakan bai sa ya daina ba, cikin k'ank'anin lokaci ya birkita gaba d'aya d'akin ya fashe komai dake cikin bedroom d'in, zamewa yayi ya durk'ushe akan gwiwowinshi, kuka yake san yayi koya samu sauk'i da sassaucin abinda yake ji amma yadda kasan an busar da idanuwanshi ko alamun kuka babu. Gidan yayi mishi bak'ikk'irin komai yayi mishi duhu, ji yake an mak'ure shi, ji yake ta ko'ina a takure yake, Babah yake san gani, Baban kad'ai zai gani yaji 'yar dama-dama, kamar wanda aka tsikara da allura yayi zambur ya mik'e ta kan gilasan daya fasa yabi ya taka wuce yaji ciwo sosai amma bai damu ba, ya fice babu ko takalmi, jijiyoyin kanshi runyi rad'o-rad'o kamar an zana su, motar da yayi parking ya shiga ya figeta ko get d'in bai tsaya an bud'e mishi ba yayi ciki da get d'in ya fice, me gadi da sauran ma'aikatan sukayi cirko-cirko suna ganin ikon Allah ga get an b'alla. Babu abinda yake gani a gabanshi sai duhu ikon Allah ne kad'ai yakai shi babban kamfaninsu, hand break yaja ya tsaida motar ya fito bai tsaya rufe ta ba yayi ciki, direct office d'in Babah ya wuce, yana zaune yana cike wasu takardu Deen ya shigo kamar an jeho shi, kallo d'aya yayi mishi ya san akwai gagarumar matsala, gabanshi na fad'uwa ya mik'e da sauri ya tako wajen Deen, zubewa Deen zayyi a k'asa Babah yayi saurin tallafe shi yana fad'in " Lafiya Deen? Baki ya bud'e da nufin yin magana amma ya nemi muryarshi ya rasa, yayi-yayi yayi magana amma ya kasa, ji yayi an shak'e mishi mak'ogwaro, bakinshi ya k'afe, zuciyarshi ta soma bugawa da tsananin k'arfi kamar zata tsaga k'irjinshi ta fito, kanshi yayi mishi mugun nauyi kamar wanda aka d'orawa dakon duniya, jinshi yake kamar a saman iska a zaune, saboda tsabar tashin hankali har yaji-yaji yake ji a idanuwanshi, fatar jikinshi kam rad'ad'i take mishi kamar ya shafa attaruhu, bakinshi ya sake bud'ewa da nufin yayi magana amma yaji numfashinshi na neman d'aukewa nan fa ya shiga kokowa da numfashinshi, yasa hannayenshi duka ya rik'e wuyanshi, office d'in ya shiga juya mishi, yayinda da idanuwanshi suka zazzago sukayi jajir kamar gauta, d'if numfashinshi ya d'auke, kafin yaji an d'aga shi sama an fyad'a da k'asa, wata irin rawa duk ilahirin jikinshi ya d'auka idanuwanshi suka kakkafe kamar me farfad'iya. Salati Babah yayi yana jijjiga shi gami da kiran sunanshi amma shiru, da sauri  ya fita ya nemo taimakon wasu daga cikin ma'aikatan kamfanin aka sakashi a mota sai asibiti, Emergency aka shigar dashi, sai da aka d'auki lokaci kafin likita ya fito. " Mugun Shock ya samu wanda ya haifar mishi da hawan jini sosai lokaci d'aya amma yanzu komai yana under control in sha Allah. " Shock? Babah ya fad'a cikin matsanancin mamaki, " eh! amma an kaishi d'akin hutu muje na nuna maka d'akin, batare da ya sake cewa komai ba yabi bayan likitan, har k'ofar d'akin ya raka shi " yana ciki, idan ya farka ka kira ni, jikin Babah a sanyaye ya amsa da to, bai san dalilin dayasa gabanshi yake fad'uwa ba, zama yayi a akan sofa yana kallan Deen dake wahalallan baccin dole sai sauke ajiyar zuciya yake yi cikin baccin, kusan awa biyar Babah yakai yana jiran Deen ya farka amma har magariba bai farka ba, mik'ewa yayi dan yaje masallaci yayi sallah. Yana fita Deen ya farka dishi-dishi yake ganin komai, a hankali ya dafa kanshi komai na dawo mishi, sai a lokacin ma ya tuna ainahin abinda ya gani a video, sai lokacin yake ganin komai tarrr, cikin kanshi yake hasko hotan Ajlaal kwance saman ruwan cikinta, k'arin ruwan ya fisge jini yayi tsartuwa daga jijiyar hannunshi, bai kula ba ya mik'e ya fita har lokacin dishi-dishin yake gani, yana tafe yana tangal-tangal kamar mashayi. Me adai-daita sahu ya tare ya shiga, dakyar ya fad'a mishi inda zai kaishi, sauka yayi ya shiga gidan yana fad'awa me gadin " ka sallame shi, bibbiyu yake ganin komai, tana zaune bakin gado duniyar tayi mata zafi saboda ta jiyo ihuunshi kuma bayan fitarshi taje ta dubo dakin taga yadda ya tarwatsa komai, a d'osane take zaune a bakin gadon a matuk'ar tsorace take, banko k'ofar da yayi ne ya sata mik'ewa zumbur, had'i da fashewa da rikitaccen kuka tana fad'in " dama na fad'a maka Yaya, na fad'a maka da kaina da baki na amma kak'i yarda dani, ganin yadda ya koma cikin yini d'aya ba k'aramin firgita tayi ba, baya ta soma ja tana girgiza kanta. Yana d'ora idonshi akanta yaji wata irin muguwar tsana da k'iyayyarta na ratsa shi, lokaci d'aya yaji babu abinda ya tsana a duniya sama da ita, duk wannan tarin soyayyar da yake yi mata babu d'igonshi, kallanta yakeyi kamar bak'in kumurcin daya kashe mishi iyaye. Muryarshi na creaking yace " meyasa Deeyanah? "Meyasa kika k'aurace min tsayin shekaru uku kika hana ni hakk'i na kika je kina bawa wani k'aton banza can? "Why Deeyanah? Ya fad'a a haukace yana nufarta, baya tayi da sauri cike da tsoro, da iya k'arfinshi ya damk'i wuyanta ya gwara da mirror, mirror ya tsage kanta ya fashe, sai lokacin yaji kuka, aiko ya fashe da mahaukacin kukan mutuwa wiwi, kamar k'aramin yaro ya rink'a rusa kuka, ya zage iya k'arfin shi ya shiga dukanta kamar yadda zai daki namiji d'an uwanshi, yana dukan yana fad'in " me ya fini? "Soyayya ya fini iyawa ko kuma sex d'in ya fini iyawa? "Joy stick d'inshi tafi tawa girma kuwa dad'i ya fini? "Dame na rage ki? "Me na gaza mishi dashi? "Nawa ne adadin kud'in da yake baki da ni bazan iya baki ba? "Kika k'aurace min, kika haramta min abinda Allah ya halatta min kike je kina bawa wanda Allah ya haramta miki kanki, duk irin san da nake yi miki Deeyanah meyasa? "Meyasa zakiyi min haka? Ya fad'a yana kuka kamar ranshi zai fita, sosai yayi mata mahaukacin duka, bai daina dukanta ba saida ya tabbatar bata motsi sannan ya daina dukanta, k'asa ya zube yana mayar da numfashi, wani irin d'aci yake ji daga mak'ogwaranshi zuwa bakinshi, yasan yau kam komai nashi ya k'are, yasan yau duniyarshi ta k'are, yau al k'iyamarshi ta kama, har lokacin bai daina kukan ba. Babah na dawowa daga sallah yaga wayam sai d'igon jini, da mamaki yake bin jinin da kallo, fita yayi ya tambayi wasu suka ce sunganshi ya hau napep, mota ya shiga yaja ya nufi gida ranshi cike da tarin tambayoyi fal, get d'in dake k'arye yabi da kallo mamakinshi na k'aruwa, cikin nutsuwa yayi parking ya fito dai-dai lokacin Abbi ya fito daga part d'insu da sauri ya nufi part d'insu Deeyanah, Babah yayi saurin cewa " wai lafiya? "Meke faruwa ne? Turus Abbi yayi yana kallan Babah yace " ban sani ba tun d'azu dai nake jiyo ihuu da kuka k'asa da k'arar fashe-fashe, " to ikon Allah, tare suka shiga cikin gidan, ya sata gaba ya kifa kanshi a tsakankanin cinyoyinshi yana sharb'ar kuka, a hankali suka turo k'ofar d'akin suka shigo dan sun jiyo sautin kukanshi, cikin tashin hankali suka nufe shi, " meke faruwa Deen? Babah ya tambaya yana danne tsoronshi, jajayen idanuwanshi ya d'ago ya sauke su akansu, sai da gaban Abbai da Babah ya fad'i saboda kallan da yayi musu, " lafiya!? "Meya faru dakai ne? Babah ya sake tambayarshi yana bin d'akin da kallo, komai dake cikin bedroom ba a dai-dai yake ba an canjawa komai gurin zama, an fasa na fasawa, an lalata na lalatawa, yadda kasan filin wasan dambe na duniya, Abbi ya bud'e baki zayyi magana idonshi ya sauka akan Deeyanah dake kwance shame-shame cikin jini, " Subhanallahi!, yace yana nufarta sai lokacin Babah ya kula da ita, jijjiga ta Abbi ya shigayi yana kiran sunanta amma shiru bata motsa ba, jikinshi na rawa suka kamata shida Babah sukayi waje da ita, Deen na zaune yadda yake bai motsa ba, a kujerar baya suka kwantar da ita, Abbi ya zagaya da sauri ya shiga motar, Baba ya lek'a ta window yace " kaje da ita bari na taho dashi a dubashi kaga sai zubar da jini yake yi ba, Abbi bayyi magana ba yaja motar yabar harabar gidan. Da hanzari Babah ya koma cikin gidan, maganar duniya yayiwa Deen amma bai tanka ba da ido kawai yake binsai yadda kasan me tab'in hankali, hannunshi Babah ya kama yaja shi ya biyo shi sakaka sai kace dolo, sanda suka isa asibitin har an shigar da Deeyanah Emergency room, da Doctor Babah ya had'a Deen, likitan yasa nurses sukayi mishi d'inku nan ciwukan dayaji a k'afa da hannu, akayi treatment d'inshi, likitan yaso ya bawa Deen gado saboda yadda jininshi yake a mugun haye, amma yak'i ya kafe kan shi bai kwanciya a asibiti, dole tasa ya k'ale shi. Yana zaune kan kujera Abbi da Babah na tsaye suna magana a junansu, yayi kasak'e har lokacin bai furta koda kalma d'aya ba, bai ma san a duniyar da yake ba, har lokacin tantama yake shine Deen, shin da gaske abin yake faruwa ko kuwa dai mafarki yake yi. Likitan ya fito daga Emergency room yana cire hand gloves, da sauri Abbi ya tare shi yana fad'in " ya jikin nata? "Alhamdulillah da sauk'i amma dukan da akayi mata yayi yawa dan har ya jawo zubewar cikin dake jikinta na watanni hud'u, koma me tayi bai kamata ayi mata irin wannan mummunan dukan ba, babu kalmar dake kai komo cikin kanshi sai cikin jikinta, kalmar ta k'arasa birkita mishi komai, duk bayanin da likita yake yi babu abinda ya fahimta sai wannan kalmar, da gaske dai Deeyanah taci amanarshi, da gaske ta wargaza musu komai, ta riga ta tarwatsa ahalinsu, ta d'ai-d'aita farin ciki da kwanciyar hankakinsu, shekaru uku, shekaru uku tayi tana azabtar dashi ta hanyar k'aurace mishi, shekaru uku tayi basu had'a shinfid'a ba balle jiki, shekaru uku sukayi wata ma'amalar aure bata gifta ta tsakaninsu ba, amma itace d'auke da cikin wani, baya tunanin an tab'a cin amanar wani mahaluk'i a doron k'asa sama dashi, sosai zuciyarshi ke tafarfasa tana azalzalarshi, tabbas yau da ace shi ba musulmi bane da rufe kanshi zayyi a d'aki yasha giya yayi tatul kana ya kashe kanshi. Komai ya d'auke mishi d'if duniya ta tsaya mishi cak, wannan wacce irin b'akar k'addara ce? Ba Deeyanah ba kad'ai duk wata mace dake duniya sai da yaji ya tsane ta, a ranshi yake jin da za'a tattara mishi matan duniya gaba d'aya da sayya zazzaga musu fetur ya cinnna musu wuta, Cikin abinda bai wuce mintuna biyar ba yayi shawara tafi dubu, k'irjinshi ya dafe had'i da fashewa da rikitaccen kuka yana fad'in " mutuwa zanyi Abbi, Deeyanah ta lalata komai, ta gama tarwatsa min rayuwa da duniya ta, babu abinda yayi saura, komai ya k'are, wayyo Allah na, na shiga uku, inama mutuwa tazo ta d'auke ni, inama na mutu kafin ganin wannan bak'ar rana, inama ba'a halicce ni ba... Saurin rufe mishi baki Babah yayi yana fad'in " haba Deeni sai kace ba musulmi ba, kana neman kaucewa hanya, me yayi zafi haka? Bayyi musu magana ba ya mik'e yana dafe da kanshi ya soma k'ok'arin barin wajen, ya d'aga k'afarshi ya yanke jiki ya fad'i ji kake timmm, jiki na kerrrma Babah yayi kanshi, yayinda da Abbi ya tafi kiran Doctor. "Sai da nace mishi zan bashi gado yak'i, likita ya fad'a yana saka mishi Cannula a hannu, ajiyar zuciya Babah ya sauke a hankali cike da damuwa yace " jinin nashi bai sauko bane har yanzu? "Ina fa ya sakko, saima k'ara hawa da yayi sosai, kuyi addu'a dan komai yana iya faruwa dashi, ina jiye mishi tsoron paralyze ko heart attack. "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, wai meke faruwa a tsakanin yaran nan? Abbi ya fad'a yana kallan Babah da yayi suman tsaye kamar an dasa shi, ya kasa magana. ************************** Yana zaune saman sofa ya d'ora k'afa d'aya kan d'aya akan dinning table hannunshi rik'e da gwangwanin lemo yana sha fuskarshi d'auke da makirin murmushi idanuwanshi akan laptop yana kallon abinda ke faruwa ta mini hiding camera daya baza ta ko'ina a gidan, zan iya cewa kusan kaf gidan ya b'oye 'yar k'aramar camera sirri wacce ta nan yake ganin duk wani motsinta. Yaga duk abinda ya faru har makahon dukan da Deen yayi mata, yaji babu dad'i har cikin ranshi, ranshi ba k'aramin sosuwa yayi da dukan ba, amma tunda ita ta zab'arwa kanta hakan shikenan ya barta, da ace gari watsagal yayi mata wannan dukan da sayya tsinke mishi numfashi, mik'ewa yayi yana kurb'ar lemon yace " na fad'a miki duk duniya babu mai sanki sama dani. Bayan kwanaki biyu.... Deeyanah ta farfad'o tun a daren da aka kawo ta, anyi mata tambayar duniya meke faruwa tsakanin su tak'i cewa komai bata da aiki sai kuka, ko kalma d'aya bata iya furtawa ba, hakan ya k'ara tabbatarwa da iyayen da akwai gagarumar matsala, a b'angaren Deen kuwa har lokacin bai farfad'o ba, hankalin kowa yakai mak'urar tashi damma likita ya tabbatar musu da babu matsala. Washe gari da safe kusan gaba d'aya zuri'arsu suna d'akin Deeyanah, suna ta fama da ita kan taci abinci ko yaya yake amma fur tak'i, a d'akin Deen kuwa d'akin ba kowa dan likitoci sun hana kowa shiga a cewar su ciwonshi baya buk'atar hayaniya, idanuwanshi ya bud'e lokaci d'aya ya sauke su akan POP bai sha wahala wajen k'ok'arin tuna komai ba dan da komai ya farka tangaran babu abinda ya manta, k'arin ruwan da ake yi mishi ya fisge ya dafa bango ya mik'e yana bin bango ya fice daga d'akin yana layi da tangad'i ya nufi hanyar fita daga asibitin Abbi da Babah daya hango yasashi saurin rab'ewa dan a zatonshi wajen shi zasu, ganin sun shiga wani d'akin daban ba wanda ya fito ba ya sashi sake bin bango ya nufi d'akin, a hankali ya tura k'ofar, bayyi zaton tana asibitin ba, komawa yayi da baya. "Dan Allah ara min paper da biro, ya fad'a da kyar, ba musu nurse d'in ta mik'a mishi, rubutu yayi a paper daya yaga kana ya mik'a mata biron ko godiya bai tsaya yi mata ba yabar wajen, d'akin da aka kwantar da Deeyanah ya koma ya tura k'ofar ya shiga, hankalin kowa yayi kanshi Ammi da Ammu dake gefe suka kalli juna kana Ammi tace " ka farka? Saboda tsabar yadda idonshi ya gama rufewa bai kula da tarin jama'ar dake d'akin ba, ita kawai yake gani, gaban gadonta ya k'arasa ya mik'a mata takardar hannunshi yana fad'in " na sake ki saki uku, daga yau na datse igiyoyin da suka dabaibaye ni dake, daga yau na yanke duk wata alak'a dake tsakaninmu, bani bake har abada bana fatan sake ganinki a rayuwata. Kowa dake wajen sandarewa yayi a tsaye yadda kasan gawar da aka dasa, babu wanda ya iya motsi balle magana, ya juya ya zai fice daga d'akin Abbi ya zaburo mishi Babah yayi saurin tare shi yana fad'in " aikin gama ya gama ka barshi ya samu nutsuwa kaji dai abinda likita yace, sai a lokacin ya kula da mutanen dake d'akin, cikin matsanancin b'acin rai da zafin zuciya Abbi ya bud'e baki zayyi magana Babah yayi saurin tarar numfashin shi da fad'in " dan Allah karka ce komai yanzu cikin fushi karka k'arasa dagula komai, nasan waye Deen fiye dakai duk da kai ka haife shi, nasan bazai tab'a aikata haka bashi da kwakkwaran dalili ba, tasan masifaffan son da yake yiwa Deeyanah, yasha fad'a min bazai iya rayuwa babu ita ba, yasha fad'a min itace rayuwa shi batare da yayi la'akari da cewar nina mahaifinta ba, ka kwantar da hankalinka abi komai a sannu kar muyi gaggawa. Kanta ta kifa saman pillow ta fashe da wani irin rikitaccen kuka tana fad'in " na cuci kaina, na lalata komai nawa, babu wanda ya iya furta koda kalma d'aya balle a samu mai rarrashinta. Saki! Kalmar da take jikinta a bakin wasu, kalmar dako kusa bata hasaso ta a kanta ba, kalmar da tayi yak'ini kan baza'a tab'a furta mata ba, kalmar da take tunanin tayiwa nisan nisa, yau ita aka furtawa kalmar saki!, jin abin take yi kamar almara, jin yanayin take yi, kamar a mafarki, ta kasa gaskata abin, duk da tasan ta cancanci fiye da haka. A galabaice ya koma gida, part d'insu ya wuce ya shige bedroom d'inshi, babu abinda ya tab'a a gidan sai wasu daga cikin kayan sawarshi ya fice daga part d'in dakyar ya danni kanshi ya koma part d'in Babah, d'akinshi nada ya koma, yana shiga ya watsar da kayan a tsakar d'akin ya zauna ya had'a k'afafuwanshi ya cusa kanshi ciki. A ranar a daddare aka sallamota daga asibiti, jikin kowa a sanyaye k'afa a sage suka dawo gidan, Ammi taso ta wuce part d'insu amma tak'i tace a part d'inta zata zauna dan tayi zaton Deen nacan, zatafi samun damar rarrashinshi su fahimci juna, da taimakon masu aiki aka gyara gidan tsaf, dakyar Ammi ta matsa mata tayi wanka, abinci kam babu yadda ba'ayi da ita ba amma tak'i cin ko kad'an, dan kar a dame ta, ta kwanta had'i da rufe idanuwanta kamar me bacci, ganin haka yasa kowa ya fice, suna ficewa ta tashi zauna ta fashe da kuka. Tsakar dare da misalin k'arfe biyu da rabi tana tsaye k'ofar bedroom d'inshi tana shawarwari, tana san ta shiga suyi magana ta fahimta su fahimci juna, tana san ya bata dama ta fad'a mishi komai ta sanar dashi duk abinda ya faru, koda sun rabun tana san yasan ba amanar shi taci ba kamar yadda yake zato, bak'ar k'addara ce wacce mutum bai isa ya tsallakewa tashi ba, takai mintuna 30 tsaye ta kasa shiga, gabanta na fad'uwa ta d'ora hannunta akan handle d'in k'ofar, tana jin tsoronshi sosai amma tsoronshi na wannan lokacin yafi na koyaushe, kodan yanzu akwai kunyarshi da fargaba gami da tashin hankali oho, yawu ta had'iya had'i da runtse idonta da k'arfi ta bud'e k'ofar, wayam babu kowa, a sanyaye ta taka zuwa bathroom dan bata tsammanin zai bar mata gidan ba, nan ma baya nan, ta duba ko'ina baya nan, jikinta na tsuma ta duba wardrobe d'inshi taga ya kusa gwashe kayan sawarshi, sosai hankalinta ya tashi data tanbatar baya gidan, ita kam ta shiga uku yau ina zata saka kanta. Ana idar da sallar asuba tayi waje dan a tsaye ta kwana Allah Allah ta rink'a yi ayi sallar asuba dan bama zata iya jira gari ya waye ba, tasan muddin yana garin nan bashi da inda zashi daya wuce part d'insu Babah, d'akinshi nada ta nufa, tana murd'a k'ofar tajita a rufe gam, a fili ta sauke ajiyar zuciya kana ta soma buga k'ofar tana kiran sunanshi, while tana kuka kamar ranta zai fita. Tun tana buga k'ofar a hankali harta somayi da k'arfi tana fad'in " dan Allah Yaya ka saurare ni a karo na k'arshe dan Allah ka bud'e muyi magana ka bani wannan damar please Yaya, yadda take bugun k'ofar da k'arfi tana kuka da iya k'arfinta yasa kowa yasan abinda ke faruwa, dan sautin kukan nata har harabar gidan, Abbi da Babah da Yayyan Deeyanah da gudu suka shigo gidan dan sunyi zaton wani abu ne ya faru, durk'ushe suka sameta gaban k'ofa tana kuka wiwi tana k'oronshi kan ya saurare ta, sosai tausayinta ya kama Ammi da Abbi amma Ammu da Babah ko a jikinsu dan suna da tabbacin koma meye ya faru itace me laifi dari bisa dari, cikin sanyin jiki Ammi da Abbi suka k'arasa inda take, ta d'ago ta had'i da kwantar da kanta a k'irjinta tana shafa bayanta. D'ago kanta tayi ta saukewa Ammi kumburarrun jajayen idanuwanta duk tabi ta birkice kamar zararriya " Ammi! Abbi dan Allah kusa baki ku rok'or min shi ya saurare ni a karo na k'arshe, ku rok'ar min shi albarmar yin magana dani, zan fad'a mishi komai, zan fad'a mishi gaskiya, dan Allah ya bani wannan damar dan girman Allah, nasan nayi mishi laifi mafi girman muni a duniya, nasani ni me laifi ce, "shhh shhh shh ya isa, ya isa haka, Ammi ta fad'a tana rungume ta dan samar mata nutsuwa. Babu yadda ba'ayi da Deeyanah kan su tafi in ya huce zai saurare ta ba amma tak'i furrr, ganin haka yasa Abbi k'arasawa bakin k'ofar ya murd'a handle d'in yaji k'ofar a rufe, a hankali Abbi yayi knocking k'ofar yace " Deen bud'e k'ofar nan, shiru babu ko motsinshi, knocking Abbi ya sake yi had'i da kiran sunanshi amma still bai amsa ba, Babah da Ammu dake gefe suka had'a ido, Babah ya k'araso bakin k'ofar shima yayi knocking tare da yin magana amma Deen yak'i amsawa, sosai hankalinsu yayi masifar tashi dan sunyi zaton ba lafiya ba. "Azan kaida Azran kuzo ku b'alle min k'ofar nan, jin abinda Babah yace yasa Deen yin gyaran murya alamar lafiyarshi lau, "au da kana jin mu amma kayi shiru? Shiru ya sake yi bayyi magana ba, a hasale Abbi yace " Deen umarni na baka ka bud'e min k'ofar nan yanzu, Deen dake rakub'e can k'uryar d'aki ya d'ago runannun idanuwanshi kamar zayyi magana sai kuma ya fasa, baiko motsa ba balle yabi umarnin Abbi, abinka dama dame bak'ar zuciya, jin shiru ya k'ara hasala Abbi matuk'a ya bud'e baki zayyi magana Babah yayi saurin tarar numfashin shi da fad'in. "Ka dai san yaron nan me biyayya ne matuk'a ko? Abbi bayyi magana ba, dan bama shi da niyyar yin magana, Babah ya d'ora da cewa " kamar yadda dukkan mu muka san yana da biyayya sosai haka muka san yana da bak'ar zuciya, a halin yanzu ranshi a matuk'ar b'ace yake, ga zafin rabuwa da matarshi ga rad'ad'in sanadin rabuwar, duk da bamu san dalilin rabuwar tasu ba amma kai da ganin abinda ke faruwa kasan akwai lauje cikin nad'i, dan haka mafi masalaha a halin yanzu a kyale shi karka k'ara mishi wata damuwar kadai ji abinda likita yace ko? Ajiyar zuciya Abbi ya sauke a fili kana yace " Allah ya kyauta, suka amsa da " Amin. Dakyar Ammi taja Deeyanah suka bar part d'in, yadda kasan wacce ta haukace haka Deeyanah keyi, tsayin kwana uku kenan kullum sai tazo bakin k'ofar d'akinshi tayi kuka amma yak'i bud'ewa, yayinda shima tunda ya rufe kanshi a d'aki bai fito ba. A wayewar kwana na hud'u anayin sallar isha tazo ta dasa kuka da magiya a k'ofar d'akin amma shiru, babu yadda ba'ayi da ita ta tashi ba amma ta kafe, dole tasa aka kyale ta a wajen, a k'ofar d'akin ta kwana har garin Allah ya waye tana nan zaune ko k'ifta idanuwanta batayi ba balle tayi bacci yadda taga rana haka taga dare, a bathroom d'in falo tayi alwala ta fito ta dawo k'ofar d'akinshi tayi sallah, haka da azahar tayi, duk abinda tayi idon kowa na kanta, tausayinsu ya kama kowa amma banda Babah dan ya tabbatar akwai wani gagarumin al amari a binne, sallah kad'ai ke tada Deeyanah daga k'ofar d'akinshi. K'arfe uku na dare ruwan shan shi ya k'are ga matsananciyar k'ishir ruwa data adda be shi, cikin mutuwar jiki ya mik'e ya bud'e d'akin, yana fitowa yayi tuntub'e da ita, kallo d'aya yayi mata ya kauda kanshi babu d'igon tausayinta cikin ranshi saima zunzurutun k'iyayyarta dake ratsa shi, yi tayi kamar tana bacci, yasa k'afa ya tsallake ta, yana barin wajen tayi wuf ta mik'e ta shige bedroom d'in, store ya shiga ya d'ebo ruwa carton biyu da maltina carton biyu da carton d'in madara peak ta ruwa dan su kad'ai yake iya sha, ruwan da madara ya fara d'iba ya fito dasu, dayaga bata wajen bai d'auka ta shige bedroom d'in ba, yayi zaton gajiya tayi dan haka ta tafi, koda ya shiga d'akin ma bai ganta ba, ya ajiye ya koma ya d'auko sauran ya dawo, k'ofar ya mayar ya rufe da key hasken d'akin ya kashe ya koma saman bed ya kwanta idonshi yana kallan pop, dan rabanshi da bacci har ya manta tuni bacci ya k'auracewa idonshi. Fitowa tayi daga inda take labe ta zare key d'in kana ta kunna hasken d'akin, d'agowa yayi cike da mamaki, yana d'ora idonshi a kanta yaji wani k'ululun bak'in ciki ya tokare mishi mak'ogwaro, d'an sauk'in daya samu kwana biyu take ya gushe, fuskar nan kamar wanda aka saukarwa da sak'on mutuwa, babu d'igon annuri, tashi yayi zaune yana tsare ta da idanuwanshi jajaye, saban tashin hankali da tsoronshi ne suka saukar mata lokaci d'aya, tsare tan da yayi da ido yasa ta dabarbarcewa, jikinta na kerrrma ta nufe shi, kallan karki soma zuwa inda nake yayi mata, amma ta cigaba da nufarshi, gabanshi ta zube had'i da d'ora hannunta saman cinyarshi tana kuka wiwi, ai ji yayi kamar ta nana mishi k'arfen daya shekara a cikin wuta, zabura yayi ya mik'e had'i dasa k'afa yayi ball da ita yana huci yace " wallahi karki soma rab'a ta, bata damu da fashewar da bakinta yayi ba, kota kan jinin dake zuba bata bi, ta mik'e tana fad'in " dan Allah, dan Allah Yaya ka saurare ni. "Bazan saurare ki ba, bazan tab'a saurarenki ba har a tashi duniya dan baki da abinda zaki fad'a min, baki da abin cewa, hawayen bak'in cikin suka taru a idonshi, bayyi k'auron hanasu zubowa ba. "Kin san k'arfin sha'awata, kin fi kowa sanin yadda nake san sex, amma kika hanani kanki duk da haka na jure har tsayin shekaru uku ban fad'awa kowa ba, Allah shine shaida ko hannun mace ban tab'a rik'ewa ba, na kama miki kaina na killace da yak'inin kema zaki killace min kanki, a kullum zuciyata tana k'ok'arin zarginki amma ina dannewa ina baki uzirin akwai dalilin daya saki kike yin hakan, duk daren duniya k'ofar d'akina a bud'e take har garin Allah ya waye ina sa ran wata rana zaki zo, hawayenshi ya goge had'i da had'iye abinda ya tokare mishi mak'ogwaro. Wallahi Yaya ba asan raina abin ya faru ba, kidnapping d'ina yayi, daga nan ta bashi labarin farkon sake fad'uwarsu lokacin da zata je asibiti da lokacin daya turo mata video, "idan zaka iya tunawa a lokacin har kwanciya nayi a asibita na shiga matsananciyar damuwa. "Babu irin tambayar da ban yi miki akan ki sanar dani damuwarki ba amma kika k'i, har rok'onki nayi. "Tsorata ni ya rink'a da video da kuma zai kashe kowa nawa yayi, ta fad'a cikin matsanancin kuka. "Yaya cewa yayi idan na baka kaina sayya kashe ka, sayya k'arar da gaba d'aya zuri'armu, da nak'i jin kashedin shi na baka kaina shine fa ya caka mata wuk'a a zuciya. "Wallahi Yaya nima ba'a san raina komai ya faru ba dole yayi min, "shiyasa har kika d'auki cikinshi? "Jin tambayar tayi kamar daga sama dan bata san da maganar b'arin da tayi ba, cikin mamaki tace " ciki kuma? Murmushi yayi me ciwo yace " likitan daya dubaki bai fad'a miki kinyi b'arin cikin wata hud'u sakamakon dukan danayi miki ba? Cikinta ta shiga shafawa tamkar wacce ta zauce tana girgiza kanta ta kasa furta koda kalma d'aya. "Kin kai mak'ura Deeyanah da aure a kanki kika d'auki cikin wani, mijinki na aure daban uban d'an cikinki daban. Kanshi ya shafa yana tattare gaba d'aya damuwarshi a k'irjinshi, dakyar ya furta cikin Aj.... Sai ya d'anyi shiru kana yace " Ajlaal, bayan kin san irin tsanar danayi mishi, kin fi kowa sanin na tsane shi fiye da mutuwa ta, wallahi gwara ace min duka mazan Nigeria sun sanki a 'ya mace akanshi kad'ai ya sanki, nasha fad'a miki bana k'aunar ko sunanshi, amma duk da haka kika bashi kanki, zan iya yafe miki idan akace min mazan duka duniya sun kwanta dake amma bazan tab'a iya yafe miki ba idan Ajlaal ya rik'e hannunki balle ya sanki."Abin da ciwo! Deeyanah, da ace baki sani bane da sai nayi miki uziri to amma kin sani, kin san komai. Cikin kukan mutuwa tace " idan nak'i yarda dashi zai kashe ka, zai kashe kowa... Cikin hargowa yace " to sai me!? "Meyasa baki bari ya kashe duk wanda zai kashe ba? "Meyasa baki bari ya kashe ni ba? "Wallahil azim na gwammaci mutuwa sau dubu idan anayi akan ganin wannan mummunan rana, amma kije bakomai burinki ya cika kin lalata min komai kin tarwatsa min rayuwa da farin ciki na, nida jin dad'in duniya har ranar da mutuwa ta zata riske ni, amma kafin nan zan tabbatar min da kalamaina na idan kika sake kika ci amanata zan rabu dake rabuwa ta har abada kuma har a tashi duniya baki sake ganina ba, zatayi magana yace " dan Allah karki sake nuna min wannan bak'ar fuskarta ki. "Dan Allah ka fahimc..... Wani k'ululun bak'in ciki ya had'iye hawaye nabin fuskarshi da wata irin murya me tsartsi yace " Deedee d'a na ne ko shi ma....? Tun kafin ya gama maganar ta soma girgiza kanta while hawaye me k'una nabin kuncinta. "Wallahi d'anka ne, Abduljalal d'anka ne halak malak Yaya. "Abun harya kai haka Yaya? "Har ya kai ka fara zargin Abduljalal ba d'anka bane? "Dan Allah karkayi min haka Yaya, karfa ka manta kaine ka fara sani na 'ya mace, kaine kayi disvirgin d'ina. "Bani da tabbaci akan budurcinki balle kasancewarshi d'a na. Zatayi magana yace. "Fita! "Please Yaya! "Out...! Ya fad'a da k'arfi har saida d'akin ya amsa. "Yaya kayi min uzuri please. I said get out! Ko gezauna batayi sai sautin kukanta data k'ara, hak'ark'arinta ya damk'a ya jata zuwa waje, k'ofar ya soma k'ok'arin bud'ewa yaji ta a rufe sai lokacin ya tuna da ya rufe k'ofar ta d'auke d'an mukullin hannunta ya murd'e da k'arfi ta saki k'arar azaba gami da sakin key d'in, ya d'auka ya bud'e d'akin ya hankad'a ta waje ya mayar da d'akinshi ya rufe. ************Sandarewa Ajlaal yayi a zaune cikin matsanancin mamaki kamar mutum mutumin da aka shuka, ya zubawa system d'in ido kamar yana jiran wani abu ya fito ta cikinta, cikin kame-kame ya furta " wait what!? "Ciki!? " Deeyanah ke d'auke da ciki na har na wata hud'u? Jin abin yake kamar a mafarki, wani bak'on yanayi yake ji a jikinshi, ya kasa fahimtar komai, idan dai ba kuskuren fahimta yayi ba, Deeyanah ta samu ciki, amma sakamakon dukan da Deen yayi mata cikin ya zube, ihuuu ya saki da k'arfi ya d'auki laptop d'in ya buga da k'asa, ranshi yakai k'ololuwar b'aci, abinda fa ya dad'e yana nema ne, amma shine dan tsabar mugunta yayi sanadin fitar cikin? Yadda kasan mayunwacin zaki haka yake nishi yana fitar da gurnani, sai huci yake kamar kububuwa, "no! tab! wallahi akwai bala'i tunda ya salwantar min da d'ana wallahi saina rama saina kashe tilon d'anshi ai d'a baifi d'a ba, ya fad'a out of control. Mik'ewa tayi daga kan stool d'in daya jefa ta, ta bugu sosai, tana tafe tana tana tangal-tangal, Ammu da Babah suka sauke ajiyar zuciya a tare, cikin sanyi Ammu tace " ya kamata a kira yaran nan aji meke faruwa a tsakaninsu fa, " munyi magana da Abbi zamu kira su in sha Allah. Tana dafe da k'irjinta while tana haki ta shiga part d'insu, a falo k'asan carpet ta zube tana mayar da numfashi, k'afarshi dake kan d'aya ya sauke yana kallanta deep down yana jin wani abu dabe san kome nene ba yana ratsa shi, a kasalance ya kira sunanta " Deeyanah! Cak zuciyarta ta tsaya, wanda ita kanta bata san dalilin tsayawar zuciyarta ta ba, kodan batayi zaton yana wajen bane sai jin muryarshi tayi oho, zambur tayi ta mik'e, tana kallanshi, ta cikin kwayar idonta ya hango zallar k'iyayyarshi, guntun murmushi yayi yana fad'in " duk abinda nayi sanki ne sila Deeyanah, ya riga ya sake ki saki uku babu abinda yayi saura tsakaninku, please ki dawo min, kakin majina tayi ta kwamb'ala mishi a fuska, ta d'ora da " tur da kai da halinka, wallahi ko zan mutu bazan tab'a aurenka ba, koda kuwa hakan yana nufin mutuwa ta, Allah ya tsare ni wallahi, murmushi ya sake yi a karo na biyu kana yace " duk ba wannan ne ya kawo ni ba yanzu, nasan akwai lokacin da dole baki da zab'in daya wuce ni. "Wallahi koda zan rasa kowa da komai, koda duniya da abinda ke cikinta zasu guje ni wallahi bazaka tab'a zama madogara ta ba, bazaka tab'a zama zab'i na, na k'arshe ba. "Ashe duk wannan lokacin kina d'auke da gudan jina na ban sani ba, sai da ya cije lips d'inshi alamar zafin zuciya kana yace " shine wancan tsohon mijin naji bak'in mugu azzalumi munafuki yayi sanadiyyar salwantar min da d'ana na fari? Sosai yadda yake magana da kwarin gwiwa ya bata mamaki, ya wani hak'ik'ance akan d'an shege, "akan d'an shege d'an zina kake jefar mijina da wad'annan maganganun? "Out of correction, ba mijinki ba tsohon mijinki. Kalmar tsohon mijinki ta dake ta sosai, ta maimaita kalmar cikin kanta yakai sau biyar, " bariki ji wallahi tallahi saina rama akan d'anshi yadda ya kashe min gudan jini na, sai na d'auki fansa akan Deedee wallahi, tashin hankali wanda ba'a saka maka rana, sai yanzu ta yarda da ake cewa tashin hankali ma hawan hawa ne, wani wan wani ne, dan sai da numfashinta yayi fitar bargu na wucin gadi, a haukace ta nufeshi tana girgiza kanta, " a'a dan Allah kome zakayi min kayi min amma karka tab'a min yaro dan Allah, karka saka shi cikin wannan abun ba ruwanshi please. "To idan ban tab'a shi ba wa kike san na tab'a wanda ya kashe min nawa d'an? Cak ta tsaida kuka danta fahimci Deen yake nufi. K'arasa zarewa tayi ta hukace tana fad'in "kome zakayi min ni kad'ai nina jawowa kaina amma banda su please, karka tab'a su dan Allah, dariya sosai yayi ya juya ya fice batare da yayi magana ba, tabi bayanshi da gudu, amma bisa mamakinta yana fita daga k'ofar data bishi ya b'ace babu ko alamunshi, a haukace ta nufi part d'in Babah babu ko d'an kwali balle takalmi, da k'arfi take bugun k'ofar d'akin Deen tana fad'in " ka fito zai kashe Deedee, dan Allah ka fito ka saurare ni da gaske nake yace sayya kashe Abduljalal, cike da mamaki Ammu ta k'araso inda take tana tambayarta waye " zai kashe Deedee d'in? "Ajlaal ne Ammu, dan Allah ku taimake ni karya kashe min shi, Ammi da Abbi suka k'araso wajen dan Abbi yaga wucewar Deeyanah a haukace, da gudu ta nufi Ammi zaninta a hannu tana kuka wiwi " Ammi zai kashe min Deedee dan Allah ku fad'awa Yaya da gaske nake, kallan juna Ammi da Ammu sukayi cike da neman k'arin bayani, ganin duk sun tsaya suna kallanta yasata komawa k'ofar d'akin Deen ta shiga bugun k'ofar a haukace tana ihuuu kamar zata b'alla k'ofar, da sauri Ammi ta k'arasa inda take ta rik'ota amma ta turje, " Ammi zai kashe shi da gaske yake, bashi da d'igon imani. "Naji muje kiyi mana bayani a tsanake, Ammi ta fad'a tana jan hannunta, k'ara turjewa Deeyanah tayi, ganin abun nata kamar hauka yasa Abbi, Ammi da Ammu suka jata tana ihuu suka dannata a d'aki suka rufe dan sun lura tsoratarwa bazatayi mata aiki ba, bugun k'ofar d'akin da aka rufeta take yi a haukace tana fad'in " dan Allah Yaya ka fito ka ceci d'an mu. Duk abinda ke faruwa Deen na ji, ya dayyi shiru ne kawai, abun kuma ya fara bawa iyayen tsoro duk sun dabarbarce kansu ya kulle babu abinda suka iya fahimta, tun Deeyanah na bugun da k'arfi harta gaji ta zube a k'asa tana sharb'ar kuka. K'arfe shida na safe sautin kukan Ammi da salatinta ya cika gaba d'aya Estate d'in, kowa ya fito cikin tashin hankali ta fito harabar gidan d'auke da Deedee a hannunta, mazan gidan suna masallaci dan idan suka yi sallar asuba basa fitowa sai k'arfe shida, gaba d'aya suka fito har Babah da Abbi, Abbi ta nufa cikin tashin hankali ta mik'a mishi yaron tana fad'in " Alhaji na tashe shi zan shirya shi makaranta yak'i tashi babu irin tashin da banyi mishi ba yak'i tashi, tana kara kunnena a k'irjinshi banji komai ba, jikin Abbi na tsuma ya karb'i Deedee bai tsaya b'ata lokaci ba yayi asibiti dashi, su Babah suka bi bayanshi, gwajin farko likita ya gano yaron ya mutu a wanni biyu zuwa uku da suka wuce, sai dai sunyi duk wani binciken da zasuyi sun kasa gano dalilin mutuwar yaron. Gaba d'ayansu jikinsu a sanyaye suka dawo gida d'auke da gawar Deedee, dakyar Babah yaje bakin k'ofar d'akin Deen, muryarshi bata fita sosai saboda yadda yake kokawa wajen danne abinda ke taso mishi, " Deen ka fito Allah yayiwa Deedee rasuwa, yakai ruku'un sallar azahar, jin abinda Babah ya fad'a ya sashi d'agowa had'i da cewa " Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, mutuwa! Deedee ya mutu? Ai ya manta da batun sallar da yake yi, jikinshi na b'ari yayinda da zuciyar ke tsalle kamar zata fad'o ta bakinshi ya bud'e k'ofar, Babah na tsaye yana jiranshi, hannunshi ya kama kamar k'aramin yaro ya fito dashi falo inda gawar Deedee ke kwance, gaban gawar ya zauna had'i da dunk'ule hannunshi ya saka a baki ya cija gami da fashewa da wani irin kuka me k'una, shi kad'ai ne abinda ya rage mishi shima gashi nan sun raba shi dashi, Deeyanah ta cuce shi mak'ura duk wani abu da yake so sai ta raba shi dasu, da gaske yake jin tsanarta har cikin jinin jikinshi, a sanadinta ya rabu da d'anshi, cikin k'araji ya rungume gawar Deedee yana kuka kamar ranshi zai fita, duk da yaji tana ihuun ya fito ya taimake ta zai kashe Deedee ko kusa bai tab'a tunanin da gaske take ba, bayyi zaton rashin imanin shi har ya kai haka ba. Ammu na rik'e da hannun Deeyanah kamar daluwa take bin Ammi, cikin sanyi murya Ammi na share kwalla tace " mun rasa Deedee, bata fahimci inda zancen Ammi ya dosa ba dan haka ta zubawa Ammi ido, gane bata fahimci maganar ba yasa ta sake fad'in " Deedee ya rasu Deeyanah ga gawarshi nan. "Wanne Deedee kuma? "Waye Deedee? Ta fad'a tana bin kowa dake falon da kallo dan kanta ya gama kullewa gaba d'aya. Sai da su Ammi suka kalli juna cike da tsoron kota haukace kana cike da fargaba Ammi ta dafa ta tace " Deeyanah d'anku keda Deen. Wani abu taji yana yawo saman kanta, lokaci d'aya taji duk ilahirin jikinta ya d'auki k'aik'aiyi. Ji tayi kamar an kama jijiyoyin jikinta an tsinkasu lokaci d'aya, komai ya gama kunce mata, duniyar ta tsaya mata cak, babu abinda bai tsaya mata cikin kanta ba, a hankali ta zube bisa gwiwowinta so take tayi kuka amma ta kasa, magana take sanyi amma bakinta yayi mata mugun nauyi, cikin ranta take fad'in " dama dayace mata zai kashe d'ansu da gaske yake yi? Duk da tasan zai iya aikata komai dan mafitar kanshi batayi zaton rashin imaninshi yakai mak'ura har haka ba, batayi zaton zai iya kashe yaro ba, rashin imanin yayi yawa, ita da kanta tayi sanadin d'anta, addu'a take san ta bud'i baki tayi amma yadda kasan an d'aure mata harshenta. Cikin mutuwar jiki ta duk'a, cikin sand'a ta mik'a hannu zata tab'a gawar Deedee yayi saurin rik'e hannunta had'i da janye gawar Deedee d'in, idonshi cikin nata sun kad'a sunyi jajir, sai da k'irjinta ya kusa tsagewa saboda yadda ya doka da k'arfi, kanshi ya girgiza muryarshi na sark'ewa yace " karki soma tab'a min d'a dan bazan tab'a baki wannan damar ba, jikinta a sanyaye ta zame hannunta had'i da mik'ewa tabar falon, d'akinta ta koma ta jin gina bayanta da jikin k'ofar d'akin so take tayi kuka amma yadda kasan an shak'e ta haka take ji. "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un na kashe d'ana, na kashe shi da kaina, nice nayi sanadiyyar mutuwar tilon d'ana. Ta fad'a a haukace kamar zararriya. Deen da kanshi yayiwa Deedee wanka yayi mishi sutura kamar yadda musulunci ya koyar, aka kaishi gidan shi na gaskiya. Tun bayan mutuwar Deedee abubuwa suka k'arasa jagulewa gaba d'aya family aka zama gidan zaman makoki babu me walwala ko fara'a, ganin halin da gaba d'aya family aka shiga yasa manyan family had'a family meeting, gaba d'aya an hallara a babban falon, gyaran murya Abbi yayi ya soma magana da fad'in " Alhamdulillah mun godewa Allah abisa jarabawar da yayi mana ta rashin d'a kuma jikan mu, sai dai dole tasa dole sai mun taru anan dan jin hak'ik'anin abinda ke faruwa tsakanin Deen da Deeyanah, gumin dake tsatstsafo mata a goshi ta goge deep down tana jin wani irin mugun tsoro na ratsata. Abbi ya mayar da kallanshi ga Deen dake zaune d'osane kamar an dasa shi a wajen, cikin sanyin murya Abbi ya kira sunanshi " Deen..! Cikin nutsuwa ya d'ago kanshi ya kalli Abbi batare daya amsa ba, " Deen meke faruwa tsakaninka da Deeyanah ne? "Me yasa kayi mata saki har uku? Ido ya runtse da k'arfi jijiyoyin kanshi sunyi rad'o-rad'o kamar an zana su, still bayyi magana ba, tausasa murya Babah yayi yace " kayi mana bayani mana Deen, idanuwanshi da suka gama rinewa zuwa asalin jajaye ya saukewa Babah su, a kasalance muryarshi na sark'ewa ya bud'e baki da niyyar yin magana amma ya kasa "Babah....Babah... kawai yake fad'a bayan sunan ya kasa fad'in komai, dunk'ulallan kukan daya cure mishi a mak'ogwaro ya kufce mishi, wani irin kuka yake yi me tuk'uk'i da k'una, a hankali Babah ya sauko daga kan kujerar da yake zaune yaje wajen Deen, kamar jira Deen yake ya fad'a jikinshi ya k'ank'ame shi sosai. " Deeyanah ta cuce mu, ta lalata mana komai, na tsaneta fiye da tsana, na tsaneta fiye da komai da kowa. Ya fad'a kamar ranshi zai fita. Kyale shi Babah yayi kukan me isarshi while yana bubbuga mishi bayanshi, ya dad'e yana kukan kana ya d'ago daga jikin Babah ya goge hawayenshi, "alfarma d'aya nake nema a wajenku please, da ido Babah yayi mishi alamar ya fad'a. "D'an Allah ku barni na tafi, ku barni nayi nisa da wannan duniyar nayi nisan nisa da kowa da komai, d'an jimmmm Babah yayi kana ya juya ya kalli Abbi da Ammi, a kid'ime ta rarrafo inda yake ta rik'e k'afafuwanshi "A'a dan Allah karka tafi ka barni a wannan k'azantacciyar rayuwa, kai ya kamata ka tayani yak'in Yaya, dan Allah karka tafi ka barni ni kad'ai bazan iya ba, fad'an yafi k'arfi na Yaya, ta k'arashe maganar da wani irin kukan mutuwa. K'afarshi data rik'e yasa ya hankad'a ta baya da k'arfi, bata damu da hankad'ata da yayi ba ta sake rarrafawa gaban Abbi " Abbi ku taimake ni dan girman Allah, na rasa Deedee shi kad'ai ya rage min Abbi, kada ku bari ya tsige kanshi daga gare ni, mik'ewa yayi ya fice tabi bayanshi da gudu har zaninta na fad'uwa, gabanshi tasha ta zube a k'asa ta rik'e k'afafuwanshi gam " dan Allah karka barni. "Dana fad'a miki idan kika ci amanata zanyi miki nisan nisa baki yarda ba? "Kamar ban tab'a fad'a miki ina sanki fiye da so ba amma muddin kika ci amanata zan barki har abada ba? "Deedee shine 'yar zaren igiyar data alak'anta ni dake yanzu ko babu ita, babu wani abu dayayi saura a tsakani na dake, ko a lahira bana fatan sake ganinki, yasa k'afa ya tureta yayi gaba, Abbi zayyi magana Babah yayi saurin dakatar dashi yana tuna wani lokaci a baya.... Tunani.... Cikin shagwab'a Deen ya kwantar da kanshi a kafad'ar Babah had'i da sanya hannu ya dafe k'irjinshi saitin zuciyarshi yace " wash! Babah yace " ya akayi ne namijin duniya? "Deeyanah ce Babah, ya fad'a yana k'ara narkewa Babah, "me Deeyanah tayi maka? "Zata kashe ni Babah, santa gaf yake da sa zuciyata tayi bindiga. "Har haka kake santa? "Fiye da haka ma, ina santa fiye da so, ina santa fiye da rayuwata, ina santa fiye da komai da kowa, zan iya rabuwa da kowa a kanta Babah, Deeyanah itace rayuwata, itace hasken duniya ta, itace haske a gare ni a duk yayin dana kasance a cikin duhu, itace duniya ta, itace ji na itace gani na itace komai nawa Babah, ina fatan na rayu da ita har rai da mutuwa, ina rok'on Allah yasa har a aljanna mu kasance tare... Ajiyar zuciya Babah ya sauke bayan ya gama tunaninshi, cikin ranshi yana juya girman al amarin da zai juyar da irin wannan k'arfefaffiyar soyayyar zuwa cakud'add'iyar k'iyayya, ya tabbatarwa kanshi akwai gagarumar matsalar da saita shafi kowa. ************************** Tana durk'ushe ta cusa kanta tsakankanin cinyoyinta ba kuka take yi ba, abin duniya ya ishe ta, kyalkyalewa yayi da mahaukaciyar dariya har da buga k'afa, tana jinshi amma ko gezau batayi ba, sai da yayi me isarshi kana ya durk'usa kusa da ita ya zuba mata ido yana kallanta yana dariya, ya d'an d'auki lokaci a haka kana yace " mijinki na farko ya kashewa mijinki na biyu d'a, shi kuma mijinki na biyu yaga bazai iya hak'uri ba shine ya rama ya kashewa mijinki na farko d'anshi shima, kinga mijinki na farko ya rasa d'a d'aya haka ma mijinki na biyu, sai dai ke 'ya'ya biyu kika rasa, ya kenan? Zaman dirshan yayi a k'asa ya nutsu sosai kamar gaske yace " Deeyanah yanzu dai duk abinda zai faru ya riga ya faru sai dai a guji gaba laifi ne kunyi min keda mijinki amma ba komai na yafe muku, abinda nake so dake yanzu shine ki dawo mu cigaba dayin normal life d'inmu kamar da, mu cigaba da tsinkar korayen fure, sai lokacin ta d'ago da kanta ta sauke mishi ramammun jajayen idanuwanta akanshi, ko gezau bayyi ba saima cigaba da magana da yayi " mu cigaba da jin dad'in mu muna morar juna, amma fa sai inkin so zamu cigaba da aikata zina, muna iyayin auren mu, a wanke minke tass tass akai min gida na. Bata san sanda k'untaccen murmushi ya kwace mata ba, lips ta cije da k'arfi har sai da hak'oranta suka fasa lips d'in, " me jiya tayi balle yau Ajlaal? "Abinda jiyan batayi ba shine nake san yau d'in tayi ai. Ya bata amsa yana gyara zamanshi, cikin kwayar idonshi ta kalla sosai kana tace " wallahi tallahi kasa a ranka nice ajalinka Ajlaal Basaan, a wad'annan tafukan hannun aka rubuta mutuwarka, ta fad'a tana nuna mishi tafin hannunta, "wow! wannan wanne irin daddad'an albishirin ne, aiko dana kasance mutumin dayafi kowa sa'a a duniya zan mutu a hannun abin k'aunata, itace abu na k'arshe da zan gani, akan tafukan hannayenta zan ja numfashi na na k'arshe, amma kafin nan kizo mu more rayuwarmu mana. "Dan Allah me nayi maka a rayuwa? "Wanne laifin na aikata maka da kake azabtar dani har haka? "Guje min Deeyanah! guje min da kikayi shine kad'ai laifinki kuma ko yanzu kika ce zaki cigaba da guje min wllh bakiga komai ba. "In dai k'auracewa sab'an Allah shine laifi na to kuwa yanzu na fara guje maka, kuma har abada zan kasance me guje maka me addu'ar neman tsari daga sharrinka. Murmushin gefen baki yayi kana yace " wallahi tallahi idan baki dawo mun cigaba da rayuwarmu ba ko kizo muyi aure ba wallahil azim saina sakarwa duniya videonki dan bazai yiyu ki lasa min zuma a baki ba sannan kizo ki hana ni wallahi k'arya ne. "Ba duniya ba ka sakarwa har lahira ka sakashi a majigi ka haska kowa ya gani koka harba shi duniyar mass yadda kowa zai gani bai dame ni ba, kuma ko'a jikina abinda na sani shine har abada bazan tab'a dawo maka ba, ko'a mafarki bazan tab'a aurenka ba, kai Allah ya tsinewa mafarkin da zai zo min dakai a cikinshi. Tuntsurewa ya sake yi da mahaukaciyar dariya yana fad'in " to kuwa ki shirya dan daga yau komai yana iya faruwa, dan muddin bazan same ki ba sai dai ayi biyu babu kowa ma ya rasaki, mik'ewa yayi tsaye yana kallanta yace " zan baki lokaci kiyi tunani kafin ki yanke hukuncin da zai k'arasa wargaza miki d'an sauran farin cikin daya rage miki. "Babu wani tunanin da zanyi indai akanka ne wallahi, nayi maka alk'awarin bazan tab'a dawo maka ba har abada. "A'a fa Deeyanah!, kada kiyi wasa da wuta. "Wasa da wuta kam aina gama yinshi harma ta k'ona ni, da tabanta zan mutu. "To kuwa ina yi miki albishir d'in sakin videonki a social media wallahi tallahi. Bakinta bud'e tace " da waya hanaka ka saki? "Ka dad'e baka saki d'in ba sakarai shashasha kawai. Dariya yayi ya juya ya taka zuwa k'ofa, har zai fita ya juya ya kalleta yace " ina yi miki albishirin duk duniya babu namijin daya isa ya mallake ki wannan alk'awarina ne, yasa kai ya fice, taso taje ta sanar da Deen halin da ake ciki amma tasan kota je bazai saurare ta ba dole tasa tayi hak'urin amma tasan tunda yace zai saki videon to kuwa tabbas ba makawa sayya saki d'in. K'arfe goma sha biyu na dare ya saki video a Instagram, Twitter, Facebook, WhatsApp, TikTok, da Snap Chat, dayake sababbin account ya bud'e bada tsofaffin nashi yayi amfani ba yasa video bayyi saurin karad'e social media ba, sai da yayi rubutu a k'asa video kamar haka. Wannan wata matar aure ce da take aikata zina da aurenta me suna Deeyanah Abduljalal matar Deen Abdulrasheed, aiko kafin asuba video ya gama karad'e duk wata kafar sada zumunta, aka rink'a forwarding groups to groups, cikin rashin sa'a aka tura videon group d'in da Azan Yayan Deeyanah ke ciki, yana zaune a falon Ammu tana kallan Tv shi kuma yana chart videon ya shigo shi bai ma kula da rubutun da akayi a k'asan videon ba kawai ya kunna videon kasancewar fuskarta ta fito tarwau sosai yasa ya gane ta, hannunshi na wata irin rawa ya koma group d'in sai a lokacin ya kula da rubutun ya maimaita sake karanta rubutun cikin kanshi yafi sau 100 kafin ya fahimci abinda aka rubuta. Tashin hankali, bai san sanda wayar ta sub'uce daga hannunshi ba while videon yana yi, kamar ance Ammu ta kalla idonta ya sauka akan videon, taso ta kawar da kanta daga kan videon amma ina yadda kasan dansu kalli videon aka halicce su, kamar an dasa su akan videon Azan bayyi k'ok'arin hana Ammu kallan videon ba dan bai ma san inda kanshi yake ba, sai da videon ya gama ya kashe kanshi, wani irin abu Ammu take ji aduk sassan jikinta, dukkansu sun sandare a zaune, wata irin rawa da kerrrrma jikin Ammu ya d'auka lokaci. "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un dama abinda Deen ya gani kenan? "Kenan wannan shine dalilin sakin da Deen yayi mata? "Lalle Deen yayi namijin k'ok'arin daya iya daurewa ya jure ya rik'e wannan masifar shi kad'ai a cikin ranshi, zuciyarshi tayi dauriya da bata fashe ba Ammu, Azaan yayi maganar kamar zararre, suturai marasa kan gado ya rink’a zubawa Ammu, ya dad’e yana soki burutsun shi kafin ya fahimci shirun da falon ya d’auka, kallan Ammu yayi tare dakai hannu jikinta ganin idanuwanta a bud’e amma basa motsi, duk jikinta ma babu inda yake motsi, yana tab’a ta tafi luuuuuu sai timmmm! Ammun ta kifa ta fad'i k'asa tana daga zaune, jikin Azaan na b'ari ya mik'e tsaye yana salati. Hannun Ammu d'auke da towel ta fito daga kitchen tana amsa sallamar Abbi daya shigo, lokaci d'aya idanuwansu suka sauka akan akwatin tv, b'aro-b'aro hotan fuskarta ya fito sai dai an saka dishi-dishi an rufe tsiraicinsu, da dabara Abbi ya had'a kalmomin ya karanta headline d'in jikin labarin, cikin firgici Abbi da Ammi suka kalli juna kana sukayi saurin mayar da kallansu ga tv, da gudu su Azran suka shigo part d'in, turus sukayi gaba d'ayansu a falon Abbi ya kallesu suka kalle shi. "Gaba d'aya social media da duniya ta d'auka Abbi babu wanda baiga videon nan ba, duk k'asar nan har k'asashen k'etare babu wanda bai san halin da ake ciki ba, abokanaina daga wajaje daban-daban sai kira na suke yi, Vakil ya fad'a cikin k'unci. "Wai meke faruwa ne? Azran dake tsaye k'afarshi na kasa d'aukar shi ya fad'a, "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, Abbi yace yana zama akan kujera had'i da cire hular kanshi, jiri ne ya d'ebi Ammi Azaan yayi saurin tare ta. Fad'ar halin tashin hankalin da zuri'ar su Deeyanah suka shiga b'ata lokaci ne, duk yadda suke tunanin zasu shiga cikin k'unci da damuwa sun shiga fiye da haka, gidan ya koma tamkar mak'abarta babu walwala kai ko maganar kirki babu meyi sai in ta zama dole, Ammu kam sai da tayi sati d'aya a asibiti unconscious bata san inda kanta yake ba, jininta yayi masifar hawa, duk iya taimakon da likitoci zasu bata sun bata amma a banza, likitan yayiwa Babah bayani da fad'in " gaskiya komai yana iya faruwa dan tasamu mugun shock wanda ya haifar mata hawan jini sosai, sai dai muyi addu'ar Allah yasa idan ta farfad'o kada wata matsala ta biyo baya. Kusan gaba d'ayansu suna a asibitin duk sunyi jigum-jigum Vakil ne ya fara lura da idon Ammu na motsi, cikin sanyin magana yace " Abbi tana motsi, gaba d'aya sukayo kanta, so take tayi magana amma ta kasa, tana ta k'ok'arin d'aga hannayenta ta kasa, Babah ne ya lura da hakan, da gudu ya tafi kiran likita, basu b'ata lokaci ba suka dawo tare da likitan, ya duddubata sosai, ya d'ago cikin jimami ya kalli Abbi da Babah a nutsu yace " sai dai kuyi hak'uri kamar yadda nayi muku bayani a baya, koda ta farka wata matsalar tana iya biyo baya, ta farka amma ta had'u da shanyewar b'arin jiki, kuma shima d’ayan b'arin jikin nata bamu da tabbacin zayyi aiki sosai kamar da. "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un Babah ya fad'a had'i da zama sakwaf ba kwari, nan damuwa da bak'in ciki suka k'aruwa sukayiwa zuri'ar yawa, mazansu da matansu manyansu da yaransu sai rusgar kuka sukeyi wiwi, zuciyoyinsu sunyi duhu dind'im babu d'igon haske a ciki, kwanan Ammu hud'u da farfad'owa zuciyarta ta buga ta samu heart attack, Allah ya karb'i rayuwarta, nan fa koke koke ya k'aru, duk abin nan da akeyi Deeyanah na gida kulle a d’aki sai da aka kai gawar Ammu kana ta fito tare da fad’awa kan gawar tana wani irin kuka tana fad'in " dan Allah Ammu ki tashi, ki tashi karki tafi ki barni a sanda nafi buk'atarki fiye da koyaushe, nice sanadiyyar mutuwarki ki yafe min dan Allah Ammu, karki mutu baki yafe min ba dan Allah, dakyar aka b'anb'areta daga jikin Ammu aka kaita makwancinta na gaskiya. Tun bayan rasuwar Ammu komai ya k'arasa lalacewa Deeyanah dan babu me kulata balle ayi mata magana kaf gidan dan sun d'ora mata alhakin mutuwar Ammu akanta a cewarsu ita ta kashe musu uwa, rasuwar Ammu ta k'ara cunkusa k'iyayyar Deeyanah a zuciyar Deen dan ita ya d'auka uwa ba Ammi ba saboda ita ta reneshi, a d'aki ta keb'e kanta ta rufe babu abinda take yi sai kuka, har ta gaji da kukan hawayenta ya k'afe, komai na duniya ya fice mata daga rai, ta tsani kanta, in banda kashe kai babban laifi ne a addinin musulunci da tuni ta dad'e da kawo k'arshen numfashinta, ji tayi kamar taita tsigar gashin kanta d'aya bayan d'aya har su k'are, kanta ta shiga bugawa a bango tana fad'in " koban kashe kaina ba saina azabtar da kaina azabtarwa me tsananin gaske, duk da fashewar da kanta yayi jini yana zuba bai sa ta dena ba, har jinin ya rufe mata ido ruf bata ganin komai sai duhu, wata irin d'iba jini yayi mata ya kada ita gefe. Cikin dare cincirundan zanga zangar suka taru a k'ofar get d'in su Deeyanah, suna ihuuuu suna jefa duwatsu gidan, kan kace kobo an farfashe musu windows da duk wasu glass dake gidan, har mutanen gidan da ma'aikatan gidan ba'a kyale ba, an fasawa da yawa daga cikinsu kai har Abbi da Babah saida aka ji musu ciwo, dakyar da taimakon jami'an tsaro aka kori mutanen, Commissioner of police ne ya basu wasu 'yan sanda dansu basu tsaro, ranar kam a tsorace suka kwana dan saida suka rurrufe ko'ina, washe gari asibitin dake cikin Estate d'in akayi musu treatment. *********Bayan sati d'aya da lafawar 'yan zanga-zanga wasu mutane a manyan motoci suka zo gidan, Abbi da Babah sukayi musu iso har babban falo, bayan sun gaisa d'aya daga cikin mutanen yayi gyaran murya ya soma magana " daga k'ungiyar addinin musulunci ta k'asa muke, dama munzo kan maganar yarinyar nan da tayi wannan aika-aika, d'an shiru yayi ya kasa k'arasa maganar, Abbi yace " uhunnn muna jinka. "An aiko mu ne kan muzo mu sanar daku cewar dole za'a JEFE! ta saboda tayi zina tana da aure kuma a koyarwar addininmu jefa shine hukuncin mutane irinta. "Me? "Ban fahimta ba!. Abbi ya fad'a cikin zallar tashin hankali, "eh! kamar yadda kaji, an tsaida nan da sati biyu za'a jefe ta a gaban mutane dan hakan ya zama gargad'i da jan kunne ga 'yan baya. Kasa magana Abbi da Babah sukayi har mutanen suka mik'e suka fita, yadda kasan iska haka maganar OIC tabi k'asa, nan fa k'ungiyo sukayo caa musamman Human Rights and Amnesty suka nemi ganin Babah mahaifin Deeyanah ba musu Babah ya amince, a office d'in Human Rights akayi zaman, inda daga k'arshe suka nemi ganin Deeyanah, dakyar ta amince ta zauna da Human rights d'in, ganin halin da take ciki yasa basu nemi jin komai daga bakinta ba, suka karb'i sa hannunta. An d'ibi watanni ana fafata shari'a tsakanin OIC da Human Rights sai da aka kai ruwa rana kana Allah ya bawa Human Rights nasara kotu ta hana jefe Deeyanah, duk da ita Deeyanah da yayyanta sun so ace an bari an jefe tan, amma Abbi da Human Rights sukayi tsaye sukayi tsayyuwar tsayin daka, tasha bin dare tana addu'ar Allah yasa OIC suyi nasara a jefe ta, har a kotun sai da ta nemi kotu ta bada izinin a rataye ko a jefe ta amma Human Rights ta hana. Har lokacin babu wanda yake yi mata magana a gidan, ita kad'ai take rayuwar ta, sai da Abbi yaga halin tsangwamar da take ciki kana ya nemi ganinta a falonshi, tun faruwar abun babu wanda ya nemi ganinta koya san halin da take ciki, kanta k'asa cike matsananciyar kunyarsu ta shiga falo, daga kallan farko da Abbin yayi mata bai sake sha'awar sake kallanta a karo na biyu ba, ta yankwane ta yamushe ta lalace abun dai ba'a cewa komai, da muryarta da tuni ta zama dashashshiya ta gaida su, ba yabo ba fallasa Abbi da Ammi suka amsa yayinda Babah da Deen ko kallan inda take basuyi ba, dan babu d'igon tausayinta a ransu. " Deeyanah!, Abbi ya kira sunanta a nutse, kanta k'asa batare data d'ago ba ta amsa, " na kira ki ne dan ina san nasan ainahin hak'ik'anin abinda ke faruwa, kiji tsoran Allah ki fad'a min gaskiyar abinda ke faruwa dake. A hankali ta d'ago kanta ta sauke idonta akanshi tana k'ara ganin girmanshi, tun da abin ya faru kowa gudunta yake yi, babu wanda ya tsaya ya saurare ta, ko sau d'aya tak babu wanda yaso jin ta bakinta ko abinda ya faru, a karon farko kuma mutum na farko daya saurare ta, ya kuma so jinta bakinta, kanta ta sunkuyar k'asa tana san hawaye su zubo mata amma babu ko d'igo, a fili ta sauke ajiyar zuciya tana sake d'agowa ta kalli Deen da Babah da kallo, duk da kallo d’aya tayi musu ta gane dolen da akayi musu shinfid'e akan fuskokinsu, kanta ta sunkuyar had'i da bud'e baki zata soma magana Deen yayi saurin mik'ewa ya kalli Babah yace " bari na amsa waya, Babah ya gane guduwa zayyi dan haka yayi saurin cewa " jeka!, dan kar Abbi ya hana shi, shima dole ce ta zaunar dashi. Murmushin yak'e Deeyanah tayi kana ta soma bada labarin komai tun daga farkon had'uwarta da Ajlaal a makaranta har kawowa mafarin abun bata b'oye komai ba. "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un lalle Deeyanah kin tafka babban kuskure kece babbar me laifi duk abinda ke faruwa ke da kanki kika jawowa kanki, kin shuka BAK'AR SHUKA... shiyasa duk abinda Allah yace a bari barin nashi shine mafi alkhairi, shi kuma Ajlaal yayi amfani da k'uruciyarki yaci moriyar kwakwalwarki ta mace ya dasa miki tsoronshi da firgici cikin ranki da haka yayi amfani ya cimma burinshi a kanki, yayi wasa da kwakwalwarki, ina ita RALEEYA DATA JEFAKI CIKIN WANNAN MUMMUNAR K'ADDARAR? "Tana ina? "Ina labarinta yake? "Sau Dama k'awaye suna da tasiri a rayuwar mutum, sukan kai mutum su baro shi, kamar yadda RALEEYA ta cuce ki ta jefa cikin gagarumar masifar da fitarki sai Allah yaso, ta zuga ki, ta baki shawara kin d'auka, meyasa data baki shawarar baki nemi shawarar kowa ba? "Gashi nan ke abinda kuka aikata yake farauta ita tana can tana rayuwa cikin jin dad'i da walwala ta barki cikin danasani da nadama, shi kam Babah wani irin haushinta da tsanarta yaji sun k'ara ratsa shi da kafi, musamman ma da yaji sanadin abin ya d'auka k'addararta ce tazo mata a haka, amma yanzu daya ji ita ta jawowa kanta haushinta yake ji sosai, a fili yaja tsoki had'i da mik'ewa ya kalleta yayi kwafa, kamar bazayyi magana ba sai kuma yace. "Kin cuci kanki kin cuci rayuwarki, kin jefa wad'anda basu ji ba basu gani ba cikin masifar da kika jefa kanki, d'an itaciyar BAK'AR SHUKAR... da kikayi ke kad'ai gashi nan kin raba mana muna cin shi tare dake, gangancinki yayi sanadiyyar mutuwar mahaifiyarki da d'anki, Allah ma kad'ai yasan iyakacin wad'anda zaki zama ajalinsu, nayi takaicin haihuwarki, nayi nadamar aurawa Deen ke, dama ban haifeki ba, ke inama ban auri uwarki ba balle na haife ki, da nasan bak'ar daga zaki zama dana sa an zubar da cikinki tun kafin ki zo duniya, kin b'atawa zuri'ar mu suna har a tashi duniya, kin jefa mu cikin kunyar duniya har mu mutu, kin zubar mana da k'ima da mutumcinmu dan yanzu bamu da wani sauran mutunci a idon Jama'a, muna sanye da tufafi amma ana kallan mu tsirara, matar da tayi dakon cikinki har tsayin watanni tara, tayi nak'udarki, kika tsaga tsatsanta kika fito, ta shayar dake daga jikinta, ta reneki amma ki rasa dame zaki biyata sai da mutuwa Deeyanah bayan ita ta baki rayuwa? "Allah ya d'auki ranki kamar yadda kika zama sanadiyyar mutuwar Aina’u. Da sauri ta amsa mishi da " Amin Babah, Amin ya Allah, Ubangiji ya amsa rok'onka ya karb'i raina na huta dan nima na gaji da wannan bak'ar rayuwar, zayyi magana Abbi yayi saurin mik'ewa ya jashi zuwa waje, bai jima ba ya dawo, sai da ya d'an saita kanshi kana yace " wallahi ko abinda na mallaka a duniya zai k'are saina ga bayan Ajlaal da duk wanda ya d'aure mishi gindi, yadda ya saki kuka saina zubar da hawayenshi, yadda ya saka mu cikin halin bak'in ciki da damuwa shima saina saka ahalinsu kaf a cikin kwatankwacin halin daya saka mu, saina tona mishi asiri duniya tasan waye shi. ********Cikin kwana d'aya Abbi ya gama duk wani shirye-shiryen da zayyi ya d'auki manyan kwararrun lawyers wad'anda zasu tsaya mishi a kotu, ranar litinin aka kaiwa iyayenshi sammacin kotu, babu yadda Babah bayyi da Abbi ba amma fur Abbi yak'i sauraranshi. Abbah da kanshi ya kira Ajlaal ya sanar dashi batun sammacin da aka aiko, yayi dariya had'i da cewa " na sani ai tun kafin ma yakai kotun nasani, Allah ya kaimu ba damuwa, ashe ma iyakacin nan ya tsaya duk cika bakin nashi, Abbah yayi mamakin ganin ko a jikin Ajlaal dan haka yace " kaji tsoran Allah, kaji tsoran ranar had'uwarka da Allah, wallahi idan kaine wanda ka lalatawa yarinyar nan rayuwar to ka sani kaima Allah bazai barka ba, da sannu Ubangiji zai saka mata, ya mayar dakai abin kwatance, ya wulak'anta ka kafin mutuwarka ta riske ka. "Na lalata mata rayuwa kodai muka lalatawa juna rayuwa? Dan yaji maganar da Deeyanah ta fad'awa su Abbi sai a lokacin shi kanshi Ajlaal d'in yasan hak'ik'anin abinda ke faruwa, ya kuma alwashi akanta. "Ina zaman zamana lafiya ta shigo rayuwata ta wargaza min duniya ta Abbah, duk abinda ya faru itace sanadi itace ta jawowa kanta, da kanta tayiwa kanta BAK'AR SHUKA.... Abbah zayyi magana Mamah tayi saurin tarar numfashin shi da fad'in " dan zatin Allah ka kyale yaron nan ka shafa mishi lafiya wannan wacce irin masifa ce ka saka yaro gaba ka tsare shi da maganganun banza, Ajlaal fa ba yaro bane ya girma ya isa ya yankewa kanshi hukuncin dayace da rayuwarshi. "Yanzu maganar tawa ce ta zama maganganun banza? Fuska ta yatsina had'i da tsare shi da ido tace " eh! koba hakan bane? Abbah bayyi magana ba ya mik'e ya fice. Ranar zaman kotu Kotun ta cika mak'il da mutane da wad'anda suka zama dole da gayyar sod'i 'yan san ganin kwakwaf, masu san su gani da idonsu ba abasu labari ba, bak'ar mota Range Rover me bak'in tint da duk bin kwakkwafin mutum bazai ga wanda ke cikin motar ba, ta faka a harabar kotun ,daga ita sai Abbi ne suka zo kotun dan kowa k'in zuwa yayi, Babah ko cewa yayi bada shi za'a d'aurewa k'arya gindi ba shidai dayaga zai iya yaje can yayi tayi. Doguwar rigar atamfa ce a jikinta sai hijab data sakko dashi fuskarshi ta rufe fuskarta ruf Abbi na binta a baya, ihuuuuu mutane suka soma yi mata had'i da jifanta da duwatsu, aiko kan kace me anyi mata jina-jina an fasa mata goshi da bakinta sai jini ke zuba, dakyar aka kwace ta a hannun mutane aka shigar da ita kotun, sai da rigar jikinta da hijab d'in suka yage, yana zaune a bancin farko kusa da Abbah da Mama, akanshi idonta ya fara sauka ya sakar mata shu'umin murmushi had'i da kashe mata ido d'aya, Abbah na d'ora idonshi akan yarinyar matsanancin tausayinta ya kamashi, ita kam Mama in banda uwar harara babu abinda take watsawa Deeyanah. Tana cikin jikin Abbi yana ta kakkare ta suka zauna, bayan an natsa magatakardar kotu ya mik'e ya gabatar da k'ara, ya karanto k'orafi, Alk'ali yayi gyaran murya had'i da cewa " ina me k'ara? Cikin nutsuwa Abbi ya mik'e da ita a jikinshi suka fita gaban kotu, Alk'ali ya sake cewa " ina wanda ake k'ara? Cikin izza ta tak'ama ya fito ya tsaya daga d'aya b'angaren suna fuskantar juna, Alk'ali ya kalli Abbi yace " fad'awa wanda kake k’ara akan abinda kake k'ararshi, Abbi ya kalli Deeyanah yace " kada kiji tsoron komai da kowa ina tare dake, Allah zai tsaya mana, kiyiwa kotu bayanin komai bisa gaskiya da amana, bakinta na rawa, muryarta na shak'ewa while hijabinta na zamewa ya fad'i saboda yagar dake jikinshi, ta kwashe komai ta fad'awa kotu bata rage komai ba, nisawa Alk'ali yayi had'i mayar da kallanshi ga Ajlaal yace " to kaji abinda ake tuhumar ka dashi? "Eh naji!. "To me zaka cewa kotu!? Gyaran muryar yayi kana cikin shariya yace " to ni dai gaskiya ban san komai akan wad'annan maganganun ba, yadda kowa yaga videon ta haka nima na gani, ni nama manta da ita, na dad'e da rufe babinta a rayuwata. Alk'ali ya mayar da kallanshi gasu Deeyanah yace " to kunji, a hankali ta d'aga ido ta kalli Ajlaal ya d'auke idonshi gami da basarwa, Alk'ali yace " kuna da sheda ne? Abbi ya kalli Deeyanah cike da tausayawa, itama shi ta kallan kana ta mayar ga kallanta ga Alk'ali tace " eh akwai shaidu. D'an shiru Alk'alin yayi yana nazari kana yace " ku koma ku zauna, sai da yayi rubutu sannan ya sake d'agowa ya kalli inda lauyoyi suke yace " ina lauyan me k'ara? Lokaci d'aya lauyoyi bakwai suka mik'e tsaye sosai mamaki ya fito k'arara saman fuskar Alk'alin cike da mamakin yace " dukkanku lauyoyin me k'ara ne? Suka da eh cikin girmamawa, bayyi magana ba ya juya b'angaren Ajlaal yace " ina lauyanka? Murmushin gefen baki yayi had'i da cewa " bani dako d'aya. Jinjina kai Alk'alin yayi kana yace "lauyoyin me k'ara kuna da abin cewa? D'aya daga cikinsu ya karkace ya soma magana, ya dad'e yana magana kana yayi shiru d'aya daga cikinsu shima ya fara maganar, sai da kuka gama kaf kana ya kalli Ajlaal yace " kana da abin cewa? "A'a, Ajlaal yace fuskarshi d'auke da shu'umin murmushi, Alk'ali ya fara rubutu, ya d'an d'auki lokaci me tsayi yana rubuce-rubuce kana ya d'ago, "zamu cigaba da sauraren wannan shari'ar a ranar 30 ga wantan 6 na wannan shekarar inda masu k'ara zasu gabatar da shaidunsu a gaban kotu. Da taimakon 'yan sandan kotun aka shigar da ita mota, koda suka koma gida babu wanda ya tambayesu yadda ta kasance a kotu, har shi kanshi Babah da Ammu, sosai ran Abbi ya b'aci da burus d'in da sukayi dasu, amma ya kanne bayyiwa kowa magana ba. Tana shirin shigewa d'aki Abbi yace " kina da shaidun da zaki gabatar a kotu? Cikin sanyinta da muryarta da bata fita sosai tace " eh! akwai text's d'in dayake turo min ta wayata da voice note ta WhatsApp kuma har yanzu suna nan a wayata. "D'auko min wayar. Abbi ya fad'a yana zama. Shigewa tayi cikin bedroom ta bud'e wardrobe ta zaro wayar tana fitowa ta kunna wayar dan ta manta rabanta da amfani da waya, yana zaune ta rusuna ta mik'a mishi wayar, ya karb'i wayar dai-dai lokacin data gama kunnuwa, mik'a mata wayar yayi yace " saka password d'in, ta karb'a ta cire password d'in ta sake mik'a mishi, yana k'ok'arin shiga WhatsApp wayar tayi hooking yayi-yayi wayar ta dannu tak'i dannuwa, sai kuma ta farfarfar, sai wayar ta kashe kanta, kallanta Abbi yayi yace " dama wayar nada matsala ne? "A'a bata da matsalar komai, zayyi magana wayar ta kunna kanta, ta dad'e kafin ta zama normal bisa mamakin su komai na wayar ya sauka wayar ta dawo kamar sabuwa, babu abinda bai goge ba, murmushin takaici Abbi yayi yace " an datsi wayar (hacking) an goge komai dake kan wayar, cikin tashin hankali ta warce wayar daga hannun Abbi ta shiga duba wayar hannunta na rawa, amma yadda kasan yanzu ta bud'e wayar daga kwalinta, cikin tsoro idanuwanta waje tace " yanzu ya zamuyi a kotu bamu fa da wata shaidar bayan wannan? Murmushin takaici ya sake yi a karo na biyu kana yace " sai dai mu jira ikon Allah. Kotu Day2 Kotin tayi mak'il da jama'a, Alk'ali ya shigo kowa ya mik'e tsaye sai bayan ya zauna kana kowa ya zauna, bayan an natsa Alk'ali ya nemi lauyoyin me k'ara suka fito gaban kotu. "Yana duba takardun gabanshi yace " ina shaidar da zaku gabatarwa da kotu? Kallan juna lauyoyin sukayi kana d'aya daga cikinsu yace " babu wata shaida mun rasata, a fili Alk'ali ya fitar da nannauyan numfashi kana yace " zan sake baku dama ta biyu kuma ta k'arshe kuje ku sake binciko shaidar da zaku gabatar a gaban kotu, lauyoyin suka rusuna had'i da yin godiya suka koma suka zauna, d'an shiru ne ya ratsa kotun, Alk'ali yayi ta rubuta kana d'ago yace " an d'aga shari'ar zuwa nan da sati uku zai kama 20 ga watan gobe na wannan shekarar, kooootuuuu! ya mik'e ya fice kana kowa ya fice, fuskarshi d'auke da murmushi ya kalleta hannuwanshi hard'e a k'irjinshi yana tauna cingam, bayyi mata magana ba ya wuce ta gabansu yana fito. Daga Deeyanah har Abbi jikinsu yayi mugun yin sanyi dan sun hango fad'uwa da rashin nasara k'arara, basu da wata makama ko mafita, jikinta a sanyaye ta wuce Abbi dake zaune a falo, d'an tari yayi yace " Deeyanah babu abinda za'a iya samu wanda zai tabbatar da laifin Ajlaal a kotu? Jimmmmm tayi tana nazari kana ta d'ago kanta dake k'asa ta kalli Abbi tace " wallahi babu dama a waya ta ne kuma ya goge komai dake kan wayar, cikin jimami Abbi yace " bakomai akwai Allah, kuma yana bayan me gaskiya, muyi addu'a, ta d'aga mishi kanta had'i da wucewa bedroom d'inta. Kotu Day3 Abbi da Deeyanah jiki ba kwari a sanyaye suka isa kotun cike da sanyin gwiwa, shiko yasha kwalliya da k'ananan kaya sai k'alli yake yana shek'i fuskarshi d'auke da wadataccen murmushi, ya kafe ta da ido baya ko blinking, tana jin yadda idonshi yake yawo a jikinta amma tak'i kallan inda yake, Alk'ali ya shigo kamar yadda aka saba kowa ya mik'e sai bayan ya zauna kowa ya zauna, magatakardar kotu ya mik'e ya karanto shari'ar da za'a saurara, bayan ya gama Alk'ali ya nemi ganin lauyoyin me k'ara. "Kunzo da shaidar? Kansu k'asa cikin rashin kwarin gwiwa suka amsa da a'a dan sunyi iya yinsu wajen neman hujjar da zasu gabatar a gaban kotu amma dayake Ajlaal shege ne baibar kafa ko d'aya ba yasa basu samu komai ba, sunyi duk wani bincike da bin kwakkwafi amma babu abinda suka samu. Alk'ali ya d'auki lokaci me tsayi tana rubutu kana ya d'ago ya kalli Ajlaal yace " kana da abin cewa? Baki ya d'an tab'e had'i da girgiza kanshi yace " a'a bani da wani abin cewa. "Sakamakon rashin hujja da shaidun da za'a gabatar a gaban kotu dan kotu ta samu gamsuwa yasa ni Alk'ali Bala Muhammad na yanke hukuncin korar k'arar had'i da rufe kundin shari'ar a ranar 20 ga watan 4 na wannan shekarar, ya buga stamp a jikin wata takarda ya mik'e, hannuwanta ta dunk'ule da k'arfi had'i da runtse idanuwanta. "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Abbi ya furta a zahiri cike da takaicin rashin nasarar da sukayi, jiki a sanyaye suka fito daga kotun suna shirin shiga mota ya k'araso inda suke yayi mata kallan cikin ido gami da tauna cingam, har ya juya zai tafi sai kuma ya dawo ya kalli cikin idonta yayi murmushi had'i da cewa " kina tunanin zakiyi nasara akaina ne!? "Shifa Ubangiji ba azzalumin sarki bane, Ubangiji na kowa da kowa ne ko arne wanda ba musulmi ba ya rok'e shi zai amsa. Hawayen data dad'e tana addu'a da fatan zubar su ne suka gangaro kan kuncinta, tasa yatsa ta d'auke hawaye had'i da kawar da kanta ta kalli gefe na tsayin seconds 2 kana ta mayar da kallanta gare shi tace " ka kuma yin nasara akaina, meyasa kake yin duk wad'annan abubuwan Ajlaal!? "Meyasa kake san lallai dole saika lalata min rayuwata? "Akan me wanne laifin nayi maka!? Kallan rainin hankali ya watsa mata kana yayi murmushi yace " nima tambayar dana dad'e ina yiwa kaina kenan kafin na samu amsa ta a ranar da kike fad'awa mahaifinki da ahalinki sirikinki labarin silar faruwar komai, kuma ki daina cewa na lalata miki rayuwa, idan da wanda ya lalatawa wani rayuwa a tsakaninmu kece kika lalata min rayuwata, meyasa Deeyanah? "Meyasa kika dagula komai keda k'awarki akan san zuciyarku? " Meyasa ina zaman zamana lafiya da rayuwata a duniyata kuka shigo duniyata kuka tarwatsa min komai? "Me nayi miki? "Kin cuce ni! kin zalunce ni kin lalata komai Deeyanah, bamfa isa na canja kaina ba, ban isa na koma daddad'a kuma sauk'aka'k'iyar rayuwata kamar ta baya ba fa, ya k'arashe maganar hawaye nabin kuncinshi, ba k'aramin firgici ta shiga ba, tayi bala'in tsorata dan bata tab'a tsammanin yaji labarin ba, lalle akwai k'ura tunda har taga hawaye a idanun Ajlaal. Cikin rawar murya tace " am....am... dan Allah kayi hak'uri wallahi ban san abun zai zama haka ba, nima shawarar k'awata nabi, na sani ni me laifi ce nice ummul aba'isin faruwar komai amma dan Allah kayi hak'uri ka kyale ni haka, idan ma fansa zaka d'auka akaina ka d'auki fiye da fansarka. Yatsa yasa ya kawar da hawayenshi yayi murmushin da saida gabanta ya fad'i, lokaci d'aya taji yammmmm a cikin jinin jikinta. "Gamuwar Gayya tafi ta gayya zafi Deeyanah! ada daban san silar faruwar komai bama banyi niyyar na kyale ki ba balle yanzu dana san kece kika zab'i hakan da kanki, wallahi bakiga komai ba yanzu ma aka fara wasan, sannan duk wanda yayi k’ok’arin shiga tsakanina dake saina ga bayanshi ko waye, haka duk wanda ya hanani aurenki a baya da kuma yanzu shima ya shirya ina nan zuwa gareshi, haka zalika duk duk wanda yayi k'ok'arin dakatar dani.... Lips d'inshi ya cije yana kallan Abbi, ya juya yabar wajen tabi bayanshi da kallo cike da matsanancin tsoro da fargabar da suka shige fiye dana koyaushe. Ran Abbi a matuk'ar b'ace ya shiga gidan Ammu na zaune kan sofa tana sauraren karatun alkur'ani mai girma tana bi ya shigo, d'an kallansu tayi ta kawar da kanta gefe tana fad'in " sannu da zuwa! Banza yayi da ita be amsa ba, dan yau haushin kowa yake ji kuma dai-dai yake da kowa, "saboda wulak'anci ace kana shari'a a kotu babu wanda zai tambaye halin da ake ciki, ko maganar babu wanda ya tab'a yi min, ta gane da ita yake dan haka ta mik'e zata bar wajen. " Au wato ma dan wulak'anci shine ina magana zaki tashi kibar wajen? "To Alhaji me kake nayi? "Babu! nace babu! ya fad'a a harzuk'e, " Allah ya baka hak'uri bani nakar zoman ba, ta fad'a had'i da saurin barin wajen, nan Abbi ya zauna yana ta bambami babu wanda ya kula shi, Babah ma har yazo bakin k'ofa zai wuce zai shiga yaji bala'in yayan nashi, dan haka ya juya, sukayi kacib'us da Deen da shima part d'in zai shiga, " karka shiga neman wanda zai huce takaicin rashin nasararsu a kotu yake, aiko karaf a kunnen Abbi, nan fa ya k'ara harzuk'a ya zage yaita ruwan masifa kan me uwa da wabi har ma'aikatan gidan bai kyale ba, yayi iya yinshi babu wanda ya tanka mishi balle a samu wanda zai kula shi harya gaji dan kanshi ya bari. K'arfe biyun dare tana zaune zaman dirshan a k'asan tile's a falo ba kuka take yi sai dai bala’in da take ji deep down gwara kukan sau dubu, ba zato ba tsammani sai ganinshi tayi a kanta tsaye, ta d'aga kai ta kalle shi batare da tayi magana ba, ta sunkuyar da kanta k’asa, “ Deeyanah! Ya kira sunanta cikin taushin murya, kamar bazata d’ago ta kalleshi ba sai kuma ta d’ago, zubewa yayi gabanta bisa gwiwowinshi ya fakaici idonta cikin zafin nama Ajlaal ya shak'a mata wani abu a hancinta, a galabaice tana marisa ta kalle shi had'i da cewa " meee meee kaaaaa shak'aaa minnn!? Baya tayi luuuuu zata fad'i ya tare ta, ta fad'a jikinshi ya sab'eta a kafad'a tare dayin waje da ita, d'an nesa da gidansu ya kaita inda zata iya hango gidansu tarwai ya ciro wata 'yar kwalba a aljihunshi ya shak'a mata a hancinata, batafi minti biyar da shak'a mata abun ba ta farfad'o, zambur tayi ta mik'e ta ja baya kanta ta kalla sosai kana ta fara waige-waige ta kasa fahimtar inda take ta dad'e kafin ta fahimci a inda take, ta juya ta fuskance shi maganarta na sark'ewa tace " meeeee neee neee kuma? Murmushi ya sakar mata had'i da kallan cikin idonta ya d'age mata gira d'aya tare da nuna mata gidansu da idonshi, a d'an tsorace ta juya ta kalli gidan, ganin bataga komai ba, yasata sake kallanshi tace " me kake shirin aikatawa? Bayyi magana ba illa murmushin daya sake yi mata had'i da sake nuna mata gidansu da idonshi, gidan ta zubawa ido na wajen minti biyar amma shiru, " wai me....... Wata irin mahaukaciyar k'ara ce ta sakata yin shirun dole, saida k'asar wajen tayi girgiza ji kake durummmmmmmm! Dammmmmm! yadda kasan k'arar fashewar dutsen zuma rock ko gigitacciyar tsawar da akeyi lokacin damuna, durk'ushewa tayi a k'asa gami da sanya tafukan hannayenta ta toshe kunnuwanta. Iface-ifacen mutane da salati ta fara jiyowa, a hankali ta zame hannayenta daga kan kunnuwanta, wani rikitaccen tsoro ne ya ziyarce ta lokaci d'aya, tana daga durk'ushen amma tana jin yadda k'afarta da jikinta ke rawa, dakyar ta tattaro d'an ragowar k'arfin daya rage mata ta mik'e, kallanshi take yi tana san tambayarshi k'arar meye amma ta kasa koda motsa bakinta balle ta iya furta koda kalma d'aya, fahimtar abinda take san tambaya yasa shi sake nuna mata gidansu da ido, tsoro, firgici da tashin hankali ne suka hanata juyawa ta kalli gidansu, hannunshi ya d'ora saman kafad'arta ya juyar da ita, idonta ne ya sauka akan gidansu dake ci da wata irin mahaukaciyar wuta, wata irin rawa k'afarta ta d'auka kafkafkaf jiri ya d'ebeta ya watsar gefe, kwakwalwarta ta tsaya cak, zuciyarta ta daina bugawa, komai nata ya tsaya cak ya daina aiki, yadda kasan mutum mutumin da aka dasa haka ta koma, tana ganin mutane nata ihuuuu ana tururuwar zuwa kai taimako amma ta kasa ko motsi, akan idanuwanta iyayenta, mijinta, yayyanta, 'yan uwanta da ahalinta gaba d'ayansu kaf suka k'one k'urmus tana jiyo salati da ihuuun azabar fitar ransu a cikin kunnenta amma babu yadda zatayi. Duk iya k'ok'arin mutane sun kasa tunkarar gidan saboda tsananin k'arfin wutar daga nesa ma suna jiyo hucin wutar balle sunje kusa, ko mutum d'aya ba'a iya cetowa ba har ma'aikatan gidan sun k'one, jama'a sai tururuwa akeyi ana salati, bazata tab'a manta wannan bak'ar rana ba, ranar data rasa kowa nata a duniya, ta zama ita d'aya tilo tana reto a duniya, hoton wannan mummunar ranar bazai tab'a goguwa cikin kanta ba. Babu abinda ke motsi a jikinta har idonta baya motsi yadai tsaya cak akan gidansu, murmushi yayi had'i da sunkuyawa ya kama hannunta yajata ba musu kamar rak'umi da akala tabi shi sukuku, duk inda ya cire k'afarshi nan zata d'ora tata kamar mutum mutumin da aka sassak'a da ice, babu abinda ta sani, ta manta komai da kowa, ita kanta ma ta manta wacece ita, babu abinda zata iya tunawa, yana rik'e da hannunta suka isa can nesa inda ya aje motarshi, ya bud'e mata gaban motar yace " shiga! amma ko gezau batayi ba, da kanshi ya saka ta cikin motar ya zaunar da ita, kana ya zagaya ya shiga yaja motar, bai tsaya ko'ina ba sai a harabar gidanshi, ya fito ya zagaya ya d'auke yayi cikin gidan da ita. Saman bene ya hau da ita ya shiga d’aya daga cikin bedrooms ya shinfid’e ta saman gado, ya juya zuwa fridge ya bud’e ya d’auko kwalbar ruwan allura da saban sirinji yaja ruwan allurar ya kifa ta tare da mayar da gashin kanta gefe yayi mata allurar a k’eyarta, wata irin jijjiga jikinta ya d’auka lokaci d’aya hak’oranta suka rink’a kaf kaf kaf, bak’in cikin idanuwanta ya d’auke sai farin while idonta na far far far, ta dad’e haka kafin jikinta ya saki ta kwanta lakwas. Kwashewa yayi da mahaukaciyar dariya tare da fad’in “ nayi miki allurar mantau na shafe miki duk abinda ke cikin kwakwalwarki kinyi loosing control sai abinda na sanar dake zaki yarda, ni kad’ai ne zab’inki kamar yadda na fad’a miki a baya, abinda naga dama dashi zaki yarda dole, nine dolenki sai yadda naga dama zanyi dake……