﻿[6/28, 11:15 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of majesty*✨


Na
💄 _Meryerm Abdool_💄


© *Pure moment of life writers*
       P.M.L💪🏽




```zanyi amfani da wannan damar nayiwa dukannin masoya da abokai da 'yan uwa musulmi murnan kammala Ramadan lafia, sannan nayi muku barka da sallah fatar Allah ya karb'i ibadunmu ameen```👏🏽





📝 *Episode* 1⃣⏩5⃣




بسم الله الرحمن الرحيم
 
Dukkan yabo da godiya su tabbata ga Allah mad'aukakin sarki, mamallaki sarkin iya halitta, tsira da aminci su tabbata ga Annabi Muhammad(S.A.W) 
Tare da sahabbansa da iyalan gidansu da duk wad'anda sukabi tafarkinsa har zuwa ranar ceto


_Banyi niyyan rubuta wannan littafin don cin zarafi ko fuska ga wani ba, idan kuma yaci karo da halinka/ki saiki/ka gyara, a guji zargi._

*Ban yadda wani ko wata ya juyamin koda kalma d'aya ne sai tare da izinina*


Tukuici gareku ahalina ina alfahari daku a duk inda naje, Allah yabar kauna ya rayamu a musulunci damu da sauran musulmi baki daya. *ILYSM❣





             *KADUNA STATE*

*kofar mashi*


Garden ne matsakaici mai cike da furanni masu fitar da daddad'an k'amshi da itatuwa ma'abota fruits, gurin yayi kore sharr sai wata sayyayar iska ke kadawa wacce kowane ma'aboci halitta zaiyi sha'awar ya shaka, gurin d'auke yake da resting chairs farare,  ga wata k'orama a gefe tana gudana abin gwanin sha'awa da burgewa.

Na shagala da kallon gurin, inata baza idona abinka da bakauyiya, can gefe cikin daya daga cikin rest chair na hango wani matashi a kwance.

Daf dashi naje domin naji dad'in d'akko maku rahoto dakyau, idanuwansa a lumshe sanye da wani siririn farin glass da alama medical ne, amma hakan bai hanani gane cewa matashin ma'aboci golden eyes bane saboda yadda eyes balls nasa ya fito akan fatar idon, hancinsa ba dogo bane hasalima za'a kirasa da guntu in short, kalar fatarsa abin burgewace wato chocolate.

Kallon nai masa da sama har k'asa na fahimci baida tsayi sosai, baida jiki ko kad'an saidai yana da k'irar k'arfi, gashin kansa irin na hausawa ne amma kan yasha gyara yayi kyau ya kuwa kwanta ba laifi, yana da round face kamar mace wacce ke zageye da man pride, bakinsa mai matukar kyawu d'auke da soft red lip, ina cikin nazari banyi aune ba naga ya mik'e tare da sauko da k'afafunsa kan shoes nasa, mashaa Allah k'afarsa abin sha'awace kamar a rangada mata lalli.

Mik'ewa yayi tare da d'aukar phone masa da iPad nasa dake kan desk yayi, sanye yake da shirt orange da jean baki, idonsa na kalla saida k'irjina ya buga kwayar idon brown ce yayin da farin ya surka da pink, bansan time d'inda nace subhanallah ba, ban tab'a gani irin idonsa ba before.

Inacan duniyar mamaki sai ganin nayi yakai k'ofar fita daga garden d'in, hakan yasa na bisa a 150 saboda ci gaba da samo maku rahoto. Lolz

Wata 'yar k'aramar k'ofa naga yabi sai kawai na gammu '' cikin wani matsakaicin parlour wanda yaji kayan more rayuwa dai2 irin na masu rufin asiri, wata matace zaune wacce i k'iyasce zatayi shekara arba'in da d'ori, a fizge tana kama da matashin, husnul musleem rik'e a hannunta tana dubawa.

Sai wata yarinya dake kwance gefenta tana barci a kalla zatayi ten year, sai yaro a k'asa sai faman zane yake a littafi sa'an wacce ke bacci da alama ma twins saboda kamar da sukeyi.

Zama matashin yayi kan 1seat bayan yayi sallama sannan YACE.

"Maamii sannu da gida."shima yaron yace " welcome ya Abdool. "
 
"Yawwa big boy me akeyine?"
 
"Homework ne."

"Ok a bada himma."

Itama Cikin kulawa bayan ta ansa sallamarsa tare da aje husnul musleem tace "yawwa Abdool dama ba fita kayi ba kenan?"

"Eh Maamii nad'an garden ne."

"A toh madalla, toya maganan horsemanship naka?"

"Eh Maamii inshaa Allah 2/3 week dai zasu kiramu."

"Sokoton dai koh" ta fad'a tare da kallonsa.

Shafa kansa yayi yace "itace Maamii."

"Nikam Abdool bansan meyasa ka nace sai Sokoto ba duk hospital d'inda ke Kaduna da zagaye ba wacce tai maka ne ko meye?"

Smiling yayi yace "ba haka bane Maamii inadai son naje gidane nayi wa garina hidima, kuma kinga zan k'ara sabo da 'yan uwana."

Nisawa tayi tasan abinda d'an nata ya gad'a gaskiya km hakan dazaiyi yayi dai2 saidai batason tayi nisa dashi ko kad'an.

Yaron da ke drawing jin yayan nasa na maganan tafiya yasa ya aje book d'in yaje kusa da yayansa yace "yace Ya Abdool da gaske tafia zakayi ka barmu?"

Shafa kansa yayi yace "Ajb ba dad'ewa zanyi ba, kuma zan ringa zuwa ina dubaku kaji my boy."

Girgiza kai yayi yace "nidai zan bika Yaya" ya fad'a yana narkewa jikinsa.

"To karatunfa Ajb?"

"Nayi a can."

Murmushi yayi yace "Ajb rigima, ita Husna tayi nata homework d'in?"dan ya d'auke masa hankali.

"Aa headache takeyi."

Mik'ewa yayi tare da zuga gaban seat ya dafa goshinta yace "Subhanallah tasha magani kuwa?"

"Aa batasha ba tai bacci."

Cikin nuna damuwa ya mik'e zuwa d'akinsa dan d'akko mata magani, Maamii kuwa sai kallonsa take tana k'ara godewa daya had'a mata kan 'yayanta suke tausayawa juna da k'aunar juna, sosai Abdool ke nuna kulawarsa akan kannensa ga saukin kai, yakan wasa dasu sosai sannan ya tsawatar musu idan sukayi ba dai2 ba( _shine gaskiyar rayuwa_).



^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^




            *SOKOTO STATE*
*Garin kilgori dake*


"Laure! Laure!! Laure!!!" Firgigit ta juyo tare da baro tagar ajin tazo gun mai kiranta tace "Delu ahe kece ina zakina halan?"

"Kekam Laure bakijin maganar Iya Hari, hi yassa kullum taka bugunki kaman ganga tase bataso kiyi boko, missa kika dagewa sai keyi, wane dadi agga boko?"

Dafa kafad'ar Delu tayi tace "Delu bansan missa Allah ya jarabceni dason boko ba, kullum inaji cikin raina zanyi boko kuma nayi alfahari dahi, amma bansan sai yauhe ba, duk ni gitto ta makaranta ji nikai kamar an damremin kafwa inji hena tsaya naji kara2" ta K'arashe maganar tare da zubar da hawaye.

Cikin tausayawa k'awar tata ta share mata hawaye tare da rungumota jikinta tace "kiyi hank'uri Laure da nuhar Allah zakiyi boko wata rana, yanzu ki d'auko turenki mu wuce gida tun kafin ki husata Iyaa Hari ta jibgeki tunda ba mutunci gareta ba."

Haka taje bakin tagar daga k'asa ta d'akko tiren gyad'arta, suka bar makarntar mai d'auke da 'yan ajijuwa da basu wuce biyar ba, suka doshi cikin gari.......



_Tirkashi to ma'abota karanta novel d'in Meryerm ko biyoni a sannu kuji da wanne salon nazo wannan karon_ love u friends💞










💄Meryerm Abdool💄
[6/30, 6:44 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽



```Jinjinar ban girma gareku zak'ak'uran marubuta, da girman kujerarku manyan mata masu duniya, gareku members of pure moment of life writers, ❤ more Greece 2 ur shinning elbow💪🏽```




       📝 *Episode* 6⃣⏩🔟



Da d'an jayawa kafin a isa cikin garin tafe suke k'awar tata naci gaba da bata shawara da k'arfafa mata gwiwa.

Gari wanda za'a kirasa k'auye kuma garin fulani kai tsaye duba da yanayin gine-ginenda ke cikin garin, amma da alama manoma ne kuma makiyaya dan ko'ina ka duba shukace tun daga dajin garin har zuwa cikin garin, kama da gero, Masara, maiwa, albasa, tomatur, ata, tattasai kai har noman taba sunayi, ga kuma dabbobin na ciwo, a takaice dai da alama ba talauci a garin.

Dai-dai k'ofar wani gida Wanda zance duk garin ba irinsa naga sun tsaya, nan k'awarta tace "to Laure ni zan isa gida saike hito anjima Dandali" ta fad'a tare da tafiya.

"Tau Delu ki gaida Gwaggo" cewar Laure tare da sanya kanta a soron gidan, amma kuma fuskar taf tashin hankali k'irjinta sai bugawa yake dan batasan yau kuma wane kalan zagi zata samu ba.

Wata dattijuwace zaune tsakar gidan tana tunka tsawo, bakace mai tsamuraren jiki, ba laifi fuskarta irin ta fulanice saidai ta tamure itama, ga taba ta k'unsa a bakinta redio gefenta tana jin wakar *Barmani toge* cikin sanyin murya tayi sallama.

Dagowa tsohuwar tayi ba tare da ansa sallama ba tace "to gantalalliya sai yanzu kikk'are gantalin naki, keman Laure anyi tambad'add'iyar yarinya yanzu tun abun Hantsi sai yanzu kika dawo mini."

"Subhanallah, haba Hari wanga bacin k'are dangi da kikai ma diyanga marainiyar Allah dami yayyi kama? Hari wai mi diyanga tayyi miki da baki tab'a nuharta da alheri ba se sheri?" Wani farin dattijo ya fad'a yana aje buta fitowarsa kenan daga bayi.

"Haba Ardo wai missa kullum kurkiiyarga tayyi min laihi baka gani? Saima nawa kaka gani sannan ka bini da ganin laifi, koni kabar yimin irin haka ai sai kasa ta hwandare dama yaya lahiyar kura bale tayi hauka" ta fad'a cikin nuna bacin rai.

Girgiza kai kawai yayi tare da cewa "Allah ya kyauta" inda sabo ya saba da halin Hari Sam batason gaskiya.

"Ramlatuna shiga daga ciki ki aje turen saiki kawomana ruwan alwala garka kejina 'yar Albarka" ya fad'a tare da ficewa daga gidan cike da tausayinta.

Matse hawaye tayi tare da shigewa d'aki ta adon aje tiren, da harara ta rakata tare da banka tsaki tace.

"Munahuka dangin mayyu tai ki dawo ki iskoni saike hwadamin inda kittsaya."...........



_tofa meye sanadin wannan k'yayyar? Nida Ku mubi a sannu harmu gano bakin zaren_🤔😔 



^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^



      *KADUNA STATE*



*3 weeks later....*


Gabadaya sun fito waje domin raka Abdool zai wuce Sokoto saboda an kirasu, sanye yake da jean blue da shirt purple yana sanye da glass nasa as usual, left and right nasa yana rungume da Husna da Ajb, momynsu na bayansa, sai k'anwarsa Nihal data dawo Hutu week before tana rataye da lodge nasa.

Bakin motarsa suka tsaya ana k'ara bankwana, su Husna sun lafe jikinsa Sam basaso ya tafi saidai ba yadda zasuyi saboda tafiya ta zama dole...

"Abdool ka kula sosai ka tsare mutuncinka da kimarka, ka kula da ibadarka ka rike Addu'a sannan ka sada zumunci da 'yan uwanka kada ka nuna musu komai sai Alkhairi, Allah ya kiyaye hanya, ya Baku sa'a da nasara akan abinda kukajeyi."

Ba kad'an yaji dad'in addu'ar Maamii tasa ba, yace "inshaa Allah Maamii zan kiyaye, aci gaba dayi mana Addu'a, Addu'arki itace silar cigabarmu."

"Addu'a ba fashi Abdool Allah ya k'ara shiryaku baki d'aya."

"Ameen Maamii" ya fad'a sannan yace "my guy missing u" yace tare da rungumesu, suma rungumesa sukayi sukace "missing u too bro.

Dak'ar suka rabu yaja car d'insa cike da kewar familyn ya d'auki hanyar birnin Shehu..........



_wasa farin girki muje zuwa friends_ 🏌🏽⛹🏾‍♀ 





💄 Meryerm Abdool 💄
[7/2, 11:55 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽



```Manzon Allah (S.A.W) yace:-```
*Yana daga cikin kyawawan dabi'un musunci mutum yabar abinda bai shafesa ba.*

( _Tirmizih da wadansu suka ruwaitoshi, daga hadisai arba'in_ )






        📝 *Episode* 1⃣1⃣⏩1⃣5⃣



Saida ya biya ta Unguwar Rimi ya d'auki friend d'insa Hakeem Wanda shima a Skk zaiyi horsemanship nashi saidai shi pharmacy ne, t'uki yayi cikin Jean vitae hankali suna tafe suna sauraren wak'ok'in larabawa na *Mishary Raseed Alfasy* dama Abdool ba rigima, tun Hakeem na mitar t'ukin har ya hak'ura dan ba yadda ya iya da mutumin nasa, gashi shi yace bazaiyi driving ba, dole ya bisa a yadda yakeso.

Basu suka isa ba sai after ishaa, direct family house nasu suka wuce, estate ne guda, mai d'auke da compartment 5 mafi girma daga ciki naga sun dosa, direct main parlour suka sauka.

Da sallama suka shiga, wani dattijone zaune kan kujera, ga wasu samari gefensa alaman magana suke dukkansu kusan tsaran Abdool ne, cikin farinciki suka juyo yare da ansa sallamar, tasowa sukayi suka rungume Abdool da Hakeem tare da fad'in.

"Ur highly welcome home bro" sannan sukayi musabaha, shima cikin murmushi, yace "fatar na sameku lafia?"

"Alhmdllh" suka fad'a tare da k'arasawa gurin dattijon gaba d'aya, fuskarka d'auke da murmushi ko ba'a tambaya ba kasan yana farinciki da zuwan jikan nasa.

Kan hannun kujerarsa Abdool ya zauna tare da rungumesa yace "tsoho mai ran k'arfe  kaga jiya kaga yau."

"Zanga gobe da yardar Allah kuma, likkita bokan turai yau kaina a sakkwato?"

"Sharri kayan kwalba, sai yau ka saba ganina a sokoton?"

"Kai bature kada ka wayance yaushe rabonka da garin?"

Sudai samarin da Hakeem sai kallon drama suke suna dariya babu mai barin ta kwana cikinsu.

Saida suka gama rigimarsu sannan aka gaisa.

"Abdulmajeed ya Maman naku da kannenka duk kuna lahiya dai ko."

"Lafiya qlau Alhaji sunce a gaisheku sosai."

"Kai madallah, haka akason ji, kai sama'ila kuje dasu ciki sud'an huta, kasan halin likitoci basu son wahala" ya fad'a yana kallon Abdool.

Smiling yayi "haba tsoho nida nike sabon jini saidai kai daka kwana biyu jini yayi nisa."


"Ho dan nemanga tahi ka dawo ka taho mu gwada kaga aikin tsohon kashi"

Dariya yayi tare da bin bayan su Hakeem da suka fice suna dariya yace.

"Rufamin asiri dattijo A d'auri kashi ko a bata igiya" ya fad'a tare da ficewa.

Shima dattijon dariya yayi yana maijin dad'in ganin jikan nasa da aka kwana biyu ba'a had'u ba..............




^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^




Sumui-sumui ta shigo kamar munafuka taje bakin randa da niyyan d'aukar buta tayi alwala, taji muryar Iya Hari tace.

"Tau jikan mayyu, waje Musa ciki Fir'auna kinzo kina wani Abu kamat ta kwarai kewai ga musulma, ki gama gulmarki kizo ki sameni saike bani labarin ubanda kika d'auka a makarantar bokoko da ki k'wuk'wema zuwa dudda na hissheki ciki, ko wani salon karuwancin na a haka eye."

Itadai shiru bata motsa ba bare ta tanka, inda sabo ta sama da irin wad'annan cin fuskar da zagi daga Iya Hari, Sam bata ragamata ko k'adan akan laifin da ba ita ta aikatashi ba, amma kullum a Kanta take saukewa.

"Oho ina magana keyimini tsaye k'ik'am kamar icce niddasa ko, kedai anyi shegiyar yarinya mai bakin hali, maza ki aje butan nan ungu ki kaima Lanti saura ki wuce wurin gantalinki da kissaba."

Cikin sauri hadda hard'ewa ta amshi ledar tare da ficewa da sauri kamar mai jiran cas, da tsaki ta bita tare da cewa.

"Tai ki dawo ki iskoni kici na jaki, bak'ar iri."


Tafe take cikin nutsuwa idan ka ganta ba zakace 'yar kauye bace, saboda tafita daban dasu komai nata a natse kamar wata babbar mace duk kuwa da k'arancin shekarunta.

Daga sama taji ana kiranta, ko bata juyo ba tasan me kiran nata, tsayawa tayi ba tare data ansa ba kuma bata juyo ba.

Wani hargitsatsen matashi ne ya tsaya gabanta, kalar irin ta 'yan daban fulanin nan bakinsa bak'i k'irin irin na 'yan sha, ido jajir kamar gauta.

"Waike Laure minana abbusa kanki, walle keci azzikin ina sonki daba haka ba hmmm khattt...." Yayi kwafa.

Itakam kallo kawai ta bishi dashi ba tare da tace uffan ba.

"Ke halan icce kike ina magana sai kallona kikai ko nayi miki kyauna" ya fad'a yana wani k'wanbewa.

Sanin halinsa idan ba maganan tayi ba ba barinta zaiyi ta tafi ba yasa tace.

"Jauro daga ina haka?"

Wani dad'i yaji ya lullub'esa dan ba k'aramin so yakema Laure ba shiyasa yake daga mata k'afa lokuta da dama ita kadaice weak point nashi, ko Abu ya had'aku da kace don Laure tofa yanzu zai sarara maka, duk kuwa da tsagerancinsa dan duk garin kowa shakkunsa yake saboda dan Sara sukane kowanne lokaci yana tare da makami, ganin badan arziki bane yasa Iya Hari amincewa da soyayyarsu da Laure, saboda kawai ta musguna mata.

Ardo yaji duk abinda ake ciki amma bai nuna ya sani ba, ya barsu yaga iya gudun ruwansu, abinda kawai ya sani bazai taba Aurar da marainiyar Allah.

"Daga daji nike, kehwa INA zakina?"

"Hmm gidan Gwaggo Lanti" ta fad'a a takaice, tare da juyar da fuskarta ganin irin kallon da yake mata na k'urillah.

"To..toh mutai in rakaiki?"

Ganin no way 2 escape yasa ta yadda suna tafe yana mata hira, ita kam sai uh da uhum da to take binsa dashi.

Aiko har suka isa ba'a samu Wanda ya daga ido ya kallesu ba saboda sanin hali, haka yake gadinta kamar kwai, ba kuwa ubanda ya isa ya kalleta balle yace yana sonta duk kuwa da dimbin masoya da takeda shi, amma suna gudun rasa rai dan k'aramin aikinsa ne, kisa.

Saida yaga shigarta sannan ya juya zuwa sabgarsa..........



_Rikici ba gado ba_ 🤣😜 









💄 Meryerm Abdool💄
[7/4, 10:31 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽



    *DOLE NA JINJINA MUKU*

*MAMAN USSEY*
*ABDOOL AAJ*
*FATYY AZLAND*
*UMMI A'ISHA*

_kud'in daban kuke, kamar yadda halinku na k'aramci ke nuna Ku, bazan gaji da fad'a ba wato da bazarku nake takawa 💃🏻 halin kirkinku yabiku har gadon bacci_ 👏🏽



      📝 *Episode* 16--20




Saida sukayi fresh up suka d'an ci abinci da yake an shirya musu better, amma Abdool kad'an yaci dan idan da abinda ke bashi wahala to cin abinci ne.

Maamii ya kira ya fad'a mata sun sauka lafiya tare da gaisawa da k'anninsa wad'anda ya fara missing tun yau, cikin gida suka shiga suka gaida da kakarsa wato Haj, Saude wacce ta ansa su sama2 ko halinta ne haka oho!.

Daga nan suka shiga sauran gidajen suka gaisa da iyaye, yayyi, da kanni, daga nan suka koma inda tsoho mai ran k'arfe inji Abdool fa.

Hira suka sosai kaman ba wad'anda suka sha hanya ba har 12, Alhaji Sada yace suje su huta zuwa gobe kuma aci gaba.

"Wane gobe Alhaji nida zanyi sammako saidai na barku da Hakeem."

"Au abun 'yar hakane shine ka gudu *Yabo* dan kada ka zauna Sakkwato ?" Alhaji ya fad'a yana hararan Abdool.

Dariya yayi "Alhaji aiba laifina bane kuma ai anan Sokoto akwai consultant doctors da yawa k'auyukan sunfiku bukatar likita."


"Ho dan nema badai iya fad'a ba, Allah ya taimaka, k'ilama acan ka samo 'yar budurwa, koda yake naga alaman tsoron mata kakeyi, kila sai munyi maka gangami an d'aura maka a k'afa."

"Hhhhhhh kajika da shirmen tsufa, an gayama ni Kaine, aini matata ba'ama haifeta ba" shidai Hakeem sai dariya yake suna burgesa.

"Aa kak'i cewa mamarta ma ba'a haiheta ba, ja'iri zanso naga wacce zata aureka da shirmen nan naka, kaidai ba abinda ka bari na 'yan fari"

Dariya sukayi banda shi murmushi kawai yayi tare lumshe ido.................




     _wannan kenan_




^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^



Zaune suke a Dandali, wasu na gad'arsu yayin wasu ke samartaka, wasu na siye da siyarwa, "Laure kina zuwa Yabo ran juma'a kai nono?"

"Kai Delu kema kesan dolena intahi inhar inason in tsira da mutuncina, Iya Hari, tun yau tayo tatsarta baki ganai ba mai yawa kuma nid'ai."

"Aa na d'auka ko mutuminki ya hana kinsan shi dole yabi dokarsa koya taka ta."

B'ata fuska tayi tace "wane mutumin nawa?"

"Jauro mana ko kinada wani bayan shina?"

"Ni wallah Delu kibar had'ani da wannan mugun abu" sai hawaye sharrrr..

Tasowa tayi da sauri tare da rungumeta "yi hankuri abukkiyata nifa da wasa nikai miki, amma ai bana fatan ki kasance matarsa koda maza sun k'are ko."

Sauke numfashi tayi tare da share hawaye "wallahi Delu na tsani Jauro bansan ya nikai dashi ba, amma ita Iya Hari ba Wanda takaso saishi, saukina Ardo har yanzu baice komi ba, ina tsoron kar shima ya yadda."

"Ina Ardo bai tab'a aura miki, Jauro kuma inshaa Allah saikin auri d'an arziki kamar kowa, me ake da J......" Kasa isuwa tayi saboda arba ta tayi dashi yana zuwa, da alama a buge yake sai layi yake ya tunkarosu ga muk'arrabansa bayansa suna take masa.

Jin k'awar tata tayi shiru ne yasa ta d'ago dan ganin meke wakana, arba tayi dashi ya kusa kawowa wurin da suke, d'aure fuska tayi tare da d'auke kai.

Cikin muryan 'yan sha yake magana "ya ke Laure baki ganeni ba halan kiyi fuskar shanu tare da d'auke kai" sannan ya kalli Delu da tasha jinin jikinta "ke munahuka tashi wuce gulmammiya."

Aiko da sauri ta d'auki tirenta ta cika bujenta.

"Haba Jauro wai meyasa kakaimin haka, kaga banson haka, hakad'ai ka korar min abokiyata."

Tunda ta fara magana kallonta kawai yakeyi cike da sha'awa Sam shi bai gane fad'a take ko hira take masa saboda tsananin so.

Wani daga cikin yaransa ne yace "ke oga kika dagama murya saboda ke rammai?"

Tsawa ya daga masa "kai Shago Laure ce fa, kakewa fwad'a?"

Ya fad'a yana zare ido kaman ya maresa, "tuba nike oga."

"Ka kiyaye gaba" koda ya duba har ta bar gurin, murmushi kawai yayi tare da k'arawa gaba.


_so kenan hana ganin laifi_




*Pls friend kuyi hak'uri dani ina fama da matsalan wayatane shiyasa bana typing da yawa.* love u all😘 








💄Meryerm Abdool💄
[7/7, 8:42 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽



```Where r u? Here is ur page, Momyn sultan, Sakwara, Iya Amima, Sadnap, Sadnas, kanwata jannart, Rukie kax and d rest. ur d best among besties. 💕```






     *In dedicated 2 Abdool all over d world* 💘







      📝 *Episode* 21--25






Bayan sun dawo da sallar asubah a d'akin kakan nasa ya yada zango, ya iskoshi zaune kan kujera tasbaha a hannunsa yana ja, hannu ya bashi sukayi musabaha tare da yimai barka da asuba sannan ya zauna k'asa dai2 kafarsa yace.

"Ina kwana Alhaji?"

"Lafia lau Abdulmajeed ya gajia?"

"Gajia ta tafi, ya girma ya kuma hak'uri da jama'a?"

"Alhamdullilah, zuwa yaushe zaka tahi yabon?"

"Um zuwa goma nakeso na tafi, shima Hakeem tare zamu fita yaje yayi report a Uduth d'in?"

"Amma anan zai zauna ko?"

"Aa zasu bashi gida to inaga acan zai zauna"

"Ikon Allah tahiya zakuyi gabad'ai?"

"Aa ai Hakeem zai ringa zuwa yana gaida ku, ni kuma zan ringa zuwa end of week inshaa Allah."

"Tau ba damuwa, Allah ya taimaka ya baku nasara a aikinku" sannan ya k'ara da cewa.

"Kaci gaba da hak'uri Abdulmajeed, dama nasan kai mai hak'uri ne, kowane bawa da yadda Allah yake tsara mishi rayuwarsa, idan aka d'auke shi a jarrabawa akayi hak'uri sai kaga ya wuce sai labari, Allah yayi maku Albarka."

"Ameen Alhaji nagode, zan shiga daga ciki nad'an kintsa kafin lokacin yayi."

"Tau yaushe zakaje Argungu can inda kakanninka?"

"Shima idan nayi clearing abubuwa zanje."

"Tau ka shiga ciki kayi sallama da iyayenka da kakarka kaji ko?"

"Inshaa Allah" ya fad'a tare ficewa yana share hawayen da suka zubo masa Wanda ni kaina bansan dalilin zubarsu ba, (tofa kona meye? Mubi a sannu zamu fahimci na meye nan gaba).


Tsaf ya kimtsa shida aminin nasa bayan sunyi sallama da mutan gidan, uduth suka nufa saidai ya tabbatar anyi komai daya kamata ayi sannan ya wuce yabar Hakeem tare cousin nashi su Isma'il, saboda a dalilin sa ya cika garin yaso su samu asibiti d'aya saidai hakan bai samu ba.

Hakeem aminine na kwarai ga Abdool Wanda bayada kamarsa amintarsu ta samo asaline daga secondary har jami'a Wanda har takai ga iyayensu, kullum Hakeem yana lura da akwai wata b'oyayiyar damuwa tattare da Abdool yasha tambayarsa amma kullum amsar d'aya ce ba komai,  ya dad'e da sanin halin Abdool na zurfin ciki Sam baya bari damuwa tayi tasiri akansa yana k'ok'arin boyeta, dole shima ya hak'ura yasan in lokacin ya Sani yayi to tabbas zai gayamasa.

Shima dai ya isa garin Yabo kuma ya samu karb'a mai kyau daga mutanen garin amma kam asibitin na buk'atar ma'aikata da kayan aiki, a dalilin haka yayi alkawarin taimaka musu iya k'arfinsa Dana aljihunsa.

_wannan kenan_




^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^



Tana tafe tana tunanin irin k'iyayyar da Iya Hari da Gwaggo Lanti ke nuna mata basu tab'a sonta ba, kullum cikin zaginta suke, k'arshe k'iyayya yakai su zab'a mata jauro a matsayin masoyi.......

"Ramlatuna" ko bata juyo ba tasan duk fad'in duniya bamai kiranta da wannan sunan sai shi kad'ai, juyowa tayi da murmushi akan fuskarka yana zaune bakin gidan yana duba littafi ashmawi Sam bata lura dashi ba ta tafi duniyar tunani.

Dawowa baya tayi tare da duk'awa tace "sannu Baffa, ban kula dakai ba."

Murmushi yai mata "daga ina kike da darenga?"

"Baffa daga Dandali tallen gujjiya."

"Bana hanaki zuwa Dandali da daddare ba?"

Duk'ar da kanta tayi ba tare da tace komai ba.

"Koda yake ba laihinki naba, kiyita hank'uri Ramlah da Hari inada tabbacin wata rana zata gane batai miki adalciba, kuma da yardar Allah inaji a raina sai ke zama abin alfahari a wanga karkara."

Wani k'unshi ya d'auko bayan shi ya mik'a mata "kici wanga nasan da wuya in keci abinci"

Ansa tayi zata shiga ciki tare da cewa "nagode sosai baffa" dakatar da ita yayi tare da nuna tabarma.

"Zauna nan kici" saboda sanin halin Hari idan ta gani ba barinta taci zatayi ba.

Ba musu ta zauna tare da kwance ledar nama ne agashe da zafinsa ci take hannu baka, kallonta Ardo yakeyi cike da tausayi yana mamakin hali irin na Hari, Sam batada zuciyar imani.

Cikin k'ank'anin lokaci ta cinye, ruwa ya bata tasha sannan yace ta shiga ciki, cike ta shiga zuciyarta wasai tana mai jin k'aunar Ardo har cikin ranta.

Shima d'auke kayansa yayi tare da shigewa ciki dama ita yake jira.


*Washe gari*


Kamar yadda ta saba tashinta da ruwan sanyi yauma hakane, dasu ta tasheta tare da binta da zagin k'are dangi kamar yadda ta saba.

Haka ta tashi tayi abinda ya zame mata dole sannan tayi shirin zuwa Yabo.

Zuwa karfe 9 sukaje titi don zuwa Yabo, sun kuwa yi sa'a sun samu mota, tunda suka fara tafia sai murmushi take kallonta Delu tayi "Laure missa meki na farinciki sai murmushi kikai ked'ai."

"Ni kaina bansani ba, nadaiji yau farinciki nikeyi Wanda bansan dalilin inaji a jikina wahalata ta kusa zuwa k'arshe."

"Tau Allah ya tabbatar."

"Ameen abukkiyata."



 *A garin Yabo*

Abdool ne zaune kan mota bakin asibiti kasancewar yau ba aiki da yawa patients basuda yawa yaje yayi round shine ya fito waje yana shan iska, yau tunda ya tashi gabansa ke fad'uwa baisam me yasa ba, ya kira Maminsa yaji suna lafia, haka bangarensu Alhaji suma lafia.

Jin bugun zuciyarsa ya tsananta yasa ya rik'e gurin tare da yin Addu'a.

Jin ta sassauta yasa ya d'ago kansa karaf idanunsa suka sauka kan na NATA...........

Lokaci d'aya zuciyarsa ta buga kamar ta fito.....



_wacece wannan_
🤔 




*Friend kuyi hak'uri da jina shiru da kukayi hakan ya farune a dalilin rashin nepa da mukayi 2days* love u❤ 







💄Meryerm Abdool💄
[7/10, 1:32 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽




*Annabi Muhammad (S.A.W) yana cewa:-*

_baya shiga aljannah wanda mak'wabcinsa bai amincewa ha'incinsa ba._


*'yar uwa koda kafiri kike mak'otaka ya zama dole ki sauke nauyin hakk'in mak'otaka daya rayata akanci, makota abune mai girma saboda fadar manzonmu.*

"Jibrilu ya kasance yana yimin wasiyya da mak'oci har saida na d'auke idan na mutu zai gajeni".


_Allah yasa mu gyara_ 👏🏽




         *Point of correction*

_Abdool service sukeyi ba internship ba, fatar kun gane frnds_.




      📝 *Episode* 26--30





Sanye take da kaya irin na Fulani, fuskar nan tasha d'ige-d'ge ga k'waryar nono a kanta, kyakkyawace ba laifi farace ga mai tsayi da jiki, tanada kyawun fuska ba can sosai ba, fuskarta d'auke da murmushi amma zaka fahimci tana tare da damuwa, duk cikin sakan da bai wuce 50 ba Abdool ya karance yarinyar wacce ke tare da k'awarta, amma da alama yarinyace sosai saboda fuskarta ta nuna girman jikine kawai, amma abin tambayar meyasa yake ganin kamar ya Santa?, meyasa k'irjinsa ya harba saboda ganinta?

Ganin baida wad'annan ansoshin kuma gashi zasu wuce yana bukatar nonon yasa ya kirasu.

" 'yan fulani masu nono kuzo in siya".

Laure da saukarsu kenan, jin ance 'yan fulani yasa ta kalli, gurin me kiran nasu, k'irjinta ne ya buga ba shiri ta kalli k'awarta.

"Delu kega me kiranmu ko? Diba kigani kamar ba d'an nanniya ba, duba kalar idonsa abun tsoro, jishi d'an gaye, da kayan lifitoci irin na binni, muje ko kar muje"?

Me Delu zatayi inba dariya ba, saida tayi mai isarta ganin mutuniyar an fuske yasa ta sassauta.

" wlh Laure wani lokacin shirme ke dibarki yoni mi'arruwanmu da shi, nono yace zai saye fah, bayan shi mizaiyi muna? Nidai mutahi kar yace ya hwasa".

Tana gama maganar ta Kama hanya, ganin k'awar tata ta tafi yasa tabi bayanta da sauri.

Abdool kuwa dake kallonsu duk da baiji me suke fad'a yasan akansa ne, ganin suna zuwa yasa shi d'an d'aure fuska.

Suna zuwa yace "ke me kike fad'a mata, wato kikace a kalli idona ko"?

Cikin tsoro ta girgiza kai cikin siririyar murya irin ta Fulani " niya bance komi ba akanka".

K'ara d'aure fuska yayi yace "kinsha ba banji me kika fad'a ai naji komai kikace dan haka gun 'yan sanda zan kaiki"

Wayyo zanso kuga Laure kamar ta saki fitsari kunsan bafillace da tsoron d'an sanda, ba ita kad'ai ba har Delu saida ta tsorata jin an kira 'yan sanda, tuni suka fara da sun sani da basuzo inda yake.

Abdool ganin sunyi tuk'u tuk'u dariya suka bashi amma saiya danne yace.

"Nawa ne nonon"?

"Um...em.. Na nawa kakeso"? Suka had'a baki gurin tambayarsa.

D'an yatsina fuska yayi " nawane duka"?

Kallon juna zukayi sannan Delu tace " jikka talatin"

Maimata kalmar jikka yayi "meye jinka"? Ya tambaya yana kallon Laure.

Tsuru tai masa da ido dan batasan me zatace ba, suna hakane saiga wani nurse d'an garin ya taho gurin.

" Sir dama kanason nono"?

"Sosai nake shansa Jabir".

" Ayya ai bansani sir na d'auka bakasha da kullum na kawo maka shi, ke kutafi abinku zan kawo masa yanzu".

Ai su Laure dama kamar a k'aya suke tuni suka m'ike suna shirin d'ora nononsu.

"Aa bari nasiya tunda na tsaidasu" ya fad'a tare da mika musu 1k.

Delu CE ta ansa tare da zuba mishi "gashi mun gode, sai anjima" a lokaci d'aya ta fad'a tare da Dora nononsu sukabar gurin ba tare dajin ansa ba.

Jabir ne ya anshi nonon, shikam Abdool da kallon kawai ya bisu har suka bar gurin sannan ya kalli Jabir tare da cewa.

"Bari na shiga gida nad'an huta, idan an samu patient u should let me know".

 "yes sir".

Gidanda aka bashi na cikin quarters d'in asibiti ya shige, murmushi kawai yake idan ya tuna yarinyar komai nata abin burgewa a fili yace " beautiful and silly girl" can kuma yace "meke shirin faruwa danine ni *Abdulmajeed*"?

"Kai no impossible".

(Tau kai kad'ai ne dai) lol.


Su Laure kam suna barin gurin sunyi nisa tace " Delu yau Allah ya cecemu da wanga d'an binni mai glass yakaimu inda 'yan sanda aida munci bone".

"Wallahi ko zuwan wannan mutumi ta cecemu".

"Hmmm amma kam dan binni nada kuddi har nonon jikka biyar"?

" Aida gani kilama shina kayinsu diba kigani sabuwa dal".

"Amma kam ban komawa ta hanyagga kar atai ya ganmu ya had'amu da 'yan sanda".

"E walla mubi ta waccen hanya".


Haka dai sukayita tattaunawa har suka isa kasuwa........




^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^












Wasa-wasa tunanin yarinyar yayi tasiri a zuciyarsa shi yasa kullum daya gama aiki zai fito ya tsaya waje, amma ko mai kamarta bai tab'a bai gani, mamaki yakeyi meyasa ya damu da yaga yarinyar? Meyasa yake son sanin labarin yarinyar?

Ba Wanda zai ansa mishi amma tabbas zuciyarsa ta matsa mishi daya ganta yaji boyayyiyar damuwarta.......



 *A garin kilgori...*


Kamar kullum Ardo tare da Amininsa Malam Garba ne zaune daf da magrib yana jiran Ramlah ta kawomusu ruwan Alwala, numfasashinsa ne yaji yana sassarfa kamar zai d'auke sai k'ok'arin janyosa yake.

Malam Garba da suke fira da Amininsa jin yayi shiru, yasa shi d'agowa ya kalleshi, ganin halin da yake ciki yasa ya tashi da sauri tare da kamashi yace.

" subhanallah Ardo ciwon ne ya tashi" duk ya rikice ana haka saiga Laure ta fito ganin halinda Baffanta ya yake, sakin buta tayi cikin kuka ta isa gareshi tana "wayyo Baffa, meya sameka Baffa" kan jikinsa ta kwanta tana kuka.

Jayeta Malam Garba yayi "ba kuka zakiyi ba Laure, jeki kiro Hari muje asibiti".

Da gudu ta shiga gidan "ke tambad'add'ya minana kika shigoma mutane uwa kamun hauka".

" Iya Baffa ....." Ta kasa magana sai nuna mata k'ofar gidan take.

Ganin taki magana taja tsaki "ko minana babu ruwana can ta matsemuku ke dashi" ta bud'e baki zatayi magana.

"B'acemin da gani sauna" ta fad'a cikin tsawar da ya firgitata a guje ta fita, koda ta fita har Malam Garba ya kira mashin ana shirin d'ora Ardo.

"Ina Harin"?

" tana zuwa" kawai ta fad'a D'ora shi yayi shima ya hau tare da cewa su samesu a can.

Aiko suna wucewa ta bisu da gudu tana kuka, d'an clinic ne garesu a garin, ba kuma likita sai nurse kawai, ganin yanayinsa yasa sukace a wuce dashi Yabo kawai.


Koda ta iso har an samo mota, an sakashi, ai bata jira jin komai ba ta fad'a ciki driver yaja........




_manage pls friends_ 👏🏽 







💄 Meryerm Abdool 💄
[7/11, 4:04 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽




```WASIYYAR LUKMATUL HAKEEM GA D'ANSA ITACE :-```

*Ya kai d'ana kada kayi shirka ga Allah(kada ka had'ashi da wani a gurin bauta) domin shirka itace mafi munin zalunci, ka zamo mai biyayya ga iyaye, domin neman dacewa duniya da lahira.*

*Yakai d'ana ka tsaida sallah, kayi hak'uri da abinda ya sameka, kada ka nemi biyan buk'atarka ga mutane, kada kayi tafiya a cikin k'asa kana mai alfari da tak'ama, domin ubangiji bayason mutane masu alfari da tak'ama.*

*ka zamo mai tafiya cikin nutsuwa, kada ka zamo mai d'aga sautinka a gurin magana domin mafi munin sauti shine sautin jaki.*( _suratul Lukman_)

_Allah sarki, mutum mai mutum mai hikima kenan, ni dah keh dasu wance mun tab'a tunanin yima 'ya'yanmu wasiyya, tofa musani 'ya'ya amanace kuma abin tambayawa ne gaban ubangiji ranar gobe k'iyama._

Allah yasa mudace👏🏽






       📝 *Episode* 31--36





Suna isa aka k'arbesu I&E aka wuce dashi, haka Laure da Malam Garba suka bi gadon da aka d'orasa, sai hawaye kebin fuskarta ganin yadda numfashin Ardo ke zuwa yana dawowa gani take rasashi zasuyi, idan Ardo ya tafi ya barta shikenan batada sauran gata (Allah ne gatanki Laure).

Suna isa bakin k'ofa aka dakatar da su daga waje, anan reception suka zauna kan bench, sai addu'a take duk Wanda tazo bakinta nah nemama Kakan nata lafeeya, Malam Garba safa da marwa kawai yakeyi yana jiran tsammani tare da tausayawa aminin nasa, dan ciwon bai tab'a taso masa irin hakaba zuwa d'aya, saidai fatan samun lafia yake masa.

Taimakon gaggawa suka fara bashi ta hanyar saka masa oxygen, nurse Zainab ce ta fito, sanye da uniform irin na nurse, domin kiran Dr, Abdool saboda baya nan yaje gida yanzun, gashi ta kira wayarsa yana busy, da sauri ta fita, ganin ta yasa suka taso suna tambayarta jikinsa "da sauki" kawai tace ta fita.

Knocking tayi "yes" aka bata Umurnin shigowa, flat ne gidan mai one sitting room and 2bed room sai kitchen, irin dai na quarters d'innan, kwance yake kan 3seat idon sa lumshe yana waya, kan 1seat ta zauna tana k'arema gidan kallo dan shine first time d'inta shiga, komai neat sai k'amshi ke tashi kamar gidan mace.

"Hmm haba Hakeem duk matan da na gani ABU basu dama min lissafi ba, sai wannan 'yar fillon? Never."

Banji me Hakeem yace ba, murmushi yayi "any way yanzu inada bak'uwa, amma zan shigo end of week inshaa Allah".

'Yar dariya yayi tare da cewa "shegen kaya" sannan ya katse wayar.

"Yadai Zainab" ya fad'a ba tare daya bud'e idon ba.

Zainab da tunda taji ya ambaci 'yar fillo, k'irjinta yai mummuman bugawa sai zafi yake Mata.

Zainab itama Attachment takeyi daga Sokoto tazo, tunda taga Dr Majeed haka suke kiransa, taji ba Wanda takeso duk duniya kamarsa, tun daga lokacin take shige masa muddin yana hospital to tana tare dashi tanada kyau sosai itama siririyace mai matsakaicin tsayi kalar fatar tah bak'a CE amma irin mai kyallin nan.

Tayi mamakin yadda ya kira sunanta bah tareda yaga waye ba, kodai shima yana sonta neh? Waye zai ansamata wannan tambayan? Abun ko ba haka bane normally idan Abdool yaji muryanka sau biyu to yana noticing idan ya k'ara jinta.

Jin shiru nad'an mintuna ya sakashi mik'ewa zaune tare da ware manyan idonsa a Kanta.

Karaf ya idonta cikin nasa, cikin rawan murya tace "Sir we have a patient right now, he is in a very critical condition".

" OK am coming " kawai ya fad'a.

Mik'ewa tayi ta fice, binta yai da kallon "ko miye damuwarta oho!" Ya d'aga kafad'ar sah tare da tab'e baki.....




Sosai ya tausayawa tsohon dan yana jin jiki sosai, kusan 30mnt yayi a kansa kafin yayi nasarar daidaituwar numfashinsa, allurar jijiya yayi masa sannan yasa aka maidashi d'akin Hutu.

Fitowa yayi yana cire hand glove tare da Handkerchief ya fito dashi yana share zufa, dai2 lokacin Malam Garba ya iso inda yake "dofto ya ake ciki ya mai jikin"?

Murmushi yayi masa " kwantar da hankalinka Baba, ya samu sauki yanzu yana d'akin hutu muje muyi sallah koh"....

Laure data shige duniyar tunani bata masan Malam Garba ya tashi ba sai dubawa tayi bata ganshi ba d'agowa tayi ganin shi da Dr suna magana saidai bayansa kawai take gani, tashi tayi zuwa inda Suke.

Kaman ance ya juyo sukayi four eye cikin mamaki yace "you again"? Itakam tsoracewa tayi ganinsa, ita tama manta dashi.

Sunkuye kai tayi ba tare datace komai ba don batasan meyace ba, ganin idonta jajir alaman tasha kuka " me kikeyi anan."

Malam Garba ne yace "kasantane dofta"?

" eh to na tab'a ganinta anan garin tazo saida nono harma nasiya toh shine nake mamaki."

"Ayyo! Ai kakanta neh  baida lahiya."

K'ara kallonta yayi cikin ransa yace "dalilin kukan kenan"? A fili yace "OK, amma meyasa kuka taho da ita Baba"?

" wallahi d'anga an rud'e ne, ni bammasan ta shigo ba."

Wayarsa ya d'auko yayi kira " Zainab d'anzo reception zakiyimin wani aiki" ya fad'a tare da tsinke wayar.

Minti kad'an sai gata tazo "kije da yarinyar nan gidanku pls" kallonta tayi sannan tace "muje ko" tana mata murmushi.

Binta tayi sannan ta shima Abdool suka fita jin an fara kiran isha'i, bayan sun fito gida yaje ya d'akko bargo da filo ya kawoma Malam Garba sannan yaje yayi round ya wuce gida, har yanzu Ardo bai farka ba, saboda hadda alluran bacci a ciki.

Tana zaune k'asa sai raba ido take, Zainab ce ta fito daga kitchen abinci ta aje mata tare da ruwa da drink, "ya sunanki ta tambayeta"?

" Ramlah " ta fad'a a takaice.

"Wow nice name."

Itakam name kawai ta gane, da yake tadanyi makaranta zuwa primary four Iya Hari ta fidda ita.

Murmushi yake tayi mata, "ciki abinci sai kizo kiyi sallah" Zainab ta fad'a tare da shiga bedroom d'in ta, da yake gidan su 2 ne dashi tare da wata Christan.

Aiko tana shigewa Laure ta kama cin abinci hannu baka, sai dadi ke ratsa mata k'wak'walwa tana jinjina ma 'yan birni akan cin dad'i.

Cikin minti biyar ta gama dashi tsaf, cikin kayan gida Zainab ta fito ganin plate kawai tayi, smiling tayi sannan ta d'auke takai kitchen, kunyace ta kama Laure, amma saita share kada ta Renata(hoho su Laure aja girma) lol.

"Muje kiyi sallah" dakin tsaf2 ba wani tarkace gado ne sai wardrobe, toilet ta nuna mata "ruwa nanan a bocket kiyi wanka akwai ruwa a bota na alwala" nagode " ta fad'a tare da shigewa.

Girgiza kai Zainab tayi tare da cewa "kodai itace 'yar fillon"? Tab'e baki tayi tare da fitar mata da kaya, sannan ta shimfida mata dadduma.



^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^




*A k'auye...*


Iya Hari jin shiru har bayan isha ba Malam ba Laure yasa hankalinta yad'an d'aga, fita tayi ganin ba kowa yasa ta koma gida rikice ta d'auki mayafi, a waje taga wani yaro ta tambayesa nan yake shaida mata yagansu bakin asibiti an sakashi mota a mace.

K'ara rudewa tayi ta rasa inda zata saka Kanta, 'ya'yanta ta aikawa Lanti da Shatu, suma tuni suka iso a firgice.........




_love u friends_ ❤. 





💄Meryerm Abdool 💄
[7/13, 10:01 AM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽





```Manzon Allah (S.A.W) yana cewa:-```


_Baya shiga aljannah, maiyin annamimanci._


*Annamimanci yana nufin munafurci, munafurci yana nufin kayi maganan mutum koda abinda ka fada gaske ne abayan idonsa, Wanda ya kasance tozarci ne garesa.*

*a wannan zamanin da muke ciki abin ya zama ruwan dare saidai fatan Allah ya kawo mana sauki, ni dake dasu, muyi k'ok'ari mu duba yadda muke tafiyar da rayuwarmu ta yau da kullum shin mun kiyaye harshenmu ko kuwa Aa.*

Allah yasa mudace👏🏽




_Where r u? Rukie gwando, mlm ubaida, mino, qwlly, Maman Ramlah, Maman Nana, Sarat, Maman xee, sisto shafcy Abdool, oh kuyi hak'uri wadanda ban kira ba, mu had'u wani jik'on. ILYVM FROM D BUTTON OF MY❤_  








         📝 *Episode* 36--40



Suma rud'ewa sukayi ganin halinda mahaifiyarsu take ciki, barin ma Lanti taji, Shatu CE ta tambayeta cikin nutsuwa, nan ta gayamusu abinda wannan yaron ya fad'a mata, asibitin  garin sukaje suka tambayi inda akaje dashi nan sukai musu bayani, gida suka dawo suka fad'a mata sannan sukai mata sallama da niyyan gobe suyi asubanci.

Iya Hari sai k'ara tsinewa Laure take a nata ganin mugunta tayi Mata tak'i gayamata (oh wannan tsohuwa sai Allah).


B'angaren Abdool kuwa zuwa ten ya k'ara komawa asibiti koda yaje ya samu Ardo ya farka, nurse na cire mishi ruwan da aka saka mishi Malam Garba na gefensa ya d'aga mai filo ya jingina dashi, murmushi yayi tare da cewa.

"Sannu Baba jiki yayi kyau" lokaci d'aya Ardo yaji yaron ya kwanta mishi a ransa, Sam baida alaman wulak'anci ko d'aga kai irin Wanda wasu likitoci keyi (ai ba duka aka zama d'aya ba).


"Alhamdulilah naji sauk'i sosai docta, gashi numfashina ya daidaita, saidai k'arfin jikinne ya rage."

"Ayya shima zuwa gobe zakaji ka dawo normal" ya fad'a yana d'an dubashi, maganinda ya siyomai ya basu tare dayi musu saida safe, sauran ward d'in ya shiga ya dudduba patients.

Wani massenger asibitin ne ya kawo mishi wata leader "gashi Sir an samo dak'yar" ansa yayi sannan ya d'aga mishi hannu "well done  zaka iya tafiya" ya fad'a tare da wucewa, gidansu Zainab yaje kiranta a waya yayi.

Tana zaune tana duba wani littafin biology, Laure na gefe a k'asa bacci yayi gaba da ita, ba yadda Zainab batayi da ita ba, akan tahau kan seat tace k'asa ya isa, ita batamasan tayi bacci ba, dan atunaninta kallon da ta saka mata takeyi.

Wayarta ce tashiga Neman agaji "Dr Majeed" tace d'an mamaki a fuskarta, sai kuma tai smiling mai k'ayartarwa kamar tana gabanshi sannan ta d'aga.

"OK" kawai ta fad'a, tare da zura hijab d'in sallarta sai k'asa, dayake kayan bacci ne a jikinta, tana mamakin da Daren nan ya taho gidansu, smiling ta k'ara yi, gefen Laure ta kalla taga bacci yayi gaba da ita "sllly girl" ta fad'a sannan ta fice.

Yana jingine da motarsa ya rungume hannuwansa a k'irji, sanye da blue jean da shirt red ya d'ora lab court a sama, as usual glass dinsa na mak'ale a idonsa, duk kafin ta k'araso ta k'are masa kallo, itadai wannan gayen na tafiya da ita ba kad'an ba.

Sallama tayi masa ya ansa bayan sun gaisa ya Ciro Leda a mota ta bata "gashi ki bama yarinyar nan, dan naga da alama kayan jikinta ne kawai tazo dasu".

Ansa tayi tare da cewa "ai dama baka siyo ba dan nama bata wasu dana d'inka ban riga na saka ba, amma duk cikin k'ari ne an gode."

"Nine da godiya Zainab, thanks once again"

Murmushi tayi "wannan k'anwar taka akwaita da kunya, sam bata magana" (bugun ciki taji ya Suke).

Shima smiling yayi "zan tafi saida safe" ya shiga motarsa...

"Tau gudnyt Sir" ta fad'a tare da wucewa ciki cikin farinciki, tada Laure tayi takaita d'aki "da sannu zanyi nasara ishaa Allah (tunda kikace Allah kin gama komai Zee).



↑←↓→↑←↓→↑←↓→



Laure asuban fari ta tashi saboda sabo, kan gado ta ganta, sauka tayi a gefen gado taga Zainab kan dadduma, murmushi tayi mata " kin tashi cute Ramlah" itama murmushin tayi mata ba tare datayi magana ba.

"Je kiyi alwala kiyi sallah inaga time dinma yayi" girgiza mata kai tayi tare da murd'a k'ofan "am akwai brush a gefe mirror da MacLean sai kiyi" nanma kai ta d'aga mata dan bata fahimci me take nufi ba tadai ansa kawai.

Zuwa 8 Zainab ta shirya cikin uniform bayan sun gama breakfast itama Naomi fitowarta kenan "Sainab kayi bakone" yes Naome she's my sister ".

" wow so beautiful like u" dariya tace "as said always and u are beautiful too".

" ha ah Sainab don't said that again, see me se troubIe, Hmm look like fate-fate"

Dariya sosai Zainab tayi hadda kama ciki, Laure sai kallonsu take tana inama tanajin me suke cewa abin ya birgeta duk da bataji.

"U are too funny Nao, oya let go time is going".

" Hah! na true shaa"


Kallon Laure Zainab tayi "Ramlah zamu tafi asibiti, zan dawo naje dake idan Dr yai magana" narai-narai tayi da ido cikin sanyi tace "zan biku inga baffa".

D'an tunani tayi kada taje da ita kuma Dr baice ba, can dai ta koma d'aki, fitowa tayi tare da kayan Ramlah da wadanda Dr ya kawo mata da NATA wad'anda tazo dasu, da wadanda ta cire jiya " kinga wad'anda yayanki ya kawo maki" tana nuna mata kayan da Abdool ya kawo mata.

"Yayana"? ta fad'a cikin mamaki, " eh doctor da ya had'ani dake koba yayanki bane"?

Kad'a mata kai tayi alaman eh, "well to muje, aranta tace " koma ke meye tasa a sanadinki nad'an samu kusanci da Dr, hmm inasonka Dr Majeed" tai smiling mai tashi tare da lumshe ido....


Suna shiga ward d'in da Ardo yake da gudu ta isa garesa tare da rungumesa, yana zaune wani messenger ya kawo kayan breakfast da Abdool ya aiko ya kawo musu Malam Garba ya had'a mishi shayi yana sha, ajewa yayi tare da Shafa Kanta.

"Ramlatuna Ashe dake akazo, kinga wannan Dr mai karamci da mutunta mutane ko"?

Kai ta girgiza alaman eh " Baffa ya jikinka" na samu sauki Ramlatu ba in kemin ciwo yanzu".

"Allah ya k'ara sauki Baffana" nan malam Garba yayi ta tsokanarta ga Ardo nan bai tafi ya barta ba, haka tai ta cewa jiya tana kuka, fuskarta ta rufe tana murmushi dai2 nan su Zainab suka iso suka duba jikinsa sannan suka wuce suna mishi fatan samun sauki.

Nan Ramlah ta gayamai Alkhairin da tayi mata aiko kiransu yasa tayi yana ta kwararo musu addu'a da sanya Albarka "ba komai Baba yiwa Kaine" ta fad'a tana murmushi don taji dad'in addu'ar.....

Kusan 10 su Iya Hari suka iso Yabo, basu sha wahala ba gurin gane ward d'insu, suna isa Iya Hari sai masifa tahau Laure dashi ba tambayan Ardo jiki ba komai, sai ruwan bala'i hadda fad'in da mijinta ya mutu da sai tayi k'ararta (jimin k'arfin hali).


Ardo kam kwantawa kawai yayi ya rufe ido, yanajin zafi har cikin zuciyarta, wannan wace irin musiba ace ko gaidashi batayi ba ta hau masifa akan rashin dalili, a bak'on  wuri ma ba zata rage ba, kai Allah wadai da hali irin na Hari.

Itama Shatu tunda ta gaida mahaifinta da jiki, ta koma gefe tayi tagumi, ta tsani irin halin mahaifiyarta, musamman yadda take nuna tsana akan 'yar d'an uwanta saboda dalilinta mara tushe, Lanti murna take dan halinsu d'aya da uwar shiyasa tafi k'aunarta.

"Kedai Laure anyi muguwa mai bak'ar aniya jikar mayyu" Kanta sunkuye ranta sai suya yake, malam Garba sai tausar Hari yake amma kamar zugata yake.

Karaf a kunnen Abdool Wanda fitowarsa kenan, maimata maganar yayi "muguwa mai bak'ar Aniya, jikar mayu, wacce ce haka...."?.........






_love u friends_ 😍 








💄 Meryerm Abdool💄
[7/16, 10:50 AM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽 




```Annabi Muhammad (S.A.W) Yana cewa:-```


_Mafi sharrin mutane mai mummunan masauki a gurin Allah (ranar alk'iyama) shine wanda mutane suka guje masa saboda alfasharsa_ (hakkun mubeen.)

*nida ke dasu, ya kamata musan me muke furtawa, me muke aikata saboda mu tsira a ranar gobe k'iyama.*

Allah yasa mudace 👏🏽




      📝 *Episode* 41--45


Kansa ya danna cikin d'akin, da kallon wannan fa yabi Iya Hari dashi, ganin sai masifa take zubawa ita kad'ai, ga Laure kanta duke da alama ita ake mawa.

"To meye had'inta da ita, me tayi mata" ya tambayi Kansa a zuciyarsa.

Malam Garba ne ya kula da tsayuwarsa saboda kowa hankalinsa baya gun "Dr sannu da fitowa" ya fad'a.

Jin hakane yasa Ardo bude idonsa, a dai2 lokacin itama Laure ta d'ago nata idon kan nasa ta sauke dama ita yake kallo, ganin yadda fararen idanunta sukayi ja ranta a dagule.

Gyaran murya yayi sai lokacin Iya Hari tasan da zuwansa, d'an kame-kame ta farayi dan ba k'aramin kwarjini yayi mata ba tare dayin shiru.

"Haba Inna meye, haka a asibiti kike fa? Marar lafiya baya buk'atar damuwa, pls kud'an fita daga waje".

Jiki sanyaye suka fice aka barshi daga shi sai Ardo " kayi hank'uri don Allah docta, kasan mata sai a hankali" murmushi yayi masa.

"Ba komai Baba dama dan lafiyarka ne, ya kakejin yanayin jikinka yanzu"?

"Madallah jiki inajinshi dai2 babu inda kaimin ciyyo yanzu".

D'an duddubashi yayi kujera yaja ya zauna sannan yace "yanzu komai ya dawo normal saidai kana buk'atar rage tunane-tunane saboda bayan asthma har hypertension kanada (baiyi mamaki ba saboda jarabar Hari kad'ai ta isheshi) kuma yawan saka damuwa a zuciya ba naka bane pls ka kiyaye Baba kodan lafiyarka" ledar magani ya bashi.

"Ga wannan kayi amfani dashi" sannan yayi mishi bayanin yadda zaiyi amfani dasu.

"Yanzu zanyi discharge naku, zaku iya tafiya" ya fad'a tare da mik'ewa "Allah ya bida lafeeya.

" d'an nan to nawane kudin maganin"?

"Aa Baba ka barshi Allah dai ya baka lafia" godiya sosai Ardo ke kwarara masa yana jinsa kamar d'ansa "dama akwai sauran irin wad'annan mutanen Ashe" ya fad'a a ransa.

"Ba komai Baba, nima nagode da addu'arka Bari inyi magana dasu, yanaso ya tambayesa game da Laure da alak'arsu saidai yana ganin rashin dacewar haka toya zaiyi?.

Can wani tunani yazo mishi, smiling yayi tare da ficewa.



√√√√√√√√√√√√√√√√√√√√




"To shi kuma wanga wanena? Yaka korarmu iyii"?

Malam Garba yace " dofto na, mai kula da Ardo".

Zata k'ara magana sai gashi ya fito da kallo ya bita Wanda yake na raini, yawu ta had'iye, gefen Laure ya kalla ta rabe Kanta cikin cinyar ta, girgiza kai yayi alaman tausayi.

Shatu dariyace ta k'onota saidai ba damar yi ganin yadda uwarta ke raba ido alaman tsoro, dan Hari akwai masifa amma tsoro kamar farar kura, haka take tsoron Jauro kamar ranta.

"Dofto ya ake ciki"?Malam Garba ya tambayesa.

" zaku iya tafiya sai a kiyaye b'ata masa rai, sannan a ringa kula da shan maganin pls Ku kiyaye".

"Inshaa Allahu dakata" Iya Hari ta fad'a don Neman sulhu.

"Madallah dofto za'a kiyaye inshaa Allah, mungode da hidima fa, takardar magani fa? Wanda za'a siya".

" no ku barshi kawai na kai masa maganin, adai kula sosai".

"Kai madallah mun gode sosai Allah yayi Albarka, Bari intai in samo mota, Ku kutai ku kimtsa" yace dasu Shatu.

"Ameen, amma indai wannan Ku had'a kayanku zan kaiku, sai kumin magana idan kun shirya" ya fad'a tare da wucewa.

Da Zainab ya had'u yana daf da shiga office "morning Sir".

" morning Zainab, am kiyima Dr bakori magana yayi replaced d'ina zan fitane".

"OK Sir".

" koda maganan?" ganin ta mishi tsaye ta kashesa da ido.

"No" ta fad'a tare da wucewa, girgiza kai yayi tare da smiling ya Shafa sumarsa "ciwon mu iri d'aya ne, son maso wani" ya fad'a tare da shigewa office d'insa..........

Har k'ofar gida ya kaisu, wannan karon harda su Iya Hari sai godiya ake zubawa (su iya ansha A/c) lol.

Fura zallah Ardo yasa aka damo masa wacce tasha kindirmu damun kyale mod'a(ba'a saka ruwa a ciki) yaji dad'in hakan sosai dan dama Abdool ma'aboci shan furane da nono, nan waje suka zauna da Ardo suna d'an fira, yara kuwa sun zagaye mota sai shafata Suke sunga irin wacce basu saba gani ba, mata kuwa sai lek'e Suke ta Katanga, mutane sai kwararowa suke gaida Ardo da jiki.

Har ya shiga mota zai tafi sai ga Laure ta fito, nono ne da kwan zabi tace Ardo ya bata, tsayawa tayi ta k'asa magana Kanta k'asa, kallo ya k'are mata tsaf komai nata mai kyaune yanzun ma da take yarinya to inaga ta girma Hmmm.

Ganin tak'i magana ga lokaci na tafiya yasa yace "yadai da damuwa ne"?

" Um nagode sosai Allah ya saka da Alkhairi" still Kanta a k'asa itakam har yanzu tsaronsa takeyi da gaske.

"Hmm damefa"?

Bata ansa ba sai Ledar da ta Mik'a mishi " gashi ka kaima Aunty Zainab ina gaida ita sosai " duk cikin sanyayyiyar murya take maganar.

"Allah ya kiyaye" tana fad'a ta juya ba tare dataji me zaice ba, binta yayi da kallo harta shige, Shafa Kansa yayi tare da smiling harda lumshe ido (tofa me kenan Dr?)...........

Zainab taji dad'in kyautar Laure kuma ta nuna hakan a fuskarta wanda hakan ba k'aramin dad'i yayi ma Abdool ba, amma kuma k'asan ranta tanajin kishi sosai saboda zuwa yanzu ta gane itace dai 'yar fillon da yake magana, to amma meyasa ta damu da yawa batada tabbacin sonta yake ko tausayinta, dan tasan Abdool da tausayi a d'an zaman da sukayi yana d'aya daga cikin hayensa dake k'ara nutsata a k'aunarsa, amma kuma tanaji a jikin ta na Laure ya wuce tausayi to amma meye mafita saboda a gaskiya tana matuk'ar k'aunar sa tare da kishinsa (tofa Zee u say something oo).

"Sir pls idan zakaje Skk dis week zan bika ka ragen hanya"?

Saida yayi Jim sannan yace "OK".....


*End of week....*

Har k'ofar gidansu ya taho d'aukar ta, sanye ta fito cikin Arabian gown black tayi rolling da light blue d'in kashka, light make up tayi, tayi kyau ba k'arya.

Tunda ta fito ya bita da ido for d first time daya k'are mata kallo, tayi masa kyau amma kuma bata a zuciyarsa maganan gaskiya, dan ya dad'e da harbo jirginta musamman a d'an lokacin nan da take shige masa yasan sonsa takeyi, kuma har cikin ransa yana tausaya mata saboda yanzu shima yasan dafin so.

Tunda suka gaisa suka d'auki hanya bamai cewa uffan kowa da abinda yake sak'awa a ransa.

K'ira'a ya kunna musu ta *Shaik sudais* cikin suratul bak'ara, cikin kwarewa yake tuk'in yana bin karatun a hankali cikin daddad'ar muryarsa mai killing d'in Zainab, aiko lup tayi a kujera tanajin inama su couple ne, direct gidansu zasu wuce yanzu sai imagining takeyi a ranta tana murmushi( boyar Allah).

Batama san sun iso ba saida taji yana fad'in " ina muka nufa" cikin kasala tace.

"Mabera" gidane mai kyau madaidaici dan Baban ta yana da hali dai2 gwargwado, saboda ma'aikacin gwannati ne kuma ba laifi yanada salary, Zainab CE babba 'yarsa sai k'annenta 4, yana ajeta har zai ja mota tace "pls sir ka shigo Ku gaisa da Momy na".

"Oh! Sowie Zainab I'm urgent now but i promise zanzo when  I'm free".

Godiya tayi masa sannan yaja motarsa zuwa family house nasu.............





*na shiga busy, ga matsalan b3, kuci gaba da hak'uri Dani* one love friends❤👍🏻




💄 Meryerm Abdool💄
[7/17, 12:08 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽



*Annabi Muhammad (S.A.W) yana cewa:-*

_baya shiga aljannah mai yankewa(yana nufin mai yanke zumunci)_

*to 'yar uwa nidake dasu muyi k'ok'ari muga mun sada zumunci, musamman wanda yayi nisa, ba wai sai zumunci na jini, Aa harna musulunci saboda dukkan musulmi d'an uwan musulmi ne.*

Allah yasa mudace 👏🏽




```Double love belong 2 u, ina yinku 😍 momma (Ayshat garkuwa, neighbour(zee Yabour), indon kauye, Fashuna, swerry, Husna, ummyn yusrah,  momyn ihsan, Maman khadija, Seemaluv, Rufy, ummimi, eshat asym, ummu safwan, ummi garkuwa, zarah adami, maskurah, Ayshat hanwa, shukrah, ummihaneefa. Pls wad'anda ban fad'a su tsumayeni next page love u all dearest😍😍```





        📝 *Episode* 46--50



'Yan dubiya sai zuwa Suke ciki harda jauro anzo kamar mutumin kirki hadda wani duk'awa waishi a dole ladabi yake, Ardo dai kallonsa kawai yayi, yasan dai ba Wanda ya isa ya Aurar da Laure sai shi, ya barsu da shirmensu, 'yar ledar dubiya sai ciki yaje da ita ya bawa Iya Hari, dan ya k'asa ba Ardo.

Ita kuma mai kwadayi baki har kunne ta ansa tana shi masa Albarka, ita da Lanti sai rawar kai Suke, Shatu dai idone kawai nata, Laure ita harta manta dashi d'an kwana daya da basu had'u ba, data ganshi kamar ta hadi zuciya, shiko gogan naka dad'i kasheshi yaga rayuwarsa gata cikin kayan 'yan birni ji yake awa ya d'auke ta ya tafi, ba laifi shima yayi shigar arziki yau anzo dubiyar suruki cikin manyan kaya hadda hula, kamar abin arziki, saidai idonnan kam nanan kamar garwashi (chain! d'an kwaya baiyi ba, Allah ya karemu da zuri'armu Ameen).





Abdool yana isa b'angaren kakansa ya shige, yana zaune kamar kullum yana duba littafan musulunci, gaisawa sukayi cikin fara'a tare da tambayarsa yanayin aiki ya ansa da komai qlau, nan sukayi barkwancinsu da suka saba tare da tab'a hira, sannan ya shiga ciki ya gaidasu kamar kullum kakarsa fuska ba annuri suka gaisa, sannan ya dawo ya gayama Alhaji zai isa inda Hakeem dan zasuje Argungu ne.

"Madallah Hakeem yaron kirkine kullum sai yazo dubani ga dawainiya, Allah dai ya sanyama abotarku Albarka kuci gaba har abada ".

" Ameen Alhaji, ai indai Hakeem zaiyi abinda yafi haka" ya fad'a da murmushi dan yasan abokin nasa sarai akwai kirki matuk'a (shi akeso aboki na gari Allah yasa mudace).




~~~~~~~~~~~~~~~~~~






Hakeem ne kwance parlour gidansa sai bacci yake cikin kwanciyar hankali, Ac sai sanyaya sa takeyi, Abdool tsaye kansa ya kama k'ugu kamar mace yana tunanin kalar tasuwar da zai masa.

Saidai ya daddage yakai mishi bugu a baya, aiko sai gashi zaune yana Sosa bayan saboda yaji bugun sai raba ido yake kamar Wanda yayi k'arya.

Abdool kuwa dariya yake masa, dariyarce ta sanar da shi mai aikin, harara ya watsa masa "kaidai anyi mugu wallahi, mutum na baccinsa kazo ka tashesa fisabilillah".

"Kaiko idan ba wauta ba, meyasa ka kwanciya a parlour kuma k'ofa a bud'e salon a saceka ka bani aiki".

Dariya ya basa " imaging a saceni fa? Meye amfanin securitys d'in? A side ma waya kwanciyar bakai ba tun ten na shirya ina jiran ka, amma shiru kaman an aiki bawa garinsu" ya fad'a tare da K'ara da dalla mishi harara.

Siririyar dariya yayi tare kwanciya a seat hadda lumshe ido "hmm ka Bari kawai dude d things are much fa".

" Hmmm ba wani things lover boy, kadai kace love na nuk'urk'usarka period, wai ina labarin 'yar fillo taka"?

"Hmm! Wani bunch of surprise, ina last time da muke waya nace maka ina guest? Kakanta aka kawo emergency....." Nan dai ya bashi labarin duk abinda ya faru.

Hakeem hadda buga k'afa saboda dariyar k'eta "I told oo ur in love, lallai makashin maza, mazane ke kashesha, ina zanga Shukrah da Memzy alhakinsu ya fita.

" kaifa matsala dakai kenan! Ana maganan arziki kanata tsiya, ai kaima kasan ban musu walak'anci ba, an rabo lafiya wata kil ma sunyi aure, whatever dai yanzu meye way out"?

"Hmm kana sonta ka Aureta kawai".

" what! In aureta fa kace, kasan me kake fad'a kuwa?"

"Na sani mana, meye ribar soyayya idan ba aure?"

"Abinda nakeso ka gane, yarinya ce sosai inaga ko sa'ar Nihal batayi ba, sannan gata tsorona takeyi, abar maganar wannan ma ina matuk'ar tausayinta da alama tana cikin damuwa kamar yadda na gayamaka kullum cikin damuwa zaka ganta koda kuwa tana fara'a ne zaka tsinkayo damuwarta".


"Kaji Smart! Well tunda kakanta Nada saukin kai inaga ka fake da zuwa dubashi daganan sai kud'an saba, kaga kamai zaizo da sauk'i".

" wow good idea friend, hakan za'ayi".

"Hhhhhh toya maganan Zee kuma?"

"Kaji wata kuma ai ina gayamaka tare muka taho da ita nayi dropping din ta, hmm taso ta kaimi cikin gida na zille mata".

Dariya sosai yaba Hakeem yanayin yadda yayi maganan " kaji na 'yar fillo da Zainab".

"Fad'i ka k'ara ai gwandani nayi kasuwa kaifa?"

"Hhhh ba komai dai".

" amma kasan me? Ina tausayawa Zainab fa, saboda yanzu nasan rad'ad'in so".


"To ka auresu duka mana".

" caff! God forbid, bazan Iya ba".

"Nidai kaika Jiyo, kaga tashi muje time is going".

" oh zuwa Argungu is no big deal fa, nan da one hour mun isa, kuma ai bayau zamu dawo ba, yawwa ina sak'ona, dan bazan dawo tanan ba".

"Au abin 'yar hakane" Hakeem ya fad'a yana bashi wata k'aramar Leda, dama ya fito da kayansa shi kawai yake jira, ta motar Abdool suka tafi......

Tarba mai kyau suka samu daga kakannin nasa na Uwa, da Kawunsa, gaisawa sukayi cikin fara'ar ganin jikan nasu, bayan sun hutane Abdool ya d'auki Hakeem ya zaga dashi gari, dan yasan garin sosai, kamar su gidan Al'adu, matan fada, mala, grand fishing, da dai sauransu basu suka dawo ba sai magrib, bayan sunyi sallah kuwa suka dasa firar yaushe rabo da kakannin NASA.....


Washe gari ma sake fita sukayi dan garin ya burge Hakeem sosai( ai dole ne Hakeem, Argungu garin nabame kowa sarki, gari mai ni'ima da dinbin tarihi, garin sarautar gargajiya data zamani, kabawa ikon Allah Ku adda ruwan nan) lolz.

Basu suka baro Argungu ba sai bayan la'asar tare da tsarabarsu ta kifi.

Anan yabo suka rabu Hakeem ya shiga motar baya zuwa Skk, kamar yadda Abdool yace hakan yayi akayi.

Wanka kawai yayi ya canja kaya, ya d'auki hanya kilgori dan ganin mintin zuciyarsa...........


  




_manage pls_ 😇 




💄Meryerm Abdool💄
[7/18, 10:05 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽



```#one love # just for u guys,😍 Aunty kausar, Aunty khady, Suhana, Ummu khady, sisin Mama, fateey nashuka, Meryerm mukhtar, Lemancykhan, Salma(momma), samrah, Biebie die, biebie, sumyn bash, Rafe'at, Ayshat Yabour, waleeda wazir, deeja wazir, beebah wadata, Nana fa'ad, miss Hafsy, miss feedy. Heart u guy, ❤Allah yasa ban manta kowa ba😢```








    📝 *Episode* 51--55




"Ke bakiga yadda nirrud'e ba jikina sai rawa yake, awa in saki hitsari cikin wando, da nigga nai".

" hhhh hhhhhh dama nasan haka za'ayi ainayi mamaki da nigga ya dawo daku daga asibiti, ahe dama likita na? Hi yassa ni matsu mu had'u in ha labari".

"Yo nima bansan likita na ba, na aza d'an sanda ahe likita na, keni koda munka shiga Yabo hankali na bai tare dani kwata-kwata bangane komai ba saida nigganai nittuna ai nan niya na munka ganehi ranar".

" toya kunka k'are miya hwada ma su Ardo?" 

"Ke walle bansani ba danni gidan wata 'yar binni ya kaini nikkwana, Ashe sunada kirki kala biyu ta bani irin na binni, kuma tabbani abincinsu mai dad'i ke shima yanada kirki bakiga hidimadda yayima su Baffa b.........." Nan dai taci gaba da zuba kamar 'ya'yan kanya dan Laure badai surutu ba idan ta had'u da wadda ta saba, dan ma a gida batada abokin yine sai Ardo, ga tambaya amma ai dole fillo akwai tambaya. Lolz

 

Tun daga nesa ya tsinkayo su da tuluna akai, da alama firar da Suke tayi musu dad'i sai kwasar dariya Laure takeyi, rungume hannuwa yayi a k'irji ya jingina da motarsa sai faman kallonta yakeyi, Ashe tana fira haka? Ashe tana dariya haka? Yake tambayan Kansa.

Dan ba k'aramin kyau tayi mishi ba yadda take dariyar gwanin sha'awa komai tayi burgesa takeyi, komai nata unique ne (oh Dr ka fad'a da yawa fa).

Har sukazo suka wuceshi sam basu kula dashi ba, da yake suna right shikuma yana left.

"Hmmm ki bari Abukkiyata Jauro ya dameni ya hani jin dad'i kamar nid'ai a macce".

" ai bakiga komi ba kwana gudan da kikayi bakyanan baki ga zarya ba wai sai in hwada mishi ina kikaje wai yaje gidan ba kowa, seda niyyi ta yimai rantsuwa sannan ya yadda".

Ta bud'e baki zatayi magana kenan.... " 'yan fullo masu tulu aka" ya fad'a cikin daga murya saboda su jiyoshi ai kuwa sunji, k'irjinta ne ya harba, dan ta gane mai muryar tome yazoyi kuma? Ta tambayi Kanta.

Itakam Delu tuni ta jiya ganin mai kiransu tana ganin shine ta tab'o Laure datak'i juyowa "Laure mutumunki ne hwa".


Takowa yayi har inda Suke, cikin girmamawa suka gaidashi, tuni bakin surutu ya d'inke kamar ruwa ya cita " daga ina haka?" Delu ce ta ansa "daga rahi debo ruwa".

" Baba na nan?" Ya fad'a yana kallon Laure, data wani takure saboda bako hijab sai wani siririn mayafi, duk ta jita wani iri dan dama bata saba fita hakan ba, yauma bala'in Hari ne ya fitar da ita ba shiri.

"Um yana nan" ta ansa kai tsaye.

Kowama yayi gurin motarsa yayin da su kuma suka nufi gida, saida yaga sun bace ma ganinsa sannan yaja motarsa.


Yana zaune kamar kullum yana duba littafansa na addini, jin tsayuwar mota yasa ya d'ago, yayi mamakin ganinsa, amma bai nuna a fuska ba, da fara'a ya taresa, bayan sun gaisa, ya shiga ciki yasa. Aka kawo masa fura wacce taji damu da nono fara k'al, yasha sosai dan dama favorite d'insa ce.

Booth yaje ya fito da kayan fruits shake a Leda, sannan ya d'akko wannan ledar sak'on daya ansa gun Hakeem.

"Baba dama maganine na kawo maka wannan in heeler ce da kaji alaman asthma ka shaka ta baki ta saurin saukar da ita, wad'annan kuma magungunan hawan jini ne...." Nan dai yayi mishi bayani yadda zaiyi amfani dasu, godiya Sosai Ardo yayi tare da sanya masa Albarka, shidai yana ganin hankalin yaron sosai har yana raya Wani tunani a ransa game dashi.

Cikin firarsu ne yake cewa yanayin garin na matuk'ar burgeshi, zaiso yad'an zaga garin.

"To ai Bari in kira Ramlatuna ta d'an nuna maka gari, kafin magriba kad'an ga wasu guraren" zanso kuga zuciyar Abdool farincikin bai misaltuwa, dama haka yakeso.




••••••••••••••••••••••••••••••••••••



A k'afa suka fito tana gaba yana biye da ita, suna tafe kamar gumaka ba mai cewa uffan, ja yayi ya tsaya yak'i tafiya, saida tayi d'an nisa taji alaman ba'a binda aiko tana juyowa ta gansa tsaye abinsa.

Dawowa tayi inda yake ba tare da tayi magana ba, ganin tsayuwar bamai k'arewa bace ga marece na k'ara yi yasa yace "a haka zaki nunan garin muna tafe kamar kurame? Idan ba zakiyi magana ba mu koma kawai" ya fad'a tare da had'a rai.

Rau-rau tayi da ido tare da turo baki "yo ai Kaina baka dariya, sai had'e huska, ni tsoronka nake".

Dariya sosai ta bashi yanayin yadda take maganar, aiko dariya yayi hadda tafa hannu, itakam tsuru tayi tana kallonsa, saida yayi mai isarsa sannan yace.

"Wama sunanki"?

" Laure" ta fad'a a tak'aice.

"Aa ba shine sunanki ba, ni bazan ringa kiran ki dashi Wanda Ardo ke kiranki dashi nike nufi".

Saida tayi murmushi dan ita Kanta tafison sunan " Ramlatuna " ta fad'a.

Shima murmushi yayi yace "yawwa shi amma Ramlah luv zan ringa kiranki kinaso ko?"

D'aga masa kai tayi dan ita batasan me luv din yake nufi ba "yawwa zamu zama abokai daga yau kin yarda?"

Namma kai ta d'aga mishi "daga yau mun zama friend zakina ringa bani labari?"

"Au wallah zan baka, badai kanaso ba?"

"Inaso sosai".


Haka suka tafi suna hira tana ta bashi labarai barkatai shidai biye mata kawai yakeyi duk inda sukaje tana masa bayanin gurin, aiko yasha labarai sai mamaki yake Ashe haka take da surutu, ada bayason mutum mai surutu shiyasa yake kwaban Nihal saboda itama akwai surutu, amma surutun Laure burgesa yayi duk da kuwa mafi yawa duk shirme ne sa soki burutsu.

Sai ana daf da magarib suka dawo ransa fal farinciki ji yake kamar kada su rabu, shikam Allah ya d'ora masa k'aunar Ramlah, anan yayi magrib tare da Ardo bayan sun dawo ya wuce, yana tafe yana tuk'i tunaninta kawai yakeyi yana murmushi a gaskiya dole ya sanya ranar yau a cikin tarihinsa dan babbace a gurin sa yayi enjoyed nata ba kad'an ba....


Sannu-sannu shak'uwa mai k'arfi ta shiga a tsakaninsu duk da har yanzu Ramlah batasan meye so ba, amma tanijin da Abdool a ranta. Duk k'arshen sati yake zuwa, suje su zaga gari daga nan su dire rafi, inda yake koya mata kara2, dayake tw bashi labarin tayi primary har 4 iya Hari ta fidda ita, zuwa yanzu ba abinda bai Sani ba game da ita da irin musgunawar da Iya Hari take mata, yanajin tausayinta sosai k'aramar yarinya da ita amma tasan wahalar rayuwa, duk abinnan da akeyi Jauro baida labari, saboda irin ranar bai  zama gari suna jeji gurin farauta (kome zai faru idan ya sani? Allah masani).

Iya Hari kuwa cewa tayi dama daga ganin wannan likitan dan iskane yana fama da gilashi awa dan daudu, yazo yaba malam kud'i ya saida mutunci jikarsa, sannan tace "yo dama ai zani ce ta cimma muje dama can tsohuwar sana'arta ce" duk ta yadda ta yadda ta debo musu ciki saidai suk'arasa ita da makwad'aicin kakanta.

Haka taita sakin magana ba dad'in ji, sudai kunnensu kawai suka dad'e, suka barta da Allahu.

B'angaren Zainab kuwa ta d'age da gayawa Allah buk'atarta ba dare, ba rana, shikam Abdool tausayi take nashi, dan yasan dafin so, shiyasa yake d'an sake mata fuska kota samu sassauci (Allah sarki Zee, ba komai kina tare da Allah.)...........
.







💄Meryerm Abdool💄
[7/20, 9:59 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽



😭😭 *kulli nafsin za'ik'atil maut(each and every soul should test d bitter of dead) may ur gentle soul rest in perfect peace, may jannatil firdous be ur final home sisto Hauwa'u (Aunty 'yar gande) may Allah bless ur children's, Ameen👏🏽*





 
       📝 *Episode* 56--60






Kwatsam aka samu wani munafiki ya gayama Jauro, aiko kuzo kuga kunfar baki, kaman yayi hauka wai Laure da wani, gidansu yayi sa'a kuwa Ardo bayanan, nan ya hau Iya Hari da masefa ai duk laifinta ne da take bari tana fita amma zaiyi maganin ko wane shegen ne.

Bud'ar bakinta sai cewa tayi "Yo ai ba laihinshi naba, ita ka biye mai kuma ai da sanin malam shiya d'aure Musu gindi wainan gari taka nuna mai."

Cikin muryan 'yan tasha "wai wane d'an kazar uba ne?" 

"Hehehe likitan Malam na, yana kawo musu mai dad'i da mask'i ai dole baki ya mutu(kamar bada ita ake ci ba).

" to nidai ko shi'a asibiti ba likita ba billahillazi ya kiyayi had'uwarmu, bamai kyauta ba aha" sannan ya fita yana huci kamar zaki.

Laure dake gefe tunda ya shigo gidan batace uffan ba, hasalima ko inda yake bata kalla ba saboda tsabar takaici, yanzu idan ba rashin tunani ba taya za'ace gardi kamar Jauro ya ringa shigowa mutane gida kamar gidansu, siririn tsaki taja, Wanda yayi dai-dai da maganar Iya Hari.

"To isasshiya, tsigaggga, sai kitahi ki bashi hak'uri, ke wani lahe kamar d'iyar arziki, shegiya me bak'ar aniya."

Itakam bataga dalilin bashi hak'uri ba, koda kuwa an bada ita gareshi balle ba'a bayar ba...."kin tashi kin tafi kosai nayi mid'imid'i dake anan niya" iya Hari ta katse mata tunani aiko tana shirin d'aukar muciya, aiko a guje tayi soro gidan ba shiri.

Yana tsaye yana jiran fitowarta, dama yasan zata fiton dole, had'e girar sama da k'asa tayi, murmushi yayi yace "haba gimbiyata mi'a na huskar shanu, sakin ran mana".

Harara ta balla mai " haba Jauro missa zaka yimin haka? kasan shi waye gareni?"

"To meye shidin bayan masoyinki".

Dariyar takaici tayi dama hakan ya zamo gaskiya da taji dad'i " haka ar tunanin ka dama? Mizaiyi dani 'yar k'auye? Kabar wanga tunani ma, iyaka dashi mutunci sai kara2 da yake koyamin".

Haka dai ya tafi bawai dan ya yarda ba, sai dai baison ranta ya b'aci, shiyasa ya yadda ya tafi, tare da shan zasu had'u wata rana.



**************************



Zaune Suke kamar kullum bakin rafi ga littafi da Biro gefensu dan yanzu har sun fara koyon, sai kuma k'awa'idi da ka'ida na musulunci, dan har nan Suke tab'awa, bayan ya gama koyamatasu, ta maimaita sannan yace.

"Gud gul, yanzu sai mu koma karatunmu na wancen satin ina fatar kin hadda CE".

"Eh mana, Bari ma kaji" ta fad'a tare da mik'a mishi littafin, tiryen-tiryen ta kawo su ba gyara.

Jinjina yayi mata da hannun tare da tafa mata, yana jinjina saurin ganewa irin nata, da an gayamata abu ta haddace irin su ne gifted by nature, amma anaso a kashe mata dama ga banza.

"Aboki my glass?"

Saida yayi dariya saboda sunan da take kiransa dashi "um Ramlah luv, ya akayi".

" kacce love na nuhin soyayya ko?"

Cikin mamaki yace "eh meya faru?"

"To naji kana kemin Ramlah luv, yana nufin Ramlah soyayya kenan, ma'anar sunana soyayya kenan?"

Saida yayi Jim yama rasa me zaice mata gashi ta kifeshi da ido "Aa nadai had'a sunan naki da Kalmar soyayya, kinga kenan ke soyayyar kowa ce saboda kinada ganewa sosai" ya k'arashe tare da yi mata alaman wasa, saboda ta shanshance da zancen.

Aiko dariya tahau nan sukaci gaba da karatunsu cikin nishadi(kara2 yafi jiga idan ana had'awa da wasa)lol.

"Kan ubancen yau za'ayi kazar uban nan niya" sukaji an fad'a daga sama, a tare suka juya dan ganin wane hatsabibin ne.

Kallon wannan fa Abdool ya bishi dashi, Jauro kuwa sandar da ke wuyansa ya d'aga da niyyan kai mishi bugu.

Da hannu d'aya Abdool ya rik'eta tamau yadda ko motsata Jauro bazai iya yi ba, yanzu kam da kallon kama renani yake binsa, Laure ce ta mik'e a fusace cikin fulatanci take magana.

"Haba Jauro Wanga wace irin haukata? Na hidi maka mia tsakanina dashi, wai shin imma masoyina ne, mi zakayi? Hala an baka nina?"

Ba tare daya bata ansa ba, ya dawo da kallon sa ga Abdool.

Cikin muryan 'yan tasha, yana juye baki yake magana "Hai kad'o ina gargad'inka, daga hita hanyar Laure, da duk Ahalin ard'o idan ba haka ba Hmmm".

"Kai kuma waye kai? Kuma meka isa kayimin" Abdool ya fad'a cikin gadara da binsa da kallon renin hankali.

"au bata hwadama ni'a wa ba, toni zan fad'a maka, nina mijinda zata Aura, nina uban d'iyanta, kuma kiyayi had'uwarmu ta gaba" yana gama fad'i yaja sandarsa ya kama gabansa.

Abdool dake tsaye kamar Wanda aka dasa, haka yaji zancen kamar saukar aradu, cikin jarumta da dakewa ya tattaro sauran k'arfin halinsa, ya maida kallonsa ga Laure dake tsaye tana hawaye.

Idan ka kallesa zaka tsinkayo kishi da bacin rai kwance a fuskarsa, amma da yake akwai k'arancin shekaru gareta bata fahimci komai ba.

"Abinda ya fad'a gaske ne?" Tayi ya tambayeta, girgiza kai tayi "ba haka bane hasalima dagashi sai Iya Hari suke zancen, Baffa baice komai ba...." Nan tayi mishi bayani sosai, ya d'an samu nutsuwa amma kuma jin hali irin na Jauro yasa hankalinsa yad'an tashi, dan yana tsaoron yaje yayi mata illah, amma tunda yana sonta yasan kila ba zaiyi mata komai ba.

Shikam ko batason Laure bazaiso a aura mata wannan shashashan ba, balle kuma son nata yake, ganin hankalinta bai kwanta yasa yace suje kawai an k'are kara2.

Sallama yayi Ard'o, bayan sun dan tattauna, sannan ya gaya mishi zaije gida Hutu, fatar Alkhairi yayi mishi "don Allah in kaje ka gaidasu sosai, inji ka gayama mutuniyar taka?"

"Aa Baba".

"Ato bari tazo kuyi sallama, Ramlatuna karatu zai tsaya kenan." Ya fad'a yana murmushi tare da shigewa ciki.

Da zabi da k'wayak'wayi ta fito wai inji Baffa "aboki mai glass hala ina zakana nijji Baffa yace wai ka kai Musu?".

"Gurin Mamana zanje Ramlah luv".

"La ina Maman taka take hala?"

"Can da nisa kinsan Kaduna?"

Girgiza kai tayi cikin mamaki "dama ba Yabo an garinku ba?"

"Eh".

"To nima zan biyoka inda mamar ka".

Smiling yayi " kina son zuwa inda Mamana?"

Da sauri ta girgiza mishi kai alaman eh.

"To inshaa Allah, zanje dake, idan zan koma kinji".

" Aa nidai katahi dani yanzu" ta fad'a cikin shagwaba.

"Oh friend yaushe kika iya rigima, kiyi hak'uri kinji zanje dake next time" haka ya lallab'ata har saida ta hak'uri sannan ya tafi, bye ta ringa yi mishi har saida ya bacema ganinta sannan ta share hawayen da suka zubo mata, tabbas zatayi missing d'insa.

Tafe yake yana tuk'i amma yana tuno maganganun Jauro, "Nina mijinta, nima uban d'iyanta".

Da k'arfi ya daki sitiyari  " no it can't happen ever".................













💄Meryerm Abdool💄
[7/22, 6:46 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽



```Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi yana cewa:-```

_Hak'ik'a Allah mad'aukakin sarki baya duba zuwa ga suffofin jikinku ko dukiyoyinku, saidai yana duba zuwa ga zukatanku da ayukanku._


*kyawu da dukiya, ba zasu taba zama guarantee na shiga aljannah, gareni, gareki, garesu ba, tsarkakakkiyar zuciya da kyawun hali, shine kad'ai zai kwacemu a gun Allah ranar gobe k'iyama, nidake dasu mu guji rud'in da sharrin kyawun halitta dana dukiya, mu tsarkake zukatanmu, muyi k'ok'ari mu gyara tsakaninmu da mahaliccinmu domin goben mu, duniya labari ce, komin dad'ewa zamu barta, Allah yasa mudace da rahamarsa👏🏽*





  


    📝 *Episode* 61--65



A yau ne su Zainab suka kammala attachment d'insu, k'warya-k'waryar walima mai gari yasa aka had'a musu tare da taimakon likitocin asibitin, sun yaba musu tare da jinjina musu akan k'ok'arin da sukayi, tare dayi musu fatar Alkhairi.

A tare suka wuce Sokoto da Abdool, dan shima ya d'auki Hutu gobe sai wuce Kaduna, bayan ya sauketa fitowa yayi ya fito mata da kayanta dake booth, ita kuma gida ta shiga ta kira gate man da driver domin su shigo mata da kayan ciki, ta samu har ya shiga motar yana shirin tafiya, gurin k'ofar ta sunkuya cikin marairaicewa.

"Sir pls ka tsaya Ku gaisa da Momyna har nayi mata magana".

" Oh! No Zainab ki bari next time...." Katsesa tayi.

"Pls Sir kai kayi alk'awari fa" ba yanda zaiyi, haka ya fito dole, a parlour Dadynta ta saukeshi, ga kayan motsa baki an shirya kamar hauka,  ciki ta shiga ta kira Mamanta, cikin girmamawa suka gaisa, yau dai taga Dr Abdulmajeed d'inda take shan labarinsa gurin Zainab, itama ta yaba sosai da yaron,  godiya tayi mai da irin kulawar da yake bawa 'yarta, tare dayi musu fatar Alkhairi, shikam kunya yaji kardai Maman tasan Zainab na sonsa.

Bayan fitar haka k'anninta sukayi ta zuwa suna suna gaishesa kudi ya basu shima dak'ar suka ansa sunayi masa godiya ya yaba da tarbiyar yaran "Sir kaci wani Abu mana" ruwa kawai yasa yace zai wuce, ba taso hakan ba amma ba yanda zatayi, dan ita idan son ranta ne, su tabbata haka har abada, har mota ta rakashi.

Wani ring ta Ciro a yatsarta ta bashi "wannan d'in na meye Zainab"?

Murmushi tayi tasan yasan tana sonsa, saidai koda sonsa zaiyi ajalinta ba zata tab'a fad'a masa ba " Sir ka rik'eshi a gunka, idan ka kalla ka tuna dani, pls Sir kada manta dani".

Sosai ta bashi tausayi, ansa yayi yasa a k'aramin yatsarsa, tare dayi mata murmushi "bazan tab'a mantaki ba Zainab ki saka wannan a ranki".

Taji dad'i har k'ashinta koda ba har ransa ya fad'i zancen ba, itakam ya faranta mata, shikam yayi hakane kawai dan ya kwantar mata da hankali.

Saida ta daina hango motarsa sannan ta juya gida cikin farinciki harda tsallenta na murna (hohoho! So manya).




××××××××××××××××××××××



*Washe gari*



8:00am sukayi sallama da mutan Sokoto suka d'auki hanyar Kaduna garin gwanma, wannan k'aron Hakeem ne yaja motar sai sharara gudu yake, yayin da Abdool ya kebin k'ira'ar da ke tashi a cikin suratul Maryam, idonsa a lumshe.

12:00pm suka isa, gidansu Abdool suka sauka, sun samu Maamii ta tarbesu da tsararran girkinta ko office bata fita ba saboda d'okin dawowar Son d'inta ita Kanta tasan tayi missing d'insa sosai, su Abj ma sai murna dawowar Yaya Abdool Suke, suna nanik'e dashi suna mishi surutu, saida sukayi dam, sukayi fresh up, sannan Hakeem yayi musu sallama, da motar Abdool ya wuce gida, idan yaje ya dawo da ita.....

Hutun one month sukayi sannan sukayi shirin komawa, a wata d'ayan ba k'aramin dad'i hutun yayi ma Abdool ba duk kuwa da tunanin Ramlah na mak'ale a zuciyarsa, sukanyi waya da Zainab time to time, sai yaji inama da Ramlah ne, sai yanzu yakejin haushin rashin barma Ardo waya da baiyi ba, Aida sun rik'a gaisawa da sahibarsa.

Saura kwana uku su koma suna zaune da Maamii suna hira dan a duniya bashida abokiyar hira da shawara kamar ita, har suka gangaro kan hirar Ramlah.

"Yawwa maganar yarinyar nan da muka fara".

"To ai banji daga gareka bane Son, tunda ka dawo bakace komai ba".

Shafa Kansa yayi " Eh wlh Maamii kamar yadda na gayamiki, yarinyar na cikin k'unci, ba K'aramin wahala takesha gun Kakarta ba, gashi shi kakan nata bamai magana bane, wani abin tausayin ma very young inaga iyakarta in tayi Nihal" ya k'ara she cikin pity face.

Itama tausayi kwance a fuskarta tace "toya kake ganin zamu iya taimaka mata ne?"

"Eh ni a tunani na in nemi kakanta ya bani ita na kawo ta nan gurin ki, sai a sakata makaranta in fact dai ta dawo hannun mu sai dai takai musu ziyara amma me kika gani".

"Eh to Zamanta anan d'in ba matsala a ciki amma kana ganin iyayenta zasu baka ita haka nan daga had'uwar asibiti?"

D'an jim yayi shima dan gaskiya maganar abar dubawa ce "hakane Maamii amma zan gwada na gani idan zai yuyu".

"Ina ne garinsu naji kace ba anan Yabon bane?"

"Eh nan kusa dasu ne wani k'auye Kilgori".

"Kilgori" ta maimaita haka taji kamar ta tab'a jin sunan garin saidai ta manta ina taji, sharewa tayi nan dai sukaci gaba da tattaunawa akan lamarin..

Tsaraba sosai yayi mata na suturu dogayen riguna da d'inkuna hijabai hadda takalma da kayan rubuta da kara2 hadda Zainab saida yayi ma tsaraba dasu Ardo su Alhaji, kai har mutanen Argungu anyi ma, Maamii ma ta bada nata.

Ranar da suka dawo bayan ya huta ya bawa su alhaji tsarabarsu, a ranar ya wuce Yabo, zainab ma a tsaitsaye yaje, danko ciki bai shiga ba, mutan Yabo sunyi farincikin dawowar dan ba k'aramin k'ok'ari yake a asibitin ba, mutum zaizo bako asi ya dubasa kuma ya siyamai magani, shiyasa sukejin dad'in sa, suma Suke kawo masa kaya irin nasu na k'auye, nono, kwai, har kaji da zabi.

Da sassafe yaje kilgori, Laure tafi kowa murnar dawowarsa, sai murmushi take, ganin tayi ya kara kyau da gayu, hadda cewa "iyye d'an binni d'an gayu dai" dariya ma ta bashi cikin ranshi yace "Ramlah kuruciya ho".

Sunyi murna da godiya da tsarabar da yayi musu, yaji dad'in yadda suka yaba, bayan ya tafi Iya Hari, kwace kayan tayi ta cirema Lanti da Shatu kala d'aya 2 hadda hijab, wai ai wannan salon munafurci ne menayi mata kaya kaman ya ganta a tsumma, wannan kayan kamar na Aure, imma sonta yake yayi k'arya dan bazata bashi ba( ni kuma nace tunda ke zaki bada ita ba).

Laure kam a ranta tace mi hikai da 'yar k'auye duk matan bunni.

Cikin kala ukun da suka rage ta d'auki d'aya ta kaima aminiyarta Delu, sai murna take da sanya Albarka.

"Nidai Laure anya d'an bunnin nan ba sonki yake ba?"

Murmushi k'arfin hali tayi tace "banda ke da abinki Delu mi yakai Dani, ai wutsiyar Rak'umi, tayima k'asa nisa".

" Hmmm abokiyata ai ba daganan take".

"Kega bar wagga zance, d'auko wata" murmushi kawai tayi sannan suka canja hira.

B'angaren Jauro kuwa ya lashi takobin sai yaga baya ga Abdool muddin yaci gaba da shige  hanci...............



( _tofa gamu gani, wai ansa munafiki bikon aure_😏 )









💄 Meryerm Abdool💄
[7/23, 7:02 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽







      📝 *Episode* 66--70





*life goes on....*



Zuwa yanzu Laure, ta fahimci abubuwa da dama game da karatun da sukeyi, both Islam and western, har rubuta ta iya, bak'ak'e da wasulla tana banbance su, har hadda izo biyu tayi a gunsa, a tak'aice ba k'aramar rawa Abdool ya taka a gun Ramlah ba, wani sa'in har Delu yake had'awa idan taje gurinsu, dan yanzu anan inuwar gidansu suke zama, da yake Laure ta gayama Ardo abinda Jauro yayi, shiyasa yace su rik'a zama nan, dan yasan kad'an a cikin aikin mahaukacin ya kwaso shegu irinsa suje suyi mashi illah.

Shikam Abdool baiso hakan ba, yaso su k'ara had'uwa da Jauro danya banbance masa aya da tsakuwa, a bangaren Jauro kuwa zuwanshi biyu bai samesu ba anan ba tare da rundunarsa kamar yadda Ardo ya tsammata, yana ganin basu nan yayi wani ihu irin na 'yan iska.

"Aradun Allah ya tsorata, saini Jauro mai sa maza su sheka da gudu, dan banza yana tsoron uwarshi ta haihi wani ba shiba" haka yayi ta cika baki 'yan korensa naci na k'ara fashe mishi kai.....

Yauma bayan sun gama kara2 zai wuce saiga Laure da leda waiya kaima Aunty Zainab, murmushi yayi tare da rik'e baki "ayya Ramlah luv baki d'oran aikin da yafi k'arfina ba yau kuwa?"

K'walalo ido waje tayi "Aboki mai glass kaima kana kyuya irin ta yara ashe?"

Dariya ta bashi yadda tayi maganar "Waya gayamiki kyuya ce, Zainab d'in ce batanan ai".

" to ina taje?"

"Tana Sokoto gidansu".

"Laa itama ba Yabo take ba kamar kaiya?"

"Um itama Bautar k'asa tazo anan kamar ni, kuma ta k'are nata tun tuni".

"Amma shina baka hwadamin ba, kuma in nicce INA gaisheta saika ke zataji" ta fad'a tana mishi kallon tuhuma.

"Oh my gosh! Mantawa nayi, amma fa ina gayamata gaisuwarki".

"A ina?"

"Ta waya mana, ko in kira maki itane?"

Washe baki tayi "eh inaso kirata".
 
Wayarsa ya Ciro ya danna mata Kira, ring 2 ta d'auka, bayan sun gaisa ya had'ata da Laure sannan yaje inda Ardo dake zaune yana kallon rigimarsu yana murmushi jin dad'i.

" Docta har zaka tahiya".

"Eh babba amma da magana nazo" gyara zama Ardo yayi dan yaji me yazo dashi "ince dai lahiya ko?"

"Eh lafiya lau dama akan maganar Ramlah ne nazo neman alfarma" nan dai Abdool ya kora mishi jawabinsa nason bashi ita ya tafi da ita idan ya tashi tafiya, dan duka 2week suka rage mishi.

Jim Ardo yayi yana nazari can yace "Bawai nak'i bana yaro, kuma ba ban amince maka naba, saidai hanzari ba gudu ba, kasan yanzu duniya mutum aka ciyyo ba dabba ba, kuma yana zama abin zagi gareni da ita Kanta Ramlah, kasan Abu ga k'aramin K'auye kowa da yadda zai hwassara zancen ga" tunda ya fara bayani Abdool ya k'asa kunne yana saurarensa, sai zufa ke keto mishi, yasan duk abinda ya fad'a gaskiya ne, to amma shi yanzu ya zaiyi da son Ramlah? Kar yaje yana can gida yana jiran ta girma yazo ya aureta yaji labarin an ba wani ita...Ardo ne ya katsesa "kayi shiru d'an ga da hwatar dai ba ranka ne ya b'aci ba".

Murmushin yak'e ya k'irk'iro "Aa Baba ko d'aya ai abinda ka fad'a gaskiya ne, amma kana ganin babu mafita?" danshi kanshi gabadaya ya k'ulle.

"Mahitar d'aya CE" bai San lokacin da yayi sanyayyen murmushi ba "Baba meye mafitar" cikin zakuwar son yaji.

"Aure! Idan har kana sonta ni zan baka Aurenta, saboda ka kwanta a raina" Ardo ya fad'i hakanne, saboda ya fahimci yana sonta.

Abdool kuwa k'irjinshi ne yayi mummunan fad'uwa, kamar saukar aradu yaji zancen, cikin rud'u ya kalli Ard'o duk da ba wacce yakeso kamarta, amma bai tab'a tunanin abin zai sama haka, shikam gani yake tayi k'ank'anta da Aure yanzu, bayan haka shi kanshi bai kawo yin Aurensa yanzu ba duk da yasan yana buk'atar auren.....baffa ne ya katsa masa tunani.

"Abdulmajeed kodai baka sonta na" karo na farko daya tab'a kiransa da sunansa.

"Aa Baba wlh ina sonta, Inadai ganin kamar tayi k'ank'anta da Aure ne" murmushi irin na manya Ardo yayi.

"Ina ai takai mataki, indai kana sonta kada kayi tunanin komi, katahi ka shawarci magabatanka, kace 'yan uwanka duk nan Suke ko?"

"Eh"

"To ka tahi kayi shawara dasu ba abin tashin hankali bana, sadaki kawai nika buk'ata ko nan da sati guda kazo a d'aura muku Aure".

"Inshaa Allah Baba, zanyi magana dasu zakaji yadda mukayi dasu" sannan yayi mishi Sallama.

Laure da batasan wace wainar ake toyawa ba, bayan sun gama waya da Zainab, ganin suna magana, yasa taja gefe kan dakali tana duba littafanta, wayarsa kadai ya ansa yayi mata sallama, ganin shi kamar baya cikin yanayin dad'i, yasa yaja jinin jikinta, ba surutu da salo yau, itama haka ta shige gida jiki a sabule....

Bayan gida kwantawa yayi kan kujera yana tunanin to ta inama zai fara? Daga k'arshe kawai yayi deciding d'in ya kira Maaminsa.

Bayan sun gaisa ya kora mata bayanin yadda sukayi da Ardo daga farko har k'arshe.

"Abdulmajeed" jin ta kira sunashi complete yasa k'irjinsa bugawa kaddai Maamii tace bata amince ba....katsesa tayi.

"Ka tabbatar kana sonta?"

"Eh Maamii" ya fad'a cikin sanyi.

"Hakan da wannan dattijon yayi shine dai2, kuma ya nuna yasan meyake yi, dan haka kaje ka samu kakanka kayi masa bayani, sannan ka Baba(cewa da babanta) nima inanan zuwa, kamar  yadda ya fad'a cikin sati d'ayan za'ayi komai inshaa".

"Tau Maamii zanyi kamar yadda kikace.....................













💄Meryerm Abdool💄
[7/27, 10:17 AM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽



💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞
*TUKUICI GAREKU SANYIN IDANIYATA*
💕💕💕💕💕💕💕💕💕💕
Abdulmajeed
Ramlah
Rufaida
Baffah
Kausar
Affan
Hanan
Abdallah
Aminah
Amerah
Salma
Salim
Nuseey
Twins
Zee
Amir
Al'ameen
Jidda
Khadija
Khairat
Fatima
Halifa
Mufeeda
Muzammil
Fidoo
Aysha
Muhammad
Ilham
_Hmmm kunada yawa nd rest_
❣may Allah bless be wit u always my kids😘





   📝 *Episode* 71--75


Sauke numfashi yayi bayan sun k'are wayar da Mami, hankalinsa ya kwanta yanzu dan dama ita yakeji kada tak'i aminta, duk da yasan sauk'i irin nata, saidai yaga abin ne, a gaggauce yasan kuwa batason aikin gaggawa, shikam yayi mamakin saurin amintar ta.

"Yes! Any way I'm so much happy, zan auri love of my life" ya fad'a cikin farinciki, a ranar kwanan farinciki yayi, da sassafe ya d'auki excuse ya nufi Sokoto.

Alhaji Sada, yayi mamakin ganinsa saboda bai saba zuwa ba sai weekend, sanda ya kora masa bayanin abinda ke tafe dashi, yaji dad'i har cikin ransa, fuskarsa ta k'asa boyewa, kuma ya bashi goyon baya d'ari bisa d'ari, tare da tabbatar masa idan ya tashi komawa yazo ya d'aukesa suje tare a can k'auye.

Daga nan inda Hakeem ya wuce da yake ya gaya mishi zai shigo garin, saidai bai mishi bayanin komai ba.

Dariya sosai Hakeem yayi har saida Abdool ya nuna b'acin ransa sannan ya saurara.

"Aure fa kace dude! Kuma in a week, common kace u r joking, hw come wane irin aure kenan?"

Tab'e baki yayi "koma me zakace, I don't care, nidai nasan Aure zanyi kuma a satin nan, that all I know" ya fad'a tare da daga kafad'a.

"Tau naji Amma dai ba wancen yarinyar ba ko?"

"Ha'ah see u se trouble meye naka a ciki, ina nine me Aure ko, kai naka ido ne kawai, so put ur eyes and shout ur mouth".

Dafasa yayi saboda yaga da gaske ransa ya baci, " cool down! Nifa abin mamaki ne yake bani kawai, kuma naji kace yarinyar is too young" danshi bai tab'a ganinta ba.

"Hmm ai Kaine da abin haushi, na gayamaka dalilin auren nan, ba zuwa zamuyi mu zauna zaman Aure ba, ita Kanta nasan batasan ma me auren ke nufi, Hmmm kuma ai tayi k'ank'anta ba zata iya dani ba" ya fad'a ya shafo sajensa daya kwanta lup.

"Shegen kaya! Wlh bakaji Dr, kai killer ne in silent way, baki kawai na fika".

Smiling din gefen baki yayi "kaga ni ka tashi muje, time is going" tare suka fita gwanin Sha'awa, suka Lula zuwa Argungu.

A can d'imma ba'a samu matsala ba sunyi na'am da da abin da yazo dashi, Innah hadda tsokanarsa wai daga zuwa Har da yi mata kishiya, saboda yanzu ya daina yinta sai ta had'a shi da Ayatul kursiyyu yace ya fasa.

Dariya yayi yace kada ta damu zai bata eating noise, nan dai sukayi ta barkwancinsu sai marece suka koma Sokoto.

Washe gari sukaje Kilgori tare da Alhaji da Hakeem, Ardo ya tarbesu cikin karamci da mutuntawa kuma yaji dad'in ganin Alhajin hakan ya nuna yaron d'an gidan girma ne.

Amininsa Malam Garba kawai ya kira ya tabbatar da ya bawa Abdool, Ramlah ya dawo nan da sati d'aya a d'aura musu Aure, kuma baya buk'atar komai face sadaki.

Godiya sosai Alhaji yayi masa da wannan Karamcin da yayi musu, sannan yace yayi hak'uri amma zasuyi komai da akeyi a al'adance saboda itama a nuna mata 'yace kamar kowa, Ardo yaso su barshi kawai amma Alhaji ya nace shi zaiyi komai, dole ya Hak'ura amma da sharadin komai sai ranar Auren za'ayi, anan take suka bada kud'in nagani inaso dana gaisuwar iyaye, haka dai suka rabu cikin farinciki kowa na ganin karamcin d'an uwansa.



********************



"Ramlatuna!" D'agowa tayi ta kallesa k'irjinta na dukan Tara2 dan tunda Baffa ya kirata taji, gabanta na fad'uwa "na'am Baffa" ta ansa cikin siririyar murya.

"Ke yadda ina k'aunar ki?" 

"Baffa ba Wanda yaka k'aunata duk duniya baya gareka".

Murmushin jindad'i yayi " yawwa Ramlatuna tunda harke yadda bani cuta miki, inason sanar dake inshaa Allahu, juma'a mai zuwa za'a d'aura miki Aure".

"Aure baffa!" Kalmar da ta fito bakinta kenan cikin firgici da zaro ido.

"Ko bakison Auren ne Ramlatuna?"

Girgiza tayi alaman aa dan ita bamasan maganan ta fito fili ba "Baffa nasan Bazaka cutar dani ba, Allah yasa hakan shine mafi Alkhairi".

" Ameen Ramlatuna,  inshaa Allahu zakiyi hwarin ciki da wanga Aure, da yadda Allah k'arshe k'arshen wahalarki ya zaka, sannan kiyi shiru kakki hwadama kowa kinji?"

Kai ta daga masa "yawwa 'yar Albarka tashi ki tahi Allah yayi miki Albarka".

" Ameen " ta fad'a tare da fita jiki a darare ba k'wari...


B'angaren Mami ma sai shirin zuwa takeyi, tunda Abdool ya kira ya gayamata an tsaida magana sai shiri take sosai, amma sai ana gobe aure zata zo...



"Mutumina wai sai yaushe za'a buga I.V kaga fa lokaci sai k'urewa yakeyi".

"Kaidai ka cika neman rigima wlh, ai sai  kaje kaita bugawa" ya fad'a tare da juya masa baya.

Dariyar ciki yayi, "Yawwa wai ka gayama Zainab kuwa?"

"Oh! Allah wlh shaf na manta, abubuwa sun sakani a gaba" ya fad'a bayan ya tashi daga kwancen.

"Wo sabon Ango duk rud'un bikin ne".

" kaji dashi, magulmaci" yana gama fad'a ya bar parlour gaba daya, da murmushi ya bisa "wannan yarinyar ta rikita min Aboki da yawa".

Bedroom ya shiga tare da zanyo wayansa ya kira Zainab, yasan zataji ba dad'i amma gara taji a bakinsa da taji wani gun.

Bayan sun gaisa nan yake gayamata maganar Auren nasa, dif taji ta daina ji, wani k'olulun bakin ciki ne ya tokare mata mak'oshi cikin rawar murya tace.

" Allah ya sanya Alkhairi "ta fad'a kawai tare da kashe wayar gaba d'aya, dama yasan za'ayi haka amma toya zaiyi, gara ya gayamata gaskiya taji Haushinsa a lokacin zuwa gaba tasan bai yaudareta ba daya rufe dan tayi farinciki zuwa gaba ta gane yaudaranta yayi(komai zakayi da mutum ka tsaya akan gaskiyarka, dan k'arya fure take bata 'ya'ya, gaskiya kuma dokin k'arfe Allah yasa mudace).

Kuka takesonyi amma yak'i zuwa, lallai ta tabbatar Dr Majeed baya sonta, har iya fad'a mata, zaiyi Aure, shikenan ta yayi mata nisa, nisan da bazata iya cimmasa ba, juyi kawai takeyi duk duniya tayi mata zafi, lallai rashin masoyi bala'i ne.

Tana haka ne ilham k'anwarta ta shigo wai tayi mata assignment, hantararta tayi tare da cewa tafice ta bada guri, kota takata anan, aiko a guje ta fita tana kuka dan bata tab'a mata irin haka ba.

Ganin tana kuka ne yasa Momyn su ta tambayeta meya faru, ta gayamata Zainab ta korota.

"Zainab  kuma Ilham? Me kika mata" dan tasan yadda takeda sauki ga k'anninta.

"Banyi mata komai ba Momy, nadai ganeta kwance ranta a bace" mik'ewa kawai Momyn tayi zuwa d'akin Zainab.

Harta zauna daf da ita batasan tazo gurin ba, saida ta d'ora kanta kan cinyarta tana Shafa mata kai alaman rarrashi sannan tasan da zuwanta, fashewa tayi da kuka kamar ita take Jira "Momy na rasashi, shikenan na rasashi".

" Haba Zainab ki idan hankali ya gushe hankali ake sakawa ya nemosa, d'aure kiyimin bayani yadda zan fahimci abinda ke damunki" duk taji a jikinta bazai wuce Dr Majeed bane.

Saida ta gama kukanta, da sai yanzu yazo, uwar bata hanata ba sannan ta gayamata abinda ya faru.

Sosai ta tausayawa 'yar tata saboda tasan yadda takeson Abdool, sai dai bata nuna mata ba, saboda kada tasa ta k'ara karaya.

Cikin taushi da rarrashi ta shiga bata baki "kiyi hak'uri Zainab dama ita duniya haka take bafa komai da akeso ake samu ba a rayuwa, sannan duk abinda kikaga ya kub'ucewa mutum to dama ba'a k'addara zai samesa ba, kuma duk abinda ya samu mutum, dama ba'a k'addara zai kub'uce masa ba, dan haka ki kwantar da hankalinki idan da rabon Aure a tsakaninku sai kiga yazo har gida ya aureki, kedai ki dage da Addu'a da Neman zabin ubangiji".

Lafewa tayi jikin Momyn nata tana ajiyan Zuciya, sosai jawabin uwar tata ya ratsata tana k'ara godewa Allah daya azurtata da uwa ta gari mai maida ita kan seti idan ta juye(Allah ka k'ara ma iyayenmu baiwa da fasaha, ka k'ara muna k'aunar su da kyautata musu ameen, mungode da ni'imar iyaye na gari).

Saida ta tabbatar ta samu nutsuwa sannan ta fito ta barta.


Ana saura kwana biyu Aure Laure duk abin duniya ya mata yawa ita dai tasan bata murna da wannan aure haka kuma bata bak'in ciki dashi, ga rashin Aboki mai glass, tun ranar bai k'ara dawowa ba, dan ranar da sukaje bata nan.

Kilama Baffa cewa yayi kada ya k'ara dawowa saboda zaiyi mata Aure shiyasa ta ganshi wani iri a ranar, gashi za'ayi Aurenta ba tare dasun k'ara had'uwa ba, wata kila sai lahira ji kawai tayi tana hawaye, da sauri ta share kada wani ya ganta dan Iya Hari da Gwaggo Lanti, tsakar gidan, taci gaba sharan turken dabbobin da take yi.....

Iya Hari kuwa da basusan meke gudana ba sai nanayensu Suke ita 'yarta, Ardo ne ya shigo bayan sunyi mishi sannu da zuwa daga can zaune, k'arasawa yayi inda Suke hannu ya zura aljihu ya zaro kud'i ya bata.

Nan da nan ta Washe jajayen hak'oranta "Malam wanga kudd'i na minana?"

"Auren Ramlatuna, gobe idan Allah ya kaimu" ya fad'a mata kai tsaye.

Cikin zaro ido da masifa "Aure? Wa zata aura?"..................





_pls kuyi hak'uri da juna shiru da kukayi hakan ya farune akan rasuwar da akayi mana_ 😞





💄Meryerm Abdool💄
[7/29, 9:10 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

( We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers)







❣❣❣❣❣❣❣❣❣❣
```ina kuke masoyan Abdulmajeed, ga shafinku, ina matukar kaunarku a duk inda kuke Allah yabar kauna.```
❣❣❣❣❣❣❣❣❣❣



*Yan uwa masu yimin ta'aziyya, da masu yimin sannu da jiki, nagode sosai da kulawarku, Allah ya barmu tare nagode bunch of love#❣#*






  📝 *Episode* 76--80


"Gara ma kace ba'a ta kakai, dan bai tab'a yuyu ayima Laure Aure gobe, ni kuma a hwadamin yau, sai kace ban da had'i da ita, kuma ai Laure da mijinta" shidai Ardo ido kawai ya zuba mata.

"Nasan ko Jauro dani yaka magana bada kai ba, ni nibbashi Laure ba kaiba, to k'ak'a akai mata Aure gobe ace sai yau zan sani, ai wanga maganar banza ta" duk cikin d'aga murya da masifa take magana, ganin ta dasa aya, murmushi yayi.

"Hmm khadijatul kubra kenan" ya kira Iya Hari da anihin sunanta "kamar yadda na fad'a gobe da izinin Allah za'a d'aura wannan Auren ba hwashi, danni adda ikon aurar da Ramlatu, maganar kin tsayar mata da miji ko minana ma, ke kissani kuma ke yashahwa, bakida hurumin tsayarwa da Ramlatu miji, wadda baki k'auna, taya za'ayi ki zabar mata miji na gari? Kina tunanin bansan komi da kukeyi ba, ina sane nadai tsaya naga iyakar gudun ruwanku ne, daga ke har ita lantana nasan baku k'aunar Ramlatu saboda hauka irin taku, kullum tunaninku yaya  zakuyi Ku ganta cikin k'unci shine tunaninku, toshi zakaran da Allah ya nufa da cara ko ana muzuru ko ana shawo to sai yayi" cikin kwanciyar hankali ya shiga zare musu magana kai ba kace cin mutunci yake musu ba.

Saida yayi musu tass sannan ya sarara musu, tsabar bak'inciki kamar zuciyar Iya Hari ta fito waye wannan shine ga duka ga tsinka jaka, magana ma kasa yi tayi, Lanti kuwa sai harara take aikawa Laure jira kawai take Ardo ya fita ta jibgeta, kamar ya sani yace.

"Ke Ramlatuna zonan" sannan ya fita aiko har tana had'awa da tuntube bisa da d'an gudunta, da harara su Iya suka rakasu "lallai Malam ni zaiyima cin mutunci akan wannan d'iya".

" Hmmm Inna bari ta dawo yau sai taci na jaki in yaso, gobe akaita gidan miji da kumburaren jiki, shegiya 'yar matsiyata" nan sukaci gaba da zaginta ita Ardo (ni kuma nace Allah ya Baku lafia, dan ciwonku saida Addu'a) lol.


"Ramlatuna naso ace na sadaki da dangin mahaifiyarki kahin in aurar dake, sai dai gashi Allah bai nuhwa ba, ina rokon Allah ya sadaki dasu ko nan gaba kema kiji dad'in dangin uwa Ramlatu" ya fad'a tausayinta cike da ransa, ba kad'an ba yake tausayawa Ramlah Sam batasan wani dad'i na uwa ko danginta ba.

"Ameen Baffa".

 "Yawwa ungo wannan" biba bag ya mik'a mata.

"Kitahi gidan Gwaggonki Aisha,  keda abukkanki kinji a can zaku kwana kuyi abin da kukeyi irin naku na Mata" sunne Kanta tayi alaman kunya.

Murmushi yayi, sannan ya wuce yanajin farinciki a ransa, gidansu Delu taje nan Delu ke mata mitan rashin fad'a mata da wuri, hak'uri tare da fad'amata dalilin rashin fad'ar, haka suka biyama sauran k'awayenta sai gidan Shatu, d'aki d'aya ta ware musu da yake tasan da zuwansu.



******************


Bayan fitar Momy sosai nutsuwa ta zoma Zainab tashi tayi ta d'auro alwala tayi nafila tare da karanta Qur'anil Kareem, tuni taji zuciyarta wasai saidai abinda ba'a rasa ba.

Gift ta bawa k'annenka suka kaima Abdool, yaji dad'in sosai duk dan hadda na Ramlah a ciki, agogo ne nashi mai kyau na azurfa, Ramlah kuwa sarka ce da abin hannu masu kyau k'irar silver, tare da card na marriage wishes, tukuici ya basu k'annin nata cikin da farinciki.

"Allah sarki Zee" ya fad'a cikin slow voice.

Hakeem kuwa cewa yayi "lallai wannan ko'a mata ita ta daban ce, son gaskiya take maka( bawai nuna zafin kishi ke nuna soyayya ba, so na nufin kyautata da mutuntawa a kowane hali take note girls) lol.

"Hakane" ya fad'a a tak'aice saboda sanin halin Hakeem da jan abu yanzu suyita rigima.

Lumshe ido yayi yau tsawon sati biyu rabonsa da Ramlah yana missing d'inta sosai.........


*Washe gari....*


Tun 12 angwaye suka shirya tsaf cikin farin wanka daga sama har k'asa sak, iri daya komai nasu, su isma'il ma su had'e cikin nasu kalar gayun, Alhaji da kawu Sani(da yake shi kad'ai ne a gidan yanzu) kawai Suke jira su fito dan sunfi son da suyi juma'at a can da an sauko juma'a a d'aura auren kawai.

Alhaji ne ya fito cikin shirinsa tsaf hadda su rawani, haka suka d'auki mota biyu, duk maza ba mace ko d'aya dan koda Alhaji ya gayama Hajia Inna cikin rashin Kulawa tace Allah ya kyauta shikenan maganar, sam baiji dad'i ba, ko kad'an, fatar ganewa kawai yayi mata.

Ganin saukar baki a garin yabawa wadanda basu san me ake ciki ba mamaki ciki hadda Jauro wanda baisan wainar da ake toyawa ba.

B'angaren su Laure kuwa gyara Shatu irin nasu na k'auye dai ba laifi, baffa ma yayi mata nashi k'ok'arin dan tunda satin ya kama yake bata tsumi mai kyau kuwa irin na fulani ko yanzun ma ya aiko hadda kaza, suna cikin d'aki tayi shiru dan k'irjinta ne ya tsananta bugamata ba k'akk'autawa, su kuma su Delu sai tsokanarta suke wai ta gayamusu sunan mijin, shiru tayi dan ba ansa.

Sai Murmushin yake da take yi musu, haka dai sukaci gaba da gadarsu cikin nishadi da raha.

Gidan Ardo, kuwa iya Hari ganin har wayewar gari ba Laure, ga Ardo yaki bada damar ta tambayesa dan shima bata samu ganinsa ba, haka ta zauna zuru cikin rashin jin dad'i, can ga Lanti da kwailarta, nan take tambayarta Laure dan sai mangariba tabar gidan da alwashin dawowa yau ta cika burinta na jibgarta, nan uwar ke gayamata har yanzu bata dawo ba hatta Malam bata saka a ido ba tun jiya.

"Hmm Inna akwai abinda Baffa yaka shiryawa to missa ya boyeta?"

"Nima abinda nika son Sani kenan, gashi bansan yaya nikai da shedanin d'anga ba Jauro, kesan baida mutunci(ato k'aik'ayi koma kan maishi).

"Kyaleshi Inna bai isa yayi komi ba, ai yasan inda yaka haukatai...." Jin k'arar motoci ne ya saka su lekawa.

Ardo ne shima cikin shigar girma tare da Malam Garba suka tarbesu an gyara d'akin gaban gidan tsaf an shimfida tabarmi, komai tsaf, cikin farinciki suka tarbesu, su Isma'il sunyi mamakin k'auyen wai Abdool yaga matar Aure tab! Amma ba laifi sunada karamci.

Abinci na alfarma aka kawo musu daga gidan Malam Garba aka dafa ga fura da abin sha, komai dai mashaa Allah, nan aka gaggaisa ana jiran isowarsu Baba da Abdool yaje d'aukowa kamin lokacin d'aurin auren yayi.

Baba da kawu Mansur ne suka ya d'auko, suna isowa yayi dai2 da fitowar Ardo daga cikin zauran ido hudu sukayi da Baba.

"Malam Umar!" Cewar Baba, cikin tsananin mamaki daya bayyana a fuskarsa.

"Malam Abubakar!" Ardo ya fad'a shima cikin zaro ido........




*to masu karatu munga alaman Sanayya amma a INA sukasan juna?*


*ya makata mu warwayi baya, dama hausawa sun ce waiwaye adon tafiya* 

*muje zuwa wasa farin girki* ⛹🏾‍♀⛹🏾‍♀




💄 Meryerm Abdool ce😘
[7/30, 8:07 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate, we touch the heart❤ of the readers📝).



_falyakul khairan auli yasmut_ 🤐


👏🏽 *Allahumma yashfikah👏🏽 wishing d most quickest and fastest jet recovery dear Abdool💋*









     📝 *Episode* 81--85



     *ASALIN LABARI*



Malam Abubakar d'ane ga Malam Mudi Wanda sana'ace ta kawo garin Argungu, d'an asalin wani k'auye na Argungu mai suna, birnin lafiya, ganin ana samu a harkar ga yawon zuwa da dawo yasa ya gina gidansu k'arami ya tare da iyalansa, zuwansu ba dad'ewa ya saka Abubakar da kanwarsa, Hurera makarantar boko da Islamiyya a cewarsa zamanine gara a dama dasu, sannu a hankali sukaci gaba da gungurawa da raywarsu cikin rufin asirin Allah, a haka su Abubakar suka tasa, Abubakar ya tashi yaro Wanda yasan ciwon Kansa kullum burinsa bai wuce ya zaiyi ya tallafawa iyayensa ba, shiyasa kullum ya dawo makaranta to yana kasuwa inda mahaifinsa yana taimaka masa.

Ranar bak'in ciki garesa itace ranar da sak'on rasuwar ahalinsa ta iskosa a sanadin gobara data kama gidansu Wanda komai ba'a samu ya fita ba, da yake cikin dare abin ya faru lokaci yana poly birnin Kebbi, Abubakar yayi kuka yayi bakin ciki amma kuma ba yadda zaiyi dole ya hak'ura, bayan anyi sadaka, dangin mahaifinsa suka da tafi dashi, da yake itama innarsa marainiyace, dangin mahaifi kawai suka rage mishi.

Zaman k'auye ba dad'i koga Wanda ya saba balle wanda bai saba ba, amma ya zama dole haka Abubakar ya dawo d'an gona, kullum suna gona, amma da yake jarumine hakan bai wani damuwarsa ba, lokacin da Hutu ya k'are ya taso da maganar komawa, ina wuta in fad'a haka sukayo caa su basusan wannan zancen ba, saidai yabar karatu, shi kuma ya had'e kai da fata akan yanason karatunsa, ganin ya nace suka yadda ya koma amma da sharad'in sisin su ba zata shiga ciki ba, haka ya koma makaranta bako asi nasu.

Allah ya taimakeshi daf da faruwar wannan abun babanshi ya tura mishi kud'i masu dan dama saboda karatunsa dama kuma yana d'an bige bigensa, da haka ya samu ya biya kud'in makaranta, sannan ya sayi mashin ya fara achab'a, da haka yake biyan kud'in makarantar sa yake d'aukar kan shi haka dai da dad'i ba dad'i har ya kammala diploma, bai wangarta ba ya cika D'E form ya jona HND, yakanje gida ya gansu lokaci zuwa lokaci, su kuma sun zuba mishi ido cewarsu idan ya gaji da kanshi zai dawo.

B'angare gida kuma yana gyaran tsohon gidansu daya k'one, haka ya kammala karatunsa cikin nasara, zuwa lokacin yasan rayuwa dan ya ganta kala-kala saidai ya yadda ba maraya sai raggo, dan haka ya k'ara zage damtse da neman na Kansa, ana hakane Allah ya had'a shi da Habiba anan Argungu, k'anwar wani abokinsa ne, nutsuwarta da hankalinta ne yaja ra'ayinsa gareta, bawani sha wahala ba wajen amincewarta.

Bayan sun sasanta ne yaje gurin danginsa da maganar, bud'ar bakin su cewa sukayi yanada gurin ajeta baiyi mamakin jin haka daga garesu ba, in yayi la'akari da yanda suka danne mishi gadonsa ya lura da mutane su da Kansu kad'ai suka Sani, fatan shiriya yayi musu sannan ya gayamusu ya gyara tsohon gidansu.

Ba'a d'auki lokaci ba akayi aka gama aka dangana da Amarya Habiba gidan angonta, zama sukeyi gwanin sha'awa dan Habiba akwai hak'uri, ko sabani suka samu ko itace mai gaskiyar zata hau bashi hak'uri, shiyasa ba'ajin Kansu duk da Abubakar ya zamo mai zafin zuciya da kafewa akan abu daya.

Haihuwarsu ta farko Mahmud Wanda yaci sunan babansa yana d'an shekara biyu ya rasu daga nan kuma sai Ameena, Asma'u sai auta Mansur.

Suna cikin hakane Allah ya kaddari Abubakar da samun aiki, sunyi farinciki sosai da wannan ci gaban da suka samu, sun wadatu da komai na rayuwa dai2 k'arfi baifi jiki ba, cikin 'yan shekaru ya gina musu gida mai kyau irin dai na mai k'aramin k'arfi, haka yaransu suka tashi cikin tarbiya musulunci.

Amina da Asma'u ba wasu kyakyawa bane na gani kasheshi hasalima ba za'a sakasu cikin ajin farko irin dai bamu cikin 'yan tusa 'yan zawo sun tseremana saidai kam Allah ya azutartasu da diri mai matuk'ar d'aukar hankali Wanda ba namiji ba macce ta gani sai taji kishi. Lolx

Shiyasa kullum suna cikin hijab gudun yad'uwar fitina a al'umma, sannan Allah yayi musu baiwar sauti wato murya kenan, mai matuk'ar sanyi da d'aukar hankalin mai sauraro.

Lokacin su Ameena suna SS3 sun taho ten days d'in nan da ake bayarsa dayake boarding school Suke, Asma'u tana SS2 lokacin, da yammaci taje gidan wata k'awarta Firdausi anso wani Abu data manta a hannunta, bayan ta Amsa sun fito kenan zata wuce gida, a k'ofar gidan sukaga wata mayyar mota ta tsaya k'ofar gidan, wani had'adden guy ne ya fito ciki ba laifi yanada kyau dai2 shi, ga iya wanka, dan kam ya wanku ba k'arya.

Cikin farinciki Firdausi tace "Oyoyo Yaya Auwal kaine a garin yau" glass d'in idonsa ya gyara ma zama yana murmushi yace "Fido 'yar mama kece kika girma haka?".

Murmushi kawai tayi, ita kuma Amina gaidasu tayi tare da jan hannun Firdausi alaman su tafi.

Kallonta yayi Sam bai kula da ita ba wani shock yaji har cikin d'an yatsarsa, dakyar ya ansa da lafia, Firdausi CE tace " Yaya zan rakata na dawo, suka wuce.

Baima ji me take fad'a da kallo ya bisu har suka karya kwana, sannan yayi smiling tare da Shafa Kansa.

Anan Firdausi ta sameshi yanata Murmushi shi kad'ai "Aa Yaya meyasa baka shiga daga ciki bane".

" uhm Fido wannan k'awar taki fa"?

Murmushi tayi "Laa Yaya kaddai kasa..."

Katsaeta yayi "Nidai ina ne gidansu wlh tayimin".

" Aa Yaya daga ganin sarkin fawa sai miya tayi zak'i? Nidai mu shiga ciki ka huta zan yi maka bayanin komai " ta fad'a cikin zolaya dama taubashinta ne..................





_nayi muku typing mai yawa na taho zan tura ya goge😢 kuyi manage_ 😘 


*muje zuwa 🤸🏻‍♀*






💄Meryerm Abdool 💄
[8/1, 8:03 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)





         📝 *Episode* 86--90



"Fido ina wasa dake ne wai? sai yawo da hankali kikemin, jiya dak'ar nayi bacci tunanin yarinyar ya Addabeni, sonta nike da gaske, pls joke a part ki gayamun mana" tunda ya fara magana Firdausi ta kwalalo ido tana kallonsa dan ita ta d'auka wasa yake amma yanzu kan tana gaskiya a cikin idonsa.

Zama tayi bayan ta d'ora break d'inda ta kawo mishi kan center table "Ya Auwal Allah na d'auka da wasa kakeyi, amma kayi hak'uri, indai akan Ameena ne bakada matsala".

" Ameenah!" Ya maimata sunan cikin lumshe ido.

"Wow what nice name" dariya Firdausi tayi ganin yayan nata na shirin zarewa, "lallai ma Yaya abun naka azimun ne".

"Hmmm ba zaki gane bane, yanzu dai ya za'ayi nifa tayimin sosai ina ne gidansu".

" kwantar da hankali  yaya zanje nayi magana da ita nasan batada matsala, komai zaizo yadda kakeso".

"Yawwa Auntan Mama zaki kuwa samu tukuici mai tsoka" dariya tayi "yanzu dai kayi karinka anjima kad'an zakaji yadda mukayi" sannan ta fice.

Koda taje gidansu Ameena ta sameta tana taya Mamanta aiki, bayan ta gaida Maman, Ameena ta jata zuwa d'akin su.

"K'awata da sassafe haka, fatar dai lafia"?

Nisawa tayi " lafiyarce ta kawo haka...." Nan ta koro mata jawabin abinda ya kawota.

A firgice Ameena ta kalleta tana girgiza kai " Aa Fido bazan iya ba, pls ki bashi hak'uri kawai".

B'ata rai Firdausi tayi "kome yasa ko kinada Wanda kakeso ne daban?"

"Ba haka bane....." Katseta tayi.

"Nagane jini nane bakyaso wato, nina d'auka na wuce haka a gurinki Ameena, har ina bashi tabbacin samunki, ashe nice ke haukana, well thanks" tare da mik'ewa shaye da toka.

Riketa Ameena tayi "wlh ba haka bane Firdausi kuma bawai sonsa ne banayi ina tsoron Baba ne, baya barina tsayuwa da saurayi ban tab'a yi ba, amma kiyi hak'uri".

Komawa tayi ta Zauna "indan wannan ne, Baba ya hanaki kula samari saboda gudun b'ata gari da kuma karatunki, yanzu kuma meya rage mu k'are? Kad'an ne, sannan kada kiyi kwankwanto akan Yaya Auwal mutumin kirki kuma da gaske yazo gareki, amma idan kinji baki sonsa har ranki, to wannan daban ne, dan ba'a dole a soyayya" ta fad'a tana kallonta.

Ita kam tun jiya data ganshi taji ya kwanta mata a rai saidai a gaskiya tanason karatu, kuma muddin Baba ya gane tana soyayya tasan aure ne k'arshe maganar.

Tabota Firdausi tayi "bakice komai ba?"

"Fido in nace banason sa nayi k'arya, amma gaskiya karatu nakeso nayi" dariya Firdausi tayi.

"Lallai ma Meenal to aure na hana karatu ne ko karatu na hana aure?"

Lumshe ido tayi "ya danganta da kalar mijin da ka Aura".

" Hmmm Yaya Auwal baida matsala kamar yadda na fad'a miki, kedai in har kina sonsa ki amince kawai".

Ba yadda ta iya da rigimar Firdausi haka ta amince, tsallen murna kawai Firdausi keyi sunyi nasara, itadai Ameena sai dariya take mata, nan ta wuni gidan tare sukayi aikin rana sai bayan Azzahar ta wuce cike da farinciki dan zatafi kowa murna yayanta zai auri Aminiyarta.

Lokacin da taje masa da labarin amincewarta murna kamar ya taka kan jariri, amma ta bashi shawarar yaje gurin Babanta kai tsaye.

Lokacin da ya samu Malam Abubakar da zancen, yaji dad'in hakan domin ya nuna mishi yasan Kansa bai tari 'yarsa kai tsaye ba, yace yaje zaiyi bincike akansa idan ya gama zai nemesa, ansar number sa yayi tare dayi masa godiya.......



******************


*WAYE AUWAL*

Auwal Muhammad Sada shine cikakken sunansa d'ane ga Alhaji Sada canji, tsohon d'an kasuwa Wanda yayi suna a duniyar canji, mutum ne na mutane duk da tarin dukiyarsa hakan bai saka mishi girman kai ko d'agawa ba, kowa nasane, yanada matar aure d'aya Hajiya Kaltume, mace mai nuna isa da tak'ama wacce bata d'aukar raini komai k'ank'antarsa, ta tsani talaka kamar yadda ta tsani mutuwarta, ko a hanya bataso ta had'u dashi, Hajia Kaltume kenan manya masu duniya!.

Suna da 'ya'ya shida Ayuba, Auwal, Sani, Salisu, Rabi'u, sai Iggenta kuma Auta Maryam. Ya'yan sun tashi cikin kulawa, ba abinda suka nema suka rasa, a rayuwarsu sun tashi cikin tsananin gata amma hakan bai saka sun sangarce ba, sun tashi cikin cikakkiyar tarbiya ga girmama na gaba dasu, sunyi karatu a makaranta mai kyau, Ayuba da Auwal tuni sun kammala degree d'insu inda suka fad'a harkar kasuwanci kamar mahaifinsu, Sani da Salisu suna final year inda Rabi'u yake level 3, Maryam kusan sa'an Asma'u ce k'anwar Ameena, itace ta rage secondary a yanzu, Ayuba yayi aure ba da dad'ewa ba, inda ya Auri 'yar k'awar Hajia kaltume, Rafia Hajia taso Auwal ya Auri k'anwar Rafi'a wacce tunda ta ganshi ta mato akansa, amma yace bayaso, su Rafia suma sunada arziki sosai shiyasa Hajia ta yadda aka had'a auren, saidai kam ba tarbiya kota sisi, saidai gyaran Allah kawai.


( *To yanzu ga Awwalu ya d'auko magana wai yanason 'yar talakawa ya kuke gani friend?* ) 🤔




Too busy🤦🏽‍♀ manage pls😘




💄Meryerm Abdool💄
[8/2, 6:53 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



*# ka zama mai ra'ayin kanka, bamai bin ra'ayin wasu, bazaka iya ma mutane ba, koda kuwa goyasu kake kullum kana zagaye gari dasu, tofa sai sunga laifinsa wataran, kaidai gyara tsakaninka da Allah domin gobenka#* nasiha ce👌🏻


_#one love 😍 Abdulmajeed fans😍 ina yinku guys keep fallowing😘❣❤💘#_






       📝 *Episode* 91--95



Bincike sosai Baba yayi game da Auwal, sannan ya kirashi tare sukazo da Jafar yayan Firdausi gaidashi sukayi cikin girmamawa sannan suka zauna k'asa kan carpet,  ya sunkuyar da kanshi k'asa.

"Nayi binkice kamar yadda addini ya tanadar, na kuma gamsu da tarbiyarka, saidai hanzari ba gudu ba, Abu na gaba shine kaje ka nemi soyayyar ta idan ta aminta walillahil hamdu, idan bata amince ba ka hak'uri ba rabonka bace".

Tunda Baba ya fara magana, baice komai ba, saida ya gama, godiya sosai sukayi masa, sannan suka tafi cike da farinciki, Jafar sai zolayarsa yake.

Bai wani sha wahala gurin shawo Kanta ba, duk da ta tsaya jan aji irin namu na Mata, amma komai yazo da sauki tunda dama Firdausi ta share masa hanyar, anan tayi masa maganar son ci gaba da karatu ya tabbatar mata babu matsala zatayi sai Wanda ta zaba.

Saida Baba ya kirata ya tabbatar tayi na'am dashi sannan ya K'ara kiransu " to Alhamdulillah ta bani tabbacin ta aminta dakai, saidai ka sani ka fito gidan arziki duk da inada tabbacin bakwa cikin masu raina ma mai k'aramin k'arfi, amma duk da haka banason wulak'anci, ina nufin kada a walak'anrta min 'ya, ina so gami da k'aunar ta amma a hakan zan hak'ura na baka ita saboda ya zama dole tayi aure koba da kai dole zatayi dan shine kimarta, ban kaba ita dan abin hannunka ba aa na bakane saboda ka nuna kana k'aunarta kuma na yarda tarbiyarka, don  haka nake rokonka da kada kai ko danginka su ya walak'antamin 'ya idan naga da walak'anci to zan janye gaskiya" dago ido yayi yace.

"Inshaa Allah Baba hakan bazai faru da yardar Allah, zan kasance cikin masu rike amana".

"To shikenan sai kaje ka turo magabatan naka, Allah yayi muku albarka" da ameen suka ansa sannan suka tafi.

Dama jiran ansar Baba ya tsayar dashi, a ranar ya koma Sokoto dama a can Suke zaune.

A ranar ya Sanar da mahaifinsa yayi murna dad'in labarin dama sun k'agu ya kawo matar, bai tsaya wata ba ya kira mijin k'anwar tasa ( Dadyn su Firdausi) ya tabbatar mishi da yarinyar ta fito gidan tarbiya kuma itama mai tarbiyarce, dama abinda yakeso yaji kenan, anan ya tabbatar masa suna nan zuwa k'arshen sati saboda ayi komai cikin lokaci.

Lokacin da yajema Hajia kaltume da zancen tambaya ta farko datayi masa shine waye mahaifinta?

"Am Momy dama Babanta ba wani bane Headmaster ne a wata primary...."

"What!" Ta katsesa ba tare data barshi ya k'arasa ba.

Mik'ewa tayi tare da nunashi da yatsa "kai Auwalu idan ma barci kake toka farka, dama shiyasa kace bakason Ummita saboda saboda kanason had'ani da dangin tsiya ko? To wlh ahir d'inka badaini Hajia kaltume zaka had'a ma jini da matsiyata ba".

" Momy.... "Katsesa tayi

"Get out, banason jin komai daga bakinka" ta fad'a tana nuna mishi k'ofar fita.



Tashi yayi ya fice jiki b k'wari, dan yasan halin mahaifiyarsa tasa tsaf.



**************************

A satin Alhaji Sada da kannensa sukaje akayi komai na Al'ada aka tsaida rana, wata d'aya bayan sunyi graduation, haka suka watse cikin farinciki da ganin girman juna, dan anyi abinne na mutunci, lokacin su Ameena sun koma tuni.

B'angaren Hajia kaltume jin bata k'ara ji daga Auwal ba ta d'auka yabar maganar taci gaba da sha'aninta, aiko ranar da Alhaji ya gayamata sunje an tsaida rana, tub'ure masa tayi hauka zallah, saida yayi Mata Jan ido tare daci mata mutunci sannan yayi mata kashedi da kada ta yadda tayi abinda auren zai baci muddin tayi to a bakin Aurenta.

"Shima so kikeyi kiyi masa mugun zabin nan da kika yima Ayuba ko? To ban aminta ba tunda ya nuna Wanda yakeso, kuma bata wata matsala to banga dalilin hanashi ba, akan wani bazan dalilin ki Mara asali da tushe"  a babin dole ta hak'ura dan tanason aurenta, amma tace ba ruwanta da auren kuma ko sisinta bazai yi ciwon kai akan tsinannen aure ba.

Ba Wanda ta fad'ama maganar auren, ko 'yan uwanta ko, Rafia da taji batun Auren ba k'aramin tashin hankali shiga dan ita har ga Allah son Auwal take, dan batasan dashi ba sai bayan Aurenta da Ayuba, shiyasa take wani shige masa(wa'iyazu billah kina matar aure wani namiji na burgeki wannan wace irin rayuwa ce, Allah ya gyara).

Ga k'anwar ta Ummita datake mutuwar sonsa taso ya auri Ummita ko an ta d'anji sauk'i tunda ya auri jininta, nan take taji ta tsani wacce zai aura kuma tasha alwashin rabasu, musamman ma da taga Hajia itama batason Aure, Murmushin mugunta tayi(koma take sak'awa a ranta oho! Wai Ameena tun kan ki shiga kin fara samun mak'iya 😞 ).

Alhamdulillah su Ameena sunyi graduation successful, nan aka shiga hada-hadar biki ba'a kama hannun yaro, karma Firdausi taji amara k'irjin biki, itace amarya itace ango, a gefe d'aya kuwa Auwal da Ameena ji Suke kamar sun shekara goma tare saboda tsabar k'auna dake yawo a tsananin su.

Biki akayi mai k'ayatarwa inda kowane b'angare ya taka rawar gani, ba k'aramin k'ok'ari su Baba suka yi ba gurin gyara wa Ameena d'akin ta komai yaji dai2 dai k'arfi baifi jiki, sai fatan zaman lafia, haka aka gama lafia kowa na farinciki, inka d'ebe uwar ango data nuna k'iyayyarta baro-baro, danko dangin ta sai daga baya sukeji, kin gayyatar kowa tayi, duk Wanda ya kawo Kansa kuwa tas takeyi masa, tace munafukai ne.

A sabon gidansu da basu Dad'e da tarewa ba Wanda Alhaji Sada ya Gina, shida 'ya'yansa estate mai d'auke da apartment biyar, anan suka tare, akai amanar gurin surukarta, dutse idan yana magana tota tanka sai k'anwar ta ganin shirun yayi yawa tw ansa musu,haka suka dangana da ita sashinta cike da mamakin uwar mijinta, Allah ya kyauta sukace sannan suka k'ara yi mata nasiha,tare da fatar Alkhairi haka suka barta suka dawowarsu (aure kenan! Shakan yaro)

 k'auna mai tsabta ma'auratan Suke gudanarwa, cikin tsantsar so da kulawa kowannesu tattalin d'an uwansa yake.

Duk safiya zataje ta gaida surukanta Alhaji har janta da hira yake dan yarinyar ta shiga ransa jinta yake kamar Maryam d'insa, sabanin Hajia da sai ta gaida ita kusan sau uku kafin ta ansa da lafia, ko inda take bata kallo, bare tayi tunanin tasan da ita haka take karake zaman ta dawo, bai hana gobe ta k'ara zuwa,  haka komai ta dafa zata aika Musu, ko kallon abinci batayi balle tasaran zataci saidai in mai aiki ta taho taci ko taba almajirai.

Sabanin waccen 'yar iskar da bata iya komai ba sai fitsara da kinibibi, ko ruwan zafi bata iya dafawa saidai tazo nan inda Hajia taci ko kuma Ayuba yayi musu take away, gaisuwa ko sai tayi Mata suger takeyi, Alhaji kam saidai in hanya ta had'a su yake samun gaisuwarta.

Auwal duk yana sane da wulak'ancin da Hajia kema matarsa, shima baida bakin hanawa saidai ya sakata d'aki ya bata hak'uri da lallashinta, "lah ba komai wlh ai iyayenmu ne dole mu bisu" kullum maganarta kenan, hakan ba k'aramin dad'i yake mishi ba, yaji sonta ya k'ara nunkuwa ransa.

Kamar yadda yayi mata alkawali har makaranta yaje da kanshi ya anso mata foam, ranar tayi tsallen murna burinta zai ciki, saidai kash!.

Labari na jema Hajia tace batasan zancen ba in Aure, aure in karatu, karatu ..........



_wayyo silly Ameena_ 🙆🏾🤦🏽‍♀



💄Meryerm Abdool💄
[8/3, 2:09 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)


*wata rana manzon Allah yace da Mu'azu bin jabli "ya Mu'azu shin bana baka labari akan, kan al'amari ba da kuma gimshik'insa da tsororuwar tozonsa?".*

Sai yace *" fad'a mini ya ma'aikin Allah".*

*"kan al'amari shine musulunci, gimshik'insa shine sallah, tsororuwar tozonsa shine jihadi, sannan ya k'ara cewa shin bazan gaya maka abinda ya mallaki dukkansu ba?*

Sai yace *"sanar dani ya ma'aikin Allah"*

Sai ya kama harshensa sannan yace *"ka kiyaye wannan.*

Sai Mu'azu yace cikin mamaki *"ya ma'aikin Allah, dama ana kamamu da abinda muka fad'a?"*

Sai yace *"kaiconka ya Mu'azu, shin meyasa ake kifarda mutane da a cikin wuta da fuskokinsu ko da tsinin hancinsu sai face akan abin da harshensu yake girbarmusu.*

_Hadisul hasanu_

_to nidake dasu mu guyi fad'ar kowace kalar magana, musan mu muka fad'a, dan wallahi nidake dasu sai munyi bayanin kowace kalma bayan kalma gobe k'iyama ( Allah yasa mudace_ 👏🏽




     📝 *Episode* 96--100





Koda Auwal ya gayama Ameena abinda Hajia tace, abin ya Sosa ranta don Allah ya sani tanason karatu, kodon halin rayuwa, amma saboda ta kwantar masa da hankali ganin ya shiga rud'u, bata nuna komai a fuskarta tana murmushi tace "ba komai mijina, bin Umarnin Hajia dole ne, koda kuwa yaci karo da nasu ra'ayin, ina k'aunar ka dole na k'auna ci, abinda Hajia takeso, saboda haka karka damu nina hak'ura da karatun".

Tsabar farinciki rasa bakin magana yayi sai rungume ta yayi yana Sanya mata Albarka, tare dajin k'imarta da darajarta cikin ransa.

Lokacin Alhaji Sada yaji zancen da kanshi ya kira Ameena akan meyasa ta yadda da barin karatunta, kodai dole akayi mata? dan baisan Hajia ta hana ba, Auwal dai yace ta fasa ne,  " Ameena idan iyayenki sukaji ai ba zasuji dad'i ba".

"Baba aina gayamusu nice na fasa yi" duk da cikin ransa ya shakkar haka kawai kuwa, nan dai yayi mata nasiha kamar yadda ya saba tare da bata kud'i masu yawa akan ta fara Sana'a tunda batason karatu, godiya sosai tayi masa sannan ta wuce, girgiza kai yayi tare da cewa "Allah ya kyauta" dan yanaji duk inda aka zagayo aka dawo akwai sa hannun Hajia.

Ameena Nada wata 6 ta samu miscarriage, Wanda basu Masan da cikin ba, tsawon sati biyu tayi a asibiti, ba Wanda baije dubata ba, harda Rafia kusan kullum sai taje dayake ita 'yar duniyace bata nuna k'iyayarta a fili.

Hajia ce kawai bataje ba, saima cewa tayi ai gara da tsinannen cikin ya zube, kuma Allah yasa mahaifar ta lalace gaba d'aya, da dai a haifemata dangin tsiya, maganganu dai ba dad'in ji taita fad'a.

Ko bayan an sallamesu, saida Alhaji ya nuna b'acin ransa sannan taje ta dubata Wanda shine  zuwanta na farko sasan shima daga k'ofar parlour ta tsaya tayi sannu tana wannan cika da batsewa, tayi mamakin ganin yadda aka gyarama Ameena guri, sai tab'e baki tayi tace ai duk dukiyar d'anta ce, dansu basu da komai sai tsiya (oh talaka bawan Allah, komai saidai anyimishi kenan?, kai sharri kayan kwalba😔).




*************************

Sani da Salisu sun kammala karatunsu lafia, kuma sun fad'a kasuwanci kamar 'yan uwansu dama karatun anayi ne saboda zamani da k'arin experience akan business d'in, nan maganar Auren su ta tashi to anyi sa'a sun d'auko diyan masu dashi, nan fa Hajia akayi biki na kece raini, sai bak'ak'en maganganu ake yab'awa Ameena, bawar Allah yi takeyi kamar batasan da ita akeyi haka akayi biki aka k'are amare suka tare.

Haka dai akaci gaba da zama yayin da Ameena ke k'ara fuskartar cin fuska da walak'anci ga surukar tata saboda dai ta kasance 'yar talakawa, banbancin launin fata ake nuna mata sosai, sauk'in abin mijinta ta na k'aunar ta kuma suma matan saurin nata ba wacce ke nuna mata raini a gabanta sai dai ko bayan idonta, haka share tace ci gaba da kyautata mata, dai dai da rana d'aya bata taba gayama iyayenta ba.

Haka rayuwa taita shurawa kwanci tashi hasarai rai, duk surukan gidan kowa na d'auke da ciki inka debe Rafia wacce tace haihuwa ba yanzu, sai ta gama shanawa ba zata tsofe a banza ba amma da yake 'yarso CE shiru kakeji, Hajia ko tari (ooh da Ameena ce da anga yakin basasa...hhhhhh) lol


Ameena CE ta fara haihuwa, murna gurin Auwal kamar ya taka kan jariri ya zama Baba, haka ma Alhaji anyi jikan fari, kowa ya nuna farincikinsa nan da asibiti ta cika da 'yan uwa da Abokan arziki, hadda su Rafia anje na munafurci, saida aka tabbatar lafiyar uwar da d'anta sannan aka basu sallama, gida suka wuce dama k'anwar Mamanta tazo Asma'u k'anwar Ameena da yake sunyi Candy, hadda su Firdausi amarya an iso, haka suka dunguma suka wuce gida dan kankanta mata guri dan yau zasu wuce Argungu.

Hajia dak'ar taje shima ko d'an bata ansa ba daganan ta ganshi a hannun Asma'u wacce tunda yaron yazo duniya, taji k'aunar sa ta mamaye mata ilahirin zuciyarta, tanajin jinsa har ranta...

Ranar suna yaro yaci *Abdulmajeed* anyi shagali an kashe nera dan Auwal yayi rawar gani Alhaji ma yayi tashi yace jikan farine, Baba ma yayi nashi k'ok'arin, sai fatan Allah ya raya Abdool, su Firdausi da Asma'u uwar da sune k'irjin biki, Hajia kam ko kallo basu isheta ba dan da alama k'iyayyar uwar ta shafi d'an.

Auwal kuwa duk sati yana Argungu gurin d'ansa mai kama dashi fatar CE kawai baiyi hasken Baban ba, kuma yafi uwar haske yana nan dai tsakiya, Mama kuwa sai aikin gyaran 'yarta ta ciki da waje aiko tuni ta d'auki sheki tun balle bata kusa ga Hajia.

Abdool kuwa kullum yana hannun Asma'u, shan nono kad'ai ke had'ashi da uwarsa, tsabar sonda Asma'u ke mishi ko cikin barci taji kukansa saita farka, Mama tace lallai kuwa ranar da suka koma zai barki da kewa.

Auwal da kanshi ya roki Baba su basu Asma'u, ganin yadda ta shaku da Abdool, kuma tunda tace karatu zatayi, dan tunda taji abinda ya faru da yayarta(ta gayamata abinda ya faru, dan itace abokiyar shawarar ta)tace Aure ba yanzu ba, duk Wanda yazo hak'uri kawai take bashi.

Dak'ar suka shawo kan Baba ya amince, Auwal ya samo musu admission a *Usmanu danfodiyo* ita da Maryam k'anwarsa, Hajia nan habaici ya tashi hadda fad'in saboda an samu banza shine hadda kwaso k'anwa, anga dukiya shine akazo a dangwala, cin fuska dai zalla abinda Ameena ta guda kenan.
[8/6, 8:09 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



_💘💘 where r u my  berries😘 Fatima Bello(momy shatima), Shamsiya Isma'il(fresh daughter) Aisha wanzams (my kanwa) I heart u guys 😘 *#1love#*_




   




    📝 *Episode* 101--105







Saida tayi mai isarta ta godewa Allah, dak'yar ta mik'e idonta sunyi jajir tare da kumbura, sai Kanta dake matsanancin sarawa tsabar kukan da tasha, Abdool ta d'auka wanda shima sai kuka yakeyi ganin mamarsa nayi, dabin bango ta shiga part d'inta, saboda jirinda ke d'ibarta, a parlour ta zube zuciyarta kamar an d'ora mata dutsi dak'yar ta jawo wayarta ta kira Asma'u akan tazo gida, rud'ewa Asma'u tayi jin murya yayarta wata iri tasan ba lafia, kafin tace komai harta tsinke wayar, aiko kota kan Maryam bata bi ba tayi bakin titi tare da taron taxi.

Auwal kuwa yana shiga part d'insa ji yayi duniyar gaba daya tayi mishi zafi, ga rad'ad'in da zuciyarsa ke masa, ga kukan Ameena da Abdool da yake jiyowa yana tab'a masa zuciya, duk da cewa ita mai laifi ce a gareshi amma zuciyarsa ta k'asa yadda da bak'on al'amarin da ya same shi na rabuwa da Ameena, key kawai ya d'auka yabi ta k'ofar baya, normally kowa nada k'ofar baya wacce zai fita ba tare da sanin wani, motar shi ya d'auka ya fita gidan a tsiyace, tafiya kawai yake shi kanshi baisan inda ya dosa ba.

Ganin yanayin da ta isko yayarta ciki ga Abdool sai ihu yake amma uwar ko kallonsa ta k'asa yi balle tayi tunanin shayar da shi, Abdool ta d'auka, abinci ta had'a mishi saida ta tabbatar ya k'oshi sannan ta goyashi ba dad'ewa bacci yayi gaba dashi sai ajiyar zuciya yace, gurin yayarta ta matsa wanda itama jikinta a sanyaye yake, dafata tayi, nan ta d'ago ta kalleta da rinannun idanunta, "Aunty komai yayi tsanani maganin shi Allah, ki d'aure ki gayamin meke faruwa?"

Kama hannayenta duka biyu tayi, bakinta na rawa, sai a lokacin wasu zafafan hawaye suka zubo mata, sharewa tayi, nan ta labartawa k'anwarta duk abinda ya faru bayan wucewar ta makaranta.

"Inalillahi wa'inna ilaihirraji'un" shine kalmar da Asma'u tace maimata tawa iya tashin hankali kenan, yanzu ta fita tabar mata da mijinta lafia, amma kuma cikin k'ank'anin lokaci komai ya canja, farinciki ya koma bak'in ciki, batasan lokacin da hawaye suga zubo mata ba, nanta rungume yayarta sukaci gaba da kuka bamai lallashin wani.

Bankad'o k'ofa akayi da k'arfi, a tare suka d'ago dan ganin wanene, da kallon k'ask'anci ta bisu, ba kowa bace face Hajia "to matsiyata 'yan gadon lalata(sadnaf), me kuke jira yanzu kuma?, ina auren ya k'are ko kuma da sauran zance ne iyye" duk cikin masifa tace maganar.

Saida ta saka full stop sannan Asma'u tace "yi hak'uri Hajia yanzu zamu tafi" tsaki tayi tare da cewa "aikin banza sannan ta fice.

B'angaren Rafia kuwa suna isa part d'in Hajia bayan tayi Jim na mintuna tace "Hajia Bari in tafi zanyi wani aiki" part d'inta ta shiga, wannan gardin ne zaune a kureja amma ya maida kayanshi, wata shu'umar dariya tayi sannan ta d'aga mai babban farcenta "weldone Wizzy aikin ka ya tafi yadda akeso" murmushi kawai yayi ba tare da yace komai ba, bedroom ta shiga sai gata ta fito da rafar 'yan duba, bashi tayi tare da bud'emai k'ofar baya ya ware.

Asma'u ce ta d'ibo musu kayan sawarsu trolley biyu, drop suka d'auka sai k'ofar gida.



************************

Lokacin suka isa dak'ar suka shiga ciki, Mama na tsakar gida tana aiki, Mansur kuma na gyara mata alayyahu, ganin da kaya nik'i-nik'i sannan fuskacinsu a jeme duk sun wani yamutse, yasa tasan ba lafia ba, gaisa sukayi sannan suka shiga ciki, itama wanke hannu tayi tabi bayansu, ba wani boye-boye Asma'u ta gayamata abinda ya faru.

Ba k'aramin tashin hankali ta shiga ba, amma saita daure tace "Allah yasan hakan shi yafi zama mafi Alkhairi" dama tunda k'anwarta ta gayamata halin Hajia da irin wulak'anci da tayi musu, yasa ko sha'awa zuwa gidan bata tab'a yi ba, amma wannan sharrin dame yayi Kama, idan so take a saketa basai ta had'a da sharri ba, dan ta yarda da tarbiyar 'yarta ba zata taba aikata hakan ba koda bada Aure ba balle da Aurenta, Allah ya saka Mata, shine kawai ta fad'a a ranta.

Baba ma daya dawo yaji ba ransa ne yayi mummunan b'aci, musamman sharrin da akayi mata, dama Baba akwai zafi, abin ya bala'in k'ona ransa, fad'a yayi tayi da cewa zaije Sokoto gobe, saida Mama ta tausheshi sannan ya hak'ura, dan tasan idan yaje da wuya ayi mai kyau, amma yace gobe su Hafsat da Usman(k'anwar Mama da d'an kanin babansa) suje su kwaso kaya sannan su anso masa
 takardar 'yarsa.

Auwal kuwa bayan gari yaje bakin ruwa,  a can yayi zamansa dan gari ya riga yayi mishi zafi, nan yayi ta sak'awa da warwarewa har dare bai samo mafita, ganin duhu ya shigo, yasa shi hak'ura ya koma gida.

Hajia kuma ganin har dare ba Auwal ba labarin sa gashi ta kira wayoyinsa a kashe yasa hankalinta tashi, bakin k'ofar part d'insa ta tsaya zaman jiran dawowar sa.

Dai2 part d'insa yaga Hajia, jiki sukwana ya k'arasa gurinta tare da gaida ita, bata ansa sai fad'a data haushi dashi "wai kai Auwalu wane iri yaro kake, kabi ka tada hankalinka akan yarinyar da ta gama cutar da kai, gara ka fiddata a ranka dan kun rigada kun rabu kenan ehe, to garama tun wuri ka yakiceta a ranka ka rungume Ummita dan har nayi magana da hajiyarta nan ba dad'ewa za'ayi bikinku, sannan ka rubuta takardar waccen matsiyaciyar ka kawo min, zan aika mata har gida" Auwal da zuciyarsa ta gama k'ek'ashewa "tau Momy" kawai yace, sannan ya shiga ciki, itama ficewa tayi tana fad'in "daga Allah ya tona mana 'yar iska" tana shiga part d'inta nan ma Maryam ta isko ta had'a kai da guiwa, dan tunda ta dawo Hajia ta fad'a mata abinda ya faru, ta shiga damuwa hadda kukanta dan ta saba da Aunty da Asma'u ga Abdool Son d'inta, ita sam bata yadda aunty zata aikata abinda akace tayi ba, dan tasan ta farin Sani kullum cikin yi musu nasiha take itada akan su tsare mutuncinsu sannan ace ta aikata wannan barnar.

Tsaki Hajia tayi "kwayi kwa gama" sannan ta shige ciki tana mitar halin irin na 'ya'yanta Sam basu biyota ba(ai sun huta basuyi bak'in gado ba) waya ta kira hajia Umma mamarsu Rafia danso take ayi komai cikin lokaci, saboda ta k'ara cusawa Ameena bak'in ciki.

Auwal na shiga ciki jin ba motsin wata halitta ko'ina shiru, sabanin da, koda zai shigo a parlour zai samesu suna kallon sunnah TV wata ran kuwa su kalli zee TV ko kuma su zauna suna hirarsu gwanin sha'awa, Murmushin takaici yayi tare da shigewa ciki, takardar ya rubuta kamar yadda ta buk'ata yakai mata.

Washe gari kamar yadda Abba ya buk'ata haka su Hafsat da Usman Suka taho da babbar motar kwasar kaya, amma me Hajia tace ba wani kaya da zasu kwasa ai danta ne ya saya, haka aka shiga rigima sun nace sai kwasa itama tace basu isa ba, hayaniyar ce ta kawo hankalin mutanen gidan wad'anda duk abinda ya faru basuma San anyi ba sai lokacin.

Ganin rigimar tak'i k'are wa yasa Sani kiran Auwal ya tambayesa nan ya tabbatar kayanta ne ko tsinke bai siya mata ba, da yake a hand's free ya saka kowa yanaji yasa ta basu suka kwasa, tana biyarsu da habaici da bak'ak'en maganganu, ba Wanda ya kulata har suka k'are tun kafin su tambayi takardar 'yarsu ta kawo musu, tare cin mutunci.

Auwal da tun safe ya fita zuwa yayi ya tattara duk wata k'addara tasa ya sayar, banki yaje ya bud'e kid account ya zuba kudin, iya wad'anda zai rike a hannun sa ya rage, bashi ya dawo ba sai goman dare, d'akin sa ya shiga yayi wanka ya kimtsa sannan ya d'auka diary sabo kal, rubuta sosai yayi sannan ya sake rubuta wasik'u har uku, part d'in Hajia yaje yace Maryam ta d'auko mishi key din part d'in Alhaji dan duk wannan ruguntsumin da ake Alhaji bayanan ya tafi umrah, d'auko mishi tayi bud'ewa yayi sannan ya shiga bedroom, wardrobe d'insa ya bud'e wata leda ya saka daga can sama sannan ya rufe ya fito, Maryam ya kira ya bata keys d'in da wasik'a tare da tabbatar mata da ta bawa Hajia zuwa gobe da tau ta ansa masa sannan ta shige ciki.

Washe gari bayan sun gama breakfast ta d'auko wasik'ar ta bama Hajia.

"Lahaula walah k'uwwati illah billah" shine Kalmar da Hajia ta fad'i tare da zubewa k'asa a sume........




_friends ina barar Addu'arku akan wata buk'ata tawa, ina da tabbacin zan samu. Love u all_ 😍 









💄Meryerm Abdool💄
[8/6, 8:15 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



```Wannan page d'in nakune 'yan makarantar madarasatul nurul Islam littahafizil Qur'ani
 Kareem,kabino area,Argungu```🕌

 _Irinsu Nafisa muh'd, Fareeda Nana b/mashaya, Mamu Aliyu, Saudat yahya, Meena dikko, Amina Garba, Bilkis, Hajjo, Aina'u Idris and rest kuna raina koda yaushe#❤❤❤#_







   📝 *Episode* 106-110






Maryam wacce tana mik'awa Hajia sak'on Auwal ta shige bedroom room d'inta, sai jin k'aran fad'uwar abu tayi aiko da gudu ta fito ganin mahaifiyarta kwance ba numfashi yasa tayi Kanta cikin kid'ima tana jijjigata, amma ko alaman tashi batayi ba, aiko da gudu tayi part d'in Rafia tayi sa'a Ayuba nanan, jin abin ya faru yasa suka biyota cikin tashin hankali, Rafia ce tayi Kanta ta rungume ta yayin Auwal yace a kawo ruwa, da sauri Maryam ta kawo ruwa Shafa mata akayi, nan take ta sauke ajiyar zuciya, bud'e ido tayi a hankali ta sauke a kansu sannan ta maida kallonta ga takardar da ke jinke a hannunta, wani kuka ta rushe dashi "why Auwal, meyasa zakayimin haka".

Ayuba ne yayi k'arfin halin cewa " Momy me kuma Auwal yayi miki?" Takardar ta mik'a masa, ansa yayi tare da karantawa a fili.

_"kiyi hak'uri momynah nasan koda wasik'ata zata sameki ba zakiyi farinciki da ita ba, sai ba yadda zanyi dole ce tasa zan barku, bazan iya ci gaba da zama kusa da inda zanji labarin Ameena ba, alhalin bama tare, dole zan nisanta kaina daku da kowa nawa, kada  ku wahalda kanku nemana danni kaina bansan inda na dosa ba, pls kiyafemin Momy kiyimin fatan Alkhairi, kada ki tsinemin, idan kikayi haka rayuwa zata ga garari, ma'assalam_

D'anki *Auwal Sada*

Koda ya gama karantawa zuface ke keto masa duk da fanka da na'oural sanyi dake aiki, yama kasa magana, Maryam tuni hawaye ya wanke mata fuskarta, Rafia ma tashin hankali taf fuskarta dan batasan haka abin zai zama ba.

Momy kuwa sai sambatu takeyi tana kiran Auwal dan Momy akwai son d'iya, hakan yasa wutar k'iyayyar Ameena da d'anta ta k'ara ruruwa a ranta dan duka ita d'orama laifi, wai ba a banza tabar Auwal ba, wannan son ya wuce hankali, tunda harya kasa ganin girman laifinta ya barsu saboda ita.

Nan dai suka wuni cikin jimami ga tsoro fal ranta na idan Alhaji ya dawo me zatace masa, gashi gobe Suke tsumayen dawowar sa, dak'yar ta kira Maman su Rafia ta gayamata abinda ya faru, Ummita kuwa da raji rud'ewa tayi, dan ita harta fara shirye,-shiryen Amarcewa(tab to ai sai aje a rungumi big sowie Ummita) lol.




****************************



*Washe gari*


*12:00pm.........*

Jirginsu Alhaji Sada ya sauk'a a Sakkwato birnin shehu, Sani, Hajia, Maryam ne sukaje tarbonsa, yayi farincikin ganinsu amma yafi k'osawa yaje yaga 'yan jikokinsa musamman Abdool dan yaron ya shege masa ransa, sonsa yake sosai bada wasa ba, saidai baya nunawa gudun tashin hankali, sanda suka isa kowa saida yazo gaidashi amma ba Auwal da familyn sa, k'asa daurewa yayi ya tambaya ko sunyi tafiya ne.

Ganin yayi kowa yayi shiru, hakan yasa jikinsa yin sanyi dan yafi ba, lafiya a jikinsa, Hajia ce tayi k'arfin halin cewa "Alhaji ka bari kaci abinci ka huta tukunna sai ayi maka bayanin komai" jiki a sanyaye tayi maganar.

Ba shida zabi hakan akayi bayan yaci ya huta haka ta kora masa bayanin komai daya faru, har zuwa tafiyar Auwal, shiru yayi nad'an lokaci kafin ya dago idonsa da suka rine sukayi ja ya nuna Hajia da yatsa.

"Ke bani mamaki kaltume duk da babu mamaki in ankai la'akari da rashin son da kike nunama Ameena, tau burinki ya cika Ameena tabar miki gida Auwal ma ya bita yanzu sai kije ki zauna da wad'anda kikeso" ta bud'e baki zatayi magana, ya dakatar da ita "bannson jin komai daga gareki tashi ki tafi" ya fad'a yana nuna mata k'ofa dama daga ita sai shine a d'akin, tashi tayi ta fice jiki ba k'wari, dan tasan hak'uri irin na Alhaji duk yakai gayin fad'a to an kureshi ne, amma ai bai kamata yaga laifinta ba, komai ya faru au Ameena ce sila, itakam wannan shine adakeka a hanaka kuka.

Alhaji sai safa da marwa yakeyi ransa a jagule, tabbas Auwal bai kyauta ba, koma meye ya faru bai kamata yabar gida, duk da iya cuta an Riga an cucesa, dan wannan dagaji sharri ne akayi mata, dan yasan Ameena ba zata tab'a aikata wannan danyen aikin ba, kuma yasan Hajia nada tsananin zafi da ak'ida Mara tushe da asali, amma yasan ba zata aikatawa Ameena wannan aikin ba, to abin tambaya anan waye ya aikata? Babu ansa "Allah ya sawwaka" ya fad'a a fili, dama iya zaman da Allah ya d'ibar musu kenan, koda wannan koba sa wannan ba tabbas sai sun rabu dai2 wannan lokacin

 Bud'e wardrobe yayi dan d'aukar Abu kawai sai Leda ta 
Fad'o takardune na bud'e account da komai daya k'unsa sai diary da wasik'u guda biyu, bud'e d'ayar yayi yaga ansa *zuwa ga Ameena* rufewa yayi ya bud'e d'ayar Wanda ta kasance tashi ce.

Shima dai ban hak'urin ne da Neman gafara, sai Amanar *Abdulmajeed* daya d'anka masa da kuma bayanin diary da information na Account ya aje hannunsa har sai Abdool ya mallaki hankalinsa ya mallaka masa, sai wasik'a da yake rokon ya bayar a kaiwa Ameena, bayan ya gama karantawa yace "na yafeka Auwal duk da baka kyauta min a matsayina na mahaifi ba, wannan dalilin bai isa yada ka tafi ba, amma ba komai Allah ya tsareka a duk inda kaje ya kuma dawo mana dakai lafia wuri kusa kazo ka kula da d'anka da kanka".......

B'angaren Ameena kuwa kokai waye idan ka ganta dole ka tausaya mata, ta fita hayyacinta gaba d'aya tayi bak'i ta rame sosai kullum cikin kuka take musamman ganin an kwaso kayanta, yanzu shikenan ta zama bazawara, abin tafi tsana a rayuwarta ada sai takega duk matar da ta zama bazawara a dalilin saki to laifinta ne, ita tayi abinda yasa aka saketa, amma a yanzu ta gane ba haka abin yake k'addara wacce bata wuce fata, ta gane Ashe ba matar da ke son a saketa koda kuwa ita tayi laifi, balle irin su da basuji basu gani(to in banda Ameena wake so yayi aure yau gobe ace ya dawo gidansu ai saida k'addara wacce ba'a fata Allah ya kyauta).

Ga Abdool kullum kukan Dadynsa yakeyi Abu duk ya had'e yayi mata yawa, danma ga Asma'u kusa ita ke d'auke masa kewar Dadynsa, Mama da Baba kullum cikin kwantar mata da hankali suke, Mansur kullum yana cikin kawo Abdool kayan wasa da kayan kwalama irin na yara idan yaje School 'yan Kud'insa duk can suke tafiya duk dan su kwantar Mata da hankali, Firdausi ma tazo lokacin da taji, itama Sam abin baiyi Mata dad'i, musamman ma sharrin yafi komai cin rai, inda Allah ya sota duk Wanda yaji kai tsaye yake k'aryatawa, saboda sanin halin kirkinta(tau zama dan kwarai Nada rana dan wata rana ake gujewa mu d'aure mu k'are mutuncinmu).

Alhaji washe gari yazo Argungu, Baba ya tarbesa kamar ba abinda ya faru dan yasan ba laifinsa bane, hak'uri ya k'ara bashi akan abinda ya faru, tare da tabbatar masa Sam koda abin ya faru bashi gari, saida ya dawo yakeji nan yake gayamai tafiyar Auwal, nan Baba ya jajantamai tare da fatar Allah ya bayyana shi, tsaraba  Ameena da Abdool ya fito dasu hadda ma Asma'u yayima dan yasan tana gidan lokacin da ya tafi, tare da kayan buk'atar Ameena da Abdool na yau da kullum, dan yayi Alkawarin kula dasu har sai tayi Aure.

Baba saida Alhaji ya nuna b'acin ransa tukun ya anshi kayan dan yace bazai Ansa ba, saida Alhaji yace bai hak'ura da abin da yw faru ba kenan, ai sun Riga sun zama d'aya tunda har rabo ya shiga tsakani, hakan dai dole ya ansa, har Mama saida ta fito suka gaisa sannan ya bata hak'uri itama.

Lokacin da Ameena tazo nasiha sosai yayi mata tare da bata hak'uri sannan ya tabbatar mata har yanzu shi ubane gareta komai ya sameta ta sanar da shi, kud'i ya bata tare da wasik'ar Auwal, saida yayi mata fad'a sannan ta Ansa, haka ya tafi yana tausayawa mata dan bazaiso hakan ra faru akan Maryam ba.

Sosai ya k'ara daraja da girma akan idon Ameena da iyayenta.

Sai dare ta d'auko wasik'ar Auwal da tunda aka bata ta kaita ta ajiye, dan ita yanzu lamarin maza ya fita Kanta kuma duk haushi Suke bata(dama ai duk macen da aka saka tofa duk maza haushi zasu rik'a bata zata d'auka duk Wanda ta aura zai iya sakinta komai soyayyar da yake mata kuwa.

Bud'ewa tayi ta fara karantawa..

_"gareki masoyiyata tahar abada, Ameena nasan zanyi bak'i a gurin ki dan duk wacce aka saka saki uku kai tsaye tabbas zata girgiza kuma zata tsani wannan mijin, harga Allah duk da abinda idanuwana suka ganemin, zuciyata ta k'asa yadda da abinda wani barinta ke gayamata akanki, saidai ki sani dole ne na shiga rud'u dan nina gani ba ji nayi ba, amma inaso ki d'auki wannan a matsayin k'addarar muce, ki tausayawamin ki tausayawa d'ana *Abdulmajeed* ki zame masa uwa da uba agareshi ki bashi dukkanin tarbiya ta gari, dan kuwa ke uwace ta gari a gareshi, pls kada kibar rayuwarsa tayi garari koda kinyi aure ne, ki zama majib'incin lamurransa a dai2 gab'ar da ya rasa dukannin kulawata a matsayina na uba agareshi, na tafi bawai dan bana k'aunar sa ba Aa sai dan samun maslaha a gareni, ina miki fatan Alkhairi, ki saka a ranki zan rayu da sonki a kowanne second na rayuwa"._

*naki Auwal Sada*.


Koda ta gama karantawa hawaye sun wanke mata fuska, zuciyarta sai rad'ad'i take mata da suya, Abdool ta rungume tsam a k'irjinta tana tausayawa rayuwarsa, yaro k'arami ko wace rayuwa zaiyi nan gaba.

"Allahumma ajirni fi musiba"..................






*ina mai Baku hak'uri sa babbar murya, akan jina da kukayi shiru kwana biyu, na shiga busy ne, amma Ku sani kuna raina#1❤#*








💄Meryerm Abdool💄
[8/8, 7:45 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)




👌🏻 *d best way 2 love is love for d sake of Allah. And tell d one u love d fact about him, show him d true faith, never tell him lies just 2 make him happy, hmm day he/she find d true u will become his biggest enemy, may Allahu (S.W.T) show us true way of life ameen👏🏽*

Small quote👌🏻



_Aunty Khaleesat Haiydar ur r so grateful, Aunty Ummi shatu wishing oll d best in ur exams👌🏻_    #heart u aunty's😘#



   



     📝 *Episode* 111--115




Saida aka kai ruwa rana kafin Baba ya yadda da komawar Asma'u makaranta, dan yace ta dawo tayi NCE kawai, dak'yar ya amince amma da sharadin zata kare mutuncin Kanta, ranar da zata tafi da kuka suka rabu da Abdool dan lik'e mata yayi sai taje dashi, Mansur ya fita dashi sannan ta samu ta wuce kice da kewar gida da Son d'inta, dan tasan zatayi missing nashi, Hostel ta koma da zama inda ta dage da karatunta baji ba gani, tayi mamakin rashin ganin Maryam sai daga baya takeji ga k'awayensu an canja Mata school, Hajia ce tasa aka canja mata, a cewarta kada Asma'u ta lalata mata d'iya, tunda tasan muddin suna school d'aya Maryam ba fita hanyar Asma'u zatayi ba, hakanan bataso aka maida ita nursing.

B'angare guda kuwa shakuwa ce ta k'ara shiga tsakanin Asma'u da Abdulrahim kullum zaka Kansu tare yana koya mata karatu musamman yanzu data dawo hostel dama shi a hostel yake dan ba dan garin bane, tun basujin komai a ransu game da juna har takai yanzu sunajin zukatansu sunaso su zama d'aya.

( *Tofah wai waye Abdulrahim?*)


Abdulrahim dan asalin kilgori ne wadda ke k'arkashin Yabo local government dake jahar Sokoto, D'ane ga Malam Umar wadda akafi Sani da Ard'o, sarautace irin ta Fulani wato mai gari kenan, Ard'o ya zamo mai garin kilgori ne bayan rasuwar mahaifinsa wato tsohon Ard'o, yana da matar Aure d'aya Hadizatu wacce akafi sani da Iya Hari, auren zumunci ne akayi musu, Ard'o mutum ne na mutane mai sanyin hali, kowa nasane, yayin Iya Hari ta kasance masifaffiyar mace, Mara mutunci kullum cikin masifa take da bala'i, tunda Ard'o ya aureta bai taba k'arda dad'in ta ba, anadai zaune ne zaman hak'uri, bai isa ya sata tayi ba haka bai isa ya hanata ta hanu ba, amma a haka sukaci gaba da zama da yake Allah ya zuba mishi hak'uri, komai tayi kauda kai yake kamar bai gani ba, sunada 'ya'ya uku Abdulrahim ne na d'aya Wanda take kira da Modibbo saboda kasancewarsa d'an fari, sai Lantana wacce ake kira Lanti sai Aisha wacce ake kira Shatu, sam halin Aisha da Abdulrahim ba irin nata bane halin babansu suka d'auko, kai harma kamar dansu farare ne sirara dogeye, kyawawa dasu, yayin da lantana ta biyo kama da halin uwar sak.

Tun Abdulrahim yana k'arami yake sha'awar boko, mahaifinsa kuwa ganin yana sha'awa yasa ya sakashi A yabo dan lokacin ba'ayi anan garinsu ba, haka yake tafiya kullum zuwa yabo don daga k'arshe da mahaifinsa yaga wahalar zatayi yawa sai ya had'ashi da wani malami, yake zama gidansa sai Hutu yake dawowa, Wanda hakan Sam baiyima Iya Hari dad'i ba, rigima ta tada akan ba inda zaiye ya tsaya yayi kiwo in zaiyi, rokonta yayi tayi akan ta barshi, amma tak'i amincewa, dama Abdulrahim baisan dad'in ta ba Sam, dan bata janshi a jiki, wai d'an fari ne, ba wani sabo a tsakaninsu yafi sabawa da Ard'o, haka kuwa ta dage akan ba inda zaije, saida Ard'o ya nuna b'acin ran yaje ya gayama iyayenta, ganin tunda take dashi bai taba nuna Mata bacin ransa haka ba balle har aje ga kai k'ara yasa ta shiga taitayinta ta amince  akan dole.

Hakan Abdulrahim yayi ta karatunsa tun daga primary har secondary duk anan Yabo yayi su, gashi kanshi naja(dama Fulani akwai kai) tunda ya fara harya k'are bai tab'a yin na 3 saidai na 1 ko 2 hakan yasa malamansu bawa Ard'o shawarar kaishi university hakan kuwa ta kasance inda yake karatun medicine, ita dai Iya Hari akan dole yake karatun badon son ranta ba, dan ita gani take lalata yara kawai boko keyi, shiyasa ta hana a saka Lanti Shatu, Abdulrahim kuwa ya goge idan ka ganshi bakace dan k'auyen bane, hakan yasa 'yan matan garin kowa sonsa take, 'yar k'anwar Iya Hari ganin kowa sonsa yasa hankalinta ya tashi, ba kunya taje ta gayama Iya Hari itafa shi takeso, dama itama sunada burin hakan itada k'anwarta na had'a su aure, nanta tabbatar mata da Abdulrahim baida matar aure sai ita, shikam Abdulrahim Sam yarinyar bata mishi ba saboda batada nutsuwa Kanta rawa yake, itakam Saude sai d'aga kai take a garin da tak'ama zata auri d'an boko.


_wannan kenan_



B'angaren Ameena kuwa ganin Asma'u ta koma makaranta, Mansur ma ya koma dake boarding school yake, gidan ba dad'i duk da Asma'u na zuwa duk k'arshen sati, yasa tayima Baba magana tanason itama ta koma makaranta bai musa mata ba, saidai yake ba zataje nursing kamar yadda ta buk'ata ba, dan ko lokacin da Auwal ya kawo mata form abinta ta cike kenan, wannan burinta ne tun suna secondary, amma dole ta hak'ura da ita dan dalilan da Baba ya gayamata na hanata zuwa wani gari kara2, ya gayamata 'yan uwansa zaginsa zasuyi suce a maimakon yayi mata Aure ya turata karuwanci, hakan yasa ta hak'ura zatayi NCE anan *Adamu Augie college of Education Argungu* da kanshi ya anso mata form ta cike inda aka bata Agric/education, nan Baba ya sakata gaba yayi mata nasiha akan taci gaba da tsare mutuncinta tayi abinda ya kaita kawai banda bin k'awaye barkatai, itama Mama tayi tata, nan Ameena ta fara zuwa school cikin nasara, ba abinda takeyi sai kara2 ba ruwanta da kowa haka zatayi shigarta ta kamala taje data gama lec, ba wani tsaye-tsaye direct gida take wucewa dama can daga gida sai makaranta, sai kuma bikin yan uwa ko barka shima akan tilas take zuwa kada ta yanke zumunci, saidai abinda ke kona mata rai data had'u da taubasanta yanzu zasu fara takanarta da kiranta bazawara ina zawarawanta, yake kawai take musu amma Kalmar ba k'aramin k'onata takeyi ba, saidai ba yadda zatayi k'addara ta riga fata, shisa sam bata cika son shiga mutane ba.

Zuwa yanzu ta kwantar da hankalinta ta maida kamarta ta kuma rungume k'addarar ta, saidai Aure ya fita ranta gaba d'aya, shiyasa duk Wanda yazo da sunan yana sonta hak'uri kawai take bashi dan bataji zatayi aure yanzu.

Lokaci zuwa lokaci takan tuna Auwal da rayuwarsu ta baya, koyana ina yanzu oho!, Abdool zuwa yanzu ya manta da Dadynsa yayinda ya d'auki Baba a matsayin Babansa, yana 1¼ ta yayesa dan komai ci yake ga kafafu har gudu yake hak'ora ne kawai bai cika ba, bata sha wahala a yayensa ba, dan wani sa'in sauya wuni baisha ba sai dare, tunda ta aka yayesa ya koma hannun Mama can yake baccinsa.

Ta dage sosai da karatunta k'awa d'aya tayi mai suna Sakina mungadi, department d'insu d'aya, tasu ce tazo d'aya shiyasa sukayi k'awance dan itama sakina ba ruwanta da sha'anin kowa abinda ya kaita kawai takeyi(a kowanne lokaci muyi k'ok'ari muyi mu'amala da mutanen kwarai, dan kuwa har lahira kana tare da abinda kakeso, kuma zama da mad'auki kanwa shika haddasa farin kai) a hostel take zaune dan a bk suke zaune da iyayenta, kullum suna tare idan ka gansu gwanin sha'awa cikin shiga ta kamala, Sakina tasan komai gane da Ameena dan har gidansu tana zuwa, tana kuma son Abdool sosai, haka rayuwa taci gaba da tafiya yau dad'i gobe sabanin haka, rayuwar duniya kenan haka ta gada, a gefe d'aya kuma Ameena naci gaba da kasuwancinta kuma duk k'arshe wata har Alhaji Sada na zuwa dubasu da hidima sosai kamar yadda yayi alkawari, su Baba ma na iya k'ok'arin su, so batada matsala a yanzu saidai wacce ba'a rasa ba.....

Suna NCE 2 wani malami na education ya basu Assignment to group discussion ne, kuma each group ten people ne, shiya rabasu da kanshi, from d different faculty, anan aka hadasu da wani Yusuf normally tasanshi saboda suna had'uwa GSE da EDU saidai magana bata tab'a had'asu ba, shine team leader nasu ita kuma assistant, shi d'an ENG/ISS, wannan Had'uwarne ta zama sanadin shakuwa tsakaninta da Yusuf, dan Yusuf social man ne, kokai waye ka zauna dashi sati yayi wuya Baku saba ba, dan akwai barkwanci gareshi burinshi bai wuce yasa mutane cikin farinciki ba, Sam shima ba ruwan sa da shashanci, kara2 kawai ya saka gaba kuma ga kwakwalwarsa tana ja ba dama, dan 3point kawai yake bugu ga G.P, hakan yasa ya saba dasu Ameena ko bayan gama assignment d'insu saiya kasance duk lokacin da basu da lectures sukan zauna suyi discussion a tsakaninsu based on their studies.

Yauma Zaune suke suna tattaunawa sai wayanta tayi k'ara, dauka tayi basuji me aka fad'a a d'ayan b'angaren, sun daiji tace.

"Subhanallah Asma'u meya sameshi?"

Still suka k'ara jin tace "tau ganinan zuwa" mik'ewa tayi a rud'e, tare da musu zataje gida, amma yanzu zata dawo, Sakina CE ta tambayeta meya faru, nan take gayamata Abdool ba lafia.

"Aa to inzo muje kawai".

Murmushi tayi Mata " kada ki damu Besty is not so worst fa, nima I will be back soon inshaa Allah " sannan ta wuce.

Duka sun tausaya mata ganin yadda ta rude har Yusuf ke tambayarta halan k'aninta ne, nan Sakina ta gayamishi a yaronta, ba k'aramin mamikine ya Kama shi ba danshi duk kallon budurwa yake mata ba Wanda zai ganta yace tanada aure hadda d'a, yace

"Amma fa bantaba tunanin matar aure bace, duk da kuwa naga tanada kamun kai".

"Hakane amma yanzu bata tare da mijin" nan dai Sakina ta bashi labarinta, sosai ya tausaya mata, hadda k'wallarsa, tare da sak'awa ransa wani tunani.


*life goes on......*


Kwana d'aya, sati, wata, shekara, haka shekaru keta tafiya a guje kamar ana kora su, zuwa yanzu Abdulrahim ya kammala karatunsa inda yake internship a nan Uduth, Asma'u kuwa tana rubuta final exam nata, soyayya suke gudanarwa cikin tsafta, dan sun dad'e da bayyanawa juna sirrin zuciyarsu, jira kawai suke Asma'u ta kammala karatunta su sanar da magabatansu, ayi taimaka a aurar dasu. Lol

Ayau ne ta kammala jarabawarta cikin nasara, kuma a yaune kowanne su ya shirya tsaf ya doshi familyn sa dan fallasa sirrin da ke ransa,  dan cikar burin zukatansu, lokacin da Abdulrahim yaje da maganar gidansu Ard'o ya goyamasa baya d'ari bisa d'ari, dan yasan d'ansa bazai zabo abinda zai cutar dashi ba, dan haka ya bashi tabbacin a satin zasuje har shi A Argungu domin ganawa da iyayenta.

Tashin hankali Wanda ba'a sa mishi rana, ai Iya Hari dukane kawai bata mishi ba, amma ta inda take shiga ba tanan take fita ba, tas tayi masa ta kuma tabbatar masa baida matar aure inba Saude ba, dan bai isa ya banna mata lokaci a banza ba dole ya Aureta(Niko nace kamar shi yace ta zauna).

B'angaren Ameena na kuwa ta kammala karatunta cikin nasara, harta anshi resi d'in ta, Abdool kuwa an girma dan yanzu yakai shekara 5 yana nursery 2 a Emirate dake garin Argungu, gashi da k'ok'ari sosai sai dan Neman wayo da surutu har tsoro yakeba Ameena idan ya fad'i wata magana kamar wani Babba, Niko ya had'u da Asma'u aifa shikenan d'an biyemasa takeyi suyi tayi, itadai Ameena kallo kawai nata tana mamakin wannan shak'uwa dake tsakaninsu.....

Asma'u yayarta ta fara sanar ma soyayyarta da Abdulrahim, Ameena tayi farinciki da jin k'anwar tata ta had'u da *muradin ranta* (maman ussey), amma saida tayi Mata mitar k'in fad'a mata tun farkon soyayyar sai yanzu take gayamata, hak'uri ta bata tare da had'e hannayenta biyu guri d'aya.

Dukan wasa takai mata tare da Kama hannayenta ta maida ita kan bed "ki rage zurfin ciki kanwata kada ya cutar dake wata rana"

Tana dariya tace "yes Aunty ur wish...." Dariya sukayi baki d'aya dai shigowar Abdool shima ya dane gado tare da kamu rungume Asma'u tayi tare da jan guntun hancinsa tace..

"Clever boy kasan me akewa dariya ne hala?"

"Yes tunda Aunty da Mami na dariya nasan suna farinciki ne.." Nan dariyar sukayi gaba d'aya suna mamakin wayo irin na yaron...

Ameena nace taje ta sanar da Babban su game da maganar Asma'u, har da maganan zuwan su Ard'o dan Abdulrahim ya kirata ya gayamata suna zuwa cikin satin.

B'ata rai taga Baban nasu yayi yace ta kira Asma'u, jiki sanyaye ta fita, tare suka dawo.

Asma'u ya kira sunanta cikin kaushin murya, bai jira amsawarta ba yaci gaba da magana.

"Yayarki tazo min da zancen yaron da kike so, yanzu abunda ya faru da 'yar uwarki bai zama izina gareki ba, har kike tunanin Auren 'yan jahar Sakkwato, to bama wannan ba na Riga mun gama magana da Malam Musa zamu had'aku Aure da d'an wajensa Mustapha" tunda ya fara magana Kanta na k'asa haka itama Ameena, harda hawayenta jin anyi mata fami akan ciwon ta.

Sannan yaci gaba "dan haka inaso ki kira wannan yaron ki gayamishi karma yazo da iyayensa dan an Riga anyi miki miji, kinji ko?" Kai ta girgiza masa alaman eh.

"Yawwa kuje Allah yayi muku Albarka" Ameen suka ansa sannan suka wuce, bayan fitarsu inna dake zaune tunda aka fara maganar bata ce komai ba.

"Amma Alhaji kana gani anyiwa yarinyar nan ad......." Katsesa yayi.

"Ya isa Habeeba wannan ba huruminki bane" shiru tayi da bakinta tare da fadin "Allah ya kyauta"...

K'arshen tashin Asma'u ta shiga, rabuwa da masoyi da rana tsaka siddin akwai wahala, sai dai ya zama wajibi gareta tabi umarnin babanta, Ameena da itama d'aure kawai take amma k'anwar tata ta bata tausayi tasan zafin rabuwa, dafata tayi tana tare da k'arfafa mata guiwa(dan uwa rabin jiki, Allah ya barmu da yan uwanmu).

Wayarta ta d'akko ta kirasa amma ina bata zuwa saboda matsalar network, ko ranar da ya kirata saida yaje kan titi dan basuda network cikin gari, haka taita kira tak'i shiga, tsawon kwanaki uku amma ba labari, ana hudun kuma tace bama zata kira ba.

 Ard'o kuma duk bala'inda iya Hari yi yayi kamar bai san tanayi ba, Sam bai yarda da tarbiyar Saude ba, kuma bazaiyima danshi auren dole ba, haka suka shirya tsaf  shida Malam Garba  da k'annensa guda biyu sai Abdulrahim suka doshi hanyar Argungu ba tare da sanin Iya Hari ba,  Abdulrahim yaso ya kira Asma'u ya gayamata sai kuma yace kawai bari ya bata surprise.

Basu sha wahala ba gurin gane gidan dan sunbi kwatancen da Asma'u tayi, har k'ofar gida suka isa da motar da yake ta Abdulrahim CE, sunyi sa'a sun samu Baba k'ofar gida tarba ta karamci yayi musu, kamar yasan da zuwansu bayan sun gaisa sukayi mishi bayanin meke tafe dasu, mamaki ya kashe shi wato shi yarinyar zata renawa hankali, tambayan Abdulrahim yayi akan bata kirasa ta gayamai komai ba yace eh bata kirasa ba(kusrensa bai fad'a masa sunada matsalar network ba).

Gyaran murya yayi Sam bai nuna musu b'acin ransa ba "ah naji mi a tahe daku, idan a shirye kuke bani da buk'atar komai daga gareku sadaki kawai zaku bani a d'aure Auren yanzu" cikin mamaki suka shiga kallon juna kamar 'yarda aka gaji da ita.

Kamar yasan me sukewa mamaki yace "ko d'aya ban gajia da ita ba saidai ta zabi abinda takeso dan haka shi za'ayi Mata, kuma in Baku taho da niyyan aure ba to Ku tashi Ku tafi abinku, amma kai kar in sake ji ko ganin kafarka a gidana ko ka kira yata, ka fita hanyar ta gaba d'aya" ya fad'a tare da nuna Abdulrahim.

Duk ya k'ara d'aure musu kai, haka malam Garba ya Zare dubu 20 ya bashi ansa yayi tare da mik'ewa 10 ya d'auka na Sadaki 2 na goro, ya maida musu da saura, cikin k'ank'anin lokaci sai gashi da goro da wasu mutane nan take akayi Addu'a aka d'aura Aure, duk wannan bidirin da ake cikin gida basusan meke faruwa ba sun dai San yayi bak'i amma basusan su waye ba.

Nan yace su jira ya fito musu da Amaryarsu su wuce da ita, sudai kallonsa kawai suke mamakin duniya ya ishesu Abu kamar tatsuniya, ciki ya shiga tare da d'aure fuska tamau ya fara kwalawa Asma'u kira kamar hauka.

A tare suka fito ita Mama Ameena suma cikin mamakin kiran.

"Asma'u ungu wannan" ya mik'a mata kud'in, ansa tayi jiki a sab'ule.

"Sadakinki na inaso ki shiga ciki ki d'auko mayafinki Angonki na waje yana jiranki, saidai inaso ki sani tunda kin zabi Abdulrahim akanmu to daga yau bamu bake, baki sammu ba haka muma bamu sanki, kada ki kuskura kiyi tunanin mu ko tunanin tahowa inda muke, mun yafe masa ke har lahira" ba Asma'u kad'ai ba har Mama da Ameena saida kalamansa suka girgiza su, sai yanzu ta gane kuskuren ta na rashin fad'a mishi, ita kuma taki fad'i gudun matsala, Ashe hakan babbar matsala zai haifar mata.

Cikin sheshshekar kuka ta isa gabansa ta duka da duka gwuiwarta, bakin ta na rawa "Baba don....." Katseta yayi

"Kul kada ki yadda kice komai kiyi kawai yadda nicce miki" rik'e mishi kafafu tayi tana gunshekar kuka, Ameena kukan take haka Mama, Don tafi kowa sanin halin mijinta idan ransa ya b'aci Sam bayaji baya gani, zuciyarsa rufewa take.


Ameena ma ta bud'e baki zatayi magana ya hanata, haka Asma'u ta rarrafa inda Mama ta rungume ta itama Ameena zuwa tayi ta rungume su, suna haka saiga Mansur ya d'auko Abdool daga school, a cikin wanga yanayi suka isko su ga Baba tsaye sai huci yake.

Da gudu Abdool ya yaje ya rungume su shima yana kuka

"Mama kukan mi kukayi, Aunty kema kuka na kikayi, Mami kema" yana tambayan su yana yi shima gwanin tausayi.

Baba ganin zuciyarsa naso ta karaya yasa ya shiga sa kanshi ya d'akko mata hijab d'inta, ya saka mata ya jata, su mama na riketa suna magiya suna komai a banza, Mansur shima tuni hawaye suka wanke mishi fuska, Abdool shima rike ta yayi GAM.

"Baba ina zaka kai Aunty?"

"Abdulmajeed, Aunty bata buk'atar Ku, zan kaita inda wad'anda take buk'ata" ya fad'a tare da banbareshi ya mik'a ma Ameena, sannan yayi waje da Asma'u, Abdool sai kuka yake yana kiran "Aunty" amma Sam bata bai saura ra ba, haka magiyar su Mama suna kika duk bai saurara ba.

Yana fita bai zame ko'ina ba, sai cikin motar ya turata tare da basu Umarnin su wuce, anan su Ard'o  suka fahimci da matsala, suka shiga bashi hak'uri akan ya tsaya a sananta, amma Sam yak'i sauran su, saima kashedi da yaka k'ara yi na karta sake ta tako kafarta gurin su, tare sa gayamusu ya yafe musu ita har lahira, ganin ransa ya gama b'aci yasa suka rubuta no- da garinda Suke idan ya wuce dan Allah ya kirasu, sannan sukaje mota suka tafi...

Asma'u na ganin an tada mota ta k'ara rushewa da wani irin matsanancin kuka................



        🤦🏽‍♀🙆🏾🙆🏾  



_Masoyan Abdulmajeed INA alfahari daku aduk inda kuke, pls kuci gaba da karfafa mini #ILVMNM❤guys# keep fallowing_






💄Meryerm Abdool💄
[8/9, 6:17 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)





*Yakai d'an Adam meye tak'amarka/ki, meye alfaharin da kake/kike, meye fad'in ran naki/ka, meye d'agawar taki/ki, keda/kaida farkonka/ki ya kasance k'azantaccin ruwa, tsakiyarki/ki fitsari da kashi, k'arshenki/ka abincin tsutsa, mushe to meye abun jinkai da nuna isa.*

Nasiha ce👌🏻




_bazan gaji da gode muku ba, a zahirin gaskiya kune ni haka nice Ku, sai daku zanyi rubutu wato masoyana masu bani k'arfin gwiwa akan rubutuna, ina alfahari daku, ina rokon Allah yaci gaba da bani damar da zan rubuta abinda zai sakaku nishadi ya kuma amfanar da Ku, #heart u ❤ guys# ina k'aunarku a duk inda kuke #double love😍#_





  📝 *Episode* 116-120





Tunda suka d'auki hanya, take kuka bil hakk'i da gaskiya, kuka take mai tab'a zuciyar mai sauraro, suma mutane cikin motar duk zuciyoyinsu a tsince suke, tausayin yarinyar ya lullub'e musu zuciya, shiru kake ji ba abinda ke tashi sai sautin kukanta, ba Wanda yayi yunk'urin dakatar da ita dan wani lokaci kuka rahama kana jin sauk'i a ranka, sanda tayi mai isarta, sannan ta tsagaita, hakan yasa Ard'o fara bata baki.

"Kiyi hakur'i 'yata duk da bansan ainihin abin da kikayima mahaifinki ba, yayi miki wanga hukunci, a gaskiya hukuncin yayi tsauri, saidai ki Sani su iyaye komai suka yima d'ansu to ya zama dole yayi hak'uri dasu kuma yayi musu biyayya mudin baici karo da Umarnin ubangiji ba,  saboda sun riga sun gama dashi tunda suka haifesa, inaso ki rik'eni a matsayin mahaifi a gareki ni kuma nayi miki alkawarin zan zamo uba a gareki, kuma bawai ina nufin kibar iyayenki ba aa sunanan a iyayenki ba Wanda ya isa ya maye gurbinsu a gareki, kuma inaso ki d'age da Addu'a Allah ya sassauto zuciyar mahaifinki ya yafe miki kuma ya nemeki, muma zamu tayaki da Addu'a inshaa Allah".

Sosai taji dad'in maganar Ard'o, hakan yasa hankalinta yad'an kwanta, ganin tayi sa'ar suruki na gari, cikin nutsuwa ta gayamusu abinda ya faru, sun jinjina abun a ransu tare da  gayamusu kuskurensu daga ita har Abdulrahim d'in, sannan kowa ya bata baki da kalamai masu dad'i, tare da gaya mata ta d'aukeshi a matsayin k'addararta domin rabon ayi auren ne yasa hakan ta faru, tare da sanya ma Auren Albarka, Abdulrahim dake jan motar shima jiki a sanyaye duk sonsa da Asma'u baiso Auren su ya kasance haka ba, amma ba yadda zasuyi dama tun ran gini tun ran zane sai fatar Allah yasan hakan shine mafi Alkhairi a garesu, Ard'o ko tuni yaji yarinyar ta kwanta masa a rai da alama zatayi hak'uri, haka dai suka doshi kilgori kowa da abinda yake sak'awa a ransa, kowa zuciyarsa ba dad'i......




***********************

Baba kuwa yana ganin sunja mota ya buga babbar rigarsa yayi cikin gida, anan ya jefar da takardar da suka bashi nan iska yayi gaba da ita, yanda ya barsu haka ya samesu suna kuka, kallonsu yayi cikin b'acin rai yace.

"Yanzu kunaga banyi muku dai2 ba ko? Baku dubi irin abin yarinyar tayi ba, ta nuna bata buk'atar mu a rayuwarta ta zabi wad'anda takeso amma Ku duk Baku gani ba, to bari kuji duk Wanda ya yadda ya kusanceta koda hanyar bani bashi, kuma ban yafema koda kuwa keda kike uwarta ne" ya fad'a cikin b'acin rai tare da nuna Inna, sannan ya buga rigarsa yayi waje.

Bai zame ko'ina ba sai gidan aminin nasa Malam Musa, dan gayama abin ya faru da Kansa kada yaji a wani gu, yayi sa'a kuwa ya samesa bayan sun gaisa ne yake bashi labarin abinda ya faru tare da bashi hak'uri.

"Kai amma Abu baiyi kyau ba, dama ko bakazo ba inada niyyan zuwa akan maganan, dama na samu Mustapha da maganan to shine yace shi gaskiya yana wacce yakeso abar zancen kawai, to shine naso inzo in fad'a maka sai kuma ban samu zuwa ba har ka taho.

Tsananin mamaki da imani ne yayi mishi yawa, yama k'asa magana lallai kowa ya daka ta mutane toya rasa turmin daka nashi, saida sukayi da mutumin nan komai lafia amma yanzu yace ba haka ba, shiya salawantar tashi 'yar akan farinciki wasu, yayin shi kuma ya bawa d'an shi abinda yakeso, nan take nadama ta rufesa lokaci na farko d'aya yi tir da (zuciya irin tasa na Ayusher).

"Alh, Abubakar bakace komi" boye damuwarsa yayi tare dayin murmushi yake Wanda yafi kuka ciwo "ba komai Alhaji Allah ya kyauta, sai anjima" ya tashi ya wuce ba tare dayace komai ba...

Gida kuma bayan fitar baba zaune saukai jugum suna jajanta wannan Abu d'aya samesu, wannan shine ga duka ka kuma tsunka jaka, Abdool Ameena takai d'aki Wanda yayi bacci sai ajiyan heart yake, sannan ta dawo inda Mama suna tattauna wad'annan ibtila'i dake bibiyarsu a d'an tsakanin, lallai Allah shike jarabtar bawansa suna fatar su zamo cikin masu cinye ta, Ameena gani take tafi kowa ganin rayuwa, Asma'un da ta rage mata mai bata shawara sa d'auke mata kewa gashi k'addara tazo ta rabasu, yanzu ma ta ina zasu samu labarin Asma'un bayan ko waya batada ita yanzu, dan daga ita sai kayan jikinta tabar gidan komai bata d'auka, gashi ta manta sunan garin dan tabbas ta fad'a Mata amma bazata iya tunawa ba, ko wacce irin rayuwa zatayi a gidan Aurenta a wannan yanayi sa taje musu zasu karb'eta kosu wulak'anta ta? Nan tayi saurin nema mata sauk'i gurin Allah, haka suka wuni gidan ba dad'i kowa sai jimami yake.

_such is life_


Baba kuwa k'asa komawa gida yayi bayan yazo gaf k'ofar gidan ya dudduba kozai ga wannan takardar amma ina bata ba labarin ta, jin yayi komai baya mishi dad'i, sai gashi hadda k'wallarsa sam baiyima Asma'u adalci ba, yafi kowa sanin biyayya irin ta 'ya'yansa amma ya rufe idonsa, lallai zuciya mugun nama CE, kowa ya biye mata zata kaishi ta baro ne, lallai kowa yahau dokin fushi k'arshen sa nadama ne (yana daga cikin karantarwar manzo S.A.W idan kana cikin fushi kada kayi magana sannan kada ka yanke hukunci cikin fushi dan k'arshen sa dana sani ne) Allah yasa mudace.

Sai dare ya samu sukunin komawa gida, shima jiki ba k'wari ya shiga, kamar yadda Inna ta saba tarbonsa haka ta tarbesa ba tare data nuna mai komai ba, kamar ba abinda ya faru, k'ara jinjina hak'uri irin na Inna yayi sau da yawa yakan tauye mata hakki shikansa ya sani amma bata taba nuna mishi damuwar, lallai mace tagari ni'imace(haka yake duniya d'an jin dad'i ce amma mafi jin dad'in ta Wanda ya dace da mace ta gari).

Haka suma su Ameena sukazo suka gaishe shi kamar yadda suka saba, zasu tashi yace su tsaya yanada magana, ayan da yayi maganan cikin taushin murya, abun har mamaki ya basu, nan dai ya labarta musu yadda sukayi da Abokin nasa, tare da nuna musu nadamarsa.

"Alhaji ka dad'e kana tauyeni sau da yawa kana maida damuwar kowa ba damuwa, damuwarka kad'ai kake dauka damuwa, kama rayuwa da fushi kana yankewa mutane cikin fushi, to yanzu gashi wagari ya waya, ka salwantar mana da yarinyar akan son ran wasu, me kayi kenan" Inna ta gayamai magana cikin nutsuwa.

"Baba shiyasa ake son bawa mutum uziri a rayuwa, lokacin da ka shigo nida Asma'u munaso muyi maka bayani amma haka rufe ido kak'i bamu dama" nan ta basu labarin abinda ya faru a lokacin da Asma'u ta kira Abdulrahim" Amma kayi hak'uri In na fad'i ba dai-dai ba".

"To kaji ma abinda ya faru ko amma saboda rashin bata uzirunka a rayuwa kak'i sauraren kowa".

Shiru baba yayi nadama na k'ara lullub'esa, duk abinda suka fada gaskiya ba karya, sai hango lokacin da Asma'u take rik'e mishi kafa takeyi amma yayi biris yak'i saurarenta, tuni tausayinta ya kamashi lallai baiyi Mata adalci ba.

Hak'uri ya basu tare da tabbacin inshaa Allah zai nemota duk inda take.

Kwana ki sun shura watanni sun wuce kullum Baba yawon Sokoto da garuruwanta saidai kuma ba'a dace ba, ganin abin yayi yawa duk ya dami Kansa yasa Mama cewa.

"Ka hak'ura da yawon nan haka idan da rabon mu gaba zaka ganta ta kawo Kanta har gida, idan kuma babu rabo zafin nema bazai kawo samu ba, hakan ya hak'ura dole tare da bibiyarta da Addu'ar fatan Alkhairi aduk inda take.

Ameena kuwa zuwa yanzu zaman gida ya gama isanta gaba d'aya saukinta ma tana teaching da Baba ya samo mata yanzu tsawon shekara biyar kenan da rabuwarsu gashi duk masu zuwa sun d'auke kafarsa, a halin yanzu ba abinda takeso irin tayi aure shine akwai kwanciyar hankalinta (dan Mace komai kamewarta, idan batada aure to mutuncinta ragaggene a idon mutane, balle kuma wad'anda suka d'auki zawarci a lasisin iskanci suka samu tunda yanzu su zawarane ba namijin da zai Aure yace yana Neman budurci, to ai ba anan gizon yake saka ba, walla d more kikayi zina kina bazawara bakida wani hukunci daya wuce a jefeki, ba riba kenan, a tunani zawarci wata damace da mace zata K'ara sanin rayuwa, ta kuma gyara halayenta, kowanne aure yanada sila a rabuwarsa saiki duba meya kashe miki aure dan gyarawa gaba, bawai ki lalace ba, Allah yasa mudace) ayuwar zawarci rayuwace mai cike sa kalubale da tashin hankali, zaman gida ya gama isarta yau idan mace takai munzali tofa da batayi Aure ba, zaman sai kasance gashi nan dai na ganin laifi ne keda iyayenki, shiyasa Ameena ta damu sosai da rashin Auren, sai ba yadda zatayi dan tasan komai lokaci ne.

Yau kamar kullum Mansur ne yaje ya d'auko Abdool daga school, da gudu ya shigo yana murna "Mami kinga Nina yi na d'aya" ya fad'a yana nuna mata result d'in da gift d'inta aka bashi.

"Iyye yaron Inna kaifa akwai rashin ji amma akwai k'ok'ari" Jan tayi zuwa jikinta tana duba idonsa "waini kam idon nan naka Abdool anya lafia ko?"
Inna dake fitowa tace "me idon yayi?"

"Kiga farin yana surkawa da pink," duba idon Inna "tabbas ya kamata kuje asibiti" shikam sai k'ok'arin nunama inna report sheet yake, ba abinda ya damesa....

Likitan ya tabbatar musu ba wata babbar matsala bace, ciwon a jininsa yake so yayi inherited ne saidai ya kamata a nema mishi medical saboda idon yayi lasting, sai yanzu Ameena ta tuna tana ganin idon Auwal suna irin hakanan sometimes, no wonder shiyasa yake amfani da glass always Ashe medical ne.


**************

Har k'ofar gida suka sauke malam Garba da k'annin Ard'o sannan suka isa gida suma.


Da kallon mamaki iya Hari ta bisu sannan tace "malam ina kuka shige tun safe, wagga kuma fa?"

"Ai dai kin kawo tabarma tukun" tabarma tasa Shatu ta kawo tare da shimfida sannan ta kawo musu ruwa.

Zama sukayi sannan Baba yace Asma'u tasha ruwa ba musu tasha, guri ya nunawa Hari da tayi musu tsaye k'erere tana musu kallon dibar arziki, tuni jikin Asma'u yayi sanyi.

Zama tayi sannan Ard'o ya gayamata dukkan abinda ya faru, mik'ewa tayi cike da gatsali.

"Mi wagga uwar mata"................






💄 Meryerm Abdool💄
[8/11, 3:14 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)




*All thankful and praises be to Almighty Allah, d one who give me chance to live and make Muslim in Muslim ummah without my knowledge,🙏🏻 Patience is a key 2 every success in life,  everything come to he/she who have patient and wait in everything in life, may Allah give us d heart of patient👏🏽*

```Alhamdulillah, mashaa Allah, after long journey and go up and down crossing over many obstacles finally I get it, I mean my NCE result, I wish my self, big success in every stage i go, thank you Allah for every blessing upon to me hidden one and d one that appear``` 👏🏽




     📝 *Episode* 121--126




"Mi! Wagga uwar Mata? Hehehe ah dole daga zuwa gaisuwar iyaye da nema, a baku aure baki d'aya, yo dama daga ganin wannan kasan neman kai ake da ita, an tsofe gida ba mashinshini  yo ai  dole, tab wayaga akwala" sannan ta juya ga Abdulrahim tare da nuna shi da yatsa.

"Tir! Amma ka bani kunya, dama akan wannan mai bak'ar huska da bak'ar kamane yassa kak'i 'yar uwarka, yo Allah na tuba wannan ai sa'a tace, to nidai bani cikin wannan kwaba taku ehe" ta k'ara sa tare da hararan Ard'o.

"Ke! Hari ashe dama haukarki da rashin hankalinki yakai har haka, ashe baki da imani bansani ba, yanzu da ace cikin d'iyanki ne hakan ta faru dasu zakiji dad'i?"

"Aa Malam yada kiramin rashin hankali da hauka daga fad'ar gaskiya? Kuma ni d'iyana tuff! Tohe musu mugun yawu, nidai nace bana cikin wannan auren, kuma ban d'auka a sirika ba ehe" tana gama fad'i ta wuce tana gunguni.

Girgiza kai Ard'o yayi "Allah ya shiryeki" sannan ya dubi Asma'u wacce tunda Hari ta fara tu'annatinta kanta ke k'asa tana zubar da hawaye zuciyarta  sai zafi take Mata "inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un, Allahumma ajirni fi musibatih wa'akhlilni khairun minha, oh ni Asma'u tawa kalar jarabawar kenan, ya Allah ka bani ikon cinyeta...."

"Kiyi hak'uri 'yata Kada kalamanta su dameki, kamar yadda na gayamiki zan rik'e kamar 'ya'yana, kada ki damu ba abinda zai faru sai Alkhairi" sannan ya dubi Shatu wacce duk jikinta yayi sanyi abinda uwar tasu tayi sam baiyi Mata dad'i ba, ita bataga aibun Asma'u ba, dan daga gani tafi Saude nesa, ita dama can Saude bata yi Mata, wannan saidai Lanti da suke k'awance kullum suna tare, tasan Idan taji itama sai tayi tata haukan(dake anyima Lantanar aure).

"Aisha kai matar yayanki wancen d'akin, su fara zama can kafin a Gina mata na, ni zan koma d'akin zaure" (d'akin sa ne da Abdulrahim gina mishi bada dad'ewa ba).

"Muje Aunty" mik'ewa tayi ba musu ta bita, daga Leda sai katifa, kujerar roba sai kwaba da littafan musulunci ke cikin d'akin, zama tayi gefen katifar, ita kuma Shatu ta zauna k'asan Leda "Aunty don Allah kiyi hak'uri da abinda iya tayi miki, haka take komu data haifa yimana take yi".

Murmushi yak'e ta k'irk'iro " ba komai k'anwarta ai nima uwace a gareni kada ki damu" jinjina kai Shatu tayi "lallai yaya yayi dacen mata, duk wannan abun da iya tayi mata" ta fad'a cikin ranta, ita kam Wallahi ta kwanta mata a rai, nan tayi ta mata fira dan ta kwantar mata da hankali.

"Modibbo kaje ka rarrashi matar ka, ni zan fita na samo mata abinda zataci" yace ma Abdulrahim da yayi sugum tsabar kunya da bak'in ciki abinda  uwar sa tayi.

"Baffa Aida ka Bari naje, ka huta kaima" .

Murmushi Ard'o yayi "kaidai kayi yadda nicce kawai" tare da ficewa daga gidan, shima tashi yayi ya shiga d'akin, shigarsa yasa Shatu yi mata sallama ta fita.

Zama yayi daf da ita tare da ciremata hijab jikinsa ya janyota yana d'an bubbuga mata baya Alaman rarrashi, cikin muryan rad'a ya fara mata magana "kada ki damu matata koda duka duniya zata taru ta k'iki nikam ina tare dake, bazan taba barin ki cikin kad'aici ba, zan game miki bango abin jinginawa" haka yayi ta rarrashinta da tsadaddin kalamansa na k'auna, ita kuma tai lahu a jikinsa tana saurarensa yayinda wasu kasu na damuwarta suka tafi ( hmmm k'auna kenan Allah ya had'a kowa da masoyinsa na gaskiya Ameen).




**************



B'angaren Yusuf kuwa tun ranar da Sakina ta bashi labarin Ameenah yaji wani irin tausayi da k'aunarta sun k'ara lullub'esa danshi tun ranar da ya fara ganinta a school d'in, yaji ta kwanta masa komai nata burgeshi yake musamman natsuwarta, saidai bai San ta inda zai fara ba, dan iya sananinsa da ita bai tab'a ganinta da ta kebe da namiji ba, sai shi shima d'in da sunan karatune kuma tare da Sakina, gashi shiba ya tab'a soyayya ba balle yace yasan yadda sai samota barin abin a ransa yayi kawai, saidai daga ranar kullum cikin tambayanta Abdool yake yana lafia, haka zai sayo kayan wasa dana kwalama ya bata ta kai mishi, koya kirata a waya yace ta bawa Abdool suyi hira, yaita yi masa shirme yana biye masa, ita abun har dariya Suke bata wai friends ne, dama ance mai da wawa hakan yasa ta sakance dashi wani lokaci sai sake-sake zuciyarta ke Mata game dashi saidai nan da nan take saurin ka yima Kanta fad'a akan bama zai yuyu ba.

Ko bayan kammala karatunsu zumunci bai yanke ba, yakan kira ko ita ta kira lokaci zuwa lokaci, ko lokacin da akayi Auren Sakina yaje Bk dan kawai ya had'u da Ameena danshi asalin d'an Koko-besse(local government ne a Kebbi) ne karatu ya kaishi Argungu.

B'angaren su Hajia kaltume kuwa tun suna saka ran dawowar Auwal shiru shekaru sun tafi ba labari hakan yasa suka fitar da rai, har anyi Auren Maryam da wani Dr, inda suka wuce Germany an turashi course, Ayuba ma ya k'ara Aure, yayi yayi da Rafia suje hospital amma tak'i tana tsoron tonon silili, Hajia kin amince tayi da Auren saboda kar abatama 'yar gaban goshinta, saida ya nace sannan ta yadda dan itama rashin haihuwa na damunta, saidai duk da haka Rafia CE ke mulkinta a gidan sai abinda tace.

_wannan kenan_



***************

Kawunnan Alhaji Abubakar sukazo daga k'auye sukayi masa tas wai ya maida d'iyansa d'iyan yahudawa, ita waccen saboda ta isa da Kanta tabi namiji ta barsu cewa da Asma'u (baki ke yanka wuya shiya kira ya fad'a musu) sannan ita kuma wanga shekararta nawa da rabuwa da mijinta ance karatu to ai tw gama, zaman me take idan ba tana bin maza ba, taya za'ace bata damu ba, cin mutunci dai inda Suke shiga banan Suke fita ba, kalamansu sun mugun b'ata ransa, amma ba yanda zaiyi iyayensa ne.

Bayan tafiyar su ya kira Ameena yace mata tayi k'ok'ari ta fitar da miji cikin masu sonta tayi Aure, amma cikin sanyi yayi Mata maganan dan shima tausayi take bashi, itakam ya zatayi bayan bamai zuwa inda take, da za'a bud'e ranta tafi son tayi Auren nan kota huta da surutun mutane, amma ya zatayi.

Cikin satin Alhaji Sada yazo dubasu shima dai maganar d'aya ce ta daure ta manta baya tayi Aure.

Kwance take kan gado tunanin abin duniya ya isheta, tana matuk'ar son aure dan itama ai rayuwa ce kuma matashiya mai cikakikiyar lafia, saidai tasan komai yanada lokaci da lokaci yayi ba makawa zatayi shi, tana rokon Allah, kuma tana da tabbacin zai ansa mata, ringing din wayarta ne ya dawo da ita daga duniyar tunani.

Sunan Yusuf ne ya bayyana kan screen sauke numfashi tayi sannan ta d'auka, bayan sun gaisa ya tambaya Abdool daya dad'e dayin bacci yake CE mata.

"Ameena wai yaushe ne zamuzo Argungu musha biki?"

A bazata taji tambayan shima kenan ya k'osa tayi Aure? Murmushin dole ta k'irk'iro "Umm Yusuf bada dad'ewa ba inshaa Allah"

Jin sukayi gaba d'aya kowa na sak'a Abu a ransa, shikam yau ya shirya fallasa sirrin ransa gareta kota amince ko tak'i, gyaran murya yayi "Ameena" ya kirata cikin wata irin murya "Na'am".

"Inaso kiyima magana ta kyakkyawar fahimta ki d'ora a mizani mai kyau," sannan yaja hanci "maganan gaskiya Ameena I'm deeply in love with u".

" what " shine abinda ta fad'a cikin firgice, tare da katse kiran.

Kanta ta dafe "lahaulah walakuwwati, meke shirin faruwa ne, kai never yaudara kawai zaiyi...." Karan shigowa message taji, bud'ewa tayi.

_"everyone is a someone dream, and ur a my dream, pls don close ur heart to d one that is in need of u, never say goodbye 2 ur lover accept it as destiny, as I said I really love u with one heart, don't let me go astray..!"_

Tana gama karantawa kiran sa na shigowa d'auka tayi ba tare da tayi magana ba "Haba Ameena ki yadda dani da soyayya ta nayi miki alkawarin bazan cutar da ke, zan rikeki Amana da zuciya d'aya pls Ameena ki yadda dani".

" taya Yusuf taya zakace ni, koma manta nifa bazawara ce, bazawarar ma mai d'a, kaifa saurayin da bai tab'a Aure ba, to taya hakan zata kasance?"

"Haba Ameena kada ki canja daga yadda ba sanki mana, nasan ke mai ilimi CE, fiyayyen halitta da wace Mata ya fara? Nina ganki a yadda kike nace ina sonki, saidai idan sonane bakyayi daban ne, amma kima var wancen maganar.

K'aryane ne tace batason Yusuf domin ya had'a komai daya cancanci aso namiji domin shi, to amma ya  fa?.

" Koda zan amince mata saika je kayi magana da iyayenka idan sun amince maka, sannan zan amince ".

"Shikenan Ameena inshaa Allah, zanyi yadda kikeso, ki shafan kan Abdool, saida safe".

Wayar tabi da kallo, ita haka take ganin abun kamar almara, mik'ewa tayi ta d'auro alwala tahau dadduma tayi raka'a 2, sannan ta fara Addu'ar istikhara(Neman zabin Allah) kamar haka:-

_Allahumma inni astahiruka bi ilmika, wa'astagfiruka bik'udratika, wa'as'aluka min fadlikal azim, fa'innaka tak'dir wala ak'dir, wata'alam wala a'alam, wa anta allamul guyuwbu, in kunta ta'alamu anna hazal amru(saika fad'i buk'atar ka) khairun liy fiy deeniy wama'ashi wa'akibatu amri, fak'durhu liy wayassirhu liy summa barak liy fiyhi, wa'in kunta ta'alamu Anna hazal amru sharrun liy fih deeniy wama'ashi wa'ak'ibati amri, fasrifhu anni wasrifni anhu wak'dul liy khairan haisu kana summa raddani bihi._

Fassara

*ya Allah ina Neman zabinka domin iliminka, kuma ina Neman ka bani iko domin ikonka, kuma ina rok'onka daga falalarka mai girma, domin Kaine mai iko ni kuma bani da ikon, kuma kaine masani ni kuma bani da sani, kuma Kaine masanin abubuwan fake, Ya Allah! Idan kasan cewa wannan al'amari (ka ambaci buk'atar) Alkhairi ne a gareni cikin addinina da rayuwata da k'arshen al'amarina (wata rayuwar ) da magaggaucin al'amarina da majinkircinsa, ka k'addara mini shi, kuma ka sauk'ak'e mini shi, sannan ka Albarka ce ni a cikinsa, kuma idan kasan wannan al'amari sharri ne, gareni a cikin, addinina da rayuwa da k'arshen al'amarina (a wata rayuwar) da magaggaucin al'amarina da majinkircinsa, ka kawar da shi daga gareni, kuma ka kawar dani daga gareshi, ka k'addara mini Alkhairi a duk inda yake, ka kuma sani in yarda dashi*

(Cikin husnul Muslim take, yana da kyau komai bawa zai gabatar a rayuwa ya nemi zabin Allah a ciki. Allah yasa mudace)


Bayan ta kammala ta nad'e dadduma tare da kwantawa kan bed, tana tunanin wannan al'amarin,sannu a hankali natsuwa ta fara shigarta, a haka bacci mai dad'i yayi gaba da ita.................





_masoyana ina Neman addu'o'inku, I really in need of it👏🏽 ina muku fatar Alkhairi a duk inda kuke_






💄 Meryerm Abdool💄
[8/12, 6:07 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)





🙏🏻 *From he we are, and 2 he we return, oh! Allah forgive our dead one, that find their self in absence of no one to pray 4 them, ya Allah have mercy on them, and make our dead day the day of happiness 2 us, ya Allah don't take our souls until urs happy with our souls ameen🙏🏻*








      📝 *Episode* 126--130






Koda Yusuf ya jema iyayensa bai samu matsala da yake yayi dace da iyaye masu hangen nesa, sunce tunda shi yake sonta in har anyi bincike 'yar kirki ce to su basu da matsala, amma 'yan uwansa sunce sudai basu amince ya auri bazawara ba yana saurayi dashi, saida Baban yayi  musu fad'a yace "meye naku a ciki tunda a hakan yakeson abarsa, kuma ma in banda abinku, fiyayyen halitta ma da bazawara ya fara, to meye dan yace zaiyi koyi dashi idan har ba zaku bashi k'warin gwuiwa ba bai kamata Ku hanashi dan haka kar in sake jin wani daga cikinku ya soki wannan tafiyar" da haka Baban ya kwabesu dole suka hak'ura badan ransu yaso ba.

Koda ya fad'ama Ameena tayi farinciki sosai a ranta amma bata wani nuna mishi cewa kawai tayi "to yayi" sauke numfashi yayi "Haka kawai zakice Ameena tah, kamar bakya farinciki".

" um inayi mana tome kakeso ince ne".

Smiling yayi kamar tana kallon sa harda lumshe ido " cewa ya kamata kiyi yaushe zaka turo my love".

Dariya zancensa ya bata dama tasan Yusuf da barkwanci kamar me "au dariya KO, ai gara ma ki gayama Baba dan kada ayi mai ba zata, dan bazan tsaya kallon ruwa ba kwado yazo yamin kafa" nan ma murmushi kawai tayi dama Ameena ba yawan surutu...

"Um nidai bana Abdool dan naga yau miskilancin ya motsa" nan ta ba Abdool sukayi ta fira kamar wani babba dama Abdool badai wayau ba, in yayi wata magana ka d'auka fad'a mishi akayi.

Malam Sa'id mahafin Yusuf yayi duk binciken da ya dace ya kuma tabbatar da Tarbiyar Ameena, hakan yasa ya gaya ma 'yan uwansa domin Suje su nema nasa auren.

Lokacin da Ameena taje ma su Baba da labarin sunyi farinciki Sosai dama babban burinsu kenan Ameena tayi aure, shima yayi nashi bincike kamar yadda addini ya tsara, hakan yasa saka shiga cikin maganar har an tsaida rana wata uku masu zuwa.

Suma su Yusuf ba wasu masu arziki bane akwai dai rufin asiri, nan family house d'insu, aka gyara wasu dak'una biyu aka maida mata room and parlour sai toilet, ba laifi zaman dai mutum d'aya a talauce ba sarauce ba.

Alhaji Sada ma da yaji maganan Auren yayi mata murna Sosai, kuma yace ko bayan tayi Aure Abdool zaici gaba da zama gurin su Mama, dan yasha alwashin saidai in Abdool ya girma yakai Kansa Sokoto da kansa tunda dai sun nuna basa ra'ayinsa har gara iyayensa maza suna zuwa dubashi sa'in sai kuma Maryam kafin tayi aure duk da Hajia ta hanata zuwa hakan bai hana in Alhaji zaije ba, ta bishi wani sa'in kuma ta bada Abubuwa akai masa.

Cikin ikon Allah Anyi Aure lafia cikin farinciki ranar Ameena tasha kukan rabuwa da iyayenta uwa uba kuma Abdool shima dai yasha naji kukan dakyar aka banbareshi jikinta, a son Yusuf ma yaso abasu shi amma Baba yace Aa a barshi nan yayi karatunsa lokacin yana 6years yana primary 1, haka dai Ameena ta tare cikin aminci a gidan Angonta Yusuf.

Farkon Auren ta had'u da kalubalen dangin miji haka zasuzo suna yad'a mata magana, da yake macece mai matuk'ar hak'uri hakan yasa sam bata nuna tamasan sunayi, Amma kam surukarta suna zaune lafia, yawan kyautata Mata da dawainiya da take Mata, haka zata saka Yusuf ya d'auko kayansu ita da Abbansa su had'u su wanke su goge, komai ta dafa da nasu, suma 'yan uwan nasa da yake yayin nashi Mata ne duka suna gidan mazajensu sai dai in sunzo, shine namiji babba sai k'annin sa, hakan yasa in sukazo tana yawan kyautata musu gada Sam batada rowa ko kyashi tuni suma ta saye zukatansu(dangin miji saida kyautata ake zama lafia note women).

Taci gaba da teaching d'inta dan an samo mata transfer haka tana business d'inta, shima dai Yusuf teaching yake yana kuma zama kasuwa inda mahaifinsa da haka suka rufama junansu asiri Sam bakajin Kansu, zaman k'auna da soyayya suke dan sai yanzu tasan lallai Yusuf son gaskiya yake mata, kullum cikin tattali da nuna mata k'auna yake, Sakina ma anzo bikin tayi murna sosai dama ta dad'e tana hango son Ameena a idon Yusuf.

Tana zuwa Argungu lokaci zuwa lokaci har yanzu dai ba labarin Asma'u abin kullum yana ranta "oh ina zamu ganki Asma'u, Allah ka bayyana mana ita ka tsareta a duk inda take" kullum shine Addu'arta, Abdool na zuwa mata idan anyi Hutu.

Shekararsu 2 da Aure Yusuf ya samu Aiki a NNPC KADUNA, ba k'aramin farinciki sukayi da cigaban da ya samesu ba, haka yaje yayi interview aka bashi upper, watansa uku sannan ya dawo, nan ya gayama iyayensa zai wuce da Ameena dan an bashi gida, nan sukaje Argungu sukayi musu sallama, nan ma Yusuf saida ya tada maganar son abasu Abdool, hak'uri Abba ya basu yace kada su katse mai karatu, hakan suka wuce badan ransu yaso ba, irin kulawarda Yusuf ke bama Abdool shiyasa Ameena k'ara sonsa da ganin girmansa, haka sukayi bankwana da yan uwa da abokan arziki suka lula garin gwamna...


_safe trip_ 🚗 



~~~~~~~~~~~~


Lokacin da labarin Auren Abdulrahim ya bazu a k'auye Kilgore mutane sai tururuwa sukeyi gidan dan ganin amarya da 'yan gulma da 'yan ganin kwam, da masu yabawa da masu tsinewa, su Lanti anzo sai yatsine take dan Uwar ta kitsa mata tana yad'a bak'ak'en maganganu, Abdulrahim ko dayaji tass yayi Mata sannan yace karta k'ara zuwa gidan muddin ba abin kirki zai kawo ba, aiko iya Hari ina wuta in fad'a inda take shiga banan take fita ba, cin mutunci gaske tayi masa, wai karya kuskura ya takurawa 'yarta akan wannan korarriyar wanda iyayenta suka sallama, cin fuska dai sai Wanda ta manta, ranar Asma'u tasha kuka tare da kewar gidansu lallai kowa yabar gida ya barshi, gata ana mata gori ba yadda zatayi, hakan ya k'ara ba Lanti kwarin gwiwar yi Mata iskanci son ranta, saidai batayi in Abdulrahim nanan dan tana shakkarsa, Saude kam haukane kawai batayi ba, da taji Auren Abdulrahim haka tazo har gida tayima iya Hari rashin kunya, wai ai ita tayi mata alk'awari amma tsabar munafurci ta bari ya auri wata ba ita ba, itako Sam bataga laifinta ba saima hak'uri ta bata akan lallai zai aureta ta shigo ta biyo, tace Allah ya kiyaye ta zama ta biyu ta d'auki sauran wata, ta yafe, dama ba sonsa take ba sha'awa ce kawai.

Kamar yadda Ard'o yace haka kuwa akayi an Gina mata ciki da falo hadda bayan gida. Lol

Shanu biyu Ard'o ya Ware yayi Mata kayan d'aki a matsayin sa na uba gareta, an gyara d'aki ba laifi, nan kuma wani gorin ya tashi habaici kam tasha harta gode Allah, zuwa yanzu ta fara sabawa da cin mutuncin Iya Hari da Lanti, amma kullum abin na kona ranta bata dai yadda zatayi ne, ga uban aiki gidan da yanzu ya dawo Kanta, komai ita danma Shatu na kamata inba idon Iya Hari, dan tuni tayi Mata iyaka da Asma'u, in kaga Asma'u saika tausaya mata duk tayi baki ta rame danma ta Saba da aiki a gida da sai tafi wahala, Abdulrahim baida halin magana a balbaleshi da bala'i itama Asma'u tace ya dena magana kada ya had'u da fushin mahaifiyarsa tunda ita ta haifeshi ya zama wajibi yayi mata biyayya, Ard'o ma yayi fad'a harya gajia amma a banza da maganan sa da babu duk d'aya suka ha Hari, saidai in ya samu tanayi yace ta aje inya fita ace tazo tayi dan ubanta (oh Asma'u kina ganin rayuwa).


Sauk'inta Mijinta na tausasa mata da nuna mata k'auna, inta zauna sai taita tunani "wato mu haka tamu k'addarar take an jarabcemu da uwar miji, haka aunty Ameena tayi fama, ashe nata nafila ne, gwanda ita ina kusa kuma zata kira gida taji dad'i to nifa ba ko d'aya, yanzu ko sakina akayi INA zan nufa, ya Allah ka sassauto da zuciyar Baba yafemin ya mai domin da family i'm in need of them badly".

Ana hakane akayi posting nasu gurin service ita da Abdulrahim, ba state d'aya aka ajesu ba shi Katsina ita kuma Edo, hakan yasa yaje ya nemi alfarma aka maida ita Katsina, nan ma anyi rigima da Iya Hari wai ba inda zataje, k'aryane meyakai mace bautar k'asa, nan ma saida Ard'o yayi da gaske sannan ta Shafa musu lafia, zaman su Katsina zamane mai dimbin tarihi a cikin rayuwar Auren su dan sai a sannan ne suka samu nutsuwa, dama Dr gida ake bashi, so basuda matsala haka suka gudanar da service d'insu cikin kwanciyar hankali, ko marmarin dawowa basuyi,ranar da suka isa Abdulrahim ya sayomata waya nan ta kira numbobin gidansu amma ba wacce ke nan jikinta ya k'ara sanyi da d'auka kodan karta kirane yasa Baba sasu canja layuka(ba haka bane baraye suka kwase musu wayoyi dare d'aya) lokacin da suka gama zasu dawo kamar karsu dawo sukeji, haka sukayo tsaraba sosai suka dawo amma kam Asma'u ranta fal tsoro za'a koma 'yar gidan jiya.

Hakan ko takasance bayan dawowar su akaci gaba daga inda aka tsaya wannan karon hadda gorin rashin haihuwa ganin suna cikin shekara ta uku da Aure ba haihuwa, Abu dai kullum ba sauk'i sai abinda yayi gaba, gashi anyi Auren Shatu mai tausaya mata.

Cikin ikon Allah Abdulrahim ya samu aiki a uduth Sokoto hakan yasa Ard'o yace ya d'auki matarsa su koma can da zama, Iya Hari cewa tayi bak'in ciki ake mata tunda tana taya ta aiki, banza yayi da ita danya San Neman a tanka ne.

Haka suka tattara suka koma Sokoto, kuma Ard'o yayi Iya kashedin duk ta taka Sokoto bakin Aurenta, dole ta lahe dan tasan rabuwa da Ard'o babbar asarace gareta.

Suna shekara cikin ta 5 da Aure Asma'u ta samo ciki, fad'ar irin farinciki da sukayi ba'a ma magana, haka sukaci gaba da kula da cikinsu cikin so da k'auna har ya isa haihuwa inda Abdulrahim da Kansa ya anshi haihuwar zankad'ed'iyar 'yarsa me kama dashi, baki kamar gonar auduga, su Modibbo anyi 'ya, Ard'o yaje yazo dasu da sunan ayi mata wankan jego tunda haihuwar fari CE batasan makari ba, Amma abin takaici ko kallo basu ishi Iya Hari ba, anyi ba'ayi ba dai kenan dan komai Asma'u ce kema Kanta, da bata iya ba saidai ta rub'e anan, tayi kukan rashin 'yan uwanta harta gode Allah, lallai naka sai naka, da sunanan da bata wulak'anta ba, Abdulrahim ne ke kama Mata aiki sai kuwa Shatu idan tazo shima idon uwarta kamar ya tsiyaye gurin harara, Abdulrahim ko saidai tace shanyayye Mara tayi.

Haka sati ya zagayo ranar suna yarinya taci suna *Ramlah* rago biyu da sa aka yanka, Abdulrahim yayi k'ok'ari dan yayi musu komai na goyo tsadaddi Hari ko sai yad'a magana  anyi Aure ba dangi haka suna ma, Abu sai kace mayya, ita Kanta Asma'u abun na matuk'ar damunta, dan Abdulrahim yasha cewa ta bari suje Argungu suba Baba hak'uri, sanin halin mahaifinta na kaifi yasa tace cewa Aa su jira dai(tab aiya canja duniya ta horashi) lol.

Tun kan suyi arba'in ganin wahala tayi ma Asma'u yawa, balle Abdulrahim ya kawo sai k'arshen sati yake zuwa yasa,  ga dawainiyar kula da kai da jaririya gana gida yasa Ard'o yace ya d'auketa su wuce kawai, duk k'arshen sati Abdulrahim na zuwa duba iyayensa, idan Asma'u bata zo ya zama abun zagi idan taho ma aci Mata mutunci.

Abdulrahim arziki sai bud'ewa yake tana ganin haske saboda biyayyar iyaye da yake, ga kulawa da iyalinsa da yakeyi, har Saudiya ya biyama Ard'o da Iya Hari, amma Iya cewa tayi ya bata kud'in kawai (hasararriya Mara rabo) Ard'o kam ya k'ara tsorata da lamarin Hari, haka ta kashe su a banza.


~~~~~~~~~~


B'angaren Ameena da Yusuf kuma zaman su lafia lau gwanin sha'awa, kowa na kaffa,-kaffa da d'an uwansa, tare suka kowa makaranta inda take karantar Botany (ilimin tsirrai) sam rashin haihuwar bai tab'a dagama Yusuf hankali ba, shine ma mai kwantar Mata da hankali, idan tana nuna damuwarta, yace "haihuwa ta Allah ce idan sunada rabo zasu samu idan babu Abdool ya ishesu".

Suna shekara 4 da aure ta samu ciki, murna sosai sukayi da kyautar da Allah yayi musu, wata tara cip ta sunbulo 'yarta mai kama da Yusuf sak, a Besse suka koma akayi suna inda yarinya taci sunan mamar Yusuf Aisha suna kiranta Nihal, mutane Argungu anzo an kwashi shoki!

Musamman Abdool daya zama dan samari sai murna yaks yayi k'anwa.........




*lol every body a kame kam sabuwar rawa 🕴🏾🕴🏾🕴🏾🕴🏾*




_kuyi hak'uri Dani friends abubuwan ne da yawa #one love# 😍_






💄Meryerm Abdool💄


👌🏻😉
[8/16, 8:27 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



```Manzon Allah (S.A.W) yace ma wani yaro:- kayi bismillah(idan zakaci abinci) kaci da hanun damanka, kaci daga abinda ke gabanka.```

_Ladubba ne nacin abinci mu kiyaye sannan mu koyar da yaranmu_ Allah yasa mudace🙏🏻



*Ina mai farinciki da wannan Auren da kikayi Aunty Kausar (kausar M Hasan) Allah ya sanyawa aurenki Albarka tare da zuria dayyiba Ameen #HML💏*


_Ina mik'a ta'aziyya ga Feedo Deedo (marubuciyar mamata gimbiyata) akan rashin mahaifiyarta da tayi, Allah yayi mata rahama yasa mutuwa hutuce ameen, Ku kuma Allah ya Baku hak'urin rashin da kukayi👏🏽_






    📝 *Episode* 131-135






Bayan sunyi Arba'in sukaje Argungu ganin gida da kai musu jaririyar su gani, lokacin da Ameena ta shiga d'akin su, nan taga wasu kayan Asma'u wad'anda ba'a kyautar ba, batasan lokacin da hawaye ya wanke mata fuska cikin jimami take magana  "Asma'u kina ina? Tsawon shekara biyar kenan, Asma'u kina lafia kuwa? Kina cikin farinciki ko sab'anin haka, Asma'u kizo gida mu ganki wlh Baba Neman ki yake ruwa a jallo, pls Husnatah sisto na friend dita ever kizo garemu muma buk'atar ki" cikin kuka tace maganar gwanin tausayi, kullum safiyar duniya  kira gida maganarta kenan Asma'u tazo, Mama dake tsaye bakin k'ofa rik'e da Nihal dake motsi alaman yunwa dan tunda suka zo take sharar bacci abinta, Abdool na kusa da ita sai kallon ta yake ya tab'a nan ya tab'a can yana matuk'ar son k'anwar tasa, ko yanzun ma Baba ne ya kirashi suka fita.

Itama hawaye take daga nan tsaye, ita ta haifesu gaba d'aya, amma tasan akwai shakuwa mai girma a tsakaninsu sau da yawa idan matsala ta taso a tsakaninsu suke maganceta ba tare da ta sani, saidai idan tafi k'arfin su suka kawo mata, to ya zasuyi k'addara ta riga fata, saidai su bita Addu'a Allah ya k'are ta aduk inda take ya dawo musu da ita lafia, share hawaye tayi kada ta rauna nata.

K'arasawa tayi ciki tare da kamata zuwa bakin gado, cikin muryan rarrashi da tace "Ameena kuka bazai dawo da Asma'u ba, Addu'ar mu kawai take nema, kiyi hak'uri ki daure ki daina kuka kiyi mata Addu'a" haka tayi ta rarrashinta daga k'arshe ta bata 'yarta data fara kuka tare da ficewa cikin sanyi, dan ganin Ameenan kad'ai tuna mata da Asma'unta yake yi.


*****************



Satinsu d'aya a Argungu sun zaga dangi sosai har birnin lafia sunje, gidan Firdausi duk taje, Abdool kuwa kullum yana rik'e da Nihal har goyata yakeyi Mama tayita zolayarsa, da sunan mati sai cewa yake ai k'anwarsa CE, a satin Yusuf yazo nan ya dage da rokon Baba ya basu Abdool su wuce dashi tunda ya k'are primary, ganin sun dage kuma yaga shima yaron yana buk'atar uwarsa a kusa dashi duk da suma ba abinda basa yi masa amma  d'a sai uwarsa, kuma ya yaba yadda Yusuf d'in ya nuna kulawarsa akansa, yanada tabbacin zai rik'e sa da Amana, amma duk da haka saida ya kira Alhaji Sada ya shaida masa abin da sukazo dashi.

Kai tsaye Alhaji ya amince dan yasan waye Ameena yasan zata bashi tarbiyar da ya dace, shi kanshi yaron zaifi jin dad'i gashi ga uwarsa, nan Baba ya basu Abdool sunyi murna Sosai bakin Yusuf ya kasa rufuwa danshi harga Allah yana son Abdool yana jinshi a ranshi kamar yadda yakejin Nihal.

Ban kwana sukayi ma Argungu garin nabame kowa sarki, sannan suka wuce Besse anan ma sam dangin Yusuf basu nunawa Abdool wata fuska k'ama ko wulak'anci ba, Wanda hakan yayima Ameena dad'i sosai, daganan suka shirya tsaf suka lula Kaduna.....

Zamansu kaduna zamane mai cike da k'auna da kulawa da yaran su sosai Yusuf ke kula da Abdool kaman ma yafi sonsa akan Nihal, dan Ameena cewa take Nihal ce babynta shi kuma yaron Dady, tare suka zuwa masjeed kullum muddin yana gida, haka zai baje a parlour yana mishi lesson don tuni suka sakashi secondary wata private, muddin Yusuf na gida to yana tare da Abdool hakan ba k'aramin dad'i yakewa Ameena ba, hakan ya k'ara wanzar da zaman lafia  a familyn.

Sannu a hankali rayuwa taci gaba da shurawa kwanaki na tafiya, Nihal nada four years Ameena ta k'ara haihuwa wannan karon twins ta haifa mace da namiji, nan Ameena ta roki Akan a sakama macen sunan Asma'u hakan kuwa akayi inda ake kiranta da Husna namijin kuwa Abduljabbar, zuwa yanzu Yusuf ya gina musu gidan Kansu a unguwar K/mashi inda Ameena ta k'awata gidan da kalolin furanni masu dad'in k'amshi ga kuma garden had'adde Wanda ya k'unshi kayan more rayuwa, kai da ka taho gidan ba tambaya kasan ka taho gidan miss Botany tun farfajiyar gidan zaka fahimci haka.

Abdool yana SS1 Nihal na nursery, tuni ya saba da saka medical d'insa inda a school d'insu wasu ke ganin jin kai ne da tsabar raini dan yaga yanada Brain yasa yake saka glass dan sauka haka kawai yake sakawa ganin yadda ya zauna mishi tsaf, Abdool ya taso yaro mai kuzari da sanin ciwon kai ga k'auna da yake nunawa kanninsa haka sai saka Nihal gaba yayi mata lesson in Dadynsu bayanan shi kuma inya dawo yayi mishi, shi har mamakin k'ok'arin Abdool yake yaro sai kace dan Jamia komai kana ana bud'e kwakwalwarsa ana zuba masa, ita ma dai Nihal Kanta naja ba laifi sai yake danganta hakan da ilimin Ameena, haka sukaci gaba da gudanar da Rayuwarsu cikin farinciki, sukanje Hutu lokaci zuwa lokaci haka Alhaji Sada na zuwa har Kaduna ya dubasu, yanajin dad'in yadda suke kula da Abdool, tuni Alhaji ya saba da Yusuf haka zasu zauna suyi ta hira in yazo dama ga Yusuf da barkwanci wuni guda kukayi a tare zaku Saba.




*****************




Ranar rabuwa ranar da zukata suka nisanta da juna ranar ruhi da gangar jiki suka shiga maraici ranar da mai rabawa ta raba, ranar da Yusuf yayi accident a hanyarsa ta dawowa Kaduna ya fito daga Besse anan on d sport wuyansa ya kare nan take ya ansa kiran maliccinsa, sai gawa su Ameena suka gani fad'in kalan tashin hankalinda suka shiga anan dan page d'in ga bazai ishemu ba, kowacce ta kwatanta da mijinta ne da babanta ne da d'anta ne da k'annin ta ko yayanta ne ya zataji haka suma Familyn Yusuf sukaji da rashin da ya sameso, a Besse aka wuce da gawar akan kayi komai daya dace da shari'ar sunnar Manzo S.A.W, ba'ayi wani zaman makoki ba, duba da yadda zaman ya koma zaman hira da tsegumi da cin shinkafa, Wanda ya mutu shiya mutu kawai sai kuwa na kusa dashi, da suke cikin jimami rashin sa, duk wannan abun Abdool baida labari dan lokacin yana ABU zariya inda yake matriculation, Wanda Yusuf ne da kanshi ya kaishi ya kuma zaba mishi medicine, ganin yanata kiran Dadyn nashi wayanshi bata zuwa yasa ya kira Maminsa, nan ta sheda mishi suna Besse ba charge a wayansa, sannan tace idan da chance ya samesu Bessen k'arshen sati, nan ya tambayeta lafia dai tace qlau ba komai, amma jikin na bashi ba lafia.

Lokacin da yazo ya samu abinda ya faru, yayi kukan rashin Dady dan sosai ya maye masa gurbin Auwal yanzu gashi ya tafi ya barsu.

(Duniya labari)


Anan ta zauna harta kammala takabanta, akayi rabon gado kamar addini ya tanadar daga an kammala hada komai, tayi sa'a gidansu na Kaduna ya shigo cikin rabonsu hakan yasa tace zata koma Kaduna, sun so tayi zaman ta nan tare dasu dan Ameena mutum ce wacce kowa ke sha'awar zama da ita, saboda iya zamanta da mutane da kyautata,tafi so  koda zata cutu ne wani yaji dad'i amma batason wani ya cutu akanta, hak'uri ta basu saboda ta riga ta saba da Kaduna ga kuma karantun yara (weather ma akwai banbanci sosai tsakanin Kebbi da Kaduna) haka taje Argungu tayi musu sallama nasiha sosai Baba da Inna sukayi mata duk da susan Ameena zata tsare mutuncinta aduk inda ta riski Kanta, sannan ta wuce da Mansur d'an yad'an rage mata kewa, da yake Abdool ya koma Zariya saboda karatu, shima Mansur ya kammala NCE inda zaiyi degree a can.

Bayan komarsu ta shiga neman aiki tuk'uru, shine amfanin ayi karatun koba mutuwa akwai sayin yanayi Wanda miji zai nemi agajin matarsa musamman ma inga nauyin iyali, cikin sa'a ta samu aiki ministry of Agriculture inda zata ringa basu shawarwari akan dashen itatuwa da fulawowi da dai duk wani dangin tsirrai, haka kuma gefe d'aya ta bod'e nata gidan koma inda ita kula da abinda sai Mansur da wasu matasa data d'auka take biyansu, in fact dai ita keda mallakinsa nata ne, ga business tana yi da tana bada odar kaya daga Dubai, Alhamdulillah, tafi k'arfin buk'atunta dana yaranta, yayin su kuma ta saya musu shares da gadon su ana jujjuyawa a Ja'iz bank inda suka halattacen kasuwanci da kud'in.

Wata rana in ta zaune sai tayi ta tuna maganganun Yusuf da yake cewa "Ameena ko a yanzu nabar duniya bana shayin Wanda zai kulamin da yara na da tarbiyar su, saboda nasan zaki iya ke namijin duniya ce, wacce kowane namiji ya sameki zaiyi alfahari da ita, ina k'aunarki Ameena har numfashi na, na k'arshe" ita kuma idan yana fad'ar haka saita rufe masa baki tace.

"Ba zaka mutu ba mijina kai kad'ai inshaa Allah saidai mutuwa ta doke mu tare bana fatan ka barni a duniya ni kad'ai, pls ka dena fad'ar haka" murmushi kawai yakeyi ya canja zance, gashi yanzu tana tunawa shikenan ya tafi ya barta, nema masa gafarar ubangiji take dan shine kadai ya rage a tsakaninsu yanzu, ga zawarawa sunyo mata caa abokan Yusuf da abokan aikinta itakam hak'uri kawai take basu, yanzu kam renon marayun yaranta ne a gabanta bata sake jajibo wani Auren ba, ko iyayenta da sukaji sun goyi bayanta dan yanzu tasan meye mai amfaninta da Wanda baya amfaninta...

Ciwo ne ya tasowa Alhaji Sada da gaske har anyi admitting nashi hospital, hakan yasa Abdool zuwa kiran Maminsa akan zaije ya dubasa, sosai ta tausaya masa itama taso taje ta dubasa dan Alhaji kamar ubane gunta ga kirki, har Besse yaje mata gaisuwar Yusuf, amma kuma tana tsoron yadda familyn zasu karb'eta, tsoron abinda zaije ya dawo yasa ta fasa zuwa tace Abdool ya gaishesa sosai.

Alhaji yayi murna sosai da zuwan Abdool Wanda shine na farko tun bayan rabuwar iyayensa haka 'yan uwa da iyayensa maza ga su Isma'il sa'anninsa ga kuma k'anninsu gida ya cika sosai sa zuria, Hajia tunda ta ansa gaisuwarsa a dak'ile bata koda kalli inda yake ba, dan ita har yau haushinsu takeji shida uwarsa, Rafia kowa sai wani son munafurci take nuna masa amma shi Sam bata kwanta masa a rai ba tunda ya ganta(INA kuwa kaga shedan mai raba aure).

A tare dashi akayi jinyar Alhaji har murmure, aka sallamesu a part d'in Alhaji ya tare wadda hakan yasa ta daina shigowa, satin sa 1 yace zai koma saboda makaranta, nan Alhaji ya d'auko wasiyyar mahaifinsa ya danka masa, d'akin da ya zama NASA a part d'in Alhaji ya shiga ya, direct da diary ya fara.

_"zuwa gareka d'ana abin Alfahari sanyin idaniyata, kayi hak'uri d'ana nasan koda wasik'a ta zata sameka, zakace banyi maka adalci ba dana barka tun bakasan waye kai ba, nasan zaka zargeni da tauye maka hakk'inka, saidai ina da tabbacin Ameena zatayi dutyn ta ta kuma had'a da nawa tayi, saboda na yadda da ita"_

Hawayen da suka zubu masa ya share tare da cewa "wannan hakane Abba Mami mace tamkar dubu" sannan yaci gaba, duk wani labari tun daga had'uwarsu da Ameena auren da k'uncin da ta shiga da soyayyar da Asma'u ta nuna masa har zuwa rabuwarsu saida ya rubuta masa, zuwa yanzu kuma yake harda majina yana tausaya iyayen nasa, tare dajin k'ara son aunty Asma'u dayi mata Addu'a akan Allah ya bayyana ta, sannan yace "Abba banga laifinka akan komai ba sai akan tafiyar ka meyasa Abba? Meyasa zaka tafi ka barni, shin kayi tunanin rayuwar da zanyi? Meyasa ka guji mahaifarka kabar iyayenka da begenka, kana ina Abba!? Where r u Abba??" Ya fad'a da k'arfi cikin sheshekar kuka.

Alhaji Sada ne ya shigo jin k'aran sa, yasan za'ayi haka duk baisan mai wasik'ar ta k'unsa ba, dagoshi yayi tare da rungume shi yana dan bubbuga masa baya, alaman rarrashi "yi Hak'uri Abdulmajeed ka d'auke shi a matsayin k'addarar ka, ka yafewa mahaifinka tare da masa fatan Alkhairi kaji" rarrashinsa yayi da kalamai masu kwantar da zuciya....

A ranar yaje banking, ya girgiza da ganin tsabar kud'in da mahaifinsa ya aje, masa kud'i bana wasa ba, tun lokacin bare kuma yanzu da komai ya canja, (Allah ya zuba Alkhairi a harkar kasuwanci, don abinda annabawansa sukayi Kenan, muddin bawa zai tsarkake sana'arsa tabbas  zaiga akhairai a ciki).

Transfer kud'in yayi zuwa account d'insa, nan ya nemi shawarar Alhaji akan yadda zaiyi da kud'in dan kud'in da yawa kuma shi baya da buk'atar kud'i dan Alhaji ne ke d'auke da karatunsa yanzu tun bayan rasuwar Yusuf, kuma shima yana dan business dan Abdul yarone da yasan ciwon kansa, ko lokacin da yake Argungu shik kula shagon kawu Mansur in ya shiga school kuma tsab zai dawo ya isko kayansa, haka Mami na turo mishi sosai duk da yana cewa ta barshi.

Alhaji shawarar a fara Gina mishi hospital ya bashi tun da medicine yake karantawa, hakan kuwa akayi dan itama Mami hakan tace nan suka sayi fili mai kyau aka fara tsara hospital ta gani a maganta inda kawu Mansur ke kula da ganin da yake yana gari.


*****************


B'angaren Asma'u kuwa yanzu bata da wata matsala dan ba'ayi mata sai in taje Wanda zuwa yanzu ta Saba da jarabar Iya Hari, Abdulrahim kuwa ya rik'e ta da Amana kamar yadda yayi alk'awari suna zaune lafia abinsu bakajin Kansu ko sabani suka samu suke shirya Kansu ba tare da wani yaji ba, Ramlah kuwa sai girma take abinta ga kulawar iyaye tana samu suna matuk'ar kula da ita da bata tarbiyar islama, tuni ta iya haruffa k'ananan surori tana 4 year, er lukuta da ita yanayin jikin irin na Asma'u ne, nan kad'ai suke kama.

A 'yan kwanakin nan mafarkin su Baba da Inna da Aunty Ameena, Abdool ya matsawa Asma'u har yakai ko kwanciyar rana tayi sai tayi, hakan yasa hankalinta ya koma gida baki d'aya, yanzu kam ta shirya runkarar Baba duk da tsawon lokaci bai nemata ba, amma tana fatan idan taje ya yafeta ya maida mata iyalanta, hakan yasa ta tunkari Abdulrahim da maganar son zuwa gida, hakan yayi mishi dad'i sosai dama ya dad'e yana bibiyarta suje tana cewa ba yanzu ba, suka tsara zasuje k'arshen sati.

Da sukaje Ard'o da zancen yayi murna sosai, dama shima ya dad'e ya maganan zuwan, iya Hari ce sai tace taje ita kad'ai da 'yarta amma bada d'anta garin mayu ba, nan ma Ard'o yayi mata fad'an ta daina haka aiko su waye an Riga an zama d'aya tunda ga zuria anyi dan Asma'u na d'auke da wani cikin Wanda harya fara fita.

Koda suka tashi tafiya suka nemi Ramlah suka rasa 'yar gidan Lanti ta shiga gari da ita daga zuwansu hakan yasa sukace zasu wuce, Ard'o yace suje in yaso idan sun shawo Kansa sai su je gaba d'aya hadda su, iya Hari tace bada ita ba gaisuwar uwar kishiya. Lol

Tunda suka d'auki hanya zuciyar Asma'u ta tsinke, tunanin ya zasu k'arke da Baba, tuni ta fara zubar da hawaye, hakan ne ya tada hankalin Abdulrahim ya shiga lallashinta sam hankalinsa ya koma gareta baiji odar da ake masa sai da yayi gab da motar nan ya taki birki da k'arfi Wanda yayi sanadin suka yanke daji, duk sun rud'e ya rasa makama ba abinda ke fita bakinsu sai "innalillahi wa'inna ilaihirraji'un" kiiiiiiii!! Kakeji sun bugi katon icce Wanda yayi dai2 da kamawar motar da wuta....

Koda ja'ama sukazo saidai gawarwaki amma abin mamaki wutar bata kai cikin motar ba so bata k'onasu ba, amma kuma ba rai a tare dasu.

_subhanallah such is life, Allah yasa muyi kyakyawan k'arshe_


Ta hanyar id card jami'an tsaro suka gane garin su, sai gawarwaki aka dawo ma su Ard'o dasu abinda bai wuce 1 hour da rabuwarsu, Allah sarki Ard'o dattijo mai nutsuwa, duk da hankalinsa ya tashi amma sam nutsuwa bata bar jikinsa ba, shida Kansa yayi musu wanka, aka sallacesu dashi aka Sada su da gudansu na gaskiya Wanda kowa sai yaje komai daren dad'ewa.

Iya Hari fa? Sai ihu take zunduma tana fad'ar maganganu na sab'o da rashin hankali, some some ko ba iya sai dai duk a banza dan wannan duk bazai dawo dasu ba, haka aka zauna zaman makoki, mutuwar Abdulrahim ta tab'a gaba d'aya k'auye Kilgori da kewaye dan kowa yasan shi yasan Alkhairinsa da taimakonsa, haka itama Asma'u ga tausayin ta na bata samu ta sadu da iyayenta ba, rayuwa kenan ga Ramlah marainiyar Allah kowa ya kalleta saiya zubar da kwalla, sai Neman Ummi da Abi take tana kuka gwanin tausayi.

Iya Hari tayi sanyi dan mutuwar Abdulrahim ta tab'a sosai d'anta mai biyayya gareta mai kyautata mata, dama sai babu kai ake gane kirkinka ko rashin sa.

Bayan sati d'aya Ard'o da kanshi yaje Sokoto ya tattara duk wani Abu nasu akazo akayi rabon gado, na Ramlah dana dangin mamarta, sokoto jaye ya bud'e account ya zuba su, sannan ya boye duk wani Abu da yake mai Amfani ne gareta, dan yasan Hari ladabin kura ne tayi, hakan  kuwace ta kasance dan tunda kafafu suka d'auke ta tada mugun halin ta, har cewa tayi Asma'u takai mata d'a garin 'yan shan jini an shanye(sai kace ita bata mutu ba amma kuma Abu ga jahili ayi mata uziri) tsabar uwar sai tattaro ta dawo kan 'yar bata mata komai na dangin wanka, wanki da duk wani Abu, duk Ard'o ne keyi mata saiko Shatu in tazo kota aiko a ansa, amma iya Hari da Lanti zagi da duka ne kawai ke had'a su, haka ta kashe kayan Ramlah ta bawa yaran Lanti dan tasan Shatu kota bata bata ansa daga k'arshe ta bita da guntuwar nasiharta, tun Ramlah bata fahimtar komai ta gane Iya Hari bata sonta tun batasan meye zagi ba da duka ba harta k'ere dasu, kullum magana Ard'o keyi amma a banza bataji sai abinda ya k'aru, tuni sunanta ya koma Laure abinka da k'auye, Ard'o ne kawai ke kiranta sunanta na asali, tun tana fad'a har saba itama saidai Sam batasan sunan.

Ganin wahala na shirin kashe k'aramar yarinya yasa Ard'o zuwa Argungu kozai gane dangin mahaifiyarta ya hadata dasu amma shiru ba labari haka zaije tun safe har marece ba sa'a haka yake dawowa cike da tausaya mata, duk wani aikin gidan Ramlah ke yinsa ga zagi da duka kamar ganga, talla kuwa tafi kowa a garin safe rana dare aikin kenan, wahala kawai ta sani a rayuwarta, duk Ard'o na iya k'ok'arin amma anfi k'arfin sa ne, dan da maganar da babu duk daya ga Iya Hari.

Haka ya sakata boko, ta fara kamar abin kirki, tana aji hudu Hari ta tada k'ayar baya, ita batasan ta famdare mata kamar yadda ubanta ya famdare akan boko, haka tanaji tana gani ta fidda ta, saida Malaman makarantar suka suka gayama Ard'o dan Ramlah na cikin d'alibban da sukeji dasu saboda hazak'arta, yace suyi hak'uri, amma Iya tayi mirsisi ta hana, karshema sai dukan tsiya yaja mata dole ta gayamai bataso da Kanta, yasan ba yin Kanta bane amma ya kyaleta dan yasan tunda Hari bataso to magana ta k'are, haka Ramlah ta tashi cikin wahalar rayuwa ga Ard'o da Gwaggo Shatu kawai take jin dad'i, haka take rashin iyaye tasan da sunanan da bata tagayyara ba, suma dangin mahaiyarta kullum fatar ta Allah ya bayyana mata su, Ramlah kenan, yarinya k'arama taga rayuwa......


*ASALIN LABARIN KENAN*



MUJE ZUWA YANZU MUKE FA🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀⛹🏾‍♀🤾🏻‍♀


_yan uwa wad'anda suka damu da rashin ganina suka bincikani nagode sosai da kulawarku, kuma na samu lafia sosai saidai mura ta rage🤧 #one love#_




💄Meryerm Abdool💄
[8/17, 3:52 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



*💘 d best way 2 love is to love and to be loved by sake of Allah*💘





  📝 *Episode* 136--140






   *CIGABAN LABARI*



Kallon kallo, Abdool da kawu Mansur suka shiga yiwa juna alaman tambaya k'arara a fuskar su, Mansur yayi k'arfi halin cewa "Baba kunsan juna ne?" Kasa magana Baba yayi sai nunashi da yake da yatsa baki na rawa..

"Alhamdulillah! Mashaa Allah" shine kalmar da Ard'o ya fad'a tare da k'arasawa fitowa daga zauren ya tunkaro inda suke.


"Dak'yar Baba ya iya bud'e baki yace " Malam Umar ina Asma'u tah, ina 'yata? Ina buk'atar ganinta ina take Malam Umar" duk cikin firgici yake maganar.

Jin abinda Baba yake fad'i yasa Abdool zuwa gabanshi da sauri ya rik'e hannuwansa "Baba Aunty Asma'u kace fa? Yasan inda take ne? Yimin magana Baba" kai kawai yake juyawa ya k'asa cewa tak.

Cikin nutsuwa Ard'o ya kama hannun malam Abubakar sannan ya kalli su Abdool dake tsaye hankali a tashe "kuzo muje daga ciki wannan maganar bata tsaye bace" ba musu suka shiga ciki kamar yadda yace.

Da sauri Alhaji Sada ya taso yana bawa Alhaji Abubakar hannu don su gaisa, shima hannun ya bashi suka gaisa, saidai ganin yanayin yadda suka shigo abin ya bawa kowa mamaki Allah dai yasa lafia.

Zama sukayi bayan an gaisa a fizge abinci aka gabatar musu, amma ba Wanda yayi sha'awar yaci, Malam Abubakar ne ya sake kallon Ard'o cikin rauni "Malam Umar kayimin bayani Ina 'yata ina mijinta Abdulrahim?" Malam Garba jin an ambaci Asma'u da Abdulrahim yasa ya k'ara kallon Baba da kyau tabbas shine bazai manta fuskar ba.

Shima Alhaji Sada cikin son k'arin bayani dan yasan lokacin da abin ya faru da irin Neman da Baba yayi tayi yasa ya kalli Ard'o, su kam su Isma'il basu San komai ba shiru sukayi suna saurare.

Nisawa Ard'o yayi "tabbas bansan ya kake da Abdulmajeed ba, amma zuwanka nan yayimin dad'i ba kad'an ba, kazo lokacin muke matuk'ar son ganinka" nan ya shiga basu labarin abinda ya faru komai bai boyeba har cutar war Hari gareta zuwa Rasuwar su da halin da Ramlah ta shiga zuwa neman sa da yayi tayi sannan yace "ko cikin satin ga natahi Argungu don kawai na nemawa Ramlatuna dangin mahaifiyarta suzo ayi aurenta dasu amma ban dace ba ashe zaka iskoni har gida" ya k'arasawa maganar idonsa jajir don tunawa da mutuwar 'ya'yan NASA.

Baba kam kuka yake sai hawaye wani nabin wani duk taurin zuciya irin nashi Ashe iyakarsa da Asma'u kenan ba rabon ya kara ganinta balle ya nemi yafiyarta, haka Abdool da Mansur, Alhaji Sada sai jinjina lamarin yake yi shida malam Garba, su Isma'il ma jikinsu sanyi qlau, Abdool yayi k'arfin halin magana.

"Yanzu Baba kana nufin Ramlah 'yar  Aunty Asma'u ce?" Cikin ransa kuwa girmama al'amarin ubangiji yayi "Dama asje dan wata gaskiya ta bayyana Allah ya k'addaresa da zuwa Yabo service kuma ya had'ashi da Ramlah ya kinsa mishi k'aunar ta, ashe soyayyar su ta jini da hanta ne, dole yaso jinin Aunty Asma'u dan tayi mishi komai a rayuwa.." Maganar Ard'o ce ta katsesa.

"Tabbas Abdulmajeed Ramlatu jinin jikin Asma'u CE, kuma jikar Malam Abubakar CE, saidai kai bansan ya kake da Malam Abubakar amma jikina na gayamin kaima jinin Asma'u ne?"

Kawu Mansur ne yace "tabbas Allah yayi gaskiya shine keyi a inda yaso kuma Wanda yaso, dani da Aunty Asma'u da Aunty Ameena duka abu d'ayane uwa d'aya uba d'aya".

" ikon Allah kaddai shine Abdool d'in da Asma'u ke yawan fad'a kai kuma Mansur ko? Lallai Allah mai girma ne, Ashe ma kai Yayan Ramlatu ne, kaga aikin rashin sani"(Wanda yafi dare duhu).

Sai lokacin Baba ya samu magana Wanda tsananin danasani yake k'ara rufeshi lallai idan baka godewa Allah ka godewa azabarsa, ko yaushe zai daina Dana sanin wannan kuskure dayayi? "Yanzu Shikenan nida Asma'u ta tahi ba tare data yafeni ba".

Dafashi Ard'o yayi " ka dena fad'ar haka Malam Abubakar, Asma'u bata tab'a rik'eka a rai ba kullum Kanta take d'ora wa laifi, ba safiyar da bata Neman tafiyar ka, har ranar mutuwarta maganar kenan ka yafeta" jinjina kai yayi.

"Asma'u na yafeki tun dad'ewa nifa ki yafeni, naso na had'u dake koda sau d'aya na rok'eki, Allah yayi musu rahama baki d'aya Allah ya Albarkaci abinda kuka bari" nan kowa ansa da Ameen anan aka sake kwararo musu Addu'ar Neman gafara da rahama, kowa jinjina lamarin yake, da k'ara girmama girman Ubangijin talikai (Allah mai girma buwaya).

Nan suke tambayan Ramlah, Ard'o zasu ganta bada dad'ewa ba....

Abdool kuwa zame jiki yayi ya kira Maminsa dan yanzu network a kilgori har d'akin ka, bayan ta daga ne sun gaisa yace.

"Mami yau naga wani bak'on Al'amari".

"Meya faru Abdool?"

"Hmm Mami zakiyi farinciki da abinda naji yau, nasan har tukuici zaki bani".

"Oh nikam meye wannan fad'amin mana".

"Mami maganar tafi k'arfin a fad'eta gani yafi, ki shigo mota yanzu ki ganema idonki".

"To ai bansan gurin ba matsalar".

 "ki taho yabo daga kin iso kimin waya zanzo na d'auke ki"

"OK" kawai tace dan ta k'agu taga meye wannan da baya fad'uwa, shima da sauri ya koma saboda jin an fara Hudubar juma'a....


********************



Delu ce ta gifto ta masallaci ta fito da gida gurin d'akko kayanta, dai2 lokacin taji mai shela na fad'in "madallah aure ya dauru an d'aura Auren *Abdulmajeed Auwal da Ramlah Abdulrahim* kan Sadaki naira dubu 50k, lakadan ba ajalan ba fatar Allah ya d'aure ya basu hak'uri" tanajin haka cikin farinciki ta kwasa da gudu sai gidan Gwaggo Shatu tana haki tana fad'in.

"Laure Ashe dama dan binni ne mijinki, shine kika k'i hid'imana" Ramlah cikin tsananin kad'uwa ta kalleta dan son tabbatar da maganar daga bakinta take fitowa.

Gwaggo Shatu ce ta dafata tare da girgiza mata kai alaman gaske ne, da yake ita tasan komai, sauke idonta kasa tayi tama rasa gane yanayin da take ciki, jinta take kamar ba ita ba kuma kamar mafarki takeyi.

Gwaggo Shatu ce ta mik'ar da ita tsaye tare da Kama hannunta janta zuwa d'akin ta, wani hadd'ad'en material ne milk color anyi mishi ado da fulawowi coffee color, lallausa dashi sai k'amshi ke tashi Ard'o ne ya dinka mata, Cikin sa Shatu ta shirya ta tare yi mata kwalliya mai kyau irin ta 'yan binni, mayafi coffee da shoes coffee suma wow Masha Allah zanso Ku hango Laure a kwalliyar dama gata mai kyau ce.lol ba Irina ba


A can masallaci ana maga d'aurin Aure, Abdool yaji vibration din k'aramar wayarsa dake cikin aljihu, sallat ya zare jikinsa ya fice, Maminsa ce ke kiransa ta iso yabo, hakan yasa bai tsaya ba yaja mota zuwa d'auko ta.

Jauro kuwa Wanda kamar an aiko sa yau ya halarci sallar juma'a Wanda salla sai tayi masa suger yakeyi, cikin kaftan kamar mutumin arziki, bayan an gama salla yaji ana sanar war za'a d'aura aure har zai tafi kuma sai ya tsaya, abinda kunnensa ya jiyo masa ne yasashi dask'arewa nan wai Laurensa aka aurawa wani, ihu yayi iyakar k'arfin sa Wanda ya janyo hankalin jama'a cikin d'aga murya yace.

"Kan ubanga waiisa ya Armi Laure bayan ni, kai liman maza warware armen nan dan bai d'auru, ni kad'ai ne mijin da zai Armi Laure, dan tawa ce nid'ai" sai sambatu yake, mutane kuwa sai kallonsa suke, 'yan gari kam basuyi mamaki dan sun san waye Jauro.

A hankali Ard'o ya tako zuwa inda yake, "Lamiru" Ard'o ya kirashi da asalin sunan shi, kallon shi yayi tare da ansawa dan duk iskancin Jauro yana shakkar Ard'o, duk zuwa gidansa da yakeyi sai tabbatar bayanan.

"Na tab'a alk'awarin baka Ramlatuna koda da rana guda ta?"

Girgiza kai yayi tare da cewa "Aa" murmushi Ard'o yayi.

"Madallah, to ni adda hakk'in armar da Ramlatu ga Wanda nikaso kuma Lokacin da nisso, kuma gashi nayi, dan haka kama gabanka kuma kar in sakejin ka taka gidana" babu gardama ya juya tare da ficewa daga masallacin tare da k'udure haduwarsa da Iya Hari ba kyau.

Duk Wanda ke cikin masallacin abinda Ardo yayi ya burgeshi, dama sun san shi kad'ai ne maganin Jauro da d'iyar wani daban ce da Allah kad'ai yasa yadda zasu k'arke.

Bayan komai ya lafa ne aka dunguma zuwa masauki saidai koda aka duba Abdool babu shi, haka suka koma Wanda zuwansu yayi daidai da isowar Gwaggo Shatu da Ramlah da Ard'o yace suzo bayan D'aurin Aure, tun da Baba ya ganta zuciyarsa ta bashi itace Ramlah dan ga yanayin Asma'u a tartare da ita duk kuwa da basa kama, tafiyar su tsayuwa duk iri d'aya haka yanayin jikinsu saidai ita tafi Asma'u tsayi tun yanzu da take yarinya kuwa.

Itama tana ganinsu saida k'irjinta ya harba, ciki suka shiga gaba d'aya.

"Malam Abubakar ga Ramlah nan" kallon yayi tare da cewa "zonan 'yata" ba musu taje ta tsugunna a gabanshi Kanta k'asa.

"Ba shakka wannan 'yar Asma'u nah ce, wannan jinina ce"cikin firgici ta d'ago ta kalleshi jin ya ambaci sunan umminta, saidai me kama taga yanayi da Umminta duk da foto kawai ta Santa amma tabbas suna kuma ga abinda taji yana fad'i.

Kallon tambaya tabi Ard'o dashi " tabbas Ramlatuna duk Wanda ya dogara ga Allah to zai Isar masa, kuma akai hak'uri akan tabbas zai wuce akai ga nasara, lokacin da muke tunanin da yanke tsammanin ganin dangin mahaifiyarki sai gasu Allah ya kawo mana har gida".

Sannan yaci gaba, "kinga ikon Allah ko, wannan shine kakanki mahifin Asma'u" ya nuna Malam Abubakar, "wannan kawun kine, k'anin Asma'u" ya nuna Mansur, "wad'annan dangin mahaifin Abdoolmajeed ne"  ya nuna su Alhaji.

"Kuma wani abin jin dad'i Abdoolmajeed yayanki ne na jini Ramlatuna d'an Innarki Ameena ne" hawaye kawai ke fita daga idonta tsabar farinciki tama k'asa magana......


***************


Tunda ya d'auko ta take tambayan sa ya gayamata menene hak'uri kawai yake bata tare da cewa ta kwantar da hankalin ta Alkhairi ne, kuma yanzu zata gani, hakan tasa taja bakinta tayi shiru taga inda zai kaita, daidai k'ofar shagon yayi parking tun kafin ya kashe motar ta fito.

Cikin shagon tasa Kanta saboda yadda taji k'irjinta na bugawa, bayan kawai take kallo tana tsugunne gaban Babanta ta bata baya, Sam bata kula da wad'anda ke Cikin shagon ba, Kanta tayi gadan gadan.

"Asma'u nah!"......










💄Meryerm Abdool💄
[8/18, 5:45 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



_A sanadin *HAD'UWATA DAKE* nayi tunanin *WATAN WATA RANA* ni *ABDULMAJID* zan ciri tuta, saidai ina tsoron na shiga musiba kamar yadda *A DALILIN PRE-WEEDING PICS* wasu suka shiga matsala (my next novel inshaa Allah)_


*ina kike k'awata ta kaina, 'yar mutan Niger Raheenat mohmodou, Allah ya barmu tare ya kuma raya mana Nana khady😘*


_Momyn zee, Aysha D na fahimci kuna k'aunar sakwatanci to kuyi cooling zan koya muku😝, wallah kuna k'aunar Abdulmajeed nima ina yinku😘_






     📝 *Episode* 141--145





Kallon kallo suka shiga yiwa juna cikin mamaki, "lallai Allah mai girma na, tabbas badan nasan Ummina mutuwa tayi ba, ba Wanda ya isa yace wannan matar ba itace ba wanga irin kama ta b'aci" Ramlah take fad'a a zuciyarta.

Itama Ameena fad'i take a ranta" wannan ba Asma'u bane, amma behaviors d'in Asma'u kaf irin nata amma basa kama wacece wannan" Baba ne ya bata ansa kamar yasan me take sak'awa "Ameena 'yarki ta, d'iyar Asma'u ce, jininta ce".

Jan Ramlah tayi zuwa gaban Baba " Baba ina Asma'u nah idan wannan 'yarta ce?"

K'wallar da ta taru idonsa ce ta zubo, kafin tace wani Abu Ard'o yace " 'yata Ameena saidai mu d'auki hak'uri" muryan sace ta ganar da ita da mutane a gurin "Kamar ya Baba?" Ta tambaya cikin son jin meke faruwa.

Nan fa labari ya dawo sabo, koda aka gama gayamata hawaye sun gama wanke mata fuska, "Allah sarki Asma'u ashe ba rabon mu sake had'uwa Allah ya had'a fuskokin mu a Aljannah don rahamarsa" Ameen suka ansa daga ta shiga gaida iyaye dake gurin sannan su Hakeem suka gaida ita.

"Zo nan 'yata Ramlah zo kiji domin uwa wanda kika rasa, daga yau baki ba maraicin uwa da yardar Allah"  tare da ware mata hannayenta, cikin nutsuwa taje gareta tare dayin lup a jikinta wata sansanyar ni'ima na ratsata wacce bata tab'a tsinta a Cikin rayuwarta ba, lallai uwa rahama ce, dangin uwa ma rahama ne (duk Wanda yayi nasarar rayuwa da uwarsa ya godewa Allah)

Duk Wanda ke Cikin shagon sunyi matuk'ar bashi tausayi musamman yadda Ramlah ke sauke heart, Abdool dake tsaye bakin k'ofa ya rungume hannayensa a k'irji sai kallon su yakeyi, wani farinciki yakeji burin Maminsa ya cika kullum maganar ta kenan K'anwarta Ameena, yau gata ga d'iyar Ameena, gyaran murya yayi tare da Wanda yasa hankalin mutanen ya dawo kansa karaf idonsa ya had'e dana Ramlah wacce ta d'ago, dama shi ita yake kallo tayi kyau abinta kamar ba Laure ba, inji 'yan garin.

Kallonsa take bata ko kiftawa tsawon sati biyu rabon ta dashi, har ta d'auka sun rabu kenan, Ashe yayanta ne, Ashe shine mijin da Ard'o ya zaba mata, oh yau ina zata saka kanta don murna gata ga dangin mahaifiyarta, ga d'an binni mai glass a matsayin Yayanta kuma mijinta......

Ard'o yace "shigo ciki koni Abdulmajeed, kayi tsaye ga kulkin kohwa"

Murmushi ya sakar mata Wanda yasa tayi saurin sunne Kanta k'asa, shigowa yayi ya zauna kusa ga Alhaji Sada.

"Tau Alhamdulillah mashaa Allah dukkan yabo da godiya su tabbata ga Allah, daya nuna muna wagga rana mai cike da Albarka da farinciki, Abdulmajeed bakada buk'atar ince zan baka Amanar Ramlatuna, k'aunarka ta kuma matarka nasan zaka aza bisa inda nittsaya (zaka d'ora inda na tsaya).

Sannan yaci gaba da cewa " haka kema 'yata Ameena su duka d'iyanki na Allah ya baki ikon rik'o, Ramlatuna" ya fad'a yana dubanta jiki a sanyaye tace "na'am Baffa".

"Ke d'iyata ta gari mai hak'uri, karki canza daga halinki na kwarai da nissanki kici gaba dashi, gida zakina ba daji ba inda 'yan uwanki na, zakina don Allah Ramtuna kici gaba a yadda nissanki Allah ya arbarkace ku gaba d'aya" tuni idanunta suka kawo k'walla duk son da take na had'uwa da dangin ummin nata, gata kuma gaban su a yau amma kuma sai taji batason rabuwa da mahaifarta batasan rabuwa da Baffanta mai k'aunarta, shi kanshi Ard'o daurewa kawai yakeyi amma yasan zaiyi kewar Ramlatunsa...

Mami CE ta share mata hawayen da zuka zubo mata tare da bubbuga mata baya.

Suma Malam Garba da Alhaji nasiha sukayi musu da sanya musu Albarka, anan Ard'o yace zasu iya wucewa, Mami ce tace a kaisu inda iya Hari suyi mata godiya sannan tayi sallama da Ramlah, shikam Ard'o yama manta da wata Hari dan baiyi niyyan sakota a ciki, kai ya jinjina lallai karamcin dangin Asma'u yawane dashi duk da sunji kalar cutar war da Hari tayi ma Asma'u da Ramlah amma duk da haka godiya zasuyi mata..

"Aishatu kikai su inda innarku" Shatu da itama farinciki da ganin yau Ramlah ta had'u da dangin umminta, dama ta dad'e tama mata fatan Alkhairi a rayuwarta ga Alkhairin yazo kuwa, "to Baffa" sannan ta wuce gaba sukabi bayan ta...


*****************

Su Iya Hari da ke zaune zugum kamar masu zaman makoki, tunda sukaji karar mota suka leka, dawowa sukayi suna jiran shigowar Ard'o, saidai babu shi babu labarin shi, kamar an aiki bawa garinsu, tuni suka shaka wai ya wulak'antasu(ji hauka ita da akaba kud'i tayi abinci batayi ba) suna zaune sai zaginsa suke shida Ramlah ko salla sunk'i tashi suyi, yo dama sai anga dama akeyi, sallamar Shatu ce ta katse su.

Ganin Ramlah bayanta yasa Lanti mik'ewa da sauri da niyyan zuwa ta cafkota, ita kuma Iya Hari tana shirin bud'e baki ta fara cin mutunci, sai suka ga ta shigo, a firgice iya Hari ta mik'e tsaye tare da zaro k'ananun idonta, itama Lanti tsayawa tayi cak, kamar photo, murmushi Mami ta sakar musu tuni tsoro ya lullub'esu dan sun d'auka Asma'u ce.

Shatu ce taje ta d'auko tabarma ta shimfida mata, zama tayi sannan tace "ina wuni Iya mun sameku lafia" sai nan Iya Hari ta motsa tabbas kama sai yanzu da taji muryarta tafi ta Asma'u girma, jiki a sab'ule ta ansa itama Lanti haka ta jayo kafafu tazo ta Zauna.

"Nasan ba zaki ganeni ba, sunana Ameena ni yayar Asma'u ce kuma mahaifiyar Abdulmajeed mijin 'yata Ramlah" wani irin kwarjini tayi musu cikin rawar murya tace "Toto madallah" taja baki ta tsuke.

Shatu ce tayi musu cikakaken bayani sun girgiza ainun dajin wannan sabon Al'amari, amma maimakon suyi nadama sai b'acin ciki ne ya rufesu saidai ba damar su nuna dan suna tsoron matar danko shigarta abin dubawa ce.

"Iya dama naso ne da d'iyata tayi muku bankwana sannan kuma nayi godiya da rik'on da akayi mata, mungode Allah yayi Albarka".

Wani irin gunguru gum taji kanta yayi " kodai batasan irin rik'on tayi mata bane ita da Uwarta" ta fad'a a ranta, a fili kuma murmushi yak'e ta k'irk'iro Wanda Sam bai mata kyau ba dan bata saba yi ba.

"Aa babu komi d'iyagga, tau Laure a tahi aita Arme Allah ya Baku zama lahiya" Ameen" tace itama Lanti sanya Albarka tayi, nan Mami ta tashi ta debo kud'i cikin jakarta ta raba musu, sannan ta dunk'ule wasu masu yawa taba Shatu, nan kuwa su Lanti sai hararan Shatu ake, har waje suka rakasu koda suka fito harsu Baba sun fiffito sun tsaya a bakin mota suna jiran su, gaisawa sukayi dasu Iya Hari, sai wani d'ari d'ari sukeyi, ba Wanda ya nuna musu komai a fuska.

Hakan yasa suka d'auka basu sani ba suka d'an saki jiki, hadda yi musu gaisuwan rasuwar munafurci, shikam Abdool kallon su kawai yana jinjina kai lallai mutum ba kyau, nan k'awayen Ramlah suka iso rungume ta sukayi suna kuka itama kukan take, kud'i Mami ta raba musu suma suka wuce Delu ce kawai ta tsaya tana ta kuka, sun rungume juna ita da Ramlah dama itace k'awar ta ainihi sauran duk copy ne.

Ard'o ya rabasu tare da basu hak'uri, Cikin jikinsa ta shige tana Mara yan kuka, shi kansa ya sakata mota tare da rarrashinta "keko dai Ramlatun Baffa ai nace miki idan Mijin naki ya tashi tafiya zan biyoshi inga Mazaunin Ku, ko bakiso in taho na"?

Kai ta girgiza alaman tanaso "Yawwa share hawayen kije kinga ke kawai ake jira" da wayo ya samu tayi shiru Mami kam mamaki wannan soyayya kawai takeyi, Abdool kuwa kallon yadda take kukan take Cikin shagwaba shi dariya abin yake bashi shine zaija motar sai kawu Mansur gaba, ita da Baba da Mami ne baya, kwantar da ita Mami tayi kan cinyarta, tana rarrashinta sannan yaja suka wuce, dama su Alhaji tuni suka wuce.....

Wasai Ard'o kejin ransa yau ya sauk'e wani nauyi a kansa, saidai zaiyi kewar Ramlatunsa, godiya yayi Malam Garba sannan ya shiga gida.

"Tau Hari kega yadda Allah ka ikonai ko, Yau dai keda dangin Asma'u dakikai mata gori kullum akansu kuma ke tabbatar da suna sonta, inama tana raye taga wagga rana...."

Cikin harara ta katsesa "yo Malam mi a sabo nanga (meye sabo anan) dan Mayu sun d'auki d'iyarsu daga sun taimaka mana ma, kuma in kudd'i wane irina a bangani".

Murmushi yayi tare da cewa " baki tab'a ganewa Hari, Allah ya ganar dake" sannan ya wuce abinsu, nan kuwa suka zauna sai fad'a suke ita da Lanti kamar su ari baki (kuwwa baya ga yak'i) itakam Shatu zamewa tayi tai gida abinta tana nema musu shiriyar Allah dan ta fahimci sunyi nisa har yau basu san Annabi ya faku ba(rayuwa shirin Allah inji k'awata swerry)...


********************

A Argungu zabon zaman makoki akayi kowa yazo ganin Ramlah sai yayi hawaye, shikam Abdool ganin abin yayi yawa yasa ya zame ya dawowar sa yabo sai waya yayi ma Mami cewar ya koma, kwanansu biyu har birnin lafia sunje inda dangin Baba, sunyi farinciki da ganin Ramlah da akayi imma iya baki ne can musu, a kwanakin Mami ta Samar ma Ramlah passport sukabi flight sai Kd dan tabar su Husna inda Nanny su Saboda school, Inna kuwa ji tayi kamar a barmata Ramlah saidai ba dama hakan, saukinta ma yanzu matar kawu Mansur nanan tana debe Mata kewa, dan ya dawo yayi aure har da 'ya.

A yau ne mutanen yabo suka shiryama Abdool walimar girmama sunyi k'ok'ari Sosai to ai Abdool d'inne na mutane kowa nashi, sun bashi kyaututukka sosai haka ya baro Yabo cike da kewar garin dan adan zamansa ya saba dasu, suma dai basu so tafiyar sa saidai ta Riga ta zama dole.

Saida ya biya ta Kilgori ya d'auki Ard'o sannan suka biya Sokoto suka sallami Alhaji Sada, tare da d'aukar Hakeem suka nisa hanya.........




🚗

Safe trip





💄Meryerm Abdool💄
[8/19, 10:15 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)







    📝 *Episode* 146--150




Ramlah  data rud'e da ganin Argungu ta d'auka k'arshen kallo kenan, ashe kallo na gaba, balle ta taga jirgi ai gigicewa tayi, saida Mami ta rik'e ta a kafad'arta aiko ta k'ank'ameta, Aa ashe da sauran rigima da jirgi ya tashi, kuwwa tasa saida Mami ta rufe mata baki, tare da boye mata fuska a cinyarta, nan tayi baccin tsoro(tsoron k'arya ne Ramlatun Baffa aida bakiyi bacci ba).

Suna sauka driver yazo ya d'auke su, nan fa kallo ya samu ga Ramlah ido, baki, hanci duk abu d'aya sukeyi taga garin Gwamna ashe na Argungu wasa ne, lokacin da suka isa gida, nan ma wani sabon kallo ganin furanni ko'ina sai kalolin k'amshi suke fitar wa, ita dai Mami sai dariya take mata, ganin Abin bana k'are bana yasa Mami taja hannunta tana fad'in "Ramlah muje ki huta ai idan kallo zakiyi har ki gaji tunda kinzo kenan" kunya taji ta kamata tayi d'an Smiling.

Su Abj da Husna ne suka fito a guje suna fad'in "oyoyo Mami" dama ta kira Naninsu ta gaya mata dawowar ta, jin tsayuwar mota yasa suka fito, turus suka tsaya suna kallon Ramlah.

"Mami wannan wacece?" Cewar Husna.

Janyota zuwa jikinta tayi tare da fad'in "sannu sarkin surutu  bako sannu da hanya sai tambaya ko? To Aunty Ramlah ce, itama kamar Aunty Nihal auntynku CE" Ajb zaiyi magana tace.

"Enough kids Ku bari mu huta mana, Mrs Ask" itakam Ramlah kallon take gwanin sha'awa, sun had'e cikin k'ananan kaya sunyi kyau 'yan birni dasu, rik'e mata hannu da Husna tayi tana murmushi "Aunty Ramlah muje" itama murmushi tayi mata, ciki suka shiga Ajb na rik'e da hannun Mami..

Da murna Inna Kande ta tarbesu, nan suka naje Parlour su Husna sai surutu suke ma Ramlah, abinci Inna kande ta gabatar musu bayan sunci sukayi hamdala, d'akin Nihal Mami ta bud'e ma Ramlah sannan ta nuna mata yadda zatayi amfani da komai, wanka tayi tare da d'auro alwala, gefen wardrobe d'inda Mami ta nuna mata na kayanta ta bud'e daga sama har kasa cike da suturu, wata atamfa ta d'auko a aje gefen gado, gaban mirror taje tayi Shafa, tare da fesa turare powder kawai ta shafa sai lip gloss, kayan ta saka, juyi tayi gaban mdubin tare da sakin murmushi har da rufe fuska da tafin hannunta "nita shin? Yau Ramlah nita a birni cikin daula, ba bugu ba b'aci sai lelena akai" ita kad'ai ke sambatu murmushi ta sake yi.

"Allah na gode maka" dadduma ta shimfida tayi sallah sannan ta fita parlour, da kallon sha'awa Mami ta bita itama da alama yanzu ta fito "iyye 'yar gidan Mami har kin fito, ba zakiyi bacci ki huta ba?"

Murmushi kawai tayi dan batasan tayi magana ayi mata dariya, zama tayi k'asa, tace "Mami ina wuni".

" lafia lau 'yata, ya gajia? "

"Uhm" ta kawai tace.

"Ki saki jikin ki kinji Ramlah nan ma gidane kamar inda Baffa, ni mamanki ce ga k'annin ki".

"Yawwa Mami kikace Aunty Ramlah itama Auntyn muce to ita take ne bamu ganta ba sai yanzu?"

"Oh Abduljabbar rigima, ba gata kun ganta yanzu, Bari dai ina Aunty Asma'u da nake nuna muku fotonta?"

A tare da Husna sukace "an ganta Mami?" Kai ta jinjina "eh kuma wannan 'yarta ce kunga kenan itama Auntyn Ku CE ko?"

"Eh Mami" suka fad'a tare.

Gata sosai Ramlah ta sameta gurin Mami gasu Husna suma suna nan nan da ita, gari aka zaga da ita Tasha kallo kamar idanu su cire, tun tana d'ari d'ari harta sake dasu, haka zatayi ta biyema su Husna, suyita wasansu da hira, maganar ta dad'i take musu suyita kwaikwayonta suka cewa ta koya musu, Mami dad'i takeyi a ranta ganin yadda ta saki jiki dasu, haka take tasata gaba suyi fira kamar k'awarta, dama haka take da 'ya'yanta tana jansu a jiki(sai mun ja yaranmu a jiki mun kusantosu damu muke gane damuwarsu harma mu samar musu mafita, yin watsi dasu ko d'aure musu fuska shike kaisu ga fad'awa a halaka, Allah ya shirya mu dasu baki d'aya).




*********************



4:00pm cikin Kd tayi musu Hakeem suka fara saukewa sannan suka k'araso gida, tarba sosai suka samu gurin Mami, dan tun safe suke kitchen ita yaran dama idai tana gida ita ke shiga da kanta kuma tare da yaranta saboda su koya, Ramlah da yake akwai kaifin baseera ga tambaya tuni ta fara gane makamar aiki irin na birnin, dama ta iya na k'auye tunda ita keyima Hari.

Baffa yaji dad'in yadda yaga Ramlatun sa ta saki jiki, tana mak'ale dashi sai firan birni take mishi dama Ramlah badai surutu ba.

Abdool kam tun da sukayi lunch yayi sallah ya kwanta so ko gaisawa sosai basuyi ba.

Baffa ne zaune da Mami suke fira, k'aramar jakarsa ya d'auko ya fito da takardu da ya mik'awa Mami "Ameena wanga takardu ne da suka shahi gadon Ramlah danaku na wajen Asma'u, sauran takardun haihuwar Ramlatu na, gasunan kuyi mata abinda ya dace dasu, ayi mata komai na d'aki irin naku na nan idan zasuyi, kuma don Allah kada Ramlatuna tazo garemu nan kusa, ni zan ringa zuwa da kaina ina ganinta".

Takardun ta duba kud'i ne masu d'an dama " to Baffa ban katse maka hanzari ba, amma ni ana tunanin tariyar Ramlah ba yanzu ba, karatu nakeso tayi".

Sannan taci gaba "idan akayi la'akari da k'arancin shekarunta, duka shekara 14 tayi karanta da Aure, to ana tunanin in siya mata shares da kud'in ta kamar yadda nayi ma su Nihal, ni zan d'auki nauyin karatun ta, sa'an Nihal ce to ina  tunanin kaita school d'in su Nihal amma ya kake gani."

Murmushi yayi yasan karatu shine babban burin Ramlah duk kuwa da Hari ta tauye ta yasan hakan zai sakata farinciki, amma kuma ai Aure ya wuce komai "hakan nan na Ameena amma baki tunanin in ankai haka an tauye shi Abdulmajeed"?

Tasan Abdool na buk'atar Aure, dan tun yana 18year yake fama da ciwon Mara, Wanda ke nuni dashi mai k'arfin sha'awa ne, to amma ai ita Ramlah za'a cutar ita, abinda ba zataso ga Nihal ba, so duk d'aya da Ramlah gunta, mema ta sani da Aure as 14 kuma tashin k'auye tana buk'atar wayewar kai da ilimi "Baba bana tunanin akwai matsala amma zamuyi magana".

" to ai dan dai kuna nan binni ne amma ai warin Ramlatu ta isa zama d'akin miji".

Murmushi tayi "haka akeyi a k'auyuka shiyasa zakiga anata samun  matsala da wasu yaran akan Auren wuri, aje haihuwa aita had'uwa da yoyon fitsari da wasu ciwuka k'arshe mijin yaji bazai iya ba yayi saki, a maida yarinya bazawara ga kuma ciwo ga yara da k'ananun shekaru" jinjina kai yai alaman gamsuwa d'anshi kanshi ansha kawo mishi irin wad'annan cases a can Kilgori, nan dai sukaci gaba da tattauna wa ya bata goyon baya 100%.

Washe gari ya koma kice da tsaraba, hadda nasu Hari, Mami ta kira Abdool sun tattauna game da karatun Ramlah, dama shima tunanin sa kenan, toshi me zaiyi da ita a hakan ko k'irjin kirki babu, ai bayama tunanin tasan me Aure ke nufi, k'aunarta yakeyi amma badan wani Abu nata ba.

Sun yanke idan anyi Hutu tunda third term ake sai akaita JSS 3 tare da Nihal tunda tana saurin d'aukar Abu, kuma zai cigaba dayi mata lesson kafin shima ya fara aiki.

Zai fita yaci karo da ita ta shigo tsayawa tayi tare da cewa "ina wuni" hararar wasa yayi mata "um baxan ansa ba, bayan kin manta dani da karatun mu kin manta d'an binni mai glass".

Dariya ya bata a yanayin yadda yai maganar kaba baki tayi tare da cewa " Laa Ya Abdool baka barin sunan ga ko?" Tana turo baki.

Shima dariya yai "to ai ke kika sakamin INA"?

" um tona d'ebe maka".

"To 'yar k'anwata Ramlatun Baffa, ya maganan karatun mu?"

"Yawwa Yaya Abdool muci gaba".

" Allah kinaso in sakaki makaranta" gira ta d'aga mishi tana murmushi.

"Lalalala! Yarinyar nan........."





_kuyi hak'uri ban Zauna bana yau, kuma yau kiwar typing ya kamani_




💄Meryerm Abdool💄
[8/20, 11:17 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)




```Abdulmajid fans, naga kuna k'aunar sakwatanci da yawa fa😜 to Ku kwantar da mind d'inku Ramlatun Baffa tace zata koya maku😝 love u guys bohot bohot👌🏻😘```





     📝 *Episode* 151--155




"Lalalala! Yarinyar nan ni kike d'aga wa gira?" Tare da zare ido hadda kama baki, sunne kai tayi Rana dariya k'asa-k'asa.

"Yo ai e a nuhina" dariya yayi tare da lak'ace mata hanci "basakkwata kawai".

Turo baki gaba tayi " kaima ai" murmushi yayi yana feeling special "ai zaki koyamun"  corridor yabi tare da fad'in "jirani ina zuwa".

Dawowa yayi da wata k'aramar leda mai kyau bata yayi " sako ne daga Zainab tace tayaki murnar Aure" cikin zumud'i tace "LA Aunty Zainab tana ina?" Harara yai mata "sai yanzu kika tunata, tana gidansu".

Rungume ledar tayi tana dariya " Yaya ka had'ani da ita ta waya inyi godiya" tau" yace tare da cewa "jeki nuna wa Maminki" da sauri tayi ciki tana murmushi, binta yayi da kallo tare da shafa sumar Kansa, yana murmushi, sannan ya wuce d'akin sa.

Cikin farinciki ta shiga nunawa Mami gift d'in ta "iyye kai madallah kinga ko 'yar cas da ita zatayi miki kyau, kin gode, taji jeki aje a kayanki" da yake Mami tasan da labarin Zainab d'in, gaban madubi ta tsaya tana gwadawa tayi kyau a wuyanta gwanin sha'awa, sai juyi take tana dariya ita kad'ai, dama Ramlah da kwalliya (Ramlatu hankali).


Da dare bayan sunyi dinner suna zaune parlour suna kallo tasa TV a gaba, duk wani attention d'inta ya tattara ya koma can, gani take kamar mutanen fitowa zasuyi saboda girman Tv gashi kuma ta zauna daf da ita, su husna kam rabi ne kallo rabi Assignment Mami kuwa nakan computer tana aiki, Abdool ya shigo har gaida Mami su Husna suka gaidashi, Ramlah kam batasan ma ya shigo ba.

Daf da ita yaje ya saka waiwaya mata hannun sa gaban idon ta "La Ya Abdool yaushe kazo?"

"Ina kuwa zaki sani duka imaninki na a watching, kinga ki dena zama kusa da TV haka kada ya bata miki ido".

Dariya Mami tayi " Ai Ramlah tawa ne da kallo" Tab'e baki yayi "aiko daga yau zata daina dan gobe zamu fara lesson ya zube mata text book da lesson book da sauran instrument a gaban ta.

" hada tadai rage amma ba maganar dainawa, kaima dai ka fad'a ne" Mami ta fad'a.

Itakam Ramlah ganin littafin birjik gabanta haka ta manta da maganan kallo sai tab'a littafan take tana murmushi, yadda takesan karatu aiki daina kallon zata iyayi....


**********************



Kullum da safe da marece suke lesson wata rana ma hadda su Husna akeyi idan basuje gurin lesson d'insu ba, islamiyya kuma da rana sukeyi anan ta unguwarsu mai had'e da tahfiz, uniform hijab har k'asa.

Garden suke shigewa suyi lesson d'in, idan aka gama ta koya masa sakwatanci, in yanayi taita dariya bai iya amma ya daga anan wai ya iya, musamman inya karemata bayan, sai yace "ke hwahinta" waita gane yake nufi aiko dariya takeyi harda rik'e ciki, shiko kallo yake bin ta dashi komai tayi burgeshi takeyi shidai yana k'aunar Ramlah, amma ai dole ya sota kodon k'aunar da Aunty Asma'u ta nuna masa.

Zuwa yanzu kam ta fahimci abubuwa da yawa, dama gata da saurin gane Abu, har turanci tana ji saidai bata iya mayar da kowanne, math ma haka take tsargesa tsab.

A General hospital ta Kaduna Abdool ya nemi aiki, dama Neman ma'aikata suke so nan take suka bashi upper, Hakeem ma anan ya nema shima dai sun dauk'eshi so ana tare har yanzu, kullum suka had'u zai ta tsokanar sa ina 'yar renonsa, banza yake yi masa wata kuma yake "kaji dashi aini naji dad'i tunda inada 'yar reno, kaifa ba wadda ta taya" dariya yakeyi "tab na daik'i rayawa aini matata Unique ce".

Tab'e baki yake "munji zamu gani".

Tuni aka kammala ginan asibitin an zuba komai na amfanin asibitin saidai yace saiya k'ara samu experience tukun zai bud'e ta.

Ranar da akayi Hutu Nihal ta dawo, tana ganin Ramlah nanfa murna ta k'aru dama Mami tayi mata waya gurin malaninsu ta gayamata komai, nan da nan suka sarke kamar dama sun San juna parrot ta had'u da parrot dan kowacce ba baya ba, musamman Nihal ga barkwanci kamar Yusuf, nan ta shiga bata labarin makaranta,

Ramlah sai murmushi take tana imaging irin gata a school a class ana damawa da ita a hostel suna shagalinsu, oh ji take Kamar ace gobe za'a koma duk ta matsu ta ganta da uniform a school, kamar yadda take ganin yara da safe idan sunje kaisu Husna, kaga yara da uniform kala2 kowa tsaf dashi zaije makaranta shi yake burgeta ba kamar k'auyensu ba da sai can suke zuwa kuma sai rana ta fito muraratan wani ma sai yayi sati baije ba, kuma ba wani kwakwaran dalili.

Yanzu Abdool ya rage zama gida tun safe idan ya fita sai shida yake dawowa wani sa'in kuma inyai fitar marece sai 10 yake dawowa shiyasa basu cika had'uwa ba, lesson kuma ya dawo end of week.

Yanzu girkin gida sukeyi sun hutar da Inna kande da Mami, komai sun iya dama ita Nihal ta iya tun can, Ramlah ma yanzu anyi expert........

Hutu ne ya kusa k'are wa hakan yasa Mami taje school din tasu Nihal ta nema nata sukace a kawota ayi mata interview, sun yaba da kwazonta JSS 3 suka sakata kamar yadda Mami ta buk'ata aji d'aya da Nihal, uniform da house wears suka bata nan ma house d'aya aka ajesu, provision sosai Mami tayi musu, komai nasu a had'e, shima Abdool ya dad'a musu, Husna ganin tulin kayan da aka jibgo musu yasa tace itama a had'a da ita a kaisu tare, dariya sukai mata Mami kuwa tace "kwantar da hankalinki baby na 'yar k'anwata aike naki lokacin damasu zakiyi a komai ko school taki ta daban ce".

Dariya ta ringayi tare dayi musu gwalo, dariyar kawai sukayi dan sun San baho ne Mami ta maida ita, satin da aka koma Ramlah ta matsa a kaisu haka aka tattara aka kaisu bayan Mami ta sanbad'a musu kashe din kada su fad'i Ramlah matar Aure ce, musamman ma Nihal dan ta Santa da mugun surutu.

Ita Ramlah har ga Allah mantawa take da Auren sai sha'anin gabanta takeyi, tau 'yan boarding dai an isa ko wace wainar za'a toya a can oho!🤔



*********************



Yauma kamar kullum Mami ta fito zataje office, sai ganin motar Abdool tayi alaman bai fita ba, mamaki ya kamata dan a tunanin ta ya fita tun dazu dan dama bai cika tsayawa ya karya ba, ciki ta koma, can kan bed na hango shi yanata  murk'ususu, cikin gid'imewa ta isa garesa " menene Abdool?"

Cikin muryan wahala yace "Mami cikina marata, Mami ciwo sukemin kamar su balle" tallabe kansa tayi ta d'ora akan cinyarta tana Shafa masa kan cikin tausaya wa tace "ka kuwa sha maganinka Abdool?"

Kaiya d'aga mata alaman eh, cike da tausayinsa tace "kuma har yanzu bai daina ba?" Nan ma da kai ya ansa mata.

Daga shi take son yi "Mami bazan iya tashi ba, d'an samo ruwan zafi ki dannamin gurin" cikin hanzari ta debo a flask tare da k'aramin towel sannu a hankali ta shiga Danna mishi, tun yana 'yar k'ara yana lumshe ido har ya rufesu ruf sai saukar numfashi Mami taji alaman ya samu bacci.

Gefe ta zauna tare da tallabe kumatunta ganin yadda d'anta keshan wahala, kuma tasan maganin abin amma ta zuba mishi ido, to amma meye mafita har ga Allah idan ta bashi Ramlah yanzu ta cutar da ita, dan tayi  k'ank'anta a wannan sabgar, kuma hakan na nufin barin boarding kuma a shekarunta aka had'a mata karatu da Aure an cutar da ita, idan kuma aka cireta itama cutar wa ce "meye mafita" ta fad'a a fili.

Ta dad'e tana sak'awa da warware wa kafin wani tunani yazo mata murmushi tayi ganin ta samo mafita.

Sai 2 ya farka, jikin ya saki gaba d'aya, ciwon ya rage sai kad'an ya rage, kusa dashi tazo dan tana d'akin dawowar su Abj ne ya fitar da ita ta sallamesu suka wuce lesson tayi sallah sannan ta dawo, office ma anata kiranta sai excuse ta basu.

"Abdool ka tashi? Sannu ya k'arfin jikin?"

Murmushi yayi yana k'arajin k'aunar mahaifiyarsa a ransa "da sauk'i Mami kina nan baki fita ba?"

"Bazan iya fita ba Abdool kana wannan halin" mik'ewa yayi tare da rungume ta "love u so much Mamina" itama peck tayi mishi a kumatu tare da Shafa sumarsa "bari inyi wanka Mami".

Fresh up yayi yai sallah, tea mai kauri ta kawo mishi tare da farfesun hanta, kad'an yaci sannan yasha tea tare da shan magani.

Zama yayi kusa da ita " Abdool" ta kirashi, d'ago wa yayi "na'am Mami"

"Ya labarin Zainab?"

Jim yayi danshi harga Allah ya manta da wata Zainab "tana nan Mami wani Abu ne"?

" batayi aure ba?"

"Eh gaskiya banji ba".

"In har bakada wata wacce kakeso bayan Ramlah, to kaje ka nemi Auren Zainab".

A firgice yace " Mami Neman Auren Zainab kikace fah?"

"Hakane Abdool kuwa kai kanka kasan dalili na nayin hakan, bazan iya baka Ramlah a yanzu ba, haka bazan iya ci gaba da  ganin ka a wannan halin ba, kuma banyi dan rashin Adalci wa Ramlah ba, nasan ko ita taji zata fahimceni, dakai a matsayin ta ita kuma a matsayin ka, iya abinda zanyi kenan" jinjina kai yayi Cikin gamsuwa da zancenta.

Saidai ta ina zai fara tambayan da yayi ma Kansa kenan...

Sallamar Hakeem ce ta katsesa yayi ta kiran wayo yin sa shiru, ya biyo yaji lafia......



_wata sabuwa_ 😳

*wai ina labarin Zainab*





💄Meryerm Abdool💄
[8/21, 10:58 AM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)







      📝 *Episode* 156--160






Gaisawa sukayi da Mami tana tambayan iyayensa sannan ta wuce, kusa dashi ya zauna "wai ya haka ne yau ba'a ganka ba, ba'a kuma jika ba, menene inata kiran wayoyinka a kashe" yamutsa fuska yayi.

"Hmm ka Bari kawai ciwon ne ya zagayo, na yau is too pain, maganin ma kamar bansha ba, na jigata fa, sai yanzu nake tashi, ga Mami ko fita batayi ba yau".

Cikin tausayawa ya da kulawa yace " ayya sannu to ya jikin yanzu?"

"Not bad! da sauk'i" ya fad'a ya lumshe ido,

"Haka zakayi ta zama Abdool bayan kasan maganin matsalar ka? Fisabilillah?"

"Maganar da muke yi da Mami kenan, wai in nemi Auren Zainab".

Murmushin jin dad'i yayi " best way, kai gaskiya Mami tayi tunani mai kyau"

Girgiza kai yayi "ba zaku gane bane, nifa ba mata biyu a tsarina, ni Ramlah is OK for me".

Dafasa yayi " common my friend, sau nawa muke tsarama kanmu rayuwa, kuma ba shine tsarin Allah ba, kuma ita Ramlah koda baka ita akayi yanzu I believe ba abinda zaka iya mata cos kana sonta kuma tausayinta kakeji, as her age, so as an advice kayi amfani da wannan damar ka Samar ma kanka lafia, and then in ma son Zainab ne bakayi saika nemo wacce kakeso ba dole sai ita ba, mu'allin shahid d'in dai kayi aure".

Tabbas gaskiya ya fad'i Ramlah is too young so bazai so ta cutu ba, and shi k'aunar ta yake so yanason ci gabanta ilimi shine gishirin rayuwa sai dashi ne zatasan yadda zata Zauna dashi ma, anan yayi na'am da shawarar abokin nashi, shi baya ma tunanin matsala daga Zainab dan yasan tana matuk'ar k'aunar sa, kuma tana son Ramlarsa so shi kad'ai ya isa yasa ya koyi sonta ko kad'an ne, nan dai sukaci gaba da tattaunawa.


************

B'angaren Zainab kuwa tun ranar da Dr Majeed ya gayamata Auren sa take k'ok'arin yakiceshi a ranta, saidai abun ya faskara kullum iyo take cikin sabuwar k'aunarsa, shawarar Momyn ta tabi, duk lokacin da abin ya dameta sai ta dangana shi da Qur'anil Kareem, sosai takejin sauk'i a ranta, hakan yasa ta fara kula wani d'an uwanta dake bacin sonta, amma badan tana jin sonsa ba, danso d'aya ne tak kuma Dr Majeed takema shi, dan shidai take gani a matsayin namiji, amma kuma hakan bai hanata kula Waleed dan tana yak'inin tunda yana k'aunarta zai kula da ita, ba dole ka rayu da abinda kakeso ba kaidai kawai kaso mai sonka, shiyasa take kula Waleed.

Yauma zaune take dawowar ta kenan daga hospital ko uniform bata cire ba, taji k'arar wayarta, "Dr Majeed" ta fad'a tana zare ido, dan rabon tun ranar da sukayi wayar nan, shine last, 5 months kenan a tunanin ta yama manta da ita, ita kuma tak'i kiransa ne saboda batasan abin da tayar mata da hankali shiyasa ta nisanceshi gaba d'aya.

Duk da Murmushin farinciki da take yi, dan har ga Allah taji sanyi a ranta, amma sai ta samu Kanta da k'in d'agawa.

Shi kuma tunanin bata kusa da wayar ne yasa ya k'ara kira nan ma sai nada daf da tsinkewa ta d'aga, sallamrsa ce cikin muryan nan tasa mai sakata suman dad'i, jin tayi kafin ta ansa tana cin magani kamar a gabansa take, tambayan mutanen gida yayi da kuma ita da bayan rabuwa.

"Lfy" ta ansa a tak'aice, sam bai kawo komai ba yace.

"Zainab Inaso ki bani aron hankalin ki magana mai muhimmanci zamu tattauna".

" inaji" ta fad'a in short.

"OK magana ce ta Aure in har kin aminta inaso mu kulla dangantaka ta aure".

" Aure" ta maimaita a ranta "anya Dr Majeed ne kau" amma a fili yi tayi kamar ba zata ansa har saida yace "kinaji na kuwa".

"Eh naji me kace, saidai sorry to say bana burin hakan".

Mamaki ne ya kashe shi wai Zainab ce kuwa mai k'aunar nan tasa ya fad'a a ransa.

" meyasa kikace haka Zainab? "

"Nothing bana dai ra'ayine so sai anjima" kitt yaji ta katse wayar, sororo ya bi wayar da kallo yana Mamakin Zainab ce kuma to amma ai muryanta ne, dogon tsaki yaja.

"Aikin wofi, har ma kin isa".

Ita kuma tayi hakane saboda ta kwatar wa Kanta 'yanci in har gaske yake zai bibiyeta.

Lokacin da ya gayama Hakeem dariya yayi " tokai ka d'auka sauk'i ne dashi dole ta kwaci 'yancinta a hannunka tukun" siririn tsaki yaja, tare da tab'e baki.

"Dama dai son karya ne take min, ta samu wani ne".

Danne dariya Hakeem yayi "haba Malam ai saurin fushi ba naka bane, Aure fa kake nema, ka yarda dani nasan tana sonka kai kanka kasan da hakan son da take maka yafi gaban yaudara, just be patient itama mace ce so dole ta ja aji irin nasu musamman ma idan ka duba yadda kayi auren ka ka kyaleta".

" aiko sai tayi tayi can mata" dakyar Hakeem ya lallasheshi yace yaji, wasa wasa Zainab sai garashi take dan yanzu yana kiranta kullum yana lallashinta ko don cika Umarnin Mami da Samar wa kansa lafia, har saida Hakeem ya saka baki sannan ta sassauto, shiya bata labarin yadda Aurensa ya kasance da yadda suke da Ramlah, da kuma makarantar da aka maida ita "to kinga ko abin a tausaya masa ne, kodon lalurarsa sannan yana sonki Zainab ki kwantar da hankalin ki, ko nacin  da yake miki ya isheki shaida".

Nan take tausayinsa da sabuwar k'aunar sa suka mamayeta, nan ta gaya masa ta Amince suzo su sami Dadynta, ita da Kanta ta gayama Momyn ta yadda sukayi tace" ke gani ko Zainab na gayamiki ai idan rabonki ne zaizo har inda kike, dama hak'uri ne kawai idan ba'a saba, jinjina kai tayi Cikin farinciki.

Mami suka gama yadda sukayi kuma cikin satin sukaje Sokoto, Babanta ya karb'esu cikin karamci, da yake yasan Alhaji Sada, nan take yace su turo magabatansu, tare da Hakeem sukaje inda Alhaji sukayi mishi bayani, har Kilgori suke inda Baffa shima sukayi mishi bayani, yayi na'am kuma yace dashi za'aje Neman Auren.

Daga nan suka wuce Argungu Baba yace tunda yana da Baban sa Mansur yaje masa, ita kuma inna tace kishi take taya Ramlah, nan dai sukayi wasan kaka da jika.

Sunje an tsaida rana  wata uku masu zuwa aka saka sunyi komai na al'ada da Ard'o akayi komai, haka sukaci gaba da soyayyar su da Zainab duk dashi ba wani jinta ransa yake ba, adai rashin uwa yayi Uwar d'aki ne.

Zainab kuma ta dage da kula dashi da nuna mishi salon soyayya dan tasha alwashin saita koyamasa sonta saita samu gurbi a zuciyarsa ko baikai ba kamar na Ramlah ba (fatar Alkhairi Zainab).


*******************

B'angaren 'yan boarding kuwa ranar da aka kaisu Ramlah taga students birjik da irin uniform d'inta, dad'i kamar yayi killing d'inta, bale data ganta a class, gata kan desk ga malamai na shigowa suna yi musu lesson, duka attention nata yana gunsu, 'yan aji kuwa sai zuwa suke suna mata welcome tare da tambayan sunanta suma suna gaya mata nasu.

Ana tashi suka d'auki kayansu zuwa hostel, nan sai murna take tsarin ya burgeshi ga gado up and down, suna sallah suka huta tace ma Nihal.

"Nifa yau tuwon milk zanyi insha miyar Milo" ganin tulin madarar da aka jibgo musu, dariya Nihal tayi "aiko kiyi abinki nidai abincina zanci" 

Nan ta kwaba madara kamar tuwo ta dama Milo tana dibar madaran tana tsoma Cikin Milo, tana ci tana daga k'afa sama Nihal kam sai dariya take mata, suna cikin hakane sukaji an buga CSTA.

Maida abincin Nihal tayi "Ramlah ki kwanta an buga kwanciyar rana" shekeke ta kalleta "haka nan mutum baijin bacci ya kwanta, tab kidai kwanta ke, in kinaji".

Jin alaman senior zasu shigo yasa Nihal kwantawa ita kam sai k'ara daga kafa take tana dariya, " kutuma kit! Ke dan Ubanki me kikeyi baki kwanta ba" wata daga Cikin su ta fad'a.

"Nidai ba Ubana, yo mutum bayajin bacci, na dole zaiyi ne?"

"Ke!! Wa kike zagi d'an kazar ubanki" wata ya fad'a tare da gara bulala zata watsa mata.

Da Sauri Nihal ta tashi "yi hak'uri Senior Zulfa, new comer ce yau tazo".

" me ai irinsu nake nema dama, naga alaman Kanta na rawa tashi muje, filin daga dan k'aniyarki yau zakisan kin shigo boarding "


"Me, meye shi d'in? wallah ba inda zani....."





    *WO Ramlatun Baffa 'yan boarding*🤣















💄Meryerm Abdool💄
[9/3, 9:37 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)




*_Alhamdulillah bini'imatihi tatimmusalihat, may wishes 2 all as d witness of seeing eid~el Mubarak bil khair indeed, takabbalallahu minna wa minkum.ina taya daukacin musulmin duniya barka da sallah, Allah ya maimaita mana shekaru masu albarka Amen, eid Jamil 2 all🙋🏾🙋🏾_*



_And I need ur wishes cos 2morrow is my day, I mean is my birthday, so I need ur concern, hope I will get it!_




*Sallah gift just for u my fans*🎁👌🏻







       📝 *Episode* 161--165






Da sauri Nihal ta sakko daga gadon, duk'awa tayi gaban wata daga cikinsu wacce tunda sukazo gun ko tak batace ba, sai wani kallo da takebin Ramlah dashi wanda ni kaina basan ma'anarsa ba.

"Pls senior Safara'u kuyi hak'uri wallahi bak'uwa ce batasan komai ba akan harkar school" tasan shirun Safara'u ba alkhairi bane dan duk a cikinsu tafi kowa k'eta.

Mugun kallo ta watsa mata "go back to ur bed stupid! Ko sai na had'a dake ne?" Ta fad'a cikin tsawa.

Sannan ta k'ara cewa "me kuke jira ne Zulha a kaita mana idan ba zata da kafanta ba" tare dayi gaba.

Jiki a sab'ule Nihal ta koma kan bed tare da kwantawa tasan halinsu sarai idan ma kana begging nasu kamar zugasu kakeyi, kuma shi yafi komai sauk'i su had'a da ita, gata tsoron a tab'a mata lafiyarta, sam basuda imani shiyasa daga an dawo Hutu suke dawowa basa k'ara ko kwana d'aya(tau anyi missing cin amana).

Ramlah sai kallonsu take d'aya bayan d'aya ko a jikinta wai an tsikari kakkaura, unexpected taji an figxota da k'arfin tsiya, kaman ta kife, haka Zulfa ta fara janta kiiii! A k'asa, turjewa ta farayi amma da yake Zulfa namijin gaske ce, cikin k'arfi taci gaba da janta, a haka suka fice daga room d'in.

Wani corridor sukabi saiga fili ya bayyana tsakanin room zuwa room, already Safara'u na gurin damin buloline gabanta, fuskarta murtuk'e ba rahama a ciki, tsakiyar filin Zulfa ta jefa Ramlah, mik'ewa tayi tare da kakkab'e jikinta tana binsu da kallon renin hankali..

Nihal tana ganin sun fice ne, ta d'ora hannu aka dan tasan yau k'ashin Ramlah ya bushe tunda ta shiga hannun wad'annan hatsabiban miyagu ba da kowa shakkarsu yake, wani tunanine yazo mata da sauri ta sakko a gadon tare da ficewa zuwa room d'in metrum d'insu..

"Wato kega fitsararriya ba, tabas yau zakisan kinzo boarding yau zamu sauke miki kome ke kanki" kallo sauran tayi tare da zabar zabgegiyar bulala, nan fa kowacce ta zabi tata, suka rufa Kanta da duka ta ko'ina.

Ramlah akwai taurin rai kuma idan bugune ai Inda sabo ta saba, saidai fa wannan dukan ya girmi na Iya Hari, amma taurin rai da kafiya irin na Fulani, ya hanata ko motsawa balle kuma ayi tunanin tayi kuka kota basu hak'uri, hakan ya k'ara tunzirasu su ci gaba da jibgarta kamar Allah ya aikosu gareta.

Da gudu ta isa dak'in metrum d'in "Inna Yashe ga can su Senior Zulfa sun rufa da duka akan 'yar uwata da aka kawo yau, kawai saboda tak'i ta kwanta CST".

Mik'ewa tayi tsaye tana salati "Oh ni yashe! Ba an dawo ba, wad'annan ja'iran yara bazasu tab'a barina na huta ba, ke mutahi kahin su la'anta 'yar mutane" a tare suka fita Nihal ta koma d'aki ita kuma ta nufi filin daga.

"Lahaulah wala kuwwati, me nake gani haka? Ke Sanfara kasheta zakuyi eye? Walle ku rabu da 'yar mutane ko 'yanzu in hadaku da firansafal" duk tana k'ok'arin janye Ramlah take wannan maganar, saidai ko kallo bata ishesu ba balle tayi tunanin suji magananta.

Ramlah ta bugu iya buguwa amma saboda taurin rai da kafiya tak'i basu hak'uri kuma tak'i kuka duk kuwa da tanajin bugu har ranta, hakan ya k'ara tunzurasu suketa gibgarta a dole saita basu hak'uri.

Inna yashe kuwa gurin ansar Ramlah aka tsala mata bulala, nan fa ta shiga tsine musu hadda kukanta, gyale ta Zara tana tafe tana bala'i "shegu bak'ak'en d'iya yau iya shegen naku harni bai bari ba, idan na gayama ita firansafal ai sai Ku had'a har ita" a haka ta isa gidan Mama picy tana banbami, nan ta shiga zayyana mata hadda k'ara gishiri, nan take ran picy ya b'aci labour master da sagen ta kira nan suka hadu suka nufi hostel d'in a motarta.




*****************




"Don't ever touch her again useless girls" a tare suka tsaya cak da dukan da suke mata jiyo muryan principal d'insu, a razane suke kallonta tare da sauran mutanen da suke tare dan basuyi tunanin inna yashe zataje ba.

Itama Ramlah jin muryan matan da kuma tsayawar dukan da ake mata dataji ne ya sakata d'agowa da rinannun idanuwanta da suka yi jajir tsabar azaba ta taji.

"U should meet me at assembly ground right now, and announce it 2 all" ta fad'a tare da mik'awa Ramlah hannu alaman tazo.

"Come here dear" da sauri ta isa gareta, rungumeta tayi sannan suka juya gaba d'aya suka nufi mota.

Su Safara'u jiki a mace sukayi announcement d'in sannan suka shirya in house where dake lokacin pref ma ya kusa.

Principal umarni taba labour master akan a kira sauran malamai sannan ta wuce da Ramlah gidanta, ruwa masu zafi tasa maid d'in ta ta tafasa, Inna yashe ta gasama Ramlah jikinta Wanda yayi rud'u-rud'u da zanen bulali ga wani jawur da tayi abinka da fara, rub aka shafe mata jiki dashi sannan aka bata magani tasha, daganan suka nufo assembly ground d'in.

Students da teachers gaba d'aya sun hallara an shiga layi as always, da yake ma farkon dawowane wasu basu dawo ba, fuska murtuk picy ta hau saman gurin tare da Ramlah da inna yashe, addu'a akayi as usual sannan akayi taken k'asa kana picy ta fara jawabin mak'asudin taron na gaggawa.

"Na samu abinda banyi tunani ba a wannan makarantar tawa, wato seniority abin ya bani mamaki da tsoro, kamar yadda kowa ya Sani wannan makarantar private ce, ba government ba, kud'i mai tsoka iyayenku ke biya su kawoku nan dan Ku samu ingantaccen ilimi, da kuma rayuwar 'yanci amma abin takaici Ashe akwai wasu 'yan iska wad'anda sam ba karatune gabansu sai tsabagen k'eta da cin amana, I shock in dis school ace ana irin wannan abun, tanx god dan ba yau aka fara ba amma Allah ya tona mana su yau."

Taci gaba cikin murtuk'e fuska har iya yau "to ba zamu lamunci wannan sakarcin ba ya zama wajibi ayiwa tukkar hanci gudun abinda zaije ya dawo, kuma ya zama darasi ga duk mai niyyan aikata irin abinda sukayi" nan ta kira sunayensu jiki a sanyaye suka hau gaban Assembly duk jiki a Mace, nan aka umurci sajen yayi musu 30 lashes and then labour master ya yanka musu field mai girma gashi schools tayi haki ko'ina, tare da anshe musu prefect ship nasu da tabbacin duk wacce ta k'ara kwantanta hakan to za'ayi withdrew nata ne kawai kuma ba dawowa ko waye ubanta ko, sannan taja kunnen junior akan hakan bazai zama dalilin su raina senior nasu ba, su basu respect a matsayinsu na na gaba dasu, duk wacce aka kawo da laifin raina senior tofa zata fuskanci hukunci.

Da haka taro ya watse junior sai murna suke sun samu freedom, yayin da Senior suka shanye jinin jikinsu.

K'ara kiran Ramlah ta bata hak'uri akan abinda ya faru tare da bata tabbacin hakan bazai sake faruwa ba, a mtsayinta na new comer kada ta tsorata tace ba zata dawo ba, daganan suka wuce class don gudanar da pref, tun daga ranar komai ya dawo normal ba wani seniority a school d'in tuni su Safara'u suka shiga taitayinsu suka kama Kansu.

Sannu a hankali Ramlah ta fahimci boarding da rayuwar boarding, ta saba da ita a yadda take, bata wani sha wahala dan duk k'uncin rayuwar boarding tafi ta gidan iya Hari saidai tana kewar baffa da mami da uwa uba d'an binni mai gilashi, kullum suna tare da Nihal ita kad'aice k'awarta, ba Momy ba Darling duk da dinbin masu son k'ulla alaka da ita da takeda.



***************

B'angaren Zainab kuwa ta Dage gurin Neman fili a zuciyar Dr kuma da alama tayi nasara, don Zee mutum CE mai kulawa da nuna damuwarta akan Abu, tun Abdool bayajin komai game da ita har yanzu yakai yana jinta a ranshi soyayya tsabtatacciya suke gudanarwa kowanne na kaf kafa da d'an uwansa.

Lokacin da ta gayama Waleed ya shiga tashin hankali dan harga Allah yana k'aunar Zainab, saidai dole ya hak'ura don yanason farincikinta, fatan Alkhairi yayi mata, itama tayi masa fatan dacewa da mafi alkhairi.



****************



*End of month* 

Tsaf su Mami suka shirya zuwa visiting d'insu Ramlah cike da provision kaman ba'a zo musu last month da irinsa ba (ni kuma nace koya zasuyi dashi oho) Abdool ne ke driving cike da nishad'i zaije yaga Ramlatunsa, su Husna sai zumud'i suke zasuga Aunty's.

Tun gate Ramlah ta tsinkayo aiko da gudu ta kwasa taje garesu, Nihal sai k'urarta ta hanga itama nan ta bita da nata gudun.

Tasa isa jikin Abdool ta fad'a tare da sakin...........





_Fatan Alkhairi masoya barkanmu da Sallah, barka sake saduwa_🙋🏾






💄 Meryerm Abdool💄
[9/5, 11:49 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)





```😱 Wallahi i'm so speechless, bansan da wane word zanyi amfani na gode maku ba friends, kun nunan k'auna sosai, kunyi min k'ara nagode da birthday wishes naku, Allah yabar zumunci da k'auna Ameen👏🏽💋```







     📝 *Episode* 166--170




Tare da sakin kuka "subhanallah Ramlah kuka again menene kuma ko an k'ara dukanki ne?" shiru tayi tare da lafewa, yayi dai2 da isowar Nihal da murnan ta, ta rungume Mami "uhm ba'a mata komai bafa kawai dai tana murnan ganinku ne, kunsan munyi missing naku".

Dungure mata kai Mami tayi "tau parrot munji, aifa yanzu zaki fara surutun naki" sannan ta Shafa kan Ramlah "dota haka zaki dinga mana ko, aiko saimu daina zuwa tunda tayar maki da hankali muke, sai a ringa aiko maku Sale driver kawai".

" Aa Mami na daina baran k'ara ba, kinji Mamina?" Ta rungumeta, su Husna sai dariya suke mata, Abdool kuwa kallonta kawai yake yana murmushi, a haka suka k'arasa Filin visiting d'in.

Wani babban carpet suka shimfid'a aka zazzauna, abinci aka gabatar nan sukayi lunch gaba d'aya, sai nishad'i su Ramlah keyi, ji suke kaman a gida ake, daga nan aka shiga fira, sunata basu labarin School wahalarta da dad'inta, nan suka gangaro firar gida Mami ke gayamusu Auren da Abdool zaiyi.

Duk da k'aranci shekaru irin na Ramlah saida Abinda ya daketa a zuciya, amma dake tanada wayo saita waske, murmushi tayi tare da d'an tsalle.

"Allah Mami, waye matar?" Nihal kam kwab'e fuska tayi tare da turo baki, Abdool kam ji yayi ba dad'i duk sai yaji wani iri.

"Auntynki ce fa Zainab".

"Lah! Aunty Zainab? Wlh nayi murna sosai Yaya, pls d'an kira mana ita mu gaisa Yaya"

Shidai baice komai ba sai kallonta yake, Nihal sai jifanta da harara take irin ta bata Haushin nan (oh su Nihal akwai aiki kenan) Mami kam sai murmushi take ba kad'an ba Ramlah ta burgeta, saidai dama tasa hakane zai kasance dan tasan ai yarinya ce da wuya ta damu tunda ko ma'anar auren bata sani ba.

"Kaji Yaya" ta k'ara fad'a hakan yasa dole ya kira mata ita, aiko da murna suka gaisa, hadda su Nihal duk sun gaisa ta tare da tambayansu karatu.

Zainab ta yadda da Ramlah yarinyace sosai kamar yadda Abdool ke fad'a, ko a jikinta bata nuna ta damu ba hadda kiranta da Aunty, nan take ta sak'a a ranta zatayi zama mai kyau da Ramlah zata rik'eta kamar su Amal k'anninta, zata roki Allah ya yaye mata azabar kishi da takeda.

Anan suka wunin musu tun safe sai marece suka wuce, suka barsu da kewa, haka suka kwashi kayansu nik'i-nik'i sai hostel, Nihal kam tun tana mata fushi ganin bata kulata yasa ta ware sukaci gaba da sha'anin gabansu...


********************


Kwanaki sunja wata ya wuce tuni su Ramlah sun zana jarabawarsu anyi Hutu, an dawo gida cike da farinciki, sai kuma hada hadar biki da aka shiga basu can basu nan Nihal ma tuni anyi giving up, dan ta fahimci Aunty Zainab akwai kirki tuni suka saba da ita kullum suna mak'ale a waya, tuni sukayi sabo har ma da Amal kanwarta kusan sa'arsu ce, Baffa kamar yadda ya alkawaranta yazo ganin Ramlah ranar kuwa kamar ta koma cikinsa tana nanik'e dashi har dare bacci ne kawai ya rabasu, kashe gari ya koma da kukanta da komai na kar ya tafi, haka Mami ta cikasa da tsaraba, itama Ramlah ta bada tata akaiwa iya Hari da gwagwaninta da Aminiyarta Deluwa.

Komai aka saka masa lokaci to za'a yazo kamar wucewar iska, a yau dubban jama'a suka shedi d'aurin Auren Abdulmajid Auwal Sada da Zainab Salis Madaki, taro yayi taro can na hango Ango da abokansa su Hakeem k'irjin biki, su Ismael da sauran su, gefe d'aya su Alhaji Sada na hango su Baba, Ard'o ma ansha rawani, su kawu Mansur, su Dady Ayuba, Sani, salis, Rabi'u, Dadyn Hakeem, duk ba'a barsu a baya uban amarya ma baki har kunne tsabar farinciki taro dai mashaa Allah sai fatan Alkhairi.

Cikin gida na garzaya, ya cika ya batse dak'ar na zak'ulo Amarya subhanallah zanso Ku hasko Zee tayi kyau like take away, ni kaina sai daga baya na ganeta sanye take cikin wani Arnen code lace Red and golden, head, shoes, purse duk golden ne, anyi mata d'auri irin na Amare fuskar tasha make-up sosai irin na amare, sai k'amshi take zubawa kamar anyi barin perfume a jikinta.

Ido ta k'ara warewa dan ganin 'yan biki dakyau can na hango su Ramlah ansha ankon wani material black and silver su uku da Nihal da Amal, ware ido nayi nace su kuma wad'annan yaushe gari? Harara ta balla min "naki wasane ai tun ranar da aka fara even muka bayyana" ah lallai kunsha gari na fad'a tare da k'ara wa kafata iska, Uwar Amarya sai nan da nan ake da bak'i zuciyarta fal farincki ayau sun sauke wani nauyi d'aya rataya a kansu, sosai ta yaba da Ramlah don tun zuwansu yarinyar ta kwanta mata arai duk Wanda aka nunama ita a matsayin abokiyar zaman Zainab saiya yaba don dagani yariyar batada matsala ita kam batamaso ana nunata, sai sunne kai take tanajin kunya dan harga Allah mantawa take da auren.

Zuwa karshe 4:00p suka nufi giginya hotel inda aka gudanar da mother's day, last even nasu sai dare aka tashi inda su Ramlah suka rak'ashe kamar ba gobe, su Abdool kam basusan ma anyi ba, dan ana gama d'aurin aure suka d'auki hanya don gudanar da tasu walimar da Hakeem ya shirya musu.

Washe gari da saffafe motocin d'aukar Amarya suka sola hanya, bayan tasha nasiha sosai daga iyayenta, sai kukan rabuwa take da gida duk soyayyarta da Abdool.

2:00pm a Kd tayi musu gidan Mami suka sauka bayan sunci susha an dank'a amanarta ga surukar tata, daganan Mimi da k'awayenta sukayi musu jagora zuwa gidanta dake unguwar malali Wanda Abdool ya kama dan yace gidan sa na cikin asibitinsa ba yanzu zasu tare ba sai ya an tashi bude hospital din gaba d'aya.

Gidane matsakaici mai kyau dashi, sosai danginta suka yaba, har kuryar d'aki kan gadonta sannan suka barta da k'awayenta suka koma gidan Mami inda sukayi masauki.

Haka k'awayenta suka sakata gaba da tsokana yaudai gata ga Dr tsami yakar, shiru tayi musu tanata murmushi Allah dai tasan farincikinta a yau, yau gata gidan Aure kuma da masoyin rayuwar ta Dr Majeed......





Manage



💄 Meryerm Abdool💄
[9/8, 12:01 AM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)






```SAKI KOWA KAMA ALLAH, YI SOYAYYA DOMIN ALLAH, KAYI KIYAYYA DOMINSA, KA YARDA DOMINSA, YI FUSHI DOMINSA, KA JUYA BAYA DOMINSA, KAI KOMAI MA YA ZAMO DOMINSA ZAKACI RIBAR RAYUWA```

Small quote👌🏻







     📝 *Episode* 171--175





Haka sukayita nanayensu a cikin gidan, daga gidan Mami aka kawo musu abinci zuwa k'arfe 4:00pm suka gudanar da waleemar da su Ramlah suka shirya, wacce sai 6:00pm aka tashi, wata malama ce tayi lecture inda tayi tsokaci akan zaman Aure, Ramlah hawaye har gemu kamar itace amaryar duk da k'arancin shekarunta ta fahimci abubuwan da akayi bayani akai dan Ramlah akwai wayo kamar ba 'yar fari ba, bayan an tashi dasu akayi gyaran gidan tsaf aka gyare ko'ina nan take gida ya d'auki sheki da k'amshi, gida suka koma suka kawo musu dinner sannan sukayi musu sallama, kowa sai yaba hankalinsu da k'ok'arinsu yake.


9:00pm sukaji tsayuwar motocin angwaye, amarsu k'ara jan lafaya akayi aka rufe ruf, sai murmushi take Wanda da gani ba tambaya na farinciki ne, suma dai k'awayenta kimtsawa sukayi tare da kama baki.

A parlour ya tsaya da abokansa su biyar ne harshi, sanye yake da danyen boyal dan ubansu milk colour riga da wando harda babbar riga ya d'ora bak'ar hula, glass nasa as usual sai watch na azurfa cover ne bak'ake a k'afansa, wow Dr Majeed ya Had'u over kamar a sure a gudu, ciki ya shiga tare da cewa su fito parlour su gaisa da abokansa.

Babbar k'awarta ce ta rik'ota suka fito, nan akayi gaishe-gaishe da barkwanci irin Wanda ake as an al'ada daga nan suka siya baki tare da sallamar 'yan matan Amarya dan sammako zasuyi gobe, 'yar nasiha sukayi daganan taro ya tashi da addu'ar rufewa, nan k'awayenta sukayi mata sallama dan da wuya su samu shigowa gobe, sannan abokan ango suka saukesu gidan Mami.

Rakiyarsu yayi koda ya dawo bata parlon murmushi tare da danna kansa cikin bedroom, can k'arshen gado ya hango k'udundune ga sautin kukanta na fita a hankali, tsayawa yayi tare da zuba mata ido, "kukan me kenan" ya fad'a a ransa, d'an tab'e baki yayi "au na munafunci irin na Amare ba" da sauri ta dago ta kallesa da jajayen idonta, karaf idonsu ya had'u, sam baisan maganan a fili yayi ba, saurin waske wa yayi ta hanyar sakar mata murmushi, tare da kanne ido d'aya, cikin sauri ta sauke idonta tana ci gaba da kukanta.

Takowa yayi zuwa inda take, tare da zauna wa dab da ita, hannunta ya kama "Zainab" ya fad'a cikin muryan nan tasa mai sakata ladabi, bata d'ago ta kallesa ba amma ta tsaida kukanta, k'ara kiranta yayi a karo na biyu wannan karon ma bata ansa ba saidai ta d'ago idonta, cikin salo yasa yatsarsa akan fuskarta ya lakuto hawayenta cikin iyawa ya lashe hawayen, k'uri tayi tana kallonsa, dan yazo mata da sabon salo Wanda batasan dashi ba, da haka ya shanye hawayen tsaf, sannan ya ciro handcar ya goge mata fuskarta tsaf itadai da kallo kawai take binsa anya ko Dr Majeed ne, Wanda har yau daya zamo mijinta bai tab'a furta mata kalmar I love u ba "Hmm nashi salon soyayyar kenan" ta fad'a a ranta.

Batayi aune ba tana sak'ar zuci taji ya zame mata mayafi da d'ankwali nan k'ananun kitsonta ya zubo baya, kan sai fitar da sinadarin k'amshi yake, hannunsa d'aya ya tura a cikin gashin yana shafawa d'aya na rik'e da hannunta yana shafa lallen da aka rangad'a mata, kansa na kan kafad'arta idonsa a lumshe yana shako daddad'an kamshinta, cikin muryan maye yace.

"Wa yayi maki wannan abubuwan?" 

Itama duk ya saukar mata da kasala, "gurin salon ne" ta fad'a cikin rawan murya.

Murmushi mai sauti yayi tare da mik'ewa itama mik'ar da ita yayi sannan ya ja hannunta zuwa toilet alwala ya umurceta tayi ba musu tayi shima anan yayi sannan suka fito darduma babba ta shimfid'a musu sannan ya jasu nafila, addu'a sosai yayi musu sannan yace.

"Zainab ayau kin zama sirrina nima na zama sirrinki, mun zama one, nasan kina k'aunata nima ina k'aunarki" d'agowa tayi ta kallesa.

Kanne mata ido yayi "yes I love u are u surprise?" Batace komai ba sai ido datake binsa "ina k'aunarki da gaske, so inaso mu gina aurenmu akan k'auna da hak'uri su kad'ai idan muka rik'e sun ishemu saboda suna nufin abubuwa da dama a cikin aure fatar kin gane?"

Girgiza kai tayi "na gane kuma inshaa Allah zan kiyaye".

"gud gal" ya fad'a tare da mik'ewa ya fita tare da dawowa da tire mai girma, kaza ce k'atuwa sai fresh milk da exotic ga cup da flates, gabanda ya diresu sannan ya janyota jikinsa ya fara bata a hankali tare dayi mata rad'a a kunne Wanda ni Meryerm Abdool bansan me yake gayamata ba.

Murmushi naga tanayi daganan ta fara bashi itama cikin kunya, a haka suka ciyar da juna, cikin ransa yana sak'awa "inama tare da Ramlatunsa ne, hmmm ko yaushe zai gansu haka da ita?" har cikin ransa yanason Zainab koba komai tanada hak'uri da kirki kuma yayi alk'awarin zama da ita tsakani da Allah tunda harta kasance mallakinsa.

A ranar dai an gwangwaje amarci tsami yakar Dr Majeed an angonce.


( _Sorry Ramlah team 😜_ )



*******************





*washe gari.....*


12:00pm su Ramlah ne, suke fitowa daga room d'insu wanda tashinsu kenan, tun da sukayi asuba suka koma saboda tsabar gajia duk da ba al'adarsu bane, ko yanzu ma yunwa ce ta kwakwulosu ko kayan bacci bata cire ba ta fito dan samun abin tab'awa tana fitowa Abdool na shigowa gidan da sallama idonta ya sauka a kansa sanye da yadi baki anyi mishi aiki da farin zare, sai sheki yake alaman ya angonce, kallo d'aya tayi masa ta kauda Kanta tare da ansa sallamarsa wayancewa tayi tare da gaidashi tana tambayan Aunty Zainab tun kafin ya ansa ta shige kitchen sai wayam ya gani, dai2 fitowar Nihal itama gaidashi tayi amsawa yayi "waiku sai yanzu kuka tashi kuke nufi" eh wlh Yaya duk gajia ce".

Tab'e baki yayi "gajia ko lalaci" tare da shigewa d'akin Mami, turo baki tayi "haba dai ai idan ba,a yaba ba bai kamata a tsine ba, kan kujera ta fad'a.

Minti kad'an Ramlah ta fito rik'e da plate d'in indomie " oh so much heart u Sisto thanks " harara ta dalla mata "no more thanks baby shige ki had'o mana tea kawai" mik'ewa tayi tare da cewa "done maa!" Smiling tayi "kyaji dashi tare da shigewa room d'insu.

A gurguje sukayi break tare da fresh up, yauma akon atampha sukayi brown and milk mai ratsin black anyi musu gown, koda suka fito parlour Mamace sai matar uncle Mansur da Abdool da kuma su Husna " Ahh Morning Mami" suka fad'a a tare "morning daughters, an samu tashi"

"Eh wlh Mami gashi har mun shirya, am Mami naga gidan saiku kaddai duk sun tafi" 

"Naku wasa ba kunacan kuna bacci ba, kila ma sun wuce zamfara yanzu" 

Zaro ido Ramlah tayi "nafaji kamar maganar Amal tana cewa sukam zasu wuce, duk a mafarki da d'auki zancen Ashe gaske" 

"To lallai ai su sunji k'amshin gida"

"Allah ya kiyaye hanya zamuyi mata waya da wayan Yaya" cewar Nihal

"Oh Aunty Sarat barka da safiya ya gajia" um sai yanzu kuka ganta amma ai gwara ma ke matar uncle kin samu nikam ko oho" murmushi kawai tayi tare da ansawa da yake bamai son surutu bace.

"Lalala! Kai Yaya kaifa muka fara gaidawa duk gidannan".

" tab wannan gaisuwar anayi ana guduwa kitchen bana sonta" 

"Uhmm to Morning Yaya Abdool ya Aunty Zee?"

"Kokefa lafia qlau, Zainab kuma tanacan tana jiranku"

"OK ai yanzu can zamuje" 

"Yawwa naji Mami tace wai zakubi matar uncle Argungu kuyi hutu?"

Cikin murna sukace a tare "eh Yaya" 

"Hmm kuna sane da one week ya rage a resuming school ba" 

"Eh ai sati kawai zamuyi sai mu dawo mu koma kawai".

" to ba inda zaku" ya fad'a yana tsuke fuska "pls Yaya munyi missing Inna sosai" Ramlah ta fad'a, da muryan shagwab'a, ita ma Nihal begin nasa tayi.

Mami dake kallonsu tana murmushi bakinta ta sako "kaiko ka barsu suje mana, tunda driver zai kaisu kuma shizai koma ya d'akko su" duk da ta fahimci tafiyar Ramlah ce bayaso dan ko school yaso tayi day.

"Kunyi sa'a Mami ta saka baki" 

"Yeeep! Mungode Mami" suka fad'a suna rungumeta, nansu Husna suka saka rikicin suma zasu, dak'ar Mami ta shawo Kansu akan zasuje da ita, kwashesu yayi har Matar Mansur ya kaisu gidansa.

Tun daga parlour suke zuba mata kira "Aunty Zee"

"Um nayi fushi Aunty Ramlah" dake haka take kiranta.

"Kema Nihal juya kawai banaso, matar uncle sannu da zuwa shigo mana, twins d'in Mami kuma banaso" ta fad'a tana musu hararan wasa.

"Sowie Aunty Zee pls wlh bacin gajia ce ya sacemu, pls apology" suka fad'a tare sukan su Husna sai dariya suke.

Juyamusu baya tayi, gaban ta suka shige tare dayin kneel down hadda kama kunnuwa, dariya ma suka bata aiko darawa tayi.

Suma dariyar gaba d'aya sannan suka k'arasa ciki, nan sukaci gaba da firansu kaman wasu k'awaye, tare sukayi girki rana da yake an kawo musu break da gidan Mami sanin suna can yasa bata aika musu na rana ba, sai 6:00pm Sukabar gidan cikin nishad'i dak'ar Zainab ta barsu suka tafi.

Koda Abdool ya dawo sun wuce dan tunda ya ajesu ya wuce gurin abokansa sai after magrib ya shigo, daya isko sun wuce sai jinini yake akan meyasa basu kirasa ya kaisu ba.

Abune ya tokare mata wuya dan tasan duk akan  Ramlah ne yake fad'an da sauri ta nemi tsarin ubangiji akan wannan zazzafan kishin nata, bata Bari ya fahimci komai ba ta shiga rarrashinsa cikin salonta tuni ta shawo kan abinta.lol


********************


Washe gari su Ramlah suka Lula Argungu, cike da gargadi da dokokin oga Abdool.

Satin d'ayan da sukayi Argungu ba k'aramin enjoying sukayi ba, ga kakkaninsu sai nan nan suke dasu, sun zaga gari sosai sunga abubuwan tarihi birjik (dama duk Wanda yasan Argungu yasan garin tarihine musamman game da kamin kifi 😜 )


Har besse sunje da birnin lafia, sannan driver yazo ya kwashesu cike da kewarsu suka barsu suka Lula Kd.

Shirye-shiyen konawa school suka shiga.........



 _ayi shiri lafia 'yan boarding kaddai a manta da kwaki da k'anzo_ 🤣😂 







"Meryerm Abdool"
[9/9, 3:14 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)





```Nafeesa Nuhu(Sadnaf) here is ur page for ur support, thanks much momyn Affan, Allah ya raya Affan& Ikram kan tafarkin musulunci ameen #Ana mugun tare#🤝```





*Manzon Allah S.A.W yace "idan kayi imani da Allah da ranar karshe to kasowa d'an uwanka abinda kake sowa kanka" ingantaccen hadisi ne. 👌🏻*







   📝 *Episode* 176-180



Babban mall Abdool ya kaisu sukayi provision, tare da Zainab sukaje itace ke tayasu d'ibar kayan, siyayya sosai, gidan Mami suka wuce direct da ita akayi gyaran kayan tsaf, sannan ta shiga K'ara musu haske game da rayuwar boarding dayake itama ita tayi, sosai sukaji dad'in bayaninta dan sun k'aru dashi, nan ta wuni sai bayan isha suka Abdool yazo d'aukarta nan wata firar ta ballewa.

"Um kasan me ya Abdool? Nifa inaga journalist zan zama dan gaskiya akwai ni da tambaya" cewar Ramlah.

Murmushi yayi "kema kin gane da kanki kenan, aini har tsoro tambayan ki nake kada na kasa ansawa, musamman lokacin da nike d'an binni mai glass".

Dariya aka kwashe da ita har ita sannan tayi mishi hararan wasa tare da turo baki "badai zaka daina ba ko yaya?"

"Kyalesa Aunty Ramlah sai munyi maganinsa d'an binni mai glass kawai dashi, kinga rabuda shi ki koyamin filatanci kinji" Zainab ta fad'a tana k'unshe dariya.

"Kai Aunty Zee da wayo kema kin k'ara fad'a ba" Nihal ta fad'a itama dariyar ce take k'asa-k'asa.

"Ba ruwana daku gaba d'aya ai duk na harbo jirginku" mik'ewa tayi da niyyan shigewa d'akin Mami da yake ita bata parlon, da sauri Abdool ya rigo hannunta yana fad'in "haba Ramlah love Ramlatun baffa wasa muke fa."

Abu ne ya tsayama Zee a mak'ogoro dak'ar ta had'iye da addu'a tare da murmushin yake "Eh Aunty Ramlah wasa muke fa".

Kwace hannunta tayi ba tare data juyo ba " naki nayi d'in " dai2 da fitowar Mami tana dariya itama "kai kun fa dami dota da tsokana banaso fa" janta tayi zuwa seat tana Shafa mata kai, su kuma sai rike dariya suke ganin yadda ta kumburo baki wai ita a dole fushi tane, Abdool sai kallonta yake cikin K'auna shikam komai tayi burgeshi takeyi "Ahhhh ina sonki 'yar K'anwata" ya fad'a a ransa..

Zainab na ankare dashi tuni abin ya motsa (oh wannan kishin Zee anya kuwa, um barin yi shiru kada Zee team suji).

Agogo Mami ta kalla har tara ta gota "kai Ku tashi Ku tafi haka nan mungode" dariya Abdool yayi "Mami abin harda kora"? " eh dai Ku tafi dai, Ku kuma kuje Ku kwanta kunsan gobe sammako zakuyi tunda in schools days ne".

Zainab da ta matsu su tafi kada ta k'asa controlling Kanta har a fahimta inda Ramlah taje tana murmushi tare da jan kumatunta "haba Aunty Ramlah saki fuskar mana daga yaune fa" had'i dayi mata chakulkuli aiko batasan lokacin da ta saki dariya ba.

Nan sukayi musu sallama har mota su Ramlah suka rakasu, nan sukace sai sunzo gobe rakiya da yake sune zasu kaisu, saida safe sukayi kana suka koma ciki, su Husna suka kai d'aki wad'anda bacci yayi gaba dasu a parlour...

Washe gari tun da sassafe su Zainab suka zo, anyi sa'a suma sun kintsa tsaf nan suka sallami Mami, suka wuce su Husna suka fara ajewa a school sannan suka Lula *F.G.C* su Ramlah hadda hawaye sai shagwab'a take zubuwa Abdool yana biye mata, Zainab dai d'aurewa kawai take amma kam abin tsikarta kawai yake.

Dak'ar ta barsu suka wuce, cike da missing nasu, dan zamansu sun saba sosai kamar kada su tafi sukeji musammam Abdool zai nisanta da mintin zuciyarsa.


( _Asha karatu lafia 'yan makaranta_ 🤣 )




********************




Abdool ne zaune cikin office yana rubuce-rubuce, turo k'ofa akayi da sallama ya shigo, ansa sallamar yayi ba tare daya d'ago ba "kaga mijin mata biyu fa, mijin Ramlatu angon Zainabu" Hakeem ya fad'a cike da tsokana.

Malalacin smiling yayi masa "kaji dashi dai imma da gatse ka fad'a haka abin yake dai, point of correct angon Ramlah zakace don itace uwargida kuma amaryar gaban goshi".

Dariya Hakeem ya kece da ita " ahaf ai kuwa saita gaban goshi shisa naga an rangad'a mata rival, kai yaron nan ko kunya bakaji k'arami dakai sai fitina har biyu gamu ko d'aya bamu ije ba".

"Kanka akeji kuma, nidai nasan menakeyi, hmm wani abun ma sai kaji an fara kirana Dady".

" Hhhhhhh, cool man muma fa muna hanya kuma ni matata da 2 zata fara".

"Ka tsaya wasa dai harna kai Ramlah gida itama ta aje nata, oh imma ka jinkirta ai sai na baka 'yata"

Harara ya banka mai "cuti amma kai baka sona wlh, saina zauna harka bani 'yar da ba'a haifa ba ma".

Dariya ya sheke da ita "naka wasa, kadaici gaba da ruwan ido kaga"hmmmm ba zaka gane ba amma I will give u much surprise, um ni kaga yaushe tafiyarka?"

"OK till u give it!, kaga ma file d'in wurina nakeso na hahhad'a nayi submitting nasu, ina ga dai zuwa upper week zan wuce" India aka turashi course na one year.

"OK but da Zainab zaka wuce ko?"

"Umm gaskiya saidai naje naga yanayin gurin in yaso daga baya saita biyo jirgi in naga akwai damar tazo saboda tsaro" ya k'ara sa fad'a yana dariya.

"Kaifa ka gama lalacewa fa yaron nan".

" lalalalah mutum da iyalinsa ana kira masa lalata" ya fad'a yana bud'e bakin tsokana.

"Kaji d'an tsari"


A cikin satin ya kammala komai, sallama yajema su Ramlah da yake time d'in suna school, aiko yaga kukan shagwab'a wai ita zata bishi can, tayi karatun a can shiko sai biyemata yake tabbas zaiyi missing nata sosai ya sani, Zainab ta tausaya musu dan tasan irin son da yake mata, baya iya boyesa ko kad'an ita kuma dole taso abinda yakeso tun balle Ramlah da takeji har ranta, saidai kasan zuciyarta sai zafi yake amma kuma tana Neman tsarin Allah da wannan kishin dan bata fatan cutar da Ramlah koda da fatar bakine, dak'ar suka rabu bayan ya cikasu da provision da pocket money.

Watan 2 a India ya turowa Zainab visa ta iskoshi, saboda tsaro inji shi, amma kuma kasan Ransa Ramlah yake missing sosai dan ko ganinta kad'ai ba k'aramin nutsuwa yake saukar masa ba.

Suna wasa time 2 time a wayar Mami in kuma suna school ta hanyar malamansu duk k'arshen wata yakan turo musu kud'i duk da Mami ta hanashi amma ganin yake ai nauyinta na kansa kuma dole ya sauke, zamansu a India zamane mai cike da nuna kulawa da tsantsan soyayya, kowa tattalin dan uwansa yake musamman Zainab har tausayi take bashi Sam bata gazawa da lalurarsa kullum cikin hidimarsa take.

B'angaren su Ramlah sun maida hankali sosai akan karatu, duk abinda ya shige mata duhu zata tambaya hakan yasa ta zama zakaran gwajin dafi malamai da dalibai kowa sonta yake....


********************

Suna SS1 aka kawo wata new comer class d'in su, 'yan class sukayi ruu kowa son magana yakeyi da ita ganin ta mai kyau ga class, amma banda Ramlah da Nihal sai sha'anin gabansu sukeyi, tsab ta kalle class d'in da mutanen ciki ganin kowa na welcome nata amma banda su yasa hankali ya koma garesu, gaban seat d'insu taje tare k'are musu kallo tayi tare da sakin malalacin murmushi.

"Hi" ta fad'a Nihal tago tare da cewa "hello" Ramlah kam kallon d'aya tayi mata ta maida kanta gun text book d'inta, smiling ta k'arayi tare da mik'awa Nihal hannu.

"I'm Sadeeya M Bashir, buh u can call me Sadee M bash"

Itama hannu ta bata "I'm Aisha Yusuf Besse, Nihal by family name"

"Wow nice 2 meet u" sannan ta juya gurin Ramlah ta mik'a mata hannu tare da gayamata sunanta kamar yadda ta gayama Nihal tana murmushi.

Itama murmushi tayi mata "Ramlah Abdulrahim modibbo by name".

"wow i like ur style, may I have a seat here?"

Kallon Nihal Ramlah tayi sannan tace "why not" ta fad'a tare da nuna mata seat...

Tun daga ranar suka zama k'awaye irin sosai d'innan akayi sa'a kuma itama House d'insu aka ajeta room d'insu d'aya, nan suka koma su uku komai tare sukeyi.

Sadee irin marasa jin nannan irin bata yadda d'innan ba, classy girl ce ta sosai ga rawar kai kaman me, saidai fa itama akwai kai shiyasa zamansu yayi kyau, a class kuwa ji yake dasu suke d'aukar 1,2,3 position, zamansu da sadee sun k'ara wayewa idonsu ya bud'e sosai musamman Ramlah.

Sun koyi saka k'ananun kaya a gurin ta, haka tazo dasu trolley guda haka ta shiga basu tana koya masu yadda zasu saka, nan fa suka shiga nuna Kala ko'ina suka wuce 3stars kakeji, har Senior burgewa sukeyi.

Har Mami tasan Sadee haka iyayenta har sun kulla zumunci suma, su Abdool ma daga India suna shan labarinta.

Yanzu su Ramlah anyi mastering gurin swag haka idan suka dawo Hutu a gida ma sun daina saka atampha ko less English wears kawai, mini skirt, top, tight, pencil, body hug, bomber short iri-irensu dai.

Haka idan zasu koma Hutu zasu shiga boutique su sissiya tare da M bash suke zuwa dake itama anan Kd take, Mami dai ta zuba musu ido ganin iya gidane kawai basa fita dasu.

B'angaren su Abdool kuwa tunda suka tafi basu zo ba, dan ba damar d'agawa nan da can amma har cikin ransa yana missing gida yana missing Ramlah sosai, abun haushin ma an k'ara musu rabin shekara abun ya bata masa rai saidai ba yadda ya iya dole ya jure.

Su Ramlah an zama sun zama cikakun 'yan mata sosai musamman ita dama gata kamar kajin Agric, komai na cikar mace ya cika gareta, 8 shape d'in nan ya fito sosai, dukiyarsu ta Fulani ma sun cika barakallah, duk namiji lafiyayye ya kalleta sai yaji wani Abu a ransa........




_to friends ya kamata fa mu waiwayi Iya Hari, muji wace wainar suke toyawa 😜🤣_







💄Meryerm Abdool💄
[9/10, 4:14 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)







```Allah mad'aukakin sarki tsarkakakke ne kuma baya karb'a sai Abu tsarkakakke👌🏻```

Muyi k'ok'ari mu tsarkake tsakaninmu dashi.👌🏻



*Namecy ur a d most grateful ever meet ur d best namecy, ur ur ur hmmm am speechless dear, may Allah bless be wit u always namecy _Maryam Y Zango_ here is ur page.💋💋💋*







  📝 *Episode* 181--185




Iya Hari tun ranar da aka d'aura ma Ramlah Aure aka kuma ga 'yan uwanta tasan lallai Ramlah tayi mata nisa, kuma tayi mata fintinkau saidai tsinka, musamman ganin irin dukiyarda ke garesu, amma saboda bak'ar zuciya irin tata da sharrin shed'an(Allah yayi mana tsari da kaidinsa) suka had'u suka yi mata b'akar hud'uba na yadda zatayi ta maida Ramlah baya taya zata maida ita k'auye taci gaba da musguna mata.

Duk masifa da bala'in Hari da d'ibar albarka irin tata bata zuwa gurin boka ko malamin tsibbu saidai tayi addabeka ka gwammace inama baka Santa ba a rayuwa, amma a yanzu ta fara tunanin zuwa inda boka domin ya lalata auren Ramlah sannan ya saka mata bak'in jini a idon dangin mahaifiyar tata su korota inda take daga nan taci gaba da musguna mata bayan tasa an rufe bakin Ard'o, wannan kullum shine tunanin amma ina zata samu kudin zuwa shine matsalar dan kudi sam baya zama ga Hari saboda shegen kwalama da kwad'ayin tsiya, ga Ard'o yanzu zama k'ankamo injita, dama can halinsa ne (Inji fa).

Tunda aka wuce da Ramlah Ard'o bai k'ara maganarta a gidan ba, ko tanaso ta tambaya ba dama duk zuwanda yake Kaduna da zuwan da Abdool keyi gurinsa bai taba gayamata, saidai taga kayan tsaraba kawai ko tambaya tayi ina, cewa kawai yake ba damuwarta bace.

Ganin zaman kad'aici ya isheta ita kad'ai a gida yasa ta d'auko Hinde d'iyar Lanti dan tayata zama da taimaka mata, amma kuma sai hakan bata samu dan Hinde gantalliyar yarinya ce, b'atacciya kuma 'yar iska irin ta k'auye nan.lol

Inta kwanta bacci sai hantsi ya dubi ludayi take tashi, ko tsince bata kawar mata hasalima ko Inda ta kwanta bata gyarawa da kuma ta samu abin kari ta fita bata gidan biki bata na suna bata dakin saurayi bata matattarar 'yan iska ba ita zata dawo ba sai bayan isha, shima tana zuwa taci abinta sai dandali daga ta dawo sai bacci, aikin sisi bata mata kuma datayi mata kallon banza ko fad'a rashin kunya take mata inta zageta ta rama, inta doketa kota hanata abinci taje ta gayama uwarta, haka Lanti ke kwaso jiki wai akan me zata dokar mata 'ya kota hanata abinci ko tana nufin yadda tayi Laure ne zatayi ma 'yarta, wallah bata yadda ba dan ba jaka ta haifar mata ba, haka zata tasata gaba da masifa akan 'yarta kuma ba halin kwab'arta dan tarbiyarta ai(kaikayi koma kan mashekiya) wani sa'in Ard'o na jinsu bai cewa k'ala, saidai yayi murmushi kawai yasan farawane ma indai alhaki ne.

Haka Hinde ta zamewa Hari wani bala'i kadangaren bakin tulu a kar ka akai tulu a barka ka bata ruwa, gefe d'aya kuma Jauro ruwa a jallo yake Neman Hari, dan Ard'o ya masa kashedi da gidansa shiyasa bai sameta a can ba, amma yasa alwashin idonsa idonta ba'a mai kyau.

( _Sorry Iya Hari, farawa ne ma_ )..😏😂



******************





Komai aka masa rana tau za'a cimmata a yaune Dr Abdulmajid tare da Zainab suka diro Nigeria cike da nasarori ciki hadda tsulelen cikinsu d'an 8months, sunyi fresh abinsu musamman Dr Majeed idan ka kallesa saika k'ara kaman wani saurayi d'an 20 ya hade cikin suit ash, yasha cover ga glass as usual ya zauna daram, sumar sai sheki take, man pride nasa yasha gyara, Zainab kuwa cikin Arabian gown ja tayi rolling da gyalenta ga cikinta daya fito tutsu dashi, tad'anyi jiki irin na cikin nan.

Sale driver ne yazo d'aukar su, direct gidan Mami suka wuce wacce ta shirya musu better tana jiran isowarsu, tayi murna da ganin su musamman ganin Zainab da ciki cikin ranta fad'a tace "Ashe gwanda da akayi auren nan gashi har rabo ya samu zanga jikana" sai nan da nan take da Zainab ina zan saka ina zan d'auke, itakam sai sunne kai take alaman kunya, Abdool kam sai murmushi yake gaskiya no place like home.

Yanzu babban burinsa ganin Ramlah yasan ta k'ara girma yanzu, anyi sa'a kuwa end of week ne visiting, surprise yakeso ya musu....

Ranar visiting su Ramlah ne zaune kan bench su 3 sai fira suke sama-sama, lokaci zuwa lokaci zata kalli gate, duk da tarasa dalilin hakan, sai smiling take tana felling special.

Can ta hango su Husna d'auke da basket, zame jiki tayi sallat ba tare dasu Nihal sun sani ba sunyi nisa da hiran Uncle lukman wani Cooper da aka kawo musu dake bala'in son Ramlah, itakam Sam bata bashi fuska ba, dan tasan ba kyau ko a musulunci and then yanzu tasan ma'anar so kuma mutum d'aya takewa so shi kad'ai yayanta mijinta, shine fa Sadee ta d'age wai tasoshi ya had'u...

"Husna, Abj ina Mamin ne" ta fad'a tana isowa gunsu, ita Sam bata kula dasu Dr Majeed ba, inama zatayi tunanin ganinsu tunda tasan basa k'asar kuma ko jia sunyi waya.

Rungume hannayensa a k'irji yayi, tabbas girman d'an mutum ba wahala, ta canja gaba d'aya, badan yayi mata Sanin kwarai ba ai kila bazai ganeta ba.

"Aa ya ina magana kunmin shiru kodai Ku kad'ai ne?" Smiling Husna tayi tare da nuna mata inda su Abdool suke.

Idonta ne ya sauka kan na Abdool dake mata murmushi, cikin ihu ta daka tsalle "Lah Yaya what bunch of surprise" ta fad'a tare da fad'awa jikinsa, wani shock ne ya ziyarcesa tun daga yatsar kafa zuwa brain d'in sa.

Wani bak'on lamari wanda bai saba ji game da Ramlah shine ya ziyarcesa a yau, duk kuwa ba yau ne lokaci na farko da ta saba rungumesa ba, cikin wayau ya zameta daga jikinsa, Zainab na ankare da halin da ya shiga saurin d'auke kanta tayi zuciyarta sai harbawa take, ba abinda take ambato sai "innalillahi wa'inna ilairajiun" sannan ta samu nutsuwa, murmushi ta k'irk'iro "wato Aunty Ramlah Dr kawai kika gani".

" laa Aunty Zee ba haka bane ai kune kunyi min bazata Allah " ta fad'a tana isa gunta, rungume juna sukayi suna dariya.

"Um um" Abdool yace, inda yake suka kalla, tuni Zainab ta gane yaren wato ayi masa a hankali da baby, hararan wasa ta jefa masa, Ramlah tace "wani abun ne yaya?"

"Um ba komai Ramlatun Yaya, ina su Nihal ne?" Ka gansu can, basu ma San nazo ba" nuna musu gun bench d'in tayi, can suka nufa a tare sai tambayan su take game da India (kunsan dai Ramlatun baffa da tambaya).

"Kinaji ko besty ni banga illar uncle Luku ba kawai ki amince masa" Sadee ta fad'a saidai me ba Ramlah da takema magana a gun.

Baza ido sukai suna nemanta can ta hangota tafe tare da wasu da bata sani ba sai su Husna "la haula Yaya Abdool ne da Aunty Zee yaushe suka dawo bamu sani ba" Nihal ta mik'e tana fad'a.

"Nihal wai wannan shine ya Abdool d'in?"
"Eh wlh shine kinga matarsa Aunty Zainab"

"Kai Amma wlh ya had'u ba k'arya gashi Dr, wow gaskiya I love him"

Zaro ido Nihal tayi "me? Rufamin asiri kafa matarsa can" to meye ba sai naje ata biyu ba" 

"To ai.." Shiru tayi.

"To ai me?"

"Uhmm share kawai Sadee" zata yi wata magana suka k'ara so hakan ya tilasta yin shiru.

Anan suka shimfid'a darduma, lunch sukayi as usual bayan an gaisa sun gabatar musu da Sadee, firan Yaushe rabo suka shigayi da Aunty Zainab ta yaushe rabo, jefi-jefi Abdool ke saka bakinsa, duk hankalinsa ya tattara ya tafi ga Ramlah sai kallon ta yake in style, mamakin girmata kawai yake, Zainab na ankare dashi, dama tasan za'a rina tun tana kwaila ya kalla balle kuma yanzu data cika fam, Sadee ma ta kula da kallon ta dai share ne kawai.....


**************

Sokoto sukaje suka kai musu tsarabansu, har gidan Alhaji Sada sunje, momyn zee tayi murnar ganin hankali kwance harda albarkar aure.

Sunje Kilgore inda Ard'o shima yayi murnar ganin su, daga nan suka wuce Argungu, nan fa Mama ta shiga tsokanar Zainab wai daga zuwa India sai dawowa da babbar tsaraba ita dai sai sunne kai take kunya, Abdool ne mai shige mata.

*2 weeks later...*

Wayarsa ce tayi k'ara my Zee ya bayyana a screen, da sauri ya d'aga "yadai Zee ko jikin ne?"

Cikin walahalalliyar murya ta ansa "Dr kazo gida banda lafia".

" u see saida da na gaya miki bazan fita ba labour kika saboda naga syn nata kikace lafia qlau kike, koma dai ba shine ganinan in d next 2mnt" saida ya gayama wani Dr abokinsa sannan ya d'aukota dan shi duk b'angarensa ne, bazai iya k'arbar haihuwarta ba, balle yanda yaga tayi wujiga-wujiga da ita, Mami ya kira tuni ta dira a asibitin.

Suna nan Zaune tun abin safe har har rana ana Abu d'aya, sai fitowa nurse keyi suna cewa ta kusa dai, yanaso yaje saidai zuciyarsa ta gama tsinkewa, ya tausaya mata sosai irin doguwar nak'udar nan ce, ganin tasha wahala tayi har k'arfinta ya k'are, yasa suka yanke hukuncin yi mata C/S.

"Dr ka yafemin bana tunanin tashi daga gadon nan, don Allah ka yafemin duka laifuka na" ta fad'a da muryan rad'a Wanda shi kad'ai yaji dan yakai kunnensa dai dai bakinta, cikin wahala take maganar, kama hannun Mami tayi amma ta kasa magana sai bakinta dake motsi.

Mami sarkin tausayi har da hawaye ganin yadda surukar tata ta koma "Aa Zainab bakiyimin komai ba, Allah ya fito dake lafia, Allah ya saukeki lafia" daganan aka shiga da ita 
Operation room.

One hour...

Jariri ne kato kaman ka lashe don kyau aka fito dashi, an shirya shi tsaf cikin Round up Red, cikin murmushi Mami ta amshi babyn tare da cewa "Mashaa Allah, barakallah".

Dr kam tambayan uwan kawai yake kota kan babyn baibi ba, kasha nurse tayi dakai " sorry sir...." What "ya katseta tare da tafiya luu k'asa a some.


_😭🙆🏾 Zee bazan iya ci gaba ba_



💄Meryerm Abdool💄
[9/12, 4:05 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



```Manzon Allah S.A.W yace da d'an Abbas:-```

_"yakai yaro ka kiyaye Allah zai kiyayeka, ka kiyaye Allah zaka samesa a gabanka, idan zakayi roko toka roki Allah, idan zaka nemi taimako toka nema gurin Allah, ka sani da ace al'umma zasu taru gaba d'aya akan su amfaneka da wani abu, to bazasu iya amfanarka da komai ba face abinda Allah ya kaddaro maka, kuma da ace zasu taru akan su cutar kai da wani Abu, to ba zasu iya cutar da kai da komai ba face abinda Allah ya kaddara maka, takardu sun bushe, an d'auke alk'alami,_tirmizih

A wata ruwa daba ta tirmizih ba cewa yayi _ka kiyaye Allah zaka samesa a gabanka, ka tuna da Allah yayin farinciki sai tunaka yayin ki'unci, ka sani duk abinda ya sameka ba'ayi shi dan ya kubuce maka ba, haka duk abinda ya kubuce maka dama ba'a yishi dan sameka ba, ka sani dukkan nasara tana tare da hak'uri, haka bakinciki yana tare da farinciki, kuma dukkan tsanani yana tare sauk'i_ ( Arba'una Hadith).👌🏻


*😘 k'anwata Jannart lamed'o ki sani kina raina kullum, bazan mantaki ba koda kuwa ke kin mantani ne😁 #ana mugun tare iya wuya# 🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀*






    📝 *Episode* 186--190




"What nonsense u done here Nusaiba?" Dr Ma'aruf ya fad'a cikin tsawa yana fitowa daga theatre room d'in.

"Sorry sir" ta fad'a cikin tsoro, "get out in my sign, ki jira query dan bakisan aikinki ba" sum2 ta fice cike da fargabar abinda zai faru, umarni yabayar na d'aukar Dr Majeed sannan yaje gun Mami dake tsaye kamar an dasa jikinta sai rawa yake kamar mazari, Allah ya tsare yaron bai fad'i ba.

"Mama don Allah ki kwantar da hankalinki kada abun yayi yawa, dukkan rai bata wuce lokacin ta, don Allah ki zauna, barin duba Dr" babyn ya ansa tare wucewa d'akin da aka shiga da Abdool.

Taimakon gaggawa ya shiga bashi cikin 'yan mintuna ya fardad'o da sunan Allah a bakinsa, sannan a hankali ya fara bud'e idonsa ganin d'akin da yake ciki ya tabbatar masa ba makarki yake ba komai ya faru da gaske kenan, sauke idonsa akan Mami dake gefensa yayi, sai Dr Ma'aruf dake tsaye Kansa, bakinsa ne yayi masa nauyi yana son magana amma ya kasa sai bakinsa dake motsi, hannunsa Mami ta kama "ka daure Son" shine kawai ta Iya fad'a, saboda yanda zuciyarta ta tsinke, tasha ganin mutuwa kuma tasan zafin mutuwa saidai wannan akwai tausayi a ciki musamman ma jaririn da d'anta su tafi tausayawa.

"Mami na daure fa kikace kina nufin, da gaske Zainab ta tafi ta barni da tabar  jaririnta?"

Dr Ma'aruf ne ya dafashi tare da bubbuga masa kafad'a "Abokina kada ka mantafa kaine mai bawa wasu hak'uri da nuna musu yadda da k'addara idan sukayi rashi, kayi hak'uri Addu'arku kawai tafi buk'ata yanzu"

"Hakane Dr Ma'aruf, na yadda da k'addara kuma na yadda kowace rai bata wuce lokacinta, Zainab inshaa Allah ke 'yar  Aljannace, ke matar kirki ce, ke mai addine, ina miki kyakkyawan zato, Allah yasa mutuwa ta zamo hutu a gareki Allah ya arbarkaci abinda kika bari" sai hawaye kebin fuskarsa kaman fanfo, haka Mami, Dr Ma'aruf ma saida ya zubar da nasa hawayen gwanin tausayi.

"Dr ina abinda aka Ciro" yace ganin ba baby a d'akin, "yana hannun nurses bari na karb'oshi" dawowa yayi tare da babyn, ansarsa Abdool yayi tare da kafesa da ido, tuni k'auna da tausayin yaron suka rufesa, sai bacci yake abinsa, baisai mai ake ciki ba, maganar Zainab ya tuna.

_Dr pls idan namiji na Haifa ka maida mishi sunanka, idan kuma mace ce, ka saka mata sunan Aunty Ramlah_

Wasu hawaye ne suka zubo masa yasan yayi rashin mai k'aunarsa da gaskiya mai son duk abinda yakeso, hud'uba yayima yaron da _Abdulmajid_ sannan ya mik'a shi ga Mami, "Dr Kaine gurin Gawar Zainab" yace tare da sakkowa.

Addu'a sosai yayi mata, yana hawaye ganin ta a kwance kamar me bacci amma kuma ba barcin duniya bane.

_Duniya! Bakida tabbas_ 😭 


Wani envelope Dr Ma'aruf ya bashi yace Inji marigayiyar ta bayar a bashi, ansa yayi sannan suka d'auki gawar zuwa gida dama tuni Mami ta kikkira kuma duk sun taso don samun jana'izar.



***************

Wasik'u ne guda 3 cikin envelope d'in, ta sama a rubuta zuwa ga mijina, bud'ewa yayi ya fara karanta wa.

_"Amincin Allah ya tabbata a gareka mijina, nasan koda wasik'ata zata sameka, watak'il bana numfashi a duniya, kayi hak'uri da rashina inada tabbacin Aunty Ramlah zata maye maka fiye da gurbina, addu'arka nafi buk'ata a yanzu mijina, naso ace na  rayu a dai2 wannan lokaci da nake buk'atarku saidai Allah yafimu sanin gaibu, naso na rayu koda na minti gudane da abinda na Haifa naso naji duminsa shima yaji nawa, ina rokonka daka zame masa uwa da uba dan Allah karka barshi ya koka da rashina kaida Aunty Ramlah, ina muku fatar Alkhairi, sannan ka sani ina k'aunarka har numfashina na k'arshe, ka bawa aunty Ramlah wasik'arta a ranar da ta tare gidanka, d'ayar ka bawa iyayena, pls kazo ga gawata ka wankeni kamin sutura sannan ka sadani da gidana na gaskiya, nagode da k'aunar da ka nunamin a iya zaman mu mijina_

Zainab Salis.

Sanda ya gama karantawa hawaye kwance a idonsa, yana tuna rayuwarsu da Zainab tun daga ranar da ya fara saninta har yau data barshi, bari na har abada, murmushi yayi irin na k'unci "ina miki fatar Alkhairi Zee ta".

Kamar yadda ta buk'ata shi yayi mata wanka da sutura, cikin ikon Allah natsuwa ta saukar masa, sai addu'a yake mata har ya kammala.

Tuni gidan Mami ya cika da mutane masoya da mak'ota sai zuwa suke ta ko'ina haka abokan Abdool su Hakeem duk sun zanzo duka ma'aikatan asibitin sunzo maza da mata dan itama Zainab can take aiki.

Flight mutan sokoto da Kebbi suka biyo ciki kuwa hadda Ard'o, bayan sallar La'asar aka sallaceta aka sadata da kushewarta.

Iyayen Zainab duk da sunji mutuwar 'yar tasu saidai sunyi farinciki yadda ake yaba kyawawan halayyarta musamman mijinta, sun San ta dace dan duk maccen da mijinta ya koka da rashinta ya kuma yaba halayyarta bayan bata ana mata kyakkyawan zato.

Bayan anyi addu'a uku da zasu wuce sun so wucewa da babyn saidai Mami tace a barshi anan zata kula dashi da tsakani da Allah, basu Musa ba saboda sun san zata iya kamar yadda ta kula da uwarsa, dan sunajin labarin kirkinta a gun 'yarsu.

Ranar suna ba wani taro da akayi yanka kawai akayi masa tare rad'in suna kamar yadda sunna ta tanadar a masallaci akayi, Inda su Husna sukayi masa inkiya da junior, dukkan kulawa junior na samunta ga ingantattun madara wad'anda zasu taimaka masa da  Abdool ya siyo masa saidai ko yayane basuyi ya maman uwa ba, kullum Abdool ya kallesa tausayinsa ne ke rufewa dan yasan yayi rashi.

Tarraro duk wani mahimmin abu da yake buk'ata yayi na gidansa ya dawo gidan Mami tsohon d'akin sa dan bazai iya ci gaba da zama gidanda yayi rayuwa da Zainab ba, bayan bata a doron k'asa.


*****************

B'angaren su Ramlah kuwa wasa-wasa Uncle Lukman ya sakota gaba ya takura mata, ta rasa ya zatayi dashi tana tsoron ta gayamasa matar Aure ce a samu matsala yakai report a koreta, daga k'arshe dai ta yanke shawarar in Abdool yazo visiting zata gayamasa kawai.

Sadee kuwa ta saka Nihal gaba ita Ya Abdool yakeso ta yadda taje ata biyu, Nihal dai cewa tayi tabar maganar kuma kada ta bari Ramlah taji data tambayeta dalili tace tadaiyi shiru kawai.

Hakan yasa ta shiga tunanin dalilin Nihal na fad'ar tayi shiru tunawa tayi da kallon da taga yana yiwa Ramlah ranar da sukazo musu da "oh no wonder soyayya suke kenan shiyasa komai zatayi tace ya Abdool kuma aiba biological sister nashi bace, idan ko hakane dole na lahe dan bazan iya breaking heart d'in Besty ba" da wannan tunanin tabar zancen kuma ta daina mata zancen uncle Luku.

Haka ranar visiting tazo su Ramlah basuga kowa daga gida for d first time da suka rasa visiting duk da basuda matsalar komai, saidai hankalinsu ya tashi sunaji ba lafia ba, Sadee CE ta ringa kwantar musu da hankali, akan kila wani uzirin ne ko kuma kila Aunty Zainab ce ta haihu.

Sharewa kawai sukayi amma idan haihuwace aiya kamata a gaya musu, koma dai meye zasuji idan sun koma tunda an kusa Hutu..

Ranar da suka koma gida sukaji mummunan labarin Rasuwar.........





_still in sick ur pray is needed my Fans_
🤢😔 











💄Meryerm Abdool💄
[9/23, 8:51 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



Ga shafukan mu nan da zaku ringa samun k'ayatattun novel namu👇🏻

*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*





```An karbo daga shugaban mummunai, uban hafsy umar bin khattab (A.R) yace:- naji manzon Allah (S.A.W) yana cewa```

_"dukkannin aiki baya yiyuwa saida niyya, kuma kad'ai abinda mutum ya kudurce a ransa yake samu, Wanda yayi hijira domin Allah da manzonsa to hijirarsa tana ga Allah da manzonsa, wanda kuma yayi hijira domin duniya da k'alek'alenta ko kuma wata matar da yakeso ya aura, to hijirarsa tana ga abinda yayi dominsa._ ingantaccen hadith ne daga sahihan nan Bukhari da musleem.
(Arba'una hadith).










      📝 *Episode* 191-195



Ranar da suka sukayi Hutu suka koma gida sukaji mummunan labarin Rasuwar Aunty Zee ba k'aramin girgiza sukayi ba, sunyi kukan rashinta dan Aunty Zee ta zama wani b'angare nasu, sunji mutuwar matuk'a dan kusan itace mutuwa mafi kusanci wacce suka ji da girmansu, tunda koda akayi wad'ancen basu da wayau.

Tunda Ramlah ta d'ora idonta kan junior taji k'aunarsa Mara adadi na ratsa jini da jijiyarta, rungumesa tayi tana zubarda hawaye tare da k'udurcewa a ranta zata zamo uwa a gareshi, zata soshi ta kula dashi iya yanda zatayiwa 'ya'yan da ta haifa, saidai kuma tasha jinin jikinta da haihuwa, tace junior ya isheta ba zata yadda tayi ciki ba( haba ramlatun baffa ai kowa baya wuce lokacin da turbar tafiyarsa)

Dawowar su Ramlah ya samarwa Dr Majeed nutsuwa sosai dan ganin da yake mata kad'ai yana rage masa tension, kullum tana mak'ale da junior itace cinsa shansa, har wanka take cewa ita zata masa Mami tace ta bari harya k'ara kwari, amma ita ke shiryasa tsab, har bacci tare sukeyi, Inna ta data tsaya dan taya Mami kula dashi ganin Ramlah tayi kane-kane komai ita ke masa dak'ar take bari wani ya d'auke sa tace itakam zata koma gurin tsohon mijinta tunda iyayen d'a sun iso sai a basu guri, itakam ko a jikinta sai ma ala kiyaye data rakata dashi.

Yanda take nuna K'aunarta akan junior, ba k'aramin dad'i hakan kema Abdool da Mami, musamman Abdool da yake da tabbacin Ramlah zata taimaka masa su cika burin Zainab.

Saidai sabon salon da Ramlah tazo dashi yake Neman da masa lissafi, ya lura basu da kayan sakawa yanzu daya wuce English wears ita da Nihal Wanda hakan ba k'aramin tayar masa da hankali yake ba a matsayin na lafiyayyen namiji kuma babuk'aci, iya saninsa k'aunarta a cikin jininsa take tun kan ta mallaki hankalinta, tun kan ta zama cikakkiyar mace, amma kuma yanzu wani abu yakeji a jikinsa muddin ya ganta a irin wannan shigar.

Yauma kamar kullum a parlour ya sameta tana k'ok'arin sakawa junior safa ta shiryasa cikin jean blue da red shirt sai red sock da take saka masa, sai k'amshi suke zubawa itada shi, da sallama ya shigo gidan ba kowa ita kad'ai ce a parlon, ansawa tayi tare da cewa "sannu da zuwa ya aiki?" Lafia qlau Ramlah saiku kad'ai a parlour " ya fad'a yana ansan junior.

"Eh wlh duk suna ciki, bari na kawo maka abinci" mik'ewa tayi tabi hanyar kitchen, da kallo ya bita tana sanye da wasu riga da siket na English wears, siket din iya guiwa sannan an tattare dai hip nata sun zauna daram a ciki ya kuma kamata, itama rigar an tartare gaban rigar gurin dukiyar Fulani itama ta kamata sosai sai Kanta data Parke da k'aton ribbon tsakiya sai sheki yake yasha gyara.

Haka ya bita da ido har saida ta shige kitchen din sannan ya sauke ajiyar zuciya tare da K'ara rungume junior, part d'insa ya nufa yana fad'in "wai me yarinyar nan ke nufi ne? Dole na dakatar da wannan shigar kada a samu matsala fa" daga haka ya shige d'akin sa, kwantar da Junior yayi Wanda tuni yayi bacci sannan ya rage kayan jikinsa ya fad'a toilet.

Da k'aramin tray ta fito a hannunta, ganin bashi a parlour yasa ta wuce direct d'akin, ganin bashi a d'akin yasa tasan ya shiga toilet ne, ajiyewa tayi kan stool sannan ta d'auki junior tayi ta fice.

Hakan ce dai tayi ta kasancewa Abdool nason mata magana akan shigar yana tsoron kada ta masa wani fahimta, dan har yanzu da sauran ta.

Sadee har gida yazo tayi musu gaisuwa, nan ta wuni suka sha firarsu cikin firan nasu ne Sadee ke cewa "Besty nikam nace wannan Yaya Abdool d'in anya??"

Yi tayi kamar bata fahimci inda ta dosa ba "me kenan Besty?"

"Oh besty Sadee ce fa, nafa sanki sarai kinsan me nake nufi".

Shu'umar dariya tayi " Ai Ina sane dake d'in ce, amma kinsan me?

"Aa saikin fad'a"

"Bafa soyayya muke ba, kawai dai shakuwa ce"

"He he he! Idan ko hakane nikam kimin hanya" ta fad'a cike da tsokana.

Wayance tayi duk da dukan da kirjinta yayi Tare da cewa "no wahala bakida matsala"

Dariya Nihal dage jera kaya a wardrobe ta fashe da ita, harara Ramlah ta jefa mata "keko me akayi na dariya"

"Me ko" ta fad'a tanaci gaba da dariyar ta, Sadee ma darawa tayi tace "um su Besty manya Ashe zakiyi sacrifice wani".

"Me?" Tace tana zuba mata ido.

"Hmmm Allah Besty kin ban mamaki banyi tsammanin banda matsayi a gun ba sai yau na tabbatar, amma ba komai Allah ya sawwaka" mik'ewa tayi da niyyan tafia, riko mata hannu Ramlah tayi.

"Pls yi hak'uri Besty wlh ba haka bane, abin somehow kuma kinga yanzu muna school ne so ba maganan soyayya, amma dai tun da kin gane ya wuce kiyi hak'uri".

"Uh um Besty banni na tafi kawai nasan bana kayanki shiyasa" dak'ar ta samu ta shawo Kanta ta hak'ura sannan sukaci gaba da firarsu, Nihal ma ta k'are aikinta ta jona su.

Haka dai suka gudanar da hutunsu, da yake mai dan tsayi ne Wanda da sun koma zasu shiga SS3.

Abdool ne zaune kan sofa suna hira da Mami a d'akin ta "Niko Mami kinga sabon salon da yaran nan suka tsiro dashi na maida kayan sawansu English wears kamar wasu 'ya'yan turawa?" murmushi Mami tayi.

"Aifa na gansu nima har mamaki suka bani ni bamma san yaushe suka siya ba".

"Hmm ya wuce idan sukaje provision suke siyan su"

"Hakane kuma, amma ai ba abin damuwa bane tunda iya gida suke sakawa sannan kuma idan anyi baki suna saka hijab ai naga ba damuwa ko"

"Eh hakane" yace ganin Mami ta kama musu, amma shikam a gaskiya ana shiga hakkinsa, da haka ya rufe firar ya janyo wata.


*******************


Koda hutunsu ya k'are Abdool ya kaisu yin provision haka yaga suna jibgar English wears dan Sadee tace su k'aro new design a k'ara darasi saboda tsaro, nuna yayi baima san sunayi ba hakan ya basu damar jibgar son ransu.

Daren ranar da zasu koma har d'aki ta isko Abdool, ya zaune kan bed cikin jean and t-shirt yana aiki a system d'in sa, goye take da junior, tana sanye da pencil brown da top milk hullace a kanta, ga k'ananun kalaban da tayi sun zubo baya, Cofee ta aje masa bayan ta gaidashi, zama tayi kan sofa, d'agowa yayi "Da wani abu ne Ramlah" ya fad'a yana k'are mata kallo, d'auke idonsa yayi gudun shiga damuwa yanzu ana zaune qlau.

"Eh Yaya um dama um" yes ina jinki feel free" nan ta zayyana masa yadda Uncle lukman ya dameta da yana sonta wai.

Kallonta yayi na sakwanni yace "kuna irin wannan shigar mezai hana malamai cewa suna sonku"

D'an zaro ido waje tayi "Allah yaya bamayi sai a hostel"

"Um to naji, jeki zanyi magana dashi gobe idan naje" dan yasan ci gaba da zamansu a haka za'a iya samun mishkila.


********************


Koda yakaisu sai yaga ashema yasan lukman d'in yana bayansu a ABU amma suna mutunci, bayan sun gaisa ne yake mai bayanin alakarsa da Ramlah "ya ilahi tuba nake Babban Dr namu, wlh ban sani ba shiyasa amma kayi hak'uri don Allah".

Murmushi yayi " kada ka damu lukman nasan baka sani bane ai, dan nasan ko ni bane ai ba haka aikata irin haka ga matar Aure ba" 

"Wlh kuwa na isa, itama tun farko aida ta gayamin"

"Hmm kasan yarinya ce a nata tunanin idan ta fad'a maka zaka gayama school authority a koreta, batasan tunda aka kawo su anyi bayani ba"

Smiling lukman yayi "hakane Dr kasanta ai akwai son kara2 kamar me, Allah dai ya sanya Alkhairi ina taya ka murna" yace tare da bashi hannu.

"Ameen nagode" yace sannan yayi mishi sallama.

Da Uncle Lukman ya had'u da ita yace "sai kuma kika boyemin ke matar Aure ce ko matar Dr?" Boye fuskarta tayi tana murmushi, shima murmushin yayi, "ba komai Allah ya sanya Alkhairi, saidai inason k'awarki Sadee tunda kekam kin zama matar Dr Majeed, sai kimin hanya.

Cikin jin kunya tace " inshaa Allah sir" sannan ta wuce abinta, koda tajema Sadee da zance a take ta amince, Ramlah kuwa har da zolayarta "Besty da wuri haka kamar ba Sadee classy girl ba" tana dariya.

"Hmmm Besty kenan ai Uncle lukman d'in ne da zafinsa fa" 

"To ai shikenan tunda kinyi giving up" 

"Aa fa banfa ce ki gayamasa ba, keko sai an jan masa eh...." Ta fad'a tana kashe mata ido, dariya Sukayi a tare har Nihal.

"To saura ke Nihal muji waye gwarzon" cewar Sadee.

"Wa! ni ai ba yanzu ba wannan saiku" ta fad'a tana zaro ido.

"Hehehe yarinya zatayi wari dai maji" cewar Ramlah.

"Ba wani wari da zatayi ai"

"Um midai namu ido" cewar Sadee nan dai akaci gaba da chapter.

Wasa-wasa Sadee ta shiga gara Uncle Lukman, har sai second term ta amince da soyayyarsa Sadee classy an bada kai.

Amma basa wani soyayya yadaije gidansu babanta yace a bari harta kammala school sai ayi maganar a natse a haka sukabar maganar.

Kwanci tashi asarar rai yau gasu Ramlah an kammala school success, Wanda hakan ba k'aramin dad'i sukaji kunsan dai SS3 irin dad'in da sukeji in suka kammala exam, a lokacin sun matsu suje jami'a, gida suka kira don azo musu prize and giving days da zasuyi.

Shiri sosai su Mami sukayi, gaba d'aya family har Ard'o yazo Inna, junior lokacin tafia yake ko 'ina ga gwarancinsa yanayi abinsa, wannan Karon har da Hakeem dan yake zashi taya K'annensa murna( Niko nace kodai da wata ne a k'asa).


Koda suka isa an fara gabatarwa kenan, quiz aka fara gabatar wa inda Ramlah ce team leader Inda suke tafka muhawara akan girls education is better than boys education, sai sambado bayani take cikin turancinta mai dad'in sauraro yanda take kawo hujjoyi da yadda take fitar da kalamanta abun ayi kallo ne tuni ta sake zuciyar mafi yawan samarin gurin, ta sanya zuciyar iyaye inama ace 'yarsu ce, yayin da sa'anninta kejin inama sune ita, team d'insu duk guraye ne ita, Nihal, sadee, da wata Umaima ta nan fa aka shiga tafka muhawara kowacce ta nuna iya bajintar ta tuni suka doke masu goyon bayan boys education, da zunzurun maki, nan fa aka shiga basu tafi raffff kakeji ta ko'ina tuni hawayen farinciki suka wanke mata fuska.

Itace yau a tayi kara2 har ta kammala secondary, gashi ta samu ilimin da bata taba tunani ba, ware ido take ba Wanda takeson gani sama Ya Abdool tasan kome ta zama shine sila, aiko can ta hangosu zaune sai tafi suke musu idonsu ne ya had'u murmushi ya sarkar mata tare dayi mata jinjina da hannu, share hawaye tayi tare da sakar masa tattausan murmushi, ta matsu a sallamesu taje garesu ganin hadda Baffanta anzo dashi.

Haka akaci gaba da gudanar da program d'in akayi drama da wak'ok'i na bankwana sannan aka gabatar musu da gift d'insu, kusan sune suka an she gift d'in musamman ma ita, ana sallarmu da gudu ta isa runfar da suke zaune, haka ta shiga rungumesu suna tayata murna, Nihal haka, ita Sadee Inda Familyn ta ta dosa, jikin baffa tayi masauki, sai hawaye sharrrr.

Murmushi yayi "haba Ramlatuna yaufa ranar farinciki ne a gareki ba ranar kika ba, ko ke manta yaune burinki ya cika ne Ramlatuna"

Murmushi take cikin hawayen "baffa kukan farinciki ne wallahi, baffa Mami da ya Abdool sunyi komai a rayuwa, baffa suna matuk'ar k'auna ta".

" na sani Ramlatuna karamci a cikin jinin zuri'ar Asma'u yake, Allah ya saka musu da Alkhairi, ya biya musu buk'atunsa na Alkhairi "

"Ameen baffana"

Junior ta ansa a hannun Husna dake ta jillewa yana mik'a mata hannu yana kiran "Maa" dan haka yake ce mata.

"Oyoyo mai Son yaudai mun samu freedom zan rayu dakai ba kara tafia kaji Son" ta fad'a kamar mai magana da wani babba, shikam sai dariya yake mata yana jin dad'in ganinta da yayi, dan ya Santa kamar me.

Hakeem kam an kame gefe sai kallon k'asa -k'asa yakewa Nihal Wanda ita kad'ai ta gane yaren.............






_Thanks so much my sweet dota(Ramlah Abdallah mazoji) for d care, ur momma really appreciate_ 😍😘 



*Nagode da addu'o'inku sisters am feeling better now thanks one again* 👌🏻👌🏻 





💄Meryerm Abdool💄
[9/23, 8:51 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



Ga shafukan mu nan da zaku ringa samun k'ayatattun novel namu👇🏻

*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*




```🎂🎂🍰🍧🍬🍾may Allah Blessing and protect be wit u here and after, may ur birthday b d key 2 ur success in each and every step u go, may Allah bless ur remaining year wit his Rahma and barakat Ameen ```😍👌🏻

*happy birthday day*

*Namecy*

Maryam y Zango.💝💐










  📝 *Episode* 196--200





Tun tana k'aramarta abokin yayan nata ke burgeta, bayan girmanta ne ta fahimci sonsa takeyi, amma a matsayin ta na 'yar bahaushe da kunya tace tana sonsa shiyasa tabar abin a ranta kowa bata fad'awa ba duk kuwa da surutu irin nata, Ubangiji kawai take gayama kukanta.

Shima Hakeem hakance a gurin sa ya dad'e yana k'aunar Nihal a ransa, duba da k'arancin shekarunta yasa ya b'oye a ransa kawai, a tunanin sa batasan meye soyayya ba, hakan yaci gaba da rainon sonta a ransa, koda Dr Majeed bai tab'a gayamasa ita yakeso ba, yace zai masa surprise.

Saidai tun can yana bata kulawa as a sister, saidai kulawar da yake bata daga baya is like more than a sister, har take tunanin kodai shima yanajin abinda take jine game dashi, Abdool baiyi noticing komai ba cos normally yasan Hakeem na kula da komai daya shafesa, kamar yadda shima yake kula da nasa, ita kam Ramlah tana shakkar wannan kulawar shiyasa da zancen saurayi ya tashi idan Nihal tace ita bata soyayya Ramlah ke cewa indai tayi wari saji, ita kanta Mami ta fara zargin wani abu a shakuwarsu inda take fatan hasashenta ya zama gaske, dan tasan Hakeem yaron kirki ne, iyayensa haka, zatayi farinciki idan ya zamo daga cikin zuriyarta.

Duk da bai furta kalmar so ga Nihal ba, amma yayi amfani da hikima ya koyar da ita k'aunarsa, baisan dama akwai k'aunar ba....

Kallon ta yake mai kice da ma'anoni Wanda ni kaina Meryerm bansan ma'anar ba, ita kuma sai sunne kai take tana murmushi.

Anan aka gabatar da jawabin bankwana, students sukayi bankwana da teachers nasu da juniors, nan aka rufe taro da addu'a, pics students suka shiga yi da k'awayensu da iyayensu, nan suka rabu kowa ta kama cike da kewar juna hadda koke-koke tare da ansan numbobin juna had'e da alk'awarin ziyartar juna.......

_School days kenan is d best days_




***************





A gida ma da aka dawo saida suka gabatar da kwarya-kwayar walima, Kyautar latest phones Abdool ya basu as his give, Samsung galaxy new version, had'e da sim tare da full credit na 5k, tare da Hakeem aka sayi phones d'in shine ya siya sims tare da credit yace tashi gudummuwar, hakan yayi ma Abdool dad'i sosai.

Tsabar dad'i  tsalle Ramlah da daka tare da rungume yayan nata ita Nihal haka, tagal-tagal yayi zai fad'i da sauri Ramlah ta janyoshi tare da manna shi a k'irjinta, janye ta yayi daga jikinsa saboda yanayin da yaji mai wuyar fassarawa "Ramlah k'asa zaku Kaini kam?" 

"Sorry sweet bro, duk murna ce fa"

Smiling yayi tare da wucewa yana fad'in "to ayi celebrate lafia, amma fa Ku kula sosai banda shiririta" Mami da Nany da Ard'o suka nunawa cikin farinciki, sunyi musu Ala sanya albarka Ard'o yace "to nima ga irin namu na k'auye".

Tsumi ne jarka d'aya, galon d'in zuma dana madara, da sauransu, shima rungumesa sukayi suna godiya, dama sun saba sha duk zuwan da zaiyi zaizo musu dashi, har Husna da Abduljabbar sha suke dan baida wata illa saima fa'ida, Mami kuwa tace su fad'i me sukeso ta basu as give, sukace is OK, ta barshi kawai but a duk da haka tace zatayi musu special gift.

Nan suka k'ure d'aki basu sha wahalar gane kan wayar ba tunda dama suna tab'a ta Mami da Abdool dama dai yace sai sun k'are school before su mallaki na Kansu, No d'insa data Mami ta baffa, data Hakeem ne a cikin sim d'in, Cikin zakuwa Nihal ta kira Hakeem don yi masa godiya.

Bayan sun gaisa " Yaya Nihal CE, munga abin Alkhairi mun gode sosai".

Smiling yayi "a murya na ganeki sweet sis, and meye na godiya 'yan matan Yaya Hakeem?"

Rufe ido tayi kamar tana gaban sa "uhm" kawai ta fad'a tare da saurin katse wayar, dariya ta bashi lumshe ido yayi tare da cewa "my shy girl".

" ke kuma keda waye hadda rufe ido" Ramlah ta fad'a idonta nakan phone d'inta da suke buga game ita da junior.

"Sa'idawa bansani ba" Nihal tace tana watsa mata harara.

"Hehehe A juri zuwa rafi dai...."

Harara ta watsa mata tare da shigewa toilet..


*************


Wasan rufe ido suke sai kuwwa suke kamar wasu yara duk sun hargitsa parlour, Ramlah ce aka daurewa ido wannan Karon, lalube take Wanda yayi dai2 da shigowar Abdool aiko kamar wacce aka tura ta fad'a a k'irjin sa, kamar da gayya ta k'ank'amesa tana fad'in "yarinya na kamaki" a tunanin ta Nihal ta kama, saukar masa kasala tayi gaba d'aya jikinsa, dama a gajiye ya dawo, ga azumi da yake faman yi yanzu kusan kullum, k'asa koda kwakwaran motsi yayi yana binta da kallo sanye da half gown peach anyi mata love shape da black, iya guiwa ta tsaya sai legging black data saka, ta kama Kanta da ribbon sannan ta saka bandana tayi masa kyau Kamar wata India, zameta daga jikinsa yayi karta karya masa azumi, jin shiru yasa ta janye d'aurin idon da niyyan yin masifa idonne ya sauka a nasa.

"Oyoyo Yaya, ina su Nihal d'in?" Tace tana raba idon ta gansu, tunda suka ga shigowarsa suka silale suka gudu dan ya hanasu kuwwace-kuwwace da mugun wasa.

Itama data ganshi ta razana amma da yake 'yar duniya ce saita maze, kallon ta kawai yayi ba tare da yace uffan ba ya wuce abinsa.

Ji tayi bata kyauta ba, hakan yasa ta bishi dan bashi hak'uri, kwance ta samesa rigingine yana kallon silin, bakin gadon taje tare da duk'awa "pls Yaya so sorry ba zamu k'ara ba" Sam baiji sallamarta da shigowarta ba dan yayi nisa a tunani muryanta ce ta dawo dashi.

Hannu yasa ba tare daya d'ago ba ya janyota zuwa jikinsa, gaba d'aya kan k'irjin sa ta zube kamar wata kayan wanki "meyasa kikeson azabtar dani Ramlah?" Taji ya jeho mata tambaya, sai raba ido take cikin tsoro jin yadda ya matseta a k'irjin sa dake harbawa da sauri-sauri, "Um..em..pls kayi hak'uri bazan k'ara ba" tace duk da batasan ainihin azabtarwar da take masa ba.

Ware ido yayi wad'anda sukayi jajir dasu, saida ta firgita da ganin yanayin sa, duk da idonsa ba farare amma wannan yafi karfin a kirasa kalarsu, duk ta tsure sai mutsu-mutsun kwace Kanta take, lumshe ido yayi tare dayin murmushi, ganin duk ta rikice a ransa yace "hmm sai tsoro amma ta iya jama mutum rigima, ashe ranar.... akwai rigima" sassauta rikon da yayi mata yayi aiko da sauri ta kwace kanta tare da sauka kan bed d'in sai sauke numfashi take tana raba ido.

Still idonsa a lumshe yace "meyasa kike irin wannan shigar?"

Shiru tayi masa, zaune ya mik'e tare dayin wani Smiling bayan ya ware idonsa a kanta, dariya ma ta basa ganin tayi tsuru kamar mara gaskiya "kinfison kiyita tayar min da hankali ko?"

Girgiza kai tayi alaman aa, "well jeki" yace aiko da gudu tabar d'akin kamar mai jiran kiris, dariya yayi "yauma na rasa azumin Kenan" yace tare dayin Mik'a rage kaya yayi sannan ya fad'a toilet dan yin fresh up.

"Ina Azabtar dashi.. To da meye?" Tace tana duba jikinta ita bataga laifin shigar ba, "yaya rigima yakeji, nidai gaskiya manyan kaya nauyin su nakeyi" ta fad'a tana tura baki gaba, kamar yana ganinta.

Jan k'afa tayi ta isa d'akin su Nihal ce kwance tana waya saidai baka iya jiyo abinda take fad'a saboda yanda tayi k'asa da voice nata, junior ne ke bacci gefenta, gadon ta haura tana fad'in "Juliet ta romeo ana baki aiki kenan, Yaya Hakeem yayi ya fito a shige ciki dake dan naga alamar a matse kuke" ta fad'a cike da zolaya.

"Bye sweet bro, sai na jika anjima" sannan ta juyo ta watsa mata harara "wai renin hankali, keda daga ina kike yanzu, ai kece zance Ku kara gaba Ku barmu musha iska".

Zaro ido tayi " Lalala  yayan kike gayawa haka aiko zan gayamasa"

"To saime ? Karya ne?"

"Uhm naga alaman yaya Hakeem ya zarar dake mudai ba ruwanmu kada ki lalatamu, bacci ma zanyi ni kyaleni" ta fad'a tana kwantawa gefen junior, tare da rufe ido.

"Kwaji dashi dai" Nihal tace tanaci gaba da danna wayarta...


"Kai nima fa na samu matar nan yauma zaka rakani zance".

" hhhhhh new system wannan wacece mai sa'a haka?"

"Ahaf yi cooling kawai anjima kad'an zaka ganta....."

"Uhm na lahe"

Bayan sun tashi ne yace suje yakaisa ya ganta, da motar Hakeem sukaje, ganin ya d'auki hanya gidan yasa mamaki ya kamashi, bai gama mamaki ba ya gansu bakin gidansu, horn yayi gate man ya bud'e musu suka shiga parking yayi tare da fitowa shima Abdool fitowa yayi yana mishi kallon tambaya, yi yayi kamar ba kula ba ya d'auko phone d'insa yasa kira "baby gani Harabar gida fa, OK" ya fad'a tare da hang up, Abdool kuwa ido kawai ya zuba masa yaga iya gudun ruwansa.

K'ofa ya kafe da ido don ganin waye zai fito duk da zuciyarsa na gayamasa is just a joke Hakeem ke masa, ganin yadda yake masa dariya.

Nihal ce ta fito sanye da gown ja da shadda sai walkiya take, tayi d'aurin gwaggwaro, sai bak'in gyale data sagala a kafad'a, fuskarta tasha make-up sai k'yalli take, tana fitowa idonta ya sauka ana yayanta aiko ba shiri ta juya a guje cike da kunya.

Da mamaki ya juya yana kallon abokin nasa "don't say anything all d answer are here" Hakeem yace yana dariya.

"Habi! Guy u take me 2 d world of surprise oo, yaushe akayi banda labari" yace yana jin dad'in lamarin har ransa.

"Aiko matar sonka ta sani, da ita akayi komai" 

Tuna masa da 'yar rigimarsa ya sakashi smiling "aiko bata gayamin nasan Nihal ta hana a fad'a, well congrat" yace yana bashi hannu, hannu ya mik'a masa shima nan sukayi musabawa daga ya goce tare dakai masa duka a kafad'a, tare dayin d'an gudu shima Ya bisa ya dan ramawa.

Cimmasa yayi tare da d'aga hannu zaikai masa duka "kai saika dokan yanzu nifa in low Kane".

" tab ban d'auka tanan ba balle abu ya dameni" rungume juna sukayi suna dariya.

_friends forever_


Abdool ne ya gayama Mami tayi farinciki da sosai tare da sanya albarka, tasan Hakeem tun kuruciya baida wani matsala, amma duk da haka saida ta gayama dangin babanta sukayi bincike game dashi.

"Um dama Mami zance yaushe Ramlah zata tare ne?" Abdool ya fad'a yana Sosa k'eyarsa.

Mami tambayan tazo mata a bazata "tariya Abdool? Aina d'auka sai exam d'insu ya fito sun samu admission tukun, kaima zuwa lokacin ka kammala komai na bud'e, hospital d'inka ko ya ka gani ne?"

"OK Mami ba komai a barshi a haka" amma har ransa yana buk'atar mace kusa dashi, har gaji dayin azumi wani sa'in saidai su karye a banza don kuwa Ramlah bata daina shigar k'ananun kaya ba saima abinda ya k'aru.

Itakam ko a jikinta kuma a haka take iskoshi har d'akin sa don neman rigima kuma daya tab'ata ta fara zare ido da kyarmar jiki...


**************


"Wlh naso naje amma kinga inaso na kammala buk d'in nan wlh akwai tausayi, kice ma Besty tayi hak'uri zanzo special zuwa, inshaa Allah" Ramlah tace da Nihal wacce ke cikin shirin fita.

"Yanzu saboda buk d'in nan zaki zauna ke kad'ai a gida, ko tsoro bakyaji?"

Smiling tayi "ai buk d'inne sisto so sweet, ai da kin fita zan rufe k'ofar parlour inaga ma garden zanje".

" muga wane iri ne?"

Buk d'in ta mik'a mata an rubuta *Darkness of sorrow* gaban bangon "um Besty ki ta riga ta b'ataki da novel, gashi har abin ya shafeta".

" nidai banason mita ki gaidamin ita sosai" tace tare da warce buk d'in ta.

Su Mami duk sun fita unguwa har junior ba yadda batayi dashi ya zauna ba yace zaije da Mami.

Zama tayi parlour tayi dai2 tana karatunta sai aka d'auke nepa "kash" tace tare da huro iska a bakinta.

Mik'ewa tayi don zuwa garden tasan zatafi jin dad'i a can.

Sanye take da mini skirt omo color na jean wanda ko cinyoyinta bai gama rufe mata ba, sai shirt pink mai hannun best wacce keda sakakken wuya duk rabin k'irjinta a fili, kanta ba d'an kwali sai kamawa da tayi da ribbon pink, tazo zata wuce taga d'akin Abdool bud'e, mamaki tayi dan batasan ya dawo ba, har zata wuce abinta tace bari dai ta duba ko yana ciki.

Abdool da tun safe yakejin sa wani iri wit 2much feeling ko azumi bai samu ya d'auka ba, ga Cikin sa sai ciwo yake koda ya fita bai Dad'e ba ya dawo, bai bari kowa yasan yana nan ba ya shige d'akin sa magani yasha ya kwanta, amma INA sai gaba abin keyi ji yake kamar sai mutu idan bai kusanci mace ba.

Iskar bakin sa ya furzar "wannan wane irin musiba ne, tsawon shekara 1⅛ ba mace a tare dani, wlh am tired, inada mata amma aikin banza, mtsss" yaza tsaki dan da alama hak'urin sa, yakai k'ololuwa k'are wa musamman dake shi mabuk'aci ne.

Turo k'ofa yaji anyi, sauri ya d'ago dan ganin waye, ganin yanayin shigar ta yasa yai saurin kauda kansa, ganin halin da yake ciki yasa ta ajiye book d'in da sauri, tana fad'in "menene Yaya? Meya same ka?"

Da hannu yake mata alaman kada ta matso Inda yake, duk da ta fahimci me yake nufi amma sai k'ok'arin isa Inda yake take yi.

Tana isa ta rungume sa tare da Shafa masa baya, aiko ta tono fitina da Kud'in ta, wani irin yarr yaji tun daga kansa har zuwa yatsarsa, hannayensa ya zageyita dasu ya kama k'ugunta.

K'ara matseta yayi a jikinsa tare da had'e bakin su, cikin kwarewa ya cafki lips nata kamar mayunwacin zaki........






Mura🤧🤥


💄Meryerm Abdool💄
[9/23, 8:51 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



Ga shafukan mu nan da zaku ringa samun k'ayatattun novel namu👇🏻

*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*



```Daga Anas d'an malik (R.D) yace manzon Allah (S.A.W) yace :-

Ina rantsuwa da Wanda rayuwa ta take a hannun sa, imanin d'ayan ku, baya cika saiya soma mak'ocinsa Abinda yake sowa kansa.

A wani gurin kuma yace "jibrillu ya kasance yana yimin wasiyya da Mak'oci har saida nayi tunanin zai gajeni idan na mutu"```

*ya 'yan uwa Ku duba girman hakkin mak'oci ga mak'ocinsa, wanda a yanzu mukayi yada gai2 da wannan zumunci muka d'aukesa ba a bakin komai ba, sai kayi wata bakaga mak'ocinka ba amma bazaka bincika lafia yake ba, ya 'yan uwa miyi k'ok'ari mu gyara ko Allah zai lullub'e mu da rahamarsa, Allah yasa mu dace ameen👏🏽👌🏻*







      📝 *Episode* 201--205




Zazzaro ido tayi cike da tsoro, jin sabon al'amarin da yayan nata yazo mata dashi, mai cike da wuyar fassarawa, " tome ke damun Yaya Abdool ne wai" ta fad'a a ranta, mutsu-mutsun k'wace kanta take, amma ko gezau baiyi ba saboda rik'one yayi mata bana wasa ba, fargaba da tsoro ne suka dirar mata lokaci d'aya, dan iyakarta dashi hugging shima daya matseta ta fara k'ok'arin kwacewa saketa yakeyi yace ta fice masa a d'aki, amma yau kam abin nasa ba wasa dan cikin sauri-sauri yake tafiyar da ita, kamar zakin da ya shekara baici ba, tuni ta fara data sanin shigowa d'akin da tayi.

Shikam gogan naku ya fara fita hayyacinsa kissing nata yake deeply cike da k'warewa, yayin da ya matseta a k'irjin sa da hannunsa d'aya, d'ayan kuma yana wasa da sassan jikinta dashi, zame 'yar shirt d'in yayi da hannun tare daci gaba da wasa da gab'ob'in jikinta, cikin mastering.

Lumshe ido tayi tare dayin lahu a k'irjin sa, zuciyarta sai harbawa take da sauri-sauri, tana karb'ar sak'onnin sa masu wuyar fassarawa, tunawa tayi da labaran da takeji a novel da kuma wad'anda takeji a bakin su Sadee na kwakwar da ake ci a first night, da alama yayan nata duniyar da yakeson kaita kenan, dan ya birkice mata ya riketa ta, ya koma kamar bashi ba, hawaye ta farayi dan tasan yau takai k'arshen zuwar masa d'aki.

Jin tsayuwa na neman gagararsu yasa ya sassauta rik'on da yayi mata da niyyan janta zuwa bed, ita kuma jin ya sassauta rik'on ne yasa ta ta bud'e ido, ta tsorata da ganin yanayinsa, tattaro duka k'arfinta tayi duk da yadda ya kashe mata jiki, ta turasa da k'arfi ya tafi luuu kan bed, ita kuma ta zura a guje zuwa k'ofa........



************



*A k'auyen Kilgori*


Abubuwa sai k'ara tab'arb'arewa suke, yanzu Hinde ta k'ara samun cigaba(amma namai ginnan rijiya) dan yanzu sai tayi kwana 2 bata dawo gida ba, tana yawon gantalinta d'akin samarin gari, idan ta dawo iya Hari ta tambayeta inda taje ansar ta aiketa balle taga ta dad'e haka in tace zata doketa, tace tana tab'a ta ramawa zatayi tunda ba jakarta bace, tasan kuma tsab zata raman dan Hinde ba kunya kota asi, ga ido tsaye na rashin kunya, ga ba damar ta fad'a Ard'o dan bashi ya aiketa dakko ta ba, gashi yanzu sam baya shiga sha'aninsu hasalima ya daina zama gidan bacci kawai ke maida shi, amma bai rageta da komai ba, amma duk da haka baisa Hari ta gane Allah ya faku ba, kullum cikin ranta bakin nufi ne takebin Ramlah dashi, musamman ganin tsawon lokacin da aka d'auka bata da labarin ta, don ko ta tambayi Ard'o game da ita cewa take, kome damuwarta da labarin ta sonta take ne, koso take taji tana cikin mawuyacin hali, to bai sani ba, ansar kenan, hakan yasa hankalinta k'ara tashi tasan Ramlah na cikin kyakkyawan rayuwa duk inda take.

Wanda hakan ta tsana a rayuwar ta taji Ramlah ta samu ci gaba, gurin boka taje nan yake gayamata Ramlah na cikin daular da bata tab'a gani ba a rayuwar ta, idan kuwa tanaso yayi mata aiki akanta saita kawo dubu dari uku, haka ta dawo gida cikin tunanin inda zata samu mak'udan kud'in, daga k'arshe shanunta ta sayar ta k'undume k'undin, a hanyarta ta zuwa inda boka taci Karo da Jauro, fitsari ne akwai bata saki a wandonta ba, amma ta firgita iya firgita, ganin yadda ya had'a rai kamar zaki sai huci yace ga adda a hannunsa.

"dama nasan idan kere na yawo zomo na yawo wata rana zasu had'u" ya fad'a yana wani juye baki irin na 'yan daban nan.

Jikinta ne ya kwari mazari cikin rawar baki tace "kayi hank'uri an Jauro ba laihi nana ba aradu kuwa malam na ya cuceka"

"Hahahaha ke! Tsohuwar banza kina tunanin irin Jauro aka cuta, to keyi kure kuma yau saikin kwashi kashin ki ga hannu" ya fad'a cikin tsawa tare da d'aga adda kamar zai Sara mata.

Zaro ido tayi Cikin tsoro hadda fitsarinta a wando " don Allah Jauro kayimin rai wallah, banda laihi, don Allah ka gahwarceni ka taho ga Hinde nan na baka"

"Kutumar kazar abun can! Ni zaki ba wannan gantalilliya, rijiyar da kowa kasa wasaki nai(gugarsa)" ya fad'a cike da k'araji.

K'ara tsorace tayi ta daburce bakinta sai rawa yake gashi daga ita sai shi a cikin jejin balle tayi kuwwa wani ya taimaketa, cike da rashin imani Jauro ya sarraremata k'afafu sannan yayi gaba da jakar kud'in, ganin mak'udai kud'i a ciki yasa yabar garin gaba d'aya zuwa birni danshi harka ta bud'e masa.

Anan ya barta cikin jini a sume batasan Inda kanta yake ba duk ta zawace zanenta..........


_shi ramin mugun ta in zaka gina ka gina gajere, dan bakasan ina rana zata fad'i ba_ 🤷🏽‍♀ 



************


Cikin rashin kuzari yana layi kamar d'an maye, ya taso k'afa yasa ya tad'iyeta ta fad'i, tsakiyar d'akin.

Jiki ta fara ja jikin tsoro "pls ya Abdool don't do this 2 me pls am scared" hannu ya d'aura akan lips d'insa yana kallon ta da rinannun idanunsa "shitt" akwai ya iya fad'a yana ci gaba ta tunkarota, a yadda yakejin sa muddin bai samu kusanci da mace ba zai iya mutuwa.

Tunkarota yake tana jan jiki harta k'ure da bango, kanta ta tura Cikin cinyoyinta ta matse tana kuka tana fad'in "nooo yaya don't come over there, pls leave to go" ko jin me take cewa ba yayi, yana isowa surar ta yayi ya jefa kan bed kamar ya d'auki 'yar baby, shima binta gadon yai, yayi kanta gadan-gadan, ganin yayo kanta da ganin yanayinsa yasa ta runtse idonta da k'arfi tare k'walla razanannen ihu saida d'akin ya amsa......

Ni Meryerm Abdool ganin abin zaifi k'arfin ganina yasa na tattara nawa da nawa na ja musu k'ofa cike da tausayin Ramlatun Baffa dan yau fuskar dan binni mai gilashi ba sauk'i a tare da ita..........lols



*****************


Tun ina jiyo ihun Ramlah daga waje har na daina jiyo komai (nace yau fa yarinyar baffa anji maza, yau ya Abdool ya d'auko magana).

Saida ya samu full satisfy sannan ya daga ta, nutsuwa ce ta fara dawo masa abin ya faru ya shiga dawo masa, dafe kai yana kallon ta cikin yanayi na galabaita ido akwai ke zubar da hawaye ko yatsarta ta k'asa daga wa "innalillahi wa'inna ilaihiraji'un" kawai yake maimaitawa, yana blaming kansa akan faruwar lamarin, shi kanshi yasan baije mata da lalama ba, amma ba laifinsa bane itace da gardama kuma is out of his control.

Agogo ya duba 3:30pm tun abun 1:00pm lallai yau ya d'auko magana, a gaggauce ya fad'a toilet ya tsarkake kansa tare da zura jalabiyasa d'aukar ta yayi tare da zanin gadon ya koma toilet, ruwan dubin da ya tara ya tsundumata ciki, k'ara ta saki cikin wahalalliyar murya data dashe don kuka tare da k'ankame masa jiki "pls yaya stop am dying".

Bubbuga bayanta yake cike da tausayinta " sorry princess, na dena ai, nine ba? bazan k'ara ba?" D'an bud'e ido tayi taga a bayi take yasa tayi saurin rufe idon tare da fashewa da wani kuka ga jikinta ko'ina ciwo yakeyi, wani irin haushinsa ne ya lullub'eta tana tuno abin da ya faru bayan 'yan a wanni dana sanin rashin bin Nihal take da dana sanin shigowa d'akinsa ashe bala'in da ke kiranta kenan, bala'i kam, "lallai ya Abdool mugu ne na k'arshe" ta fad'a ranta.

Shi yayi mata wankan sannan ya lallabata tayi na tsarki, ya maidata kan bed bayan ya canja sabon bedsheet, D'akin su yaje don dakko mata kaya, amma koda ya bud'e wardrobe ba kayan kirki a ciki duk k'ananu ne irin wad'anda suke sakawa, dakar ya samo mata wata rigar atamfa can k'asa, murmushi yayi "u see koma meye ke kika jawa kanki, irin wannan kayan ai sai gidan miji ake sakawa, gashi yau anjamin na tono rigima koya zamu karke oho" haka ya koma d'akin yana feeling special ji yake kamar ya sauke wani babban dutsi a kansa, tun da yake bai tab'a samun gamsuwa kamar yau ba(INA Zee team kuna jin Dr Majeed ko).

Duk wani taimako daya kamata ya bata a matsayin sa na likita, likitan ma na mata ya bata, sai rarrashinta da lallami yake kamar wani kwai tare da gayamata Kalamai masu sanyaya zuciya, amma ita kam ta kaurare sai kukanta ta keyi, ga wani haushinsa daya mamayeta lallai maza bata ido. 

K'arin Haushinta ya rasa inda zaiyi mata wannan danyen aikin sai cikin gidansu yanzu da wanne ido zata kalli Mami da Nihal, ya Riga ya gama da ita kawai, tun yana lallashinta cikin jin dad'i har ya fara jin haushi, kwanci yayi tare da lumshe ido yana jiyo sautin kukanta, yama rasa ta ina zai fara rarrashinta, tunawa da first night d'insu da Zainab yayi, Sam batayi masa wannan sakarcin ba,  nuna masa ma tayi ma ba abinda ya sameta duk da yasan ta wahala ita ma, amma ji wannan yadda take masa kuka kamar ya kashe mata uwa.

"Mtsss dama abinda kakeso shike wahalar da kai" ya fad'a a ransa, tashi yayi tare da zuba mata ido "meye matsalarki yanzu?" Ya jeho mata.

Kyalesa tayi tare daci gaba da kukan ta, haka yake gaba dayi mata magana cikin rarrashi, tayi masa biris tana ci gaba da kukanta tsaki yaja da k'arfi "tashi ficemin daga d'aki" yace yana nuna mata k'ofa, tashi tayi ta fara dafa hango tana tafia, tausayinta ne ya rufesa tashi yayi ya sureta, saida tayi k'ara jin ya d'agata tana wulle-wulle da k'afafu alaman bataso amma duk idonta a rufe suke gam, murmushi yayi mai sauti ganin yadda tak'i bud'e idon, a haka ya kaita har d'aki, kan bed ya direta tare da kai mata peck a goshi, sannan ya ja mata bargo, ya fice cike da farinciki..

Saida ta daina jin motsinsa sannan ta bud'e idonta harara ta balla wa k'ofar tare da rufe idonta, abubuwan da suka faru ne suke dawo mata a kwakwalwa "lallai al'amarin aure akwai girma, gaskiya yaya baka kyautamin ba" tana tuna yadda ya birkice kamar bashi ba......

Sai lokacin ya samu yayi sallar azahar da la'asar, addu'a sosai yayi musu, sannan yabi lafiyar gado dan shima ya jigata k'arfin hali kawai yace, lumshe ido yayi "yau na jawo rigima but so sweet more than word can say" yace tare da smiling mai k'ayatarwa......





_kuyi hak'uri da jina shiru da na shiga busy ne a yan kwana kin nan, #1love# ❤_




💄Meryerm Abdool💄
[9/23, 8:58 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



Ga shafukan mu nan da zaku ringa samun k'ayatattun novel namu👇🏻

*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*



An karbo daga abi Amamata R.D yace, manzon Allah tsira da amincin Allah yarda dashi yace.

_duk Wanda ya fita domin Neman ilima to kuwa yana kan hanyar daidaitacciya ta ubangiji har sai ya dawo_ 

A wata ruwaya kuma yace

_Neman ilimi wajibine akan kowa, mace ko namiji, k'arami ko babba, d'a ko bawa ba'a daukewa kowa ba_


*idan Mukayi duba da wad'annan hadisan kenan Neman ilimi dole ne garemu domin gyaran lahirar mu, sannan kuma menene banbancin mutum da dabba? hankali, taya ake sarrafa hankali? sai da ilimi kuma annabi Muh'd S.A.W yana cewa Ku nemi ilimi koda yakai birnin sin ne(China) hakan kad'ai ya isa ya nuna mana girmin ilimi, saboda haka 'yan uwa mu dage da neman ilimi wallahi jahilci babban ciwo ne, haka duhunsa yafi dare duhu, kada mu manta saita hanyar ilimi zamu San yadda zamu bautawa ubangijinmu dashi ake neman lahira dashi kuma ake Neman duniya, in fact ilimi shine gishirin rayuwa. Allah yasa mudace👏🏽*

Tunatarwa CE 👌🏻


~Namecy kyawun halinki na daban ne, haka ke 'yar baiwa CE, bazan gaji da mik'a jinjina gareki ba, Allah ya saukeki lafia ya raya baby khady akan sunnar manzo rayuwa mai albarka ameen~

Tawan tafi ta kowa😍👌🏻
Maryam Y Zango❤









      📝 *Episode* 206--210


A haka har bacci yayi gaba dashi mai cike da mafarkinta suna cikin rayuwa mai dad'i irin ta masoyan asali, masu tsananin k'aunar junansu...


Itama dai baccin  gajia ne ya d'auke ta, k'arfe 6 Nihal ta dawo gidan "iyye lallai babyn nan kina hutawa fa an gama karanta novel sai bacci, gaske Bestynki tai ta kiranki baki d'aga ba" tace tana k'ok'arin tayar da ita, jin zafi a jikinta ne yasa ta d'auke hannunta "oh ashe bata da lafia" ta fad'a tare da ficewa parlour.

Kiraye-kirayen magrib ne ya tayar da Abdool, shima dai zazzabin ne ya saukar masa a jiki, a daddafe ya samu yayi sallah yana mamakin wannan yanayi daya tsinci kansa Wanda ko a Zainab da take shine Karon sa na farko, baiji haka, amma kuma Ramlah ce ta daban ai, so yake yaje ya duba lafiyarta, mik'ewa yayi Cikin d'auriya a parlour yaci Karo dasu Nihal, Husna, Abduljabbar da junior suna kallo, da sauri junior yaje garesa dagasa yayi yana mishi wasa, shi kuma sai gwarancinsa yake masa, Su Nihal gaidashi sukayi, zama yayi kan, seat yana d'an sannan yace "saiku kad'ai Mami fa da Ramlah?" Ya tambaya kamar shigowarsa kenan.

"Mami, na ciki, sisto kuwa ba lafia itama tana ciki" Nihal ta ansa masa, "ashha meke damunta?" Ya tambayeta.

"Wlh ban sani ba, Yaya nadaiji jikinta da zafi, ko Sallah ma bata tashi tayi ba, Mami tace na barta harta tashi da kanta"

Mik'ewa yayi tare da shiga d'akin, zaune take kan dadduma tana sallah, kan sofa ya zauna yana kallon ta harta sallame, juyowa tayi dan ganin waye ya shigo, saurin d'auke idonta tayi ba tare data bari sun had'a ido ba, dama yasan za'ayi haka murmushi yayi tare da tasowa zuwa inda take kan dadduma, "baby ya jikin?" Ya fad'a yana k'ok'arin rungume ta, saurin janye jikinta tayi, Tare da kauda kanta gefe ba tare data anshi ba, smiling yayi ya dafa kanta jiyayi ba zafi sosai alaman zazzabin ya sauka "baby ya kike jin yanayin jikin yanzu, har can....nake nufi" ya fad'a yana dariya.

Bak'in ciki ne ya mamayeta "kai wlh namiji ba kunya, ai dole kace baby tun da ka halakoni" tace a ranta, d'aure fuska tamau tayi tare da mik'ewa a hankali, sannu take takawa tana d'an d'ingisawa kallon ta yayi cike da tausayawa, kan bed ta kwanta tare da jan blanket, lumshe ido tayi tana jinsa yana mata magana amma tayi banza dashi, smiling "baby rigama kefa kika kai kanki to meye laifina a ciki"? still shiru tayi masa.

Sunkuyawa yayi tare dayi mata peck a goshi, " get well soon my rigima baby" yace sannan ya aje mata tablets d'in da ya kawo mata kan bedside drawer, bayan ya gaya mata yadda zata sha, ko ci kanka batace dashi ba, shi kuma Sam ransa bai b'aci ba, saima wani nishad'i da yakeji a ransa jinsa yake ango sak.

"Yawwa Abdool ka dubata meke damunta ne?" Mami ta tambaya wacce fitowarta kenan, tana shirin zuwa duba ko ta tashi.

"Wai zamewa tayi da tiles shine k'afarta ta take ciwo da kai, amma na bata magani tasha ta kwanta" a take ya sharota.

"Ayya barin dubata" Mami tace tana shigewa d'akin, tana jin sallamar Mami ta k'ara lafewa kamar mai baccin gaske dan wani kunyar Mami taji ta saukar mata yau ba kad'an ba, gani take kamar tasan meya faru, Bata tasheta ba, sai kallonta da tayi cike da tausayawa tare cewa "Allah ya sawwaka dota" sannan ta fice.

Sannu a hankali take takawa tana fitowa daga toilet, Nihal ce ta shigo rungume da junior da yayi bacci "oh sorry sisto ashe zamewa kikayi sannu ko ya jikin?"

B'oye mamakin ta tayi dan tasan aikin Abdool ne "da sauk'i, sisto kinsan tsautsayi" tace tana fad'in "Son shine kayi bacci baka nemeni ba?" Tace tana zama gefen da Nihal ta kwantar da junior tare da shafa kansa.

"D'an rigimar yaronki ba, ai yazo kina bacci sai tada ke, Mami ta tasa k'eyarsa".

Murmushi tayi " nayi missing rigimarsa ai yau "......


*************

Haka akaci gaba da jinyarta harta murmure ba tare da Mami da Nihal sun fahimci komai ba, hadda Sadee tazo dubiya nan take fad'a musu exam d'insu ta fito kuma sunyi passing d'an ta dubo musu, murna sosai sukeyi sun kuwa zuwa jami'a nan take gayamusu kuma an saka ranar bikinta da Uncle lukman kuma ya amince mata karatu bayan aurensu, nan ma murna sukayi sosai da jin labarin, nan suka d'auko chapter Nihal sukayi ta mata tsiya saura ita Yaya Hakeem yayi sauri asha biki, itama Ramlah suka shigo nata wai Dr Majeed shima yayi sauri a tare su dagargaji biki.

Yak'e Kawai take musu amma yanzu bata son ana ko maganar Aure a gabanta dan ta tsorata da lamarin...

Yanzu ta daina shigar k'ananun kaya saidai native kawai, ta daina zama koda parlour ne, balle kuma maganan zuwa d'akin Abdool ko hanyar d'akin batasan gani, ta daina ansa wayarsa haka zaita kira da turo text duk bata kulasa tun ranar ta d'auke wuta tun yana dauk'ar abin wasa har ya fahimci ita fa da gaske ne, duk ta toshe wata hanya da zata had'asu bata fita saita tabbatar baya gidan, haka da taga lokacin dawowarsa yayi zata shige ciki.

Wannan hukuncin ba k'aramin galabaitar da jiki da zuciyar Abdool yake ba, don ganinta dai yana sanyaya masa rayuwa, gashi yanzu ganinta nason yafi k'arfinsa, shi dama ba zuwa d'akin su yake any how ba kamar ita, zai iya k'irge shigarsa d'akin, dama ciwonta ke kaishi tau ta warke, ba wata hanya zuwa, ya jigata iya jigata da hukuncin nata.

Mami ma saida ta tambayeta ko sunyi fad'a da yayan nata ne tace ba komai, batasan damunta ta kyaleta, shima data tambayesa ba komai yace, haka ta zuba musa ido tasan da wani Abu kam a k'asa.

Nihal tambayan da take mata kenan, ansar dayace ba komai, sannan ga canjin da take gani gareta ta daina k'iriniya da surutun nan any how ka English wears ta fake gefe ta daina sakawa, "uhm nidai gaskiya sister ban yadda ba da wata amma in tayi tsami maji" tun junior na damunta suje d'akin paa har ya daina saidai yaje shi d'aya...


Yaune ake kawo kawo kayan Nihal,Wanda yayi dai2 da 2week da faruwar abin, gida ya cika da mutane, Nihal tun safe tabar gidan ba yadda batayi da Ramlah suje tare ba, amma tace ba Inda zataje haka ta kyaleta ta tafi..


'Yan kwanakin jin ta take, gatanan dai ba komai baya mata dad'i daurewa kawai takeyi, kwance take d'aki surutun mutanen ne ya isheta gasu junior sai k'iriniya suke shida su Husna, tashi tayi ta wuce garden, bakin k'oramar taje tana shakar k'amshin furannin tare da wasa da ruwan da hannayenta..

Kamar an jefosa ya shigo garden d'in, shima dawowarsa kenan daga hospital, fresh up kawai yayi tare da sauya kaya zuwa k'ananun kaya sai zuba k'amshi yake.

Kamar a mafarki ya hangota gurin k'oramar ta shagala da wasa da ruwa, sanye take da atampa riga da Zane ne sun yi mata kyau, gani yayi ya k'ara masa kyau fiye da tunani.

Da sand'a ya isa, Inda take ta  bayanta yaje tare rungume ta, wani numfashi ya sauke da k'arfi Wanda ke nuna dinbin missing nata da yayi, ko ba'a fad'a tasan waye dan k'amshin turarensa na Amir ud ya sanar da ita, cike da masifa ta juyo dan sauke masa idonsu ne ya gauraya lokaci d'aya wani shock ya ziyarcesu, samun kanta tayi da yin shiru, jikinta kawai ta fizge ta fice da sauri daga garden d'in.

Sororo yayi yana binta da kallon mamaki, "shin gaske ne abinda na hango tattare da yarinyar nan? Tab idan ko hakane da hidden thing must be out soon" ya fad'a a ransa, a fili kuwa yace "hmm nawawoo there ris d fire on d mountain oo" smiling Yayi tare da shafo k'eyarsa sannan ya zube kan resting chair dake gun yana jin farinciki a ransa duk da yasan da rigima gaba k'adan.

Anyi komai daya dace, Inda suka tsaida ranar 4 months masu zuwa, haka tsaron ya watse kowa fuskarsa d'auke da farinciki, a ranar mutanen Besse suka wuce suma dai abin yayi musu sai fatar Alkhairi...

Ramlatun baffa fa jiki yak'i lafia yau ciwo gobe lafia, tun tana d'aurewa tana yi a tsaitsaye, har ya kaita kwance, ga ganin jiki ko a zaune take, ga zazzabi da amai ga rashin cin abinci, sai ramewa take a tsaye tak'i bari kowa ya sani, Mami tayi juyin duniya tace ita qlau take..

Ranar ko jikin yayi nauyi ko waje takasa tun abin safe tana dunk'ule a d'aki har 2:00, ba yanda Nihal batayi da ita ta tashi tasha koda tea amma tak'i ga juniour shima nanik'e da ita yak'i tashi shima, yana jiyan Maa, saida Mami ta dawo da office ta matsa mata dak'ar tasha tea kad'an shima tana gama sha ta Amayar hankalin Mami ya tashi, kallon tayi dakyau take a ranta ta zargi wani Abu, saurin basar wa tayi tace "is not possible" Abdool ta kira a waya ta gayamasa bata da lafia yazo ya dubata, yace to gashinan, haka suka zauna har dare babu shi.

Ranta ne ya b'aci da tasan ba zaizo ba aida asibiti zata kaita tun dazun, ganin jikin da sauk'i yasa ta bari har gobe idan baizo ba, da gangan ya k'irk'iri  kwanan hospital, sai kiran Mami yayi wai uzirine ya rik'e sa patient aka kawo emergency a can ma zai kwana.

"To" kawai ta ansa.

Da sassafe ta nufi wata private ta kusa dasu da Ramlah, Cikin karamci suka karbesu dake abokin Abdool ne mai hospital d'in, bayan gwaje-gwaje aka kawo result, kallon Mami doctor Ubaid yayi da murmushi a fuskarsa yace "Mama ai k'anwar tamu Nada Aure ko?"

Da d'an sakin fuska Mami tace "baka ganeta ba ai amaryar kuce".

K'ara fad'ad'a murmushi fuskarsa yayi" kai wlh ban ganeta Sam, da yake gani daya nayi mata a bikin marigayiya" sannan yace.

"Madallah Aure yayi albarka 'Yar reno ta zama Uwar reno kenan" ya fad'a yana dariya tare da mik'awa Mami result d'in........


*****************


Wasu Matasa ne sukaje jeji don dibar icce, anan suka hango mutum kwance cikin jini, da gudu suka koma Cikin gari suka fad'a.

A tare suka dawo da Ard'o da sauran dattijawan garin, suna zuwa wa zasu gani inba Hari ba, mamaki ne ya hana Ard'o magana shidai basai ma da fitar ta, ko daga INA take oh.

Ranga-ranga suka kwasheta gida aka wuce da ita amma abin takaici Lanti da Hinde na gidan suka k'i wanke mata zawon sai Shatu aka kira tayi mata, sannan suka kwasheta sai asibiti har lokacin bata farfad'o ba, Shatu sai kuka take ganin mahaifiyarta Cikin mummunan hali, sabanin Lanti dasai muzurai take idonta ko gezau.......








_Fatar Alkhairi gareku iyaye na gari abin alfahari, Alkhairin Allah ya cimmaku aduk Inda kuke#double love# ❤❤❤_

















💄Meryerm Abdool💄
[9/25, 2:18 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com* 





```Daga Aisha uwar mummunai (R.D) tace: Manzon Allah (S.A.W) yace "idan kika ga iska(guguwa) ya taso kuce, ya Allah ina neman Alkhairinta da Alkhairin da ke cikinta, da kuma Alkhairin da take tafe dashi, sannan ina neman tsarinka daga sharrinta da sharrin cikinta da kuma Sharrin da take tafe dashi.```

(Hakkun mubeen)👌🏻



_💋💋jinjina zuwa gareku, Fatyy Azland, Mom sultan, MSB(sakwara), Mrs fawwaz, Sadnas, sadnaf, Suhana, fannah, first lady, husna, sweery, fashuna and rest gaisuwa ta musamman my berries👌🏻😍_


Namecy na tafi ta kowa (Maryam y Zango) a kullum kina raina💋💋




    


   📝 *Episode* 211--215




Ware takardar Mami tayi, bayanai sun nuna tana d'auke da cikin 3weeks, Mamaki ne ya kama Mami Ashe dai abinda take hangowa a idon Ramlah shidin ne, "to yaushe hakan ta faru?" Tunani ta shiga, "okey wato ranar da yace ta zame kenan, kai yaran yanzu bata ido, tunda yace na bashi ita nace ba yanzu ba, shine ya nunamin iyaka, to ai yanzu yazo gatanan can su k'ara sa" duk Cikin ranta take maganar, amma a kasan ranta tayi farinciki da cikin saidai bataso ya faru kafin tariya ba, duk da tana da tabbacin Abdool bazai juyawa Ramlah baya ba, hasalima sonta ne yaja faruwar lamarin.

Murmushi tayi tare da kallon Dr Ubaid "mashaa Allah, Allah ya inganta".

Shima smiling yayi " Ameen Mama, amma Dr Majeed baya gari ne ko?"

"Aa yana nan hospital dai ya kwana shiyasa muka zonan kawai" ta fahimci so yake yasan meya hana ya dubata da kansa, tunda b'angaren sa ne.

"OK, bari nayi saurin kiransa na bashi albishir" murmushi kawai Mami tayi, sai yanzu ta gane dalilin sa na rashin zuwa wato yasan meyake damunta, kwafa tayi a ranta alaman zasu had'u.

 Magunguna ya basu yace ayi amfani dasu kafin Dr Majeed ya k'ara dubata, Ramlah dai zaune kawai take kamar mutum mutumi duk an sakata a duhu, ta k'asa gane komai, sallama sukayi masa sannan suka wuce, biye take da Mami jikinta duk sanyi ganin kallon tuhuma da Mami ke aika mata.

Bayan sun shiga mota ne Mami ta mik'a mata result d'in, hantar cikinta saida ta kad'a tare da zaro ido, sai hawaye sharr "wlh Mami ba lai....." Katseta tayi.

"I know ba laifinki bane, amma meyasa bakk gayamin gaskiyar abinda ya faru ba? Kodai baki d'aukeni a matsayin Asma'u ba?" Mami ta fad'a Cikin d'aure fuska.

Girgiza kai ta shiga kamar k'adangarwa sai hawaye ta k'asa magana, Aida nauyi ta tunkareta da wannan zancen koda Asma'un ce raye ba zata iya gaya mata ba".

"Na fahimceki yi shiru, share hawayen ki kinji" Mami tace da sigar lallashi, sannan tayiwa motar key.

Life kanta tayi a cinyarta tana kuka mara sauti "shikenan Yaya Abdool ya wargaje min rayuwa, yanzu shikenan, irin abinda ya faru da Larai ne zai faru dani, na shiga uku" wata 'yar kauyensu ce bayan an d'aura mata Aure ba tare ba mijin yayi mata ciki, aiko akayi ta rikici daga k'arshe ya saketa yace ba cikinsa bane.

Itama tunanin ta haka Abdool zaiyi mata, k'ara rushewa da kuka tayi na tausayawa kanta, yanzu shikenan idan Mami ta yadda Kilgori zata koma gurin Iya Hari "oh dota meye na kuka? Wipe ur tires zanyi maganin abin kinyi" Mami ta katseta jin sautin kukanta.

Tissue da Mami ta ta mik'a mata ta k'arba ba musu ta share hawayen, saidai ranta a jagule yake, lumewa tayi akan seat tare da lumshe ido, tunani barkatai takeyi, na neman Mafita.

Mami da kanta da had'a mata soft breakfast ta sakata gaba sanda taci sannan ta bata magani tanasha ba dad'ewa bacci ya d'auke ta nan parlour kan 2seat, jin saukar numfashinta ne ya tabbatar wa Mami tayi bacci, mik'ewa tayi bayan ta gyara mata kwanciyar.

Nihal ce ta fito "Mami kun dawo, meke damunta? Sisto ya jikin?" Ta fad'a a tare tana k'ok'arin tab'a jikinta.

"Karki tasheta mana yanzu ta samu bacci" Mami tace, sannan tace "ina junior?" Yana ciki yayi bacci " ta ansa.

Shigewa d'aki tayi ba tare data k'ara magana ba, wayar ta, ta janyo ta kira k'awarta bayan ta Zaune kan sofa, bayan sun gaisa "furnitures nakeso ayimin oda designers a satin nan Hajia in da hali" banji abinda k'awar ta fad'a ba.

"Uhum kedai bari, 'yata ce zata tare kuma Cikin satinnan nakeso ayi tariyar".

"Ada kenan, ai Abdool ya b'ata komai, ciki fa yayi mata dan ya nunan iyakata, nidai ayi k'ok'ari ayi komai in time ta tare kawai su barni na huta nima, koma kawai ki sayo komai biyu na had'a hadda na nihal ayi zuwa d'aya" ta sake ansata

Dariya itama tayi "to ai yaran yanzu sun shafawa idonsu toka ba kunya" sannan sukayi sallama, saida k'awar tata ta bata shawaran ta bashi matarsa tun da ya nuna buk'atar ta tace Aa sai sun shiga jami'a to ai ga digiri nan an samar mata Inji kawar.




**************



Yanke shawarar yaje gida kawai yaga halin da tace ciki, ba wani boyo a yanzu kam tunda Allah ya tonasa, koma ya fad'i ko kar ya fad'a bayyana kansa zaiyi, tare da Hakeem suka taho dan yace zai biya yaga sweetyn sa, Abdool sai tsiya yake masa wai baya kunyar sa a matsayin sa na sirikinsa, dariya kawai yayi yace ba wannan kuma, nan dai sukayi ta zolayar juna kamar yadda suka saba.

Nihal da har yanzu tana parlour tana jinya, itama har yanzu bata farka ba da yake harda maisa bacci a maganin, gashi tasha kuka, sai bacci take, ga hawaye sun bushe a idon, ita Nihal a nata tunanin zafin ciwo ne ya sakata hawaye.

Tsayuwar motarsu ce, tasa Nihal shigewa d'aki, dan tasan tare da Hakeem dayake ya gayama ta zuwan, da sallama suka shigo yana ganinta kwance a parlour tare k'ofa yayi wai saidai Hakeem ya tsaya daga waje Nihal ta iskoshi can amma bazai kallar masa mata ba.

"Dad'in ta dai nima inada matar ko?"

"Bamu shaida ba, kanada jingina dai" ya fad'a yana dariya.

"Zaku shaida ne very soon, kai kanka ka sani" 

"Tau naji tafi dai" ya turasa baya, girgiza kawai Hakeem yayi yana fad'in "zaka zo hannu zan rama nima" yace yana wucewa farfajiyan gidan, shi kuma ciki ya shige yana dariya "koka rame ba"

Sunkuyawa yayi tare da pecking goshinta, yana kallon ta da murmushi a fuskarsa, tayi wani fayau da ita ta k'ara haske, ga hawaye kwance a fuskarta, alaman kuka tayi kafin tayi baccin, tausayinta ne yaji yasan idan aka bibiya shine silar kukan, k'ara sunkuyawa yayi da niyyan lashe hawayen, dai2 fitowa Nihal cikin kwalliyar ta ta zuwa gurin Hakeem.

Fuskewa yayi, ita kuma ta sunkuyar da kai tare da gaidashi d'akin Mami ta wuce dan gayama ta zuwan Hakeem, shi kuma d'an siririn tsaki yaja "mutum ba damar ya sake da iyalinsa, gaskiya ya kamata mu tare hakanan" part nasa ya wuce, wanka yayi tare da sauya kaya, sannan ya fito dan shiga inda Mami.

Still bacci kawai take shaka abinta "aifa kin samu aikinyi baccin masu ciki" yace yana smiling, sannan ya shiga d'akin Mami da sallama.

Ciki ta ansa mishi fuska tamke, zama yayi a darare kan sofa, yana gaida ita "lafia" ta ansa a tak'aice, tare da mik'a masa takardar .

Shiru yayi kansa k'asa bayan yaga abinda takardar ta k'unsa Wanda already yasan dashi "sannu ko Abdool aikin ka yayi perfect" Mami tace ba tare data kallesa ba, still shiru yayi dan bai da bakin magana.

Jin shiru baice komai ba ta shiga surfa masa "wato tunda ban amince, sai kayi mai gaba d'aya ko? Yanzu ka kyauta kenan, duk da addini bai hana kaba amma ai yaci Karo da al'adar bahaushe ko? Yanzu kai fisabilillah idan akayi wa 'yarka haka zakaji dad'i eye?"

"Yanzu da ace ba gida d'aya kuke rayuwa ba, kuma ba jininka bace? Saika iskota har gidansu kayi mata cikin?" Nan fa taita mishi inda take shiga ba nan take fita ba, shiru yayi mata har saida ta sauke aya sannan ya shiga bata hak'uri

"Ba wani hak'uri ai, kaje kayi gyaran gidan ka k'arshen satinnan zata tare, ina shikenan ko?"

Hak'uri kawai yake bata, Sam baiyi tunanin lamarin zaiyi zafi haka ba, ya d'auka rigimar iya ta Ramlah ce, shi baiga abin fad'a ba, tunda dai sunnah ce yayi ba zina ba, akan wata al'ada can daban za'a damu, ai kowa yasan matarsa ce, kamar yadda Cikin ma nasane kuma ta hanyar halal, baiga abin damuwa dan miji ya kusanci matarsa kawai dan bata tare ba.

Kuma ai ko meye ita taja, tunda ita ke shigar da ke tayar masa da hankali kuma har d'aki take iskoshi fa tana kusantansa ai yayi k'ok'ari ma, a nashi ganin, kuma ai zaifi dad'in fad'a ace yayima matarsa ciki before ta tare da ace yayi zina da wata daban.

Sai bayan ya fita ne ya bawa Mami tausayi, tasan yanayin d'anta sarai mabuk'aci ne, ga shigar k'ananun kaya dasu Ramlah keyi Wanda saida yayi magana akan hakan tace ai ba laifi ne, laifin ba nasa shi d'aya bane hadda su, but still dole ta nuna b'acin ranta dan siyama Ramlah mutunci gareshi, amma ba laifi a Cikin haka a musulunci saidai al'adar bahaushe (mata iyayen kariyar al'ada).

Koda ya fito bata a parlour, ta tashi taji jikin da d'an sauk'i shine tai ciki dan watsa ruwa, wucewa yana tunanin ita kuma koda wace rigimar zata zo masa.

Murmushi yayi "unborn ka taimakamin daka zo gashi za'a bani matata cikin sauk'i, love u much 'yar baffa iyayen rigima"................






_kuyi hak'uri waya tace sai a slow matsala tace bani, Hocking take inna dad'e INA typing_








*love u guys buhut- buhut kunsan kanku😜 yes u!💋😍 #one love # all of u* 👌🏻  

















💄Meryerm Abdool💄
[9/26, 5:39 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*




```Daga Baban Darda'i (R.D) yace, Manzon Allah (S.A.W) yace:-
Duk Wanda ya k'are mutuncin d'an uwansa, Allah zai k'are fuskarsa daga wuta ranar alk'iyama.

Ma'ana Wanda ya tsare mutuncin d'an uwansa, ya rufa masa asiri, ya boye miyagun dabi'unsa shima Allah zai k'are sa daga wutarsa.

Kenan rufawa d'an uwanka musulmi asiri koda ka kamashi miyagun ayyuka wajibine ka boye su, sannan ka naima masa shiriya gurin Allah a maimakon ka fallasa shi, Allah yasa mu gyara```   👏🏽 

Tunatarwa ce👌🏻




   



    📝 *Episode* 216--220






Tsaye take gaban mirror daga ita sai k'aramin towel tana busar da gashinta da hand dryer, bayan ta gama ne ta shafa mayuka akan ta kama da ribbon, kallon kanta tayi ta mirror tare da d'ora hannu kan mararta "yanzu da gaske cikine dani?" Tace tana b'ata fuska da turo lip gaba, kamar mai shirin yin kuka "oh yanzu mai zan gayama su Besty idan suka gane, wayyo yaya ka cuceni Allah..... Shiru tayi jin an turo k'ofar tare da juyawa dan ganin mai waye.

Tsaye yayi b'akin k'ofar, yana binta da mayataccen kallon, smiling kwance a fuskarsa, tsuke baki tayi tare da d'aure fuska taci gaba da Shafa man ta, smiling yayi mai sauti tare da takowa zuwa inda take, rungume ta yayi ta baya tare da d'aura hannunsa kan mararta, kansa bisa kafad'arta.

Turashi ta shiga yi ba tare da tace komai ba, amma ko motsi baiyi ba saboda rik'on da yayi mata bana wasa bane, ganin ta k'asa kwatar kanta ne yasa ta fashe masa da kuka Wanda da gani na renin hankali ne.

Sakinta yayi tare da janta zuwa bed, zaro ido tayi sannan ta shiga turasa, sakinta yayi yana 'yar dariyar tsokana sannan ya rad'a mata a kunne " me haka baby na, lafiyar unborn d'ina, bafa abinda kike nufi bane, idan kuma Shi kikeso to sai muje d'akina, kinga da junior anan" ya fad'a cike da tsokana.

Wani takaici ne ya turnuk'eta ta k'ara bud'e baki "ka tafi Allah ko in tada junior ya ganka, kuma Allah dole ka zubar min da Cikin nan ko naje a zubar dashi haka kawai sai a ganni da ciki ba tare dana tare ba, kuma bazan yadda na haifesa yayon fitsari ya kamani a banza ba" har ya juya zai fita, yana dariya sai ya jiyo furucinta na k'arshe, tsayawa yayi cak tare juyowa fuskar murtuk'e yayi kanta gadan-gadan.

Baya ta rink'a yi cike da tsoro ganin yanayin fuskarsa, saida ta manne da sofa sannan ta dafe kanta da hannayenta, tana jiran abinda zai mata, shiru bataji komai ba, d'agowa tayi ta gansa tsaye idonsa sunyi ja.

Nunata yayi da yatsa "ke ashe mahaukaciya ce ban sani ba, to duk Wanda zai ganki da ciki shiya dad'e bai canyeki ba, da yake nina kiraki d'akin har nayi miki Cikin, to bari kiji ba yawon fitsari ba, ko yoyon kashi zakiyi sai kin haifesa tunda dan sunna ne ba zina ba, naga alaman kin renani tunda kinga gadon bacci na ba, to mu zuba nidake" sannan ya fice Cikin b'acin rai.
 
Tunda ya fara balbaleta ta rufe ido jikinta sai rawa yake dan bata tab'a ganin b'acin ransa kamar haka ba, iya sanin ta dashi, duk'ewa tayi k'asa tana rusar kuka lallai wannan shine a dakeka a hanaka kuka, kukanta ya tayar da junior shima ya tashi yana tayata.

A dole ta daina kukan ta d'auke sa tare dayi mishi wanka, shiryashi tayi itama ta shirya sannan ta wuce parlour dashi dan bashi abinci amma duk ranta a jagule yake tama rasa wane tunani zatayi, anan taci karo da Nihal ta dawo tare dasu Husna da driver ya d'auko daga school.

"Sisto kin tashi ya k'arfin jikin, wai meke damunki ne?" Ta jero mata tambayoyin same time, yake kawai tayi mata "uhm Malaria ce fa, na samu sauk'i sosai" sannan ta sauke junior ta rungume su Husna dake mata sannu tana tambayan su school.

"Allah k'ara sauk'i sis, barin shiga na fito" Nihal tace tana shigewa ciki.

"Ok" tace tare da shigewa kitchen...

Safa da marwa kawai yake tsakiyar d'akin, ransa a b'ace "lallai yarinyar nan ta gama renani at all, ni zata gayawa zata zubarmin da gudan jinjna? Lallai dole na jingine sonta a gefe na koyamata hankali, dan naga kanta na rawa, Amma zanyi maganin abin"........





*****************




Gaba d'aya ya watsar da lamarin Ramlah gefe, duk da yanda ruhi, zuciya gangar jiki suke son kasanewa da ita, a ganinsa hakan zaisa ta shiga taitayinta, bai cika zama gida ba yanzu inya fita tun safe sai dare kuma, yafi maida hankali akan gyaran gidan kamar yadda Mami ta umurcesa, duk da ba wani gyara ne sosai ba, amma kullum yana gurin ana k'alk'ale-k'alk'ale kunsan Drs komai nasu unique ne, yau ma office d'in Hakeem yaje tare da damunsa ya tashi ya rakasa ya dubo aikin da ya bayar ayi masa.

" wai kam wannan gyaran gidan na meye ne? Naga dai tare zakuyi tariyar nan da bikinmu gaba d'aya, kuma still have time"

Dariya yayi "naka wasa, ada kenan, aini a satinnan zamu tare"

"Bansan da wannan ba, kode ka k'asa jurewa ne da jiran 'yar renon taka zakayi mata k'anwa" Hakeem ya fad'a cike da zolaya.

" 'yar reno ai ta dawo Uwar reno kuma yanzu, saidai kace Maman Unborn " ya bashi amsa Cikin seriousness.

Cikin mamaki Hakeem ya kallesa, ganin iya gaskiyarsa ne yasa yakai masa duka yana dariya "amma dai wallahi bakayi ba, yanzu saida ka lalube yarinyar nan ka lallab'a kayi mata ciki, amma dai anji kunya".

" dalla matsa can mutum da matarsa zakace naji kunya, ni kaga tashi muje ayi a gama gyaran nan dan nafison ta tare da wuri kasan eh..yane..eh" ya fad'a yana dariya tare da kanne ido daya.

"Kai kam Allah shiryamin kawai zance, yaro dakai sai jarabar tsiya" Hakeem ya fad'a yana hararansa tare da mik'ewa suka fice.

B'angaren Mami sai shirye-shirye take, kullum bata nan bata can anata hada-hada, ta kira ta gayama su Inna maganar tariyar haka Ard'o ma ta kirasa, saidai yace bazai samu zuwa ba, zaidai aiko da sak'o, har gidan Zainab ta kira kuma sun ce zasuzo ai an zama d'aya, wata 'yar sakkwato Mami ta d'auko take gyara Ramlah ciki da waje tasan yanayin d'an nata saida gyara.

Ita dai Ramlah batasan ma'anar gyaran ba, sai ta d'auka ko don tana da ciki ake mata gyaran, to amma saboda me bata da Amsa dole ta kama bakinta, itama Nihal da batasan wainar da ake toyawa ba danko labarin Cikin bata bale tasan na tariya data tambayi Ramlah cewa tayi itama bata sani ba wlh, bata hak'ura ba ta tambayi Mami, harara ta rakata da ita tace meye nata inta sani dole ta kama kanta.

Sai a bakin Hakeem takejin komai aiko jiki na rawa ta fesawa Sadee M bash, da sauran k'awayensu na jiki, nan suka had'u sukazo suka yima Ramlah caaa da masifa da tsiya irin ta 'yan mate, hadda fad'in ashe taje garin....shine bata gayamusu ba, to ta basu labarin ya abin yake..

Banza tayi dasu ita abinda ya dameta ya isheta ga Mami tace ta shirya k'arshen sati zata tare, tasan tata tazo k'arshe idan ta shiga hannun yayan nata, gashi ta daina ganinsa ya daina shiga sabgarta, alaman fushi yake da ita saboda yasan ya gama da ita shida laifi shida mata fushi.




************





Gidan Mami ya cika da jama'a da yake ita mutuniyar mutane ce, kamar wani biki ake ba tariya ba, Maman Zee ma ta iso da kanwarta Amal da yake itama tayi graduation itama tare dasu Ramlah, sun ji dad'in ganin junior Cikin kulawa kowa nan nan yake dashi musamman Ramlah Wanda hakan ke nuna musu baya cikin tsangwama, Inna 'yar tsohuwa ma sunzo ita da matar Uncle Mansur, sai tsiya takema ma Ramlah wai Amarya zata tare da d'an kunshi sudai kam anyi mara kunyan yara, Abdool ma tayi masa, amma shikam saidai ya bata amsa yace su ai 'yan zamani ne ba irinsu ba k'auyawa.

Ard'o ya aiko tsumi da sauran kayan gyaran amare yace zaizo daga baya in an kwana biyu yaga gidansu, ranar Asabar aka gudanar da walima anan gidan Mami inda su Nihal da M bash suka taka rawar gani, anyi rabon kayayyaki Wanda duk sune suka d'auki nauyin yi hadda Amal, Amarsu ansha kyau, gyara tasha har ta gaji, ansha Kitso da kunshi Wanda duk akan dole tayi su dan itakam a firgice take, lafewa kawai tayi tana yak'e, da daddare bayan tasha nasiha sosai daga iyayen nata, sai kuka take dak'ar aka rabasu da Junior ta dage tare zasuje saida Mami ta amsheshi Wanda shima sai kukan yake yana kiran "Maa" Inna, da Sauran k'awayen Mami ne matar Uncle Mansur sai su Nihal sukayi rakiyar amarya zuwa tamfatsetsen gidanta dake unguwar Dosa, fad'in kyawun gidan ma bannan lokaci ne, just guest friends. Lol.

Su Nihal sai zagawa gidan suke suna ta santinsa, daga nan suka tsere, dama su Inna sun dad'e da wucewa, Nihal tana tsoron yayan nata  dan tun rana ya kirata yace ba wani siyan baki da za'ayi kada ta yadda ya samesu a gidan..

Ramlah sai shafawa tayi taji basu, zagaya gidan tayi, "mashaa Allah" kawai take fad'a da tsarin gidan yayi mata sosai kamar tsarin larabawa komai neat ba hayaniya da yawa ga furanni ta ko'ina sai K'amshi ke tashi gidan dai yayi ba k'arya.

Toilet ta zarce nan ma tasha kallo, kafin tayi wanka tare da d'auro alwala, shirinta tayi kamar yadda ta saba, sannan tabi lafiyar bed dama a gajiye take libis, bacci ne mai cike da dad'i ya d'auke ta.

Abdool ma daga bakin k'ofa ya dakatar da abokansa yace ba wani sayen baki da za'ayi kuma nasihar sun gode, nan suka kansa da zolaya da tsiya yace yadai ji.

D'akin sa ya fara shiga ya watsa ruwa tare da saka farar jalabiya, sannan ya nufi d'akin ta da ledoji a hannun sa, jin ba'a amsa sallamarsa ba, yasa ya shiga kawai dan yasan ko taji tana iya kin amsawa saboda haukanta.

Kwance take sai sauke numfashi take Cikin nutsuwa alaman tana enjoying baccin nata.

Tsaye yayi kanta tare da hard'e hannayensa a k'irji, kallon yake kamar yau ya fara ganinta, tayi masa wani irin kyau ji yake kamar ya shige jikin jikinta yai ta romance nata, lips d'inta ya kalla da suka kara jajar dasu ganin sha'awa, har ya sunkuya sai kai mata kiss sai kuma ya fasa kada ya tasheta ya katse mata jin dad'i.

Ledojin ya aje kan d'an table dake gefen gadon tare da wuce wa, har ya kai k'ofa, ya tuna kila fa bataci komai ba, kitchen ya wuce ya d'auko plate da cup ya dawo, naman ya juye Wanda yasha kayan vegetable sai tururi yake, sannan ya tsiya ya mata juice d'in ya ije.

Gefen gadon ya zauna tare shafo fuskarta a hankali, motsi ta faraji jin ana Shafa ta ne yasa ta ware idonta tare da sauke su a kansa, tsuke fuskarta tayi, shima fuskarsa ba yabo ba fallasa yace.

"Tashi ga abinci nan ciki nasan da wuya idan kinci wani Abu, and banaso ana barmin baby na da junwa" yana gama fad'i ya tashi ya fice.

Da harara ta rakasa, tare da jan tsaki, nan idanunta sukayi tozali da plate d'in, wani yawu ta had'iye, Cikin yayi k'ugi jikinta har b'ari yake, abunka ga mai yaron ciki, da sauri ta sauko ta d'auki plate d'in ta baje k'asa ta shiga d'ibarsa........








_kowa yace shine tofa ba shine ba_ 🙄 






















💄Meryerm Abdool💄
[9/27, 8:01 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*





*_Annabi Muhammad S.A.W yana cewa "Ku kasance masu yawan tunawa da mai yanke jin dad'in rayuwa, mai rabaka da masoyinka da mahaifanka, kai dama duniya gaba d'aya wato MUTUWA. Yar uwa nidake dasu anya muna tunawa da ita a kowace rana? Muna sane da tana nan tana bibiyarmu ba makawa ba gudu ba tsira? To idan hakane mai muka tanadar ma wannan doguwar tafiya? Wane guzuri muke dashi a wannan tafiyar? Mu dage don lahira anan duniya ake nemanta, kuma mutuwa bata bada alert zuwa take bagatatan koka shirya ko baka shirya ba!🤷🏽‍♀ Allah ya bamu kyakkyawan k'arshe dan alfarmar rasulillah S.A.W_* 👏🏽👏🏽



Kud'in na daban ne a gareni

```Maryam Y Zango(Wanda yayi nisa)
Raheenat Mahmoud(meye hujjarki)
Fareedat sweery (yar sarki) muna zuba👀
Fashuna
Salma Queen(momma) 

Daduk sauran member of pure moment, Ku sani kuna wuta fa, kufa unique ne, just keep d fire burning #ana tare iya wuya#💋💋❤```



  






    📝 *Episode* 221--225







Kiran farko na Asuba akan kunnenta, dama bata da nauyin bacci, ga kuma training d'in Iya Hari, a daddafe tayi alwala, dan da muguwar yunwa ta tashi jikinta har rawa yake kamar wacce tayi sati bata ci ba, har mamakin mugun cin nata take daya sameta a 2days d'in nan.

Koda Abdool ya shigo dan tayar da ita a dadduma ya sameta tana raka'atanil fajr, gaggauta fita yayi jin ana shirin tada sallah.

Tana kammala wa ko addu'ar kirki batayi ba, ta kwab'e hijab d'in tare da janyo sauran kazar data rage, ba maganan d'umamawa haka tahau ci, saida ta cinye tas, ta kora da juice d'in, ta dad'a da hollandia sannan taji dai2, ajiyar zuciya tayi kana ta d'auki Qur'an ta shiga karantawa.

K'arfe 6:00am ta gama karatun da azkar nata, mik'ewa tayi tare da d'aukar plate takai kitchen, wankesu tayi sannan ta share ko'ina tare da mopping, turare tayi nan take gidan ya d'au seti da k'amshi, to renon Iya Hari ce ba kyuya tana ganin ta cutar da ita, batasan taimakon ta tayi ba.

Saidai jin tayi turaren na haye mata kai, Allah yasa iya parlour ta saka bada bedrooms ba, d'akin ta ta shige tana toshe hanci ga zuciyarta sai tashi take kamar zatayi amai, aiko saida tayi sannan ta samu sassauci, saida ta dad'e zaune kafin ta iya gyara jikinta da wanka gaba d'aya.

Bayan ta  gama shafe-shafenta, sip ta bud'e Tun k'asa har sama duk English wears tsaki taja tare da rufewa "nice zan K'ara saka wad'annan? God forbid" (d'iyar Baffa an tuba) lol.

D'ayan gefen ta bud'e nan taga su atampha, less, shadda da materials, wata super ta ciro blue and yellow, riga da siket ne ya zauna daram, tasan gun telansu akayi dama shike kai musu dinkin, bata d'aura d'an kwali ba, sarka ta saka 'yar simple me kyau, perfume ta d'auko dan fesawa tun kan ta fesa taji ya fara hau mata kai, dafe kai tayi tare aje turaren, hollandia ta k'ara sha sannan tasha maganin ta, da Mami tayi mata gargadi kula da shansa, bed ta koma tana game daga nan bacci yayi gaba da ita.

Saida gari yayi haske sannan ya dawo daga masjeed,  direct d'akin sa ya wuce saboda a gajiye yake, duk kwanakin sunata hada-hada bai samun issheshen bacci, kwanciyar sa keda wuya bacci yayi gaba dashi shima mai cike da mafarkin 'yar rigimar tasa suna soyewa.....


**************

10:00am

Knocking ne ya tayar dashi, jiki a mace ya isa tare da tambayan waye, Nihal data shaka Dan sun dad'e wurin suna Knocking, jin muryan yayanta yasa ta waye tare da fad'in "mune" bud'e musu yayi sannan ya basu hanya, junior kuwa sai mak'ale sa yayi shi kuma ya daga shi sama suna dariya, gaidashi sukayi sannan suka aje basket d'in abincin akan dinning suna tambayan Ramlah.

"Tana ciki, and ki zubo min abincin nan, ki kawomin a d'aki" yace ma Nihal yana wucewa tare da junior.

"Kai waya gayamiki Amarya na baccin safe" Nihal tace tana Kai mata dun du a baya.

Bud'e ido tayi cike da masifa, sai taga ba Wanda take tunani bane, dariya suka sa mata Nihal da Amal, dan zaro ido tayi " yaushe kuka zo?" 

"Ina zaki sani kuwa kina nan kina bacci, keda ya kamata ace kina parlour kina jiran isowar mu" Amal ta fad'a tana harara ta.

Dariya tayi "um kinga fa daga game ne, baccin ya sureni" tace tana sauke k'afafun ta k'asa, parlour suka wuce tana fad'in "me kuka zo mana dashi ni break fa ban had'a ba nayi baccin" d'an yunwa takeji sosai, dinning Nihal ta nuna mata tana mik'ewa zuwa kitchen dan d'auko plate dan zuba abincin da Abdool yace takai masa kada ta manta.

Gyara zama sukayi a parlon tare da jona kayan kallo, ganin Nihal ta d'auki hanya d'akin Abdool yasa tace "wai bani kika zubawa ba?" Harara ta balla mata "OK jirani nazo" tace tare da wucewa, dariya Amal tayi tace "um aunty barin zubo maki" ta mik'e zuwa kitchen...

Junior ne kad'ai kan sofa yana game da tab d'in Dadyn sa "son ina Dady?" Iya toilet " yace yana cikin bagwarar hausarsa, aje abincin tayi kan coffee table nashi, tana fad'in "wato ba zakaje Inda Maa dinka ba ko?" Tana k'ok'arin ficewa.

"Maa tana iya" ya fad'a yana aje tab d'in tare da biyota baya da gudu...

"Maa!" Ya fad'a da k'arfi, Ramlah dake zaune tana d'uri Amal sai dariya take mata, aje abincin tayi tana tare da ware hannu tana mishi murmushi.

"Son d'ina ni d'aya" ta fad'a bayan ya shige jikinta ta rungume sa "iyye yaron Maa ya kake"

Nan suka zauna sunata mata tsiya wai ba'asan Amarya da sakin ciki tana d'uri, jinsu kawai take, nan Sadee ta iso tare da wasu k'awayenta suka had'u sai tsiya suke mata, wai ta fad'a musu EDD dan kada ayi musu ba zata tunda anyi basu sani ba, banza tayi musu kamar bataji su ba, nan suka wuni har 6 sannan suka wuce bayan ta cikasu da kayan make up da English wears tare tace suje suyi ta sakawa itakam tayi retired sannan tace Sadee CE ta cuceta koma mai ya faru, dariya kawai suke mata, tace suyi dakyau yana zuwa Kansu, nan sukayi sallama da Amal dan gobe zasu koma, ba yadda batayi dasu su bar mata junior ba, sukace Aa sokoto za'aje dashi gobe tare dasu Amal, kuma ma Mami tace bata gama warwarewa ba balle ta iya d'aukar rigimarsa tadaiji da kanta..

Abdool kuma yana gama Karin ya shirya, ta k'ofar parlonsa ya wuce abinsa, bashi ya dawo ba sai after magrib, yau ma kazar ya k'ara kawo mata, saidai kowa jin k'amshi yake bamai kula wani.

Washe gari su Inna sukazo tare sukayi mata sallama, ta cikasu da tsaraba suma, sati Mami ta d'auka tana aiko musu abinci saida Ramlah ta tace ta daina kawo wa ta samu sauki zata iya yi sannan ta daina, komai tanayi a gidan kama da gyaran gidan, girki da sauran su, hadda maid Mami tace ta kawo mata tace aa, saidai ita da mai house d'inne kowa a sama magana ma sai a dole sukeyi, kowa d'akin sa yake kwana saidai hakan bai hanashi kula da duk wani motsinta ba,duk da zaman ba dad'i yake mishi ba dan gaskiya yayi missing nata d most, kusan kullum saita kira Amal ta had'a ta da junior sunyi waya, Inda hakan ba k'aramin dad'i yakewa iyayen Zee ba.

Ard'o ma suna waya akai akai, kullum maganar sa suna lafia dai ko to ta k'ara hak'uri yana nan zuwa....




****************


Wasa-wasa har sunyi month da tarewa ba wani ci gaba a zamansu shi yanaso yaga iya gudun ruwanta ne, itama zaman nasu na damunta dan kad'aici ba dad'i damar ta ma bata irin laulayin nan ci daine kamar gara, wayarta da kayan kallo ne abokan hirarta, anata ganin wulak'antata ne Abdool yayi saboda ya samu abinda yakeso daga gareta, bayan itace ta d'au zafi data ganshi zata wani d'aure fuska kamar taga abin k'i, amma kuma shi ta d'aura wa laifi.

Kullum zata kira Mami ko ita ta kirata, tana tambayan ta ba matsala tace ba komai, shima abinda yake gayamata kenan kullum inta tambayesa, kuma ko zuwa tayi basu bari ta gane komai.

Yau kam ya d'auki niyyan gyara zamansu dan ya fahimci in yabi ta tata saisu shekara ba ruwan ta, shiko ya gaji da zaman ga extra care da yakeson bata ita da unborn.

D'aure mad'aurin rigar baccin ta tayi tana k'ok'arin Sanya gashinta a net ya shigo, can ciki ta amsa sallamar kamar yadda ta saba, ba tare data juyo ba, dama normally duk dare zai shigo ya dubata kawai ya fice.

Zama yayi kan sofa, yana binta da kallo, itakam sai lamarin gabanta take, shiru ya ratsa su bamai magana na y'an sakwanni.

"Meye matsalarki da zama dani a yanzu?" Ya jefa mata tambayan.

Ba tare data juyo ba "babu" tace in short.

Smiling yayi yace "OK bakya k'auna tane?"

Wannan Karon saurin juyowa tayi tare kallon sa fuska d'aure "au nice ma bana k'aunarka?"

"Of course! Bakyasona, dan da ace kina sona danna kusanceki saboda kawai baki tare ba, ba zaki d'auki zafi haka, har da fad'in zaki zubar min da ciki imaging!"

Hawaye ta fara cikin k'unan rai ta fara magana "Yaya halin ko in kula da kake numanin ne k'auna, ko kuwa saboda ka sanni a 'ya mace kafin na tare gidan ka? Haka kayi ma Aunty Zainab, a gidan su kaje ka fara saninta kafin a kawo maka ita?" 

Duk'ewa tayi gurin tana kuka "saini saboda kawai na damu dakai naje d'akin ka? Idan akayi ma 'yarka haka zakace so ne?" 

Duk ya rikice ganin yadda take kuka akan wannan abun da bai isa ayi fad'a akansa ba, meye a ciki, tashi yayi ya taka zuwa Inda take tare da mik'ar da ita tsaye ya had'a ta da k'irjin sa, tura sa ta farayi, k'ara riketa yayi Sam baya son kukan nata, kuma ya shirya d'aukar duk laifin da zata d'ora masa, zai bata hak'uri dan dai a zauna lafia, tun ta d'auki abin da zafi.

"Saurareni Ramlah kinji, pls nutsu kiyi hak'uri na sani ban kyauta ba amma kiyi hak'uri kuma ki sani sonki ne ya kawo haka" ya fad'a da slow voice nasa.

Janye jikinta tayi ba tare datace komai ba, gefen bed ta zauna tana ci gaba da kukanta, binta yayi yana rarrashinta dan kukanta ba kad'an yake tab'a sa ba, "me kikeso nayi miki na goge laifina a gareki?"

Nan ma shiru tayi masa tanaci gaba da kukanta, sai rarrashinta yake amma tak'i kulasa, ita gani take dad'in bakine kawai yazo yayi mata dan wata buk'atar sa daya samu ya biya yaci gaba da sha mata omo.

"Aiba haka ka zauna da Aunty Zainab ba, zama kake tare da ita kana sake mata fuska, kana mata hira kana d'ebe mata kewa saboda takai mata budurcinta gidan ka, ni kuma daka amsa tun gida, ai ranar da aka kawo ni bakayi d'okina ba, hasalima had'e min fuska kayi tunda ka samu abinda kakeso dani tun gida, baka damu dani ba baka zama dani kaji damuwa ta, baka debemin kewa wannan duk son ne? Yanzu ma da abinda ya kawo ka shiyasa kakemin dad'in baki, daka samu ka watsar dani"

"Oh Allah" shine abinda ya fad'a, mezai gayama ta yadda dashi, shi baiyi hakan dan tozarci gareta ba, amma ta fahimceshi opposite, gashi ba ganin surutu ba, balle yai ta mata harta fahimceshi, Sam baison hayaniya duk ta birkita masa tunani.

"Ban iya tsari ba Ramlah, kamar yadda ban iya k'arya ba, a kanki na fara son mace, kuma banso wata bayanki ba kamar yadda nakeson ki, ki yadda dani, bazan tab'a wulak'antaki ba, kefa jinina ce, kuma matata pls believe me!"

Shiru tayi tabbas tasan bai iya k'arya ba kuma tasan yana sonta, to amma maganar baiso wata ba bayanta kamar yadda ya sota ne bata yadda dashi ba kuma zata k'arya ta shi akansa, don son da ya nunawa aunty Zainab yafi nata(ayya anaki ganin ba)

Jin tayi shiru yasa ya mik'e "ina zuwa yanzu" ya fad'a tare da fita, kiran Zainab da tayi ne ya tuna masa da sak'on da ta bayar ya bata, duk da baisan meke ciki ba, yaji ya kamata ya bata a yanzu, tunda dama cewa tayi idan sun tare.

Tana nan Inda ya barta, sunkuyawa yayi har sunajin numfashin juna "gashi Zainab tace na baki" ya mik'a mata takardar tare da zuba mata ido.

D'agowa tayi suna had'a ido tayi saurin d'auke nata, jiki a sanyaye ta amsa.

Ficewa yayi ita kuma ta warware takardar ta fara karantawa kamar haka...

_Zuwa gareki Aunty Nah kuma k'anwata Ramlah_...........













💄Meryerm Abdool💄
[9/29, 9:10 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*



*_Manzon Allah S.A.W yana cewa:- yake Fatima 'yar ma'aiki zan iya baki komai anan duniya, amma ki sani bazan iya amfanarki da komai lahira ba, aikinki ne kad'ai zai ceceki da rahamar ubangiji._*

_idan har Manzon Allah zai fad'i haka akan mafi soyuwa gareshi a cikin 'ya'yansa, to ina gamu gama garin mutane? Ina mai tak'ama da ilimi, arzikin, darajar, kimar, muk'amin babanta? Nasan dai tasan koda wasa ba zata kimantasa da fiyayyen halitta ba, to ko idan hakane mu sani iyayen mu ba zasu iya ceton mu da komai ba, aikinmu ne kad'ai zai cecemu, dan haka mu dage, mu gyara gobenmu, Alla yasa mudace da rahamarsa👏🏽_











     📝 *Episode* 226--230







_"Ina rubuta miki wannan wasik'ar ne a dai2 lokacin da nake tunanin zanbar duniya, ina mai rokonki da had'a abinda zan haifa da sauran yaran da zaku haifa nan gaba, nasan zaki iya dan na yadda da kyakkyawar zuciyarki, sannan ina mai neman afuwarki akan kiyafe duka laifukan da nayi maki both known and unknown, by may size bakiyin komai ba face Alkhairi idan kinyi na yafe maki har ga Allah, a tare na sameki da Dr Majeed gashi zan barku tare dama Allah ya k'addara sai mun zauna ne a sanadin wannan d'an ko 'yar  ubangiji yafimu sanin dalilin sa na tsara hakan wata kil yasan Dr bazai iya adalci a tsakaninmu ba idan kika tare duk da dimbin kyawun halinsa da adalcinsa, Ramlah yayanki Mutumin kirkine mai adalci duk da kin zama tauraruwa a cikin zuciyar sa bai hana ya bani wani fili a rayuwarsa ba ya bani kulawa da soyayya da mata dubu suka rasa a wannan zamanin yayi zaman Aure dani kamar yadda Manzon Allah S.A.W ya umurce mu bai tauye da komai ba, Ramlah bayan Mami ba abinda yayanki yakeso a rayuwa sama dake, duk wani motsi da bugun zuciyar sa dake yake yinsa, nasha jin kishinki lokuta da dama amma innayi tunani sai inga ba dai2 ne ba, saboda yayimin karamci bai kamata naji haushin Abu mafi soyuwa a garesa ba, wallahi Ramlah tun da nike a rayuwa ban tab'a ganin soyayya irin wacce yayanki ke miki ba ana yiwa wani ita, Ramlah kin dace da masoyi na gaskiya, ki daure ki nuna masa soyayya a zamanku ki tarairayesa da dukkan kulawa kiyi hak'uri da buk'atarsa ki d'aure ki jure inada tabbacin zakuyi zama mafi kyau a rayuwar aurenku, ina muku fatar Alkhairi a zamanku, ina rokon Allah ya kawar da fitina da shaidan a ciki, wishing d most blessing, peaceful marriage life"_

Ur sister
Zainab Salis

Hawaye ne wani nabin wani ke sauka a idanunta, jimk'e takardar tayi da duka hannayenta biyu "nima nayi kishi dake sosai Aunty Zee, na d'auka kin kwace min Yaya Abdool ashe ba haka bane, na yafeki aunty Zee bakimin komai ba, kuma inshaa Allah, bazan tab'a banbamta junior da d'an da zan Haifa ba, ina sonsa sona gaske, Allah yakai haske k'abarinki, Allah ya sadamu a Aljannarsa mad'aukakiya don rahamarsa, missing u much Aunty Zee" duk Cikin kuka take maganar cike da nadamar abubuwan da tayi ma Dr Majeed, tasan komai ya faru laifin ta dan ita taja hankalinsa kuma tasan yaso ta tun kafin ta zama abarso, to yanzu ta ina zata fara bashi hak'uri?

Turo k'ofa akayi ganin tana hawaye yazo da sauri tare da rungume ta yana bubbuga bayanta, mamakine ya kamashi ganin bata tureshi ba saima k'ara lafewa da tayi a jikinsa, bai gama mamaki ba yaji ta zagayesa da duka hannayenta ta rungume shi.

"Pls yaya Sorry 4 everything I totally misunderstand u pls forgive me....!"

"Shitttt! U don't nothing wrong!" Ya katseta tare da d'ora yatsansa akan lip nata, bud'e baki tayi zatayi magana, kafin tace wani abu har had'e bakinsu guri d'aya, cikin wani irin salo yake kissing nata, itama ware wa tayi tana tayashi, sun kai 10mt haka, sannan ya fara zare bakinsa yana kallon ta k'asa-k'asa idanunsa sun canja launi zuwa ja, ita kuma sunkuyar da kanta tayi cike da kunya, mik'ar da ita yayi tare da d'aukar ta kamar wata baby doll, bai sauketa ko ina ba sai toilet, da kansa yayi mata alwala shima yayi sannan ya sake d'aukota direta yayi tare da shimfid'a musu darduma, sif ya bud'e ya d'auko mata zane da hijab, ita dai binsa kawai take da kallo, turare ya d'auko zai fesa "aa karka saka" tace, murmushi kawai yayi tare da mik'a mata, itama murmushin tayi masa Wanda rabon da yaga irinsa akan fuskarta har ya manta "nafayi sallah na" tace cikin siririyar muryarta.

Kashe mata ido d'aya yayi yana smiling "wannan special ce irin ta ma'aura wacce bamu samu damar yi ba zamuyi k'ara'i" turo baki tayi kamar wata yarinya, cikin wasa yasa yatsarsa ya buga bakin kad'an "common baby munada abubuwa a gabanmu masu yawa ga time na tafiya" d'aura zanin tayi tare da saka hijab d'in ba tare da tace komai ba.

Shigewa gaba yayi tare da jansu, raka'a 2 sukayi kamar yadda sunnah ta tanadar sannan ya dafa kanta ya shiga kwararo musu addu'a da harshen larabci da kuma hausa duka.

Saida yayi tsawon 30mnt yana addu'a, mik'ar da ita yayi sannan ya nad'e darduma tare da cire mata hijab da zanin ya ninke, gefen bed ya zaunar da ita sannan ya zauna shima, kama hannun ta yayi yace "nagode wa Allah daya nuna min wannan ranar da muka samu fahimta juna, zanyi marking nata cikin rana mai girma bayan first night namu, sannan nayi alk'awarin zan kula dake zan tarairayeka zan zamo hango abin jinginawarki zan kare mutuncinki zan rik'e amanar ki har abada, fatar zakiyi hak'uri dani da kuskurena idan nayi miki, ina mana fatar zaman lafia mai d'orewa".

Matse hannunsa tayi cikin nata " inshaa Allah zaka sameni mai biyayya a gareka, ta kowanne fanni zanyi iya k'ok'arina, Allah ya bamu Alkhairi mai dorewa a zamanmu"

Lumshe ido yayi wani dad'i na ratsashi yana feeling special, sannan yace "ameen uwargidana, one mnt" yace tare da mik'e wa yabar d'akin, plate ya dawo dashi a hannunsa, kayan cikine masu kyau a ciki da zafinsu sunji albasa, da tumatur da yaji sai k'amshi ke tashi, aiko d'iyar baffa tuni yawu ya tsinke, table ya janyo ya girke a gabanta tare da bud'e fridge d'inta ya d'auko fresh milk, stool din mirror ya janyo ya zaune yana fuskanta "bismilla" yace tare da d'aukar yanka d'aya zuwa bakinta, itama d'auka tayi ta bashi, a haka suka ciyar da juna cike da salon k'auna.

D'auke plate d'in yayi yakai kitchen ita kuma toilet ta shiga tayi brush, tare da hayewa kan bed, d'akin sa ya wuce yayi brush shima sannan ya dawo d'akin ta, kashe wutar yayi yabar deep one, sannan ya bita kan bed d'in, kusa da ita ya kwanta tare da leka fuskarta, likimo tayi yasani, murmushi yayi mai sauti tare da janyota zuwa jikinsa, anan suka shige wata duniya mai wuyar fassarawa romancing juna suke ba sassautawa duk da ranta fal tsoro, kasa daurewa tayi "pls yaya i'm scared kamin a sannu" Cikin kasalalliyar murya yace "feel free baby, ba zakiji zafi ba wannan Karon and zan biki a sannu ki saki jikinki kawai"....






***************




Tun daga ranar zaman lafia ya wanzu tsakaninsu, soyayya suke kamar su cinye juna, ga kulawa da tarairaya da take samu wurinsa kamar wata sarauniya, lallai a yanzu ta k'ara yadda da ba kowa a zuciyar Abdool sai ita natane ita kad'ai, komai tare sukeyi tun daga, kullum suna manne da juna suna soyewa, datayi d'an motsi kad'an " mene ne, meya faru, unborn ne ko" duk ya rikice yana tambayan ta, haka idan hospital yake yana mak'ale da waya suna hira har dawo gida, baya jin shakkar nuna mata soyayya a gaban kowa, ko gidan Mami sukaje bayajin kunyar nuna mata k'auna da tarairayar ta, sai ita yake bari da kunya.

Tuni suka dawo da junior gurin su Inda suke nan nan dashi, Ramlah kuwa ta had'a kiba abinta ta k'ara haske, Abdool sai tsokanarta yake wai ta zama Auntynsa yanzu tunda ta fishi kiba, had'e fuska take kamar yarinya inya tsokaneta, junior kuwa saidai yayi ta dariya yace Maa ta dawo yayinya.


*****************

Sanda Iya Hari ta farfad'o ba abinda take fad'i sai "kai mini rai Jauro karka kasheni" sai tambayan ta ake meya had'a ta da Jauro, meya kaita jeji amma ba amsa sai kuka take tana rokon Jauro yayi mata rai.

Tsawon watansu uku a asibiti sannan Ard'o yace a dawo gida tun da raunukan sunyi sauki ayi maganin kariyar na gargajia, abun tausayi iya Hari duk ta jeme ta lalace dama can ya muke muna 'yan sarki, kullum cikin kuka take tana fad'in a kira mata Ramlah, idan aka tambayeta me zata mata saidai tai ta kuka tana ita dai a kawo mata Laure, Hinde kuwa likkafa taci gaba dan yanzu tabar k'auyen gaba d'aya tabi wani saurayinta birni, wai iya Hari ta dameta da doyi a gida, da yake ba'ayi mata wanka saidai a goge mata jiki kawai Wanda shima Shatu CE keyi kullum tana gidan tun safe sai dare take komawa gidanta, da yake mijinta bai da matsala, Lanti kam sai tayi sati bata zo ba kuma ko zuwan tayi saidai ta kame gefe tana mata sannu ko Inda take bata zuwa wai d'oyi takeyi, kuma a dalilin ta tasa 'yarta ta gudu saboda azabar d'oyi.

Ard'o ma zuwa yanzu tausaya mata yake sosai ganin yadda duniya ta juye da ita (hmm duniya kenan tafi bagaruwa iya jima).

Gashi har yanzu tak'i fad'ar meya kaita jeji amma yafi kyautata zaton ba Alkhairi bane, ga shanunta ya Nema ya rasa anyi juyin duniya tak'i fad'in in da ta kaisu, kullum saidai kuka daga an tambayeta, yanaso yaje Kaduna yaga Ramlah saidai ciwon Hari ya hanashi tafiya gashi sai kashin kud'i ake amma kamar ana k'ara ma ciwon tak'i ne (to dama duniya imma shakiran ce ko imma kafura 🤷🏽‍♀) Allah yasa mudace......



Manage pls








_ina cikin damuwa ina Neman Addu'arku Friends😣_












💄Meryerm Abdool💄
[10/3, 10:53 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*



*_zuwa garemu writers, ban cire kaina ba, tambayace dani shin meyasa muke rubutu? Saboda samun fans masu zugamu suna cewa muci gaba da fire zasu bimu da fetur ko kuwa munayi ne saboda gyara? Bansan abinda ke ranku ba, amma abin da na sani shine kowace kalma da muka rubuta wallahi zamuyi bayani akanta a gaban ubangijinmu gobe k'iyama, shin muna tunanin idan muka doge da yadda muke rubutu a yanzu all about romancing sex, zamu tsira kuwa? Zamu iya hujja da rubutun mu gaban mahaliccin mu? As an advice we ar not too late even now, muyi k'ok'ari mu gyara mu, nidake dasu ana sabawa ubangiji dare da rana shi kuma mai gafara ne dare da rana muddin bawa yayi tuba mai kyau, so mu taimaki kanmu muyi amfani da basirar mu ta hanyar ceton al'umma daga wata musiba ba tsunduma su a ciki ba, idan har nayi/kikayi rubutu mai amfani koda mutum daya ya karanta ya amfana dake yafi mu rubuta barna mutum dubu su yaba mana, Wanda yabon iya Inda mukayi ne shikenan, ita kuwa azabar Allah tana can tana jiranmu a madakata, Allah yasa mu gane🤦🏽‍♀banyi dan cin zarafi ga kowa ba, duka nace so wacce ta tsargu ita taso ba ruwana.🙅🏿_*



*_oh!🤦🏽‍♀ Readers kuma ga naku....meyesa kuke son halaka kanku Ku halaka wasu gaba d'aya, without u impossible, saboda Ku ake rubutun nan, amma abin haushi yanzu idan novel ba bad'ala ba wacce zata cigiyesa amma idan ana batsa to yanzu kunyi chaa akansa kuna nema ko meye amfanin haka? Bansan meke ranku ba, amma abinda na sani shine kuna da babban kamisho a halakar writer, a duk lokacin da kuka an rubuta barna kuya kamata kuyi zanga-zanga ku kauracewa littafin Ku nuna anyi ba dai2 ba, amma ina bakwayi saidai ma Ku k'ara zuga writer d'in kuna fashemata kai kuna nuna mata masu gayamata gaskiya hasada suke mata, ko meye abin hasada a cikin rubutu na online Wanda ba riba a ciki, ribar d'aya idan ka rubuta abinda wani ya amfana ka samu lada that all fa🙅🏿 wanda muke zuwa neman lada mu tashi da zunubi, wallahi Readers kuji tsoron Allah Ku sani yana kallon mu, mu duka damu daku, kuma akwai ranar had'uwarmu dashi, so better mu tuba mu gyara, Allah yasa mudace ameen👏🏽_*









    📝 *Episode* 231--235






Three months da tarewarsu lokacin cikinta na four months, aka fara bikin Nihal su Ramlah an dage sai hidima ake kullum gidan Mami take wuni sai dare Abdool ke d'aukar su, da sassafe kuma zai saukesu, kallo d'aya zakayi mata ka gane tana da ciki dan duk alamomin sun bayyana duk da bai fito ba ya boye a k'irji da hips, aiko tanashan tsiya gasu sadee wacce itama saura 2 months bikinta, Amal ma an saka mata rana ita da Ismail cousin d'in Abdool, "hmmm kuyi abinku ai dad'in ta dai duk kuna hanya kuma" sannan ta kalli Nihal "hehehe ke sisto kima daina biyesu dan saura k'iris ki jona ni" ta fad'a tana dariya harara Nihal ta aika mata ba tare datace komai ba, dan tunda satin bikin ya kama tasha jinin jikinta ganin rawan kan ya Hakeem ya sai k'aruwa yake.

 Mutanen Besse dana Argungu duk sun iso, gida Mashaa Allah ya cika sai hidima akeyi.

Abdool ya taho d'ukarsu a parlour ya had'u dasu Inna "oh ni Habiba! Kaidai ka zama bita zai-zai to wuce yau ba inda zata" wani malalacin smiling yayi.

"Imma da abin yafi haka ki fad'a na yadda, amma ba abinda zai hanata tafiya yanzu" yace yana dialing no nata ganin bata gurin.

Turo baki tayi ganin kiran nasa, dariya Sadee tayi " 'yan matan  gidan Dr majeed yadai" harara ta jefa mata tare da kai mata duka, dariya ta k'arayi harda kashe mata ido d'aya, Amal kuwa dafa tayi  "manta su sisi jeki gani ko zai barki d'in" mayafinta ta Zara kawai tana fatar Allah yasa ya barta, dan tanaso sukai k'arshen shirye-shiryen Friends day da zasuyi gobe, gashi suna tsaka da tad'i ya k'atse su.

Bata bi takan Inna dake mata tsiya ba wucewa tayi abinta harabar gidan, saman motar ta hango shi shida Junior, suna firansu, tana isowa ya diro yana mata Murmushin nan nashi mai sanyi, mayar masa martani tayi tare da tambayansa office, ansawa yayi yana tambayan ta gajian hidima da unborn.

Bud'e mata murfin yayi kamar yadda ya saba saidai a maimakon ta shiga sai rik'e murfin tayi tana kallonsa da pity face "pls Yaya one favour?"

Ido ya zuba mata "oya said it all ears?" 

"Um... dan Allah ka barmu mu kwana anan yau kaga bamu gama tsara event d'in gobe ba ka taho" junior jin me ta fad'a yasa yayi tsalle "Yawwa Maa nima inaso mu kwana gidan Mami"

Harara ya watsa ma Junior tuni yayi tsit sannan ya lafe a jikinta, ido kawai ya zuba mata baice komai ba,

"Pls Yaya yau d'aya, kafa junior ma naso"

"Aa baby nida unborn bamaso" ya fad'a da tana shafa cikinta, duk da ranta yaso ta tsaya amma ba yadda zatayi tunda har yace Aa to ta hak'ura dan basu saba musu ba, kuma tasan yana bata dama sosai to bai kamata ta shiga hakkinsa ba.

Fuskarta ba yabo ba  fallasa tace "shikenan bari in d'auko jakata" 

Shan gabanta yayi "fushi baby.. Pls sorry banyi dan in bata ranki ba, kinsan bazan iya barin ki a wani gun ba ni kuma ina wani gu har tsawon kwana inba da lalura ba" ganin yadda ya marairaice mata, yasa ta saki fuskar hadda murmushi "am OK Yaya jaka kawai zan d'auko I understand u".

Duk da haka bai barta taje ba wai kada ta wahala sai Nihal ya kira yace ta bawa Abduljabbar ya kawo musu, ita dai sai kallonsa take wannan k'auna da Yaya ke mata anya ana yiwa wata mace irinta ko(saini akewa irinta lol)

Haka akayi bikin Nihal aka gama ta tare gidan Masoyinta dake unguwar dosa, shima cikin hospital d'in Abdool yayi nasa ginin dan shima anan zai zauna, inda hakan yaiwa Ramlah dad'i sosai sisto ta dawo kusa da ita, sun bar Mami da kewa yanzu daga ita sai su Husna.

Kullum idan mazajensu sun fita zasu had'u gidan d'aya suyi ta firarsu girki ma tare sukeyi, saidai kawai wacce ba gidanta akayi ba ta zuba a flask ta kai nata gidan basu zasu rabu ba sai dare dan bacci dan ko mazajen sun dawo saidai su zauna a yi dasu, da yake har yanzu ba'ayi lunch d'in bud'e hospital d'in ta Abdool ba.

Burin abokan ya cika na zama guri d'aya da iyalansu Wanda tun suna school suke da wannan burin, junior kam ya zama d'an gata kowa nan nan ake dashi shalelen paa da Maa da Aunty da Uncle.




***********



Lokacin da Abdool yayi mata scanning ya k'asa gane abinda ke cikin ya d'unk'ule guri d'aya, amma nauyinsa da girmansa yafi k'arfin watannin sa Wanda hakan ba k'aramin d'aga masa hankali yayi ba, saidai dole ya b'oye dan gudun tayar mata da hankali, searching ya shiga nan ya gane akwai twins masu dunk'ulewa su zama d'aya inda camera ba zata iya rabe su sai a d'auka d'aya ne, nan hankali yad'an kwanta yana jin farinciki idan suka kasance twins  saidai yana tausaya mata haihuwar fari ga, amma ai yana nan zai bata dukkan kulawar da ta dace.

Cikinta na 6months akayi bikin sadee da uncle Lukman d'in ta, zuwa yanzu cikin Ramlah ya fito sosai duk kibar da tayi ta rage, ga nauyi tsiya da cikin ke mata dak'ar tayi performance a bikin Sadee, Abdool ma dan yasan matsayin Sadee ne a gurinta da irin kulawarta garesu da bazai barta taje mata ba.

Mami ma ganin yadda cikin yayi ta tausaya mata saidai ganin yadda Abdool ke bata kulawa ga kuma Nihal kusa yasa hankalinta kantawa saidai duk da haka duk bayan kwana biyu tana zagayo su.

Ard'o ma dayazo ganin halin da take ciki yasa yak'i gayamata ciwon Hari, duk da ciwon nata ba sauk'i kullum sai k'aruwa yake, ga kullum kuka take tana kiran a kawo mata Ramlah.........







_kuyi hakuri dani dai na shiga busy ne anyi mana haihuwa ga lafia bata isheni ba, satinnan dai sai a slow pls ayi hakuri dani #one love# 😍😘_








💄Meryerm Abdool💄
[10/10, 5:46 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*






```An karb'o daga d'an Umar Allah ya yadda dasu yace "manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a garesa yana cewa :- 
                 An umarceni in da in yak'i mutane har sai sun yarda babu abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma sun yadda annabi Muhammad manzon Allah ne, su tsaida sallah su bayar da zakka, idan suka aikata haka toku tayani kare jininsu da dukiyarsu, kada a tab'a mutuncinsu sai tare da wani hakkin musulunci, hisabinsu yana a gurin Allah mad'aukakin sarki.```

*Bukhari da Muslim suka ruwaito shi(arba'una hadith)*👌🏻



❤my parrot Hafsat M(rayuwar Aurena na fire aci gaba da gashi😜) love dear thanks 4 d care👌🏻i really appreciate😍

My name sake i really miss u sweetheart😪 Maryam Y zango❤

My neighbour Zee Yabour ina cigiyarki dear kin buya😫

Am back a gain my half my true friends thanks for d care😘😘😘


Ina yabawa da readers masu bibiyar rubutu na musamman masu ganin kuskure suyi gyara heart dearies aci gaba da gyara mana kuskure a duk Inda aka hangoshi zamu gyara inshaa Allah😘😘😘😘#one love #








      📝 *Episode* 236--240












Kwanaki biyu Ard'o yayi ya koma bayan ya cikawa Ramlah galan da rubutu yace tana sha tana shafawa a jiki kullum safe da marece, kamar ko yaushe tsaraba sosai akayi masa, Ramlah ji take kamar ta bishi saidai ba daman haka duk da ya gayamata ko lafia yake jikinta na bata ba lafia, ga yawan mafarkin iya Hari da take a cikin mawuyacin hali, tanaso taje gareta dan komai tayi mata a rayuwa ba zata k'ita ba tunda tana sonta kuma tana mata fatar gane gaskiya.

Sanda ya koma ya isko ciwon Hari yayi tsanani ga wani wari da k'afar ke fitar wa hakan ya tilasta su komawa hospital, Shatu itama duk ta jeme itama yanzu har bacci gunta takeyi, saboda tausayin halin da take ciki, Lanti kam mijinta yace duk ta k'ara zuwa gidan a bakin aurenta, dama mai neman kuka an jefesa da kashin awaki Mike kafarta tayi dama ta gaji da zuwa gidan, ga Hinde ba labari ta shige duniya saidai tana yi musu sak'o hakan yasa basu damu da sai tazo ba, ita kuma tana can ta zama rijiyar kowa itadai muradi ta samu shegun(Allah ya shirya muna zuria).



****************



Zaune take tayi nisa cikin tunani, fitowa yayi cikin shirinsa na fita hospital cikin suit dark blue sai k'amshi yake zubawa kamar yayi b'arin perfume, sumarsa se sheki take, ga man pride nasa yasha gyara sai kyalli yake(ni kuma nace kai wannan da mace ne da anga iyayi, anya Dr zai tsufa kuwa kullum gashinan d'an chas dashi kamar d'an 20, shiyasa Hafsat da Ayshat suka nace a kansa shi kuma yace ba wata daga 'yar Baffa) lol.

Da saurinsa ya isa gareta tare da hure mata ido, sauke numfashi tayi tare dayi mishi smiling, bata fuska yayi "baby ba zaki daina ba ko koso kike nima nawa jinin ya hau ne?" Ya fad'a tare da kafeta da mayun idonsa.

"Sorry my half bafa tunani nake ba, koma tunani ai saidai inyi naka kawai" ta fad'a cikin shagwab'a tana shafa man pride nasa.

"Uh um Baby kada kiyi kalya fa kin san son naki yake Ba kyau, pls ki dena baby it will effect u and unborn too"

Dariya tayi "um my son Ana can anayi ma Mami rigima nasan".

Lakuce mata hanci yayi " ai wannan son naki ke kad'ai ke iyawa da kayanki Mami kam zanesa kawai zatayi".

"Ai duk Kaine ka b'atamin yaro da rigimarka" tace cike da tsokana.

Zaro ido yayi "Zainab dai" yace tare da harararta cikin sigar wasa.

"Ba ruwan Aunty Zee, Mami ma take ka fisa rigima da kake kamarsa ai sun sha fama itada Aunty Asma'u" dungure mata kai yayi "Allah sarki Aunty nah ta kaina" sannan ya harareta "Ku jimun yarinyar nan wai ta girma itama to koma dai meye nine yayanki" dariya ya bata yadda yayi maganar kamar wani Junior.

"Hhhhhh Yaya wlh bakaji" ta fad'a tana ci gaba da dariya tsura mata ido yayi yana kallon ta ko kiftawa bayayi hadda aza hannu a haba, sai da tayi mai isarta sannan ta tsagaita kallon tayi tare da d'aga masa gira alaman kallon fa.

Smiling yayi tare da rungumeta tsam yana kissing gefen wuyanta " I always love u baby I always wanna see u in happy baby, keep being like that baby love more and much in every second of my life ur love is uncountable" itama k'ara hugging nasa tayi tare da lumshe ido tana jin dad'in maganganunsa dan tasan daga zuciyarsa suke fitowa "love u too my half ur my everything ur my life soulmate" tace idonta lumshe tana shakar k'amshinsa mai sanyaya zuciya.

"Yaya time na tafia kada ka makara fa, nima zan shiga na duba sister dan tun jiya bataji dad'i ba" tace tana duba watch d'in hannunta "kodai itama tabi layinki ne?" Yace ba tare daya d'ago

"To muje kaji daga bakinta" harara ya watsa mata "kinfa renani yarinyar nan" 'yar dariya tayi ba tare da tace komai ba

Zamewa yayi daga jikinta tare da mik'ar da ita tare da saka mata hijab d'in ta, kallon ta yayi tayi kyau cikin atamfar ta red & milk, hijab milk slipper ne a kafanta milk suma batayi kwalliya ba powder kawai ta shafa sai lip gloss, tayi kyau ga cikinta yayi tutsu  a gaba kamar wacce zata haihu yanzu, light kiss yayi mata a lip "u look like take away, kodai na fasa fitane?" 

Smiling tayi "banason fitina ni Muje don Allah" shima smiling yayi sannan suka fice, a parlour suka samu Hakeem ya tasa Nihal gaba yana rarrashi sai shagwab'a take zuba mishi yana biyeta, d'aure fuska Abdool yayi bayan sun gaisa "meye wannan sakarcin kukeyi anan, ke hala yarinya ce kike wani narkewa" yace yana kallon Nihal, k'asa tayi da Kanta tare da nutsuwa dan har yanzu tsoron Abdool take.

"Ha'ah malam ya haka? Haka kawai zakazo ka takuramin mata ko lafia bata isheta ba, Aa nifa in ba jinya kazo ba kama kanka kawai banason takura haba" Hakeem yace yana watsa mishi harara.

Tsaki Abdool yayi "to me mata ni kaga tafiyata" yace tare da ficewa, binsa da kallo Ramlah tayi "kai ya Abdool rigima ko meye nasa na muzurai haka? Shegen son girma" tace a ranta.

Rarrashin Nihal Hakeem yayi sannan ya fita yana fad'in ya bawa Ramlah amana kafin ya dawo dariya tayi tace to zata yi iya k'ok'arin ta, a mota ya samu mutumin nasa yana ta cika da batsewa shi dariya ya basa wlh wai talle kema Audi gori, nan zukayi rikicinsu sannan aka dawo normal da yake kar tasan kar.

Bayan Sun wuce ne Ramlah tace "anya sisto kodai-kodai" tana dariya.

"Um bafa komai sisto Malaria ce" tace tana dariya, itama dariya tayi "gara da kika ba kanki dariya, indai ta ruba maji d'oyi....."




****************


Cikin Ramlah ya shiga wata tara ga Nihal na fama da laulayi hakan yasa dole Abdool ya d'auki Hutu shike mata komai zama dak'ar tashi dak'ar cikin kuwa yayi wani irin girma kamar ba cikin fari ba, sau hudu Abdool nayi mata scanning amma ya kasa gane komai dan abu d'aya yake gani saidai girmansa yafi k'arfin na yaro d'aya, ya shiga damuwa sosai kullum tunanin haihuwar yake ga tausayinta daya addabesa, itama duk da akwai kuruciya tana shiga damuwa akan nauyin cikin yayi mata over itakam bata tab'a ganin ciki mai girman nata ba, ga bacci dak'ar takeyi kullum cikin Addu'a suke, Mami ma tanayi musu sosai, tuni ta maida junior gurin ta, kullum saita kirata yatakejin jikinta? Idan taji ba dai2 ba ta fad'a kada tayi shiru fa? Kusan kullum hakane.


Yauma dak'ar ta samu tayi bacci, can cikin baccinta taji kamar an mintsile ta, a Mara Aa Abu kamar wasa sai gaba yake juyi ta farayi tana laluben Abdool, tana kiransa.

Abdool dake kan sallaya yana sallah kamar yadda ya saba, mafi yawan Addu'ar sa a yanzu bata wuce fatar Allah ya sauketa lafia ba, anyi sa'a yana raka'ar k'arshe.

Yana sallamewa ya isa gareta cikin rud'ewa "baby menene haihuwar ce? Ya tambayeta yana dubata, girgiza masa kai tayi cikin jin zafi " Yaya marata bayana zasu balle Yaya zafi, wayyo Yaya" dak'ar ya samu ya tattaro nutsuwarsa ya shiga dubata haihuwa ce amma tana da d'an nisa,

Wayarsa ya ciro ya kira Dr ma'aruf da Dr  Zaid sannan Dr Sharhabila, suna ganin kiransa sun San kwanan zancen dan ya gaya musu a hospital d'in sa yakeso matarsa ta haihu, dan haka su zama cikin shiri da lokacin yayi zaiyi invite nasu, Hakeem ya kira shima yana ganin kiran ko Nihal bai tayar ba ya fito a filin gidan ya samesu ya riketa suna zagayawa.

Key ya bashi na hospital d'in yace ya bud'e da musu, ba dadewa saiga Drs d'in sun iso, zuwa lokacin ko tafiya bata iyayi sai nishi kawai take, Abdool duk yayi kalar tausayi, Dr Sharhabila ce ta shiga bata taimako amma shiru ba labari, fitowa tayi duk ta had'a gumi, gogewa tayi tare da kallon su duk sun zuba mata ido.

"A gaskiya tana shan wuya and as u we know babyn yayi mata girma ba zata iya haihuwar sa da Kanta ba, so inaga data jigata ko a bata lokaci azo a samu matsala better gwanda ayi masa C/S d'in kawai yanzu.

Tashin hankali k'arara a fuskar Abdool duk dama yasan da maganar amma kuma ya kasa jurewa gani yake itama tafiya zatayi kamar Zainab, aiko idan hakan ta faru yasan yayi bankwana da farinciki, saurin kawar da tunanin yayi dan baya fatan hakan ta kasance.

Dr Ma'aruf ne ya dafa sa " karka karaya Abokina don't forget ur a Dr kasan komai game da irin wannan just be strong, inshaa Allah zamuyi nasara" haka dai sukeyi ta bashi baki har ya samu courage sannan sukeyi shirin shiga theatre.

Hakeem ne ya kira Mami, yana gayamata ko magana basu k'are ba ta katse wayar, cikin gaggawa tayima maid bayani abinda ake ciki sannan ta dauki motarta ta fito, duk da gab da asuba ba hakan bai hanata fitowa ba.

Sun shirya tsaf Dr Sharhabila ta shirya Ramlah yana fitowa da ita akan be zuwa theatre room, ganin halin da take ciki na shan wuya yasa Abdool zubar da hawaye zuciyarsa ta karye, hannunta ya kama, murmushin k'arfin hali tayi masa "Yaya ka dena kuka pls kayimin Addu'a kaji, pls ka yafemin koda ban tashi ba ka kula da son da babyn da zan haifa idan Allah ya rayashi, pls Yaya kada kayi kuka"

Maganganun ta suna kama dana Zee kaddai itama ban kwana take masa, jikinsa sanyi yayi k'alau, kasa shiga theatre room d'in yayi, ba yadda basuyi dashi ba, yak'i dole suka wuce suka barshi nan, jin yayi duniya ta masa zafi gaba d'aya.

Motarsa ya d'auka ya fice daga hospital d'in gaba d'aya, shi kansa baisan Inda ya nufa ba.

Shigarsu ba dad'ewa Mami ta iso ana kiraye-kirayen Asuba, gidan Nihal ta wuce anan tayi sallah sannan sai lokacin Nihal taji meke faruwa nan hankalinta ya tashi sosai bayan sun yi Sallah suka isa cikin hospital d'in.

Ba abin take maimaitawa sai Addu'ar nan ta samun sauk'i wato *"Allahumma la sahla illah ma sahaltahum wa anta aj'alar hazna Iza shi'ita sahla"*har akayi mata allurar bacci Kalmar da ke bakinta kenan har bacci ya d'auketa.

Cikin nasara da iyawar ubangiji, cikin sauk'i sukayi nasarar ciro jarirai guda 4 daga jikinta lafiyayyu kyawawa na gaske nan fa Dr Sharhabila ta riked'e ta dawo unguzoma cikin k'ank'anin lokaci ta gyarasu tsaf cikin lallausan over roll kowa da kalar nasa, sai santin yaran Drs keyi kowannensu rige-rigen kiran Dr Abdool yake saidai wayoyinsa duk a kashe hakan suka hak'ura da kiransa suka maida Ramlah d'akin Hutu.

Dawowar Hakeem daga masallaci yayi dai2 da isowar su Mami nan suka had'u suka shiga a tare, Wanda yayi dai da Dr Sharhabila ya turo yaran a cikin d'an bed irin na kids dake asibitin dan Hospital d'in ba k'arya taji kayan aiki designers, rige-rigen isa gurinsu su Mami sukayi mamaki da farinciki ya Hana su magana, sai murmushin farinciki sukeyi suka shiga santin yaran daketa bacci maza 2 mata 2, lallai Allah mai iko fidda rai cikin rai sai Allah, ya b'oye sanin sa da baiwarsa a cikinta ya dungule kamar d'aya Ashe har had'u ne.

Drs ne suka fito suma fuskokinsu d'auke  da farinciki barka sulayima su Mami sannan suka wuce masjed dan gabatar da Sallah.

Gurin Ramlah sukaje suka dubata har yanzu bata tashi ba, gida Nihal ta koma tare da Dr Sharhabila don tayi sallah ita kuma ta had'a musu kari, akabar Mami da Hakeem a nan.

Mami ganin har su Dr, ma'aruf sun dawo ba Dr Abdool yasa ta tambayesa nan suka ce sun d'auka ma ita yaje d'akkowa dan tun da ya fita bai dawo ba kuma ga wayoyinsa duk a kashe..

Abdool kuwa tunda ya fita baima San ina ya dosa ba tafiya kawai yake, jin ana kiran sallah ne ya cilasta masa tsayawa a wani masallaci ya shiga yayi sallah, anan yayi sallarsa ya duk'ufa da Addu'ar samun sauk'i da nasara ga Ramlah, saida haske ya fito sannan ya fito daga masallacin, hankalinsa ne ya koma a yaje yaga ya ake ciki, tunda duk ya kashe wayoyinsa bale a kirasa hakan yasa ya shiga motarsa baisan yayi nisa da hospital ba saida yaga unguwar da yake, hakan yasa ya shiga sharara gudu dan Ramlah kawai yakeson gani a yanzu.........




_every body shoki 'yan 4 sun iso_ 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💋 






@ABDRAM TEAM###😍
[10/12, 6:29 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*


*_An karb'o daga Abu huraira Allah ya yarda dashi yace" manzon Allah (S.A.W) yace :- kalmomi biyu masu sauk'in fad'a a harshe, masu nauyaya mizani, mafi soyuwa a gurin ubangiji sune, subhanallahi wabihamdihi subhanallahil azeem_* 👌🏻

(Husnul Muslim)




_gareku k'awayen kirki, alkhairin Allah ya riskeku aduk inda kuke, kuna raina koda kuwa munyi nisa da juna😥 Maryam warah, maryam D/gari, Maleeka auta, Sakina mungadi, fareeda sama'ila, Auntynah Dija #double love my boo😍😘_








       📝 *Episode* 241--245






Kicib'is sukayi da Mami a reception, harara Mami ta watsa masa "ina ka shiga ne? Kuma duk wayoyinka a Kashe tsabar renin wayo"

K'eyarsa ya shafo da hannunsa, har yanzu hankalinsa a tashe yake, amma ganin Mami cikin normal mode, yasa hankalinsa yadan kwanta "yi hak'uri Mami wlh hankali nane ya tashi shiyasa na kashe wayoyin, Ramlah fa Mami ta sauka?"

"Tana ciki" ta ansa mishi a tak'aice, tare da wucewa abinda, yasan fushi take dashi shiyasa tak'i kulashi, da sauri yayi gaba da Dr Ma'aruf yaci karo "Dr Abdool where have u been? And urs phones is off?"

"Hmmm am not in mood that time, have u successful C/S??" Ya fad'a yana zuba masa ido.

Fad'ad'a murmushin fuskarsa yayi "congrat my friends ur wife and d baby's are in good conditions"
         Wani gauron numfashi ya sauke tare da Rumgesa hadda d'an kwallar farinciki bakinsa d'auke da hamdala da godiyar ubangiji "nagode sosai abokina Allah yabar zumunci, ina take yanzu?"

Kafin ya bashi amsa su Dr Sharhabila suka iso tare jariran, ware ido sosai yayi yana kallon baby's d'in sannan ya kalli Dr Sharhabila baki sake.

Murmushi tayi "all is urs Dr" ta fad'a, anan ya zube yana sujudush shukur, Bakin bed d'in ya tsaya tare da zubawa yaran ido sai motsi suke a hankali alaman suna son tashi "lallai Allah mai girma shi keyi a inda yaso kuma ga Wanda yaso a lokacin da yaso ba tare da karfi ko dabara ba, Allah na gode maka da wannan babbar kyautar da kayi mana" ya fad'a a ransa, nan su Dr Sharhabila suka shiga tayashi murna, shima godiya yayi musu sannan yayi ma yaran Addu'a kamar yadda akewa kowane jariri na musulmi a koyarwar manzon rahama tare da yi musu Addu'a.

Dr Sharhabila ce tace ya kamata Ramlah ta farfad'o yanzu, d'akin da take yaje da sauri dan ganin ta kawai yafiso a yanzu, shigarsa tayi dai2 da fara motsinta, da sauri ya isa gareta tare da yanyota zuwa jikinsa yana kallon ta, sannu a hankali ta fara bud'e idonta fes idonta ya sauka a kansa yana mata murmushi, lumshe idon tayi tare da k'ara bud'e su, a tunanin mafarki take, shidin dai ne to amma meya kawo wannan sabon gurin? Sannu kwakwalwarta ta tariyo mata abinda ya faru, hannunta takai kan cikinta jin sakayau ga zafi da taji a gurin ya sakata fara k'okarin tashi.
      Maida ita yayi tare da shafa mata kai yana mata magana a kunne wacce nidai Meryerm Abdool banji me yake cewa ba, ganin nai ta lumshe ido tana murmushi (nace to harkin manta kenan da zafin).

Turo k'ofa akayi Dr Sharhabila ce ta shigo tana murmushi "sannu Madam kin farfad'o sannu ya kikejin yanayin jikin yanzu?" Tace tana gyara bed d'in na babys data shigo dasu dai2 gadon nasu.

Cikin siriyar murya tace "Alhmdllh da sauk'i" ba tare data bud'e ido "baby tashi kiga yaran ki" Abdool ya rad'a mata a kunne.

D'an bud'e ido tayi ganin yara har 4 yasa ta zaro ido ta kallesu dakyau sannan ta maida kallon ta gareshi mai cike da tambaya, lumshe ido yayi tare da smiling, ya Dora hannunsa kan k'irjinsa ya rungume hannayen nasa sannan girgiza mata kai alamar eh.

Murmushi Dr Sharhabila tayi tare da ficewa tana fad'in "wishing u spreed and quick recovery" sun burgeta matuk'a.

"Bansan me zance maki ba baby nagode sosai da wannan kyautar mai girma"

"Yaya ya zanyi dasu sunyimin yawa"
         Smiling yayi "baby zaki iya Allah bazai dorawa rayuwa abinda yafi k'arfin ta ba, Ki kwantar da hankalinki inshaa Allah zaki iya kinji" 

Girgiza kai tayi alaman to sannan tace Cikin sanyi" Yaya haihuwa da zafi bazan k'ara ba" dariya mai sauti yayi "haba baby nah kefa jaruma ce, nida ke tunanin next year ki bani wasu 4" yace cike da tsokana, zaro ido tayi tare da kwab'e fuska zatayi kuka "oh sowie jarumata wasa nake fa" yace yana mata dariya ransa fal farinciki tsantsa.

Ba dad'ewa su Mami tare da nihal suka dawo da abun karyawa, suka karya sannan suka kintsa aka wuce da ita hospital d'in su Abdool dama burinsa kawai Ramlah ta haihu a hospital d'in sa, admitting nata akayi nan fa akaci gaba da bata kulawa ta musamman ita da yaranta.



***********



Tuni asibiti ta cika da 'yan barka su Sadee har an kawo jiki sai yaba kyawun baby's d'in kowa keyi gasu manya ba laifi kamar d'aya d'aya, biyu sukayi kamannin uwa fatar uba, biyun kamannin uba fatar uwa.

Lokacin da junior yaga yaran washe baki yayi yana kallon su ya tab'i wannan ya yayi ma wannan kiss yayi wannan wasu duk ya rud'e yace "Maa duk nawa ne?" Smiling tayi masa Mami tace "duk naka ne beran masar saura ka koya musu bannar da rashin jin" dariya kawai yace yaga yaran da yafi girma shima ya zama babba.
 
Mutan Argungu ma sun iso jin wannan babbar kyautar wannan karon hadda Baba, Ard'o kam jikin Hari ya hanashi zuwa sai lokacin ya gayamusu halin da take ciki Mami ta janjanta sosai tace inshaa zasuzo bayan suna, Ramlah kam hadda hawayenta Ashe shiyasa tayi ta mafarkinta Ashe da gaske tana cikin mawuyacin hali fatar samun sauk'i tayi mata, Abdool ma ya jinjina al'amarin.

Alh Sada ma yazo yaga 'ya'yan nasa tare da basu kyauta mai tsoka, su Amal duk sun zo sai tarairayar yaran ake feeding kawai ke had'a su da Ramlah, Nihal, sadee, Amal kullum asibiti suke wuni sai dare ga kuma nurses masu kula dasu na musamman, ga uban gayyar shima yana kusa, satinsu d'aya aka sallamesu.

Abdool an gyara gida a tunanin sa can zasu wuce sai jin yayi Mami tace gidanta zasu nuna ba halin musawa duk da ransa baiso ba, dan har yanzu Mami bata huce dashi a ganin ai wauta ce ba rudu ba.

Nihal sai kullum suna gidan Mami sai dare Hakeem ke zuwa ya d'auketa da sassafe ya sauketa Sadee ma hakan ce, nan fa Ramlah ta samu bakinta sai tsiya take zuba musu don kowacce na d'auke da cikinta sai kwad'ayi suke zubawa Amal ma an kusa amarcewa.

Inna da Mami sun dage da gyaran Ramlah gyara na musamman irin na 'yan Sokoto Ard'o ma ya Aiko da sako, Abdool ko gida bayason komawa saboda gidan ba dad'i, yasan ko yace ya dawo Mami ba zata bari ba sai wani kaffa-kaffa take da Ramlah Sam bata barinsa zama gurinta.

Ranar suna anyi shagali wai barinyi shiru dai amma kuma dai kunsan ba dama Sa biyu da rago shida aka yanka, kaya kuwa kamar wani mahaukaci kowane jariri da nashi set, itama mai jego tasha kaya hadda kyautar mota k'arama irin ta mata k'irar Mercedes ash color.

Biki yayi biki can na hango 'yan *Abdulmajid fans* a gaban kasko my parrot an tattare zani ana gyaran hanji, mom zee sai k'ok'arin gyara wuta tace Aysha na zuba mai a kasko maman khady sai yankan nama ake ana aikawa baki anga banza ta fad'i, lubna ba sauk'i anata shan fanta, dear na Raheenat sai cin rengem ake ana korawa da coke su maman Nana, Aziza, zuzu, zee mai Kano, maryam cool sai hadije yawu ake anji hanji ya fara k'amshi, nace oh Abdulmajid fans kwad'ayi  sun kama hanji sai aiki suke masa ba sassauta to kudai ragewa dotana kada Ku cinye gaba d'aya. Lol.

Yara sunci *Abdullah, Abdurrahman, Amatullah, Amaturrahman* Allah ya raya akan sunnah yasa mahaddata Qur'an ne.

Dangi kowa ya taka rawar gani yayi bajinta sun suna 'yan hud'u 'yan gatane gaba da baya, anyi suna lafia an watse lafia, Allah ya raya yaba mai jego lafiar shayarwa...........







*Remgem ren gemgem shinkafa da dad'i wlh tanada dad'i* 💃🏻💃🏻😋😜








💄Meryerm Abdool💄
[10/13, 9:20 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*







*_Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a garesa yana cewa "ba zaku shiga aljannah ba har sai kunyi imani, ba zakuyi imani ba harsai kunso junanku, in baku labarin ta yaya zakuso junanku? To Ku yad'a sallama a tsakaninku_*👌🏻

*_Assalamu Alaikum warahmatullah wa barakatuhu ya ihwatih fil Islam* 🙋🏾









      📝 *Episode* 246--250






Abdool ya shiga busy saboda shirye-shiryen bud'e hospital nasa da sukeyi bai zaunu ba, wata rana ma through out day su Ramlah ba zasu ganshi ba saidai waya kawai, Mami kam ta dage da gyara 'yar tata,tuni na hau sheki fatarta tayi smooth tayi k'iba abinta, yan 4 sunyi bulbul dasu a dan Ramlah akwai kyawun Mama ga kuma sinadarai da madara da Abdool ya kawo musu wand'anda zasu k'ara musu lafia da kuzari, junior kullum yana mak'ale da Maa d'insa, Inna da Nany ne iyayen renon su Amatullah su Husna ma muddin suna gida suma suna tare dasu.

Bukin bud'e hospital aka gudanar Inda ya samu halartar mai girma governor na Kaduna State da k'ungiyar likitoci ta kaduna state misnistan lafia, asibitin ta samu karbesu gun k'usosin Gwannati, sannan ta cika duk wasu sharudda na asibiti mai zaman kanta, duba da yadda aka zuba kayan aiki na zamani wad'anda a yanzu ba'a cika samun a kowacce hospitals ba, an nashi number yabo tare da jinjina masa akan namijin k'ok'arin da yayi akan hospital d'in tare da jawabin yabo da mai girma governor yayi tare da Jan hankali up coming Dr dayin koyi da Matashin Dr Inda yace idan ana samun iri-irensu masu kishin k'asa to tabbas za'ayi nasara sosai a fannin lafia kuma za'a yak'i cututtuka da dama tun anan gida Nigeria basai an fita zuwa k'asashen wasu ba, haka dai kowa ya tofa albarkacin bakinsa tare da mik'a kambun girma ga iyayensa a matsayin su na wad'anda suka ginashi suka tallafa masa ta hanyar taimakonsa da bashi ilimi mai kyau har yakai wannan mataki, Aka kuma ja hankali iyaye akan suyi koyi da iyayen Dr Abdool su dage akan ilimin 'ya'yansu both islam and western dan shine kad'ai gatan da zakayi ma d'an ka a rayuwa saboda ilimi shine gishirin zaman duniya.

Mami dake gefe sai murmushi take tana jin dad'in ganin wannan rana da Allah ya nuna musu Abdool ya zama wani Abu a rayuwa har ana buga misali dashi wannan kad'ai ya isheta farinciki, Alhaji Sada hadda kwallarsa ta farinciki ina ma Auwal na kusa yaga wannan abin farinciki, Ramlah ma ji take kamar ta tashi sama dan farinciki tanaji tafi kowa sa'ar miji a rayuwa, ganin yan mata sai pics sukema Abdool yasa tasha kunu ta had'a rai ganin my parrot ta dage ta zak'alk'ale ita da my Aysha, Abdool kuwa idonsa na Kanta ganin yadda tasha kunu yasan labarin yasa sai jifarta da murmushi yake sannan yak'i kula kowa duk nacin Hafsi saida ta sarara masa, dan yak'i basu fuska, wow kawai 'yan matan gurin ke fad'i sunaji inama wannan young Dr mallakinsu ne.

Gurin dinner da akaje Ramlah na mak'ale Dr ko kunyar Mami bataji idonta ya rufe da kishi, sunkuyawa Abdool yayi Dai2 kunnenta "Haba baby irin wannan rikon ai sai ki kashemin kasuwa" harara ta watsa masa tare da kwab'e fuska tana d'an dukan k'irjinsa cike da tab'ara, nan fa masu camera suka shiga basu pics dan sun burge ba kad'an ba wasu sai fad'i suke "wow perfect match" tuni jikin wasu yayi sanyi  ganin madarar k'auna a fili, Mami sai murmushi take tana k'ara godewa Allah, su sadee, Nihal duk ana gurin ana aikin na kwad'ayi. Lol

Taron yayi perfect anan aka bashi lasisi na tabbacin Asibitin sa ta samu k'arbuwa 100%, taro ya watse kowa na farinciki da murna, Abdulmajid fans baki kamar ya yage dan murna sun cika burgamensu da kayan mak'ulashe(oh wad'anda mutanen burinsu baza ta fad'i kawai subi takai) lol.



***************





Watan su Ramlah d'aya Abdool ya fara k'orafin su dawo, gaba Mami ta saka shi ta mishi tass tace suda komawa sai sun k'ara 2 months kuma da ta k'are wanka zasuje can kilgori suga halin da ake ciki dan baffa ne da kansa ya buk'aci haka, Ba yadda ya iya Ya hak'ura saidai idan Mami batanan yakan zagaya gurin Ramlah tayi masa 'yan dubaru dan tasan kalar mijin nata, duk iya nacin sa bata yadda anje can.....ba, kullum da rigima suke rabuwa dan idan ya aza mata daru ji take kamar ta bashi ta huta amma idan ta tuna da gargad'in Mami saita fasa, fushi yahau da ita ya daina kulata iyakarsa parlour idan yazo ya nan yake zama da yaran sa, haka yai fushin har ya gaji, lokacin ne tafiyarsu ta tashi gashi yayi dai2 da auren Amal kwanansu 3 a Sokoto suka sha biki sannan suka wuce kilgori...



*************



Tunda suka shigo cikin garin take binsa da kallo tsawon shekarun da ta d'auka bata ba a samu wani dogon canji a ciki ba kusan ma yananan yadda yake saidai abinda ba'a rasa ba, tsayuwar su k'ofar gidan ne ya k'ara tsananta bugun k'irjinta da Ard'o sukaci k'aro a k'ofar gidan, washe baki yayi yana musu sannan da isowa sannan yayi musu jagora zuwa ciki.

Gidan ma na nan yadda yake ba canji, k'ark'ashin bishiyar tsakar gidan ta hango Gwaggo Shatu tana yima wacce ke kwance jagab an lullub'e kusan rabin jikinta basa hango fuskarta, mahucin Shatu ta aje tare da tasowa tana musu sannu da zuwa fusksrta cike da tambaya dan itakam bata ganesu ba "sannu Gwaggo mun sameku lafia?" Ramlah tace, bud'e baki Shatu tayi tare da nunata da yatsa "Laure keta? Keta(kece) kika bacemin gaba dai ban ganeki ba" tace tana rungumeta "nice Gwaggo ya bayan rabuwa yasu Salmanu sun girma ko?" Tace suna k'arasawa gindin bishiyar da sauri Shatu ta d'auko sabuwar tabarma ta shimfid'a musu tare da kawo musu ruwan Randa masu sanyi "su Salmanu sun zama samari, wad'annan ne jikokin nawa?" Tace tana zama tare da k'ara gaisawa dasu Mami da inna da Nihal sai kuma nany, dake inna bata koma ba sai yanzu ta biyosu su daga nan su isa can.

Murmushi kawai Ramlah tayi, sai Mami ce ta amsa mata sannan tace "ya mai jikin ko tana ciki ne" dan Sam bata kula da ita ba.

"To alhmdllh ta samu sauk'i, ai gatanan ta samu yin bacci" tace tare da nuna musu ita, idon Ramlah ne ya sauka kan Iya Hari dake kwance kamar tsumma duk da dama can bamai jiki bace amma kam ta k'ara lalacewa ta yankwane ta tsofe sosai, nan take zuciyarta ta tsinke cikin sasarfa ta isa gareta tare da sakin kuka Mara sauti ta d'ora hannunta kan nata, rike hannun tayi gam tana fad'in "Laure ce dan Allah ku kawo min Laure mu gana"cikin muryan tsananin ciwo, cikin tausayawa tace "Iya nice...nice Laure iya" da sauri Iya Hari ta bud'e idonta tana son tashi amma ina ba dama.

Rik'e ta sosai tayi tare da gyara filo ta d'agota, still tana rik'e da hannunta gam "Laure kega yadda Allah ya hitar miki hakkinki gareni ko? Kega yadda nik koma  ko?" Tace tana yaye zanin da ke rufe a jikinta, wani irin wari ne ya doki hancinta Ramlah ga k'afafun ba kyan gani duk sun kumbura ga tab'o a wasu guraren sai kuda ke bi.

Lokacin su Abdool suka shigo shida Ard'o da Hakeem " Laure banyi miki adalci ba keda uwayenki ban ba Modibbo hakkinsa ba na cutadda Asma'u sannan nabi ki da cuta kema gashi Allah ya nunamin iko nai...".

"Duniya kenan ka bita sannu ma ya kak k'are balle kayi garaje, kuma shi zakaran da Allah ya nuhwa da cara ko ana muzuru ko ana shaho sai yayi, wanga ya isheki darasi kisan duniya tafi bagaruwa iya jima" Ard'o ya fad'a hankali kwance.

"Wlh hakanan na Malam na yadda nabi Allah na kurena " Iya Hari tace tana kuka nan ta shiga basu labarin yadda ta cutar da Ramlah da iyayenta har zuwa zuwanta Inda boka da yadda ta had'u da Jauro ta k'ara sa "wlh sharrin shed'an na da son zucciya gashi sun kaini sun baro, Lanti da ni d'auka a matsayin d'iya gashi ta watsar dani bayan ada da ita mukayin komi ina ganin ita kanaso na bata tarbiya ta Ashe na dab'a ma cikina wuk'a na ban Sani ba gashi taje taba d'iyanta irin tarbiyar da nibbata, nidai kaico dani nayi hasara, dan Allah Laure ki taimaka ki yafemin ko zan samu sassauci daga ubangiji na" ta fad'a cikin matsanancin kuka mai ban tausayi.

Ko kai waye kaga Hari a wannan halin dole ka tausaya mata, duk ta k'ashe musu jiki, cikin sheshekar kuka Ramlah tace "ban tab'a rikeki a raina ba Iya, na yafemiki tuni, kullum babbar burina Allah yasa ki gane gaskiya, nagode wa Allah daya sa kika dawo hanya Allah ya yafe mana baki d'aya".

Cikin kuka ta shiga Neman gafarsu Inna duk sukace sun yafe sannan ta juya ga Ard'o " Hari kinyi abubuwa da dama saidai nikam ban tab'a rikeki a raina ba, kullum fatana ki gane gaskiya ko a haka aka tsaya nasan kega yadda duniya tace koda wannan azabar dake tare dake aka barki ga hasarar dukiya da kikayi Allah yasa wannan turbar shiriyarki"..

Sun jima suna jimamin abun, Abdool yana girmama abin wato ita duniya muddin kana cikinta zaka abubuwan mamaki, Al'ajabi, zalinci, cutarwa, cin amana da abun tausayi dana dariya, amma muddin bakabi hanyar koyar war Manzo S.A.W sai kayi dana sani a rayuwa, (Allah ka bamu ikon bin dai2 da aikata dai2).

Duba Hari yayi anan ya gane kafafun sun rub'e dole saidai a yankesu, nan suka k'ara shiga tashin Hankali, ana haka saiga Lanti ta shigo gidan tana ihu da kururuwa ta zube anan tana fad'a musu ga gawar Jauro nan da hinde an kawo wai ashe suna can tare birni suna bushasha da kud'in iya Hari da wad'anda Hinde ke karuwanci tana samowa shine sun samu matsala sun fito suna bala'i har bakin titi babbar mota ta kwashesu ba Wanda ya shura a cikin su.

Shine mijinta ya dankara mata kashi ya sakota saki uku yana fad'in ta cuceshi duk ita ta lalata masa d'iya, bud'ar bakin Ard'o sai cewa yayi "kega shuke- shuken ki ko Hari sai girba kikai da hannunki" fashe tayi da wani kuka mai cike da nadama, itama Lanti kukan take tana nadamar biyewa mahaifiyar tata musamman da taga yadda Allah yayi da Ramlah sai rok'on gafararta suke, tace ita bata rik'e kowa a rai ba.

Delu k'awar Ramlah tanajin labarin zuwan Ramlah tayi ma gidan Ard'o tsinke sai tayi da gaske sannan ta gane aminiyar tata "Laure keta kid dawo baturiya haka, ai in bisa hanya munka had'u aradu ban ganeki" delu ta fad'a tana zare ido.

"Kai Delu har yanzu kina nan baki canza ba ya bayan rabuwa" Nan suka shiga gaisawa da firar yaushe rabo, tana ta zuba mata godiya dan duk zuwan da Ard'o zaiyi sai bada tsaraba an kawo mata.

Anan suka kwana washe gari suka wuce Argungu Abdool yace su zama cikin shiri dan tare zasu koma ayima iya Hari Aiki dan kada k'afar ta janyo wata Marsala.......













💄Meryerm Abdool💄
[10/20, 4:55 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Real Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com* 




```An karb'o daga Baban Abdullah, Nu'umanu d'an Bashir (R.D) yace "naji Manzon Allah (S.A.W) yana cewa " hak'ik'a halal a bayyane take haka ma haram a bayyane take, saidai a tsakaninsu akwai wani al'amari mai rikitarwa Wanda kad'an daga cikin mutane suka sanshi, duk wanda ya kiyaye shubuha(rikitaccen al'amarin da ke tsakanin halal da Haram) hak'ik'a ya kiyaye addininsa da mutuncinsa, duk Wanda ya fad'a a shubuha hak'ik'a ya fad'a a haram, kamar makiyayi da yake ciwo a iyaka ya kusa ya ketare iyakarsa, Ku saurara! Kowane mai mulki yana da iyakarsa, Ku saurara! Iyakar Allah shine ababen da ya haramta, Ku saurara! A cikin jiki akwai wata tsoka idan ta gyaru dukkanin jiki ya gyaru, idan ta b'aci dukkanin jiki ya b'aci, Ku saurara! Itace ``` *zuciya*

_Bukhari da Muslim suka ruwaito shi(arba'una hadith)_


*ya Allah ka azurtamu da zuciyar musulunci* 👏🏽









      📝 *Episode* 251-255





Ziyara sukayi sosai a Argungu, gidan k'awayen Mami dana Asma'u, b'angaren Inna duk sunje, da sukaje gidan Firdausi suka had'u da Ameena sai hirar tuna baya suke, gashi yau sune iyaye hadda jikoki rayuwa kenan, yau da gobe ta wuce wasa, kullum ganin Firdausi na tunawa Ameena da Auwal, gashi shiru har yanzu ba labari ko a raye ko a mace allahu a'alam, sunje har Besse daga nan suke wuce mungadi inda Sakina, tayi farincikin ganin su sosai itama ta tara nata iyali hadda jikoki, nan suka shiga tuna baya rayuwar C'O'E barkwancin Yusuf da irin yadda yake assisting nasu, ita tasan tayi rashi Mara adadi ta rasa Auwal a karon farko tazo ta rasa Asma'u da mijinta, sai uwa uba jigon rayuwar ta Yusuf yanzu kam mutuwar iyayenta da 'ya'yanta kad'ai ne zatace batasan d'acinsa ba amma ai taga mutuwa mai shiga rai (Allah yayima dukkanin musulmi rahama ya kyautata tamu bayan tasu)


Sunje birnin lafia gurin dangin Baba, cike da kayan tsaraba kamar yadda suka saba, sai kunya da nadamar abinda sukayiwa Abubakar sukeyi dan sun san kaf dangin yanzu da bazar Abubakar suke taka wa, shi d'in da suka wulakanta gashi ya zame musu haske a family, ya zamo zakaran gwajin dafi, shiyasa ba'a yiwa d'a da dukiya k'eta dan bakasan Wanda zai amfana dashi ba, d'ana kowane.

Tuni su Inna sun tare sabon gidansu dake Shagari Quarters, ganin zamani ne irin mai kyau d'in nan Sosai fa, Wanda Ameena, Asma'u, Mansur suka had'u suka Gina, abinda yasa nasaka Asma'u saboda gadonta hadda shi aka hada akayi ginin da sunan ta, Mansur ma yanzu harka ta bud'e dan ya samu aiki a Navy, so yanzu familyn Abubakar sunfi k'arfin a kirasu talakawa, hakan baisa musu girman kai ko k'yamatar talaka ba face wata hanya ta taimako data bud'e musu dan sun dage gurin taimaka yan uwa da gajiyayyu(abinda ya yakama ta ko wane mai hali yayi kenan ba gina manyan gidaje a koma Abuja a lafe ba, dan sadaka haske ce gobe k'iyama, Allah ka wada tamu da halal ka bamu ikon ciyar dashi ga bayinka dominka ya Allah).




************





Su iya Hari an isa Kaduna cikin yardar Allah, akayi mata aiki, dan Dr Abdool yana da k'wararrun likitoci da suka shafi kowanne b'angare ga ingantattun kayan aiki, cikin nasara aka yanke k'afafun tare da yi mata na roba, aikin da ya d'aukesu sati d'aya, anyi aiki successfully, Iya Hari sai kuka take tana nadama abinda ta shuka a rayuwar ta ga Ramlah data wulakanta ta d'oketa a banza ta zamo silar samun lafiyar ta duk da tasamu ciwon ne a gurin cutar da ita amma ta yafe mata har da kuma taimaka mata, lallai d'an hakin da ka rena shike tsole naka ido, kuma hak'uri jigon rayuwa ne, gashi Ramlah tayi hak'uri da cutarwar Iya Hari a gareta gashi Allah ya d'aukaka ya bata komai da ake nema a rayuwa saidai godiya da hamdala ga ubangiji kawai da Neman gafararsa.

Duk da yanayin da suka shigo garin na tsananin ciwon iya Hari hakan bai hana su bawa idanun su hakkinsa ba lallai garin dad'i na nesa haka kawai su Shatu ke fad'i a ransu basu k'ara tsurewa da lamarin ba saida suka isa gidan Mami k'amshin nan daddad'a da furannin ke fitarwa da iskar ni'ima dake gidan as usual, nan fa a shiga bawa ido abinci, suna girmama Allah, ashe Laure tana cikin aljannar duniya, da aka kawo musu better sukaci nan santi ya tashi Anji girki.

Da sukaje asibiti nan ma k'auyenci tsabage suka baje abinsu wai asibiti kaman gidan wani sarki ba doyi ba komai sai k'amshi da sanyin A.C dake kad'asu a haka sukata baje gidadan cinsu har akayi aikin aka kammala, bayan ta warware sosai aka shiga dasu zaga gari kusan tashi zaucewa sukayi hadda su Iya Hari sai wasar baki ake kamar gonar auduga, banki, hanci, ido sai kallo suke, wuni sukayi zungur sunje malls, da parks sosai sun cire kwarkwatar ido, anci ansha.

Adan watan da sukayi sun murmure sosai musamman Shatu tayi ja sosai tayi jiki Ashe duk wahala ce ta lalata ta, sosai suke kama da Ramlah d'an kammaninta d'aya da marigayi Abdulrahim, Iya Hari ma da Lanti sun murmure abinsu sunyi kumari da haske, saidai har yanzu sun k'asa sakewa dasu Mami suna ganin kamar suna kallonsu da cutarwar da sukayi wa Laure, duk da Mami na iya k'ok'arin ta gurin jansu a jiki, itama dai Ramlah kullum tana tare dasu, su kuma sun dage da renon su Amatullah.

Watansu Ramlah 2 amma har yanzu shiru Mami tak'i bashi matarsa tun yana ma Ramlah naci har ya gaji ya saka mata ido ga gidan a cike ba damar ya samu ya keb'e da ita, ko gidan yaje yace tazo ta kawo mai Abu a d'akin sa, cewa tace ai haihuwa d'aya horon abin..ba abinda zai kai k'afarta ya sakeyi mata wani cikin, shi dariya ma ta basa wato har yanzu akwai sauran k'uruciya tattare da Ramlah, wato ma a d'akin sa ne, takeyin cikin tun da anyi na farko.

Mami ya samu da maganar komawarsu Ramlah, b'ata rai tayi ta shiga balbale sa da fad'a tace ba zata koma ba sai yaran ta sunyi k'wari tukun, ganin ta ko'ina ba nasara yasa ya shirya nashi plan, Mami kuwa bayan tafiyarsa tace ma Ramlah ta fara shirye-shiryen komawa dam tasan halin d'an nata zai iya k'ara wata tabargazar dan idanunsa sun riga da sun soye tuni, yanzu Sam baya kunyarta Indai akan Ramlah ne.

Washe gari da wuri ya shigo a parlour ya samu su iya Hari suna ta faman kallo, gasu Abdool a hannunsu, gaisawa sukayi cikin sakin fuska, sannan yayi wa su Amatu wasa da sai b'angalar baki suke suna dariya Sam basu da matsala indai tumbinsu ya d'auka, junior rik'e a hannunsa yana masa surutun nasa daya iya, tambayan Mami yayi suka gayamasa tana ciki.

Mami na zaune gefen gado tana yiwa Ramlah bayanin kayan dake hannunta ita kuwa tana tsaye gun sif  tana gyarawa Mami kayanta duk a kunyace take da bayanin da Mami ke mata, da eh kawai take binta shima can ciki ta maida hankalinta ga aikin da take.

Turo k'ofar yayi tare da sallama a bakinsa a tare suka amsa masa, zama yayi kan sofa yana gaida Mami, amsawa tayi tana tambayan sa aiki, gaidashi Ramlah tayi tana satar kallon sa dan ba k'aramin kyau yayi mata ba a Cikin k'ananan kayan da ya saka jean blue da shirt yellow mai dogon hannu an rubuta i'm d prince a gaban rigar da bakin penti sai zuba k'amshi yake.

Ko inda take bai kalla ba ya amsa gaisuwar tata ba yabo ba fallasa, shiru ne ya ratsa na d'an lokaci dan Mami ta aje kayan da takewa Ramlah bayani ta d'auko wata jarida tana dubawa, ita kuma Ramlah sai aikin gabanta take.

"Um Mami dama magana ce dani".

"ina jinka" tace a tak'aice ba tare data d'ago ba.

"Am dama Aure nakeso na k'ara am.." Sai yayi shiru.

Smiling tayi tare da kallon na d'an lokaci "to ai ba matsala sai kayi magana da Alhaji ko 'Yar inace yarinyar?" Ta fad'a cikin kwanciyar hankali, shiru yayi kansa k'asa "oh God I totally fail" ya fad'a a ransa, a fili kuwa yace "anan take Kaduna" a nashi tunanin idan yace haka Mami fad'a zatayi sannan ta bashi Ramlah cikin lokaci.

Ramlah Kuwa  jinin jikinta ne ya daina aiki na d'an dak'ik'u, yadda maganar ta daki zuciyarta, k'arfin halin tattaro nutsuwarta tayi zuciyarta sai suya take tuni k'walla ya cika mata idanu, ji take kamar taje ta rungume shi tace ya fasa Neman auren su wuce gida Indai akan tak'i komawa ne.

"Ok ka samu Alhaji kuyi magana sai ayi bincike ko?" Mami ta katse musu tunani "tom" yace tare da mik'ewa yana kallon inda Ramlah take dan ya ga yanayin ta, ganin sai aikinta take kamar bataji me yace ba yasa jikinsa k'ara yin sanyi a sukwane ya fice.

"Ki kwantar da hankalinki kinji dota,  ruba ce kawai yake ba wani Aure da zaiyi" sunne kai kawai Ramlah tayi tana murmushi, itama Mami murmushin tayi sannan ta fice zuwa parlour gurinsu iya Hari.

Bayanin komawar Ramlah tayi musu tace su shirya zasu rakata gidanta da anjima da dare, sannan ta basu labarin bazanar Abdool, cewa iya Hari tayi "kema dai Hajia ke rik'e mai mata da yawa ai dole yayi muku barazana kinsan yaran yanzu babu hank'uri" dariya sukayi gaba d'aya.



*************


8:00pm su Iya Hari suka kai Ramlah gidanta bayan Mami tasa an tsantsara mata Jan lalle da kitsonta mai kyau, ga gyaran jiki tasha sai shek'i take, susucewa su Shatu sukayi da ganin gidan Ramlah ashe na Mami nafila ne ga farilla anan, Dak'yar Mami ta tattarasu suka wuce sunata santin gidan.

Yara biyu Mami ta samo mata dan tayata renon yaran, nan suka shiga k'yalk'yale gidan da kimtsa sa, duk da dama a tsare yake dan Abdool akwai tsafta da k'amk'ami kullum cikin gyaran gidan yake, Nihal ma an kawo jiki dama tasan da dawowar dan tun rana Ramlah tayi mata waya dan kullum cikin damunta take yaushe zata dawo, zaman kad'aici ya isheta gashi Hakeem ya daina kaita gidan kullum yace bai son ana wahalar masa da baby da yawon hanya, abincin da ta shirya musu ta kawo musu nan ta bige da hira sai 9 ta koma kada Hakeem ya shigo bai sameta ba dan Ramlah tace kar ta gaya masa dawowarsu dan tasan tsaf zai iya tuntub'ar Abdool da maganar gashi surprise takeson bashi.

Sai 10:00pm ya shigo gidan dan a gajiye yake lilis yasha aiki, ko gidan Mami bai samu ya koma ba duba yaran sa, dan yanzu yayi giving up ya barsu in an gama ja masa rai ai ta dawo.

Tun a harabar gidan ya fara cin karo da daddad'an k'amshi, saida ya lumshe ido daya shiga parlour saboda yadda sanyin A'C ya had'e da wani tattausan k'amshi bai gama mamaki ba saida ya hango dinning d'auke da kulolin abinci aiko shawara bai tsaya ba ya haye ya kwashi gara, shi a tunanin sa Nihal ce da yake tana da spare ke na gidan kuma takan shigo tayi masa gyara girki kam kullum zata kawo mishi duk da kullum yake ci ba, wani sa'in da yaci a gidan Mami shikenan dan Sam bayacin abincin kasuwa k'yamarsa yake.

Saida yaji dai2 sannan ya wuce d'akin sa yayi wanka tare da shirya wa Cikin kayan baccinsa, parlour ya dawo dan rufe k'ofa, motsi ya ringa shi a part d'in Ramlah, rufo k'ofar yayi sannan ya nufi part d'in.

A parlour ya samu mai renon su Abdool tana bawa Amaturrahman madara, kallon mamaki ya bita dashi, ita kuma saurin sunkuyar da kanta tayi tana kwasar gaisuwa amsawa yayi tare da tambayan Mamansu bayan ya Amshi Amatu data koma bacci, "tana ciki" ta bashi amsa, wucewa yayi ita kuma ta wuce d'akin da aka keb'e musu.

Zaune take gefen gado tana feeding din Abdullah tasha kwalliya cikin wata fitinanniyar half sleepy gown Brown my santsi shara-shara sai k'amshi take zubawa, tsaye yayi ya jingina da k'ofar ya kafeta da kallon fitina.

D'ago wa tayi tare da sakar mai k'ayataccen smiling hadda kashe masa ido d'aya, da sassarfa ya isa gareta tare da kwantar Amatu gefe, matseta yayi yana hararanta matsa Maman yayi yana kallon ta " zaka sa ya kware ka tayar mana da rigima" tace Cikin slow voice nata.

Bai amsa mata ba sai d'aukesa da yayi daga kan cinyarta, ya aje shi gefe shima, sannan yayi mata mugun matsa har saida kashinta ya koka, d'an k'ara ta saki tana 'yarfe hannu tare da turo baki gaba.

Kama lip d'in yayi cike da zalama ya shiga totsar su da sauri-sauri da wasa da duga sassan jikinta cikin zafi-zafi, ganin abin nasa bana wasa bane yasa ta turesa tare da zame jikinta tana maida numfashi tare da nuna masa yaran dan har junior na kan gadon.

"Ina sauran?"ya fad'a cikin maye, idonsa sun canja launi, " suna gun masu renon su"

"Jeki dawo dasu nan" girgiza masa kai tayi alaman Aa sannan ta zura dogon hijab, ta d'auki yaran biyu ta fita dasu yasan me take nufi a can zasu kwana kenan, d'aukar junior yayi ya bita dashi, dama basa kwanciya da junior saidai in sun kammala .....abinsu suke dawowa dashi tasan yau mijin nata sai abinda hali yai kawai dan tasan yau zataci kwakwarta, (hattara iyaye Ku kad'aice yaranku koda jarirai ne bai kamata Ku tara kuna tare dasu ba, don ko jin numfashinku a garesu bala'i ne, Allah ya shirya mana zuria ameen.)

Saida ta shafesu da Addu'a sannan ta kashe musu wuta tare da ja musu k'ofa, a bakin k'ofar taci Karo da gogon nata, suntumar ta yayi kamar wata baby, muna zuwa k'ofa ya ballamin harara tare da tura kyaurensa ya barni anan ina cizon yatsa naso na d'auko muku Rahoto amma yau Abdool yace nahi(Aa).

Nan na rab'a a k'ofar ina jiran tsammani, can har bacci ya fara d'auka ta naji sai ihu Abdool ke tsundumawa, a firgice na tashi nima zan zunduma da gudu, muryan Ramlah na jiyo sannu-sannu tana magana, hakan yasa na nutsu na baza kunnena dan naji me take fad'a da kyau.

"Kada kajimin ciwo mana Yaya Bini a hankali" tace cike da shagwab'a.

"Um..aaa.. Sorry baby na ai ke d'in CE.." 

"Wayyo Yaya kada fa ka sakeyimin wani ciki"

"Aa...bazan yi miki ba baby...

" toya maganar aurenka?"

"Wane auren kuma...ni ai duk maza nake kallon mata...ash.. Baby ke kad'ai ce fa......wayyo baby ina zaki kaini...wayyo! Wayyo!! Wayyo!!"......









🤣🤣🤣🤣 dariya tasa na k'asa ci gaba da d'auko rahoto, kuma Ku dara amma kad'an fa🙄😝











💄Meryerm Abdool💄
[10/20, 5:13 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Real Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*



```An karb'o daga Abdullahi d'an Abbas (R'D) yace "Manzon Allah(S.W.A) yace " idan d'ayanku ya mutu aka samu mutune arba'in muminai wad'anda basuyi shirka da Allah ba suka sallacesa to ana mishi kyakyawan zaton samun rahamar ubangiji ```

Hakkun mubeen


*Alhaji Waiman (Mukhtar) Allah yayi maka rahama yakai haske k'abarinka yasa mutuwa ta zamo Hutu a gareka kai da dukannin wand'anda suka rigamu ya Allah ka  kyautata tamu bayan tasu ameen👏🏽*






      📝 *Episode* 256-260







A week suka d'auka ana soyewa, Abdool duk ya susuce ya zama jela wa Ramlah duk inda tayi yana manne da ita, sambatun yau daban na gobe daban, tun Hakeem na mishi mita har gaji ya kyalesa, ganin za'a damesa da kira a waya yasa ya kashe wayoyin gaba d'aya har na Ramlah, sauk'in su yaransu basu da fitina sam kullum suna gurin maid nasu feeding kawai ke had'asu da Maman su, shima junior yana gurin k'anninsa kullum yana musu wasa, hakan yasa suka tare part d'in Abdool suna cin karen su ba babbaka, madarar k'auna ta ganta a gurin Abdool wacce ba algus ko kad'an a ciki, riritawa da tattali shine suka shiga bawa juna.

Dak'yar ta samu ta korasa ya koma bakin aiki ganin har gida ake iskoshi amma sai yace shi Amarci yakeyi a barshi ya huta, hadda dan tumbin Hutu ya ije ga wani fresh da sukayi fresh milk tayi aiki. Lol.

Ranar da ta samu ya fita ta d'auka wayarta ta kunna nan fa messages sukayi ta shigo mata na wad'anda sukayi ta Neman basu samu ba, dariya tayi ta tace "duk rigimar Yaya ce ta b'oye ni" sannan ta danna number Sadee rings 2 ta daga tana fad'in.

"Kaga Uwargida a gidan Dr wato shikenan sai mukaji shiru an shige anyi luf sai karb'ar upper ake" ta fad'a cike da shakiyanci.

"Ke Yar duniya baki yimin shi shiyasa naga kinzo min keda baki k'arbar Upper"

"Hehehe! Rufemi ki saya so kike nazo Dr ya harareni yasa na haihu ban shirya ba, banni na lallab'a da Uncle luku na har ki sarara da karb'ar upper d'in"

"Wlh kedai Besty anyi shu'umar mace kin zugani kin koma gefe kina dariya wlh duk kin lalatamu nida sisto".

" wai 'Yar air kina chan kina shan dad'in ki, zakizo kimin burga, wai ya maganar amaryarki?"

Dariyar ta sheke da ita sanda tayi mai isarta tace "ai tun ranar da muka koma aka rufe wannan babin".

" kai besty kema fa silent killer ce a wannan fannin, anya ba so kike kifi malamar taki ba" tace tana dariya

"Cap aike besty k'arshe ce adaiyi shiru kawai, wai yaushe zaki b'ullo ne?"

"Hhhhhh! Kinsan ko akwai sababbin darasi kuyi ready keda Nihal ina nan b'ullowa Akwai chapter".
        " sadee fire sai kinzo muna tsumayenki, kink'i sarara wa Uncle duk da tutsetsen cikin ki"

"Kai ai ba daga k'afa......'" Hakan sukayi ta rahar su tsawon lokaci....

Watan su Iya Hari 2 a Kd sukayi shirin tafiya dan ta samu sauk'i sosai, kuma Ard'o ya matsa su koma hakanan yace dawainiyar tayi yawa, dan shi sati d'aya kawai yayi ya koma saboda jagoranci dake kansa, dan tsawon tafiyarsa 2-3 days ne, wannan Karon ne kawai yayi sati koshi dan ayi aikin yana nan ne kuma anayi ya juya ya koma yace yabar gari sakaka kar wani Abu ya faru kuma bashi nan(jagoranci Abu ne mai girma da nauyi Wanda ya zama dole ga shugaba ya kiyaye domin amanace a hannunsa wacce za'a tambayesa yanda ya gudanar da shi).

Tsaraba sosai suka sha daga gurin su ki da suka je ma Ramlah sallama itama ta had'a musu kaya sosai, ga ingantattun magunguna da Abdool ya d'ora iya Hari akai, kuka Iya Hari ta fashe dashi tana nadamar bakin halin ta na baya, da tana da damar gogesa a rayuwa data goge shi dan kullum ta tuni sai tayi kuka da nadama Mara adadi(ki godewa Allah ke kin gane gaskiya kin shiryu tun anan duniya, wasu kam sai Allah kawai, Allah ya shirya mu akan tafarkin gaskiya mu doge a kansa har abada).



**********



Rayuwa mai cike da k'auna ma'auratan ke gudanar wa, Abdulmajid hospital ta samu d'aukaka sosai saboda kyawun niyya dake kunshe a zuciyarsa, ga sauk'i da ake samu akan komai ba lalle sai mai kud'i ke zuwa ba, ta zamo kamar government hospital yanda yake taimaka talaka da marasa gata Addu'o'insu yasa hospital d'in ta samu karb'uwa a fad'in Kaduna da zagaye a yan watannin da tayi da bud'ewa kowa Abdulmajid hospital kakeji a bakin mutane suna yabawa da kod'awa..

Ramlah tuni tayi mai da zancen karatunsu ganin anaso a shantake, aiko cikin satin ya kawo musu form guda uku ita da Nihal da Sadee, mass com Ramlah ta cike dan har yanzu tana nan akan burinta na son zama journalist, Nihal ta cike nursing, Sadee kuma Pure Biology amma sai bayan su nihal sun haihu zasu fara zuwa, dake Nihal ta shiga month nata sadee kuma next month, hakan yasa Abdool ya dage da koyawa Ramlah motarta dan su samu ta zuwa school, aiko in 2 week hannunta ya fad'a dan Ramlah akwai sauk'in kai....


Nihal ta haihu successful ta samu d'a namiji chaii! Su Hakeem an zama Dady murna bata fad'uwa, anyi shagali still dai ba'a bar Abdulmajid fans ba sun zo sun kwashi banza kamar yadda suka saba, Ramlah da Abdool sun taka rawar gani sosai haka Sadee da Uncle lukman ma ba'a barsu a baya inda yaro yaci sunan Abban Nihal Yusuf suna kiransa da Aabid, Allah ya yara Aabid akan sunnah.

After month itama Sadee ta sunkuto tata 'yar mai sunan Maman Uncle lukman Salma(ihsan) still dai aminan junan sun taka rawar gani haka yan cin banza basu fasa zuwa as always, lol


Sunyi resuming school da motar Ramlah suke tafiya sai su biya su d'auki Sadee dake ita bakin hanya take, wani zubin kuma mazajensu ke kaisu saidai su had'u anan aka k'ara dink'ewa duk da kowacce faculty nasu daban hakan bazai hana idan basu da lec ba su had'u su sha chapter, dan har yanzu bakin bai mutu yana nan musamman Sadee, a gidan Mami suke barin yaran da Masu renonsu su Abdullah anyi girma sosai inka d'auka saika nisa har sun fara rarrafe ko'ina zuwa suke da rarrafe b'anna kuwa ko burgu ya sarara musu shiyasa Mami ke ce musu burguna...

Sam karatu bai hanasu bawa mazajensu kyakkyawar kulawar da ta dace ba, a cewar su karatu baya haka aure kamar yadda aure baya hana karatu saima k'ara samun experience a kowane b'angaren dan sosai majazen su ke assist nasu a kan karatun su......




**********




Wani sanyin ni'ima ne yaji yana ratsa shi lallai yayi missing k'asarsa ta haihuwa na tsawon lokaci, yaga canji sosai da ci gaba a garin, adaidaita ya tara tare da gayamasa inda zai kaishi, dake gurin sananne ne nan take mai adaidaita yace ya San gun, shiga sukayi shida matashiyar yarinyar da ke tare dashi wacce kallo d'aya zakayi mata ka gane tana da jinsi da larabawa.

A dai2 get d'in mai adaidaita ya aje su, biyanshi yayi sannan suka sauko, tsaye yayi a gun yana bin gidan da kallo duk da canje-canje da gidan ya samu hakan bai hanashi gane sa ba, itama yarinyar rakub'ewa tayi gefen sa tana kalle-kalle ta ganta a wata k'asa ta daban wacce take da matukar banbanci da k'asar ta tana rik'e da luggage nasu.

Daga can nesa na hango wani mutum a keken guragu yana tunkaro inda wannan mutumin yake tsaye cike da mamaki a fuskarsa,yana fad'in "Alhmdllh" sai sauri yake dan yaga mutumin na k'ok'arin shigewa gidan ...

"Malam dan Allah tsaya" Kalmar da ta doki kunnensa kenan, dan tabbatar da dashi ake ya juyo.

Tozali da mutumin da yafi tsana a rayuwa wanda yayi silar tafiyar farincikinsa ya dasa masa bak'in ciki a rayuwa ne yasa ya tunkaro gurin sa gadan gadan fuskar nan kamar ta zaki, itama yarinyar ganin meke faruwa ne yasa ta saki jakar tare da bin bayan mutumin tana fad'in "Abi" dayin wani yare Wanda na fahimci larabcine.

Ko saurarenta baiyi ba ya isa ga mutumin tare da cafkar wuyar sa yana huci baiyi duba da halin nakasa da yake ciki ba.

Wawuyar matsa yayi ma mutumin a wuya tuni idanunsa suka firfito waje sunyi jajir sai kakari yake "saina kasheka azzalumi macuci mai raba sunnar manzo" shine Kalmar da ke fitowa daga bakinsa, shikam sai mutsu-mutsun kwantar kansa yake amma ina ko gezau bai ba.

Kuka yarinyar ta fashe dashi tana Jan hannun mahaifin nata "Aa Abi kada ka illatashi meyayi maka Abi ka barshi" tace fad'a Cikin kuka.

Sakinsa yayi da k'arfi tare da tura sa baya, Allah ya soshi badan kukan 'yarsa da yake matukar so ba da ba zai bar wannan azzalumin ba sai ya illatashi koya kasheshi, mugun kallo kawai yake binsa dashi.

Gurgun sai Sosa wuyar sa yake dayaji shaka ajali dak'yar ya daga keken ya sake hawa yace "na cancanci koma meye daga gareka amma dan Allah ka d'aure ka saurareni" yace, still da kallon yake binsa ba tare daya ce uffan ba.

"Nasan na zalince Ku kuma na dad'e ina Neman inda zan ganka na nemi gafararka kona samu sauk'in wannan bala'i da nike ciki, ba kai kad'ai na jefa a irin wannan halin ba hasalima Sana'a tace in bata aure a biyani, kaima ba haka kawai nayi maka haka sakani akayi inyi..."katsesa yayi da cewa "gayamin wane marar imani ne ya sakaka yimin wannan danyen aiki?"

Zaiyi magana sai wata mota ta tsaya a gabansu da mamaki na cikin motar ya fito baki bud'e ya nuna shi da yatsa baki na rawa yace "Auwal!"......








_gatan da zakuyimin d'aya ne masoyana ku nema min gafarar ubangiji dani daku gaba d'aya ya yafe mana kurakurai mu dan rahamarsa👏🏽_












💄Meryerm Abdool💄
[10/20, 5:27 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Real Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*




```An karb'o daga ka'abi d'an Iyadi (R.D) yace" Manzon Allah (S.A.W) yace "kowace Al'umma tana da fitinar ta, fitinar al'umma shine dukiya```

Sahihuh(hakkun mubeen)

*ya Allah kada ka jarabcemu da dukiyar da zata zamo fitina a garemu* 👏🏽





😍 _kun nunan cewa ko bani media kunayi dani, kun nunan ni yar gata ce a gareku💕 Ku sani Meryerm Abdool ma tana sonku sosai iya wuya ana irin mugun taren nan har abada🤝 Hafsat mai Sharif, Raheenat Mahmoud, Maryam Y Zango #ILVYSM 4rm d higher rank of my ❤#_






     📝 *Episode* 261--265






"Yaya Rabi'u" shima ya fad'a yana kallon sa, k'arasowa Rabi'u yayi "Auwal dama kana raye a duniyar nan ka gujemu? Haba Auwal wannan wane irin hukunci ne kayi mana akan laifin da bamu aikata ba, haba Auwal! Haba! Yanzu dai mu shiga ciki wad'annan fa?" Ya nuna gurgun da yarinyar.

"Mu shiga ciki Yaya zakuji bayanin komai" tura gurgun Rabi'u yayi suka shiga ciki, direct part d'in Alhaji suka nufa, yana zaune kamar kullum kan kujerarsa carbi a hannun sa yana ja, sallama Rabi'u yayi tare da shiga.

Kasa k'ara sa amsa sallamar Alhaji yayi tare da mik'ewa tsaye yana nuna Auwal da yatsa cikin inna inna yace "Au..Auwalu kaine ko dai gizau kakemin kamar yadda ka saba"

Gabansa Auwal ya isa tare da sakin kuka "nine dai Auwalun ka Baba, dan Allah Baba ka gafarceni nasan nayi ba dai2 ba dan Allah kayimin afuwa Baba" yace cikin kuka tare da kama k'afafunsa.

"Alamdulillahillazih bi ni'imatih tatimmus salihat" shine Kalmar da Alhaji Sada keta maimaita wa, d'ago shi yayi tare da rungume shi tsam wani sanyi da rahama ce ta ratsa su irin ta uba da d'a, Rabi'u dake gefe sai murmushi yake, shikam gurgun sai kwalla yake yana kaico da rayuwar sa duk shine silar nisantar su, yarinyar kuwa sai kallon tsohon take ba tambaya tasan shine kakanta.

"Rabi'u kaje kayi sanarwar metting na gaggawa yanzu" Alhaji Sada ya fad'a.

Hajia Kaltume ce ta fara isowa parlon suman tsaye tayi tare da zaro ido tana nuna Auwal ta k'asa magana, duk Wanda ya shigo indai yasan Auwal turus yakeyi dan sun dad'e da cire tsammanin sake ganinsa, Maryam ma suna gari sunzo hakan yasa itama ta halarci taron da nata iyalan, wad'anda basu sanshi ba sai a labari duk dai sun ganshi wasu sun ganesa wasu kan basu gane ba, Rafi'a ce ta shigo last dan bata gida tana gurin shashancinta saida Rabi'u ya matsa sannan tazo, ganin Auwal bai wani d'aga mata hankali ba, sai bayan ta zauna idonta suka sauka akan gurgun, ki tayi kamar ta saki fitsari a gurin tsabar tsoro zaro ido tayi tuni ta fara gumi duk da sanyin Ac dake parlon, Ji take kamar ta zura a guje saidai ba damar haka.

Bayan an nutsu kowa ya hallara Alhaji yasa aka bud'e taro da Addu'a, sannan ya fara jawabi kamar haka "kamar yadda muka sani munyi rashi na d'aya daga Cikin 'ya'yan gidan nan tsawon shekaru 29 da suka wuce, wasu daga cikinmu sun sanshi wasu kuma basu sanshi ba sai a labari Wanda har mun cire rai da ganinsa, to Alhamdulillah a yau Allah Cikin ikonsa da ganin damarsa ya dawo mana da Auwalu cikin mu, Alhamdulillah Allah mun gode maka da wannan ni'imar da kayi mana ba tare da k'arfi ko dabarar mu ba" nan hayaniya ta tashi kowa yana fad'in Kalmar nuna farincikinsa game da dawowar Auwal, saida aka gama aka sake nutsuwa Alhaji yaci gaba.

"Kuma kowa nada labarin abinda ya faru dalilin da yasa Auwal ya tafi ya barmu duk da agaremu bai isa dalili akan tafiyarsa ba to shima dai ya gane bai kyauta ba ya kuma nemi afuwa akan hakan munsan wannan bazai wuce sharrin zuciya da shed'an ba, to kuma duk a lokaci d'aya Allah ya kawo mana warwara a cikin wannan lamarin ga Wanda ya zamo silar sabani tsakanin Auwal da Ameena yana ikirari da bakinsa sharri yayi ma Ameena sannan yace saka shi akayi dan haka waka a bakin mai ita tafi dad'i sai a bashi dama yayi mana bayani"

Nan fa kallo ya koma ga wannan gurgun kowa na jiran jin mai zai fad'a.

"Nidai sunana Saminu amma anfi sanina da Shago kashe aure, na samo wannan suna ne a dalilin sana'ata ta kashe aure duk yanda Aure yake muddin akazo gurina akace ana buk'atar mutuwarsa to zan kashesa muddin zan samu kud'i wannan itace Sana'a ta, na kashe aure Wanda ni kaina bansan adadin auren da na kashe ba, a haka ne waccen ta sameni tace zanyi mata aiki" ya nuna Rafia tare da koro musu bayani yadda sukayi da ita da yadda suka tsara komai har zuwa abinda ta bashi.

"Kai munafuki yaushe na tab'a ganinka ni bamma tab'a saninka a rayuwa ba, ni zakayiwa sharri" tashi tayi tana bobbotai da borin kunya, ba Wanda yace uffan sai ido da aka zuba mata, murmushi yayi "dama nasan za'ayi haka shiyasa na tanaji irin wannan ga duk Wanda nayiwa aiki" nan take ya danna wata mp sai muryanta Radau da yadda suka shirya komai.

Tass...kakeji hajia Kaltume ta wanke mata fuska da mari masu kyau "amma dai ke anyi tsinanniya, munafuka yanzu duk yanda na d'auke ki Ashe ke kurace da fuskar akuya kika nasa aka saki 'yar mutane, kikayi silar tafiyar d'ana da nake matuk'ar so, er banza Allah ya isa tsakanina dake" hajia Kaltume tace cikin kuka.

"Aa Kaltume mi a laifin Rafia bayan ke kika bata k'ofa da baki nuna k'iyayyar ki ga Ameena ba ya za'ayi Rafia ta samu hanyar yi musu wannan ta'adi ba, duk da bamu San hujjarta nayin hakan ba" Alhaji Sada yace, sanyi jikin Hajia Kaltume yayi tabbas tayi kuskure a baya na nuna tsanarta a fili ga talaka, amma tuni ta gane gaskiya dan miyagun halayen da Rafia ta b'ullo dasu na rashin tarbiya da musgunawa kowa na gidan, saidai ta riga ta makaro dan Alhaji ya fita batunta akan maganar Abdool da mahaifiyar sa baya fad'a mata komai game dasu gashi ya hana Abdool zuwa gaba d'aya.

Rafia sai raba ido take tana kyarma nan Rabi'u ya daka mata tsawa "meye dalilinki na wannan badak'alar?"

Cikin inna-inna da tsananin tsoro ta shiga gaya musu akan tana son ya auri k'anwarta ne sannan ta tsani Ameena saboda yanda Auwal ke nuna mata k'auna.... Ai bata k'ara sa bayani ba sai saukar naushi taji a baki, tare da rufeta da duka duk jikinta, sai ihu take zundumawa "Auwallu me kakeyi haka ka dawo hankalinka fa tsaketa" Alhaji yace cikin daga murya, saketa Auwal yayi tare da kama gefe yana huci "Alhaji daka barshi ya illata annoba guba, kije na sakeki saki uku kuma Allah ya isa da cutar damu da kikayi" Rabi'u yace.

"Kayimin dai2 Rabi'u"  hajia Kaltume tace, hannu Rafia ta aza a ka tare da fashewa da kuka hadda ihunta dan tasan karyar ta ta gama k'arewa "dalla Malama fice mana a gida ko yanzu in karyaki anan" Sani yace yana binta da mugun kallo, dakar taja kafarta dan ba k'aramin duka tasha a hannun Auwal ba ga bakin ta daya fasa mata sai jini yake, nan fa kowa ya hau murna sun rabu da wahala dan a gidan ta addabi kowa, kowa sai fad'ar albarkacin bakinsa yakeyi, shidai Alhaji sai kallon su yakeyi, shiru ya biyo baya "Rabi'u me yasa ka yanke irin wannan hukuncin da Allah bayaso kai tsaye?"

"Kayi hak'uri Alhaji dole ce tasa dan Rafia tana cutar damu matuka" nan ya shiga zayyana musu yadda take shan kwayoyin rashin haihuwa har zuwa da tayi aka cire mata mahaifa da yanda take bin wasu mazaje, ba Wanda yayi mamaki a ciki dan sun san zata aikata abinda yafi wannan ma, nan dai aka shiga jajantawa kowa da San barka na rabuwa da Annoba, musamman Amaryar Rabi'u tafi kowa farinciki na rabuwa da sukayi da Rafia dan tana cin azaba a hannun ta.

"Kai kuma kaje Allah ya shiryeka" Alhaji Sada yace da gurgun".

"Alhaji na gane kuskure tuni, Allah bai bani bashi ba ya halakar duk k'azamar dukiyar da na Tara, kuma ya jarabceni da rashin k'afafu shi kad'ai ya isheni ishara" sannan ya gungura kekensa ya fice yana godiya, shiru ne ya ratsa kafin Alhaji yace.

"Tau inaso mu duka mu d'auki wannan al'amari a matsayin jarabawa daga Allah, Auwal kai kuma ina ka shige wannan tsawon lokaci ba tare daka waiwayemu ba, wannan yarinyar kuma wacce ce ita?" Alhaji sada ya fad'a, hankalin kowa anan ya dawo suna sauraron suji daga gareshi.

"Ameena sunan ta amma muna kiranta da meenal 'yata wacce taci sunan Ameena, bayan nabar nan direct Abuja na nufa bayan na share sati ina tunanin wace k'asa zan dosa dan na nisanta kaina da Ameena, daka k'arshe na yanke shawarar zuwa saudiya, zamana Saudiya bani aikin yi daya wuce zama a masallaci kullum ina can bacci kawai ke maidani gida, ganin guzurin hannuna ya d'auki hanyar k'arewa yasa na tuntub'i mak'ocina inaso zan fara Sana'a hakan kuwa akayi ya je dani kasuwa ya d'orani akan Sana'a, tun zuwana garin da malam Ikbal kad'ai nayi sabo wato wannan mak'ocin nawa, suna da matuk'ar kirki kullum zasu kawomin abincin safe rana dare basu gajia, sun jani a jiki sosai duk da ban tab'a gaya musu komai game dani ba, suna da 'ya d'aya wato Ahlam sannu a hankali sha kuwa ta shiga tsakanin mu, har takanzo ta gyaramin gida idan munje kasuwa, tana zuwa ta tayani hira a idan naje gidansu kullum taga tana ganina da foton Ameena da Abdool Dana Alhaji da Momy har dai ranar ta nuna tanason taji tarihina irin shakuwar mu tasa na k'asa b'oye mata labari na, Ahlam ta girgiza dajin labarina har da kukanta ta tausayamin, kullum bata da magana saita Abdool da Ameena irin k'aunar da take nunawa ga iyalina ne yasa na k'ara ganin kimar ta a zuciyata" nisawa yayi sannan yaci gaba.

" a haka shekaru suka ja har Ahlam ta kammala karatunta iyayenta suka bijiro mata da maganar Aure, haka Ahlam ta had'a Kai da fata tace idan bani ba ba zata auri kowa ba, tsananin k'aunar da iyayenta ke mata yasa suka amince da ta aureni d'in, bawai dan sunaso ba dan kowa yasan larabawa da nuna banbancin launin fata da tak'ama da nasaba, nidai bansan abinda ake ciki, sai kirana malam Ikbal yayi ya gayamin yadda sukayi da Ahlam, nan na gaya masa komai game dani kamar yadda na gayama Ahlam Ashe itama ta gaya musu jin banyi musu k'arya ba, yasa shima ya bada goyon baya, wannan shine silar aure na da Ahlam mutuncinta da kirkinta da kuma nuna damuwarta akan dukkanin al'amari na ne ya janyo mata k'auna ta, a haka muka zauna tsawon shekara 4 sannan Ahlam ta samu juna biyu, na bata dukkanin kulawa har lokacin haihuwar ta, ta haifo Ameena itace ta zabawa Meenal sunan Ameena, Meenal Nada shekara biyu ciwo ya kama Ahlam Wanda yayi sanadin rasuwarta, tun Ahlam na raye tayi tayi dani mu zo Nigeria, har Cikin raina inason zuwa saidai ina fargabar zuwa in samu labarin Ameena ta auri wani kuma inga inda muka rayu da Ameena amma yanzu babu ita, kullum kuna a raina musamman Abdool da bansan wace rayuwa yake ba, saidai na kasa zuwa, a haka naci gaba da renon Meenal shakuwa ce mai girma a tsakanina da ita, nina reneta da hannuna dan duk yada kamannin ta sukazo ta dawo inda suke k'i tayi ko kasuwa da ita nake zuwa muddin taje gidan kakanninta to tare dani ne"

"Har zuwa yanzu da Meenal keda shekaru sha shida bata yadda da kowa ba saini, ina yawan bata labaru game da gida hakan yasa tasan labaru game daku, kuma na koyar da ita Hausa tana jin Hausa saidai hausar tata kamar ta k'abila take don bataji ga kowa sai guna, a wannan lokacin ne gida ya dawo min a rayuwa kullum cikin mafarkin Abdool Nike yana kirana hakan ya tayar min da hankali naji dole sai na dawo gida hakan yasa naje ma su malam Ikbal da maganar tafiya ta sukace ba damuwa amma zanbar Meenal anan dan tana cire musu kewar tilon 'yarsu, ba musu nace na amince amma Meenal tayi fir tace kafarta kafata, haka suka hak'ura ba yadda suka iya amma sunce zasuzo daga baya" kallon iyayensa yayi "ina Neman gafararku iyayena akan barinku da nayi don Allah Ku yafemin" 

"Mun yafeka Auwal kaima ka yafemin da abinda nayi maka kai da Ameena akan wani dalili nawa Mara asali da tushe, na gane kuskure na Alhaji dan Allah ka yafemin na tuba nabi Allah"

"Alhamdulillah nagode Allah daya ganar dake gaskiya, Allah zaki roka afuwa akan karan tsaye da kikayi akan dokarsa kin manta cewa shi yayi talaka da mai azziki ba tare daya nemi shawarar su akan kasancewarsu haka, sannan ki nemi yafiyar Ameena da Abdool akan hakkinsu da kika tauye Allah ya yafe mana baki d'aya" Ameen kowa ya amsa, kiran Meenal Alhaji yayi ya sanya mata albarka haka Hajia, nan yan uwa da iyayenta kowa ya shiga nuna mata so da gabatar da kansa a gareta.

"Alhaji ina labarin Ameena da Abdool?" Auwal ya tambaya.

Nan akayi zaman sabon labari, "Allah sarki Ameena ta, Abdool dina ya zama babban mutum harda iyali har haka, Baba ya kamata muje Kaduna a yau inaso inga Ameena da Abdulmajid" itama Hajia yanzu ba wad'anda takeson gani kamar su, haka Meenal tana cike da burin ganin takwarar ta da kuma tilon yayan nata, Alhaji cewa yayi su bari zuwa gobe sai suyi sammako suma sun d'an huta.

Da muradin ganin Ameenarsa da Abdool d'in sa, yayi farincikin jin Ameena bata da Aure yanzu kila rabon su sake zama ne.


***********


02:00pm 

A garin Kaduna tayi musu, kasancewar Weekend ne, duk suna gidan Mami, k'ofar gidan suka tsaya, Hajia sai mamaki take yanzu Gidan Ameena ne nan lallai duk abinda ya baka tausayi wata rana sai ya baka tsoro, mota had'u suka ciko, waya Alhaji ya zaro tare da kiran Abdool, ring 2 ya d'aga yana fad'in "tsoho mai ran k'arfe yau soyayyar ta motsa ne" cike da zolaya.

Dariya Alhaji yayi "kamar kana kusa ko Likkita bokan turai, shiyasa ma gani k'ofar gida kazo kamin iso" dariya Abdool yayi shima.

"Banda zolaya fa Alhaji" ba zolaya fito ka gani".

"Saidai fa gani gidan Mami" ai tazo da sauk'i dan nima nan nake nufi ba dajin Ku ba"

"Naji dai ganin nan zuwa " kowa k'ofa ya zubawa ido don ganin fitowar Abdool da yake a hands free Alhaji saka wayar.

Auwal yafi kowa zakuwa son ganin gudan jinin nasa.

Fitowa yayi cikin tafiyar nan tasa ta mai nutsuwa, turus ya tsaya yana bin motocin dake gurin da kallon mamaki dan a zatonsa Alhaji kawai ne............















💄Meryerm Abdool💄
[10/23, 9:23 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Real Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*





```An karb'o daga Abu huraira(R.A) yace daga Manzon Allah (S.A.W) yace "duk Wanda ya yayewa wani mumini bak'in ciki daga cikin bakk'an cikin duniya, Allah zai yaye masa bak'in ciki daga bak'in cikin ranar tashin Alk'iyama, Wanda ya sawwak'awa wani anan duniya, Allah zai sawwak'a masa duniya da lahira Wanda ya rufe asirin wani Allah zai rufe asirinsa duniya da lahira, Allah yana cikin taimakon bawansa muddin bawa yana taimaka wa d'an uwansa, Wanda ya kama hanyar neman ilimi, Allah sai sawwak'a masa hanyarsa zuwa aljannah, wasu mutane ba zasu taru a wani d'aki daga cikin d'akunan Allah ba, suna karanta littafin Allah suna mai bitarsa a tsakaninsu har sai ya saukar musu da nutsuwa, rahamarsa ta lullub'esu, mala'iku sun zagaye su, Allah ya kirasu cikin mutanen da ke gurin sa.```

Allah yasa mudace.

( _Arba'una hadith, rawahul Muslim_ )





❤❤❤ *kuna raina at any cost, Fatyy Azland, Maman ussey, Abdool AAG, Sumee Homa, thanks for ur love and support*😘👌🏻👍🏻






      📝 *Episode* 256--270






Bai gama mamaki ba sai ganin mutum na dosa inda yake yayi, ko da bai tab'a ganinsa a foto ba kamar da sukeyi kad'ai ta isa ta shaida masa Dadyn sa ne, bai San lokacin da murmushi ya sub'uce masa tare da fad'in "Alhamdulillah" shima Auwal murmushi yake farincikinsa bazai misaltu ba wai Abdool ne daya bari a shekara d'aya, shine ya zama complete man, abin alfahari wa kowa "mashaa Allah" shima ya fad'a, rungume juna sukayi cikin tsananin farinciki wata k'auna na ratsasu.

Da gudu Meenal ta fito itama tayi joining nasu "Abdulmajid Ahih" ta fad'a tana jin farincikin ganin tilon yayan nata da kullum take mafarkin gani, d'ago ido yayi ya kalleta tare da kallon Auwal "sister kace My Son, kada kace komai nasan ban kyauta maka ba ka gafarceni, baice komai ba sai k'ara rungume su da yayi yana jin k'aunarsu na ratsasa yau mai zai kira wannan rana mai daraja wacce ya dad'e da cire ran zuwanta.

Gyaran murya Alhaji yayi " umm likita an manta damu ko" ya fad'a yana murmushi dan shi kansa farincikin sa bazai misaltu ba, kallon yabi mutanen dasu, tun daga Haj, Kaltume, uncle Ayuba, Sani, Salisu, Rabi'u, Aunty Maryam da zuriarsu gaba d'aya hadda Ismail da amaryarsa Amal sai murmushi sukeyi suma Hajia CE kad'ai ke sunkuyar da kai cikin farinciki da kunya.

Nan aka shiga gaggaisawa sannan yace suzo su shiga ciki, Auwal yace yaje dai yayi musu iso, yace ai sanda ya gaya musu sannan ya fito.

Alhaji ne ya fara shigo bayan Abdool, Mami ta bud'e baki tana gaida Alhaji Kalaman bakinta ne suka tsaya chak, tare da mik'ewa tana nuna shi da yatsa "Auwal!!" Ta fad'a Cikin shock da daukewar wuta.

Suma su Ramlah kallon mamaki suke masa ganin tsananin kama da yake da Abdool, ga kuma sunan Baban Abdool data kirasa dashi kenan Dadynsa ne da aka basu labari.

"Ameena nine Auwal dai na dawo gareki" still shi take kallo, sai can ta nisa tare da d'auke idonta a kansa ta sauke ga bataliyar Ahalin nasa, da wad'anda ta dad'e bata saka a ido ba da wad'anda bata masan dasu ba, da wad'anda sukan had'u wasu lokuta duk dai gasunan.

Da murmushi ta bisu tana musu sannu da hanya haka su Nihal ma, duk girman falon Mami dakyar ya d'aukesu, sai nan na ake dasu su Ramlah sai hidima suke tuni suka cika su da kayan mak'ulashe da motsa baki sannan suka ja Amal da Meenal, Husna da sauran 'yan matan suka shiga kitchen dan girki.

Duk yanda Auwal yasu su had'a ido da Mami tak'i bashi dama saima basar dashi da take, Hajia kam sai kunya takeji ganin yadda Ameena keta hidima dasu ba tare da nuna komai ba, lallai Ameena ta daban ce a cikin mutane, sai yanzu take gane ba k'aramin kuskure ta tafka ba a rayuwa.

" 'yata Ameena da fatar mun sameku lafia dai" smiling tayi "Alhmdllh Alhaji muna lafia qlau inshaa Allah, sannunku da zuwa kunsha hanya" nan suka k'ara gaisawa.

"To 'yata kamar dai yadda kika gani ga Auwal Allah ya dawo mana dashi, bayan mun cire rai da sake ganin sa, kuma Allah cikin ikonsa ya wankeki a idon kowa wad'anda ke shakku akan zargin da akayi miki har ya zamo sanadin rabuwarku da Auwal" nan ya bata labarin komai.

Sannan yace " sai mu d'auki wad'annan al'amura a matsayin muk'addari ne ba makawa ba gurin gudu ba gurin tsira, sannan ga Auwal nan gabanki tare da Mahaifiyar sa sunzo Neman yafiyarki dama duk Wanda ya zargeki".


"Wallahi Baba ba komai ni ban tab'a rik'e kowa a raina ba hasalima na dad'e da yafe musu, kuma nayi farinciki da ganin wannan babbar rana mai girma".

"Don Allah Ameena kiyafe mini laifuna a gunki nasan ban tab'a yi maki ko nuhwarki da alkhairi a tsawon zamana dake saboda son zuciya irin nawa da son kai da wani dalili Mara tushe da asali dana rik'e, wanda yasa Rafia tayi amfani da wannan ta cutar damu duka, na rok'eki badan halina ba kiyafemin"

"Don Allah Hajia ki daina fad'ar haka wlh ban tab'a rik'e ki a rai ba, itama Rafia na yafe mata Allah ya yafe mana baki d'aya" ameen suka amsa gaba d'aya, sai mamakin kyawun hali irin na Ameena suke shiyasa Allah ya d'aukaka saboda kyauwun zuciyarta.

Auwal ma ya bud'e baki yayi zaiyi magana ta katse sa "Aa Auwal bakamin laifin komai ba, Iyayenka da d'anka kayiwa, ka bani mamaki na rashin yadda da K'addara da d'aukarta meyasa kayi haka Auwal"?

"Na sani Ameena ban kyauta ba kuma Allah ya jarabceni da kadd'ara na d'auka nisantar Ku zai kawo mini sasauci Ashe ba haka bane, saima azabtuwa da nayi da rashin, Son ka yafemin ban kyauta ba" yace yana kallon Abdool.

"Na yafeka Dady kuma nagode wa Allah daya karb'i Addu'armu ya dawo mana dakai lafia, Mami da Alhaji da Uncles' dasu Baba sun yaye maye mani gurbinka sun d'auke min kewarka, Aunty Asma'u tayi nata duty a kaina itama Allah yayi mata Rahama" duk aka amsa da Ameen sannan suka shiga yi mata gaisawar Asma'u da da mijinta da Yusuf, "nagode sosai Ameena da rawar da kika taka akan rayuwar Abdool, nagode sosai Baba, nagode Yaya, Sani, Salisu, Rabi'u, Maryam, Allah ya jikan Asma'u da Abdulrahim da Yusuf yakai haske k'abarinsu" ameen suka sake amsawa, sannan itama tayi masa gaisuwar Ahlam.

"Yanzu wad'annan duk jikokina ne duk yaran Abdool ne, wannan kuma Yaya ne da surukata 'yata 'yar Asma'u?"

Dariya aka saka Maryam tace "ai Yaya girma ya Riga yazo tuni" aka sake kwashewa da dariya, "Abdool sannu kuma da Rashin Zainab Allah yasa ta huta" Auwal ya fad'a, nan ma aka sake gaisawar Zainab.

"Ina Neman alfarmarki Ameena a karo na biyu ki k'ara yadda da auren ki da Auwal dan Allah" Hajia Kaltume ta fad'a cikin rauni.

Tana kuwa kallon gefensa ita yake kallo murmushi tayi "ba komai Hajia, zanyi shawara dasu Inna" tace don kada tak'i Hajia da d'auka ko bata huce bane da ita, "Ameena au wannan ba matsala bane, gobe duka zamu d'unguma muje can suma a nemi yafiyarsu" Alhaji ya fad'a.

Sai dare suka wuce tare da Meenal data Saba dasu Ramlah sosai basu Amatu da suka shige ranta lokaci d'aya...

"Yaya yau kam Ur complete am so glad 2 inama Ummi da Abi na raye" ta fad'a cikin raunin murya tana jin k'ewar iyayenta.

Bubbuga bayanta yake Cikin sigar rarrashi cike da tausayinta "Allah yayi musu Rahama Baby, kada ki damu su Mami zasu maye maye maki gurbinsu kuma ba gani ba?"

"I know Yaya kunyimin komai Wanda ko sune a raye ba zasu wuce hakan ba, i just missing them" rarrashinta ya shiga yi cike da tausayi, lafewa tayi a kirjinsa sosai.....





****************




Flight suka bi saboda basu gama huce gajiyar jiya ba,  Argungu ma mamaki ne ya cika Hajia Kaltume ganin inda su Inna ke rayuwa lallai duk Wanda ya dogara da Allah to fa zai Isar masa, bayan an maida bayani an yafi juna a ranar a maida Auren Dady da Mami, Hajia ta bada sadaki da kanta, kashe gari suka wuce sokoto saida suka biya ta Kilgori suka gansu, Hajia ta K'ara girmama Allah da gode masa wato nata yazo da sauk'i sosai, sabanin na Hari, kai lallai ba inda mugun Abu zai kai mutum face nadama Mara adadi (Allah yasa mugane gaskiya).

Satin su d'aya a Sokoto suka shirya komawa Kaduna dan aikin Abdool, Dady ma ya tattaro nasa da nasa ya bisu Kaduna dan Mami ta Riga ta saba da zaman can so bazata iya dawowa Skk ba ga kuma aikin ta, kasuwancinsa yaci gaba dayi, inda suke zaune lafia Cikin aminci da soyayya (soyayya bata tsufa saidai ba'a botanta su tsufa).

Ya rik'e su Nihal da Amana ba banbanci kamar shiya haifesu, ita dai tana jin Meenal dai2 dasu Husna a ranta mashaa Allah komai Alhamdulillah.

Gyara sosai Abdool yayi wa su Ard'o dan yace ya dawo Kaduna yace shikam Kilgori ta isheshi anan ya saba, ga kuma mulki ina zai barshi, hakan yasa ya gina musu gini mai kyau na zamani, sannan ya bawa su Shatu da mazajensu jari mai tsoka, dan Lanti tayi aure ta auri wani mutum mai kirki itama ta gyara halayenta suna zaune lafia.........



************







Hadin guiwa sukayi suka d'auki jirgi sukutun sukaje umara tun daga kwansu da kwarkwata ba Wanda aka Bari har su Iya Hari (hoho wayaga Hari a saudiya, kada ki manta Iya Hari ki kaiwa aminiyarki ta gani kashe ni ziyara wato Mom Zee) lol.

Gidansa na can wasu suka sauka wasu gidan Ikbal, wasu kuma aka kama musu.

Ikbal sunyi farinciki da ziyarar ta ba zata sun tabbata lallai Auwal d'an dangi ne, yau dai ga Ameena da Abdool sun gani da suke shan labarin su, sunyi ziyara sosai, watansu d'aya suka dawo, anyi sa'a ana Cikin Hutu su Ramlah, Sadee Ansha tsaraba har da sakwannninta an kawo mata da k'ari. 

Tare dasu Ikbal suka dawo Nigeria inda sukaga  mazauninsu, sun zaga garuruwa da dama a Nigeria sunyi dad'in ziyarar dan Nigeria ta burgesu sosai musamman suturun su da al'adunsu, wani abun ma sai a Argungu sunga gargajiya tsantsa( Argungu garin nabame kowa sarki, kabawa ikon Allah Ku adda ruwanan! Hmm da k'asar wasu gwara k'asa ta, da garin wasu gara garina.)...........








🤧 _mura on top, ur supplication is needed my Fan's, love  as always #1love# going 2 missing u_ 😥😪














💄Meryerm Abdool💄
[10/25, 8:37 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤           ```ABDULMAJEED```        🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨



Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄


© *Real Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)



*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*




*_Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a garesa yace "Ku ladaftar da 'ya'yanku akan Ladubba guda uku, Son annabinku, da son iyalan gidansa da karatun AL-QUR'AN, don su makaranta AL-QUR'AN suna Cikin inuwar Allah ranar da ba wata inuwa sai tasa, tare da  annabawansa da zab'abb'unsa.(majma'ul baharai)_*

👏🏽 _Allah ka k'ara mana son annabi da iyalan gidansa, ya Rahman ka k'ara mana son karatun AL-QUR'ANIL KAREEM👏🏽_


*komai yayi farko zaiyi k'arshe, amma banda ikon Allah, nagode sosai masoyana masu bibiyar rubutuna da hak'urin da kukayi dani har zuwa yau, nagode da soyayyar Ku gareni da k'arfafarku nagode sosai thanks 4 care and support❤❤❤😘 bazan manta daku ba gidan amana da had'in kai, gidan karamci da girmamawa, Allah ya barmu tare cikin aminci da k'aunar juna P.M.L gaba dai gaba up!👍🏻👌🏻*














     📝 *Last Episode* 271--275









       *_AFTER TEN YEARS........._*






" A yau gamu tare da shahararriya, hazik'a, jaruma, zak'ak'urar 'yar jaridar nan wacce ta kware gurin tono gaskiya da rubuta ta ba tare da tsoro ko shakka ba, wacce ta sadaukar da rayuwar ta gurin rubuta gaskiya komai d'acinta kuma kome zata zama wato, koda yace wak'a a bakin mai ita tafi dad'i, ko meye sunan Hajiyar? Masu kallo suna son sani"

Sanye take da dakakken les dan ubansu brown colour mai adon milk flowers, hakan yasa hihab d'inta ya kasance milk haka bag and shoes nata(mashaa Allah na fad'a tare da sake baki lallai da banyi mata farin sani ba bazan ganeta ba, ta canja d most tayi fresh tayi jiki ga wata irin wayewa da tayi wacce tayi dai2 da islama bata turawa ba).

Smiling tayi "Sunana Ramlah Abdulrahim Modibbo wacce akafi sani a harkar rubutu da Mrs A.A" 

"Mashaa Allah Mrs A.A nima dai shi nafi sani amma a yau ni da masu kallo munji ainihin sunanki mai cike da tarihi Allah yayi albarka"

"Ameen nagode sosai"

"To idan ba damuwa munaso muji tarihin jarumar tamu a tak'aice, gwagwar mayar da tayi da rayuwa har zuwa yau data zama mai nasara?"

Anan ta shiga bata labarin ta a tak'aice mai cike da tausayi, koda ta kammala daga ita har mai tambayan kuka suke, handcart tasa ta share hawayen tana murmushi sannan ta mik'a wa mai tambayan tata d'aya ta goge nata itama.

Gyaran murya tayi "na dad'e banji labari mai tab'a irin wannan ba, lallai Mrs A.A kinga gwagwar mayar rayuwa, saidai kuma hak'uri da kikayi ya zame miki alkhairi, Allah ya sauya miki rayuwa ya d'aukaka ki ya maye miki gurbin duk wani rashi da kikayi, hak'ik'a labarin ki ya isa misali, ishara ga mutane, Allah ya jikin magabata yakai haske k'abarinsu ya kyautata tamu bayan tasu"

"Ameen ya Allah nagode"

"Shin ko zamu iya sanin dalilin da yasa kika zabi ki karanci aikin jarida? me yaja ra'ayinki a aikin jarida? Ko akwai Wanda ya k'arfafa maki akan haka? meye nasarar da kika samu cikin aikin? Shin kin tab'a fuskar wani k'alubale ko barazana a wannan aikin?"

"To a gaskiya tun farko ina sha'awar zama journal and inaso na wanke rad'e-rad'in da akeyi game da journalist akan suna rubutu ne kawai don 'yan siyasa wato ya basu amma basa tono gaskiya akansu suna cover na laifukansu, in fact an d'auki d'an jarida baisan me yake ba sai abinda aka saka shi, to wannan yana d'aya cikin abinda yasa na zabi harkar"

"Dukkanin 'yan uwa sun k'arfafa min kuma sunyi supporting d'ina ta ko'ina musamman mijina abin alfahari na ba abinda zance sai Allah ya saka musu da mafificin Alkhairinsa" 

"A gaskiya nasarorin da na samu ba zasu k'irgu ba, mafi girma irin Addu'o'in da nake sha gun jama'a shima wani babbar nasara ce gareni, k'alubale ba'a rasa ba, don akwai time d'in da aka tare ni na d'auko yara daga school, Allah ne dai ya karemu a ranar, barazana kuma ina samu a kowacce rana, saidai na wannan bai tab'a karya min gwuiwa ko yasa naji jikina yayi sanyi ba, saima k'arfafamin da yake akan ina ba k'asa ta gudummawa kenan"

"Hakane kam, tabbas kin kawo canji Sosai a harkar jarida, kuma an samu ci gaba sosai a harkar jarida, ba abinda zamuce sai Allah ya kara dafa mana ya kuma k'ara shige mana gaba, ya kuma karemu daga sharrin mak'iya da mahassada"

"Ameen"

"Yau fa masu abune da abunsu to tambayoyi sai kin ture, ko zaki iya gama mana meye ma'anar " Mr A.A d'in nan"ta fad'a tana dariya.

"Hmmm kada ki damu zaki samu amsar kowacce tambaya taki" smiling tayi mai sauti "Mrs na belonging ga miji to A.A na nufin Abdulmajid Auwal wato Yayana mijina"

"Kai mashaa Allah,  lallai Dr Abdulmajid ya taka babban matsayi a rayuwar ki, to Allah ya raya zuria ya k'ara k'auna a tsananin Ku madawwamiya"

"Sosai Yaya Abdool shine duniya, Ameen Ameen nagode"

"Ko zaki iya gaya mana matsayin Abdool a gurinki? Kamar yadda koma komai da kika mallaka yana d'auke da tambarin Abdool kamar irinsu Abdool oil&gas naki, Abdool supermarket, Abdool Islamic scholars da dai maka mantansu"

"Hhhhhh! Abdool uba ne, Abdool yayane, Abdool miji ne, Abdool k'anine, Abdool d'ane kuma inshaa Allah har jika sai nayi Abdool, so kinga kenan Abdool na nufin Ramlah, da ina damar zama Abdool kacokam to tabbas zan zama, Abdool shine rayuwar Ramlah" (nima dai nace Abdool ne rayuwar Meryerm).

"Tofa lallai Mrs A.A kin tara Abdool koma ince ke zama Abdool ko zaki bani d'aya ne?"

"Hmm idan kinada k'ari zaki iya bani, dan ko zan tara haifi yara d'ari bazan gaji da saka musu Abdool ba, inason Abdool sosai musamman *Abdulmajid* Yayana mijina, jigon rayuwa ta, abin alfahari na, farincikin rayuwa ta, Allah ya barmu tare har mutuwa" ta fad'a cikin shaukin soya year mijin nata.

"A gaskiya kin burgeni, inama kowace mace zatayi koyi dake, taso mijinta kamar yadda kikeson Dr Abdulmajid da an samu zaman lafia sosai a gidaje da ana soyayya domin Allah, Allah ya barku tare cikin Aminci"

"Ameen nagode"

"Ko zaki iya gaya mana me kikafi so a rayuwa?"

"Yayana mijina *Abdulmajid* mijin da babu kamar sa yayan da babu irinsa, mafi tausayi a cikin mutane, mai karanci da mutunci a gurin kowa mai tausayin iyayensa mai kyautata wa iyalansa, guda d'aya tak tamkar da dubu"

"Ya ilahi da fatar Dr Abdulmajid yana gaban tibinsa yana kallon wannan hirar tamu, yana kallon yadda matarsa ke Koran ta ka da yaba ka nasan ka tsuma da zantukan ta, ina fatar Allah ya raya wannan k'auna har abada"

"Ameen ya Allah"

"Munaso ki mik'a godiyarki da gaisuwar ki zuwa ga wasu mutane masu muhimmanci a gareki"


"Tofa! Hmm da farko ina mik'a godiya ta ga Allah mad'aukakin sarki, wanda ya samar dani daga babu, ya sanyoni cikin al'ummar musulmi ba tare da iyawata ba sannan zan godewa iyayena da suka zamu sune silar zuwana duniya, ina godiya ga kakana Ard'o Wanda ya reneni cikin soyayyar da k'auna, ina mik'a godiya ta ga mamata uwar goyona kuma surukata Mami tare da Dadyn mu Allah ya saka musu da alkhairi, dole na mik'a gaisuwar had'e da godiya ga gimshik'in rayuwa Yayana Mijina Dr *Abdulmajid* gaisuwa zuwa ga Aminan Arziki 'yan uwa na jinin jiki Nihal, Sadee, Amal Meenal, Aunty Zee Allah yayi mata rahama dama sauran wad'anda ban ambata ba duk ina mik'a gaisuwa, gaisuwa zuwa ga manyan gobe 'ya'yana abin alfahari Allah yayiwa rayuwa albarka"

"Kai madallah da fatar duk kunji sak'on Mrs A.A kuma kunyi farinciki"

"Daga k'arshe meye sakonki, ga masoyanki harma da mak'iyanki, meye shawarar ki zuwa garesu? A gurguje dan na fahimci idan muka barki ba gajia zakiyi ba" tace tana dariya.

Itama dariyar tayi "sak'ona zuwa ga masoyana har mak'iyana shine ina sonsu gaba d'aya, shawara ta itace ayi hak'uri da komai na rayuwa mai wucewa ne kuma duk abinda akayi hak'uri a kansa inshaa zai wuce muddin anyi hak'uri mai kyau, hak'uri bai tab'a zama cuta saidai alkhairi ayi hak'uri nothing is parmanent even our live and world so be patients, behind every success there ris many obstacles but at d end there ris way inshaa"

"Wannan haka yake dan rayuwar ki kad'ai ta isa misali gamai lura, mun gode da wannan lokaci da kika bamu muna miki fatar alkhairi a rayuwa, muna mik'a jarumin maza Wanda ya ciri tuta a mazaje angon gurin jarumar mace mai kishin k'asarta wato Dr *Abdulmajid* likita na talaka Allah ya k'ara girma"

"madallah nima ina godiya da wannan karramawar da akayi Mani, nagode sosai da Addu'a da muka sha yau sai mun k'ara had'u wa wani lokaci, nagode"

"To jama'a duka duka anan muka kawo k'arshen firarmu da fittacciyar 'yar jarida jaruma, hazik'a Mrs A.A Wanda ni Hafsat mai sharrif na gabatar fatar kunyi farinciki da wannan firar mai cike da darasin rayuwa, saduwar alkhairi......."



********""


Abdool dake zaune kan sofa cikin d'akin sa tun da aka fara firar ko motsin kirki bayayi saboda yadda bada duka Attention nasa, hakan yasa yabar yaran parlour su kalla ya keb'e kansa saboda muhimmancin da bawa firar...


"Oyoyo Maa, oyoyo Maa..." Yaran ke fad'a cikin murna ganin mahaifiyar tasu da jin dad'in firar da akayi da ita da suka gama kallo.

"Maa u done it perfect" Junior ya fad'a tare da d'aga mata yatsa, peck takai masa tare da Shafa kansa "really Son?"

"Really Maa" suka fad'a a tare, murmushi tayi tana kai musu Peck daya bayan d'aya, K'amarar 'yarta ce wacce ba zata wuce five years ba, ita kebin su Amatullah, tak'i zuwa gunta ta koma gefe ta lab'e jikin gini tana fushi, murmushi tayi dan tasan rigimar Zainab da daru kullum k'aruwa yake.

"Lalala! Wayata tab'a min Aunty Zee na waya tab'a min autana" ta fad'a tana sunkuyawa tare da janta jikinta, turo baki gaba tayi just like Ramlah "ba Aunty Amatu bace wai baca cona cu Ya Abdool kawai kike cu, cu katai kika fad'a cunancu"

"Ya ilahi Ama zata kwanto min kura ta fad'a a ranta" a fili kuwa tace "kyaleta tsokana ne kawai ai itama ban kira sunanta ba, maza ne fa kad'ai na fad'a ina kinji"?

" to aini 'yar aunty Meenal ce, satin nan ma zanje mata weekend lololo" Amatullah ta fad'a tana yiwa Zee gwalo, "ni kuma gidan Aunty Husna zanje" itama Amaturrahman ta fad'a.

"Allah Ama zan muku duka banason tsokana fa, kinga Auta na ke kad'ai nakeso sai su ya Junior bana son su Ama" gwalo ta shiga yi musu tana dariya jin ba'a sonsu kuma za'a musu duka.

"Ash!" Ta fad'a tare da sauke Zainab, "na gaji sosai, paa na ciki"?

" eh" 


Da Sallama ta shiga, duka hankalinsa ya dawo Kanta yana mata murmushi bayan ya amsa sallamar, a jikin sa ta zube "I really tired my half"

"U done it so Amazing, barin miki messenge" ya fad'a yana mata tausa, cire mata higab d'in yayi tare da zuge zip d'in, sai wani lumshe ido take, yanda take jin dad'in tausar.

Murmushi keta yayi tare da canja tasha, zaro ido tayi "haba Yaya hospital zamuje fa duba patients d'in, barin yi wanka nama ware"

"Not now it Skip, letter 2morrow" ya fad'a yana ci gaba da abinda yake.

"Zamuje gidan Mami fa, duba Dady ka tuna?"

Murmushi mai sauti yayi "ke nifa su Dadyn nakeso na samar so yau ranata ce a barni na huta"

Ganin iya gaskiya yake yasa ta samo wata dubara " yawwa barin nuna maka abinda suka bani na girmamawa sai a Samar da su Dadyn ai nima am eager "

"Serious! Nuna min" ya fad'a tare da sakinta mik'ewa tayi ta gyara rigar ta sannan ta bud'e baka kamar zata d'auko abu, sai ganin yayi ta kwasa da gudu saida takai k'ofa ta tsaya tana mishi gwalo "an maka wayon manya"

Yunkurawa yayi kamar zai tashi aiko ta ida fita da sauri tana masa gwalo.

"Zan kamaki ne ya fad'a da k'arfi yadda zata jiyoshi, smiling yayi mai k'ayatarwa tare da lumshe ido " Sam bata girma, hoho Ramlatun baffa ta mai gilashi" ya fad'a yana rungume filo tare da tuno baya...........



*ALHAMDULILLAH*    *ALHAMDULILLAH*
     *ALHAMDULILLAH*




*dukkanin yabo da godiya su tabbata ga ubangijin da bai Haifa ba ba'a haifesa ba, Wanda ya kad'aita cikin mulkinsa da ikonsa, Wanda ya tsarkaka a sunayensa da sufofinsa, Kamar yadda ka bani ikon farawa da gama wannan littafin lafia,  ya Allah ka bani ladar da ke ciki ka shafe zunubai a rubuce da zuciya, Allah kasa nayi hujja da wannan littafin kada yayi hujja dani, Allah ka bamun ikon rubuta dai2 da aikata dai2 Ameen* 👏🏽


Sai kun jini a littafina na gaba *A dalilin pre weeding pics* just keep following my fans😘💋




Taku ce dai 

💄Meryerm Abdool💄
