*🌈 IDAN BA KE 🌈* _True Life story_ Nimcyluv sarauta _*Arewabooks@Nimcyluv*_ 1. Jimeta/Yola Njoɓoli Rugar Rome Gudu Saniyar take tana bin ta a baya itama, hannunta riƙe da sanda na korar Nagge, tamkar wanda suke wasan tsere haka Saniyar ke gudu a cikin jejin ita ma bata fasa bin ta ba, sauran Naggen suna gefe guda ko wacce na cin ciyayi wanda bisa kuskure tana can tana bin Saniya ɗaya tilo, sauran Naggen suka faɗa cikin gonar wani manomi, a yunwace suka rufarwa albarkatun gonar. Cikin siririyar muryarta mai nuni da Yarintar ta, da kuma nuna cewa ita ɗin zallar bafullatanar Yola ce ƴar Usul. "Waru! Waru! Waru" shi ne abin da yarinyar ke ta nanatawa cikin hausarta ta Fulani, yayinda Saniyar tuni tai mata nisa cikin gajiya wa da bin Saniyar ta tsaya a wajan wata gaɓar ruwa tana riƙe ƙugunta ta ce "Bone, lalashewa ta samu Nagge Aradu" da sauri kuma ta ɗauki sandar tana ƙara yin kan Saniyar ganin ta tsaya da gudun da take, cikin sa'a ta cimmata tana zuwa ta kama ƙahonta tare da ƙifƙifta idanunta alamar zallar fitsarar dake tattare da ita "d'ume ngid'd'a?" Ma'ana "me kake so?" Kallon ta Saniyar ta yi sai kuma ta kaɗa jela tare da zubewa a wajan ta shiga shura ƙafafuwa kamar zata mutu, cikin tsoro haɗi da razani HALISA ta ce "Jomirawo ka taimakeni" ta faɗa tana kallon Saniyar wacce tai male-male a ƙasa ga wani ruwa mai kama da jini na fitowa ta ƙasanta, kuka Halisa ta sanya domin idan Saniyar ta mutu a nan wajan ta shiga uku, itama watan mutuwarta ya kama. Tsayar da kukan tai kafin ta fara duba cikin jeji babu kowa sai ita, ga wani kwantaccen baƙin hadari dake ƙasa wanda a koda yaushe zai iya tashi. Juyawa tayi ta nufi wajan wata bishiya inda ta hangi ƙaramar igiya a jiki, tana zuwa jikin bishiyar ta zame hular Fulanin dake kanta, nan da nan sumar kanta ta sauka wacce take jajir babu alamar baƙi ko ɗaya, gashin ba wani cika ne dashi ba, kawai tsayin gashi gareta, domin har fatar tsakiyar kanta ana iya ganowa. cikin sayin jikinta ta fara jan igiyar tana ƙoƙarin kunce igiyar gaba ɗaya daga jikin reshen bishiyar, kamar daga sama taji saukar wani abu mai sanyin gaske zuwa kafaɗunta. Cak ta tsaya tana sauraren yadda abin ke tafiya sululuuuu a jikinta har ya gama sauka, hannunta ta miƙa da nufin kama abin da ya sakko mata domin bata da tsoro ko kaɗan, cikin rashin sa'a hannunta ya sauka saman ƙaton kan maciji wanda yake kwance a jikinta, wani santsi-santsi ta ji a jikin macijin ga wani sanyi sosai dake ratsa fatar jikinta, bata gama yadda da abin da zuciyarta ke ayyana mata ba, a hankali ta juya wani ihu ta kurma wanda ya yi daidai da ɗaukewar numfashinta, baya tayi zata faɗi kafin ta kai zuwa ƙasa macijin ya yi wata girgiza cikin sakanni ya juye zuwa wani saurayi wanda jikinsa ya ke sanye da wasu haɗaɗɗun kayan sarauta na farin saƙi, fari ne tas amma kamar Fatar mace haka fatar hannunsa da sauran jikinsa suke gaba ɗaya gashi ya kwanta luff. Zubewa ya yi a ƙasa ta faɗo jikinsa idanunsa a kan fuskarta, ya jima yana kallonta kafin cikin izza da nutsuwa ya ce "kin tsoratani, kin tsorata kanki Danejo, banyi niyyar zuwar maki ba yanzu" Danejo sunan da ƴan rugar Rome suke faɗawa Halisa ke nan. Sai da ya gama Kallon ta sosai, kallon da ya jima bai mata ba tun tana zanin goyo matsayin Jaririya. Ɗaukanta ya yi ya nufi inda Naggen suke yana zuwa ya tarar da wannan Saniyar dake Shure Shure ta haihu, ashe daman ciwon haihuwa ke damunta. Halisa ya kalla yana sakin Murmushi kafin ya zaro harshesa waje sai ga wani zobe ya bayyana, cikin sauri ya saka mata zoben mai ɗauke da tambarin wata masarauta, kafin ya yi Girgiza sai ga shi ya sauya kama, kamarsa a fuska na nan, amma kayan jikinsa sun sauya sun koma irin kayan Fulani sak komai da komai, goya Danejo ya yi a bayansa, ya ɗauki jaririn Saniyar cikin nutsuwa ya fara kaɗa Naggen zuwa Rugar Rome. Kamar ƙifatawar idanu haka ya ƙaraso Rugar.. Iskar dake kaɗawa na alamar tashin hadarin ya sanya matashin ɗaga kansa sama, yana kallon yadda gajimare ke haɗa kansa. A nutse kuma ya fara bin Rugar Rome da kallo ba wata babba bace, amma Ubangiji ya albarkaci rugar da dabbobi musamman Nagge, gasu manyan gwanin sha'awa yawancinsu jajaye ne kafin ka samu farar saniya zaka daɗe. Wasu sun dawo daka kiwo wasu kuma na hanya sbd rashin yawaitar mutane da babu a rugar, daidai wajan wata bukka ya Ƙarasa yana gyara riƙon da ya yi wa Jaririyar Saniyar kafin ya ce "Sannunmu dai" ya faɗa a taushashe jin shiru ya sanya ya ƙara buɗe muryarsa mai sanyi ya ce "Afuwanku dai" daga cikin bukkar wata ƙaramar murya ta amsa da faɗin "Waye nan?" Ta faɗi hakan tana fitowa, lokacin da Idanunta ya sauka acikin ƙwayar matashin gabanta taji ya faɗi saboda yadda taga ƙwayar idanunsa, gane cewa kamar ta tsorata da yanayinsa ya sanya ya lumshe idanunsa kaɗan tare da buɗewa ya ce "Ga ɗan uwanki na kawo shi, arado bashi da lafiya ne can na ganosa yashe a jeji ba rai, har naggenku ya samu zuri'a" yana faɗin hakan ya ajjiye Jaririyar Saniyar a ƙasa wacce take jajir da ita Kuma ƙatuwa. Shatu dai binsa take da Idanunta domin bata taɓa ganin mai kama dashi a rugar ba sai yau, kallon da yaga yai yawa ne yasa ya ce "Shai a mata magani" a hankali ya sauke Halisa Dajeno ya kwantar a ƙasa a nan gaban bukkar kamar zai juya ya tafi sai kuma ya ƙurawa zoben hannunta idanu wanda yake sheƙi sosai ga tambarin masarauta nan ya fito sosai a jikinsa, a ransa yake ji kamar bai dace daya mallaka mata wannan zoben ba, amma bashi da wani zaɓi dole ya bata ta haka ne kawai zai lalubota a duk sanda ta ɓace masa, tun tana ciki yake fama da rainonta lokacin haihuwarta ne kawai bai sani ba. Ba tare da ya ƙara cewa komai ba ya juya da sauri ya fara tafiya tare da shankwana, yana barin wajan ya ƙara yin girgiza wata iska mai daɗi da guguwa ta mamaye gaba ɗaya cikin Rugar Rome. Nan take ya koma asalin macijinsa kamar yadda ya bayyana a farko, yana iya komawa duk suffar da yaga dama cikin ƙaramin lokaci amma zama maciji yafi masa daɗi sbd yawaitar macije dake cikin jejin daya zagaye Rugar Rome, a haka ya sulale tare da komawa cikin jejin. Iskar dake kaɗawa ce tai sanadiyyar farkawar Dajeno daga barcin dolen da macijin ya sanyata a ruɗe ta miƙe tana dafe kanta dake mata ciwo sosai cikin sanyin murya ta ce. "Miyyati Allah" Shatu dake gefen Dajeno tana ɗaure Naggen a garken dake dab da bukkar ta ce "Nassu, ka shigo" Shiru Danejo tai kamar zata tuna wani abu sai kuma tai saurin ware manyan idanunta ta ce "Shai Shatu ina Dadana ya tashi daga barci hoo?" Shatu ta ce "E, yana ta kiranka baka dawo ba, ciwonsa ya tashi yana ta masa zafi" da sauri Danejo ta faɗa cikin bukkar Idanunta ya sauka akan Dada (her mother) tana kwance a rufeta da wani farin zani jikinta sai rawa yake, fara ce matar sosai amma yanayin jikinta kamar ta shekara 60 nan kuma ba tafi shekaru 50 ba idan ma ta cika. "Shannu shannu Dadana" Idanu Dada ta buɗe da ƙyar ta ce "Zakiyi Albarka Halisa ki riƙe gaskiya da amana ki zama mai haƙuri ki daina saurin fushi da rashin kunya" Kallo juna sukai da Shatu da Halisa wacce akafi sani da Dajeno "Dada me yasa kake shaiwa haka?" Dada ta kalli Shatu kana ta juya ta kama Hannun Dajeno ta haɗa dana Shatu ta ce "Meyasa ba zance haka ba? Shatu kece ƙarama Halisa ita ce babba amma zafin zuciya ne da ita, rauninta akai na yake, kuma dole na tafi na barta" da sauri Shatu ta kalli Dada tana faɗin "Ina zaka Dada kuma?bayan Rugar Rome ina muke dashi" Dada ta numfasa ta ce "Babu da inda yafi wannan Rugar, zan tafi zuwa ga Mahaliccin daya samar da Rugar Romen, ciwon nan ba zai barni ba kuɗin amanata ce musamman ke Halisa" Dajeno kasa cewa komai tai sai ƙurawa Dada fararen idanunta da tayi zuciyarta cike da fargaba. "Dadana ba zaki mutu ba, idan kin mutu wa muke dashi a nan rugar wazai dinga kulawa damu?" Dajeno ta ƙare maganar cikin sanyin murya gaba ɗaya jikinta yai sanyi sosai. Shiru kawai Dada tai can kuma ta ce "Hamma Yabi ya dawo?" "A'a birni da nisa Dadana yace gobe zai kai ki can asibitin birnin". Jinjina kai Dada tai Dajeno ta miƙe bayan ta ce Shatu ta kula da Dada yanzu zata wajan Sarkin ruga ta amso magani. Cikin sanyin jikin nan nata take tafiya kanta a ƙasa domin bata fiya kallon mutane ba, a yadda jikin Danejo yake da sanyi zaka ɗauka babu ruwan ta, musamman da fuskarta yai kala dana salihai amma zafi da zuciya gareta, ga kuma taurin kai da naci akan abu, idan tace zatai to tabbas zatai, amma idan tace A'a babu wanda ya isa juyata ko Dada sai dai ta zuba mata Idanu. Abin birgewa ga rayuwar Halisa Dajeno tana da saurin yafiya, da kuma tausayi da kuma kawaici. Cikin tafiyar nutsuwa ta Ƙarasa gaban wata bukka wacce tafi ko wacce bukka kyau da girma a cikin Rugar Rome. "Shai shai Mene haka kamar makauniya ina kwaɗa miki shandan nan Aradu" da sauri Danejo ta ɗaga idanunta ta kalli Gwaggo Niyabi wacce ke zaune tana kaɗa audiga, murguɗa baki tai ba tare data ce komai ba, jin tai shiru yasa Gwaggo faɗin "Ko njid'ud'a?" "Magani za'a bawa Dadana" Gwaggo Niyabi ta ce "To baya nan" shiru tai kamar zatai Mgn sai kuma ta juya sai da tayi nisa kaɗan Gwaggo Niyabi ta ce "Yaka Dajeno waru" tsaye Dajeno tai domin ba shiri suke da Gwaggo ba, Murmushi Gwaggo tai sosai kafin ta numfasa ta ce "Idan kinje ki tambayi Dada waye mahaifinki, mene yasa daya rasu bata bar Rugar Rome ba, ta tafi danginta ko dangin mijinta" da mamaki Danejo ta ce "To bayan Baffa ya rasu mene na tambayarsa, ki daina maganar Uwayena" Gwaggo ta miƙe tana kallon Danejo "To ana gab da kurarku a Rugar Rome, domin bama son mara gurbi" harara Danejo ta watsa mata ta ce "Miyidi saro'am" ma'ana ina son iyayena "Kalleki mai ƙaton baki da ƙwalaƙwalan idanu" tana faɗin hakan ta kwasa da gudu zuwa bukkarsu. Da ƙyar suka samu zazzaɓi Dada ya sauka tasha paracetamol sai 12 na dare ta samu barci. Shatu ma barci take kusa da Dada a hankali Danejo ta miƙe daga kwancan da take har yanzu fararen kayan Fulani ne sanye a jikinta, hula ta ɗauka ta rufe kanta a nutse ta fita daga cikin bukkar kai tsaye garken shanun dake dab da bukkar ta nufa, wanda aka kunna musu wuta tana ci kaɗan kaɗan. Gobe da sassafe take son tafiya tallan kindirmon. ƙwarya ta ɗauka ta tsuguna tare da kama nonon jikin wata Nagge ta fara tatsa gaba ɗaya hankalinta baya jikinta sai a lokacin maganar Gwaggo Niyabi ta faɗo mata, a haka ta gama tatsar nonon acikin ƙwayar ta ajjiye can gefe guda a bukkar tasu. Gari na waye ba tare da yin wanka ba ta shasshafa ruwa ƙafa duk lam'a ta dungura sallah. Dada na gefe tana kallon yadda take sallah tana son tuna wani abu amma ta kasa har zuciyarta take jin kamar yadda Danejo ke sallah ba haka ake yi ba, amma ta kasa ganewa da kuma tuna yadda ake?. "Ina Hamma Yabi?" Danejo ta kalli Dada tace "Mi naddi mo (na kira shi)". Jinjina kai Dada tai, Danejo sai kallon Dada take kamar zatai shiru sai kuma tace "Dada waye Baffa?" Da sauri Dada ta juya gabanta na faɗuwa sosai na rashin amsar tambayar Danejo tace "Kamarya Halisa? Baffa mahaifinku ne kuma ya rasu mene?" "Na sani Dada, ina dangin Baffana suke me yasa muke zaune a Rugar Rome?" A hargitse Dada ta ɗaga hannunta tare da ɗauke Danejo da mari sai kuma ta fashe da kuka ta ce "Wacce masifa ce wannan kika koya Dajeno? Bance miki nice Dangin uwa dana uba a gareku ba? Ban gaya miki ba Halisa?" Hawaye na sauka a fuskar Halisa ta ce "Kiyi haƙuri Dadana ba zan sake ba, ban san mene yasa nai miki wannan tambayar ba" kasa magana Dada tai saboda hakin daya fara cin ƙarfin ta, zuciyarta na bugawa da ƙarfi Danejo na ƙwala ihu ta shiga kiran sunan Hamma Yabi wanda ke garken shanu, tattara Dada Hamma Yabi yai zuwa wani ƙaramin asibiti dake gefen Rugar, suna zuwa kusan sune na farko amma abin mmki sai kwasar wasu ake ana barinsu sbd cin hancin da suke bawa Nurse's ɗin, har lokacin tashi yai ba'a samu damar duba Dada ba a haka suka dawo gida. Yola South Abti America Babbar makaranta ce Wacce ta kasance Private school tun daga primary school har zuwa University makarantar dake da ita, Abti America mallakin mataimakin shugaban ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na yanzu Atiku Abubakar ce. Makarantar na cikin Yola South ko ace Yola town duk ɗaya. Makaranta ce wacce sai ɗan wane da wane suke zuwanta duk wanda ka gani a ciki to ka tabbatar ubansa ya mallaki arziƙi ba dukiya ba. Adamawa/jimeta. Yola shi ne babban birnin jihar Adamawa. Yola South ana kiranshi da Yola town acan fadar lamiɗon Adamawa yake ma'ana gidan sarauta (LAMIƊO'S PALACE). Yola North, jimeta kenan. Acan fadar gwamnati yake, jimeta yafi kyau haɗuwa da tsari fiye da Yola South. Manyan abubuwa gaba ɗaya acan Yola North wato jimeta suke. Babu wani nisa tsakanin Yola South da Yola North/jimeta hasali ma roundabout ne ya raba tsakaninsu, akwai wani roundabout mai ƙwayoyin ƙwaryar nono da ludayi a kai muna ana kiransa da Yola roundabout, akan hanyar express yake daga shi sai wata ƙofa, to wannan ƙofar shine da zarar ka shigeta ka shiga yola kenan, sunan ƙofar “JIPPAJAM” da kuma “JAƁƁAMA” Ma'anar Jippajam shi ne Ka sauka lafiya. Wannan idan kazo fita kenan ta cikin yola zaka ganshi, idan shiga garin zakayi kuma za ka ga an rubuta Jaɓɓama ma'ana Sannu da zuwa. Njoɓoli wani ƙauye ne sosai dake cikin ƙauyukan dake zagaye da Yola south wato yola town,ƙauyen yawancinsu fulani ne makiyaya,amma akwai manoma ma, babu nisa da cikin gari, sannan suna da tashar mota mai tafiya ƙauyen a cikin yola. Wannan kenan. Tana tafe hannunta riƙe da sanda tana kaɗawa, a hankali bakinta ke motsawa tana karanta 1,2,3-10 cikin fillatancin karatunta bai nisa ba, babu arabi ba boko kuma ba za'a kirata da jahila ba,ita dai gata nan ne dai, ba wanka sosai ma'ana ba tsafta. Go'a 1 D'id'i 2 Tati 3 Nay 4 juy 5 Je go'o 6 haka ta dinga maimaitawa har ta ƙarasa can nesa da gate ɗin makarantar Abti America. Ajjiye ƙwayar kanta tai tare da neman waje ta zauna tana jira a tashi duk da cewa ba'a talla amma sbd ƙarancin masu sai da kindirmo yasa ake siyan nono a wajanta sosai. Tana zaune wata mota baƙa ta taho da gudu gadan-gadan zata take Danejo cikin tsoro da firgita har tana ture ƙwayar nonon Danejo ta miƙe tsaye tare da fasa ihu tana ƙanƙame jikinta idanunta rufe sbd gaba ɗaya motar kanta tayo da alama giyar motarce ta ƙwace. Motar na gab da taka Dajeno ba zato taji an saka hannu tare da yin sama da ita... 😌🫣 let's see yadda zaku amshi labarin HALISA DAJENO wanda ya faru a gaske bawai fiction story bane. *🌈 IDAN BA KE 🌈* Nimcyluv sarauta *_Arewabooks@Nimcyluv_* 2. Ihu Danejo ta fasa lokacin da taji an saka hannu tare da yin sama da ita cikin muryarta ta Fulani ta ce "Mi boni Dada'am mi nasti tati hande mi mayi" gaba ɗaya ta tsorata ta ɗauka motar za tabi ta kanta. Jin an direta gefe guda ya sanya ta buɗe idanunta a hankali a tsaye ta gansa nesa da ita kaɗan hannunsa harɗe a ƙirji yana ƙare mata kallo tare da nazartar yanayinta. Kasa daina kallonsa Danejo tai sbd yanayin shigar jikinsa wani farin yadi ne a jikin nasa amma yai baƙiƙƙirin sbd dauɗar daya haɗa gaba ɗaya yadin ya yayyage har ana iya ganin farar fatar jikinsa, sumar kansa rabi furfura rabi baƙa. Ajjiyar zuciya ta sauke da sauri kuma ta juya sbd ƙarar motar da taji sai a lokacin lura da shegewar motar cikin Abti America. Ƙugu ta riƙe tana fari da manyan idanunta cike da tsiwa ta ce "Shai mutum ya tsaya yaga yadda ake tijara aradu ina iya fasa gilahin moto ɗin" daga bayanta taji murya mai sanyi ta daki kunnenta ance "Zaki biya?" Juyawa tai ta kallesa mutumin ɗazo ne dai wanda ya taimaketa kafin motar ta bigeta, harara ta banka masa ta ce "Kai Almajiri Sukajo meye ruwanka dani? Ina ruwanka idan moto ya takani, da kayanka duk a yage" ta faɗa tana murguɗa masa baki. A hankali ya nanata kalmar “Sukajo” a ransa idan ya fahimta Sukajo na nufin “Saurayi” Girgiza kai kawai yai ba tare da yace mata komai ba ya juya zai bar wajan. Da sauri ta sha gabansa tana faɗin "hani inbano ina ka kai mini kindirmon shaniyata? Waye ya tittila a tumbinsa?" Juyawa yai tare da kallon ƙwayar nonon babu komai a ciki sbd tuni ta zubar da nonon dalilin tsoran da taji, amma ta kasa fahimtar ita ta zubar ɗin. Yana dai tsaye bai ce komai ba can kuma ya kalli cikin idanunta da sauri ta ɗauke nata idanun tana murguɗa masa baki cikin ƙasa da murya ya ce "Siya akai ai" baki ta buɗe ita ai ba taga wanda yazo ya siya ɗin ba kuma gaba ɗaya nonon aka siya kenan? "Ina kuɗin to ɗan Almajiri mai yagaggun kaya?" Da hannu ya nuna mata ƙasan ƙwayar yana rufe idanu da buɗewa ya ce "Gasu can" ta durƙusa ta ɗaga ƙwayar sai ga kuɗi da gudar dubu ɗaya da ɗari biyar guda biyu sai ƴan ɗari guda goma. Zaro idanu tai waje jikinta na rawa ta ce "Kai ɗan Almajiri mai ƙarya wannan kuɗin duk na kindirmona ne? Ai aradu kuɗin yai yawa" hannunsa dake harɗe a ƙirji ya wara tare da ɗaga kafaɗa ya ce "haka suka bayar ai" "su waye?" Shiru yai mata yana ƙoƙarin juyawa ta ce "Mene wannan a ƙafarka?" Zaro idanu waje yai tare da yin baya ganin tana ƙoƙarin zuwa inda yake yasa yai saurin faɗin "ke fillo bayanki" juyawa tai da sauri amma babu kowa a wajan tsaki taja tana kakkaɓe zanin jikinta ta ce "Mai ƙarya dai ɗan wuta" ta ƙare zancan tana ɗago kanta babu Almajirin kamar yadda ta raɗa masa suna babu ko inuwarsa sai wani farin Zomo data gani kyakkyawa dashi ya ƙura mata idanu, itama kafesa tai da idanu kamar zata kamasa sai kuma ta ɗauki ƙwayarta ta nufi bakin hanya inda zata samu motar da zata kaita Njoɓoli. Da idanu Zomon ya bita har tayi nisa sosai yana kallon sanda ta samu abin hawa, girgiza yai yana kaɗa kunnuwansa sai gashi ya koma mutumin ɗazo wanda take ce masa Almajiri mai yagaggun kaya. Murmushi yai mai kyau a kuma fili ya furta "Danejona" Da gudu motar mai ƙirar Toyota Rav 4 ta Ƙarasa shiga cikin compound na Abti American University Yola (AUN). A hankali akai parking motar a tsakanin jerin motocin da suke cikin harabar. Buɗe murfin motar tai cikin faɗa faɗa ta ce "No! I mean I lost my eye sight for a while, my Mom slapped me and i was very shouked da marin, Sbd kawai wancan banzan ya kai ƙarata gida i hate him wallah ai babu dole cikin aure ko? I'm 29 years mene ya sa za ana damuna akan wani aure?" Yanayin yadda take maganar kaɗai zai sanya kasan ranta ya ɓaci har buga kan motar take sbd zafin zuciya tsaki tai ta ce "No am okay nazo ganin Zahrah ne, i will catch you later" kashe wayar tai baki ɗaya tana fitowa daga cikin motar tunawa da yadda Yarinyar ɗazo da yadda ta firgita ya sanya tai Murmushi tana nufar hanyar wani office. Office ɗin ba kowa sai some of things da suke saman table zama tai tana danna number Zahrah. Zahrah na tsaye cikin hall ɗin da take lecturing wayarta tai ringing ta san babu wanda zai kirata at this time sai Surayyerh da sauri ta kalli students ɗin dake hall tana faɗin "Ok guys Conservation biology has two central goals 1. to evaluate human impacts on biological diversity and 2. to develop practical approaches to prevent the extinction of species (Soulé 1986, Wilson 1992)" tana faɗin hakan tace "You get it?" Gaba ɗaya suka ce "Yes Maaa" jinjina kai tai tana taɓe baki idanunta akan wani matashi da sauri kuma ta juya hannunta riƙe da Ink pen ta nufi wajan bord da sauri ta shiga rubuta. “What is Bachelor of Science in Conservation Biology?" Dake tana ɗaukar su course ɗin Conservation Biology Under Faculty of Sciences ne. Shiru duk sukai suka kasa bata amsa hakan yasa Zahrah sakin tsaki a file ta ce "Is an assignment, ba zan wasting time ɗina wajan yi muku explanation ba, i have so much work to do bye" wani daga cikin students ɗin ne ya miƙe yana dariya tare da ƙwaiƙwayar yadda Zahrah ke tafiya ya tsaya gaban ɗaliban ya ce "I have so much work to do bye... Big Maaaa The arrogant one I hate this woman. But i like her style" gaba ɗaya Students ɗin suka saka dry ba kuma kowa ke ƙaunar Zahrah ba, wulaƙanci da disga mutane ya mata yawa, kuma idan ta shiga hall babu wanda ya isa ya shiga ga bada Assignment da shegen text da Attendance. Zahrah na fita ta nufi Office a nutse take tafiya cikin takun isa da gadara tana sanye cikin wata atamfa Amarya collection mai tsada ɗinkin riga da skert ya kama jikinta sosai, idanunta sanye cikin farin cat eyes wanda ya ɗan haska ɓakar fatar jikinta she's classes and educated ƴar wanka ce ga tsafta da tarin ilimi. Ƙafarta dake sanye cikin Derby shoes ta tura cikin office ɗin tana ya tsona fuska ta ajjiye handbag ɗin L.v akan kujera idanunta akan Surayyerh ta ce "Lafiya dai?" Surayyerh taja tsaki ta ce "ina lafiya? Can you imagine yau Mom ce ta mareni sbd wancan banzan?" Buɗe idanu Zahrah tai kamar ba zatai Mgn ba sai kuma tace "mene abin damuwa?" "Zahrah mari fa? Wallahi ba zan ƙara ɗauka ba idan aka sake marina, Look at me am 29 going to 30 ace Mom bata bar marina ba?" Girgiza kai kawai Zahrah tai ba tare da ta ce komai ba. "Ina magana Kinyi shiru, wannan miskilancin naki na tsana fa" "uban me kike son nace maki Surayyerh? Your mother has been slapped you sbd kinyi kuskure sai nace bata kyauta ba? Babu abin da zaki iya sbd Uwa ce dole ki hqr" Zahrah ta faɗa cikin ɓacin rai. "i can't bazan iya jurewa ba" cewar Surayyerh "ok zaki rama kenan? Are you going to beat your mother?" Surayyerh ta girgiza kai cikin damuwa ta ce "A'a kawai zan faɗa mata kada ta kuskura ta sake marina, Nasan Uwa tace kuma sai tai ta dokana akan wanne dalili, ɓacin rana nake gudu" Kallon Surayyerh kawai Zahrah keyi kafin taja numfashi ta ce "Ina cikin damuwa Surayyerh na fara tsorata fa" Surayyerh ta ce "Damuwa akan me?" Hannu Zahrah ta ɗora akan cikinta ta ce "Am pregnant Surayyerh ina da ciki wata uku, kuma na gaji da zubar da ciki wallahi" zare idanu Surayyerh tai tana faɗin "Pregnant? ciki na huɗu kenan fa Zahrah? Kina da hankali kuwa? Wannan karan dole ki yafe cikin kin manta mai Dr yace miki ko?" Ajjiyar zuciya Zahrah ta sauke kafin ta kalli Surayyerh da kyau ta ce "I'm not ready for this, kin san ba aure gareni ba, idan na bar cikin na haihu me zance a gida? Me zan faɗawa Mimi? daman Kullum cikin faɗan naƙi aure take wai na girma da yawa, karatun boko ya buɗe min idanu yanzu kusan shekaruna 31 ne Surayyerh" Surayyerh ta numfasa ta ce "Me kike jira? Ki kira Deen mana kuyi magana ya turo iyaye kuyi aure, Mimi nada gaskiya Kinyi primary, secondary, N.c.e, degree, kinyi masters to what are you waiting for wanda ya shige kiyi aure, haba ai ta boko ai ta boko nifa idan yanzu ne wlh ba zan wata boko ba, shekara 31 ana abu ɗaya sai zallar iskanci kawai da kike kina zubar da ciki a banza, sai kin gama zubar da ƙwayayen da Ubangiji ya baki matsayin zuri'a a banza wlh" Tsaki Zahrah tai "wani lokacin wlh ke Mahaukaciya ce, ni kike tunanin zan iya auren Deen yanzu? Inda a yanzu nasan rayuwa nai boko naje ƙasashe kala-kala da ace ko secondary schl ban rufa ba shi ne zan iya auren Deen amma yanzu kam i can't, zanje hospital a cire cikin, da kike maganar haihuwa waye ya faɗa miki daman ina son raya da haihuwa da yawa ne? Abeg ta shi muje Madam am not in the mood" Surayyerh ita dai mamakin Zahrah take bata, ta rasa ita da Zahrah waye yafi laifi, ita tana ganin mahaifiyarta na takura mata domin har kusan zaginta take a zuciya, ta hanata jin daɗin rayuwa komai sai ta ce wai taji tsoran Allah, ita kuma Zahrah iyayenta sun sake mata duk abin da zatai babu me cewa dan me gidansu gidan boko ne a waye suke gaba ɗaya, hakan yasa Zahrah keta aikata alfasha hankali kwance. "Kinzo da mota ne?" Surayyerh na miƙewa tsaye ta ce "E, kefa?" Zahrah ta ce "A'a, ba zan iya driving ba wannan cikin duk ya sauyani muje kiyi dropping nawa gida" "ok let's go" Fita sukai Zahrah da Surayyerh aminai ne duk faɗan da za suyi har abada babu mai ji, su gama fushi su shirya. Mota suka shiga Surayyerh na driving Zahrah na gefe a haka suka bar cikin Abti America. Da idanu Dada take bin kuɗin da Danejo take bata, a sanyaye ta ce "Duk wannan?" "E, Dadana ɗan Almajirin mai yagaggun kaya ne yace mini aradu duk kindirmo ake siya dasu, kuɗin da yawa" Dada ta jinjina kai ba tare da tace komai domin magana bai dameta ba, tun bayan rasuwar Baffansu Danejo ta zama shiru-shiru sanadin hakan ciwonta ya sake yin tsamari. "Dadana nawa ce wannan?" Danejo ta tambaya tana nunawa Dada gudar dubu ɗaya, girgiza kai Dada tai bayan ta tsurawa dubu ɗayar idanu ta ce "Ban san sunanta ba, ki bari Hamma Yabi ya zo sai ki tambayeshi ko?" Miƙewa Danejo tai ta ce "Bari naje wajan Shatu na tayata irga Naggenmu" fita tai a hanya taci karo da Hamma Yabi, da sauri Hamma Yabi ya kama hannun Danejo ya shiga duba Funa, Fobbina, Wayla, Hirna. Ma'ana Gabas, Kudu, Arewa, da Yamma, ganin ba kowa yasa Hamma Yabi faɗin "Mun shigesu Danejo, gobe ake bikin gasar wasa da maciji, wanda Sarkin ruga yake sawa, kuma yau za'a zaɓi wanda za'ai wasan dashi" fararen idanunta ta juya sosai cikin rashin damuwa ta ce "Hamma mene abin damuwa, ni Dadana kawai nakeso ta samu lafiya ina ta mafarki wani kala" girgiza kai Hamma Yabi yai kaifn ya kama Danejo sosai ya ce "Baka iya wasa da Mashiji ba Danejo, kuma Sarkin ruga zai iya zaɓarki matsayin wacce zatai wasan, idan baki iya ba Mashijin zai iya saranki ki mutu murus, ko baki mutu ba idan baki iya ba Sarkin ruga zai iya korar mutum daga cikin Rugar Rome" cike da tsoro Danejo ta zaro idanu waje ta ce "Mi boni Hamma Yabi yaya zanyi?" "Yanzu shai mu jira muga wa za'a zaɓa, kije ki ɗauki kindirmo mai man shanu ki bawa Dada gobe zamu koma ashibiti" kai ta ɗaga alamar to Hamma Yabi ya nufi cikin jejin nemo wani sassaƙen magani ita kuma ta nufi wajan garke a nan ta samu Shatu ta kama bakinta a nonon Nagge tana ta sha hankali ƙwance. Zama tai kan wani Leggal (Icce amma kututture) samun kanta tayi da tunani wanne kalar Mashiji za'ai wasan dashi? Meyasa idan taje Birni take ganin wasu mutanan ba irinsu ba komai nasu daban ne, meyesa birni ta banbanta da Rugar Rome?. Ajjiyar zuciya ta sauke tana murza yatsun hannunta da sauri takai dubanta zuwa ga ƙadamin yatsarta idanunta ya sauka akan zoben dake maƙale da yatsar da tsananin mamaki take kallon hannu yaushe wannan abun ya zo hannunta? Mene sunansa ita bata taɓa ganin abu mai kama da zobe ba sai yanzu, ga wani zane a tsakiyar zoben kamar tambarin abu amma bata san ko mene ba, ƙoƙarin zare zoben take amma ta kasa hakan yasa dole ta hqr. Suna zaune a garken suka ji ana shelar Sarkin ruga yana neman jama'ar Rugar Rome baki ɗaya. Da Shatu da Halisa suka kalli juna zuciyarsu cike da zullumi amma Danejo tai ta maza ta kama hannun Shatu suka nufi wajan. A tsaye suka samu mutane wasu na sanye da fararen kaya na Fulani wasu kuma Kuraye yawancin su gaba ɗaya farare ne, amma sam babu cikakken addini ga rashin tsafta. Sarkin ruga ya gyara tsaiwa yana faɗin "Kamar yadda kowa ya sani, a gobe ne zamu gabatar da gasar wasan Mashiji, za'a zaɓi mutum ɗaya ya buga wasa da ƙaton Mashiji kamar yadda muka saba, idan mutum ya kashe Mashiji akwai kyautar Nagge da kuma ƙwayar nono guda hamsin, idan Mashiji ya kashe mutum Shi kenan wasa ya zo ƙarhe, idan mutum bai mutu kuma za'a kuresa daga Rugar Rome baki ɗaya, don haka yanzu zamu fito da alƙalin wasa ya zo ya zamu wanda za'ai wasan da shi" Shatu ta ƙankame hannun Danejo ita ko kalmar Mashijin bata so taji an faɗa balle ta gansa a gabanta. Dajeno kam shiru tai kanta a ƙasa tunani fal ranta domin gaba ɗaya ma hankalinta baya wajan. Alƙalin wasa ya fara zagaye mutane har ya shige kan Danejo gama dubawa yai sannan ya gyara murya ya ce "Mun zaɓi Halisa Dajeno Rome a matsayin wacce zata fafata da ƙaton Mashijin mu a gobe.... #Sarautar marubuta #True life story *🌈 IDAN BA KE 🌈* Nimcyluv sarauta *_Arewabooks@Nimcyluv_* 3. "Na shiga uku ta ya ya zan iya wasa da maciji? Wallahi kashe ni zai yi" Danejo ta faɗa a fili cike da tsora wanda ya sanya har ta kusan sakin fitsari gaba ɗaya ta firgita. Shatu ta ce "Ki faɗa masa ba zaki iya ba a zaɓi wata, idan Mashijin ya kashe ki na shiga uku na lalashe aradu" da sauri Danejo ta fito tsakiyar fili idanunta akan Alƙalin wasan muryarta na rawa ta ce "A yi mini afuwa Alƙalin wasan ba zan iya wasa da maciji ba aradu sarata zai yi" Alƙalin wasan ya kalli Danejo sosai, shi ya ɗan jima bai ganta ba, ta ƙara girma da wayo sosai ta zama ƴar budurwa irin girman ƙauyen nan dai. Sai rashin tsafta da addini dake ɗawainiyya da ita duk da ana ƙoƙarin ganin an magance hakan a cikin Rugar Rome. Murmushi alƙalin wasan ya sake yi cikin kulawa ya ce "Zaki iya mana? Ai Baffanki ya ƙware wajan iya sarrafa maciji, a wasan ƙarshe kuma macijin ya zama silar mutuwarsa, ki yi wasan ko dan ƙarasa cikawa Baffanki burinsa na zama gwarzo a Rugar Rome. Tabbas zaki iya Halisa Dajeno Rome" girgiza kai tai da sauri idanunta cike da hawaye ta ce "Ba zan iya wasa da maciji ba, mene ya sa sai ni? Baffana daban ni daban kalleni ƙarama ga maza nan da yawa a zaɓi wani daga ci" Sarkin rugar yai saurin faɗin "Ke aka zaɓa, kuma dole kiyi domin ba zamu taɓa sauya ra'ayinmu ba, ya zame miki wajibi muddin kina cikin Rugar Rome" a tsorace Shatu ta ce "Hande en boni, yau mun shiga uku" kasa cewa komai Danejo tai domin gani take kamar ma ta mutu ne lokaci kawai take jira. Da sauri ta juya idanunta cike da hawaye ta nufi cikin bukkarsu zuciyarta cike da zullumi da kuma fargabar abin da zai je ya dawo. A haka ta shiga cikin bukkar Idanunta akan Dada wacce take kwance cikin halin ciwo, domin a kullum ciwon nata ƙara tsanani yake. "Dada Alƙalin wasan ya zaɓi Danejo matsayin wacce zatai wasa da maciji a gobe" da sauri Dada tana jan numfashi ta kalli Danejo cikin damuwa ta ce "Mene ya sa baki cewa masa ba zaki iya ba?" Shatu tai saurin faɗin "Sarkin ruga ya ce wai dole tayi domin cika muradin Baffanmu" Dada ta miƙawa Danejo hannunta cikin kulawa ta ce "Waye yace muku Baffanku wasan maciji shi ne burinsa?" Danejo ta kasa magana sai ajjiyar zuciya take saukewa Shatu ce tai ƙarfin halin cewa "Sarkin ruga ne ya faɗa" Murmushin taƙaici Dada tai bata taɓa ganin zalunci irin haka ba, ta rasa me suka tsarewa Sarkin ruga da yake shirin ƙarar dasu ta hanyar kashesu da maciji wanda wasu suka tabbatar macijin tsafi ne. Cikin ƙonar zuci ta ce "Baffannku bai taɓa sha'awar yin wasa maciji ba, halima babu wannan al'adar ta wasa da maciji a Rugar Rome, daga baya Sarkin ruga ya samar da ita, bayan ya samar da ita ya zaɓi Baffanku matsayin wanda za'ai wasan dashi" shiru tai sbd tarin daya sarƙe mata numfashi, da sauri Shatu ta ɗauki ruwa ta bata, numfashi ta sauke kafin ta ce "Bisa dole Baffanku ya amince, yasha wahala kafin ya kashe macijn bayan ya samu raunuka wanda ya sa ya kwanta jinya, da shekara ta zagayo aka ƙara zaɓar Baffanku abin mamaki shi ne babu bambanci tsakanin macijin shekarar data shige da kuma wanda aka fito da shi, Baffanku ya tsorata, gashi idan ya ce ba zai ba to za'a kuresa daga Rugar Rome, tun daga wannan shekarar Baffanku ke gabatar da wasan Maciji, har zuwa shekarar da maciji ya kashe shi wanda kuma anyi hakan ne domin aga bayansa. a ruɗe Danejo ta ce "Kenan kashe Baffa akai Dada?" Dada ta girgiza kai ta ce "Ba zance ba, bani da hujja akan haka koma mene hukuncin na wajan Allah". Danejo taja numfashi cike da raunin murya na rashin sanin mafita zuciyarta cike da tarin zullumi ta kalli Dada ta Shatu ta ce "Dada ba zan iya ba, ina jin tsoro" "Halisa idan ba kiyi korarki za su yi daga cikin Rugar Rome, ni kuma ba zan jure hakan ba, Ubangiji na tare dake. Dole kiyi wasan imma ki mutu ko kiyi rai Kinji ko?" Kafin Danejo tai magana Hamma Yabi ya shigo da sauri idanunsa akan Danejo yana faɗin "Tashi mu tafi Danejo daman nasan bayanki suke son gani kamar yadda suka kashe Baffa" kallo Hamma Yabi Danejo tai idanunta ya kumbura sbd kuka ta ce "Hamma ina zamu?" Muryarsa na rawa ya ɗaga ta tsaye ya ce "Zanje na ɓoyeki sai an gama wasan zaki dawo, zan nuna ban san idan kike ba" Dada tai saurin cewa "A'a Yabi, kada ai haka kamar Halisa tare damu, idan ta tafi to Shatu ce zata maye gurbinta kasan haka ai" zama yai sosai ya ce "Yanzu haka zamu zauna? Ke baki da lafiya ita kuma muna kallo maciji ya kashe ta?" "Akwai Allah" Dada ta bashi amsa tana rufe idanunta. Halisa kasa bacci tai ga yunwa ga tsoro can cikin dare ta tuna ai ha tayi sallar issha ba, da sauri ta fito daga bukkar gaba ɗaya rugar shiru babu kowa sai wutar da aka kunnawa ko wanne garke dake ci hankali. Can bayan bukkarsu ta nufa tai tsari a wajan tai alwala babu ko shafar kai ta kwararan ruwan ta dawo. Sallar ma dungure tai Fatiha kawai ta iya cikakkiyar babu gyara. Yadda taga rana haka dare, dab da Asuba ta nufi garke tare da tatsar nono, tana gamawa ta Ajjiye. Gari na fara haske bayan tai sallah ta kaɗa shannun zuwa cikin jeji. Har zuwa lokacin bata da nutsuwa ita a yanzu ba wasan majin ya dameta ba, illar rashin lafiyar Dada idan har macijin ya kasheta waye zaici gaba da kula da Dada? Zama tai a gefen wani dutse ta shiga rusa kuka da iya ƙarfinta. Commissioners Quarter's Haɗaɗɗiyyar unguwa ce wacce take cikin Jimeta, iya haɗuwa da tsari unguwar tayi, wanda bai saba fita kasashen waje ba idan ya shiga Commissioners Quarter's zaka ɗauka a ƙasar turawa kake. Gidajene duguwa zaka gansu kamar tangaran sbd yadda suka haɗu aka zuba dukiya. Unguwa ce ya masu kuɗi wanda talaka sam bai isa ya shige ta ba. Unguwannin masu ci da gindin biro kenan. A hankali take sakkowa daga kan strains ɗin benan hannunta riƙe da waya tana latsawa, jikinta sanye da wani Short pencil jeans sai Balenciaga top a saman t.shirt ɗin jikinta. Ƙafarta cikin wani Hermes slippers. "Binta! Binta!!" Ta shiga kiran maid ɗin dake yi musu abinci tana zama saman Kujera, jinin Binta na rawa ta ƙaraso tana zubewa a gaban Zahrah ta ce "Hajiya gani" harara ta watsa mata cikin rashin ko ina kula ta ce "Kin san ban son buɗe murya sbd kawai zan kiraki?" Binta wacce a ƙalla zata iya yin shekaru 55 zasu iya kusan sa a da mahaifiyar Zahrah ta sunkuyar da kanta ƙasa cike da girmamawa ta ce "Afuwa Hajiya, ina can ina duba time table na list ɗin abincinki na me za a dafa miki zuwa dare" shiru Zahrah tai ba tare data ƙara cewa Binta komai ba, hankalinta yana kan wani abu da take searching akai, ita dai da karatun boko na yin magana a jikin mutum da tuni ya jima dayi a jikin Zahrah domin kaf gidan tafi kowa zurfi karatun boko shi ya sa take taka kowa hankali kwance. "Hajiya me kike buƙata?" Binta ta tambaya. Idanunta ta ɗaga ta kalli Binta a hankali taja tsaki ta ce "Nikam Binta na tambayeki?" "Ina jinki Hajiya" Zahrah ta gyara zama sosai tana ajjiye wayar hannunta a gefe kafin ta ce "Wai yaushe za kiyi hankali ki fahimci abin da nake buƙata, matsalar rashin ilimi kenan fa, gaba Binta ƙwaƙwalwarki bata riƙe abu ba lallai ko primary kin cika ba, wallahi na tsani harka da midille class,uneducated, villagers" da tsananin mamaki Binta ke kallon Zahrah ƴar cikinta ke faɗa mata wannan maganganun? "Kiyi haƙuri Hajiya" a fusace Zahrah ta ce "Sorry for yourself Binta, kije ki haɗa mini salad ki saka lemon sosai ciki" Binta ta jinjina kai tana Miƙewa tsaye tare da barin wajan idanunta cike da hawayen baƙin ciki. Wata mata wacce ta fito cikin parlourn ta kalli Zahrah ta ce "Why are you shouting?" Murmushi Zahrah tai ta ce "No Mimi ina game ne, akai mini game over" Zama Mimi tai ta ce "Ok, kwana biyu na jin labarin Deen a bakinki? Lafiya dai?" Zahrah ta ce "Baya nan ne Mimi" Mimi ta ce "Ai fa, naga idan yazo sai ku kai awa uku zuwa huɗu a part ɗinki kwana biyu shiru" Murmushi kawai Zahrah a haka Binta ta kawo mata haɗin salad ɗin. Mimi tabi Zahrah da kallo kafin ta ce "Wai lafiyarki ƙalou kuwa? Kullum cikin cin haɗin Salad kike?" "Lafiya Mimi, kawai zuwa makarantar nan ke sani gajiya da kwaɗayi naji bana son cin komai" Mimi ta jinjina kai ta ce "Lallai, ni banga me zaki da kuɗi ba da kuka zaɓi lecturing Zahrah" ba tare da data amsa ta ba ta ce "Mimi ina Daddy ne?" Mimi ta ɗauki waya ta ce "Jiya ya dawo, but yaje kano wajan wani babban abokinsa" "Ok" cewar Zahrah a nutse Mimi ta kalli Zahrah cikin damuwa sosai ta ce "Fatima-Zahrah yaushe kike tunanin yin aure ne, boko kin gama ta, completely sai abin da yai saura, familyna sun fara mini surutu akan wai na zuba miki idanu, wasu har cewa suke maybe yawonki kawai ki ke, ni dai nasan ba haka bane i trust you babyna" marairaicewa Zahrah tai kamar ƴar 20 nan kuwa shekaru 31 take da shi. "Mimi kin san familyn nan naki basu san darajar karatun boko ba, ta ya ya zan haɗa karatu da aure? Kana yin auren kuma ace ka haihu, kuma ba zan iya haɗa aikina da aure ba gsky Mimi a barni zuwa 35 na gama komai sai na fara tunanin auren, su kansu mazan ai mai ilimin boko suke buƙata ba kuwa ya damu da ilimin addinin nan ba, suna buƙatar mace wayayyiya a very educated women" murmushi Mimi tai cike da gamsuwa da maganar ƴarta kafin ta ce "Na fahimta, ko Dadynki sai dana kammala University mukai aure muna dai soyayyya a waje, dake kuma na wuri na shiga shcl shi ya sa na gama before we getting married" jinjina kai kawai Zahrah tai hankalinta akan salad ɗin da take ci sbd yadda cikin jikinta ya sanya mata kwaɗayi kala-kala. Da sauri Mimi ta ce "Subuhanallahi, maza kunna mini Plasma ɗin nan ki jonata da DS.TV tafsirin Sheikh sai shigeni" kwaɓe fuska tai kafin ta ce "Mimi wai kin damu da wani Sheikh, ni wallahi ban son tafsirin ɗin ko kaɗan, ga wata ƙinƙina da yake, da ƙyar fa yake iya karatun sbd ƙinƙina wani time ɗin har hawaye yake to me za'a gane?..." Da idanu Mimi tabi Zahrah tana mamakin jikar ƙirjinta a kullum "To ai kuwa da yadda, ƙinƙina kuma ai larura ce kuma a hakan Ubangiji ya ba shi bawai Zahrah". Gudu take sosai hankali a tashe sai haki take ita kam sam ba zata iya irin wannan wasan na sai da rai ba, wacce ƙaddara ce take shirin bibiyarta ne? Tsayawa tai tana mai da numfashi, sai a lokacin idanunta ya sauka akan wasu fararen Kurciyo masu kyau da tsari ita a rayuwa tana son ko wacce kalar dabba ta daɗe tsaye tana kallonsu, ɗaya daga cikin kurciyoyin ya tsora mata idanu. Tunawa da tai ana gab da fara wasan macijn ya sanya ta ƙara saurayi domin samun wajan ɓoya. Girgiza kurciyoyin sukai wata iska da guguwa ta mamaye ilahirin wajan iskar data kasance mai daɗi sosai wacce ta haddasawa Halisa Dajeno rufe idanunta wani barci na fisgarta a hankali ta sulale a wajan babu jimawa barci mai nauyi ya ɗauketa. Kurciyoyin suka rikiɗe zuwa wasu samari masu zubin halitta ɗaya daga ciki wanda yake sanye da farar Alkyabba mai taushi wacce ta sauka har ƙasa ta rufe masa ƙafafuwansa yaja numfashi a hankali cikin ƙasa da murya ya ce "Danejona ba zata iya wasan nan ba" ɗayan dage gefensa ya ce "Haba Prince me ya sa kake da taurin kai ne? Sarki yace ka yanke duk wata alaƙa tsakaninka da bil-adam musamman wannan yarinyar Danejo amma kaƙi" murmushi mai taushi Wanda aka kira da Prince yai yana sake kallon Halisa Dajeno ya ce "A wannan karan ba zan iya yiwa Sarki biyayya ba, babu haɗi tsakanin mutum da aljani, amma kasan ba zan iya zutar da wani rai ba, muddin idan ba Danejo zai cutar ba? Na jima a jikin mahaifiyar Danejo tun tana da cikinta, amma rana ɗaya akai mata magani suka rabani da ita, wanda ya sanya na kwanta jinya, wannan dalilin yasa na koma kan ɗiyarta Danejo na shirya duk wani abu da sarki zai faɗa, ƙarshe dai ya ce zai koreni daga duniyar Aljanu ba?" Ɗayan zai magana Prince ya daka mishi tsawa ya ce "Ka saurara mini Safwan" ya faɗa idanunsa na juyewa zuwa kalar na aljanu a tsorace Safwan ya ce "Afuwa nake Yariman Aljanu, yanzu me ka shirya akan raba Danejo da wasan macijin nan?" Gyara Tsaiwa Prince yai tare da durƙosawa daidai inda Danejo take kwance tana barci ya ɗauke ta cikin nutsuwa ya ce "Ubangiji nake nema ya bani Sa'a, ina son Matata bana jin zan jure ganinta da duk wani wanda zai cuceta, balle kuma ya taɓa mini ɗana dake cikinta" buɗe baki Safwan yai da Mmki yace "Prince yaushe ta zama matarka? Har kuka samu ɗa?" Murmushi Prince yai yana shafa cikin halinsa wanda yake jin farin ciki na ratsa masa zuciyarsa kafin ya ce "Matata ce ita ɗin, duk wanda ya shirya rabani da ita to ya shirya zuwansa lahira, bani da lokacin magana Safwan, maza ku ɓace daga wajan nan" kamar gilmawar walƙiya haka suka ɓace, nan da nan Prince ya rikiɗe zuwa Almajiri mai yagaggun kaya. A nutse ya fara tafiya da ita zuwa cikin Rugar Rome dai da yaje daidai bakin bukkar su Danejo ya ajjiyeta da sauri ya bar wajan, sbd gaba ɗaya jama'ar Rugar suna filin da za'a gabatar da wasan Maciji. Prince ya ce "Ubangiji ka bani Sa'a da nasara" yana faɗin hakan yai Girgiza nan take ya zama ƙaton wani baƙin maciji mai narkeken kai a hankali ya sulale ya fara tafiya tsakanin bukkokin Rugar Rome har ya Ƙarasa wata bukka kai tsaye ya kutsa kansa ciki, kwance ya samu wani maciji shima baƙine sosai, da alama shi ne macijin da Matarsa Danejo zatai wasa dashi. Kallon kallo aka fara tsakanin Maciji Prince da kuma Macijin da Danejo zatai wasa dashi. Kamar haɗin baki haka suka fasa kai a tare lokaci guda kuma suka nufi kan juna. 🫣Bala'i🚶🏽‍♀️kada a manta labarin ya faru a gaske babu ragi babu ƙari👌🏾. Muje zuwa #Sarautar marubuta #True life story *🌈 IDAN BA KE 🌈* Nimcyluv sarauta _*Arewabooks@Nimcyluv*_ 4. A kusan tare macizan guda biyu suka ƙara fasa kai tare da kaiwa juna sara, ko wanne maciji ƙoƙarin jiwa ɗan uwansa ciwo yake da ganin ya kashesa har lahira. Gaba ɗaya macizan suka sarƙafe juna tare da nan na ɗewa waje guda ko wane huci yake yana fitar da hayaƙi ta baki nisan yadda Prince wanda ya a rikiɗe zuwa maciji ya matse macijin da Za'ai wasa dashi, gaba ɗaya ya ji masa rauni a hankali kuma Prince ya buɗe bakinsa ya fara haɗiye Macijin zuwa cikinsa sai daya haɗiyesa tsaf kafin ya sulale gefe guda ya kwanta yana mai da numfashi Wahala, sai fasa kai yake kamar zaici babu zuciyarsa tayo sama baki ɗaya zai iya sarar ko waye a wannan lokacin. Sarkin ruga ya kalli tarin jama'ar da suke wajan hadda Shatu da Hamma Yabi, da sauran mutanan rugar kafin ya numfasa ya ce "Lokaci ya yi ake a kawo mana Halisa Dajeno Rome cikin fili, domin su fafata da maziji yau ranar tace" Wani mai suna Giɗaɗo ya rusuna tare da faɗin "Yanzu za'a kawota" yana faɗin hakan ya kalli Hamma Yabi tare da faɗin "Maza jeka kawo ɗiyar taku, tana ɓata mana lokaci" Hamma Yabi ya ce "Yanzu za'a kawota" yana faɗin hakan ya juya da sauri ya nufi bukkarsu tun daga nesa ya hangeta kwance a bakin bukkar inda Prince ya kwantar da ita tana barci. Cikin sassarfa ya ƙara yana faɗin "Assha Subuhanallahi barci a ƙasa Danejo" ya faɗa yana ɗagota tare da jijjigata sosai, da sauri ya buɗe idanunta tana zabura "Hamma Yabi yaushe na dawo nan?" Kallonta yai ya ce "Kina nufin baki san lokacin da kika kwanta a nan ba?" Girgiza kai tai ta ce "Aradun Allah ban shina ba, kawai naji iska mai daɗi ta lulluɓeni wani barci yazo mini daga nan ban san komai ba" Girgiza kai yai yana kama Hannunta ya ce "Danejo ƙurushiya, maza muje sarkin ruga na jiranmu" dafe ƙirji tai cike da tsoro ta ce "Na shiga uku na lalashe, Kur'ani na manta yanzu hamma yabi shikenan mutuwa zan, zan mutu na bar Dada? Zan mutu banyi karatu na zama babbar mace ba? Don Allah kada na mutu yanzu bana son wasan nan" rirriƙeta Hamma Yabi yai sosai ya ce "Ma zaki mutu ba Danejo, sai na kai ki burni Kinyi karatu kin zama babbar mace abar ƙwatance, sai kin zama mace ta farko wacce zata kawo sauyi cikin Rugar Rome, ki daina kuka kinji" kai ta ɗaga masa kafin da sauri ta ce "Kuma zan zama wannan mutumin na jikin bango?" Zare idanu Yabi yai kafin ya ce "Wannan gwamna ne fa" murɗa baki tai cikin shagwaɓa ta ce "Ni dai irinsa nake son zama" Yabi ya dungure mata kai ya ce "Aradu ƙarya kike, ina zaki iya yin siyasa tayaya zaki zama gwamna daman mata na zama gwamna ne?" Banza tai masa bai ƙara ce mata komai ba ya jata zuwa filin da za'a gabatar da wasan. Giɗaɗo dake tsaye shi da Sarkin ruga suna jiran zuwan Hamma Yabi da Danejo ya ce "Me ya sa ka zaɓi Danejo kasan ba zata iya wasan ba" murmushi Sarkin ruga yai kafin ya ce "Ina son ganin bayanta ne, kuma a hankali zan ƙarar da zuri'ar Manga a cikin Rugar nan, wannan macijin na tsafi ne hatta mutuwar Manga ni na shiryarta"... "Amma me Manga yai maka haka?" Cewar Giɗaɗo. Sarkin ruga ya ce "Sirri ne.." kaifin su ƙara magana Hamma Yabi ya ƙaraso hannunsa riƙe da Danejo wacce ta ƙanƙamesa sosai jikinta na rawa da ɓari. Alƙalin wasan ya ce "Yawwa yanzu zamu fara, Danejo ta shigo cikin fili jama'a ku buɗe idanunku da kyau yau za kuga wasa wanda baku taɓa ganin irinsa ba" Halisa Dajeno Rome na tsakiyar fili ko kuka ta kasa a wannan lokacin ta tsaya ne kawai tana jiran taga ta inda mutuwa zata zo mata, domin abune mai wahalar gaske ace yau ta rayu ko ta tsira da ranta. Sarkin ruga ya bada umarnin a fito da Macijin, da sauri Alƙalin wasan ya nufi bukkar da macijin yake. Yana kwance sharkaf yau lamo a ƙasa tare da yin gammo da jikinsa, wani irin zabura yai tare da fasa kansa a lokacin da alƙalin wasa ya shigo cikin bukkar, ƙuri yai masa da idanu yana ƙare masa kallo. Ko me ya tuna Ohhu a hankali ya fara sauka daga dokin zuciyar ya koma ya kwanta, shi kansa Alƙalin wasan ya tsorata jikinsa na rawa yasa hannu ya ɗauki Macijin da ƙyar sbd nauyin da yake da shi. Tun da Halisa Danejo Rome ta saka idanunta akan macijin taji gabanta ya faɗi, jikinta ya ɗauki rawa hawaye suka fara sintiri a saman Fuskarta, bata taɓa ganin maciji mai girman wannan ba, tama rasa wacce kalar addu'a zatai duk da ba wani abu ta iya sosai ba. Alƙalin wasan ya ajjiye macijin nesa da Halisa, aka fara kallon kallo tsakanin Danejo da Macijin, an shafe tsayin wasu daƙiƙo aka rasa waye zai fara kaiwa wani hari tsakanin Danejo da Maciji Prince?. Zaro idanu tai waje ganin ya fara warware tare da yin tsayi sululuuuu kuma ya nufo inda take, tana ja baya yana biyota har ya ƙaraso dab da ƙafarta tare da tsorawa zoben hannunta idanu. Juya tai tana neman inda zata gudu can idanunta ya sauka akan wani ƙaton dutse. Da sauri ta ɗauka tare da riƙewa a hannunta, ganin haka yasa Macijin bin ƙafafuwanta suuu haka ya dinga sufa a jikinta, har ya naɗeta ciff kansa daidai Fuskarta yana tsora mata idanu tare da kallon cikin idanunta. Jirkinta na ɓari ta ɗaga dutsen tare da kwaɗa masa a tsakiyar kansa, wani kalar ihun azaba macijin yai yana fasa kai kamar zai sarata, sai kuma ya saki kansa tare da ɗorasa saman ƙirjinsa gaba ɗaya naman Macijin rawar azaba yake, kansa tuni ya fashe ya fara zubar da jini. Ganin nasarar da Halisa Danejo Rome ta fara samu yasa Hamma Yabi da Shatu tare da sauran jama'ar Rugar Rome suka fasa ihun murna, Sarkin ruga da Alƙalin wasan hankali tashe suka kalli juna tare da faɗin "Me ya samu macijin nan? Ki dai asiri akaiwa Yarinyar nan?". Halisa a tsorace Macijin a tsorace amma a haka cikin dakiyar zuciya ta ƙara ɗaga dutsen a karo na biyu ta ƙara bugawa Maciji, Innalillahi a wannan lokaci kururuwar da Macijin yai sai da kowa na wajan yaji, jini ya sake ɓalle masa a hankali ya sulale ƙasa baya ko motsi alamar ya mutu... ajjiyar zuciya ta sauke haka kurum taji kuka ya ƙwace mata, durƙushewa tai a wajan ta shiga rera kuka tausayin macijin ya kamata musamman yadda taga jini na zuba a jikinsa, Hamma Yabi ya ƙaraso wajan Halisa Dajeno Rome tare da ɗagata yana dariya ya ce "Danejon Dada kin kashe macijin, kin kashe sa bana faɗa miki cewa ba zaki mutu ba? Zamu samu ƙwayar nono da Nagge masu yawa" ƙanƙame Hamma Yabi tai cikin kuka ta ce "Bana so Hamma Yabi, mu bar nan wajan kaina juyawa yake, bana son ganin jinin nan kaji" hannunta ya kama sukai gefe guda. Cike da taƙaici Sarkin ruga yake bin Macijin da kallo bai taɓa tunanin haka ce zata kasance ba, cike da baƙin ciki ya amshi wani sanda ya shiga kwarɗawa macijin aka tun macijin na motsi har ya daina jikinsa yai face face da jini tare da raunuka. "Ka ɗauke sa ku cillar a gefen gaɓar ruwa wani abin yai kalace dashi" Giɗaɗo da Alƙalin wasan suka ɗauki Macijin tare da nufar cikin jeji da shi. Suna zuwa suka cillar gefe guda da sauri suka juya cikin Rugar Rome. Sanyin gaɓar ruwan daya ratsa cikinsa ya sanya ya fara Girgiza yana juyi tare da murmurɗe jinsa gefe guda, wani kalar ihu yake mai nuni da azabar da yake ciki, ya daɗe cikin wannan halin kafin yai Girgiza tare da rikiɗewa ya dawo siffarsa yadda yake fitowa a mutum ba Aljani ba, yana kwance sambal gefen ruwan Farar Alkyabbar jikinsa duk ta ɓaci da jini. A hankali ya ɗaga hannunsa tare da dafe kansa inda yake zubar da jini, runste idanun yai sosai cikin ƙasa da murya ya ce "Ya Allah" yana nan ƙwance yaji iska ta mamayesa baki ɗaya kafin kace wani abu iskar ta ɗaukesa zuwa sama. Duk farin cikin dasu Shatu suke ciki banda Danejo rasa abin da yake mata daɗi tai, gashi jinin Dada ya matsa ga tunanin dake wanzuwa a cikin zuciyarta. Dada ta kalli Shatu ta ce "Farin ciki za kiyi Halisa ba damuwa ba, da tuni an rabani dake Allah bai ba, akwai ƙaddarorin da suke biye dake, amma duk wahala duk tsanani waya rana zaki zama abar ƙwatance tabbas zaki samu miji wanda zai kula da maraicinki" Danejo ta ce "Dadana nifa ba marainiyya bace, ina dake ga Hamma Yabi ga kuma Shatu" jinjina kai Dada tai idanunta akan zoben hannunsa Halisa ta ce "Ina kika samu wannan Halisa?" Girgiza kai tai cikin damuwa ta ce "Ban sani ba Dada, kawai na gansa a hannuna"... "Bana son ƙarya fa" da sauri Halisa ta ce "Da gaske nake miki, kalli kiga" ta faɗa tana nuna mata tambarin zoben, Dada ji tayi kansa ya sara idanunta akan Zoben da sauri ta riƙe kanta tare da rufe idanunta, kamar mai son tuna wani abu babu abin da take gani a cikin idanunta sai tambarin masarauta dake manne cikin zoben. Ganin yadda Dada ta rirriƙeta kanta ya sa Hamma Yabi fita da gudu ta tatso mata kindirmo mai zafi, da taimakon Halisa Dajeno Rome suka bawa Dada kindirmon nan da nan zufa ga shiga saukar mata bacci ya ɗauke ta. Juyawa Halisa tai ta kalli Shatu dake barci a nutse ta kalli Hamma Yabi ta ce "Hamma yaushe Dada zata samu lafiya ne? Kullum a ƙwance take ina tsoran na rasa ta aradu" Hamma Yabi ya kama hannun Danejo ya ce "Ba zaki rasa Dada ba, gobe zan koma asiti bamu da kuɗin kai ta asibitin burni" Da sauri Danejon ta ce "A siyar da Nagge to" zare ido Hamma Yabi yai ya ce "Aradu ƙarya ne, Uban waye zai taɓa Nagge ai mu dasu mutu karaba" ba tace masa komai ta miƙe tsaye tare da yin waje lokacin rana ta faɗi, can gefe ta nema ta zauna ita ɗaya sai tunani take a haka har akai magariba tana zaune, ganin duhu ya fara yasa ta miƙe tare da zagayawa bayan bukka ta kwaɓe kayan jikinta, halittar jikinta ta tsorawa idanu, musamman ƙirjinta tana mamakin abun mene amfaninsu a jikinta? Ita a gareta basu da wani abu kullum sai dai su ƙara girma. Ruwa ta sheƙa babu ko sabulu tana gamawa tai alwala, wasu kayan fulanin ta ɗauka farare ta saka tare da Ajjiye waɗan can, da sauri tai sallah tana gamawa taci tsiran da Hamma Yabi ya kawo musu, tana ci ta kwanta barci domin da wuri take son zuwa kiwo ta dawo ta tafi tallan kindirmo. Ciki zafin nama Prince ya saka hannu tare da ɗauke Safwan da mari ya ce "Ka fita a sabgata, kaje ka faɗawa Sarki halin da nake ciki ya ɗaukeni, kuma kasan yana gab da rabani da matata wanda ba zan iya jure hakan ba sam" Safwan ya kalli Prince cike da mamaki ya ce "Ban taɓa ganin mai taurin kai a duniyar Aljanu irinka ba Prince, cutar da yarinyar nan kake fa, babu haɗi tsakanin mutum da Aljani na faɗa maka, abin kunyane ka rasa wacce zaka so sai Bil adam? Allah zai saka mata fa" banza Prince yai da Safwan a wannan lokacin rabinsa na mutum rabi kuma na siffar Aljani da sauri ya juya zai tashi sama Safwan ya ce "Ina zaka? Ba dai wajanta ba?" Prince ya ce "Ba zan iya yin wasu daƙiƙo ba, ba tare da naga matata ba, da matata nake son kwana a yau ɗin nan" yana faɗin haka ya ɓace ɓat kai tsaye Rugar Rome ya nufa. Halisa juya cikin barci taji wani sanyi na ratsa mata jiki, ga wani mafarki da ke ƙafafuwanta sai motsawa suke amma ta kasa koda motsi bada ji take kamar ana danneta. Can dai ta farka a firgice Innalillahi a ruɗe ta fara kallon inda take, tana kwance tsakiyar dokar daji ba gida gaba ba gida baya... Waye ya kawo Halisa Dajeno Rome cikin dokar daji?... #Sarautar marubuta #true life story *🌈 IDAN BA KE 🌈* *_Arewabooks@Nimcyluv_* https://wa.me/+2348119237616 5.. A zabure ta miƙe tsaye tana ƙarewa cikin dokar dajin kallo, babu abin da ya bata mamaki irin yadda taga an sauya mata kayan jikinta, daga na Fulani zuwa na wasu saƙi farare masu kyan gaske. Jikinta na rawa sbd tsoro da tarin fargabar dake ratsa dukkan wasu lunguna na ƙofofin zuciyarta ta shiga ƙarewa jikinta kallo. Idan hankalinta yai dubu to ya tashi ta ƙara razana da halin da take ciki a yanzu, domin ba iya kayan jikinta da aka sauya mata ne kaɗai ya bata mamaki ba, zanan jan lallen data gani kwance a hannunta shi ne ya ƙara ta hanyar mata da hankali, ga sumar kanta da akai mata wasu irin kalba manyan gwanin sha'awa ita bata taɓa ganin kanta yai irin wannan kyan ba sai yau. Waye ya kawota nan Meke shirin faruwa da rayuwarta ne, ina Dadarta?. Ƙare wa cikin dajin tai babu ko hanyar da zata bi ta nufi Rugarsu, daɗin daɗawa ita kanta bata san a inda take ba, wacce kalar rayuwa ce haka? Daga yin barci kuma sai mutum ya farka ya gansa a tsakiyar daji? Bayan tasan a bukkar Dada tai barci. Tafiya ta shagayi idan ta kalli gabas da Arewa, guda da yamma sai ta saki kuka tare da faɗin "Na lalashe jama'a ina nake ina rugar rume tayi, ina Dadata, ina Shatu, ina Hamma Yabi duk kuna ina wayyooo Hande en boni, Yettore jaumirawo" ta faɗa ɗora hannunta aka tare da sakin kuka, ta fiya kawai cikin dokar dajin tun tana kuka har tai shiru sai idanunta da take rarraba wa a ciki dajin. Kukan da tayi da kuma gudun data jima tana yi sune suka taru suka haifar mata da wata gajiya wacce ta sanya ko idanunta bata iya buɗewa sosai sbd yadda kanta ke juyawa da kuma yunwar data keji, lokaci zuwa lokaci tana buɗe idanunta tare da zubawa zanan lallen hannunta idanu, tana cikin wannan hali ta ƙaraso wani waje wanda yake da rana sosai hakan yasa Danejo ta wahala fiye da zaton mutum, ga ƙishin da take ji. Daurewa tai taci gaba da tafiya sai dai duk yadda takai da daurewa ta kasa bata san lokacin da jiri ya kwashe ta ba, tai baya luuu zata kifa da sauri aka tareta ana faɗin "Subuhanallahi" mutumin ya faɗa a taushashe yana mai riƙe Danejo wacce ta faɗo jikinsa babu numfashi alamar ta soma kenan. Kyakkyawan idanunta mai ɗauke da kuriyar ƙwayar ido su ya ware akan Danejo yana mai ƙara jin nutsuwa na saukar masa a jikinsa, a hankali a kuma dukkan wata ƙaunarta ta shiga nunkuwa a zuciyar Prince Bilal. Yanzu ne zai samu cikakken lokacin kasancewa da ita, irin kasancewar nan ta har abada domin baya jin akwai mutumin daya isa ya raba shi da Matar Danejo a cikin wannan Dajin, zai zauna da ita zai rayuwa da ita, tai ta haifa masa yara, ya kuma yi alƙawarin ba zata taɓa sanin shi aljani bane, zaici gaba da zuwar mata a suffar Balarabe kamar dai suffar wani Sheikh ɗin Malami. Ɗaukarta ya yi a hannunsa zuwa gaɓar wani ruwa, jallabiyar jikinsa ta sauka har ƙasa tare da rufe masa ƙofatonsa, a haka ya Ƙarasa tare da kwantar da ita a gefen ruwan wajan da yake da ɗan danshi danshi musamman daya lura da jigatar da tai duk da cewa duk wani abu da take akan idanunsa ne. Yana kwantar da ita ya zauna gefenta idanunsa na juyawa tare da sauya launi zuwa wata kalar, hankalinsa ya karkata gaba ɗaya zuwa cikinta idan yake hango ɗansa dake maƙale a mararta hakan sai cike da farin ciki Prince ya saki Murmushi bakin na rawa ya ce. "Ubangiji ya saka mini sonkiwa zuciyata, tun kina cikin mahaifiyarki, zanci gaba da sonki ba zanyi saken da za a rabani dake ba, kamar yadda aka rabani da mahaifiyarki tun tana asalin inda take rayuwa" shafa cikin nata yai idanunsa na tsiyyayar da wani ruwa ya ce "Babu alaƙa tsakanin mutane da Aljanu, amma naji a wannan karan dama Ubangiji a suffar mutane ya halittoni, mene yasa bakwa iya ganinmu a suffarmu ta zahiri sai dai mu muganku? Ina son ki matata Danejo,ina gab da ɗaukeki zuwa duniyarmu" dariya ya saka gaba ɗaya wajan ya ɗauki rawa da Girgiza can kuma ya ɓace da wajan. Acan Rugar Rome kowa gari na wayewa suka saba Danejo na tashi zuwa garken Nagge ƙara tatsar nono, hakan yasa Dada bata damu ba sbd ganin Danejon bata cikin bukkar sai Shatu dake kwance a gefe tana barci, Hamma Yabi ya fita tun sassafe zuwa asibitin dake gefen Rugar Rome domin samawa Dada layi. Yana tsaye a a ɗan wajan da mutane suke tsayawa gaba ɗaya mutanan ba sufi mutum goma ba, suna zuwa kamar mutum biyar zai koma ya ɗakko Dada. Wani Likita ne hannunsu riƙe da waya yana dubawa ya raɓa ta gefen Hamma Yabi ya shiga office, Fuskarsa ɗauke da fara'a ya kalli mutumin dake cikin office ɗin ya ce "Dr Hamza na ganka a zaune ina patients ɗin?" Dr Hamza ya dubi Dr Iliya yana ƙara ware idanunsa ya ce "Patients suna can waje, bani da time na duba su serious,idan zaka shekara kana duban jama'ar Rugar nan ba zaka taɓa samunsu da cikakkiyar lafiya ba, ƙazanta ita take ƙara lalata musu lafiyar jikinsu na gaji wallahi, sai Shegen son shanunsu amma basu san yadda zasu kula da lafiyar jikinsu ba" Dr Iliya yaja kujera tare da zama sosai yana faɗin "Ai Dr Hamza sai haƙuri, kasan cikin karkara musamman ruga haka ba komai suka sani ba, kai dai barsu da arziƙinsu wato Nagge su kawai suka sani" Dr Hamza ya ce "Let's leave this matter, it is not in front of me" ya faɗa yana duba wani file, "I got the message you want to see me up, lafiya dai kake mini kiran gaggawa haka?" Dr Iliya ya tambayi Dr Hamza cike da jin don abin dake faruwa. Gyara zama Dr Hamza ya yi kafin ya ce "The government has given free medicine to the people of Ruga, maganin da gwamnati ta bayar suna da yawa, akwai maganin Suger, Hawan jini, Maleriya, da sauran maganin cuccutikan, yawwa sai maganin sikila irin folic acid, Paludrine, Peniciillin V,Hydroxyurea. Anfi kawo maganin Sickler sbd yawaitar samunta da ake cikin karkara, shiyasa nace a kiraka" cikin jin Daɗi Dr Iliya ya ce "Masha Allah yanzu yaya za'ai kenan?" Wani kallo Dr ya Hamza yaiwa Dr Iliya kafin ya ce "Ya kowa za'ai? Kasan Rugar nan ko an basu magani a banza, basu san important ɗinsa ba, so that zamu kwashi 88% a cikin 100 mu siyar mu raba kuɗin, kai ba kana da chamist ba? Sai ka zuba kawai acikin chamist ɗin naka" cike da gamsuwa Dr Iliya ya ce "that's good, amma gwamnati ƙoƙari sosai fa, banda haka wannan maganin sunfi ƙarfin miliyan 3 da wani abu fa,ana kula yanzu da ɓangaren lafiya sosai da masu juna biyu, anywhere zuwa dare zan zo da mota na ɗauki rabona" Sallama sukai tare da fitowa a tare ganin hakan yasa Hamma Yabi saurin kallon Dr Hamza ya ce "Aradun Allah na shafe awanni a nan gashi muna ta jira" a faɗace Dr Hamza ya ce "Wai kai fillon nan wani irin banza ne bagidaje ne kai? You doesn't know anything akan asibiti ka addabi mutane da wautarku ta Fulani, mu bamu da wasu kayan aiki cikin Asibitin nan kana kallo da idanunka ai, dan haka kada ka sake zuwa idan an kawo kayan aiki zamu sanar get out" jiki babu ƙwari Hamma Yabi ya koma cikin Rugar Rome, yana zuwa ya sake tarar da wani tashin hankalin babu Danejo gaba ɗaya acikin Rugar, sanadin hakan yasa jikin Dada ƙara rikicewa abu kamar wasa duk inda suke tunanin ganin Danejo babu ita sam har kusan kwana biyu. Tunda ya kwantar da ita a gaɓar ruwan har gari ya waye ta kwana a wajan, wani daren ya yi ta sake kwana, kwana biyu kenan amma bata motsa ba. Bata kuma da ranar tashi sai lokacin da Ubangiji ya nufa ko kuma ya tsara. A can cikin barci ta fara mafarki gata da namiji suna kasancewa waje guda, wani abu mai kama dana auratayya na gilmawa a tsakaninsu. Numfashi ta sauke tana motsa ƙafafuwanta zuwa cinyoyinta da suke mata zafi, tana jin kamar an daddaneta a firgice ta farka tana kurma ihu tare da kiran sunan Dada, ba addu'a babu komai. Cikin tsoro ta fara bin jikinta da kallo babu komai lafiyarta ƙalau domin ba wani sauyi da taji. Ajjiyar zuciya ta sauke a bayyane tare da kifa kanta a tsakanin cinyoyinta ta shiga rera kuka, kenan haka rayuwarta zata ƙare cikin dokar dajin ko yaya ne? ya akai ta tsinci kanta a dajin gaba ɗaya ta rasa amsar tambayoyin zuciyarta. A hankali ta fara jin dariya na karaɗe wajan, tare da surutu ƙasa ƙasa. Miƙewa ta yi da sauri ta shiga duba inda take jiyo sautin dryar a haka ta ƙaraso jikin wata ƙatuwar bishiya, cike da tsoro da kuma tarin zullumi ta ɗaga kansa zuwa saman bishiyar idanunta ya sauka akan wani ganyen bishiya dake lilo shi ɗaya, sai ka ɗauka iska ke kaɗa shi amma abin mamaki shi kaɗai ne yake lilo daga cikin sauran ganyen bishiyar. Prince Bill wanda a yanzu ya rikiɗe zuwa suffarsa ta asalin aljani yana kwance saman ganyen yana karkaɗa ƙafarsa wacce ita ce take sanya ganyen bishiyar motsawa, Danejo dai kallon ganyen take cike da mamaki tana tsaye taci mangoro ya faɗo kanta abinka da mai jin yunwa da sauri ta ɗauki mangoron babu Bisimillah ta shiga sha idanunta na lumshewa sbd daɗi. Daga bayanta taci ance. "Kisha a hankali da wasu da yawa idan kina buƙata" juyawa tai da sauri baki buɗe take kallon mai maganar, iya tsoro da razani ta shiga domin bata taɓa ganin halitta irin wannan ba, mangoron ta saka tare fasa wani Ihu ta ɗaga ƙafa zata gudu yai saurin riƙe hannunta. Share🥰🥰🥰 *🌈IDAN BA KE 🌈* 6.... *_Arewabooks@Nimcyluv_* "Na shiga uku Aljani Balarabe" Danejo ta faɗa a ruɗe tana ƙoƙarin kwace Hannunta daya riƙe cikin nasa. A nutse Prince ya ware idanunsa sosai a kanta yana Mmkin Yadda duk ta ruɗe kamar taga mugun abu. "Me ya baki tsoro" murguɗa masa baki tai tana suɗe hannunta dake ɗauke da ruwan mangoron ba tare data ce komai ba. Prince ya saki tattausan murmushi mai kyau da tsari yana binta da kallo musamman idan ya tuna abubuwa da suke faruwa a tsakaninsu, sai yaji nutsuwa ta kamasa. Hannunsu ta make ta ce "Sakeni haka kurum kai mini ciki, bayan Dada ta ce ba kyau namiji ya taɓa mace" ta ƙare Maganar tana binsa da kallo, sai a lokacin da a shiga ƙarewa tsarin hallitar jikinsa da kallo, fari ne tas kamar ka taɓa shi jine ya fito, yana da faɗin ƙirji fuskarsa mai cike da ilhama, ga wani gudun saje wanda ya kewaye fuskarsa zuwa ƙasa wajan gemunsa, fuskarsa mai faɗi ce babu wani abu da zai bamban tasa da jinsin larabawa. Prince ya saketa yana mai faɗin "Ciki na nawa kuma?" Zuciyarta na bugawa sosai ta ce "Me kace?" Ya girgiza mata kai yana ware hannun shi ya ce "Babu komai Danejo" zare ido tai tana dafe ƙirji sosai a tsorace ta ce "Kasan sunana? don Allah kasan rugarmu wallahi ɓata nayi ka taimaka kaji ɗan Balarabe" idanunsa ya ɗaga sama tare da daidaita juyawar launin idanunsa ganin yana neman rikiɗe masa, jikinta duk rawa yake tai saurin cakumarsa tare da rirriƙesa wanda yai sanadiyar fitowar wata jela a bayansa, sbd ko yaya ya samu kusanci da ita, baya iya zama a zallar mutum, dole sai wani sashi na jikinsa ya juye zuwa na aljani. "Ukkkkk heee" ya faɗa cikin kumburarriyar wacce ta amsa kuuwa cikin kunan Danejo. Gaba ɗaya rikicewa tai ganin yadda take neman maƙalesa baki ɗaya saboda tsoro da fargaba har take shirin bayyanar da kofatonsa yasa yai saurin riƙo Fuskarta tare da hura mata iska a fuska. Ƙuri tai masa da idanu a rarrabe ta shiga faɗin "Ka kaini wajan Dadata kaji, bana son zama a nan tsoro na keji Da...da...ta.." ta kasa ƙarasa maganar sbd idanunta da suka ruf wani barci mai nauyi ya ɗauketa. Fuskarta yabi da ido yana hango lokacin da yake tare da mahaifiyarta, duk yadda ya nunawa Dada so da ƙauna amma haka wani mugun babban Malami ya raba shi da ita, ba shi da niyyar cutar da Dada kawai ƙauna ce tasa yake tare da ita, yai ihun tare da magiya amma haka Malamin ya fatatakesa daga cikin Dada bayan ya ƙona shi. Wannan dalilin ya sa yai jinya sosai har bai san inda Dada tai ba sai kwatsam ya ganta lokacin tana ɗauke da cikin Danejo, tun daga wannan lokacin ya ɗauki son duniya ya ɗora akan Danejo, ya manta da batun Dada ɗan tayin dake cikinta kawai yake muradin yaga ya zo duniya. Sauke numfashi yai yana binta da idanunsa daya gama rikiɗewa har wani hayaƙi yake fiddawa, hannunta ya riƙo ya kama yatsan dake ɗauke da zoben daya saka mata ya jima yana kallonta kafin ya saketa zuwa ƙasa ya kwantar. Tsakiyar dajin ya koma yana Girgiza da surutai cikin ƙaramin lokacin ya koma asalin suffarsa ta aljani yana wani ihu da gurnani kafin kace wani abu ya gama haukata dajin can kuma ya ɓace ɓat. Yamma Yabi ne da Shatu tare da Sarkin ruga da kuma Giɗaɗo kwance a gaban Dada wacce take cikin halin rayuwa ko mutuwa, bata san inda kanta yake ba, sunan Halisa Dajeno Rome ne kawai a bakinta. Giɗaɗo ya ce "A jiƙa wannan maganin a bata" da sauri Hamma Yabi ya amsa tare da jiƙawa da taimakon Shatu ya ɗaga Dada suka ɗora mata maganin, wani shaƙuwa tai jikinta ya shiga jijjiga can kuma ta kwanta shakaf barci ya ɗauketa. "Na shiga uku na lalashe Hamma Dada ta mutu wayyo yanzu yaya za mu yi Dada ki tashi" idanun Hamma Yabi na taruwa da ruwan hawaye ya kama Shatu tare da riƙeta ya ce "Assha Assha Shatu Dada nada rai, daina kuka yaro barci Dada tai" kuka kawai Shatu take, duk da ƙarancin shekarunta amma ta fahimci cewa Dada ita ce cikon farin cikin su, tare da jin daɗinsu. Sarkin ruga ya sauke ajjiyar zuciya ya ce "Allah shi bata lafiya, Aradu tana gab da mutuwa" jin kalmar Sarkin ruga yasa Shatu ƙara sakin kuka tana jijjiga Dada tare da faɗin ta tashi kada ta mutu ta barsu cikin ƙuncin rayuwa. Cike da takaicin kalamar Sarkin ruga Hamma Yabi ya bisa da kallo yana addu'ar Ubangiji shi ya ɗauki rayuwarsa yabar Dada a duniya ko dan farin cikin Shatu da Halisa. "Ba a samu labarin Danejo ba har yanzu?" Girgiza kai Hamma Yabi yai yace "Aradu ta ɓace babu ita kaf cikin ruga da kuma daji" cikin tausayawa Giɗaɗo ya ce "Wayyo Allah shi baiyyanata" "Kawai iskanci ta tafi, amma ina ne Danejo bata sani ba cikin ruga da dajin ba har kiwo take zuwa ba?" Da sauri Hamma Yabi ya ce "Danejo ba zatai iskanci ba, domin bata san shi ba" fita duk sukai daga cikin bukkar. Hamma Yabi ya dubi Shatu da barci ya ɗauketa a jikinsa a hankali ya kwantar da ita, tare da fita daga cikin bukkar. Yana fita ya shiga irga Nagge wanda ya zama al'adarsa kullum tunaninsa za a iya sace musu Nagge shi ya sa a rana sai ya irgasu sau biyar. Kai tsaye asibiti ya nufa lokacin ana zubawa Dr Iliya magani a cikin mota. Saukar ruwan ruwan sama ne ya haddasa farkawar ta daga barci, da sauri ta miƙe tsaye jirkinta na rawar ɗari sbd gaba ruwan ya gama yi mata doka, ganin bata da wata mafita ya sa ta fara ƙoƙarin ɗaga ƙafarta Innalillahi sai a lokacin ta lura ashe a kan wani ƙaton dutse mai tsayin gaske take, ita kanta bata iya hango ƙasan dutsen, a hankali ta koma tare da zama saman dutsen "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un wacce kalar rayuwa ce take ciki haka? kenan akan dutsen ta kwana? ina ne nan kuma kwananta nawa? ta haukace ne ko mene? Anya ita ce ba wata Danejon bace daman?" Wani raunataccen kuka ta saka kuka take da dukkan ƙarfinta kenan ita da Rugarsu har abada ina za taga Dadarta? Kuka take sosai na rashin mafita ga rayuwarta ga ruwan sama na dukanta, yunwa take ji sosai, hannunta ta tara ruwa ya shiga sauka a hannun cikin sauri ta shiga shan ruwa sai daya isheta sosai sannan ta koma ta kwanta barci ya ƙara ɗauketa saman dutsen. "Ke! Ke! Baiwar Allah" aka shiga kiran sunanta wanda yasa ta buɗe idanunta da sauri tare da fatan Allah ya sanya a cikin Rugar Rome take, wasu fatake ta gani su wajan biyar tsaye a kanta ko wanne hannunsa riƙe da abu. Sai a lokacin ta lura ashe a kwance take saman wani ya shi saɓanin ɗazo da take kan dutse. Idanunta take rattabawa tare da binsu da ido ganin ba wanda ta sani yasa ta mayar da kanta ƙasa "Baiwar Allah wace ke daga ina kike? Kin san ina ne nan a Maiduguri kike fa?" Da sauri ta kalli mai maganar sai bata ce komai ba. Wani daga ciki ya ce "Ko bata magana ne? Kamar bafulatana" "Akwai abin da ke damunta Allah kaɗai ya sani" cewar wani, yin duniya sukai tai magana ko ta faɗi garin da take amma tai shiru kamar an kulle mata baki dole suka barta bayan sun yi mata fatan alkairi. "Danejo" aka kira sunan a taushashe sautin Muryarsa da taji yasa tai saurin Miƙewa yana tsaye kamar kullum sanye da fararen kaya ga tarin nutsuwa da ilhama a tattare da shi. da sauri ta nufesa kamar zata riƙesa sai kuma ya tsaya dab dashi tana sakin kuka tare da faɗin "Ɗan Balarabe ka kaiki gida kaji, tsoro na keji ina son nasan halin da Dadata ke ciki" Prince ya sake mata murmushi yana faɗin "Waya kawoki nan?" Hannu ta watsa alamar bata sani ba da sauri ta ce "Amma ka sanni ko? naji ka iya kiran sunana do Allah ka kaini wajan Dadata" yana kama hannunta ya ce "Ban san inda kike ba, Danejo kuma sunan matata ne ina iya kiran sunan kowa da ita" da fararen idanunta ta kallesa ba tace komai ba, sai hawayen dake suntiri a cikin idanun nata. Hannunta ya riƙe yana janta da Shira tun tana kuka harta daina, tana zaune taga ya kawo mata naman kaji da yawa da kuma kayan marmari ƙin cin komai tai sai da ya fara mata wasa yana bata labarin abin dry sannan ta saki jiki taci kayan marmarin. "Zan kaiki gida" da sauri ta ce "Da gaske kake Balarabe?" Kai ya ɗaga mata yana faɗin "E, Matata" turo baki tai ta ce "Ni ba matarka ce ba" ya ce "Daman ba dake nake ba" kamar ba zatai Magana ba sai ta ce "Yaushe zaka kaini wajan Dada" yana riƙo hannunta ya ce "Ko yaushe, amma kiyi mini Al'ƙawarin na dinga zuwa ina koya miki karatu, kuma kiyi al'ƙawarin zamu zama ƙawaye a duk sanda na buƙace ki, kizo gareni ba zan cutar dake ba na rantse da Ubangiji al'arshi, ba zan bari kuma kowa ya cutar dake ba" tunda ya fara magana take kallonsa cikin rashin sani ya ce "Kuma Dadata zata samu lafiya?" Shiru yai mata an riga anyi masa iyaka da mahaifiyarta, babu abin da zai iya a gareta, sai dai ya sanya Safwan yai wani abu akai. "Uhm ni kayi magana mana" ta faɗa tana jijjiga hannunsa kai ya ɗaga mata ya ce "E, kina zuwa ya kiga ta samu lafiya" Murmushi tai Wanda ya bayyanar da kyanta a hankali ya dinga ɗauke mata tunani harta manta da batun gida sulalewa tai ta kwanta saman ƙafarsa barci ya ɗauketa. ISLAMIC UNIVERSITY OF MADINA. _Jami'ar Musulunci ta Madinah_ masarautar Saudi Arabiya ta kafa jami'ar bisa umarnin sarauta a shekarar 1961 a tsattsarkan birnin Musulunci na Madina. Koda yake wasu sun danganta akidar Salafiyya da bude jami'ar, ana ganinta a matsayin rashin fahimta sakamakon halayyar da cibiyar ta ke da ita ga kowane akida. Jami'ar ta sami takardar shaidar digiri na jami'a ba tare da banbanta ta ba daga Hukumar Kula da Ilimin Kimiya da Nazari a watan Afrilun 2017. Jami'a ce mai tsarin gaske musamman Ɓangaren Addini. Ga nagartattun Malamai, da yawan ɗaliban na son karatu a jami'o'in Saudi Arabia sbd dalilai masu yawa. Manyan jami'o'in Saudi Arabia an basu shaidar yabo a bangaren ilimin kimiyya. Wasu daga cikin jami'o'in Saudi Arabia suna cikin manyan jami'o'i a duniya dangane da cibiyoyin bincike. Jami'o'in Saudiyya suna ba da kyakkyawan yanayin binciken ilimin, ta hanyar ingantattun cibiyoyin bincike. Yankunan ilimi da al'adu iri daban daban a jami'oin Saudiyya. Akwai daliban duniya daga sama da kasashe 165 da ke karatu yanzu haka a jami’o’in Saudiyya. Baya ga manyan masana ilimi da ma’aikata da ke aiki a waɗannan jami’o’in. Jami'o'in Saudiyya suna ba da cikakkiyar kulawa mai kyau ga ɗalibanta da kuma malamanta. ire-iren wannan manyan dalilai yasa akeso da burin karatu a jami'o'in Saudi Arabia. Da sauri ya fito daga ɓangaren hall ɗin da aka ɗauki darasin Islamic Studies and History. Kansa a ƙasa ya tatatare hannayensa cikin milk ɗin Arabian jallabiya daya saka sai wani ƙaramin baƙin hirami da yai rawani dashi, ɗaya hiramin kuma ya ɗora saman kafaɗarsa. Wasu matasa ne manyan suke take masa baya hadda wasu securities. Yanayin yadda yake tafiyar kaɗai zai tabbatar maka babu sassauci a zuciyarsa, idanunsa yai jajur bai taɓa shiga ta shin hankali na yau ba, yana zuwa bakin wata farar mota jikin Umar-khan na rawa ya buɗe masa murfin bayan motar ya shiga, Malamin na shiga mota, Umar-khan ya shiga gaban motar bayan driver ya shiga. Da sauri Driver yai wa motar key ganin haka yasa Saif-Wazir ya shiga wata motar kai tsaye daga cikin University ɗin Prince muhammad bin abdul'aziz international airport suka nufa. Ta cikin madubin motar Umar-khan yabi Sheikh Aliyu Haydar wanda ke bayan motar da kallo, ya jingina da jikin Kujera sai huci yake fitarwa, ya rirriƙe Jallabiyar jikinsa da hannu bibbiyu, gumi na tsastsafo masa ta tsakiyar goshinsa sbd yadda zuciyarsa ke masa zafi da ta fasa. Girgiza kai Umar-khan yai cike da tausayin yanayin yadda Sheikh Aliyu Haydar ke gabatar da rayuwarsa. Juyawa yai yaci gaba da kallon yadda driver ke sharara gudu, har suka ƙaraso filin tashi da saukar jirgin, The plane is ready to take off. Tun daga bakin wajan securities ɗin suka firfito tare da mamaye motar Sheikh, Umar-khan ya buɗe murfin motar ciki. Sauri Sheikh Aliyu Haydar ya fito a wannan lokacin ma kansa a ƙasa, yana hawa strains ɗin jirgin Saif-Wazir na biye dashi, sai Umar-khan wanda ya ɗan tsaya yana amsa kiran Father. Cikin damuwa Umar-khan ya ce "Kayi haƙuri Father, Sheikh ba zai taɓa aikata hakan ba, zargi ne kawai ake masa, yanzu jirginmu zai tashi be patient Father" tsaki Father yai ta cikin wayar kafin ya kashe. Yana shiga jirgin aka bawa Pilot daman keta hazo, a hankali jirgin ke zagayawa a ƙasan kwalta ya jima a haka kafin ya kete zuwa sararin samaniya. Jeniyar motocine suka tabbatar da Father Sheikh Aliyu Haydar ya ƙaraso gida Nigeria, da sauri ya miƙe daga zaunan da yake yana zaga haɗaɗɗan parlon gidan, tare da jiran shigowar Sheikh ɗin. Da mamaki Umar-khan ke bin ƴan jaridu da kallo, daga na gidan Redio, T.v, media. Abin har yai tsamari haka yana da tabbaci Sheikh ba zai taɓa aikata abin da ake tuhumarsa ba, zargi ne kawai. A nutse ya sakko da ƙafarsa daga cikin motar kai tsaye ƙofar shiga cikin gidan nasu ya nufa, Umarninka da Saif-Wazir na karesa daga ɗaukan da ƴan Jaridu suke masa. Sako ƙafar da Sheikh Aliyu Haydar yai cikin parlon yai daidai da lokacin da Father yake sauke masa wani lafiyayyan mari wanda yasa Umar-khan saurin juyawa ya fita, domin ba zai iya jure ganin ana cin zarafin babban mutum akan idanunsa ba kamar Sheikh Aliyu Haydar, Saif-Wazir Hawayen da yake maƙalewa ne suka sakko masa, da sauri ya karawaw Umar-khan baya. Cikin faɗa da tsawa Father ya ce "Ka kyauta Aliyu Haydar, ashe wannan dalilin ya hanaka auren tsayin shekaru talatin da huɗu? Ka yaudareni kaci amanar Musulmai kana fakewa da karatun addininka kana lalata yaran mutane a makarantar Jami'ar Madina?" Har wannan lokacin kan Sheikh a sunkuye yake banda cukurkuɗe Jallabiyar jikinsa da yake da hannu babu abin da yake. Father ya girgiza idanunsa cike da hawaye ya ce "Ba shakka biri yai kama da mutum, tunda nake baka taɓa zuwa wajena kace Father na zaɓi yarinya ina son aurenta ba,You betrayed me Aliyu, you deceived me as your father" Ya faɗa yana saukewa Sheikh wani marin cikin tsawa ya ce "Talk Aliyu, kayi magana ka amsa mini Sheikh..!!!" Father ya faɗa yana Girgiza kafaɗar Sheikh. Ɗago kai Sheikh yai bakinsa na rawa laɓɓansa na karkarwa alamar yana son cewa wani abu, amma sam ya gagara sbd rashin iya magana da bai ba. "Ban damu da duk yadda zakai magana ba Aliyu, a yanzu ba zanwa ƙinƙinarka uzuri ba ka bani amsa da gaske wata kaiwa ciki?" Shaaa hawaye ya sauka fuskarsa Sheikh sbd yadda yake son furta wani abu ya kasa. Matsawa ya yi kusa da Father yana buga hannunsa a cinya a hankali hannu na rawa ya miƙa tare da kama kwalar rigar Father, idan ya ɓalle bottle ɗin gaban rigar Father sai ya mayar rufe, da ƙarfi ya buga ƙafarsa yana riƙe wuyan Father hawaye ba zubu masa cikin ƙinƙina ya ce. "Ya....ya.... ya Allah..." Ya ƙare mgnar cikin ƙinƙina yana mai buga ƙafarsa a ƙasa. Share as so much as you can💋... Not Edited👏🏻 #Sarautar marubuta #True life story *🌈 IDAN BA KE 🌈* _*Arewabooks@Nimcyluv*_ Follow my account👇🏾 https://arewabooks.com/u/nimcyluv 7... "Heeeyyy..faaa..Father,babb babu uhmuuu macen dana taɓa laaahhh latawa" a wahale ya Ƙarasa maganar sbd zafin ƙinƙinar dake cinsa take basa wahala, yana buga ƙafa a ƙasa tare runste idanunsa zuciyarsa na maza zafi da raɗaɗi sosai na cin zarafi da sharrin da ake son yi masa, amma ko kaɗan fuskarsa bata nuna damuwar da yake ciki ba, ƙinƙinar ita ke azabtar da zuciyarsa wacce take kassara dukkan wani mafarki nasa. Hannun Sheikh dake wuyan Father ya ture cikin ɗaga murya ya ce "Ok ƙarya za ayi maka kenan Sheikh? Mutane dubu nawa ne a makarantar ba ace sune suka aikata haka sai kai? Kasan halin da ake ciki yanzu gidan Jaridu na gab da sakin labaran? Mata nawa ka lalata, mata nawa kai wa ciki?" Cikin zafin maganganun Father Sheikh ya ƙara runste idanunsa kansa ma sara masa, shiru kawai ya yi ba tare da ya ce komai ba. Father ya yi tsaki yana juyawa zuwa upstairs har lokacin bai dai na faɗa ba. "Kaje ka kare kanka daga zargi Aliyu, at anytime jami'an tsaro na iya zuwa, You are accused of a serious crime, we have no evidence to defend you in court" "Wanne Irin Court Father? Laifin Aliyu har ya yi girman da za a kaisa court? Wallahi babu mai kai mini ɗana Court" Hajiya Maryam wacce suke kira da Mother ta ƙare maganar tana sakkowa daga upstairs, domin lokacin da motocin su Sheikh suka shigo Sallah take. Father ya Kalli Hajiya Maryam tare da nuna Sheikh wanne yake ta damƙi Jallabiyar jikinsa. sam bai damu da duk zargin da za a yi masa ba, idan ƙaddararsa ce ta zo da haka babu yadda za ayi ya goje mata. "Sai ki tilasta masa ya yi magana, na faɗa masa ya nutsu ya ajjiye ƙinƙinarsa a gefe ya bani bayani, amma yaƙi, kina tunanin iyayen yaran zasu ɗaga masa ƙafa ne akan laifin fyaɗe da ya yiwa yaransu? Sbd kasancewarsa Malami kuma mamallakin S.A.H BANK..? ki Ajjiye son da ki ke masa a matsayin ɗanki, ki kwatantanta adalci tsakaninsa da sauran yaran daya lalata Maryam" Cikin faɗa Mother ta ce "Look Aliyu, idan kai ba zaka iya ƙwatarwa ɗan ka ƴanci ba, zan shiga ko'ina domin ganin an wanke Sheikh daga zargin da ake masa, ba abin kunya bane ace wai kai ne mai bada goyon baya akan Aliyu Haydar ya aikata hakan?" Father wanda Hajiya Maryam ta kira da Aliyu dake sunansa aka sakawa Sheikh ya yi Murmushin ta kaici. "Idan taƙamar maki Lawyer ce, kada ki manta su ma yaran Gwamnati na iya ɗaukar musu lauyoyi, dake da gwamnati sai ku zuba muga, kada ki manta daga can Madina aka zo da zan can, an kai maganar state C.i.d idan jami'an Nigeria bata ɗauki mataki ba, na Madina zasu ɗauka suna gab da bashi takardar kora daga aiki" yana faɗin hakan ya haura sama cike da baƙin cikin abin da Sheikh Aliyu Haydar ya ja musu a cikin Alhhali. Mother ta bi bayan Father da kallo, tana mamakin rashin ko'in kula da Father yake nunawa Sheikh kamar ba ɗan cikin sa ba. Juyawa tayi tare da kallon Sheikh da har yanzu kansa yake ƙasa tasan he never talk domin damar maganar bata damesa ba, sbd ƙinƙinar da Ubangiji ya jarabce shi da ita. Tana ƙoƙarin yi masa magana ya juya da sauri zai bar parlourn sbd raunin daya hango cikin ƙwayar idanun mahaifiyar ta shi. Yana saka kansa zai bar parlourn Umar-khan ya shigo da sauri jikinsa na rawa ya ce. "Innalillahi wacce irin masifa ke shirin tunkaro Mother?" Mother na ɓoye damuwar ranta ganin yadda Umar-khan ya firgita ta ce "Me ne ya faru Umar-khan?" Idanunsa akan Sheikh wanda ya ɗan jinkirta da fitar Umar-khan ya ce "Na rasa tayaya ƴan Jaridu suka samu wannan labarin, gaba ɗaya sun cika gidan nan da waje baki ɗaya, duk yadda securities sukai ƙoƙarin hana faruwar hakan amma abu ya gagara" Sheikh na jin haka ya juya alakar tafiyarsa zuwa haɗaɗɗan sashinsa dake cikin gidan nasu. Mother ta bi bayansa da kallo kafin ta juya ta kalli Umar-khan tace "Na jima banga mutum mai taurin kai da tsayayyiyar zuciyar irin Sheikh ba, duk abin da za ayi masa ba zai taɓa cewa komai ba" Umar-khan yaja numfashi yana mai ƙara gasgata zan can Mother, domin babu wanda bai san Sheikh da kafiya ba. "Yanzu ya za mu yi Mother? Al'amarin nan ya shige tunaninmu, ba tsammaci haka ba" Mother ta zauna kujera tana tunani ta ce "Zan shigar da ƙara Court, da kai da Saif-Wazir kuji da ƴan jaridu subar ƙofar gidan nan Immediately" "Court Mother? Waye zai tsaya masa? bakya tunanin shiga Court ɗin kamar latata rayuwar Sheikh ne?" A taƙaice Mother tana danna waya ta ce "Hakan ne mafita Umar-khan, batun lawyer ni ce zan tsayawa ɗa na da kai na" "but Mother" hannu ta ɗaga masa cikin sakin murya ta ce "Umar-khan...!!! Stop asking to much" jinjina kai yai ya fita yana jinjina girman yadda abin ya lalace cikin ƙanƙanin lokaci haka. Sheikh na shiga bedroom ɗinsa yaja numfashi sbd wani sassayan ƙamshin turarensa na ROJA daya daki hancinsa wanda ya jima da zama abokin hirar ɗakin. Ƙamshin daya haifar masa sauƙi a zuciyarsa, kasa zama ya yi ya shiga kaiwa da komowa a tsakiyar bedroom ɗin, tunani fal ransa wacce yarinya ya lalata? ba mace ɗaya ba har mata da yawa, kuma harda ciki? Bayan tunda yake maganar minti 20 bata taɓa haɗa shi da mace ba, idan ka ɗauke mother. Bai taɓa jin sha'awar mace ba, duk daɗin muryar mace bai taɓa ji ba, kamar an saka masa tsanar mata haka yake ji a ransa balle a wayi gari yau wata ta birgesa ba. Yinin ranar a sashinsa yake, Mother ba tai tunanin zuwa wajansa ba, ta san ba zai taɓa saurararta ba, koda Maimoon ta nufi part ɗinsa ɗauke da try na dinner yadda taje haka ta dawo, bugun duniya yaƙi buɗewa haka ta juya tana mai jin tausayin yayan nata. Mother dake zaune a Parlourn Father dake cikin sashinsa ta gyara zama ta ce "I couldn't believe what was happening,Aliyu is your son, you gave birth to him. Me ya sa ka yarda a ranka zai aikata hakan?" A nutse Father ya ɗaga kansa ya kalli Mother kafin ya ce "na fiki sanin ɗana ne, tunda akan idanuna ki kai Labour ɗinsa, amma hakan baya nufin zan saka masa Idanu, sai yanzu na fara tunanin tsayin shekarun da Aliyu ya kwashe a wannan duniyar ba tare da tunanin yin aure ba, kamar ko wanne namiji, nasan Aliyu nada lafiya balle nace, ke shaida ce how many times da zan kira Aliyu nace ya fitar da matar aure ya ce na bashi shekara ɗaya ko wata kaza? He is thirty-three years old now, but to this day there is no thought of marriage in his mind. Ni da kai na, na fara shakku da tantama idan ba lalata yaran mutane yake" wani irin ɗaci Mother taji a ƙasan zuciyarta, wanda ya sa ta fara ladamar yarda da Mijin nata da tayi. Magana ɗaya zai yi a janye Case ɗin amma yaƙi infact bai damu da matsalar ɗan nasa ba. Miƙewa tsaye ta yi tana kallonsa idanunta na sauyawa amma ta hana kanta zubar da hawaye ta ce. "Court zata tantance mai gaskiya, kuma zata wanke Sheikh daga sharrin da ake masa" tana faɗin hakan tai waje cikin ƙonar zuciya. Bayanta yabi da kallo yana faɗin "If you give evidence that Aliyu is innocent, zan tsaya wajan karɓar masa haƙƙinsa Maryam" sosai kalamansa suka daki kunnanta amma ta share. Tana zuwa parlour ta samu yaranta zaune sun zabga tagumi "Maimoon zugi driving nawa, Zeefa ke da Fattoumah ku zauna, I'll be back 10:00 ki tabbatar kunyi alwala tare da sallah kun kwanta barci, kada na dawo naga kuna kallo ok" Fattoumah ta ce "Mother ina zaki? Yaa Lee har yanzu bai fito ba fa?" Mother ta ce "Kada ki takura Sheikh, idan kika takurasa sai ya shaƙeƙi tas kafin ya baki amsa, You better be careful, bye my babies"... "Bye Mother" fita sukai har lokacin wasu ƴan jaridun na ɓoye suna jiran ganin motar Sheikh ta fito. Maimoon na fita taja motar da gudu ta ɗauki hanyar da zata kaita Maiduguri road. Tafiya kawai Danejo take babu takalmi kalbar kanta duk ta hargitse duk wanda ya ganta a wannan lokacin babu tantama zai kirata da mahaukaciya wacce ta jima cikin ciwon haukan. Tafi futu futu baya hayyacinta baki ɗaya,ita kanta ba zata taɓa tuna kwanakin data shafe tana tafiya ba, kuma abin mamaki ko gajiya ba tayi duk wanda ya ganta tambayar duniya idan zai mata ba zata taɓa kallon inda yake ba, balle kuma ta bashi amsa. Cikin ikon Allah ta samu kanta a gefen Rugar Rome inda take zuwa kiwo, tana zuwa nan ta yanke jiki ta faɗi babu numfashi. A hankali jikinta ya shiga Girgiza wani hayaƙi nafitowa ta jikinta a hankali hayaƙin ya cure waje guda, a haka ya rikiɗe zuwa suffar Prince.. idanunsa na kanta yana ƙoƙarin zuwa inda take yaji an daka masa tsawa wacce ya sanya ya tsaya da zuwa inda take, ko ba a faɗawa Prince ba ya san wane yake masa wannan tsawar domin shi kaɗai ya isa ya yi masa tsawa ya saurara. "Ka Saurara Prince, kada ka kuskure ka taɓa Bil'adama ɗin nan" Prince ya juya idanuna ya sauka akan mahaifina wanda yake cikin suffar mutane cike da kamala. "Matata ce Abba, ina da ikon taɓa ta a lokacin da nasu kada ka hanani aikata hakan" Wanda aka kira da Abba ya kalli Prince ya ce "Ban san yaushe ka zama mai son zuciya ba, zuciyoyi nawa zaka baƙantawa? yanzu bayan wannan ƴar tayin kaje ka saka bawan Allah cikin masifa me ya yi maka?" Prince yana huci ya ce "Abba wannan bawan Allan shi ke shirin rabani da farin cikina, na jima da sanin haka shi ya sa na fara yin abin da ya dace, kashe sa naso yi ma.." Abba ya kalli Prince da mmki kafin ya ce "Shi ne daidai da rayuwarta, shi ne Bil-adam shike da ikon kasancewa da ita, ba kai ba da kake Hallitar Ubangiji ta ban ƙasa ina rabaka da son zuciya, koda muke aljanu hakan bai zama lasisin da zamu cutar da wata hallita dake duniya ba, ko me zakai ba zaka taɓa iya cutar da shi ba" A hargitse Prince jiki na rawa yana rikiɗewa zuwa suffar aljanu ya kalli Safwan ya ce "Kai ne ka faɗa masa abin da na aikata ko? Kai ke ko?" Kafin Safwan ya yi magana Prince ya ɗaga sa zuwa sama tare da buga ƙasa da jikin dutse yana ƙoƙarin sake ɗaga Safwan, Abba yai wata kururuwa hakan yasa Prince yin kururuwa shima lokaci guda suka koma aljanu... 08119237616... *🌈 IDAN BA KE 🌈* _*Zaku samu cikakken labarin a Arewabooks, kuyi searching sunan littafin ko username Arewabooks@Nimcyluv*_ 8.... Ihu da kururuwa Prince ya din ga yi, sbd tsananin azabar da Abba ya ganawa masa. Cikin wata kakkausar murya wacce take nuna cewa ko a cikin Aljanu shi ɗin nada banne, kuma taƙadiri ne. "Akan aurena dake kan Halisa banƙi na kashe kowa na illata shi ba, daga ci hadda kai Abba, ba ruwana da kasancewar ka mahaifina, kada ka rabani da Danejona zakai babban kuskure zanyi ɓarna a duniya" Bakin Abba na fitar da hayaƙi kamar zai kunna wuta a ciki ya ɗaga hannunsa sama gaba ɗaya ya naɗe Prince cikin wata sarƙa da yana bakinsa ɗauke da addu'ar neman samun nasara akan Prince ɗin. Duk ihun da yake bai hana Abba ya sarƙafesa cikin yanar ba idanunshi ya yi wata kala. Cikin ɗaga murya mai amo! Ya ce "Na raba aurenka da Halisa, babu kai ba ita, kuma a yanzu zan cire cikin dake jikinta mara imani mai muguwar zuciya" yana faɗin haka ya yi girgiza tare da ɓatar da Prince ɗin baki ɗaya daga wajan. A hankali Abba wanda Asalin sunansa ya kasance MURWAS ya sauke numfashi, tare da juyawa ya kalli Halisa dake kwance a ƙasa tana barci, juyawa ya sakeyi ya kalli Safwan dake kwance shi ma. Cikin nutsuwa wacce ba zata addabi dabbobin dajin ba ya yi Girgiza tare da rikiɗewa ya koma suffar mutane sak. Hannuna ya ya ɗauki Halisa Dajeno Rome da sauri ya nufi cikin Rugar Rome zuciyarsa fal farin ciki ganin yau ya raba ɗansa Bilal da Bil-adam. Babu kowa cikin rugar kamar an share hakan yasa ya fara bin bukkokin Rugar da kallo kamar daga sama Hamma Yabi ya fito daga cikin ruga zufa na yanko masa hannunsa riƙe da ƙwarya maganin gaba ɗaya tunaninsa ya yafi wani wajan bai lura da mutumin dake tsaye yana binsa da kallo ba. "Jamɓanduna" Abba ya faɗa yana kallon Hamma Yabi dake ƙoƙarin yin gaba, tsayawa ya yi yana duba mutumin da ya ce masa Ina kwana, cike da mamaki ya ce "Jamni tawon" ma'ana lafiya. Abba ya jinjina kai ba tare da ya ce komai ba, jikin Hamma Yabi na rawa ya amshi Danejo daga hannun Abba kafin ya ce "Ikon Allah, ina kasa meta? Tsayin mako guda ta ɓace mana ba ita ba labarinta, shai Allahamdulillah" Murmushi mai sanyi Abba ya yi cikin nutsuwa ya ce "Ayyah ni ma yanzu ina iyu a cikin ruwan na ganta kwance gefen ruwan" cikin nuna jin daɗi da manta halin da Dada ke ciki wanda duk rashin Danejo ya haifar da haka ya ce "Shannu, wallahi shannunka kaji" kai kawai Abba ya ɗaga yana ƙarewa yanayin rugar kallo kafin ya juya bayan sun yi Sallama da Hamma Yabi yabar wajan. Yana fita ya ɓace a wajan baki ɗaya. Dada na kwance bakinta na fitar da wani ruwa kamar dafara Shatu na gefe tana kuka tamkar ranta zai fita. A cikin wannan halin Hamma Yabi ya shigo cikin bukkar hannunsa ɗauke da Danejo wacce har yanzu take bacci. Jikin Shatu na rawa ta miƙe fuskarta cike da hawayen halin da mahaifiyarsu ke ciki, amma hakan bai hana Fuskarta baiyyanar da farin cikin da zuciyarta ke ciki ba na ganin Yayarta Danejo. Bakinta na rawa ta ce "Hamma ina ka samu Danejo, da gaske ita ce yanzu Dada zata tashi naji daɗi sosai" bai ce komai ba ya kwantar da Danejo gefen Dada idanunsa akanta ya ce "Maza kawo mini ruwa" Shatu ta miƙe da sauri tare da nufar tulo ta tsiyayi ruwan mai ɗan sanyi, tana bashi ya shiga shafawa Danejo yana kiran sunanta. A hankali ta sauke ajjiyar zuciya tana buɗe ido a nutse. "Danejo"... "Halisa" Shatu da Hamma suka kira sunanta lokaci guda,a sanyaye cikin sanyin jikinta kamar kullum ta shiga binsu da idanu. "Kin farka?" Kalmar Hamma ta sanya ta lumshe idanunta kana ta buɗe a hankali tana sake binsa da kallo kafin ta yunƙura zuwa zaune "Naga kuna ta kallona kamar za a cini ɗaya?" Murmushi Hamma ya yi ya ce "Munji daɗin ganinki Danejo, mako guda kenan mun rasaki kin ɓace daga idanunmu" da Mmki take kallonsa ɓata? Mako guda? Taje ina? Ita gani tayi kamar barci take mai ɗauke da mafarkai kala-kala. Shiru tayi tana ƙara sauke numfashi tare da fara tunanin maganar Hamma Yabi. "Hankalinmu ya tashi, Kullum Dada cikin kiran sunanki take, gashi yanzu ko buɗe ido ba tayi jikinta ya tashi ina tsoro kada mu rasa Dada kamar yadda muka rasa Baffa" ambaton sunan Dada ya saka Danejo saurin juyawa zuwa gefenta manyan idanunta ta buɗe "Dadata" ta furta a ruɗe ganin yadda Dada ta ƙanƙame jiki, idanunta na kafewa kamar mai shirin mutuwa cikin muryar kuka ta ce "Na lalashe ni Danejo Dadata kada ki barni kada ki mutu do Allah,Kada kibi Baffana" sai girgizata take amma ina Dada ko motsi ba tayi. Da sauri Hamma ya fita zuwa bakin hanya tare da samu abin hawa yana zuwa suka ɗauki Dada a mota zuwa asibiti, asibitin babu jama'a sosai. Dr Hamza na zaune a Office gabansa cike da kuɗi ya kalli Dr Iliya ya ce "Kawo maganin nan ya yi mana rawa sosai, na ƙara tura saƙo zuwa ɓangaren lafiya akan magungunan da suka bayar ya ƙare, sbd cututtukan da suke damun jama'ar rugar, ina saka ran cikin satin nan za a kawo maganin" Dr Iliya ya numfasa yana jinjina kai kafin ya ce "That's good. Amma da gaske maganin ya ƙare ne?".. "No ba wani ƙare wa da ya yi, har yanzu ban bawa ko mutum ɗaya ba" cikin fahimta Dr Iliya ya kalli Dr Hamza yana faɗin "huh! za a kawo maganin sauro kyauta ma a raba, sbd yawaitar Maleriya" "Na samu Information ɗin hakan, amma idan an kawo gidan sauron, asibitin nan za a Ajjiye mu zamu raba, so za a bawa Kowa akan 1500 each one" waro ido waje Dr Iliya ya yi kafin ya ce "baka ganin zamu iya samun matsala, tunda kyauta gwamnati ta bayar?" Ɗaga hannu Dr Hamza ya yi yana dakatar da Dr Iliya da faɗin "Hakan shi ne ribarmu, ba za mu yi musu bauta ba kamar wasu bayi, they have to pay" Kafin Iliya ya yi magana Hamma Yabi ya faɗo office ɗin da sauri cikin tsawa Dr Hamza ya ce "Malam ya haka zaka faɗo kamar wani mahaukaci? Me ya sa duk fulanin nan baku da ilimin zaman rayuwa ne, baku san yadda ake mu'amala ba?" Hamma baya gane zancan nasu ya ce "Don Allah ka taimaki Dadarmu, kada ta mutu cikin wannan halin ita kaɗai ta rage mana, sau wajan goma ina zuwa" "Idan munje kanta lafiya zamu bata kenan? Ko zamu hanata mutuwa? Zan maka last warning Kada na sake ganin ƙafarka cikin asibitin nan, na faɗa maka bamu da maganin ko ɗaya me kake so nayi maka? Haba kuna yi mana adalci mu likitoci sai an bimu a hankali mai ya sa zan zuciyarku ya yi yawa ne?" kasa magana Hamma yai sbd Hawayen daya cika masa idanu me ya sa su Fulani ake musu kallon mahaukata wanda basu san me suke ba? Akwai wani bambanci a jikinsu wanda ya bambanta su da sauran jama'a ne? Juyawa ya yi yana zuriyarsa babu daɗi. Danejo na ganinsa ta ce "Hamma ya naga ka daɗe, numfashi Dadata zai gudu ka taimaka, ina masu bada lafiya ɗin?" A hankali ya kama hannunta ya riƙe yana shafa kanta dake ɗauke da suma mai kyau can ƙasa ya ce "Muje gida, ba zamu ƙara zuwa asibitin nan ba, Allah ya a bamu Kuɗi mu kaita asibitin burni" shiru kawai tayi tana kallonsa tare da son fahimtar abin da yake nufi a haka suka koma gida jiki babu daɗi, kwana sukai ba su yi bacci ba, Shatu kawai ta runsta sbd ƙarancin shekarunta. A daren Danejo ta sanyawa ranta zata sai da nono iya iyawarta ta tara kuɗi masu yawa akai Dada asibiti. Hakan yasa ta tashi da asuba ta tatsi kindirmo a ƙwayar gari na fara haske ta nufi cikin burni wajan Abti America. Mother ce ke sakkowa daga upstairs kunnanta maƙale da waya idanunta sanye cikin farin glasses ta fito a Barrister Maryam ɗinta sak. A hankali ta ce "Na riga nayi reporting case ɗin, idan ba a samu good evedance ba akan wanda suka kawo ƙarar Aliyuna, kai tsaye zan maka ko wacce ƴar banza a court dama kawai nake jira" daga cikin wayar aka ja numfashi tace "Barrister Maryam kasa aje court,idan akaje to kin bawa duniya damar zata fahimci halin da ake ciki,abi komai a sannu" ɓayayyiyar ajjiyar zuciya Mother ta sauke idanunta na sauka akan Zeefa da Fattoumah "Ok za mu yi magana bari naje wajansa Allah ya sa ya yi magana, al'amarin Sheikh na bani tsoro yana bani mamaki" ƙara tattaunawa sukai kafin sukai sallama. "sannu da sakkowa mother" idanunta akan Plasma ɗin da suke kallo ta ce "Fattoumah sau nawa zan ce bana son kuna kallon zee world ne? Ashe ban isa daku ba ko?" A sanyaye Fattoumah ta ce "We're sorry Mother ba zamu sake ba" zama tayi ta ce "Change the channel immediately Mamana" Sauya channel Fattoumah ta yi zuwa Aljazeera tana faɗin "Ok Mother" kallonsu ta yi sosai ta ce "Where's Maimoon and Auta?" Zeefa ta bata amsa da "She's inside the kitchen, Auta barci take" Mother ta ce "Bana son barcin yamma taso mini ita" tana faɗin ta miƙe tare da nufar kitchen daga bakin ƙofa ta tsaya tana kallon Maimoon dake haɗa coffee ta ce "Ina Lunch ɗin Sheikh?"... "Gashi a tray mother bari na kai masa" tsareta tayi da idanu ta ce "Bani nan" tray ɗin lunch ta bawa Mother tana ci-gaba da aikin gabanta. Haɗaɗɗan part ɗinsa ta nufa tun daga nesa ƙirar arar Sheikh Muhammad didat ta ratsa cikin kunnuwanta da Mmkin fal fuskar Mother ganin ƙofar shiga parlournsa a buɗe. Ƙamshin air-cod ya ratsa cikin hancinta. Tana shiga idanunta ya sauka akan Umar-khan dake zaune gabansa ɗauke da system yana duba wani abu, ganin Mother ya sa Umar-khan saurin miƙewa tsaye ya ce "Sannu da zuwa Mother" "Yawwa Umar-khan ina Aliyun?" Hanyar da zata sadaka da bedroom ɗin Sheikh ya kalla yana faɗin "a Parlour na samesa lokacin da nazo, ina fara yi masa magana akan wannan case ɗin ya tashi ya shige bedroom har yanzu bai fito ba" jinjina kai tayi ta nufi bedroom ɗin, babu abin da bedroom ɗin yake sai ƙamshin turarensa ROJA wanda ya a jima da kama ɗakin duk da cewa bai fiye rayuwa a cikin gidan iyayen nasa ba, yafi rayuwa a Madina idan yana ƙasa Nigeria kuma yafi rayuwa a gidan Hakimi. ba kowa nan ma a bedroom ɗin sai tsarin ɗakin da Mother tabi da kallo wanda a kullum yake Sauya mata, komai na ɗakin fari ne tas, ɓangaren clothes, shoes, perfumes. Komai daban yake. Juyawa tayi zuwa parlourn tana faɗin "Umar-khan Aliyu baya nan fa? Ko dai ya tafi gidan Hakimi?" Umar-khan yai shiru ya ce "Bashi da ikon fita, kamar kullum ƴan jaridu na waje ta ko'ina maybe yana Library ɗinsa" sai a lokacin ta tuna da Library tana zuwa ciki ta samesa zaune akan wata ƙyakkyawar kujera wacce take juya kanta da kanta ya rufe idanunsa, sumar kansa ta ɗan bayyana sbd yanayin naɗin rawanin nasa wanda ya yi da farin hirami. Hannunsa harɗe a ƙirji. Zama tayi kujerar dake kusa dashi tana kama hannunsa ta ce "Abbana Babana" ajjiyar zuciya Sheikh Aliyu Haydar ya sauke sbd jin sunan da Mother's ta kirasa da shi amma ya kasa buɗe idanunshi domin baya son ta fahimci halin da idanunsa ke ciki wanda sune kaɗai suke fallasa raunin zuciyarsa. "Buɗe idanunka mu yi magana Babana, ba zan taɓa bari kayi gidan yari ba, zan tabbatar da kai a matsayin mai gsky ba zaka wulaƙanta ba" nan ma shiru ya yi mata bai ce komai ba kamar yadda ta tsammata. Hawayen da take maƙalewa ne ya kwance mata wanda ya zuba a tafin hannun Sheikh. Da sauri ya ƙankame hannunsu dake riƙe da nata yana buɗe idanunsa a hankali wanda suka sauya daka rinewar da sukai. Fararen idanun nasa ya ɗora akanta ganin hawaye a Fuskarta ya ƙara sashi cikin damuwa amma sam hakan bai bayyana a garesa ba. "Kayi magana Babana rashin maganarka shike sawa a dinga tunanin baka da gasky, zuciyata ba zata jure ganinka haka ba" Kallonta yake har lokacin bai ce komai ba. Ganin bashi da niyyar magana yasa Mother fashewa da kuka sosai tana miƙe tsaye da sauri ya riƙe hannunta gam! Yana miƙewa tsaye jallabiya ce jikinsa mai kyau da tsada ga laushi da tsantsi. Kai ya fara Girgiza mata yana matse hannunta sosai babu abin da Sheikh yake ƙauna sama da mahaifiyarsa sai Father daga su Hakimi sune duniyarsa. Hannunsa mother ta riƙe ta ce "Try to speak Sheikh ban damu ba nasan zan fahimce ka, zamu Court bani da wani proof da zan kareka, mene gasky?" Riƙe hannun Mother Sheikh ya yi tare da fara buga ƙafa yana ƙoƙarin buɗe bakinsa. Ganin haka yasa Mother taimaka masa wajan riƙe hannunsa tana faɗin "Ahha say something, speak Babana, say it" hannunta duk biyun ya kama ya riƙe yana runtse idanunsa sai buga ƙafa yake tuni hawaye ya fara cika idanunsa. "Yee... Ƙaƙƙƙaaa... M...mmm" kai ta ɗaga masa tana shafa kansa a fisge bayan ya buga ƙafarsa da ƙasa yana saka hannun Mother a bakinsa ya ce "Babbbban akaita ba, bbbb ba zan taɓa yin yin yin haka ba mother" yana faɗin hakan yana ƙara saka hannun Mother a bakinsa duk ya jiƙa mata hannu da yawunsa mai ƙamshi a ƙoƙarinsa na ganin ya yi magana daidai waya baiwa ta Sheikh idan koyarwa zai yana samu maganarsa ta fita yake fara karatu cikin sauri baya tsayawa sai ya gama yana gamawa baya ƙara cewa komai yake fita daga hall. Wani irin rauni ya kama zuciyar Mother tausayi da ƙaunar Sheikh ya ƙara wanzuwa a zuciyarta wacce irin larura ce haka wacce bata barin har babban mutum? Zare hannunta ya yi domin har ransa bai san lokacin daya saka hannunta a baki ba a hankali ya juya zai bar wajan da sauri mother tana goge hawaye ta ce "Aliyu" cak ya tsaya tana ƙoƙarin magana Umar-khan ya shigo wajan da sauri gaba ɗaya suka bisa da kallo Umar-khan ya ce "Sheikh na shirya mota a ƙofar baya, yanzu zamu bar gidan nan jami'ai na hanyar zuwa nan zasu kamaka" ko motsawa Sheikh bai ba shi dai ya san ba zai taɓa hana abin da Ubangiji ya tsara afkuwa ba. "Jeka Aliyu ka bisu su fitar dakai Sheikh" Mother ta faɗa tana jan hannunsu ganin haka yasa ya bita har zuwa bakin wata sabuwar mota shiga ya yi. Drivern yaja, Umar-khan shima ya shiga mota, Saif-Wazir ya shiga wata motar. Motar ƙarshe kuma Ishaq-hakim ya shiga kai tsaye suka nufi wata hanya ta daban. Sbd gujewa haɗuwa da jami'an da kuma ƴan jaridu, kasancewar duk sunyi connecting wayoyinsu dana juna yasa Umar-khan gyara bluetooth na kunansa ya ce "Saif-Wazir" Saif ya amsa da "Ina kan layi" haka Ishaq-hakim da kuma Drivern Sheikh. Cikin jin daɗi Umar-khan ya ce "Saif-Wazir idan mun isa Shatalelen gidan gwamna kabi hanyar Amado bello way" Saif-Wazir ya ce "Noted bro" Umar-khan ya ce "Ishaq-hakim kabi hanyar Asibitin nasarawa, Drivern Sheikh Kabi hanyar ƙofar nasarawa,ni kuma zanbi hanyar kasuwar tarauni, gaba ɗaya hanyoyin zasu haɗamu a titin Dawaki roud zamu sauka gidan Hakimi.." haka duk suka amince suna zuwa Shatalelen gidan gwamna ko wacce mota ta ɗauki hanyarta suka ɗauke tunanin jami'an tsaron daka hanyar da zasu bi, Sheikh na bayan mota ya zubawa ikon Allah idanu a haka suka ƙarasa Dawaki roud motocin suka haɗu waje guda kai tsaye suka ƙarasa gidan Hakimi. Sheikh na fito da ƙafarsa waje aka riƙe hannuna tare da saka masa sarƙa kamar daga sama yaji ance "You are under arrest..... 08119237616. *🌈 IDAN BA KE 🌈* *_Nimcyluv sarauta_* _*E.O.W*_ 9... "You're under arrest?" Umar-khan daya fito daga cikin mota ya ƙara maimaita kalmar ɗan sandan wanda ya yi ɓadda kama cikin kayan gida. Ɗan sandan ya kalli Umar-khan fuska ba walwala ya ce "As you heard" Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un! Shi ne kalaman da Saif-Wazir ya faɗa domin Umar-khan kasa motsawa ya yi idanunsa a ƙasa baya taɓa jin zai iya haɗa idanu da babban mutum kamar Sheikh Aliyu Haydar cikin wannan halin. "Yallaɓai kayi mana afuwa mu shiga ciki mu tattauna, ba sai an tafi da Yaa Lee police station ba please" Wanda aka kira da Yallaɓai ɗin ya ce "Stop interfering with our work, because we know our work well, kuma wane ya faɗa maka police station zamu kai Aliyu Haydar Aliyu? State C.i.d zamu" da tsoro sosai akan fuskar Saif-Wazir ya ce "C.i.d? Wajan da ake ajjiye manyan masu aikata criminals, ƴan fashi,ƴan daba, Kidnappers Sheikh bai dace da wannan wajan ba, don Allah kada ko taɓa mana martabarsa.....," Ishaq-hakim ya katse Saif-Wazir da faɗin "har yanzu ba a tabbatar da abin da ake tunanin ya yi ba, zargi ne kawai" Wani daga cikin ma'aikatan ya ce "Say whatever you want to say,We must arrest Sheikh Aliyu Haydar Aliyu" cikin zafin zuwa Ishaq-hakim ya kalli ɗan sandan yana nu nasa da hannu ya ce "Idan ta ƙamar kai uniform ne a jikinka mu kuma mune da garin, wallahi idan ya tabbata Sheikh bashi da laifi sai munyi Shari'a da kai" yana faɗin hakan ya juya da sauri ya nufi babban gate ɗin shiga gidan Hakimi, kasancewar daman a ƙofar gidan suke. Sheikh dai na tsaye tamkar ba akan sa ake wannan muƙabalar ba, ya tsorawa hannunsa dake maƙale da ankwa ido shi kaɗai zai iya fasalta halin da zuciyarsa ke ciki sai kuma Abba Hakimi dake iya fahimtar raunin zuciyar Sheikh ɗin lokaci guda. Suna ƙoƙarin saka Sheikh cikin wata baƙar mota mai kyau wacce babu wanda zai iya ganin Sheikh ɗin a ciki gyarar muryar Abba Hakimi ta karaɗe wajan. Cikin mutuntawa da tarin ladabi duk jama'ar wajan suka sunkuyar da kansu ƙasa. A hankali Sheikh ya ɗago kansa tare da sauke ganinsa akan Abban nasa Hakimi, raunin idanun Sheikh ya bayyana sakamakon zuwan Hakimi wanda shi kaɗai ya fahimci hakan, shi kansa ya kasa yiwa Sheikh ɗin gwaggwaran kallo, idan akwai abin da Hakimi ya keso a rayuwa bai shige Sheikh Aliyu Haydar Aliyu ba, son da yake masa ko ƴar ƴan cininsa su Ishaq-hakim ba ya yi wa soyayya ce ta musamman tun Sheikh na zanin goyo. Zame ido Abba hikima ya yi daga kan Sheikh yana mayar wa kan jami'an tsaron da suke jiran suji mai zai ce, domin su basu da wani laifi akan aikinsu suke komai, ko da basu aikata hakan ba, gwamnatin ƙasar Madina zata ɗauki mataki, matakin da zaiwa kowa ciwo da zafi a zuciya. "Zaku iya tafiya da shi" Abba Hakimi ya furta a nutse yana shafa sumar Sheikh tare da ɗaukan hiraminsa ya fara naɗa masa sabon rawani. Da sauri Ishaq-hakim ya ce "Abba ta ya ya zaka bari a tafi da Yaa Lee? Kai ne wanda nake tunanin zaka dakar dasu daha tafiya da shi?" Murmushi mai laushi Abba Hakimi ya yi yana ɓoye damuwar ransa kafin ya ce "Mulki daban, hukuma daban Ishaq-hakim a barsu suyi aikinsu muma muyi namu" Umar-khan juyawa ya yi tare da shiga mota ya kifa kansa jikin Kujera ba zai iya zuba idanu a gabansa a tafi da Sheikh ba. Saif-Wazir idanunsa ya yi jajur gaba ɗaya yanayin baya yi masa daɗi. "Aliyuna" Abba Hakimi ya kira sunan a taushashe yana kallon Abban nasa, cikin kulawa ya ce "Kayi haƙuri, ƙarya fure take bata ƴaƴa, lashakka gaskiya zatai halinta ka ɗauka kai ni kana daga cikin bayin da Ubangiji zai gwada imaninsu" ƙanƙame hannun Abba Hakimi Sheikh Aliyu Haydar Aliyu ya yi, hakan ya tabbatar wa da Abba Hakimi Sheikh ya amince da zan can nasa. Sakin hannunsa ya yi gaba ɗaya jikin jami'an tsaron ya yi sanyi bisa dole suka saka Sheikh cikin mota tare da tafiya da shi. "Ishaq-hakim kawo mota, zuwa wajan Aliyu da Barrister Maryam" jinjina kai kawai Ishaq-hakim ɗin ya yi, tare da buɗewa Abba Hakimi bayan mota ya shiga, Saif-Wazir da Umar-khan suka bi bayan motar su Sheikh domin suji inda zan can zai tsaya. Mother na tsaye ta kasa zama sai number ɗaya daga cikin samarin take gwadawa amma basa ɗagawa, hankalinta ya ƙara tashi fiye da ko yaushe tunanin abin da ya samu Sheikh ya wanzu a zuciyarta. Upstairs tayi da sauri kai tsaye part ɗin Father ta nufa yana zaune a ƙawataccen parlournsa mai kyau, hannunsa riƙe da jarida cikin baƙin ciki yake karanta inda aka saki zan can Sheikh tare da photonsa,gaba Al'amarin ya wanzu a duniya dama media baki ɗaya. Shigowar mother ya sanya Father Kallonta yana jiran jin abin da zata faɗa wannan karan. "Barrister Maryam lafiya ki kai mini tsaye?" Da mmki ta dubesa sosai kafin ta ce "lafiya kake tambaya? Wai me Aliyu ya yi maka da baka kula da al'amarinsa ne?" Hannu ya ɗaga mata ya ce "Saurara Barrister Maryam ni na aiki Aliyu ya aikata hakan? ko da izinina ya ke lalata yaran jama'a yana musu fyaɗe?At Aliyu's age, I will not be surprised at all that he did, ba a shaidar ɗan yau Maryam da ace yana da mata babu mai zarginsa da aikata haka" tarin mamaki da ya gama cika Mother ya sanya ta kasa cewa komai sai kallon Father kawai da take "Aliyu ɗan ka na cikinka kake wa wannan shaidar, shaidar iyaye ita ce shaidar Allah fa, banda na san kai ne mijina kai ka samar da Aliyu da babu abin da zai sanya nace ba kai ka haife shi ba, amma kaje lokaci ne zaka fahimta idan baka son sa muna son shi" kai kawai ya girgiza mata yana faɗin "Zaki iya zuwa ki nemi Mahaifinsa a waje, tunda kina tantama" kafin Mother tayi magana Fattoumah ta shigo Parlourn kallon iyayen nata tayi ganin kamar hayaniya suke, fahimtar hakan yasa Mother yin murmushi ta ce "Mamana ya akai? Ban hanaku zuwa waje ba without permission zan fara bulala fa" marairaice fuska tayi ta ce "Am sorry mother ina ta sallama tun ɗazo" kallon yadda Fattoumah ta tsare Father da ido mother tai cikin sauri ta ce "Ya akai to?" Da sauri ta ce "Abba Hakimi yana Parlour kizo ke da Father" tana faɗin hakan ta juya da sauri tana jin Father na faɗin "Fatimah.. Zarahh..!!" Amma tai banza da shi, Fattoumah irin yaran nan ne masu riƙo da kuma kishin iyayensu mata gaba ɗaya taji abin da Father yake faɗa akan Sheikh. Fita Mother tai tana sakkowa fuskarta ɗauke da fara'a tasan tun da taga Abba Hakimi to Sheikh yana can gida cikin kwanciyar hankali. A ƙasa ta zauna tana gaida shi ya amsa a nutse kafin ya yi magana Father ya fito shi ma ya zauna saman Kujera ya ce "Sannu da hanya Abba Hakimi" kai kawai ya jinjina idanunsa akan Fattoumah yana faɗin "Matar zo nan mana ke dawa haka?" Turo baki tayi idanunta na sauyawa ta ce "Mijin me ya sa Father baya son Yaa Lee?" Sa mamaki Hakimi ya kalli Father yana faɗin "Aliyu ya akai haka? Me ya sa kake barin raya su san abin da ke zuciyarka ne?" Father ya ce "Abba Hakimi ta ya ya zan ƙi ɗana? Shirman Fatimah ne" da sauri Fattoumah ta ce "Da gaske nake Mijin,ina jin yana faɗawa mother wai a nemo mahaifin Yaa Lee kuma ai ba kyau ƙarya" surutun Fattoumah ya jijjiga Mother bata taɓa haifar yarinyar mai kaifin bakin Fattoumah ba. "shige ki bamu waje Mamana kafin ranki ya ɓaci laɓe kike mana kenan?" Turo baki Fattoumah tayi tace "Mother kawai ki nemowa Yaa Lee Abbansa wanda zai so shi tunda father baya son sa" Abba Hakimi da Mother suka kalli juna da sauri kuma suka janye idanunsu ko wanne tunani fal ransa. Tsawa Mother ta yiwa Fattoumah ta tafi ɗakinu Maimoon tana sakin kuka ta fara bori a ƙasan carpet. A nutse Abba Hakimi ya kalli Mother ya ce "Aliyu yana state c.i.d Barrister Maryam" a ruɗe Mother ta Kalli Hakimi hankali tashe take faɗin "An kama Babana? Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un wallahi sharri ne ba gaskiya ba, kuma zan tabbata da hakan" Hakimi ya ce "Samu nutsuwa Barrister Maryam, mu duka ba zamu ja da ikon Allah ba, kuma da hujjar kare Aliyu, shi ya sa nazo naji ko ya faɗa muku wani abun?" Father ya yi dariyar baƙin ciki ya ce "Wannan ne zai magana? Ko ya yi bata da wani amfani me zamu fahimta banda, A...Aaaa...ƙikkkk... Yeee gaba ɗaya Aliyu bashi da amfani a rayuwarmu, naji baƙin cikin samunsa Matsayin ɗa namiji" wani baƙin ciki ya tukare zuciyar Mother idanunta na cika da hawaye ta ce "Sai yanzu na fahimta larurar Aliyu ta sanya kake ƙinsa? Ubangiji ya ɗora masa shi nake roƙa kuma ya ye masa" Abba Hakimi ya numfasa kalam Father sun bashi mmki a haka ya share ya ce "kayi babban kuskure Aliyu, kuma Sheikh abin Alfaharin duk wani ɗan Kano dama Najeriya ne, muhimmancin bai tsaya iya ƙasar shi ba, har ƙasa mai tsarki.. Allah ya kyauta wata rana zaka gane gaskiya lokacin da za kaji kunya" juyawa kan Mother yai ya ce "Akwai abin da ya faɗa miki ne, ina son shigar da maganar zuwa court ne" Mother ta ce "Yana cikin ƙoƙarin fahimtar dani suka taho wajanka ya faɗa mini bashi ya aikata ba, kuma ni ma na shigar da ƙara ni zan tsaya masa tare da Barrister Zainab" wayar Mother ce ta fara ringing ganin sunan Umar-khan ya sanya ta ɗauka cikin sauri ta miƙe tana faɗin "Ohhh ok on our way" kashe wayar tayi idanunta akan Abba Hakimi ta ce "Umar-khan ya ce muzo yanzu al'amarin ya shige tunani" da sauri ta nufi ɗaki tare da ɗakko mayafi da key car. Abba Hakimi da Mother suka nufi state c.i.d hankali a tashe Maimoon da Zeefa da Fattoumah sai kuka suke a rayuwa suna ƙaunar yayan nasu duk da babu wata jituwa a tsakaninsu. Ko abinci suka kasa ci sai sallah kawai da suke suna addu'ar Allah ya kuɓutar da Sheikh ɗin. Hankali kwance Father yake zaune yana waya da babban amininsa ko da wasa bai masa magana akan matsalar da suke ciki ba, duk da cewa al'amarin ya gama zaga ko'ina a faɗin Nigeria. A kiɗime Mother take bin su Saif-Wazir da kallo ganin yadda idanunshi ya yi jajur alamar kuka suka sha. "Ina Babana ina Aliyu mai ya faru da shi?" Shiru Saif-Wazir ya yi mata, ta juya kan Umar-khan ta riƙe wuyansa sosai cikin faɗa ta ce "Where's my son Umar-khan? Ina Aliyuna?" Umar-khan ya yi ƙasa da idanun shi ba tare da ya ce komai ba. Sakin Umar-khan tayi ta nufi wajan Ishaq-hakim ta ce "Ishaq-hakim faɗa mini gsky ina Aliyu me akace yana da gsky ko? Ba aikata abin da ake zarginsa ba?" Hannunsa ya ɗaga tare da nuna mata wani waje da sauri ta juya Idanunta ya sauka akan Sheikh Aliyu Haydar Aliyu wanda aka cire masa Jallabiyar jikinsa aka ɗauresa da Sarƙa tun daga wuyansa hannunsa zuwa ƙafarsa farar fatar jikinsa tayi jajir bakin Ishaq-hakim na rawa ya ce "Mother Sheikh ya amsa laifin da ake zarginsa ya tabbatar shi ne ya lalata ƴan matan hadda ciki..... _*IDAN BA KE...* labari ne da kuka daɗe ba kuci karo da irinsa ba, ƙaddarar labarin akan soyayya ne mai tsayawa a zuciya da saka shauƙi a zuƙatan masu karatu..... Tsammaci abin da baka tsammani salo na musamman🫣💋 08119237616._ *🌈 IDAN BA KE 🌈* *_Arewabooks@Nimcyluv_* 10.... Kasa magana Mother tayi sai Ishaq-hakim da tabi da kallo tana son gasgata abin da yake faɗa. "Ta ya ya Sheikh zai amsa laifi fyaɗe? Laifin da duk duniya ta san ba zai iya aikatawa ba?" Ta faɗa a fili tana sakin wani raunataccen kuka mai tsayawa a zuciya ba zata iya kallon Sheikh cikin sarƙa a ɗaure ba, kamar wani ɗan fashi ko Kidnapper. Umar-khan ne ya kama Mother wacce take ƙoƙarin zubewa a wajan sbd kukan da take idanunsu ya yi jajur ya ce "Ki daina kuka Mother, wata kila Sheikh ya amsa laifin ne sbd rashin mafita, mu duka abin ya zo mana cikin wani sabon yanayi wanda bamu taɓa riskar kanmu ciki ba, Ubangiji ka ɗai ya san gaskiya kuma shi muke roƙa ya fidda Sheikh Aliyu daga cikin wannan jarrabawar" gaba ɗaya zuciyar Mother ta karaya tunaninta ya tsaya cak duk inda take neman wata hujja ta kare ɗan nata babu. Da hannu bibbiyu ta riƙe Umar-khan ta ce "Kai ne kake tare da Babana Umar-khan, ka taimaka mini nasan kasan Aliyu ba zai iya aikata hakan ba, yana tsare imaninsa yana amsar rayuwa a duk yadda ta zo masa" Umar-khan ya mayar da hawayen dake cika idanunsa kafin ya zaunar da Mother ya ce "Be patient Mother, muyi addu'a kawai amma da ace zan iya bada shaida, da iya abin da zan faɗa ya isa ya wanke Sheikh daga cikin zargi" "That's enough, this is not a place to make noise" Wani daga cikin jami'an tsaron ya faɗa yana daka musu tsawa. Sai a lokacin Abba Hakimi ya yi ajjiyar zuciya domin shi ma Al'amarin ya girgiza shi fiye da tunanin kowa, zuciyarsa shi zafi take masa sosai. A nutse ya juya ya kalli Ishaq-hakim ya ce "Ka mayar da Barrister Maryam gida yanzu, ka ce ina buƙatar ganin Aliyu immediately" da girmamawa Ishaq-hakim ya amsawa mahaifin nasa, idanunshi akan Mother yana jiran ta miƙe. Cikin kuka ta kalli Abba Hakimi ta ce "Ina son nayi magana da Aliyu Please Hakimi" Kafin Abba Hakimi ya bata amsa wani daga cikin Jami'an tsaron ya ce. "No way Madam" tana share hawaye ta ce "Don girman ka bani 2 minutes nayi magana da ɗa na, ina son tambayarsa, tare da kwantar da hankalin shi" cutting nata out ya yi da faɗin. "Isn't necessary Maaah..." A ƙagauce Abba Hakimi ya ce "take her out Ishaq-hakim" Mother na kuka sosai tana kiran sunan Sheikh Aliyu aka fitar da ita waje, Aliyu shi ne rauninta ka kaf cikin yaranta tafi ƙaunarsa duk abin da Mother ta mallaka daga cikin dukiyar iyayenta Aliyu ta bawa, She owned all her property for him, Lands, houses, companies, all signed in the name of Aliyu's property. Su Mother na fita Abba Hakimi ya kalli jami'an tsaron cikin murya mai taushi ya ce "Kun samu hujja mai ƙarfi da kuka kama mini ɗa na?" Ɗaya ya sunkuyar da kai cikin girmamawa ya ce "Har yanzu bamu da hujja, amma a duk bin ciken da mukai Sheikh ƙara shiga ciki yake, yaƙi buɗe baki ya yi magana, gwamnatin Madina da universityn ƙasar sun matsa akan kwana biyu suka bayar idan ƙasa Nigeria bata ɗauki mataki ba, zasu ɗauka da kansu domin su irin wannan cases ɗin kai tsaye suke bincike kuma hukuncin kisa ne" runtse idanu Abba Hakimi hukuncin kisan ya daki zuciyarsa ainun. Umar-khan da bakinsa ke rawa tun ɗazo sbd masifa ya ce "Ita kanta gwamnatin Madinan idan bata da hujja dole ta haƙura, ina masu kawo ƙarar? Daga ina wannan zan can ya fito? Ina ƴan matan da akaiwa fyaɗen suke?" "Stop raising your voice, we are working on our system, nan ba Court bace" Umar-khan zai sake magana Abba Hakimi ya yi gyara murya kafin ya ce "Ka bari abu komai a nutse, shi ya sa na mai da Barrister Maryam gida" Saif-Wazir dai na tsaye duk yadda suka so a basu Sheikh su yi magana hanawa akai. Kuma a gobe za a kaisa court domin fara gabatar da Shari'a tun da case ɗin ya zo da hargitsi. Haka suka komai gida zuciyoyin kowa babu daɗi. Sheikh na zaune daga shi sai single da wani farin trousers mai laushi tunda yake a duniya babu wanda ya taɓa ganin tsari da zubin halittarsa sai yanzu, an tuzarta shi tuzarcim daya har zuƙa kuturwar zuciyarsa, shi kaɗai sai tsuma yake shi da ko sauro baya so baya ƙaunar yaga baiwar halittar da tsaraicin jikinsa, yana tsarkake jikinsa domin sirrinsa ne, amma yau da wanda ya dace da wanda bai dace ko wanne tom and jerry gani yake abin ya yi masa zafi ainun. Dalilin daya sanya ya amsa laifin kenan ba tare daya shirya hakan ba. Mother na komawa gida ta samu Fattoumah na zaune ita ɗaya a Parlour da sauri Fattoumah ta ce "Mother ina Yaa Lee? Ba zai dawo ba?" Murmushi mother ta yi tana ɓoye damuwar ranta ta ce "Ya dawo mana Manana, yan gidan Abba Hakimi where's your sisters?" Da hannu ta nuna mata part ɗinsu, Mother ya kama hannunta suka shiga ciki. Yaran duk suna zaune sanye da hijabi sunyi shiru bayan sunci kuka sun ƙoshi, cikin faɗa ta ce "Maimoon, Zeefa what's this? Kuna da hankali zaku shigo ɗaki kuyita kuka kamar anyi mutuwa, Depression kuke son ya kamaku ko mene?" Gaba ɗaya suka miƙe tsaye jikinsu na rawa za su yi magana ta ɗaga musu hannu ta ce "Ku fita a nan wajan, maza aje a kunna kallo ayi" fita gaba ɗaya sukai jiki babu ƙwari mother ta bisu da kallo tausayin su na kamata tasan duk sanadin Aliyu Haydar suka shiga wannan damuwar. Kuma ita idan har ƴar halak ce ba zata sake zuwa wajan Father ba akan maganar Sheikh Aliyu ɗin ba. Tana fitowa daga cikin bedroom ɗin upstairs ta haura zuwa nata bedroom ɗin wayarta ta ɗauka ta shiga kiran Barrister Zainab akan gobe zasu shiga Court sun daɗe suna waya kafin ta kira Yaya Halima anan ta kwantar mata da hankali ta ce ita ma ta nan zuwa dan sunyi nisa ne. Har Mother ta miƙe da sauri kuma ta koma ta zauna domin gaba ɗaya ta manta da batun Jadda cikin sauri ta danna numberta wayar ta jima tana ringing kafin a ɗaga a fusace akace "Allah dai yai gutsi gutsi da duk wanda yake addabata wannan masifar har ina, ba lallai mutum yaga Annabi ba" A hankali Mother ta ce "Jadda ni ce Maryam" Jadda ta ce "Wata abace Maryam kuma? daga wacce duniya mena haɗa dake?" Shiru Mother can kuma ta ce "Mahaifiyar Sheikh Aliyu" Jadda ta zabga salati da duk ƙarfinta ta ce "Yanzu Maryam cewa nayi ban gane ki ba? Masifar gaisuwa ce bana so, Ina shi Aliyu yana can Madina ɗin ne?" Mother ta ce "Baki san meke faruwa da shi ba?" Jadda dake kishin giɗe tayi saurin Miƙewa zaune tana faɗin "Allah ya isa, dake Maryam da shi Aliyu Allah dai ya isa wani abu ne ya samu Sheikh bani da labari?" Kafin Mother tai mgn father ya ƙwace wayar tare da kashewa baki ɗaya ya kalli Mother ya ce. "Yanzu Barrister akan wannan maganar zaki haɗani da Mahaifiyata? Su kike ta tsine mini tunda kin san bakinta ba shi da tsarki wajan sakin magana da kwasa ta" banza tai masa ba tare da ta ce komai ba, yana ƙoƙarin sake magana ta miƙe tsaye tana faɗin "Idan ka gama ka ajjiye mini wayata, I have something to do with my phone" tana faɗa ta shige toilet domin zuciyarta a kusa dake da shi. da idanu ya bita kana ya ajjiye wayar yana mmkin halin mata a wasu lokutan. Gari na waye Barrister Zainab ta zo suka fita zuwa State C.i.d ita da Mother abin mamaki gaba ɗaya ƴan jaridu sun cika gidan Redio, da t.v kowa yana jiran a fito da Sheikh Aliyu Haydar Aliyu. Cikin nutsuwa Barrister Zainab dake driving ta kalli mutanan ta ce "Am still wondering ta ya ya zan can nan ya shiga kunnuwan Al'umma" Murmushin taƙaici kawai Mother ta yi wai duk akan Innocent son ɗinta ake wannan tururuwar kamar wanda ya kashe mutum?. "Allah ya kyauta, mutane akwai su da son gulma musamman ƴan jarida wallahi" I.d card ɗinta wanda ke nuna ita cikakkiyar lawyer ce mai zaman kanta ta nuna kana aka basu damar shiga, tun kafin Barrister Zainab ta yi parking idanun Mother ya sauka akan Sheikh wanda aka fito dashi cikin wata ƙatuwar sarƙa tare da wasu manyan ƴan fashi, wani abu ya tsaya mata wanda bata taɓa jin irinsa ba, ko hawaye ta kasa a wannan lokacin. Da sauri ta fita haka ma Barrister Zainab ɗin, ana ƙoƙarin saka Sheikh Aliyu cikin mota wata mota ta shigo da gudu cikin haraba wajan hakan ya sa duk suka daka ta. Wani babban jami'in tsaro ne tare da Abba Hakimi suka fito daga cikin motar sai wata matashiyar budurwa wacce Fuskarta ta kumbura sosai sbd kuka. I.G ya kalli jami'an tsaron cikin tsawa ya ce "Maza a cire sarƙar nan, a bawa Sheikh Aliyu Haydar Aliyu kayansa ya saka, He's Innocent ya fita daga jikin zargi, Wannan matar ita ce wacce ta shirya komai, she's the reason behind, She is the one who harmed Aliyu" Gaba ɗaya kallon budurwar sukai wacce take kuka kamar ranta zai fita. A karo na farko Sheikh Aliyu Haydar Aliyu ya ɗago idanunshi tare da sauke su akan budurwar wani irin lallausan murmushi ya sauke wanda ya kusan ɗauke hankali jama'a tare da basu mamaki, hatta Mother tai mamakin ganin murmushi a fuskar Aliyun. Cikin ƙaramin lokaci aka sakawa Sheikh wata jallabiya mai kama da Alkyabba tare da wani farin hirami nan da nan kamalarsa ta fito haibarsa ta cika Idanun kowa. I.G ya bada umarnin a kama budurwa Sheikh ya yi gyara murya yana tafiya a nutse cike da kamala tsayawa yai daidai inda budurwar take, for the first time a tsayin rayuwarsa daya tsaya gaban mace kana ya juya ya kalli I.G sanin cewa ba zai iya taɓa jikin I.G ba yasa ya kama hannun Abba Hakimi ya riƙe da kyau yana runtse idanunshi, ƙafarsa ya ɗaga ya buga a ƙasa cikin In-ina ya ce "Aahhhh ahhha abarta, dooo.. do.. domin ba ba ba....ba a faɗa da Aljani. Not Edited 08119237616 🫰🏽kai tsaye ga mai buƙatar littafin. *🌈 IDAN BA KE 🌈* *_Arewabooks@Nimcyluv_* 11..... Abba Hakima ya kalli Sheikh a nutse yana mai sakin murmushi shi ma, tare da juyawa ya kalli budurwar wacce taƙi yarda ta kalli inda Sheikh ɗin yake, tun daga sama zuwa ƙasa Abba Hakimi ya ƙare mata kallo kafin ya ce "A'uzu bi wajhillahil karim, Wabi kalimaatil lahillati la yujawizuhunna barran wala fajiran, wabi asma'illahil husna kulliha, ma alimtu minha wa malam a'alam min sharri ma yanzilu minas sama'i, wa zara'a fil'ardhi, wa min sharri ma yakhruju minha, wa min fitnatillaili wan nahari, wa min ɗawariƙil laili wan nahari, illa ɗariƙan yadruƙu bikhairin ya Rahamanu. Wa min sharri kulli dàabbatin Rabbi akhizun bi nasiyatuha inna Rabbi ala siraɗin mustaƙim" jikin budurwar ne ya fara rawa sosai, tsoran Abba Hakimi da Sheikh Aliyu Haydar Aliyu suka cika mata zuciya, bata son su cutar da ita tunda ita bata zo da nufin hakan ba, kuma daman Ubangiji ya ɗora mata tsoran Sheikh ɗin tun ba yanzu ba, tana jin girma da nauyinsa tare da shakkar sa kwarjininsa yafi komai dagula mata lissafi. Idan ka ɗauke Abba Hakimi, No one understands the words of Sheikh Aliyu. "No!!!" Sheikh Aliyu Haydar ya furta a nutse yana riƙe hannun Abba Hakimi wanda bakinsa ya kasa yin shiru da addu'ar da yake, dalilin hakan yasa budurwar ta nemi birkicewa wanda kuma daga Abba Hakimi sai Sheikh ɗin ne kawai suke ganin hakan. Shiru ya yi da addu'ar yana kallonta kafin ya juya ya kalli Sheikh fuskarsa ɗauke da annuri irin na cikakkun dadtawan nan ya ce. "Yaushe Aliyu ya samu abokai haka bani da labari" a wannan karan Sheikh bai murmushi ba sai rirriƙe hannun Abba Hakimi da ya yi yana lumshe idanunsa tare da buɗewa alamar "Bai san yadda akai hakan ya faru ba" riƙe hannu Sheikh ɗin kai tsaye Abba Hakimi ya yi domin kai tsaye ya fahimci karatun idanun na Sheikh. I.G dake tsaye shi da Barrister Maryam yana bata haƙuri ya ce. "I'm sorry, action was taken without investigation, we were wrong" kasa riƙe kanta mother ta yi cikin losing control ta ce. "You have defamed Sheikh's name, all those who respect him have now stopped, Sbd Kuskuren ku my son is innocent na riga dana faɗa muku, but you refused to understand me" Bar Zainab ta numfasa cikin rashin jin daɗi ta ce "Everything that has happened has already happened, kawai a kira ƴan Jaridu a shaida masa Sheikh bashi da laifi, sharri ake masa bai san komai ba a wanke sunan shi daga ɓacin da ya yi" cikin martabawa da nuna rashin daɗin abin da duk ya faru I.G ya ce. "Aikinmu ne hakan, za muyi abin da ya dace muma ba zamu so sunan Sheikh ya lalace ba yana da girma da daraja a idanun ba" Mother gaba ɗaya haushin duk wasu jami'an tsaron take ji hakan yasa cikin sauri ta juya zuwa inda Abba Hakimi da Sheikh suke tsaye, idan ka gansu zaka ɗauka da gaske Hakimi shi ne ya haifi Sheikh sbd tsananin haibar dake maƙale a jikin ko wanne kusan duk halin Hakimi Sheikh ya kwashe shi tas. Kallonsu ta yi cike da son ko wanne wanda ke rinjayar zuciyarta ta ce "Thank you Abba Hakimi" murmushi kawai ya yi bai ce mata komai ba, tana ƙoƙarin sake magana ya yi saurin barin wajan zuwa cikin motar da Umar-khan ya buɗe masa baya. Tsaye Sheikh yana bin mahaifiyar tasa da kallo ganin tai shiru ya waro mata manyan Idanun shi yana son cewa wani abu amma ya ja bakinsa ya yi shiru a hankali ta ce "zaka bini ko Abban naka za kabi?" Bakinsa ya motsa yana rufe idanu tare da fara buga ƙafa yana riƙe jikinsa da kyau cikin In-ina ya ce "Zazzzza... zan zan zanje gida wajan fa... fa.. father ina soooo son ganinsa" haushi ne ya kama Mother ganin duk abin da ake Sheikh yana maƙale da son mahaifinsa. "Father baya gari, kaje wajan Hakimi ka huta da kyau gobe sai kazo mu tattauna, ina tunanin za a haƙura da zuwa Madina haka" girgiza mata kai ya yi bai ce komai ba ya juya ganin har lokacin Abba Hakimi na zaune bayan motar, yanzu zuwa shima ya shiga baya Ishaq-hakim ya jasu. daga nan Bar Zainab gidanta ta shige hakan yasa Umar-khan ɗaukan Mother a ɗaya daga cikin motocin Sheikh suka nufi gida, Saif-Wazir kuma ya tsaya domin magana da ƴan jarida. Suna tafe a hanya Sheikh na yiwa Abba Hakimi hira cikin nutsuwa duk da In-ina yake amma Hakimi na fahimtar komai da Sheikh ke faɗa, a duk maganganun Sheikh ba za kaji kalmar MACE ta fito daga bakinsa ba, balle har ya ware wata musamman yana magana a ganta, Murmushi kawai Hakimi yake Ubangiji ne shaidar son da ya kewa Sheikh a jinin jikinsa yake. A haka suka ƙarasa haɗaɗɗan gidan Abba Hakimi dake Dawaki roud, gida ne irin na sarauta mai kyan tsari da fasali ko'ina ma'aikata ne , motar na tsayawa Sheikh ya fito ƙwayar idanunsa na nuna gajiyar da yake ciki. Bai tsaya jiran Abba ba, kai tsaye ya nufi part ɗinsa wanda yake cikin gidan Abba Hakimin wanka ya yi da ruwa mai zafi yana gamawa ya fito ɗaure da babban towel idanunshi na janye wa barci na cin ƙarfinsa ya ɗauki wani tsadaddan lotion, Shea body butter ya shiga shafawa saman fatarsa a kasalance, Engage Cologne Spray ya fesa a fatarsa sbd ɗauke zafin da ya keji yana gamawa ya miƙe zuwa clothes ɗinsa ya ɗauki wani trousers mara nauyi ya saka ko riga bai saka ba, ya cilla mint bakinsa ya kwanta saman bed yana lulluɓe jikinsa da bargo, ganin rana ce ya sa ya kunna A.c tare da rufe idanunshi cike da fatan barci ya ɗauke shi. Washegari gari tun da Sheikh ya farka bai koma barci ba, har ya fita sallar Subhi sai da gari ya yi haske wajan 6:30 ya dawo gida jikinsa duk ciwo yake masa sbd rashin gym da bai ba, wanka ya ƙara yi ya shirya cikin Scabal wool suit white colour sai red ɗin necktie. Sai Diamond Rolex daya maƙala a hannunsa, yau a Yaa Lee ya fito ba a Sheikh ba, domin kusan siffa biyu gare shi, idan zashi bank shigar suit yake duk abin da ya danganci addini ajjiye shi yake a gefe amma yana zuciyar shi, idan kuma ya sanya Alkyabba da rawani yana matsayin Sheikh a wannan lokacin ne ba Yaa Lee ba. Wayarsa ya ɗauka jacket ɗin sa a hannu cikin nutsuwa ya fita zuwa main parlour. Ƙamshin ROJA shi ne ya fara kaiwa su Abba Hakimi ziraya yana zaune da jallabiya gefensa kuma Ishaq-hakim ne da Saif-Wazir shirya zasu shi wajan aiki, sai Momi A'isha tana zubawa Abba Hakimi Shayi mai zafi. "Mrng Yaa Lee" jinjina kai ya yi idanunshi akan Abba Hakimi ya furta. "B...bar bar barka da safi fifi fiya". "Ya ka kwana? da ciwon kan?" Rufe ido ya yi tare da buɗewa alamar "Allahamdulillah" Momi A'isha ta amsa gaisuwar Sheikh ɗin wacce ya yi mata ita cikin In-ina, tea ta haɗa masa mai zafi ta zuba 2spoon na honey ta juya kaɗan tare da bashi. Amsa ya yi a kame yake shan tea ɗin yana sauraran maganar Abba Hakimi da yake ce masa "komawa Madina ba yanzu ba, kada ya fara tunanin hakan" sanin ba zai iya ja da maganar Abba Hakimin ba yasa ya miƙe yana ajjiye cup ɗin hannunsa, Ishaq-hakim da Saif-Wazir suka miƙe tare da bin bayansa, wata farar mota ya shiga mai Sheikh no 5 yana shiga driver ya ja. Ishaq-hakim da Saif-Wazir kowa ya shiga motarsa suka nufi S.A.H BANK. tun kafin ya Ƙarasa cikin bank ɗin wanda ya kasance mallakinsa ma'aikatan bakin Sheikh Aliyu Haydar bank suka shiga mutuwarsu ƙwarai. miƙewa ake ana gaida shi hannu kawai yake ɗaga musu har ya shige wani baban office. Wunin ranar Sheik cikin duba files and Ducoments yake. 3:30 yana ƙoƙarin barin Office ɗin saƙon father ya sauka Wayarsa. Da fararen idanunsa yake bin message ɗin da kallo yana mamakin yanzu kuma kiran gaggawar mene?. Da wannan tunanin ya shiga mota Driver ya ja suka nufi unguwar su Sheikh. Tun a harabar gidan ya san akwai matsala domin kai tsaye idanunshi ya sauka akan motar Abba Hakimi data Yaya Halima sai ta Uncle Haroon. Ƙamshin turarensa ya bayyana zuwansa, Mother dake zaune saman Kujera yana kaɗa ƙafa ta kalle shi kafin ta ɗauke kai, Uncle Haroon ma kallon Sheikh ɗin ya yi, a kame ya ƙarasa kusa da Abba Hakimi ya zauna yana ɗauke idanunshi daga kan jama'ar daya rasa meeting ɗin me ake. "Tun da Allah ya kawo shi sai aji ta bakinsa, amma Sheikh ya shige lokacin da za a yi masa auren dole, a baya ba ai masa ba balle yanzu?" Yaya Halima ta furta cike da jin haushin father. Shi ma father da zuciyarsa ke kusa ya ce. "Bashi da amfani, domin ba zai faɗi abin da kowa ke buƙata ba, na daɗe da sanin cewa Aliyu shi ne ƙaddarata, shi da yake namiji wanda ya kamata ya tsaya kan dukiyata amma ya kasa hakan, duk mutanan da suke buƙatar contract daka gareni idan har suka ji yadda Aliyu ke banzar maganar shi suke contract In-inar Aliyu ta ja mini asara mai yawan gaske, don haka ni bashi da amfani a gareni" sai a yanzu suka fahimci rashin jituwar da babu tsakanin father da Aliyu cikin ladabi Abba Hakimi ya ce "Baka yarda Ubangiji ya ɗorawa Aliyu wannan larurar ba? kenan baka alfahari da Aliyun matsayin ɗa?" Cikin sauri Father ya ce "Aliyu bai taɓa yi mini rana ba, to akan me zan yi alfahari da shi? Idan yana so mu shirya dole ya daina wannan In-inar ko kuma ya yi aure cikin satin nan" "Aliyu akwai wacce ka ke so ne?" Sai a lokacin Sheikh ya kalli Uncle Haroon yana runtse idanunshi zufa na yanko masa a ƙoƙarin shi na ganin ya yi magana babu In-ina amma ina ba zai iya ba ƙaddarar shi ce hakan. Cikin fitar hayyaci yana rirriƙe jikinsa da kyau tare da buga ƙasa da hannun kujera ya ce "ba...ba ba bana son son kowa uncle.. ba ba bazan iyyyya zama dadda da mace ba" shiru duk sukai baƙin ciki ne kuma ya hana mother magana. Father ya ce "Ok good a Sbd haka ka shirya zama da Zahrah ƴar gidan babban aminina, cikin satin nan za a yi aurenku kai da Zahran babu fashi" miƙewa Mother ta yi cikin faɗa ta ce "Wallahi Aliyu kayi kaɗan ka saka Sheik ya auri wannan Yarinyar da ban amince da tarbiyyar ta ba, me Sheikh zai da ita? Yarinyar da take kusan sa'ar shi kaɗan ne babu ta girme shi ba? duk shekarun da Aliyu ya yi babu aure sai kuma ya ƙare wajan tsohuwa, ban amince ba kuma ban yarda ba, ka bawa Aliyu duk wacce kaga dama amma ban da Zahrah" murmushi father ya yi ya ce "Idan har ni ne uban Aliyu ba wani ba? Ya zama dole ya auri Zahrah idan kuma bani ne mahaifinsa ba sai ki bashi wacce kikai niyya Barrister Maryam" hawaye ya cika Idanun Mother ta ce "Oh yanzu kuma sheganta Aliyu zaka fara bayan zarafinsa da ka ke ci akan larurarsa?" Banza father ya yi mata. Uncle Haroon ya numfasa ya ce "Engineer Aliyu Wannan bai kamata ba, idan kana so Aliyu ya yi aure,Let him choose the woman he wants to marry himself, ka sassauta yanayin da ka keji game da Aliyun" Father ya ce "Abu ɗaya ne zai kawo Shira tsakanina da Aliyun shi ne auren shi da Zahrah idan bai amince ba yaje na zare hannuna daga Lamarinsa kuma ya zare sunana a matsayin Uba" Dakawa Father tsawa Uncle Haroon yai ya ce "Wai Aliyu wanne irin banzar magana ce kake haka? Ni da kai na zan iya samawa Aliyu matar aure, ka daina ganin kai ne ubansa ni ma uba ne a wajansa, ga kuma babban Uba hakimi duk mun isa mu tsayawa Aliyu, ka daɗe baka cire hannunka ba, kuma wallahi ka sake na rabaka da Aliyu ka rabu dashi kenan har abada" Girgiza kai Abba Hakimi ya yi ya ce "Ba za a yi haka ba Haroon, haƙƙin Aliyu ne samawa Sheikh matar aure a barshi ya aura masa Zahrah Allah ya sa albarka,kada ka damu da Sheikh nasan zai amince" miƙewa Sheikh ya yi cikin zafin e da kutuwar zuciya irin ta kurmaye Aliyu ya fara faɗa ta inda ya shiga bata nan yake fita ba, idanunshi gaba ɗaya ya rufe Innar ta hana ya ji abin da yake faɗa, idan kuma ya fara faɗa babu wanda ya isa ya tsayar da shi daga faɗan da yake. Saukar wani zazzafan mari da Sheikh ya ji a saman kamilalliyar fuskarsa ya sanya ya yi saurin rufe idanunsa Father ya nuna Sheikh ya ce "Ni kake ɗagawa murya Aliyu? Ni sannu kuturu uban ƴan zuciya daman zuciyar taka nake buƙata auranka da Zahraan kuma babu fashi" ƙwafa Sheikh ya yi domin baya iya riƙe kansa idan zuciyar ta motsa uban kowa sai ya san babu lafiya a gidan. Wuyan rigar Father ya riƙe da kyau zufa na mamaye dukkan goshinsa a wannan karan bai buga ƙafarsa ba amma tamkar zai ɓalla wuyan rigar haka ya riƙeta da kyau cikin huci da faɗa ya ce "heee na... na na amince amma ka ka ka tabbatar mutuniyar kirki ce" Father da yaji shaƙar Sheikh ɗin har ransa ya ce "Idan kuma ba ita bace ba fa Aliyu?" Sheikh ya girgiza kai idanunshi ya yi jajur ya ce "Haaaaa ɗakkkkkk" yana faɗin haka ya saki Father tare da barin gidan baki ɗaya... We're still in free pages🫰🏽 Littafi nan na kuɗi ne, a koda yaushe zan iya datse free pages. Salo na musamman biya 500 ta Wannan acct ɗin 6850917335 Na'ima Shu'aibu sulaiman fidelity bank. Shaidar biya 08119237616. *🌈 IDAN BA KE 🌈* *_Nimcyluv sarauta_* 12.... Bayansa suka bi da kallo ganin yadda ya fice a fusace. Father yaja numfashin wahalar da ƙyar kafin ya ce "Irin wannan ban zan yaron za a bawa mace mai ƙarancin shekaru? Ai ko Zahrah sai dai ta yi haƙuri da shi" Mother zatai magana Yaya Halima ta hanata ta hanyar danne hannunta tare da girgiza mata kai. Ganin ba wanda ya sake cewa father komai ya juya zuwa upstairs. Uncle Haroon ya kalli Abba Hakimi ya ce "Afuwa ranka ya daɗe kayi haƙuri da halin Engineer Insha Allah komai za yi daidai, Jadda ba zata barshi ya aikata hakan ba, I'll talk to him" murmushi Abba Hakimi yai yana faɗin "Me ne na haƙuri Haroon? Sheikh ɗan sa ne ba wanda zai yi jayaya da hukuncin da uba ya yi akan ɗan sa, idan hakan zai sa shi farin ciki da amincewa da Sheikh a barshi ya yi" "She's 32 years old Hakimi, tayi wa Sheikh girma ba zata iya yi masa biyayya ba, babu tarbiyya a wajan yarinyar nan na jima da saninta" Mother ta faɗa cikin damuwa. Yaya Halima ta ce "Barrister ke uwa ce a kullum, addu'a kawai za kibi Sheikh da shi, addu'ar ki zatai ta zagaya rayuwarsa sai kiga albarkacin haka Ubangiji ya daidaita tsakani kuma ya shirya yarinyar, ba a jayaya a cikin lamarin aure" Uncle Haroon ya ce "Ki bar Barrister ta faɗi abin da yake ranta, idan akwai wanda yafi sanin halin Sheikh da raninsa to ita ce mai biye mata shi ne Hakimi, babu kyautatuwar a zuwa Engineer idanu yana abin da ya ga dama, idan baya ra'ayin Sheikh a rayuwarsa sai muyi yarjejeniya mun ashe sa mu suke sunan shi daga jikin na Aliyun" miƙewa tsaye Abba Hakimi ya yi yana gyara zaman alkyabbar jikinsa cike da nutsuwa ya ce. "Wannan shawara ta Haroon ba dani ba, ban taɓa jin inda aka raba uba da ɗana ba, lokaci ku barshi ya bayyana mana komai" yana faɗin hakan ya yi waje yana dogara sanda. Uncle Haroon ma ya miƙe tare da yi musu sallama. Bayan tafiyar su Yaya Halima ta kalli Mother ta ce "Barrister ki nutsu kada kiyi jayaya da hukuncin da uban yaron nan ya zartar ni ina ji ajikina akwai wani abu ɓoyayye a ƙasan auren mu amince da hakan" ƙwafa kawai Mother ta yi tana girgiza ƙafa kafin ta kalli Yaya Halima ta ce "Kin san Allah Yaya ko zan amince da auren nan sai dai Sheikh ya auri mata biyu?" Yaya Halima ta waro idanu sosai ta jima tana kallon Mother kafin ta numfasa ta ce "Tab, mata ɗaya ya zata ƙare wajan Sheikh bare mata biyu? Ai Wallahi mantawa zai yi da zamansu a gidan" "Ai ko zai yi shekara ɗaya bai kalli ko wacce ba, Wallahi sai dai ya auri mata biyu" Yaya Halima ta ce "Naji zaɓin Uba, wace kuma zaɓin uwa?" "Bani da zaɓi amma duk wacce Allah ya nufa data kwanta mini ko ƴar gidan wace zan saka Hakimi ya ɗaura musu aure" girgiza kai kawai Yaya Halima tai tana faɗin "Wata drama ɗin abin dry a gidan Engineer da Barrister a bani abinci naci ni dai" Mother ta miƙe tana kiran sunan Maimoon. Fitowa tayi daga part ɗinsu jikinta sanye da duguwar riga ta rusuna ta ce "Ina yini Mama?" Yaya Halima ta ce "Lafiya lou Maimoon ya karatu? Kwana biyu Mother ta hanaki zuwa ko?" Maimoon ta juya ta kalli Mother wacce ta ɗauke kai tamkar bata jin abin da suke cewa ta ce "A'a Mama, karatu ne ya yi zafi amma muna exam zan zo" "To Allah ya taimaka, a kawo mini abinci" murmushi Maimoon tayi ta nufi kitchen. Yaya Halima ta kalli Mother tana mamakin zafin zuciyar ƙanwar ta ta. Arabian Mandi rice wacce ta sha kayan haɗi sai ƙamshi take Maimoon ya zubu a plate tare da haɗin salad da ya sha bama da egg with some of vegetables. "Ki sakko muci abinci Maryam" Mother ta ɗauke tana faɗin "Anya? ci kawai Yaya bana jin zan iya ci" murmushi kawai Yaya Halima tai tana faɗin "Allah ya kyauta komai ya yi zafi maganinsa Allah" Yana tsaye gaban madubi banda huci babu abin da yake maganganun father nayi masa amsa kuuwa a kunnuwansa "Bashi da amfani, bai taɓa yi mini rana ba, ya yi mini asarar contract ɗina" hannu ɗaya ya sanya ya dafe kansa dake masa ciwo sosai, ɗaya hannun kuma ya rufe kunnansa a zatonsa hakan zai taimaka wajan rage tuna maganar mahaifin nasa. Ɗago jajayen idanunsa ya yi ya tsurawa kansa ido ta cikin madubin. A wannan karan dole ya nunawa father shi ma namiji ne yana shiru ne sbd bai damu da duniya da abin da ke cikinta ba. Juyawa ya yi zuwa Library ɗinsa dake gidan Hakimi. Zama ya yi saman kujera cikin sauri ya duba dukkan mayan kadarorinsa kama daga kan filaye, gidaje, ɓangaren Library na karatun addinin dana kimiyya ya buɗe, S.A.H bank duk yana fahimtar dukiyar tasa har ya kasa shi kansa bai yi tunanin abin da ya mallaka ya kai girman hakan ba, a haka kuma bai haɗa dana wajan Mother ba wanda suke mallakinsa. Tunani ya fara tunda yana da bank a kano me zai hana ya buɗe S.A.H BANK a sauran jahohin da suke Nigeria? Da kuma kamfanin sarrafa shinkafa ƴar hausa mai kyau wacce za taiwa talakawa sauƙin siya kan fara shi mai sauƙi?. Da wannan tunanin ya yi na'am da zuciyarsa cikin nutsuwa ya fita daga Library ɗin ya koma haɗaɗɗan bedroom ɗin nasa, kai tsaye toilet ya shige tare da sakarwa kansa shower yana sauke numfashi a hankali ya fara sauka daga dokin zuciyar yama mance da batun aure baki ɗaya. Domin daman shi bai dame shi ba indai macace da kanta zata gudu ta ce bata son shi domin ba zata samu abin da take buƙata ba daga gare shi. Fitowa ya yi yana ƙamshin shower gel Shea body butter ya shafa jikinsa ko body spray bai fesa ba ya cilla mint bakinsa tare da kwanciya saman bed ya rufe idanunsa. Umar-khan ne ya shigo cikin parlourn Abba Hakimi bakinsa ɗauke da sallama. A hankali Abba Hakimi ya ajjiye azkar ɗin hannunsa wanda yake na yamma tare da duban Umar-khan cikin kamala da kamewa ya ce. "Umar-khan yaya dai?" Shafa kai ya yi yana tare da faɗin. "Abba Hakimi daman Mother ta ce ko Sheikh yana nan? Gaba ɗaya baya can gida" murmushi mai laushi Abba Hakimi yai yana zame idanunsa daga kan Umar-khan ɗin "Aliyu ai ba yaro bane?" Abba Hakimi ya faɗa a gajarce Umar-khan ya miƙe ba tare daya samu cikakkiyar amsa daga bakin Abban Sheikh ɗin ba ya ce "Ni ma zan je gida, sai da safe Abba Hakimi" yana buɗe azkar ɗin ya numfasa kaɗan cikin sakin fuska ya ce "A gaida Abdulrashid" "Zaiji sosai" Umar-khan ya amsa wa Abba Hakimi yana barin gidan baki ɗaya tare da tunanin inda Sheikh ɗin ya yi domin yana tsoro idan zuciyar ta motsa kowa sai yaji babu daɗi. Momi A'isha ce ta shigo ɗauke da tray ɗin abinci zama tayi bayan ta ajjiye ta ce "Ina ta mamakin abin da ya sanya mahaifin Sheikh ke aikata haka kamar wani mara ilimi, kuma ya dace ace ka saka baki ko auren ya keso Sheikh ya yi sai ka zaɓa masa ƴar mutunci, kaga hankalin Barrister bai kwanta da zaɓin Engineer ba" gaba ɗaya Abba Hakimi ya tattara nutsuwarsa kafin ya ce "Ku dai mata yawanci tunaninku ɗaya, bani da ikon ture umarnin uwa ga ɗan shi,kada ki manta ni uban rana ne kuma mariƙi, I don't have the courage to deny the Engineer what he wants" "Gaskiya dai, ni ina tunanin ko sbd Sheikh bashi da lafiyar yin magana cikin jama'a ya sanya Engineer ke yi masa haka? Kuma yana ganin He is the only male among his children, shi ne ya kamata ya tsaya kan harkokinsa na yau da gobe ya ɗauki buri ya saka akan Sheikh ɗin?" Abba Hakimi ya amshi fruits ɗin data gama yanka masa kafin ya kalleta da kyau ya ce "Baki ke aiki ko ƙwaƙwalwa? Babu wani abu da Sheikh ba zai iya ba, In-ina kuma Ubangiji ya ɗora masa muna fata a koda yaushe ta zama sauƙi a gare shi" "haka ne Allah ya bashi lafiya, anjima zani gidan Barrister ɗin" Abba Hakimi ya ce "Ki yi zamanki" ta kalle shi ta ce "Amma me ya sa?" Shiru ya yi mata tasan ba zai bada amsa ba, kuma tunda ya ce haka yana nufin hakan har ransa. A can commission Quarter's dake cikin garin Yola/ jimeta a hankali take driving saman makeken kwaltar da zai sadata har zuwa gida, numfashi ta sauke a karo na ba adadin tana kallon titi kunnanta kuma ma sauraran abin da Surayyerh ke faɗa tsaki ta ja ta ce "You bother me with noise wlh Surayyerh koda yaushe problems ɗinki da mahaifiyarki baya ƙare wa?" Surayyerh ke ta ce "A sbd ba ke bace ko? Gaba ɗaya ta takura ni wani lokacin gani nake kamar ba ita ta haifan ba" da sauri Zahrah ta juya ta kalli Surayyerh ta ce "Ashe daƙiƙiyya ce ke? Whatever is your problems ki barni da tawa matsalar" dry sosai Surayyerh tayi tana tafa hannu ta ce "Oh! Sorry ashe fa ciki yaƙi zubewa yanzu dole ki amincewa Deen kuyi aure" Zahrah stopped Surayyerh from what she was saying ta ce "And who told you cikin Deen ne? Ni kai na ban zan cikin waye ba, ban damu kuma dana sani ba kawai na zubar da shi ba aure a tsarina a yanzu dai" Surayyerh ta gyara zama sosai ta ce "Kin san Allah a yanzu babu abin da nake so sama da aure, sai yanzu na fahimci karatun bokon nan is nothing wani abu ne wanda kana cikin gidan mijinka ma zaka iya yinsa" Zahrah bata ce komai ba tunaninta yana can yana da tabi cikin jikinta ya zube ba tare da Mimi ta lura da shi ba. A haka suka ƙarasa gida gatekeeper ya buɗe musu. Sosai tai mamakin ganin motocin Dady yaushe ya dawo bata da labari? Dawowar gaggawa?. Fitowa tayi hannunta riƙe da L.G bag daman babu mayafi jikinta kayan sun kama jikinta sosai, jerawa sukai ita da Surayyerh zuwa cikin gidan. Dady da Mimi ta bi da kallo ganin suna magana a hankali, Dady yai murmushi ya ce "Finally She's back zo nan Zonan Zahrah" ya miƙa mata hannunsa ƙara sawa tayi ta zauna kusa dashi tana rungume shi ta ce "Wlcm Dady" kallonta ya yi da kyau ya ce "Zahrah magana za mu yi mai Muhimmanci" ta gyara zama ta ce "All ears Dad" ya ce "Kin san aminina Engineer Aliyu?" Ta ɗaga ta ce "I think I knw him Dad mene ya faru?" Ya ce "Kin san wancan dake jikin photon?" Juyawa tayi ta tsurawa photon Sheikh Aliyu haydar Aliyu dake maƙale jikin bangon parlournsu zuciyarta ta ɗan buga ta girgiza kai ta ce "Ban shi ba Dad, amma na san yana da muhimmanci tunda aka photon sa a gidanmu" ya jinjina kai ya ce "Yana da muhimmanci a gareni da rayuwata baki ɗaya, Zahrah wannan da kike gani akansa duka wasu burukana suke, ina son na haɗaku aure da Sheikh Aliyu haydar Aliyu cikin satin nan" zabura tayi ta miƙe tana zaro idanunta waje zuciyarta na bugawa sosai ta kasa magana baki ɗaya. Mimi ta ce "Daman nasan Zahrah ba zata amince ba, domin ko Tafsir ɗin ta tsana" Dady ya ce "Ya zama dole ta amince sbd karayar arziƙin dake shirin tunkaro mu ba tare da mun shirya ba, Zahrah ki yarda ki auri Sheikh zaki farin ciki namiji ko a maza samun irinsa zai wahala kiyi mini wannan alfarmar" Ajjiyar zuciya ta sauke ta ce "Dady na amince da buƙatar, amma idan har daga ni ba zai sake auren ko wacce mace ba ina nufin babu kishiya... Na kusa gama free pages. IDAN BA KE it's 500 gaba ɗaya book 1,2 har ƙarshe. Via 6850917335 Na'ima Shuraihu Sulaiman fidelity bank. Shaidar biya 08119237616 ƴan niger suyi mini magana na faɗa musu yadda zasu biya. DESTINY TRUE LOVE ROMANCE TRUST SARAUTAR MARUBUTA *🌈 IDAN BA KE 🌈* *_Nimcyluv sarauta_* 13..... Mimi ta ce "baki son kishiya kuma? Ina ruwanki da wata kishiya?" Dady ya ɗaga hannu yana murmushi ya ce "Ni ma bana fatan Sheikh Aliyu haydar Aliyu ya yi wa Zahrah kishiya,domin za a rage mini abin da nake tunani" cikin rashin fahimta Mimi ta ce "kamarya Alhaji?" "Ba sai kinji ba, ki shirya aurar da yarinyar ki cikin satin nan" ya faɗa yana miƙewa tsaye cikin jin daɗin amincewar da Zahrah ta yi. Jikinta na rawa ta haura upstairs tana zuwa ɗakinta ta samu Surayyerh ciki daman bata tsaya a parlour ba sama ya shige ɗakin Zahran. "Wayyo daɗi kashe ni, na samu mijin da nake fata da burin samu cikin sauƙi" ta faɗa gado tana sakin ƙarar farin ciki. Surayyerh ta ce "Pardon? Ban fahimta?" Miƙewa Zahrah ta yi ta ce "C'mon yanzu Dady yake sanar mini za a haɗa aurena da Sheikh Aliyu" mamaki ya hana Surayyerh rufe baki sai da Zahrah ta saka hannu ta rufe mata baki, Surayyerh ta samu damar faɗin "Are you serious Zahrah? Gaskiya am happy for you daman kina son Sheikh?" Tayi fari da idanu irin na gogaggun matan nan ta ce "Fiye da yadda bakya zato, soyayyar Sheikh ta hanani aure, abin mamaki ban taɓa ganin shi a zahiri ba sai dai photo a wajan Dady ko idan yana tafsir, nasan shi ma bai sanni ba" "Yanzu duk ba Wannan ba, ya ya zaki da cikin jikin ki tunda likita ya tabbatar ba zai zube ba? Gashi kuma aure ya zo babu shiri?" Zahrah ta ce "Kada ki damu da cikin zanyi auren, ko da haihuwa nayi sai nace bakwaini ne ai anayi" Surayyerh ta jinjina makircin Zahrah amma ta share ta ce "Idan kin ɓoye cikin ya zaki idan ya san ke ba budurwa ce ba?" "Oh! My God what exactly wrong with you Surayyerh ki ke neman yi mini baki? Ai ba zai sani bama ɗinki zanje ayi mini" Surayyerh ta ce "Uhm shi fa babban Malami ne You never lie to him Malamai sun san komai infact sun fi kowa iya soyayya kiyi tunani ki nemi mafita" share zan can Surayyerh Zahrah tayi a yanzu yadda za taga Sheikh Aliyu haydar Aliyu a zahiri shi ne burinta. Da magrib Surayyerh ta tafi gida akan gobe zata dawo domin fara shirye-shiryen haɗa events. Tun a bakin parlour Surayyerh ta san akwai matsala tana shiga Umma ta kalleta sosai ta ce "Daga ina kike?" Turo baki tayi tana musmus da bakinta kamar mai zagi ta ce "Wai ke Umma zargina kike ne? Haba don Allah na fara gajiya ciki kike tsoro ko mene?" Umma mamaki ya kasheta a tsaye ta ce "Surayyerh ni mahaifiyar ki kike faɗawa haka sbd ina kare kiwon da Ubangiji ya bani?" "Wani irin kiwo kamar wata dabba Umma? Kawai takurawar taki ce ta yi yawa, ki barni da abin da yake damuna gashi duk iskanci Zahrah rana tsaka ta samu miji na kece raini wanda ba zan taɓa samun irinsa ba" jirin dake neman yadda Umma yasa ta nemi saman kujera ta zauna. Ubangiji ya gani kuma shi ne shaida tayi iya yinta ta fara gajiya tana ganin gaba gaba Surayyerh dokanta zatai ita kam wannan karatun bokon bai mata rana ba. Hawayen daya cika idanunta ta mayar sbd babu dacewar yiwa Surayyerh kuka sai ta sake lalacewa. Surayyerh ta shiga zirga-zirga a bedroom ɗinta tunani ya yi mata yawa abin da bata tsammata ba a yanzu ya kawo mata farmaki. A firgice Halisa Danejo Rome ya farka daga nauyayyen barcin daya ɗauke ta mai cike da mafarkai wanda bata taɓa yin kamarsa ba, me ya sa Balaraban nan ke zuwar mata cikin barci ne? Amma gaba ɗaya yadda ta gansa a daji ya bambanta a farki, na cikin mafarkinta yafi kyau da kamala nutsuwarsa da kamewar shi tafi bayyana, kwarjinin dana mafarkinta yake dashi na zahiri baya da shi, duk mutum ɗaya ne? Ta tambayi kanta a cikin zuciyarta shiru tayi cike da damuwa domin ta fara gajiya da mafarkinsa. Motsin da taji kusa da ita ya sanya ta juya idanuna ya sauka akan Dada wacce take sanƙame numfashi na fita da ƙurar ciwo yaƙi ci yaƙi cinyewa. "Na lalashe na shiga uku Dada jikin ne? Sannu Dadata zaki samu lafiya" ta faɗa hawaye na wanke mata fuska gaba ɗaya ta ƙara zama wata kala damuwar ciwon Dada ya sata gaba, gashi yanzu Hamma Yabi baya yini gida sbd neman kuɗin zuwa asibitin burni. Jigum tayi tana kallon yadda kumfa ke fita ta bakin Dadar amma bata san me zatai mata ba, bata da wanda zata kira a cikin bukkar. Shatu dake rakuɓe ta kalli Danejo ta ce "Dada mutuwa zatai ko?" Girgiza kai Danejo tayi ta ce "Waya faɗa miki? Babu inda Dada zata yafi ta barmu aradu muna tare da ita" wata ƙara da Dada tayi tana sanƙamewa ya sanya Shatu fashewa da kuka, da gudu kuma Halisa Danejo Rome tayi waje. Karo sukai da Hamma Yabi wando ya shigo hannunsa riƙe da ƙwayar magani daya amsu, ya riƙe Danejo da kyau wacce take ƙoƙarin fita daga hayyacinta. "Hande en boni, Danejo lalashewa ya sameka me ya samu Dada?" Gaba ɗaya ta rikice sai ƙanƙame hannun Hamma Yabi take ganin bata hayyacinta ya jata ciki yana zuwa ya kwantar da ita yana rufe mata fuska shiru tayi har lokacin cikinta bai bar rawa ba, domin gani take kamar Dada tabarta kenan ta mutu ta tafi. Ya girgiza yana komawa wajan Dada tare da ɗagata ya bata maganinsu ya shafa mata zuwa fuska da wuya Ajjiyar zuciya ta sauke tana buɗe idanunta, hannun Hamma Yabi ta kama da kyau tana son tambayar shi mene ya samu Halisarta amma ta kasa, a haka barci ya ɗauke ta cikin mayuyacin hali. Washegari kamar kullum Danejo ta tatsi nono a ƙwayar, tun kafin gari ya yi haske ta fita kiwo da shanunsu, sai da ta ɗauki awa uku ta dawo cikin sauri tana tafe tana kaɗa naggen bayan ta ɗaure su ko abinci bata ci ba ta nufi cikin burni kawai tsaye zuwa Abti America. Yadda taje haka ta dawo babu wanda ya sanya kuɗi ya sai nonon balle su samu na abinci, a wahale ta shiga Rugar idanunta na rufewa ta kafa baki a nonon wata nagge ta shiga sha sai da cikinta ya ɗago taja Ajjiyar zuciya tare da nufar bukkarsu. Sheikh Aliyu haydar na kwance saman makaken gadonsa idanunsa akan screen ɗin laptop ɗinsa yana sauraran abin da ake faɗa ta cikin laptop ɗin. Can dai ya ja tsaki ya girgiza kai, speaking calmly ya ce "Ni ni niii da dddddd dama zaka zaka zaka sauya labarin nan naka Khalil, in anyway banga amm am am amfaninsa ba..." Dry sosai wanda aka kira da Khalil ya yi ganin yadda Sheikh ke runtse idanunsa yana buga kai duk dan ya kare kansa "To ai ni yana da amfani a wajena tun da abin da ya shafi Sheikh Aliyu haydar Aliyu ai shafi Khalil Ahmad Sarki, look Sheikh don Allah cire son zuciya ka faɗa mini mai mata sukai maka? Let me know" Sheikh ya shafa lallausan gashin kansa wanda yake kwance gwanin sha'awa, cikin son cire damuwar father a ransa ya dage yake hira da Khalil duk da yana shan wahalar magana ya jima bai magana mai tsayin haka ba, idanunsa lumshe ya ce "kakaka....ka kasan me?" Sheikh ya faɗa yana buga kansa jikin pillow yana riƙe ɗaya hannunsa sbd In-ina. Kallonsa kawai Khalil yake yana jiran jin abin da Sheikh ɗin zai faɗa, a wahale cikin In-ina wacce yake son ya saba magana da ita ya mirgina kaɗan yana riƙe kansa da hannu bibbiyu ya ce "man ta ta manta kawai, ya ya yaushe za za kazo?" Murmushi Khalil ya yi cike da ƙaunar Sheikh Aliyu haydar ya ce "Zamu zo da mai martaba wajan Hakimi, I think I will spend my two weeks vacation with you in Kano" jinjina kai kawai Sheikh ya yi ba tare da ya ce komai ba. "You are just afraid of women because you see yourself as a Sheikh, women are the happiness of a man, try and see" Girgiza kai kawai Sheikh ya yi ba tare da ya ce komai ba ya kashe vedio call ɗin. Umar-khan ne ke driving a hankali idanunsa akan titi amma hankalinsu na kan Sheikh dake manyan mota cikin wata dakakkiyar shadda fara tas ya ɗora golden ɗin Alkyabba sai rawanin daya ƙarawa fuskarsa kyau da haiba ya yi wani irin kyau kamar Balarabe ƙamshin Roja ya cika motar sosai. Yana ki shingiɗe a bayan motar tunani yadda zai sauya ya koma kamar yadda father yake buƙata, a haka suka ƙarasa Wani Restaurant mai kyau da tsari mara hayaniya, Umar-khan ya yi parking kasancewar fitar sirri ce yasa babu wasu masu take masa baya, cikin sauri ya buɗe Sheikh mota a nutse ya fito yana gyara zaman alkyabbar jikinsa tare da goya hannunsa a baya cikin kamala ya yi gaba Umar-khan na biye da shi zuwa cikin Restaurant ɗin. Zama Sheikh ya yi tare da kallon mutanan da zasu tattauna dasu, bayan sun gaida Sheikh ya ɗaga musu kai suka shiga nuna masa zanan bank ɗin daya buƙata na reshe uku, kaduna, Abuja, da Lagos. Baya cewa komai sai da Umar-khan suke tattaunawa gani ya yi zanan bai masa ba, domin babban bank yake so wanda ba a taɓa yin mai girman sa ba. Hakan ya sa ya amshi carbon paper da pen a nutse ya zana yadda yake so, zanan ya bawa ma'aikatan mamaki abin da basu sani ba, kaɗan kenan daga cikin baiwar Sheikh duk abin da ya sanya ransa yana gwadawa yake yi daidai. Sallama sukai bayan anyi musu transfer miliyoyin kuɗi domin fara aiki gadan-gadan. Ɓangaren Kamfanin sarrafa shinkafa ma tuni aiki ya yi nisa, ya yi ordern injina masu kyau daga Chaina. A gajiye ya dawo gida idanunsa na rufewa kansa ya sakarwa shower lokacin 1:30 ya saba barci tsakanin azahar zuwa sallar asr, fresh milk ya tsiyaya a cup tare da zuba honey ya sha kaɗan ya wanke baki, yana kwanciya barci ya ɗauke shi daman ya riga daya saba. Washegari ya kama weekend Sheikh bai san meke faruwa ba, sai daya farka yaji labarin tun 7 su Uncle Haroon da Abba Hakimi tare da Baffansa suka nufi garin Yola nema masa aure. Ko ajikinsa bai ɗauki auren matsayin wani abu, shi dai ya san ko farcen mace bai taɓa sha'awa ba balle ya birgensa. Da yamma su Abba Hakimi suka dawo cikin jin daɗin an basu auren Zahrah nan da sati mai kamawa za a ɗaura aure. Kasancewar yau Friday ne ya sanya Sheikh ya shirya cikin wata bugaggiyar shadda fara tas da ita mai ɗinki jamper da babbar riga, bai sanya hula ba sai hirami daya saka a saman sumar kansa ya ɗauki zagayayyen abun nan na larabawa Black colour ya ɗora saman hiramin, shekarunsa suka bayyana a jikinsa, domin kowa ya kalli Sheikh Aliyu haydar ya san ba yaro bane, girma ya fara hawa jikinsa babu mamaki ya yi aure a same shi da yara biyar haka, shekaru 34 ba wasa bane ba. Kai tsaye babban masallacin juma'a ya nufa sai da ya yi huɗu ba sosai mai ratsa jiki akan tsaida sallah a lokacin ta, tunda duk In-inar Sheikh inda karatu zai yi yana farawa ake nemanta a rasa. Bayan idar da Sallah ya nufi zaga gidan marayu kamar yadda ya saɓa idan yana ƙasa, a hankali yake tafiya hannunsa goye a bayansa kansa a ƙasa fitowar su kenan daga gidan marayu zasu shiga mota yaje gida wajan Mother, kamar daga sama wata budurwa kyakkyawa ajin farko ta tsaya a gabansu da sauri Umar-khan da Saif-wazir suka sha gabanta tun kafin securities su ƙarasu bakinta na rawa ta ce "Don Allah ku barni nayi magana da shi, na jima ina son haɗuwa da shi" Umar-khan ya daka mata tsawa ya ce "Baya buƙatar ganin kowa, kuma a mu'amalar shi baya yi da mata ki nemi wani wajan" A nutse Sheikh ya dakata tare da juyawa idanunsa zuwa inda budurwar take, waro fararen idanunsa waje ya yi yana mamakin abin da ya haɗa shi da bayin Allan nan da suke bibiyar shi. Murmushi mai laushi ya yi ba tare daya bari kowa ya gansa ba, yana mai ƙarewar budurwar kallo musamman ƙafarta. "Ka taimaka mini daga yanzu ba zan sake zuwa inda yake ba" Umar-khan ya yi mata wani ban zan kallo ya ce "Ke ko mayya ce ke baki isa kije inda Sheikh yake ba, kunne masu ƙullawa mutane sharri ko?" Sosai taji zafin maganar Umar-khan sai kawai ta juya kamar zata kifa sbd sauri. Tana barin wajan Umar-khan ya dafe kansa Saif-wazir ya ce "Are you okay?" Ya ce "Kai na ke ciwo, zazzaɓi nake ji" Umar-khan ya faɗa bakinsa na rawa kafin kace wani abu wani zazzafan zazzaɓi ya rufe Umar-khan. Girgiza kai kawai Sheikh ya yi domin ya san za a rina waya aiki Khan musayar yawo da aljani?. Da sauri Hamma Yabi ya shigo bukkarsu hannunsu ɗauke da kuɗi ya kalli Danejo wacce take sumar kanta ya ce "shai Alhmd kuɗi shun samu gobe zan kai Dada asibitin burni" murmushi Danejo tayi wanda ya ƙara fidda kyanta na fili ta ce "Kai Allah abin gdy Dadata zata samu lafiya yau ba zan barci ba sbd farin ciki aradu" Hamma Yabi ya kalli Dada dake kwance kamar haka cikin farin ciki ya ce "Insha Allah, da sassafe sai burni" fita ya yi farin ciki ya cika zuciyar Danejo Dada zata tashi su koma yadda suke rayuwa a baya. Hamma yabi bai dawo ba sai dare riƙe da ƙullin buduri da ƙosai mai zafi wanda ake a can wajan gari. Sai dai ko zama bai ba suka fara jiyo harbi ta ko wanne waje alamar ƴan fashi ne suka shigo cikin Rugar Rome. "Bone Hamma harbi harbi....," Bata ƙarasa faɗa ba suka ji an shigo bukkarsu wani mutum mai riƙe da bindiga ya kalli Hamma Yabi yana faɗin "Kuɗi,kawo kuɗi bamu da lokaci" jikin Hamma Yabi na rawa ya ce "Ba kuɗi bamu da shi" mutumin ya yi wata dry sosai ya ce "Babu? idan na bincika na samu duk hukuncin dana ɗauka akan kai ka sani" yana faɗin hakan ya fara bincike bukkar daga can waje harbi ake ta ko wanne sashe, cikin rashin sa a mutumin yaga kuɗin da Hamma Yabi zai kai Dada asibiti "Aradun Allah kuɗin asibiti ne, kayi mini ka taimaka Dada zamu bawa lafiya.....," Harbin da akaiwa Hamma Yabi a ciki ya sanya ya fasa ƙara tare da faɗuwa ƙasa ihu Danejo ta fasa ganin yadda jini ke zuba a jikin Hamma Yabi tana ƙoƙarin zuwa inda yake mutumin ya ƙara sakarwa Hamma harbi a tsakiyar kansa...... Wannan littafin na kuɗi zaka samu book 1, 2 akan ₦500 daga farkon labarin har ƙarshe ka tura ta wannan account ɗin 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman fidelity bank shaidar biya 08119237616. *🌈 IDAN BA KE 🌈* *_Arewabooks@Nimcyluv_* 14...... Cikin ƙaramin lokaci ƴan Rugar Rome suka shiga cikin tashin hankali musamman wajan su Danejo. Ko kuka ta kasa ta kafe gawar Hamma Yabi da kallo sai Ajjiyar zuciya take, shatu na gefe ta ƙanƙame jikin Dada wacce ke sanƙame bata san meke faruwa ba sbd halin da take ciki. Bata taɓa ganin anyi kisan kai a gabanta ba, yaushe gashi an kashe mata yaya wanda ke kula dasu shi kaɗai ya rage musu. Halisa Danejo Rome ta shiga halin firgici ita kaɗai tai ta razana har lokacin idanunta bai motsa daka kan gawar Hamma Yabi ba a haka Asuba ta risketa. Sarkin ruga da Giɗaɗo ne suka shigo bukkarsu Danejo ba neman iso domin basu damu da cewa Dada matar da za a nemi aminci a wajen ta bace. "Allahu Akbar Allahu ya jiƙan Yabi shai abu bai kyau ba sam" Sarkin ruga ya girgiza kai ya ce "Allah sharki aradu harbi har biyu dole ya mutu" da sauri Danejo ta miƙe jikinta na rawa ta kama hannun Giɗaɗo ta ce "Da gaske Hamma Yabi mutuwa ya yi? Da gaske ba zan sake ganin Hamma ba?" Ta faɗa cikin rauwanin muryar kana ganinta kasan damuwa ta jima da kama zuciyarta ta samu waje ta zauna. "Ya mutu mana kamar yadda Baffanku ya mutu ba zai dawo ba" ƙurr ta kafe Giɗaɗo da idanu kafin taja numfashi mai tsayi sai kuma ta sulale a wajan ta faɗi babu numfashi. A hankali take buɗe idanunta wanda sukai mata nauyi, hannunta ta kai tare da dafa kanta wanda yake mata ciwo sbd barcin data daɗe ta nayi. "Sannu kin farka Danejo?" Shatu ta furta cikin murnar ganin Danejon na motsi bayan suman da tayi. Danejo ta juya tana kallon Shatu kafin a hankali ta buɗe baki ta ce "Ina Hamma Yabi? Ya tafi da Dada asibitin burni?" Shatu tayi saurin faɗin "Hamma Yabi ya mutu ai kuma har an rufe shi a ƙasa" zuciyar Danejo ta buga da ƙarfi tana runtse idanunta sosai tsoro da fargabar makamar rayuwarsu ta dirar mata a zuciya, yaya za tayi da Dada? Ina zata samu kuɗin asibiti ko shanu zata siyar? Mai Hamma Yabi ya yiwa wannan mutunan da shi kaɗai kawai suka kashe cikin Rugar Rome?. Juyawa tayi ta sake kallon Dada wacce kawo yanzu ko motsi ba tayi ruwa ma idan aka bata ta gefen baki yake zubewa, hawayen da take maƙalewa suka sakko daga cikin idanunta Shatu wacce ke shirin yin kuka ta ce "Kuka ki ke Danejo? Me akai miki ba ga Dada ba muna tare da ita?" Danejo ta goge idanunta da kyau ta ce "Ba kuka nake ba, ki zauna wajan Dada bari naje wajan sarkin ruga na dawo" miƙewa tayi jikinta sanye da fararen kaya na Fulani sumar kanta ta naɗeta da wani zare mai ɗauke da kuran duwatsu masu kyau. Kanta a ƙasa take tafiya cikin sanyin jiki kamar ko yaushe a haka ta ƙarasa bukkar su Sarkin ruga ta tsaya daga waje tana neman iso. Matar Sarkin ruga ta ce "A'a Danejo ne bismillah shigo" kamar ba zata shiga ba sai kuma ta shiga ta samu Sarkin ruga zaune yana shan kindirmo a diririce ta ce. "Jamɓanduna. _Ina kwana_" Ya ce "Jamni.. _lafiya_" zata sake yi masa wata gaisuwar ya dakatar da ita da faɗin "mene ya kawo ki?" Kanta a ƙasa tana wasa da yatsunta ta ce. "daman cewa nayi ko zaka sayi nagge guda biyar daga cikin garkenmu?" Kallon tsaf ya yi mata yana sakin murmushi kafin ya ce. "Yabi bai faɗa miki ɗan cewa gaba ɗaya ba naggenku bane? Kiwo kawai aka baku?" Cikin rashin fahimtar maganar Sarkin ruga Danejo ta ɗaga kanta da sauri ta kalle shi tana faɗin "Dada ta sanar mini gaba ɗaya garken na Baffanmu ne, shanuwan sa ne, kuma kowa ya sani Hamma Yabi ma yasan da haka" Ya ce "E, to buɗe kunne kiji kaf cikin garken naggen nan guda biyu ne naku, sauran duk mallakina ne kuma yanzu zan ɗauka aje kasuwar burni a siyar dasu, idan kina buƙata sai a haɗa da guda biyun naku a siyar daga nan sai ku biyawa Baffan naku bashin da ake binsa ma" kasa cewa komai tayi ganin ƙarfen ƙafa da ake shirin yi musu, wanne irin son zuciya ne Wannan? A nagge sama da hamsin ace guda biyu ne nasu? Me ya sa Hamma Yabi bai taɓa cewa naggen Sarkin ruga bane? Da gaske nasa ɗin ne ko ba haka bane?. Jiki a saɓule ta dawo gida zazzaɓi na rufeta sbd fargaba. Kenan tana ji tana gani Dada zata sake mutuwa ta barsu basu da kowa a duniya?. Sheikh Aliyu haydar Aliyu na zaune yana duba yadda ginin bankunan guda biyu suka ɗauki harami cikin ƙaramin lokaci tare da kamfanin sarrafa shinkafa. A nutse cikin kulawa da haibarsa kamar kullum ya miƙawa Umar-khan Album ɗin. "Ina fatan komai ya yi yadda kake so?" Kallo ɗaya Sheikh ya yi wa Umar-khan a hankali ya juya kansa yana mai jinjina shi a nutse alamar "Ya yi" Umar-khan yai murmushi kaɗan yana jinjina halin Sheikh da yawan lokaci ba tare da ya ce komai ba ya juya ya fita. Ɓoyayyiyar Ajjiyar zuciya ya sauke yana mai miƙe ƙafafuwan shi saman table a hankali ya fara tunanin yadda zai gina rayuwar shi wanda zai sanya father farin ciki duk ƙoƙarin shi na gano abin da ke sanya father yaji zafin shi har haka ya rasa, da yawan lokaci abubuwan na damun shi nunawa ne kawai ba ya yi. Zuciyar shi na shiga tunani na tsayin lokaci. Miƙewa ya yi cikin kulawa ya shiga takawa a parlourn na shi, ƙarar wayar shi ta dakatar da shi daga tunanin da yake jin ringtone ɗin is different ya sanya ya fahimci mai kiran na shi. Farar Alkyabbar shi mai fidda ƙamshin Roja ya ɗauka tare da ɗorawa saman jallabiyar jikinsa banda dole ko hannun shi bai son a gani sbd tsarin halittar jikin na shi. Kansa a ƙasa ya nufi Main parlour babu kowa sai Hajjir bai ko kalle ta ba ya nufi sashin Abba Hakimi. A zaune ya same shi saman ladduma gabansa ɗauke da kayan marmari sai ƙwaryar zuba da kuma ta fura da nono. Zama ya yi yana fuskantar Abban na shi cikin mutunci bakin na motsa wa alamar gaisuwa Abba Hakimi ya yi murmushi ya ce. "Ba sai kace ba, Allhamdulillah" Sheikh Aliyu a lumshe idanunsa yana mamakin yadda Abba Hakimi ke fahimtar zuciyarshi da yawan lokuta. "Naga baka shirin auren naka, kamar dai you're not ready if i not mistaken?" Sheikh ya buɗe idanu da kyau akan Abba Hakimi cikin mantuwa domin gaba ɗaya ya manta da batun komai cikin In-ina yana riƙe Alkyabbar dake jikinsa da kyau tare da karkatar da kansa yana rufe idanu ya ce. "A...a...au au aure kuma A a Abba?" "E, Aure mana Sheikh haka za ka yi ta zama babu aure ni ma da kaina ban goyi bayan hakan ba, kayi aure kamar yadda Engineer ya buƙata ko dan samun kusanci da shi" Sheikh zai magana Abba Hakimi ya ƙara ɗaga masa hannu ya ce. "Kada kai musu, ka amince Allah ya sanya albarka, Engineer ya buƙata ka tura kuɗin lefin ita yarinyar tun da ba auren kake so ba, yi maka za ayi na fanshe ka na bada kuɗin lefen kamar yadda suka ce 2.5m zai isa komai na lefen" Sheikh ya ware idanu jin wai 2.5m kuɗin lefen yarinyar da ko sanin kamarta bai ba,baya buƙatar kuma ya sani ɗin. Cikin kyakkyawan lafazi Sheikh ya sake furta "2.. 2.. 2.5m A aaaa Abba yai yai yawa fa?" Abba Hakimi ya girgiza kansa yana mmkin yadda Sheikh babu abin da ya sani dan gane da rayuwar mace. "Meke sani Sheikh Aliyu? Kasan kayan mata da tsada, ko kai Alkyabbar nawa kake siya? Duk Alkyabbar ka tafi nawa kuɗi sosai, kuma a arziƙin da Ubangiji ya yi maka dan an taɓa 2.5m har wani abu ne?" Shafa gemunsa zuwa sajansa kawai Sheikh ya yi bai damu da auren ba, amma yaji daɗin yadda Abba Hakimi ke nuna kulawarsa ga duk abin da ya shafe shi. Abba Hakimi bai nunawa Sheikh ya san komai ga Bankunan da yake shirin buɗewa ba, dan haka sai ya ce "Ka tashi kaje can gidan, kuɗi kuma daman hakƙina ne na aurar da kai daga nan har sadaki" jin Sheikh yaƙi cewa komai ya sanya Abba Hakimi ɗago kansa ganin Sheikh ɗin ya yi zaune jingine jikin kujera ya dafe kansa da hannu bibbiyu zufa na yanko masa tsakanin gashinsa jikinsa na rawa kaɗan kaɗan. Girgiza kai kawai Abba Hakimi ya yi tare da jawo rubutun da ya yi da safe ya tsiyaya a cup ya zuba zuma a ciki ya juya kaɗan tare da ajjiyeta gefe guda zuwa lokacin da Sheikh ɗin zai daidai a hankali shi kuma yaci gaba da duba wani littafin Tafsir. Mother na zaune tana girgiza ƙafa cikin damuwa take kallon tilin kayan lefen dake parlourn, da sunan kayan lefen yarinyar da Sheikh zai aura. Yaya Halima ta ce. "Na daɗe banga kayan lefe mai yawan haka ba, shi Sheikh ɗin har nawa ya bada?" Motar ba ta ce komai ba sai Dr A'isha data kalli kayan da kyau ta ce. "Kalli fa Yaya iya gold guda biyar ne, Wallahi sai na ɗaukar wa su Maimoon kowa ɗaya abar shegiya da ɗaya kawai" Mother ta kalli Dr A'isha ta ce. "Tsinke na kayan nan babu mai ajjiye mini cikin gidan nan, balle su Maimoon su saka ba su rasa komai ba, a barwa wacce aka siyawa". Dr A'isha ta ce "Amma Barrister kalli kayan fa? Ni dai sai na ɗauka dukiya ai ba hauka bane" cikin faɗa Mother ta ce "Wai meke damunki haka A'isha akwai abin da kika rasa ne balle kayan nan su dameki idan su kike let me know I'll buy it for you" a sanyaye Dr A'isha ta cewa yayat tata "Am sorry Yaya"... "Sai haƙuri Barrister" cewar Yaya Halima wacce take babba a cikinsu. Miƙewa kawai Mother tai tana faɗin "Idan ban yi haƙuri ba kashe kai na zan? Ina nan dai wlh sai na aurawa Sheikh wata macan ya haɗa mata biyu" Dr A'isha ta ce "Wai ya kaga Sheikh da mata biyu" Dr A'isha ta kalli Yaya Halima ta ce "Nifa ina da shawara Yaya Halima, mai zai hana mu kai kayan lefen nan da kanmu zamu ƙara ganin ita Zahran da ake faɗa sai mu ganu tarbiyyar ta" Yaya Halima ta ce "Gulma zamu kenan? Maza ke kaiwa a bari su kai kawai?" Dr A'isha ta ce "Please mana Yaya Please" da ƙyar Yaya Halima ta amince ta ce zata nemi Engineer domin tasan yadda Mother ta ɗauki Al'amarin ba lallai tai magana ba. Da daddare duk suna zaune a parlour Mother, Yaya Halima, Dr A'isha dasu Maimoon da auta Fattoumah. Motar Sheikh tai parking a gidan da gudu Fattoumah ta miƙe yana faɗin "Yaa Lee Mother ta Yaa Lee nan" murmushin jin daɗi Mother ta yi ba tare da ta ce komai ba. A hankali ya fito da ƙafafuwansa waje kasancewar shi kaɗai ne da kansa ya yi driving hakan ya sanya gajiya ta saukar masa, yana fitowa Fattoumah na zuwa wajansa da gudu ta ce "Wlcm Yaa Lee" lumshe idanunsa ya yi tare da buɗewa, ganinta ƙarama kuma autarsu ya sanya ya sassauta fuskarsa tare da sunkuyawa ya ɗauke ta da hannu ɗaya, ɗaya hannun kuma ya rufe motar. Gemunsa taja ta ce "Yaa Lee ina kake zuwa muna ta missing naka" ya ware idanu bai ce komai ba sai hancinta da yaja kaɗan. Da idanu suka bisa yana sanye da shadda ruwan madara babbar riga da jamper bai saka hula ba sai hirami daya rufe kansa da shi fuskar shi mai ɗauke sanje zuwa gemu ta bayyana ta cikin hiramin daya gewaye fuskar. Ƙamshin Roja tuni ya mamaye parlourn da ƙamshi, Maimoon da Zeefa duk suka miƙe tsaye suna sakin murmushi a tare suka ce "Sannu da zuwa Yaa Lee" bai kalle su ba ya tattara hankalinsa gaba ɗaya ga Fattoumah dake masa surutu, bayan ya zauna saman kujera ya daidaita nutsuwarsa da kyau cikin ƙasa da murya ya ce. "Barka" ya faɗa kai tsaye ba tare da In-ina ba, Dr A'isha da Yaya Halima suka kalli juna. "Dani ka ke ko Yaya Halima?" Bai kula Dr A'isha ba ko kallonta bai ba domin yasan nemen magana ce. Tai dry ta ce "Ka gama kame fuska duk girmata da kayi dole ace da mijin iya baba, ko yanzu goma ta faɗi tafi biyar albarka dole na amsa sunan uwa a gare ka" miƙewa yai da Fattoumah ganin Dr A'isha na neman fasa masa kai da surutu. Kai tsaye Upstairs ya nufa ɓangaren father domin amsa kira. Yaya Halima tabi bayan shi da kallo ta ce "Sannu Dr da tsaurin ido, lallai karanki ya kai tsako Sheikh kike faɗawa haka? Sai da Barrister Maryam ta yi aure ta haifi Sheikh da shekaru huɗu ba aka haifeki?" Dr A'isha tai dry ta ce "Wallahi yaya ƙarfin hali ne kawai, amma ba ƙaramin kwarjini ya yi mini ba, gashi ko inuwata bata samu albarkar kallo balle Ni" dry gaba ɗaya sukai. a zaune Sheikh ya samu Father hannunsa riƙe da jarida idan kaga Sheikh da Father ba zaka taɓa cewa Sheikh ne ɗa ba, domin yafi cika idanu da jiki tsayi faɗi uwa uba fuskar Sheikh data samu sumar ƙwarai ta ƙara fidda asalin shi. A kan carpet ya zauna yana sauke numfashi kansa a ƙasa bakinsa na rawar gaida Father ya yi saurin ɗaga masa hannu ya ce. "Bani da lokacin jin faa kakkkkka yayyyya, na kiraka domin ka shirya zuwa Yola wajan Zahrah kafin akai lefe jibi, umarni na baka Aliyu ba shawararka nake nema ba" Jinjina kai kawai Sheikh ya yi bai ce komai ba. "Tashi kaje idan ka zauna ba zaka amfane ni da komai ba, zan bawa Saif-wazir address ɗin" miƙewa tsaye Sheikh ya yi sai da yaje bakin ƙofa Father ya ce "Ka kwana a nan, ban amince ka koma gidan Hakimi ba daga nan har ɗaurin aure" Sheikh ya juya da sauri ya kalli Father wato ya fahimci duk abin da yake masa baya damunsa shi yasa ya sanya Abbansa cikin al'amarin. Juyawa ya yi kamar yadda ya ce ya nufi Part ɗin nasa yana tattare babbar rigarsa. Washegari tunda ya yi sallar asuba bai koma ba, sbd wani irin mafarki da ya yi, abin ya tsaya masa yana son neman fassarar mafarkin wajan Abba Hakimi amma ya kasa, baya son mafarkin ya dangancin wani jinsi wanda ba nashi ba. Ƙarfe 7 daidai ya shirya cikin Milk ɗin shadda gezner bai saka babbar riga ba, sai golden ɗin Alkyabba daya sanya ya ɗora golden ɗin hirami, da ƙyar ya yi breakfast ɗin da Mother ta kawo masa shi ma sai da ta zauna ya gama jan ajinsa yaci kana ta fita ganin ko ƙala bai ce mata ba. Yana gamawa shirya wa Saif-wazir ya jashi zuwa garin Yola da taimakon Map. Sai da sukai nisa sosai sun ma bar Commission Quarter's ɗin sun nufi wani waje kamar daga Sama Saif-wazir yaji Sheikh yai gyaran murya kaɗan alamar ya tsaya. Waje ya nema ya yi parking gurin kamar jeji kamar ƙauye kuma. Cikin nutsuwa ya fito yana gyara zaman alkyabbar jikinsa, a hankali ya fara bin wata hanya hannunsa goye a bayansa. Sai da ya yi nisa sosai kana yaja ya tsaya. Kwance ya ganta kanta kife a ƙasa jini na zuba kaɗan a goshinta sai ƙwaryar kindirmon dake gefe guda hannunta guda riƙe da cikinta, da sauri ya zame idanunsa daga gare ta sbd kansa da yaji ya sara yana ƙoƙarin barin wajan wasu ƴan Fulani riƙe da Sanduna suka gewaye shi ɗaya ya ce "Aradu mun kama masu fyaɗen yara" Sheikh ya ware idanu amma bai nuna komai ba, wani ya ce "Wannan kamar kidnama waye kai?" nan ma shiru ya yi bai ce komai ba, Labo da yafi su iskanci ya kalli inda take kwance ganin jini a kanta ya ce "Aradu fyaɗe ya yi mata, kuma tunda kayi mata fyaɗe dole doka ta hau kanka" Sheikh trying to explain amma harshe ya sarƙe. "Kai ku saurara" Saif-wazir wanda hankalinsa bai kwanta da yadda Sheikh yabar motar ba, ya faɗa yana nufu wajan. Ƴan Fulanin suka tsaya ya kalle su sosai ya ce "Kuna hauka wanne irin fyaɗe mai yasa baku da tunani ne, yayi muku kama da wanda zai aikata haka?" Labo ya ce "Alkur'an sai na raɗeka da wannan sandan, ga jini nan muna gani ya kwantar da ita, dole kawai ya amshi hukunci" Saif-wazir ya ce "Wanne irin hukunci kuma?" Labo ya ce "Kai maza kira mana Giɗaɗo" abu kamar wasa kafin kace wani abu kusan gaba ɗaya ƴan Fulanin Rugar Bello suka zagaye Sheikh. Giɗaɗo ya kalli Sheikh kana ya kalli Labo ya ce "Zaro mana zoben hannunsa daka gani mai tsaida ne" Labo ya kama hannun SHEIKH tare da zare zoben, kusan mutuwar tsaye Sheikh ya yi yama rasa me zai ce, sai gumi dake yanko masa ya shigo ne domin tsinkar wani ganyen magani kalli yadda tsautsayi ya rutsa da shi. Kamar daga sama yaji Giɗaɗo na faɗin "Allhamdulillah mun riƙe wannan zoben matsayin sadaki" Saif-wazir ya ce "What sadakin me?" Giɗaɗo ya ce "Ai yanzu muka aura Wannan Balaraban aure da yarinyar nan, ni ne waliyin yarinyar Labo kuma waliyin Balaraban hakan shi ne hukuncin duk wanda ya yi wa wata fyaɗe a Rugar Bello, yanzu da shi da ita mata da miji ne halak ɗin sa ce.... Free pages yana gab da ƙare wa biya kuɗin ka domin shiga Paid book tuni sun yi nisa da karatu😂🤷🏾‍♀️.... Biya 500 ta Wannan account ɗin 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman fidelity bank. Shaidar biya 08119237616. Ƴan nijar sun yi mini magana. *🌈 IDAN BA KE 🌈* _*Nimcyluv sarauta*_ 15.... Saif ya ce "Aure kuma? waya ɗaura, dawa kuma?" Sheikh gyara tsaiwa ya yi zufa na yanko masa ta cikin naman jikinsa,kalmar auren ta gigita masa tunani dama lissafi baki ɗaya. Labo ya kalli Saif-wazir ya ce "Aradu aure aka ɗaura musu, babu wanda ya isa ya warware shi sai ikon Rabbi.. kai Giɗaɗo maza jawo mana su cikin Rugar Bello" cikin gargaɗi Saif-wazir ya nuna Labo da hannu ya ce "Saurara fillo kake kowa, an faɗa maka aure wasan yara ne? Kuma wanda kake cewa zaka aura masa ita already yana da aure wajan matar shi ma zamu, don haka babu wani aure idan ma kunyi sai ku warware auren yanzu nan" Labo ya ɗaga sanda sama gaba ɗaya sauran Fulanin suka ɗaga sanda sama tare da zagaye su Sheikh "ƙarya kake Aradu ina shemeka na sheme banza Alqur'anin Allah, aure kuma dole ne hukuncin duk wanda ya yi fyaɗe ko ya nemi lalata ƴar mutane ke nan, ku shige muje Rugar Bello" Saif-wazir zai magana Sheikh yaja numfashi da ƙyar yana girgiza masa kai domin sarkin yawa yafi sarkin ƙarfi musamman da yake ɓangaren Fulanin suka shigo tsaf za su yi musu gayya. And he doesn't want that to happen. "But Sheikh....," Sheikh ya ware idanu wanda suke ɗaukan hankali kamar ba zai ce wani abu ba sai kuma ya yi ƙasa da murya kamar wanda aka ɗauke wa In-inar ya ce. "Saif-wazir" kallon Sheikh kawai Saif-wazir yake cikin mamaki. Suna ƙoƙarin tsallake ta su shige Labo ya yi saurin faɗin "Waye zai ɗaukar maka matar ka? yadda ka kawo ta nan haka zaka ɗauke ta mu ƙara sa Rugar Bello" a fili Saif-wazir ya ce "Tab..." Domin yasan that's the first thing da Sheikh can't do it ba zai taɓa ɗaukan ta ba. A hankali Saif-wazir ya sunkuya zuwa inda take kwance zuciyarsa ta buga da ƙarfi lokacin da idanun shi ya sauka akanta. A ruɗe ya juya ya kalli Sheikh Aliyu haydar Aliyu wanda ya tattare Alkyabbar jikinsa idanun shi rufe lokaci guda jijiyoyin kansa suka fito hakan kuma tabbaci ne na zuciyar shi na kusa, tashin hankalin da Saif-wazir ya shiga lokacin da idanun shi ya sauka akan fuskar Halisa Danejo Rome yafi ƙarfin tashin hankalin da Sheikh Aliyu haydar Aliyu yaji akan batun auren nashi da suke ƙoƙarin ƙaƙaba mishi. Saif-wazir ya daidaita nutsuwarsa wani kuzari na zuwar masa mmkin abin da idanun shi ke nuna masa ya cika masa zuciya. Ɗaukan ta ya yi daidai lokacin da Sheikh ya runtse idanunsa yana juya baya da ɗan sauri bakinsa ɗauke da sunan Allah. Saif-wazir na gaba ɗauke da Danejo Sheikh Aliyu haydar Aliyu na binsa cikin nutsuwa da daddako haɗi da kamala yanayin yadda ya kame kansa yake tafiya zaka ɗauka sarki ko Hakimi ne. Gaba ɗaya ƴan Fulanin suka mara musu baya har zuwa Rugar Bello lokacin tuni saƙo ya isa wajan Arɗo gaba ɗaya sun fito tare da yin shimfiɗa a gaban wata bukka wacce ta cika da yalwar inuwa, tun daga nesa Arɗo ke kallon Sheikh Aliyu har cikin ransa bai na'am cewa zai aikata abin da Giɗaɗo ya faɗa ba, amma ya kasa fahimtar mene ya sanya yaji auren shi ne mafita a gare shi dama su baki ɗaya?. Saif-wazir na zuwa ya kwantar da Danejo wacce har lokacin bata farka daga suman da take ba, jini kuma bai daina zuba daga goshinta ba. Arɗo ya kalli Sheikh cikin mutumtaka ya ce "Ka zauna mana?" Ko inda yake Sheikh bai kalla ba balle ya ama shi, sai ma tsaiwa daya gyara yana ɗan duba time fuskar shi tai jajir. Arɗo ya jinjina kai yana ƙara samun ƙarfin gwiwar abin da zuciyar shi ke ayyana mishi. Cikin nutsuwa ya ce "Sannunku, an kawo ƙarar an kama wancan yana ƙoƙarin aikata abin da Rugar Bello ta hana, wasu sunce ya aikata ga yarinyar nan kwance, bisa doka duk wanda ya yi hakan muna ɗaura masa aure da ɗiyar wannan ya sanya zamu aura masa yarinyar nan a yanzu ba tare da ɓata lokaci ba" Sheikh dai jin abin yake kamar ta tsuniyar yara ko damuwa bai ba, auren Zahrah ba bai taɓa damunsa ba balle na wannan ƴar tayin yarinyar. Saif-wazir ya ce "Amma wannan kuskure ne, idan mutum baya so ba, kuma ai ba haka ake ɗaukan doka ba, shigowarmu garin kenan fa suka fara ihun ya yi me ne kamar wasu marasa ilimi?" Giɗaɗo ya ɗaga sanda zai makawa Saif-wazir Arɗo ya yi saurin cewa "A'a Giɗaɗo, ko ma dai yaya ne kuyi haƙuri aure babu fashi" Modibbo da tun ɗazo bai magana ba ya ce "Sai a karɓi sadaki wajansa ai babu lokaci" Labo ya ce "Ga wannan a wajansa muka amsa" ya miƙawa Modibbo zoben gold ɗin da suka amsa wajan Sheikh. Sai a lokacin Saif-wazir ya ƙara cewa "Ga kuɗi a bada zoben, yana da tsada sosai kuma yana da muhimmanci ga mai shi" Modibbo ya yi murmushin jin daɗi ya ce "Daman abu mai daraja muke buƙata ai" abu kamar wasa akan idanun Saif-wazir da kunan Sheikh aka ɗaurawa Sheikh Aliyu haydar Aliyu aure da Halisa Danejo Rome akan sadakin zoben gold. Modibbo ya zama waliyin Danejo Arɗo ya zama waliyin Sheikh. Mutane kusan ashirin suka shaida daga ciki harda Saif-wazir. Shiru wajan ya ɗauka Saif-wazir ya rasa ta ya ya zai kalli idanun Sheikh ya ce da gaske Danejo matarsa ce? Zai amince da auren ne ko ya ya? Kamar gilmawar walƙiya haka Sheikh ya juya yana gyara Alkyabbar jikinsa kai tsaye baki n titi kuma ya nufa,ganin haka ya sanya Saif-wazir miƙewa da sauri Arɗo ya ce "Ina zaka baka ɗauki yarinyar ba?" Saif ya juya ya kalleta rauni ya bayyana a fuskar shi har baya son kallon yarinyar gani yake kamar idanunsa ke masa gizau da abin da yake gani ɗin. Da sauri ya ɗauke ta ya marawa Sheikh baya yana zuwa titi ya samu Sheikh zaune acikin mota ya dafe kansa da hannu bibbiyu hayaniyar duk ta sauya masa lissafi baki ɗaya, Saif na shirin saka Danejo cikin motar Sheikh ya ce "N...n.. No!!!!" Ya faɗa cikin tsawa da faɗa idanunsa na fitowa waje sosai da kyau, a tsorace ya ce "Jini na zuba a jikinta kada ta samu ƙarewar jini kuma ba zamu je da ita gida haka ba sai mun fara zuwa asibiti" kallon da Sheikh ya yi masa ya sanya Saif yin shiru yana ƙasa da ƙansa. "Please Yaa Lee Matarka...." Kafin Saif ya ƙarasa Sheikh ya yi wa motar key cikin wani irin azababban gudu ya juya kan motar tare da cillata titi ya nufi hanyar da zata mayar da shi Kano ba tare daya ƙarawa wajan Zahrah ba.. Baki Saif ya saka cike da mmkin zafin zuciya irin ta Sheikh Aliyu da alama za a sha fama kafin Sheikh ɗin ya amince da batun auren Danejo ɗin. Mota ya tsayar ya ce masa asibiti mafi kusa don Allah. Kai tsaye aka kai shi Specialist Yola dake Jimeta. Yana shiga reception yaci karo da wata cikin sauri ya ce "Oh sorry it was a mistake.." Tsaki ta ja ta ce "mistake ko rashin hankali Malam? Kana tafiya kai a sama" kallonta kawai ya yi shi bashi da lokacin ta ma, Saurayina ta ce "Banza kawai" Zahrah da hankalinta ya yi gida sbd zuwan wanda yake shirin zama mijinta ta ce "Wai Surayyerh har lokacin cacar baki gareki ne? Tunda muka zo asibitin nan ki ke neman faɗa" Surayyerh ta ɗaga hannu ta ce "Saurara Zahrah ke tunda kika samu cikin nan kike ji da masifa, daidai nake da ko wanne ɗan iska Wallahi" Saif-wazir ya kalli Zahrah da kyau kaya ne wanda suka kama jikinta sosai hannunta duk farce taci gashin doki, juyawa ya yi ya kalli Surayyerh ba tare ce komai ba ya juya zuwa cikin emergency. Kai tsaye aka bawa Danejo gado Dr ya kalli Saif-wazir ya ce "Suna?" Saif ya shafa kansa sbd sam bai sani ba sai kawai ya wayance da faɗin "Dr ka fara yi mata taimakon gaggawa, sai mu yi magana" Dr ya ce "Dole a buɗe mata file ai" "I knw, amma kulawa da ita ba zai hana buɗe file ba, a duba ta first buɗe file second" Dr ya miƙe tsaye tare da nufar ɗakin da suka kwantar da Danejo abun mamaki ba ita ba alamarta, cikin hanzari ya fito sukaci karo da Saif-wazir ya ce "Yarinyar nan ta gudu bata cikin room ɗin?" Saif ya ce "What?" Da sauri ya juya zuwa waje amma neman duniya babu Halisa Danejo Rome babu ko inuwarta "Innalillahi yau na shiga uku ko dai aljana ce yarinyar nan? Amma babban asibitin irin wannan ina zata?" Ganin bashi da wata mafita ya nemi abin hawa wanda zai dawo da shi Kano domin ba zai iya komawa Rugar Bello ba yace bai ga yarinyar ba, haka kurum su kashe sa a banza. Ɓangaren Halisa ana kwantar da ita a saman gado A.c ta fara ratsa ta, ta farka da sauri tana dabe kanta, tsoro ya kamata tana mamakin yaushe tazo. Ita dai ta fito tallan Kindirmo ta ce bari ta biya ta Rugar Bello a hanya yunwa da jiri suka yarda ita, kanta ya daki wani dutse bata ƙara sanin inda take ba. Miƙewa tsaye tayi jikinta na rawa ta ce "Hande en boni gidan cire kai aka kawo ni wayyo Allah Dadata na lalashe, lalashewa ta sameni" kuka take sosai har da majina fuskarta tai jaa. Leƙewa tayi ta window taga ashe bayan asibitin ne, da sauri ta kama tagar ta dira baya duk da zafin da kanta ke mata amma haka ta dinga gudu kamar barewa a haka ta isa Rugar Rome. Shiri sosai Zahrah tayi ta tarbar Sheikh amma har dare babu labarinsa baƙin cikin duniya duk ya kamata ga ƙawayenta duk ta tara zata nuna musu haɗaɗɗan mijin da zata aura amma ya kwafsa mata. Misalin 10:23 Abba Hakimi na zaune a Main parlour dashi da Momi kamar daga sama su kaga Sheikh ya shigo hannunsa guda ɗaya dafe da kansa, Momi zatai magana Abba Hakimi ya Girgiza mata kai alamar tai shiru,babu wanda ya kula ya shige part ɗinsa dake gidan, kai tsaye bathroom ya nufa bayan ya zame kayan jikinsa abin da bai taɓa yi ba shi ne, amfani da ruwan sanyi ya tsaya a shower na sauka akansa sanyi na ratsa masa tsakiyar kansa, sai numfashi yake fitarwa dan kansa ya kashe shower ɗin ya naɗe jikinsa a cikin wata bathroom mai ɗan kauri, idanunsa na rufewa sbd azababban ciwon kai a haka ya kwanta saman gado ya daɗe kafin barci ya ɗauke sa. "Lafiyar Sheikh ɗaya kuwa?" Abba Hakimi ya ce "Kinga alamar bai da lafiya ne?" Momi ta ce "A'a, kawai yadda na shigo gidan ne" Apple ɗin hannunta da take miƙa masa ya amsa ya ce "Kada ki damu, duk sanda ya yi haka alheri ne ke bibiyarsa" tattaunawa sukai akan gobe za a kai kayan lefen na Sheikh ita ma zata a hankali ya ce "Allah ya kaimu" sai kusan 12 na dare Sannan Saif-wazir ya shigo ganin dare ya yi kai tsaye ya nufi part ɗinsa, motar Sheikh da ya gani ya bashi tabbacin ya dawo gida. Da batun Auren Sheikh ya kwana yana tunanin ya faɗawa Abba Hakimi ko ya yi shiru? Har barci ya ɗauke shi ba samu mafita ba. Washegari da yamma wajan 5. Dr A'isha ta zabga tagumi Yaya Halima ta ce "Dr wai lafiya tun da muka dawo kike wata kala?" Dr A'isha ta ce "Wallahi Yaya tausayin Sheikh nake, ina zai kai wannan uwar matar? Na girgiza ban san rashin tarbiyyar ta ya kai haka ba, kalli da ita aka amshi kayan lefen fa?" Yaya Halima ta kalli Dr A'isha tana mmkin rashin control na bakinta da bata iya riƙe zance. "Kowa da tsarinsa fa Dr Allah dai ya sanya albarka" daga bakin ƙofa akace "Ba Amin ba, mugun ji da mugun gani ruɓaɓɓan baki ya kau daga kan Gadanga, yau ko ni ko uban Gadanga ya zaɓa" gaba ɗaya suka kalli bakin ƙofa, tana tsaye taci lace ɗauri har gaban goshi ta lafta uban Glasses a fuska wanda ya cinye rabin fuska. Cikin farin ciki Mother ta miƙe tsaye tana faɗin "Jadda" haɗe fuska tayi ta nemi waje ta zauna, Uncle Haroon ya shigo hannunsa riƙe da torelly ɗin Jadda ya zauna kusa da ita. Cikin farin ciki Mother ta ƙara cewa "Sannu da hanya Jadda ashe kina tafe" Jadda ta ɗauke kai sai da Mother tabar wajan, ta juya ta kalli Uncle Haroon murya can ƙasa ta ce. "Munafuka Algunguma duk masifa da yaƙin da ake a gidan fa bata sanar dani ba, shi ya sa na haɗe mata fuska na kame kai na, ba kaga jikinta ya yi sanyi ba, ai wlh yau sai sun bala'i ya sauka" murmushi kawai Uncle Haroon ya yi ta haɗe rai tana ƙanƙantar da idanu ta ce "Kaji masifa ko? Ba murmushi za kai ba cewa zakai nayi daidai" ya ƙara murmushi ya ce "Jadda duk abin da ki kai ai daidai ne" cikin ƙaramin lokaci Mother ta cika gaban Jadda da kaya kala-kala, Yaya Halima da Dr A'isha suka gaidata ta amsa a ciki. "Kinga ba kwaɗayi ya kawo ni ba, maza kira mini mijin naki" Mother ta haura sama yana zaune yana duba Invitation ɗin bikin Sheikh dana Zahrah Mother ta shiga a hankali ya ce "Barrister ya dai?" Kai tsaye ta ce "Jadda na kira" tana faɗin hakan ta juya, yabi bayanta da kallo da sauri kuma ya miƙe shima. A hankali yake sakkowa daga benen yana sakin fuska bayan ya zauna ya ce "Sannu da zuwa Jadda" banza Jadda tayi masa, ta zare Glasses ɗin idanunta ta miƙawa Uncle Haroon, ta cire mayafi shima ta miƙawa Uncle Haroon, fuskar Father cike da tsoro ya ce "Jadda lafiya me kike shirin yi haka?" Bata kula shi ba, ta buɗe rigarta tana nunawa father ta ce "mene wannan?" Kansa a ƙasa ya kasa cewa komai ta ce "Idan ba zaka iya ba, ai Ubangiji ya tsaga mini bakin magana nonon dana shayar da kai ne, kasan Allah tun nonon yana kwance ka lalata batun auren Gadanga da wannan gantalalliyar yarinyar, idan ba haka ba zan ɗaga maka nonon sama ka lalace kaje duk inda zaka... *Not edited* Masu tambayar yadda zasu biya kuɗin IDAN BA KE. Book 1, 2 ne. Mutum zai biya ₦500 har a gama littafin baki ɗaya. 6850917335 Na'ima Shu'aibu sulaiman fidelity bank. A tura shaidar biya ta nan 08119237616. *🌈IDAN BA KE 🌈* *_Nimcyluv Sarauta_* 16.... *I am proud of my fans wherever they are, nayi mamakin yadda kuka amshi littafin IDAN BA KE fiye da ZAIN-ABEED. Masoya TSINTACCIYA, MOON, UNCLE NE duk ba a barku a baya ba🥰💋for the first time zanyi rubutu akan labarin zanan ƙaddarar soyayya zallah🫰🏿a shirya a gyara zama sosai yanzu aka fara...* #TEAM SHEIKH ALIYU HAYDAR ALIYU #TEAM HALISA DANEJO ROME #TEAM EL-BASHIR AHMAD SARKI #TEAM ZAHRAH FAROUK Jadda ta ƙara cewa "Kalle ni da kyau uwarka ce Jadda, Wallahi nono zan ɗaga maka kawai kabi duniya kaje duk inda zaka Aliyu tunda ka gagara, idan ya so ana nunaka da baki ana cewa gashi can uwar shi tai masa baki ta ɗaga masa nono shi ya sa yake ta galantuyi a duniya, duk wanda bai yarda ba, ni nai maka baki ba zaka iya kawo shi wajena na tabbatar masa" zufa ta dinga yankowa Father a hankali ya zame daga kan kujera zuwa inda take ya ce "Jadda don girman Allah kada kice haka, ki tsaya ki fahimci al'amarin nan I have a reason why I want Sheikh to get married with Zahrah." Uncle Haroon ya ce "Mene dalilin naka? Uwar yaron nan bata so, I don't agree either" Jadda dai kaɗa ƙafa take har lokacin tana riƙe da ƙirjinta cikin rarrashi Father ya ce "Jadda don ki fahimce ni Sheikh ba zai iya kula da dukkan al'amarin daya shafi kasuwancina da dukiyata ba, kullum ƙarfina ƙasa yake abubuwa na neman yi mini yawa, na bashi dama yafi sau goma akan ya kawo matar da zai aura amma yaƙi, Umar-khan yace tunda Sheikh yake magana bata taɓa haɗa shi da wata mace ba, kalli sharrin da akai masa tun daga jami'ar Madina, da ace yana da aure babu mai binsa da wannan sharrin shi ya sa na yanke hukuncin aura masa ƴar aminina tasan kan business sosai zata janye hankali Sheikh ɗin zuwa kasuwancin, Jadda ina son Sheikh Aliyu ban taɓa son wani abu kamar shi ba, kiyi mini uzuri ayi auren nan idan yarinyar ba tai miki ba sai ki ɗauki mataki" Mother ta girgiza kai cike da takaicin yadda Father yake tsara zan ce. "Aini duk bani da labarin haka, jiya jiya labari ya saman ana ta yaƙi a gidan naka, kuma yarinyar ƴar iska ce" Father ya kalli Jadda da kyau ya juya ya kalli Mother yana faɗin "ke kika faɗa mata Zahrah ƴar iska ce sbd ba ƴarki bace shi ya sa zaki ai bata musu ƴa?" Rai ɓace Mother ta ce "Ni na faɗa Engineer tunda haka zuciyarka ta shaida maka, kaga yaushe rabon da naje wajanka akan maganar Aliyu ko auren? Aje ayi aure lafiya nima zan zaɓawa Sheikh yarinyar da nayi niyya na aura masa ita" tana faɗin haka ta miƙe tare da nufar upstairs zuciyarta cike da tarin baƙin ciki. Baki buɗe Jadda ke kallon kowa kafin ta ce "Na amince ayi auren kuma na amince Maryam ta zaɓawa Gadanga yarinyar da duk tai niyya" Father ya ce "Amma Jadda daka aura masa Zahrah sai ya yi mata kishiya? Ba ai mata adalci ba" Jadda ta miƙe tsaye tana ƙanƙance idanu ta ce "Wai wacce ƙaniyar ce Zarra ko me? Ba ita ba ko uwarta ka aurawa Gadanga kwaranƙwasa sai anyi mata kishiya, Allah dai ya nuna mini ƴar banzar yarinyar da idanu naga abin da bai mini ba, maza ɓace mini da gani ko mene haɗina da kai dana tsaya shiga sabgar ka" Father ya miƙe tare da barin wajan yana faɗin "A huta lafiya Jadda" sai da yabar wajan Jadda ta sauke numfashi tana raɗawa Uncle Haroon ta ce "Ba gashi ba anyi sulhu komai ya lafa daman duk iskancin mutum ina zuwa shikenan, ai Alsulhu khair" murmushi kawai Uncle Haroon ya yi yana cewa sai Anjima zai dawo. Sai a lokacin Jadda ta lura da Yaya Halima da kuma Dr A'isha kowa yana danna waya abinsa kasancewarsu masu ilimi da dukiya ya sanya suka kame kansu basu saka baki cikin abin da babu ruwansu ba. Mother na zaune tana waya da wata friend ɗinta kamar daga sama Father ya faɗo ɗakin cikin faɗa ya ce "Burinki ya cika kin haɗani da mahaifiyata,she insulted me in front of people data hana auren Zahrah da naki auren ma sai ya mutu" tunda ya fara magana bata kula shi ba sai ƙafa da take girgizawa tana ci-gaba da yin wayarta hakan ya ƙona ran Father yaso ta tanka masa ya wanke ta tsaf. Saif-wazir na zaune gaban Abba Hakimi ya kasa cewa komai. Abba Hakimi ya ce "Ya kai ne Saifuddeen?" Ya sauke numfashi ya ce "Abba ban san ya zaka fahimci maganata ba" Abba Hakimi ya ɗaga kansa tare da kallon Saif-wazir ya ce "Tunda ba zan fahimta ba ta shi kaje" da sauri ya ce "No Abba I'm sorry" shiru yai can dai ya ce "Daman akan zuwa Yola da mukai da Sheikh ne, tsautsayi ya faɗa masa na auren wata ƴar Rugar Bello" Abba Hakimi ya ƙara kallon Saif-wazir da idanun na fahimta a hankali ya ce "Uhm Aure dai?" In short, Saif told Abba Hakimi about everything that happened daga zuwansu Yola har fitar Sheikh mota da zuwan Fulanin har auren da aka ɗaura da zoben Sheikh ɗin matsayin sadaki, har maganar zuwa asibiti da ɓacewar yarinyar. "Aiki jaa" Abba Hakimi ya faɗa a ransa wannan shi ne dalilin daya sanya Sheikh ya dawo a rikice kenan? "Kace yarinyar ta gudu? Zaka gane ita Rugar?" Saif ya ce "E, ta gudu Abba Rugar ma zan gane domin akan hanya take, amma bana ganin Sheikh zai amince da auren mata biyu lokaci guda" murmushi Abba Hakimi ya yi wanda shi kaɗai yasan ma'anar shi a nutse ya ce "Auren da ai masa na haɗi ne, wannan kuma Ubangiji ya ƙulla, Allah ya nuna mana zuwa Yola ɗaurin aure zamu je can Rugar" Saif-wazir ya jinjina kai alamar gamsuwa ta gefe guda kuma ya kasa faɗawa Abba Hakimi abin da ya gani a tattare da ƴar fillon wanda ya ruɗa masa lissafi ya hana shi bacci daren jiya. "Jirginsu Mai martaba ya tasu, zuwa ƙarfe huɗu zasu sauka yace Sheikh buƙatar ya je ɗakko shi, yanzu kuma lokacin barcin Sheikh ne" Saif ya duba lokaci ya ce "Yana barci tsakanin Zhur zuwa Asr jirgin kuma 4 zai yi landing akwai time Abba" Abba Hakimi ya ce "Mafi mushkila" Bayan fitar Saif-wazir Momi ta ce "Amma bana ganin wannan auren ya ɗauro fa?" "Me ya sa A'isha?" Momi ta ce "Naga babu wani na Sheikh a wajan sai Saif" jinjina kai kawai Abba Hakimi ya yi yana ci-gaba da rubutun shi ta ce "kayi shiru?" Bai kalleta ba ya ce "Idan kika sake cewa I'll do the same thing, aure ba shaidu da sadaki yake buƙata ba? Saifuddeen ya ce shaidu wajan 20 a wajan, Zoben da suka amsa kin san darajar shi kam?, Aure ya ɗauro kamar na ko wanne ma'aurata" Momi tai murmushin jin daɗi ta ce "To Allah ya sa albarka,ya sanya matar shi ce har aljanna sai a faɗawa Barrister" nan ma Abba Hakimi ya ce "A'a Maganar ta tsaya iya mu, bana son ko su Umar-khan da Ishaq-hakim suji, hatta Barrister Maryam da mijin nata bana son suji" hira sukaci gaba dayi. Ƙarfe 4:5 daidai Sheikh Aliyu Haydar Aliyu ya fito sanye cikin dark blue ɗin shadda jamper da babbar riga, sai ƙamshin Roja yake wanda ya a cika parlourn. Ƙafarsa cikin Leather shoe sumar kansa wacce ya rufe da hirami ta sha Ginger Geminal Oil-hair daga sajansa zuwa gemu sai kyallin Luxury Beard oil yake. Bakinsa sai ƙamshin LB Breathe herbal sugar breath freshener spray. Fitowar shi cikin parlourn ya yi daidai da shigowar Abba Hakimi, Umar-khan da Ishaq-Hakim na binsa a baya. "Daman yanzu nake shirin zuwa sashin naka sai gaka" zama ya yi Sheikh yana gyara Babbar rigarsa yau ba saika Alkyabba ba, a nutse cikin kamala murya mai ɗauke da kwarjini ya buɗe baki ya ce "Barka da yamma Abba" kallon kallo akai tsakanin Umar-khan da Ishaq-Hakim jin yau Sheikh bai In-ina ba, Abba Hakimi kam murmushi kawai ya yi hakan bai wani dame shi ba ya ce "Yawwa Sheikh Dadynka Mai martaba ya sauka yanzu kai suke jira" Sheikh ya duba agogo ya riga yasan sai biyar jirgin zai sauka yana komai bisa tsari. Bai ce komai ba ya miƙe tsaye Abba Hakimi ya bisa da kallo yana mmkin sauyawar Sheikh da yawan lokaci kamar mai cin naman wahainiya yanzu zaka ɗauka yana da yara kusan biyar sbd yana yin kamalar shi, amma fuskarsa bata nuna shekarunsa ba kullum cikin kame ta yake. Yana fita aka buɗe masa bayan mota, Umar-khan yaja Ishaq-Hakim da Saif-wazir suka shiga mota ɗaya sai airport. Zuwansu airport ɗin ya yi daidai da saukar jirgin har lokacin Sheikh na mota bai fito ba. Khalil Ahmad Sarki ne ya fara ɗakko daga cikin jirgin sai Mai martaba Ahmad sarki na uku ya shiga ɗakko cikin nutsuwa hannunsu riƙe da sanda, fari kyakkyawa da shi wanda zai iya yin shekaru wajan 65 da haihuwa. bayan sakkowar Mai martaba wani saurayi ya shiga sakkowa ganin saurayi ya sanya hantar cikin Saif-wazir juyawa, nan take kuma ya tuna da abin da idanun shi ke maza gizau. Zai iya yin shekaru 25 da haihuwa fari kamar mahaifinsa mai martaba har yari Mai martaba kyau da haske, Three-piece dinner suit a jinkinsa saɓanin Khalil Ahmad Sarki dake cikin shiga ta sarauta. Gaba ɗaya suka zube tare da gaida Mai martaba Ahmad Sarki. Khalil nata ware idanun ganin Sheikh can ya leƙa bayan mota ya ganshi zaune ya rufe idanun shi. "I expected to see you right here" Sheikh ya buɗe idanu ba tare da ya ce komai ba, cikin tsokana duk da Sheikh ɗin gaba yake da Khalil ya buɗe masa ƙofa yana faɗin "Ango kasha ƙamshi, Finally the Sheikh will get married, praise the couple's line" har lokacin dai Sheikh bai kula Khalil ba sai fitowa da ya yi daga cikin motar a hankali ya ƙarasa Wajan Mai martaba ya ɗan sunkuyar da kansa Mai martaba ya ce "Yau gani ga Sheikh tunda yaƙi zuwa inda muke" ya lumshe idanunshi tare da buɗewa ya saki murmushi wanda ya sanya kyansa fitowa sosai. Sheikh da Mai martaba suka shiga mota ɗaya, Khalil ya shiga bayan motar su Saif-wazir Mai martaba ya kalli matashin saurayin ɗan na shi ya ce "El-bashir..." Wanda aka kira da El-bashir ya ware ido murya a sake ya ce "Mai martaba zan zo" yana faɗin hakan ya juya yana tsayar da mai texsi... Abu kamar wasa ɗaurin auren Sheikh ya rage saura kwana uku cif. Har lokacin da Sheikh da El-bashir ba a haɗu ba, Sheikh ba manta da wata Yola baki ɗaya balle Auren da yake kansa na ƴar fillo. A ranar aka kammala gina Bankunan Sheikh na Lagos da Abuja, tare kamfanin sarrafa shinkafa an zuba komai da komai ranar buɗewa kawai ake jiran Sheikh ya saka sai kuma ɗaukan ma'aikata. Yana kwance a bedroom ɗinsa dake gidan father ya miƙe da sauri kamar wanda aka tsikara yana sanye da embrodiery Islamic jallabiya a hankali ya shiga duba contact ɗin wayarsa abin kunya ko number Maimoon bashi da ita, number mother ya kira aka ɗauka cikin dry akace "Yarona ya akai?" Muryar Dr A'isha ta sanya ya kwaɓe fuska ta ce "Ya akai? Ya kamata nazo na saka maka albarka" numfashi ya sauwaƙe "Uhm Maimunatu fa?" Mamakin maganar Sheikh kai tsaye ba In-ina ta cika Dr A'isha da sauri ta ce "Sorry who am I speaking with?" Kashe wayar ya yi gaba ɗaya. Dr A'isha ta juya ta ce "Maimoon kije part ɗin Sheikh wani yana kira" "wani kuma Aunty?" Dr A'isha ta ce "haka dai na fahimta" Maimoon ta miƙe tare da saka hijabi tasan tana zuwa haka zata ci ƙaniyarta. A parlour ta same shi hannunsa riƙe da Black tea wanda ya aka saka zuba a ciki. Jikinta duk rawa yake ganin yadda ya tsareta da idanun ya zame idanunsa ciki rashin tsammani ya ce "Kinga Aljani ne?" T ɗaga idanu da sauri ta kalle shi ta ce "A'a Yaa Lee kayi haƙuri" ya share zan can tana da zaune sai da ya gama shan tea ɗin son ran shi can ya ce "ki nemi number yarinyar nan" sai kuma ya yi shiru ta miƙe tana faɗin "na fahimta" waje tayi kai tsaye ta nufi upstairs part ɗin father lokacin ya gama raba Invitation baki ɗaya "Daughter ya akai ne?" "Father number Anty Zahrah zaka bani mu fara gaisawa kafin tazo" father yaji daɗin haka sosai ya bata number Zahrah ya ce "Baku fara shirin bikin babban yaya bane?" Ta ce "Father anjima zamu saloon gobe mai zana henna zata zo tai mana" waje tayi da sauri ta koma part ɗin Sheikh tare da kai masa number Zahrah. Zahrah na zaune with her best friends ana musu henna sbd anjima suna da event. Wayarta tayi ƙarar da sauri ta duba text ɗin data gani ya girgiza mata lissafi ta miƙe da sauri ta nufi bedroom ɗinta ganin haka ya sanya Surayyerh bin bayanta ta ce "Wai what's going on Zahrah looks so worried what's up?" Zahrah ta ce "na shiga uku Surayyerh kinji abin da Sheikh ya ce" Surayyerh ta amshi wayar ta shiga karanta saƙon Sheikh a fili. _I agree to marry you, on one condition if you become a good woman like Hurul-in, idan na sameki a yadda ba zan taɓa a daren zan tsinke igiyar aure ukun nan..._ "Tab ga ƙoshi ga kwanan yunwa, yaya za a yi yanzu?" Zahrah ta ce "Ba wannan ba Zahrah cikin dake jikina shi ne matsalar, kuma zan iya zuwa ayi mini ɗinki yadda Sheikh ba zai gane cewa na san namiji ba" Surayyerh ta ce "Ina da shawara kawo kunne kiji" ta raɗawa Zahrah a kunne Zahrah ta ce "Wow wlh na ɗauka jakar ƙwaƙwalwa gareki yanzu ta ina zamu fara nema, Kinga dai yanzu kira ya saman urgent" Surayyerh ta ce "Deen?" "Mtwss kina da matsala tsakani na da Deen sai after married, muje" shiryawa sukai Surayyerh na driving mota Zahrah na baya har zasu shige cikin Abti America idanun Zahrah ya sauka akan ƙwaryar Kindirmo nan da na kwaɗayi irin na masu yaron ciki ya tasu mata cikin sauri ta ce "Stop the car Surayyerh" Surayyerh taƙi tsayawa da sauri Zahrah taja burkin mota "Innalillahi zaki kashemu Zahrah are you at of your sense?" Zahrah ta fita da sauri tana zuwa ta ɗauki ƙwaryar kindirmon ya shiga sha ba tare da tunanin daga ina ya fito ba, sai ta gama sha kwaɗayi ya faɗa ta kalli ƴar fillon wacce kanta ke ƙasa tana rusa kuka da iya ƙarfinta bata san ma Zahrah ta zo wajan ba ta ce "ke nawa ne kuɗin ki?" Ta faɗa tana yatsuna fuska, Halisa Danejo Rome ta kasa magana sai kuka a hankali Zahrah ta ce "ke dallah riƙe kuɗin ki mtwss" Surayyerh ta ce "Zahrah yarinyar nan kamar zatai daidai da tsarinmu" Zahrah ta kalli Danejo da kyau sai kuma ta saki murmushi ta ce "Ƴar ƙanwata lafiya kike kuka?" Danejo ta ɗago kanta idanunta ya yi jajir cikin kuka ta ce "Dadata ce zata mutu bata da lafiya" Zahrah ta ce "Ayyah ki daina kuka to" ta ce "To ai mutuwa zatai bani da kowa kuma" Zahrah da Surayyerh sukai murmushi Zahrah ta ce "Kina son ta samu lafiya kuci gaba da rayuwa da ita?" Danejo ta ɗaga kai da sauri ta ce "Ina so Aradu ina so" Zahrah ta ce "Good, zan kaita asibitin kuɗi" da sauri Danejo ta riƙe hannun Zahrah ta ce "Da gaske kike? Hamma Yabi yace zai kaita asibitin burni shi ne aka kashe sa" Zahrah tai alamar tausaya wa ta ce "Wayyo ni zan kaita zan kashe kuɗi sosai har ta samu lafiya amma da sharaɗi guda ɗaya idan kin amince" Danejo tai shiru alamar tunani da sauri ta ce "Wanne sharaɗi" Zahrah ta ce "Kinga tunda zan taimake ki nima ki taimake ni taimako na rana ɗaya nake buƙata shi ne madadin alheri da nayi miki" Danejo tai murmushi wanda ya sanya zuciyar Zahrah bugawa sbd kyan yarinyar ta ce "Na yarda zan miki taimakon Adda" Zahrah tai murmushi tana ɓoye jin daɗin ta, ta juya suka kalli juna da Surayyerh ta ce "Tom shikenan idan kina so na kai Dadarki asibiti ta samu lafiya nima ina so ki kwanta da mijina na rana ɗaya ranar da akai kaini gidansa zai amshi budurcinki a matsayin nawa.... *Last free pages* _A nan na kawo ƙarshen free pages mu haɗu a paid group ga wanda suka biya, idan mutanan da suka biya basu kai 200 ba zan haƙura da sakinsa a whasap na buga shi zuwa kasuwa, ko kuma na sake shi iya AREWABOOKS.... Bugagge na takarda dubu ɗaya ne 1k... A whasap kuma mutum zai biya 500 (ɗari biyar har a gama labarin)... Ka tura kuɗin ka ta nan 6850917335 Na'ima Shu'aibu sulaiman fidelity bank. A tura shaidar biya ta wannan number 08119237616 ƴan nijar sun yi mini magana._ Sai mun haɗu a paid grp masoya💋❤‍🔥❤‍🔥 this time al'amarin daban yake salo wanda ban taɓa zuwa da irinsa ba. "Mijinki zai amshi budurcina a matsayin naki?" Danejo ta sake maimaita tambayar cikin rashin fahimta kamar taso ta gane budurcin, tun da a lokutan baya Dada nayi mata faɗa akan ta kame kanta sbd ita ɗin maca ce mai ƙima da kuma daraja. "Kinga ba wani abu ne na tashin hankali ba, ki nutsu ok" ta juya kan Surayyerh tana ɓata fuska ta ce "Please Surry explain to her" Surayyerh ta kalli Danejo tana sakin murmushi kafin ta ce "Yama sunanki?" Danejo ta kalli Surry kamar ba zatai magana ba sai kuma ta ɗauke idanunta zuciyarta na bugawa ta ce. "Halisa Danejo Rome" Surry ta jinjina kai ta ce "Ok Good, yawwa ƙanwata Kinga duk mun girmeki zaki iya ce mana Anty mai ma kuke kiran babbar yaya a yaranku?" Danejo ta ce "Adda" ta taɓe baki ta ce "Whatever kice mana kawai Anty, Kinga ƙawata aure za tayi cikin satin nan, kuma bata da lafiya sosai shi ya sanya ta nemi taimako akan ki zauna tare da mijinta na rana ɗaya kawai, rana ɗayanma bai shige awa guda ko 30mnts ba,idan kin amince yanzu sai ta ɗauki Dadarki zuwa babba asibiti ai mata magani" Danejo tai shiru saboda har ranta bata gama fahimtar zan can nasu ba, ita tsoro ma suke bata Wallahi musamman data gansu manya ko wacce da gashin indo anci uban kitson ƙari. Amma da abin da suke buƙata da rayuwar Dadarta wanne yafi? Wata zuciyar ta tambayi Danejo, Dada ita ce komai na rayuwarta, farin cikinta, jin daɗinta. Da ita zata zauna har abada bada su ba. Cikin sauri ta kalli Surry ta ce. "Kuma yana amsar budurcin nawa zan dawo Rugarmu wajan Dadata?" Baƙin ciki ya cika zuciyar Zahrah, jin yadda Danejo ke ta nanata kalmar “budurcin” zuciyarta kamar zatai bindiga sbd tsabar kishin dake damun zuciyar ta. Surayyerh ta kalli Zahrah,Zahrah ta ɗaga mata kai alamar ta amsa da "Eh" kawai. "E, da kin kammala aikin naki zamu dawo dake ai ba can zaki zauna ba" Danejo tai murmushi ta ce "Aikin ba wahala Aradu na yarda nidai" ɓoyayyiyar Ajjiyar zuciya Zahrah ta sauke na jin daɗin kafin ta ce. "Shiga mota muje Rugar taku" Danejo tai shiru kada taje kuma masu yanke kai ne, haka kurum su yanke kan a banza. "Shigo muje mana?" Surry ta faɗa domin tuni Zahrah ta shiga motar tare da yi mata key. Ƙwaryar nonon ta ɗauka tare da shiga inda Surry ta nuna mata, ta shiga a tsorace bakinta sai rawa yake na tsoro, a haka Zahrah taja motar tare dabin direction ɗin da map ke nuna mata har suka isa Rugar Rome. Da gudu Danejo ta fito tana ƙanƙame ƙwaryar kindirmonta. Surry ce ta fara kallon rugar Zahrah ta dinga taɓe baki kamar wacce taga makusa domin Rugar Rome abin sha'awa ce ba ƙazanta cikinta. "Bari na faɗawa Sarkin ruga anyi baƙi ko?" Da sauri Zahrah ta riƙo Danejo ta ce "A'a kada ki faɗawa kowa, sbd zasu hana akai Dada asibiti muje kawai" cike da gamsuwa ta yarda ta nufi bukkarsu, suka bi bayanta. A kwance suka samu Dada idanunta nayin sama kumfa na fita daga cikin bakinta kamar ko yaushe, Shatu na gefe tana jijjiga Dada sai ihu take domin jikin Dadar ya yi tsamari fiye da ko wanne lokaci. Surry ta zaro idanu sosai bata ɗauka ciwon yai girma har haka ba, da sauri ta ce "Kamata muje Zahrah subuhanallah haka jikin nata ya yi" Danejo na kuka ta ce "Na shiga uku na lalashe Dadata kada ki mutu ki barni kinji" Zahrah ji take kamar ta shaƙe Danejo sbd baƙin ciki haɗa jiki da zatai da mijinta nan da bada jimawa ba, hakan ya sanya taji harta fara tsanar yarinyar. A mota suka saka Dada shatu da Danejo suna baya kusa da mahaifiyar tasu, a wannan lokacin Surry ke driving motar, Zahrah na gefe lokaci zuwa lokaci tana kallon Danejo ta madubi anya batai kuskure ba?. A Specialist Yola motarsu tai parking nurse's suka fito da gado kai tsaye tare da saka Dada akai, kasancewar Babban asibiti ne kuma an san Zahrah Farouk cikin ƙaramin lokaci aka buɗewa Dada file aka fara yi mata medical check up. Dr ya fito da sauri Surry ta miƙe tsaye ta ce "Dr ake ciki?" Idanunshi akan Zahrah ya ce "ki saman office" yana faɗin hakan ya shige Office ɗinsa. Surry ta kalli Zahrah ta ce "Muje Madam" ta tsuna fuska ta ce "No I'll wait here, kije yadda ake ciki let me know" ta girgiza kai tare da bin likitan zuwa office nasa. Yana zaune akan kujera ta same shi bayan sun gaida Surry ta ce. "Dr ya ake ciki ne?" Dr ya sauke numfashi yana zare Glasses ɗin idanunshi ya ce "Allahamdulillah kun kawota lokacin da ya dace, matar na jin jiki wani ƙari ne ya fito mata a ciki shi ne ke wahalar da ita" Surry ta ce "Thank God, yanzu mene mafita zuwa yaushe zata samu lafiya?" Ya gyara zama da kyau yana duba file ya ce "Zaku biya kuɗin da za ayi mata aiki, a daren yau misalin 10 za a yi aikin, muna da ƙwararrun likitoci cikin kwana ɗaya biyu komai zai daidai a ɗora ta bisa magani" cikin jin daɗi Surry ta ce "Dr hakan ya yi, nawa ne kuɗin?" Ya ce "Dubu ɗari biyu da hamsin ne har magani" ta miƙe tsaye tana ɗaukan waya da hand bag ta ce. "Ok bari naje na biya kuɗin" tana faɗin hakan ta fito ta samu Zahrah zaune tana waya, Danejo da Shatu sun rakaɓe waje guda sai zare idanu suke. Danejo ta miƙe da sauri ta nufi wajan Surry domin tafi fuskar rahama akan Zahrah muryarta na rawa ta ce "Ina Dadata? Tun ɗazo ban ganta ba ina kukai mini ita?" Zahrah ta ja tsaki Surry kuma tai murmushi ta ce. "Haba ƙanwata kin san babu inda zamu kai Dada sai wajan likita,ya ce gobe zata fara magana ki kwantar da hankalin ki" fararen haƙoranta masu kyau suka bayyana dalilin murmushi da tayi ta kalli Shatu ta ce "Shatuna Dada zata lafiya, aradu wannan ƴa ƴan albarka ne dole nayi musu aiki suma" Surry ta girgiza kai ta ce "ku zauna nan yanzu zamu dawo, kada kuje ko'ina har abinci zamu kawo muku" a tare suka ce "To Adda" Surry da Zahrah suka nufi wajan biyan kuɗi, tare da cike komai da komai. Driving take jifa jifa tana murmushi Zahrah ta gaji ta ce "Wai murmushin me kike haka Surayyerh ko tausaya mini bakya yi wata zata kwanta da mijina?" Surayyerh ta girgiza kai tana bin waƙar dezell can ta ce. "Yarinyar ce abin tausayi bake ba Zahrah" Zahrah ta ce "kamarya? Mijina zai san wata bani ba" Driving amma bai hanata fashewa da dariya ba sosai tana buga kan motar "What funny Zahrah? Serious daneja ko Danejo take ita ce abar tausayi, look how young she is bana tunanin zata iya ɗaukan al'amarin namiji,and she didn't understand what we meant". "And so what kuma? Idan har za a amshi budurcin nata? Look Surayyerh ni bana tausayin ta yadda na kai tsuhuwar ta asibiti dole ta cika mini nawa aikin" Surayyerh ta juya kaɗan ta kalli Zahrah ta ce "I don't feel sorry for her either,kawai Sheikh ba zai iya haɗa jiki da ita a yadda take ba, dole a sauya ta" Zahrah ta ce "like how wanne sauyi?" Kai tsaye Surry ta ce. "Ta daina warin da take, ta zama mai tsafta ƙamshin ya zauna mata ki sanya ta nutsu sosai nutsuwar da shi kansa zai fahimta cewa eh da gaske ke ɗin ce" da ƙarfi Zahrah ta ce "Tab hauka kenan, Please stop it bana son jin haka.." Surayyerh taja tsaki a ranta ta ce "mahaukaciya" Maimoon ce ke zaune tana tura baki Mother ta ce "Oh kina so ace ni na hanaku yin kwalliya a bikin yayan naku ko Maimoon?" Maimoon ta ce "Haba Mother bakya farin ciki da auren akan me mu kuma za mu yi har muje muyi wani henna da saloon?" Zeefa ta ce "Wallahi Moon, ni fa tun kafin naga amaryar naji na tsaneta kamar Father ya fifita ta akanmu" Auta Fattoumah fuska a haɗe hannunta riƙe da handle ɗin game ta ce "I hate her too, because of her the happiness in our house is gone" Mother ta saki baki da hanci tana bin yaran nata da kallo kafin ta ce "Akwai wanda ya halicci Zahrah a cikin ku? Balle kuyi ƙorafin sauyin halittar ta? Kul na kuma jin magana irin wannan, musamman ke Maimoon, Mamana ke kuma waye ce miki sbd ita farin cikinmu ya tafi?" Fattoumah ta yarda handle ta ce "Mother nasan komai fa, gashi har father yana cewa ana nemawa Yaa Lee mahaifi" Mother ta runtse idanu sosai wato kaf yaranta idan aka ɗauke Sheikh babu mai kaifin tunani da basira irin Fattoumah,ga riƙo tana lura da komai. A sanyaye ta ce "Maza ga mai henna can tana yiwa Dr A'isha kuje ayi muku" tana faɗin hakan tai waje. A main parlour ta samu Dr A'isha da Yaya Halima sai friends ɗinta irin su Barrister Zainab. Mother ta zauna a kujera idanunta akan t.v ba tare data cewa kowa komai ba. "Sheikh ya yi lunch kowa?" Cewar Dr A'isha. Mother ta ɗan kalleta kaɗan ta ce "Anya? Kamar dai azumi yake" Yaya Halima ta ce "ba kama bane, yau Alhamis ai" "Oh haka ne fa, na manta azumin Alhamis da Litinin Allah ya bamu lada" Barrister Zainab tai murmushi ta ce "Wato ke Dr A'isha ba zaki iya ba? Shi yasa ɗan naki ya rainaki" tai dry sosai ta ce "Azumi kam sai manyan malamai irin su Sheikh Aliyu haydar Aliyu". Sheikh na zaune shigowar shi kenan daga masjid yin sallar asr, a hankali ya sauke numfashi. A nutse ya ajjiye azkar ɗin hannun shi tare da miƙewa yabar cikin Library ɗin na shi kai tsaye ya nufi haɗaɗɗan bedroom ɗin sa wanda yaji kayan more rayuwa ko'ina na bedroom ɗin ƙamshi yake, ya zame jallabiyar jikinsa wanda ƙa'ida idan zai shiga wanka sai ya cire komai ya rage daga shi sai boxer yake shiga. Tsarin halittar jikinsa ta bayyana yana ɗan kare jikinsa da hannu a haka ya shige bathroom tare da sakarwa kansa shower ta warm water. Fitowa ya yi sanye da towel jikinsa ka fitar da ƙamshin MUD BEGIN Natural shower Gel. Idanunsa na lumshewa kamar mai jin barci a haka ya shafa versiline mai kanshi tare da fesa body spray. Wata duguwar Jallabiya mai nauyi da tsada ya ɗauka ya sanya, jallabiyar daban take domin har wani zane ne jikinta kamar alkyabba. Yana gama sawa ya naɗa rawani kamar kullum tare da ɗora hirami saman ƙafaɗar shi. tsaf ya kammala shigar shi irinta manyan malamai wanda suka san me suke ko a maluntar. Jikinsa na fidda ƙamshin Roja wanda ya bayyanar da zuwan shi cikin Main parlour ɗin gidan. Kansa a ƙasa ba tare daya kalli kowa ba, kamar yadda zuciyar shi ta raya masa hakan ce ta kasance Dr A'isha na ganinsa ta fara buɗa tare da faɗin. "Ayyiri yiri the lastest ango of the year" ya ƙara kame fuskar shi babu walwala hannun shi akan gemunsa yana ɗan ja haka yai waje ba tare da kalle ta ba, balle yace mata wani abun duk da yaso ya tsaya yayi mata bayanin aya da hadisai Manzon Allah akan muhimmancin muryar mace. Da kuma rashin amfanin wannan ihun da take. Chevrolet silverado car wacce ta kasance blue black ya nufa, harabar gidan shiru hakan yasa ya rufe idanu yanayin na masa daɗi na shaƙar fresh air ga ƙamshin na'ana'a dake ɗan nesa da shi, Bismillah ya yi tare da shiga motar sai da ya yi addu'a kafin a hankali ya yi wa motar key gatekeeper ya buɗe masa, cikin nutsuwa da haiba yake driving motar har ya harbata kan titi. A harabar gidan Abba Hakimi ya yi parking motar, ganin motoci da yawa ya sanya shi taɓe fuska baya son hayaniya sam. Ya fito a kame yana jan gemunsa kaɗan ta baya yabi a ƙoƙarin shi na son shiga part ɗin nasa ba tare da kowa ya gansa ba. Yaje corner kenan yaji ance. "Yaa Sheikh" Khalil Ahmad Sarki ya faɗa yana murmushi hannun shi riƙe da gorar ruwa. "Yanzu nake shirin zuwa can gida muji yadda al'amarin bikin zai kama, nasan dai bikin Yaa Sheikh dole ba events ba D.j" Sheikh ya ware idanu da kyau yana bin Khalil da kallo. Khalil ya ce "na ƙosa naga matar Yaa Sheikh, nasan dole ta zama Malama kamar haka, Wow! Ga Yaa Sheikh ga Malama what a beautiful couples wlh dole love yaci ƙaniyar shi" Yaa Sheikh ya ɗauke Idanunshi tare da kama hannun Khalil Ahmad sarki suka nufi hanyar ƙofa Khalil ya ce "Ya dai kamata ka fito tun ɗazo Mai martaba ya shigo" har lokacin Yaa Sheikh bai ce komai ba, yana zuwa bakin ƙofa ya tura Khalil waje tare da rufo ƙofar ya murɗa key. Khalil ya dinga dry daman ya lura zan can damun Yaa Sheikh yake yana mmkin yadda baya ƙaunar ai masa maganar mace?. Ya juya inda yabar su Abba Hakimi yana zuwa ya ce "Abba Hakimi ai ga ɗan naka can ya gudu part ɗin shi" Abba Hakimi ya ce "Za mu yi faɗa dakai yanzu Ibrahimul-khalil" Khalil ya yi murmushi ya ce "Nikam ina ruwar gida Momi ne?" Abba Hakimi ya ce "Tana can tana kayan buɗe baki na Aliyu, ƙosai da kunun gyaɗa"... "Ah! Lallai aikin lada take kenan" Mai martaba Ahmad Sarki ya kalli Ishaq-Hakim cikin kamala ya ce "kira Sheikh" da mutumtaka ya ce "To ranka ya daɗe Allah yaja kwana" kafin Ishaq-Hakim ya miƙe El-bashir wanda tun ɗazo yake hakimce saman kujera ya miƙe cikin nutsuwa hannu cikin aljihun suit ya nufi hanyar fita Abba Hakimi ya bisa da kallo yana nazartar yanayin yaron wanda baya son haɗa inuwa da Yaa Sheikh gaba ɗaya. "El-bashir kada kai nisa" cewar Mai martaba. He just nods his head and quickly leave the parlour. Bayan sallar magrib Yaa Sheikh na zaune a ƙawataccen parlournsa gabansa ɗauke da kayan buɗe baki, inibi yaci sai ƙosan da yake mai zafi ya yi laushi sosai sbd ƙwai da aka zuba cikin haɗin, hakan yasa ya ɗan saki jiki ci ƙosan da kunun gyaɗar. Yana jin gine da jikin kujera yana kallon Aljazzera yaji Sallamar Abba Hakimi shi ne kawai ke shigowa kai tsaye cikin part ɗin na shi, ya gyara zama sosai yana mai amsa sallamar ta Abba Hakimi. Bayan Abban ya zauna ya dubi Yaa Sheikh ya ce. "Aliyu haydar" Yaa Sheikh ya ɗaga kansa gaba ɗaya tare da kallon Abba Hakimi da yake faɗin "Jibi ɗaurin auren ka, ya ya zakai da uwar gidan naka kafin amaryar tazo?" "Uuuu...uu... Uwar gggg gida? Am am amarya?" Ya faɗa yana kallon Abba alamar rashin fahimta. Abba Hakimi ya lura da gaske Yaa Sheikh bai gane ba ya ce "Yarinyar da aka ɗaura maka aure da ita a can Yola? Ka tuna?" Tab yakan manta abubuwa amma wannan abun ya zama abu na farko da ya yi saurin mantawa da shi. "Ina jinka,ina so muje can rugar tasu ne" magana zarar bunu cikin rashin sani Yaa Sheikh ya ce "Uhm bani da labarin hakan Abba, idan akwai auren ma zan kunce shi yanzu... *Don Allah kada a fitar😒 littafin IDAN BA KE na kuɗi it's 500 via this account 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman fidelity bank. Via evidence 08119237616. SARAUTAR MARUBUTA Surry da mamakin kaifin bakin Halisa Danejo Rome ya gama cika mata zuciya,domin yarinyar ƙwarai ta shayar da ita mamaki, alamu sun nuna da gaske take dukkan maganganun da take. Surry ta ƙara gyara zama ta ce. "Ok sai ki shirya biyanmu dukkan kuɗin da muka kashe, kama daga kuɗin aiki, magani, kuɗin gado, dana abincin da kuke ci?" Bakinta har kumfa yake wajan faɗin. "Aradu babu inda zani ina tare da Dadata ku bakwa abu saboda Allah ne yanzu ba lada zaki samu ba?" Surry da ranta ya fara ɓaci da abin da Halisa keyi wanda yake gab da shirin ruguza mata nata tsarin na ganin ta kai Zahrah ƙasa ta ce "To ba mu yi niyyar samun ladan ba, idan ba zaki iya biyan kuɗin ba, dole kije ko na kira ƴan sanda" Halisa na ƙoƙarin magana Dada ta kalleta tare da watsa mata harara cikin sanyin murya ta ce. "Ki manta da ita, tunda tai al'ƙawari dole taje duk da nima bana so, amma babu yadda za a yi ƙila hakan shi ne alkairi" murmushi ya bayyana saman fuskar Surry ta ce "Ai alkairi ne ma, zaki mamakin Halisa aikatau ɗin data samu mai kyau kuɗi sosai za a bata" Dada ta jinjina kai alamar gamsuwa. Halisa banda tura baki gaba babu abin da take,duk abin ta bata iya musu ki jayayya da maganar Dada maganar ta kamar yankan wuƙa take. Surry ta miƙe tana duban Halisa ta ce "Ki tabbatar kin fara aiki da kayan nan kamar yadda na nuna miki?" "To sannu Dada" Surry ta hangame baki cikin ranta al'amarin daɗi yake mata, Zahrah zata zauna da daidai ita wacce bata da tsoro sam cikin lamarin ta. "Ni kike haɗawa da Dadar taki?" Halisa ta ce "Eh Aradun Allah, naga ita kawai ta isa ta bani umarni na bi" Surry ta kasa cewa komai tayi waje abinta bayan ta ajjiye musu kuɗin mota na komawa can Rugar Rome. Dada ta sauke numfashi tana kallon Danejo ta ce "Bakin ki babu linzami Danejo?" Ta tura baki ta ce "Ni ban san wani linzami ba, kin fi so aita cutarmu kina kallo, wai Dada waye Baffa ne?" Dada ta ɗaga kai da sauri kanta na sarawa zuciyarta na harbawa da ƙarfi najin tambayar na Danejo kamar daga sama. Halisa ta ƙara cewa "Dada waye Baffa mai yasa komai nasa sai a ƙwace mana shi?" Dada tai shiru har lokacin kallon Danejo take, irin kallon meke damunki ɗin nan? Me ya sa kuma kike tambayata wannan babbar maganar mai shirin tarwatsa zuciyata. "Do Allah Dada yau ɗaya ki faɗa mini waye Baffa a cikin Rugar Rome? Kuma....," Kyakkyawan marin da Dada ta saukewa Danejo shi ne ya taimaka wajan haɗiye sauran tarin maganganun da su ke maƙale a saman harshenta, cikin faɗa Dada ta ce. "Hande en boni Danejo, banshe kada ki sake maganar Baffa? nashe ki barshu da Allah duk wanda suka ƙwace naggenku" Sai kuma ta fashe da kuka ganin yadda fuskar Danejo tai jajir saboda marin da tayi mata sai huci yarinya take alamar zuciyarta na kusa. Dr ya turo ƙofar room ɗin hannunsa riƙe da file tare da kallon Danejo dake kuka ya ce "A'a yau mai akaiwa ƴar fillo ne?" Bakinta na rawa ta ce "Ba wanda suka kawo Dadata bace wai mijinta zai..." Kafin ta ƙarasa Dr ya ce "Ƴar fillo bari na fara duba Dadar taki yau dai kuka ya ƙare Dada ta samu lafiya" nan da nan ta washe bakinta tare da goge idon kukan kamar ba ita aka daka ba. Ta tsaya gefen Dada, Dr ya fara dubata cikin nutsuwa yana gamawa ya ce. "Allahamdulillah, jiki ya samu, yanzu zan baku takardar sallama, tare da magani sai ku tafi gida" Shatu ta fara tsalle zasu gida. Cikin ƙaramin lokaci aka gama musu komai Sai da Dada tai Faɗa kafin Danejo ta ɗauki kayan da Surry ta bata suka nufi gida. Zahrah na zaune ana gyara mata tulin gashin kanta sai kiran number Surry take taƙi shiga tai tsaki, tana ƙara danna wani kiran Surry ya shigo ta sauri ta ce "Heyy what's going on, see me here stop calling" ta faɗi Maganar tana shigowa cikin bedroom. Zahrah ta miƙe ta ce "Wai ina kika je? I have been trying to call your number amma yaƙi sai yanzu yake shiga, from where?" Surry ta zauna ta ce "Kin san kayan dinner ɗina bai zama ready ba, naje wajan tailor meye kike ta ihu ne?" Zahrah ta juya ta kalli Make up artist dake tsaye ta ce "Excuse us please" ta ce "Sure Maaah" Zahrah ta kalli Surry da kyau ta ce "Surayyerh gabana faɗuwa yake, ina jin tsoron a gane ina da ciki Wallahi, ina mutuwarsa son Yaa Sheikh kamar rayuwata, kullum cikin fargabar ranar da zata zo wacce zai haɗa gangar jikinsa dana ƴar fillo, I'm scared Surry" wani shu'umin murmushi Surry tayi daman tasan tatsuniyar gizo ba zata shige ta ƙoƙi ba. "ko fasa tafiya da ƴar fillon zaki ne?" Zahrah ta waro idanu ta ce "Idan ban tafi da ita ba ya ya zan yi? Kina ganin ya ce idan bai saman matsayin mace ba zai sakeni, wlh ina son shi ba zan bari nayi wani abu wanda bai dace ba, dole zan tafi da ita, kuma dole ne ya kwanta da ita a matsayin ni, sai dai i have a plan ba zan bar ƴar fillo haka ba, dole nayi mata baƙin fenti" gaban Surry ya bada sauti sai ta share ta ce "Ya kamata kam, ƙila plan ɗinmu ɗaya me zaki yi mata ke?" Tai murmushi ta ce "sirri ne, muje lokacin na tafiya Finally Aliyuna zai zo na kansa, har imagine nayi hugging nasa nake" Surry ta ce "Uhm" kawai tana barin bedroom ɗin. Misalin 12 hall event ɗin ya cika da ƴan mata da kuma samari D.j ke tashi kamar zai fasa hall ɗin, amarya Zahrah ta sha ado cikin wata pink ɗin gwon gaba ɗaya half ɗin ƙirjinta yana waje. Yaƙe kawai sbd rashin ƙarasuwar ango Yaa Sheikh da bai ba gashi friends ɗinta sai tambaya suke kowa ya damu da yaga wanne mai tausayin ne ya auri Zahrah?. Sautin Algaita da suka ji a can wajan hall ɗin ya sanya Surry ta shi da sauri ta nufi wajan, manyan motoci ne guda wajan huɗu sabbi dal sai ƙyalli suke. Fuskar Surry ta sauya launin lokaci guda ta gane Yaa Sheikh ne da friends ɗinsa. Ta kasa motsawa wani abu na cakar zuciyarta, tana tsaye taga wasu matasan samari ko wanne da fararen kaya har ƙasa sun rufe musu ƙasa ko takalmin su ba a iya gani, motar ƙarshe wacce ta kasance da Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu wani saurayi ya buɗe ta, cikin nutsuwa ya fito shima yana sanye da fararen kaya mai Alkyabba rigar har ƙasa tana jan ƙasa. Ya ɗago kai a nutse suka haɗa idanu da Surry tayi saurin ɗauke idanunta bata taɓa ganin ƙwayar idanu mai tarwatsa zuciya irin ta Yaa Sheikh ba. Cikin sauri ya juya zuwa hall ɗin labari tuni ya isa kunnen Zahrah farin ciki ya lullube zuciyarta. Mc ya fara sanar da zuwan ango Zahrah ta tasu tunda Yaa Sheikh ya ganta sau ɗaya bai sake ganinta ba, domin ba ita yake nema ba a yanzu. A haka suka jera har yanzu wajan zaman da aka tanadar musu, lokacin zuwa lokaci idan Zahrah ta haɗa idanu da Yaa Sheikh sai ya sakar mata murmushi abin mamaki haƙura biyu kacal take gani a cikin bakin nasa, ta dai daure. Lokacin da akace su tasu zuwa filin hall ɗin idanunta ya sauka akan ƙafar shi da rigar ta zame, wani irin zaro ido tayi gabanta ya faɗi jikinta ya hau rawa sbd ganin kofato da tayi maimakon ƙafa, ta ɗago kai da sauri suna sake haɗa idanu ya buɗe mata bakinsa mai ɗauke da haƙura biyu. Wani ihu ta fasa a wajan tare da sulalewa babu numfashi. Surry da sauran friends sukai kan Zahrah ba tare da sun lura ba ango da abokan shi suka ɓace daga wajan. Wanda ake tunanin shi ne Yaa Sheikh suna fita daga hall ɗin ya yi wani ihu tare da girgiza ya rikiɗe zuwa Aljani Prince Bilal. Sauran wanda akace abokan shi ne suma suka rikiɗe zuwa Aljanu. Cikin wata murya mara daɗi Prince ya kalli Sandu ya ce "Na samu nasarar kashe babana, tsayin kwanaki ina neman matata Danejo amma babu ita, babana ya cuce ni ya sanya na manta kamarta yanzu ko na ganta ba zan san ita bace idan ba zoben dana bata na gani ba" Sandu ya ce "Ai zoben ya fara dacewa mu nema, tunda kace yana wajanta ko?" Prince bakinsa na fidda hayaƙi ya ce "Yana wajanta" hura iska daga cikin bakinsa sai ga wani photo ya bayyana na tambarin masarauta ya nuna musu tambarin ya ce "Duk inda kuka ga zobe mai tambarin nan a hannu wani to shi ne zoben hannun matata Danejo,da zoben da ita a kawo mini su, maza kuje" ɓat suka ɓace daga wajan, Prince ya juya ya kalli hall ɗin da ake partyn kamar zai koma ciki sai kuma ya ɓace ɓat shi ma. Ƙarfe 2 na daren Asabar ɗin jirginsu Yaa Sheikh ya sauka a Yola International airport, kai tsaye motoci suka ɗakko su zuwa cikin wani haɗaɗɗan hotel, tawagar Abba Hakimi daban, ta Father daban, sai su Saif-wazir, Umar-khan, Ishaq-Hakim, Khalil Ahmad Sarki, El-bashir. Dashi kansa Mai martaba. Har zuwa lokacin Yaa Sheikh ya kasa yarda wai ɗaurin auren shi aka zo, da yarinyar da ko sanin kamanninta bai ba, kuma bai damu daya sani ɗin ba. Washegari Lahadi aka ɗaura auren Zahrah Farouk da Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu akan sadaki dubu ɗari yadda Abba Hakimi ya bada. Ran Father ya ɓaci shi da ya so a bada dubu ɗari biyar ko miliyan guda. Abba Hakimi na cikin mutane Saif-wazir ya zo kusa da shi murya ƙasa ya ce "Abba ga motar can ya kamata muje" Abba Hakimi ya miƙe tsaye hannunsa riƙe da sanda yabi bayan Saif-wazir zuwa cikin mota. Kai tsaye Rugar Bello Saif-wazir ya nufa yana faɗin "Ina Yaa Lee zai kai wannan matar? Wallahi Abba kallon sani nake mata kuma na manta inda na taɓa ganinta" Abba Hakimi yai murmushi yanayin garin Yola na birge shi ya ce "Saifuddeen ina rabaka da shiga sabgar da bana ka ba" Saif ya ce "da gaske Abba, tabbas na san fuskarta na manta ne kawai" ya faɗi haka yana parking daidai inda suka tsaya last time shi da Yaa Sheikh. Abba Hakimi ya fito suka jera da Saif zuwa Rugar Bello, kamar yadda yasan Rugar haka ɗin ya sameta suka samu Arɗo dasu Giɗaɗo. Bayan duk sun zauna Saif ya ce "Nasan baka gane ni ba ko?" Arɗo yai jim alamar nazari can ya ce "Gaskiya bai shaidaka ba" Saif ya gyara zama ya ce "mun zo kwanaki ni da ɗan uwana,kuka ce wai ya yiwa wata ƴar fillo fyaɗe har kuka ɗaura masa aure da ita?" Arɗo ya ce "tuh! tuh! Masha Allah na gane shi yana ina? Ina kuma matar tashi nake?" Zuciyar Saif ta buga, ya kalli Abba Hakimi kafin ya kalli Arɗo ya ce. "Wannan shi ne babana kuma baban Sheikh ɗin, daman yarinyar baya dawo gida bane? Ai mun kaita asitibi ta gudu" Arɗo ya girgiza kai ya ce "Ayyah shai dake ba a nan Rugar take ba, muma ganinta kawai mukai amma ba ƴar Rugar Bello bace" Abba Hakimi da Saif suka kalli juna kafin Abba Hakimi ya ce "Ikon Allah, yanzu bayan wannan rugar akwai wata ne" Arɗo ya kalli Labo, Labo ya girgiza masa kai, tunaninsu wani taimako za a bawa Fulani a fili Arɗo ya ce "Ai kaf Yola nan ce kawai Rugar Fulani, ba lallai idan ƴar garin bace" Abba Hakimi ya dinga kallon Arɗo yana mamakin wannan bankaura, daga kallon sarkin fawa sai miya tayi zaƙi? Kawai daga ganin Sheikh sai sukai masa bahaguwar fassara a tirɓayar tunaninsu mara kan gado. Jiki a saɓule Abba Hakimi da Saif-wazir suka miƙe zuciyoyinsu babu daɗi. Bayan sun shiga mota Abba Hakimi ya sauke numfashi ya ce "Abin mamaki,ban taɓa jin wannan kwaɗon ba sai yau" Saif yai murmushi ya ce "Fulanin kenan Abba, yanzu ina zamu nemuwa Yaa Sheikh uwar gidan shi?" Abba Hakimi yana yin murmushi saboda wani tunani daya faɗo masa ya ce "Uwar gidan da baya so? Bari mu buga wasa waye zai nasara? Mai gidan? Ko Amaryar? Ko kuma Uwar gidan da ba a san inda take ba?" Saif ya ƙara sakin murmushi ya ce "Wannan shi ake kira da bikin zuwa ya samu babu zanin ɗaurawa, zan so naga yadda wasan ya zai fara ni ina team ƴar fillo" A haka suka koma masaukinsu ƙarfe 2 daidai jirginsu zai ɗaga zuwa kano. Amarya Zahrah na bedroom ɗinta Feedy ta shigo ta ce "Wow Zahrah kinga Yaa Sheikh wlh sai da zuciyata ta buga, na jima banga mutum mai kwarjinin shi ba" Zahrah ta miƙe ta ce "Da gaske Yaa Sheikh ya shigo?" Surry dake shigowa ta ce "Ya shige wai ai, Mimi ta ce ki sakko yanzu Kinga your husband and groom's friends" jiki na rawa Zahrah ta miƙe ta saka babban mayafi kamar ta Allah tana mai rufe jikinta sosai sbd cikin jikinta daya fara tasawa. Yana zaune saman wata haɗaɗɗiyar kujera, yaci dakakkiyar shadda gezner fara tas sai ɗaukan idanu take, ya ɗora Ash ɗin Alkyabba mai adon ruwan zuma, yaci rawani kamar kullum fuskarsa mai ɗauke da saje da tarin ƙasumma wacce tai tsayi sosai ta sauka har ƙasan haɓarsa sai ɗaukan ido take. Khalil cikin sarki, Umar-khan, Ishaq-Hakim. Sai Oga El-bashir dake can gefe sbd faɗan Your highness gaba ɗaya sun saka kaya iri ɗaya,familyn kowa na ji da kansa wajan kyau. Zahrah ana karairaya sbd ganin miji ɗaya tamkar da dubu acikin ƙawaye ta kere kowa aka ƙarasa kujerar da Yaa Sheikh yake, cikin ƙasa da murya ta ce. "Your wlcm My Excellency" idan kujerar da yake kai ta motsa to Yaa Sheikh ya motsa gaba ɗaya hankalinsa baya kanta, barcin dake addabar shi yake son yaje ya rage wanda ya saba yinsa kullum. Kamar wanda aka tsikara haka ya miƙe tare da barin parlourn, Surry tai Shu'umin murmushi, Zahrah kuma tabi bayan Yaa Sheikh kamar wata jela. Halisa ce ke kuka kamar ranta zai fita itama Dada idanunta ya cika da hawaye amma bata son tai kuka sbd kada ta karya Jaririyar zuciyar da ƴarta Halisa. "Dada dan Allah kada ki barsu su tafi dani, bana son barinki" Surry dake riƙe da kayan Halisa a wata babbar jaka data zuba mata tai murmushi ta ce "Haba Halisa, ai za a iya kawo ki wajan Dadar duk sanda kike so, kuma za a bawa Dada waya ku dinga hira" ita dai kuka kawai take farar fuskarta tai jajir. Surry ta ƙara cewa "Ba lokaci mu ake jira" sai lokacin Dada ta sauke numfashi ta ce "Halisa ki kama kanki, ki rage surutu da tsiwa, idan kika zaluncin yarinyar data taimaki rayuwata sam ban yafe miki ba, duk abin da tace kiyi mata kiyi ba musu ki ɗauke ta tamkar uwa, kuje Allah ya yi miki Albarka Insha Allah zaki Albarka zaki zama abar kwatance burukanki zasu cika, zamu zauna zaman jiran dawowarki nida Shatu" Halisa ta ƙanƙame Data sai Ajjiyar zuciya take saukewa ji take kamar ta rabu da ita kenan rabuwa ta har abada. Da ƙyar Surry ta zame Halisa daga jikin Dada suka shiga mota kai tsaye suka nufi gidan su Zahrah lokacin ana ta zuba shirin tafiya airport. Surry ta rasa yadda zata shiga ta Halisa sai kawai ta ɗakko wani liƙab ta kalleta ta ce "Maza saka wannan a fuskar ki kada wasu su gani" tana shassheƙar kuka ta ce "Ban iya ba" Surry ta ja tsaki tare da kama fuskar Halisa ta ɗaura mata Liƙab ɗin. Surry na tafe tana binta a baya tamkar munafuka ita duk liƙab ɗin ya dameta. Karon da taci da mutum ya sa cikin masifa ta ɗago ta ce "Aradu ba zan yarda ba sai na rama....," Yawun bakinta ya ƙafe lokacin da idanunta ya sauka akan fuskar Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu, jikinta na rawa haka ma laɓɓanta ta ce "Balarabe kai ne..." Ta faɗa tana ƙoƙarin cire liƙab ɗin fuskar daidai lokacin Saif-wazir ya ƙarasu wajan tare da Abba Hakimi... _IDAN BA KE It's paid book ₦500 via 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman fidelity bank shaidar biya 08119237616..... Isn't free if you read for free🤷🏾‍♀️_ "Subuhanallah yi haƙuri bata kula ba" Surry ta faɗa da sauri tana kama hannun Halisa ba tare data bari ta buɗe liƙab ɗin ba. Ita dai Halisa kallon Yaa Sheikh take kamar idanunta zai faɗo ta cikin liƙab ɗin. Yaa Sheikh ya ratsa ta gefen Halisa zai shige tayi saurin shan gabansa tana kwace hannunta, duk da ta tsorata da yanayin shi amma bai hanata ƙara binsa da idanu ba da ƙarfi ta ce. "Laa Wallahi shi ne, Balarabe ashe zan sake ganinka?" Dam! Zuciyar Surry ta buga, Umar-khan zai magana Abba Hakimi ya girgiza masa kawai alamar yai shiru. A wannan karan ba Yaa Sheikh bai kalli yarinyar dake gabansa ba, sai ƙara ɗauke idanu yake gefe guda, ganin yadda ya yi mata ya sanya Halisa ta saka hannu ta cire liƙab ɗin tare da matsawa gaban Yaa Sheikh ta ce "Baka gane ni ba? Nasan ka gane ni ni ce fa Halisa Danejo Rome ka manta ni? Ina kaje bana ganinka?" Tarin makami da ya yiwa Saif-wazir yawa ya sanya ya hangame baki, anya yarinyar nan ba aljana bace ko kuma wacce Aljanu suka shafa?. Khalil Ahmad Sarki ya juya da sauri ya kalli El-bashir dake can gefe ɗaya yana waya, ya ƙara juyawa ya kalli Halisa wacce ɗan ƙaramin bakinta ke motsawa tana yiwa Yaa Sheikh rantsuwar Wallahi ya gane ta yana sani yaƙi kulata. Ahmad Sarki da har yanzu yake kallon Danejo sai ya juya ya kalli El-bashir makami kamannin su na rikita masa lissafi musamman da yaji muryar Danejo wacce take iri ɗaya data El-bashir sak! Sai dai ita ɗin macace saɓanin El-bashir da yake namiji. "The wonder never ends" Khalil ya furta a fili na dafe kansa. Danejo ta ce "Yanzu baka gane ni ba, nice fa? har ka taɓa bani mangoro?" Yaa Sheikh ya ware fararen idanunsa sosai tare da sauke ganinsa akan zagayayyiyar fuskar ta, kai tsaye ƙwayar idanunsa ta shiga cikin nata. Danejo ta haɗiye sauran maganar sbd idanun Yaa Sheikh da sukai mata kaifi, a kallo ɗaya da ya yi mata ya saka mata shakkar shi, tsoro da kuma ganin girman shi. A hankali ya zame hannun yana mai barin wajan Danejo ta bisa da idanu.. "Kin san shi ne?" Danejo ta kalli Saif-wazir kamar zatai magana sai kuma ta murguɗa masa baki Surry ta kama hannun ta suka shige cikin gidan su Zahrah. Saif yai dariya son ran shi ya ce "Akwai rigima Yaa Sheikh za ai raino" Khalil Ahmad Sarki ya daki kafaɗar Saif ya ce. "I couldn't understand, wai wace yarinyar nan? Na ruɗe fa" Saif ya ce "wato abinne gaba ɗaya is complicated, muje mu zauna" Ya juya zuwa ga Abba Hakimi wanda ke sauraran su ya ce "Abba ita ce ƴar fillon da nake baka labari" Abba Hakimi ya jinjina kai cikin nutsuwa ya ce "Ikon Allah ya kamata mu zauna, Umar-khan maza kira mini Barrister Maryam a waya" Umar-khan ya ce "To Abba" Abba Hakimi ya yi gaba Saif-wazir ya bi bayan shi, Umar-khan ya tsaya kiran Mother a waya. Khalil Ahmad Sarki ya nufi inda El-bashir yake tsaye ya zuba hannun shi cikin aljihun wandon shi ɗaya hannun yana shafa sumar kansa. "Kaga abin da na gani kowa El-bashir?" El-bashir ya juya zuwa ga yayan nashi kamar ba zai magana ba sai kuma ya ce "A'a duk an cika waje da ihu me zan gani haba kun zama kamar wasu mata" Khalil ya ce "let's keep a joke a side wata na gani mai mugun kama da kai" El-bashir ya nuna kansa yana fiddo idanu waje ya ce "Ni kaga me kama dani?" El-bashir ya tambaya yana gyara tsaiwar shi. Khalil Ahmad Sarki ya ce "Ai kamannin har sun ɓaci hatta beauty point da gashin girarka daya rabe biyu, hatta muryarku iri ɗaya ne El-bashir na girgiza" a karo na farko El-bashir ya yi murmushi kawai yana girgiza kansa ba tare da ya ce komai ba, hakan ya fusata Khalil ya ce "Ya ina magana akan abu mai muhimmaci kana dariya?" El-bashir ya jingina jikin mota baka iya gane yanayin shi ya ce "Me zance Abu Juwairah? Kawai kun haɗu da aljana banda haka ina za a samu wata mai kama dani? ni ba ƙanwa ba ni ba ƴa ba, Please mu bar wannan maganar" Khalil zai magana wayarsa ta shiga ringing ganin matarsa ce Oum Juwairah ya sanya yabar wajan yana amsa sallamar ta. Tunda suka shiga ɗakin Danejo bata kalli inda Zahrah ke zaune ba, kanta a ƙasa ta haɗe fuska sosai. Zahrah gabanta ya faɗi ganin yadda cikin kwana biyu Halisa Danejo ta sauya kamar ba ƴar fillo ba, fatar ta na ƙyalli ko'ina na jikin fes yake duguwar rigar da Surry ta bata ta saka mai purple ta amshi jikinta sosai. Surry ta ce "kina ta kallon ƴar fillo kamar baki san taba lokaci na shigewa" Zahrah ta sauke numfashi ta ce "Kada dai ki mata matsayin mai aikatau zaki cikin gudana ƴar fillo" Danejo ta ɗago kai ta kalli Zahrah cikin sautin siririyar muryar ta ta ce "Ban manta ba, sunana Halisa Danejo Rome ba ƴar fillo ba" Zahrah taja tsaki ta ce "Ji banza ina cewa a cikin ruga muka ɗakko ki? Banda warin shanu dana Kindirmo me kike? Har kece za kice wai ke ba ƴar fillo bace?" Danejo ta shiga kallon Zahrah zuciyarta na jin zafin maganganun data faɗa mata idanunta har ya cika da ruwan hawaye saboda ba zata iya mayarwa da Zahrah magana ba bisa umarnin Dadarta. Surry taja gefe guda tana murmushi jin daɗi ba tare da kowa ya lura ba, ita kanta baza taso tun yanzu Halisa ta fara mayarwa da Zahrah magana ba. Cikin sauri ta ce "Zahrah dama shiryawa ki kai yanzu 1:30 ance 2:00 daidai jirgi zai tashi" Zahrah ta miƙe ta ce "Ina son haɗuwa da Deen wlh kwana biyu bana iya barci Surayyerh abin cikina masifa yasa mini ba zan iya jurewa ba idan ban samu abin da nake ba dole naje naga Deen" a fili Surry ta ce. "Wallahi baki da tunani Zahrah ganin Deen a halin yanzu bai dace ba kuma nasan abin da zaku aikata" a zuciyarta kuma ta ce "Well-done Zahrah ban fatan ki daina bibiyar maza tun yanzu" Zahrah ta ɗauki hijabi tare da juyawa ta kalli Surry ta ce "Meye sunan abin da kika bawa yarinyar nan ta saka bani" Surry ta amshi liƙab ɗin hannun Danejo wacce ta haɗe rai sosai taƙi yarda ta ƙara kallon inda Zahrah take. Cikin sauri ta gama shiryawa babu mai cewa Zahrah ce ta nufi ƙofar baya akan nan da 20 minutes zata dawo. Tana fita Surry ta kalli Halisa ta ce "Kina ji ƙanwata, Kinga wannan mutumin da kika ganu har kika ruɗe kina cewa Balarabe?" Halisa dai kallon Surry take kafin Surry ta ce "To shi ne mijin Zahrah, ina so ki nutsu ki fahimta Kinga daga can kano Madina zaku shige, kina wanka sau biyu ko sau uku a rana, haka ma brush da saka kaya masu kyau...." Ta ci-gaba da faɗa mata komai na yadda zata gyara jikinta da tsafta ta ɗora da faɗin "Kin fara Al'ada ne?" Danejo ta girgiza kai. Surry ta ce "stop raising your head, magana zaki" ta ce "Ni ban san wani Al'ada ba" Surry ta zare ido sai ba tace komai ba, ta shiga lodar kayan shafawa ta sakawa cikin jakar Halisa tare da faɗin. "Kada ki kuskura ta gani ko da wasa, idan ta gani ma ki san me za kice kar ki ambaci sunana" Abba Hakimi ganin maganar mai muhimmanci ce ya tattara ya barta zuwa lokacin da za su koma gida ayi a gaban kowa, duk family su san matsayin yarinyar. Yaa Sheikh yana kwance saman gadon hotel ɗin da suka sauka idanunsa rufe kamar mai tunani daga shi sai farar Jallabiya ko barcin ya kasa, har lokacin bai bawa auren muhimmanci ba, balle ya sakawa ran shi nauyi wata ƴar mace ya hau kan shi, iya auren daya san da gaske an ɗaura kuma matarsa ce bisa tsarin addinin Musulunci, na ƴar fillo kam yama mance da shi at all baya tunanin shi. Ya miƙe a hankali zuwa bathroom tare da sakarwa kansa shower ya jima kafin ya fito ɗaure da bathrobe a jikinsa, cikin sauri ya shirya cikin wani kyakkyawar Voyel mai manyan zane maroon colour ya ɗora farar Alkyabba ya wani irin sahihin kyau kamar Prince Hamdan bin Mohammed. Ya fito cikin parlourn ɗakin ƙamshin Roja ya cika ko'ina a wajan wanda ya jawo hankalin Khalil dake waya da Oum Juwairah ya ɗago kai bai san lokacin da ya ce "Masha Allah" duk rashin tsaurin idon mutum ba zai iya tsayawa gaban Yaa Sheikh ya yi ba, Ilhamar da Ubangiji ya bashi ta musamman ce, a kallo ɗaya yake dagula lissafin mutum. Yaa Sheikh da jikinsa ya bashi kallon shi ake ya ɗago kai suka haɗa idanu da Khalil ya kafe shi da ido alamar lafiya? Wannan kallon fa? Khalil ya shafa kai sbd Kunya ya ce "Muje ko?" Yaa Sheikh yana gaba Khalil na bayan shi, cikin nutsuwa yake tafiya har suka ƙarasu wani room a ƙofar room ɗin suka ci karo da wani saurayi rungome da mace wacce take rusa masa kuka kamar ranta zai fita. Yaa Sheikh ya ɗauke ido da sauri a ransa ya ce "Asstagafirullah Yaa Allah" Khalil kuma ya taɓe baki a haka suka fitar zuwa reception na hotel ɗin daidai nan kuma Mai martaba da abokin nasa El-bashir suka fito suma, haka Abba Hakimi da nasa abokan Umar-khan, Ishaq-Hakim, Saif-wazir. Father daman yana can ba Alhj Farouk mahaifin amarya. Jirginsu Yaa Sheikh daban na Amarya da ƴan uwanta da suka yanki tickets daban. A airport suka haɗu baki ɗaya har lokacin Zahrah bata taho ba, Danejo tunda idanunta ya sauka akan jirgi ta gigice tsoro ya kamata. Yaa Sheikh da Abba Hakimi da kuma Mai martaba Ahmad Sarki tare da Father duk suna Vip. Sauran kuma suna nrml waje. Jirginsu ne ya fara tashi babu jimawa Zahrah ta ƙarasu wajan ta sha kwalliya cikin wata lafaya mai kyau da tsada. Tofa kallon ya dawo kan Danejo ta rantse da abin da zai kashe ta ba zata shiga jirgin ba kuka sosai. Wasu nayi mata dry. Da ƙyar Surry ta lallaɓata gudun abin da zai je ya dawo ta zauna kusa da ita. Danejo ta ƙanƙame jikinta wanda yake rawa hawaye na zubuwa daga cikin idanunta ta ce "Na lalashe Dadata na kaɗe, na bushe shikenan zai a shige sama dani" Surry ta ce "ki nutsu Halisa babu abin da zai sameki kinji ko?" Ita dai kuka take when the plane will take off numfashinta ya tsaya cak Surry ta shiga girgizata tana amsar ruwa tare da yayyafa mata da ƙyar ta dawo daidai ta fara yunƙurin amai yaƙi zuba, lokaci guda ta fita hayyacinta jirgin yana wullawa sama ta fara wata uwar ƙara tana faɗin "Na mutu, Wallahi na mutu.." Misalin 4:45 manyan motocin da suka ɗakko dangin amarya daga airport suka shiga parking a harabar gidan Mother. Wasu ƴan uwan Zahrah da yayar mahaifiyarta da ƙanwar mahaifiyarta sune suka kamo Zahrah da aka rufe mata fuska zuwa cikin gidan sauran friends suka bi bayansu. A parlour akai musu masauƙi su gaisa da dangin miji kafin a basu masauki. Jadda dake zaune ta ce "Wai ina matar Gadangar ne sai wasu yamutsastsun fuskoki nake gani?" Ladidi ta ce "Gata nan Zahrah buɗe fuskarki ai miki bayanin dangin miji" Mother dai na zaune hankalinta na can waje guda sai kaɗa ƙafa take. Dr A'isha ma na zaune taci uban kwalliya kana ganinta kasan ba talauci inda take, Yaya Halima ma haka, sai Momi tare da ƴan uwan father, da matar Uncle Haroon. "A meye haka? Alsulhu khair buɗe fuskar uban kowa ya gani" "Ai Hajiya kin san amare da kunya" Jadda ta ce "kaji masifa ko? Waye sa dake wace ke? daga gidan wa zuwa ina?" Ladidi tai shiru amma Jadda ta fara ƙular da ita. "Muhammadur Rasulullah s.a.w wannan ai uwa aka aura Aliyu ba mata ba? Gidan ubawa Aliyu zai kai ɗirkekiyyar matar nan ni kai na ta kusa haifata yau na shiga uku da gaske wannan ce matar Malam ɗin?" Jadda ta faɗa bayan ta saka hannu ta buɗe fuskar Zahrah. Surry na gefe tana danne dariyar dake ranta. "Maryam zo kiga abin al'ajabi yoo Allah na tuba ko ke ai kinfi matar malam kyan gani? Allah sarki Gadanga an haɗaka da uwar mata" sai kuma ta fashe da kuka sosai ta ce "Innalillahi ashe har gashin doki take saka zunubi babba" ta saka hannu ta kama hannun Zahrah ta ce "Wanne tsinannen abu ne wannan kuma?" Ta faɗa tana duba farcen hannun Zahrah. "Haba Hajiya wannan abun duk na mene? Ya daga kawo yarinyar sai cin mutunci?" Jadda ta miƙe ta nufi kan me maganar ta dungure mata kai ta ce "Algunguma ai duk duniya an gama cutar Malam an haɗa shi da arniyya" "Arniyya wacce ira kuma Hajiya?" Ladidi ta faɗa rai ɓace. Jadda ta kunce ɗan kwalin kanta tare dacin ɗamara ta ce "Arniyya ƙatuwa ma, mene bambancin su? ga tafkeken zunubi ba tausayi ba komai aka cirewa doki gashin shi aka saka mata, gata narkekiyya mai idanu a tsakar kai, gashi ta wani ɗashe kamar mace mai shigar sabon ciki Innalillahi masifa ta saukarwa Malam" gaban Zahrah ya faɗi tai saurin rufe fuskarta. Dr A'isha ta fashe da dry wacce tun ɗazo take danne ta. Yaya Halima girgiza kai kawai take kafin ta ce "Kuyi haƙuri don Allah muke ga masauƙi can" Mother hankalinta na kan Danejo wacce take ɗan ɗaga liƙab ɗin fuskarta tana leƙewa da sun haɗa idanu da mother sai ta mayar ta rufe. Babu wanda Jadda bata ciwa mutumcin ba kafin su bar wajan. Mamaki ya kama Ladidi ganin uwar mijin ta Zahrah ci kanku ba ta ce ba. Kwanan su biyu suka koma Yola aka bar Zahrah tare da Halisa. Yaa Sheikh ne durƙushe a gaban Abba Hakimi da Uncle Haroon sai Uncle Bashir ga Mother da Yaya Halima da kuma Momi matar Abba Hakimi. "Ina magana kayi shiru Aliyu?" Abba Hakimi ya faɗa cikin sassauta murya. Yaa Sheikh ya ɗago kan idanunsa ya sauka akan yarinyar da ake nuna masa, ya ƙara duban Halisa da kyau sai yanzu yai mata cikakken kalo ya mai da idanunsa kan Abba Hakimi ya ce. "Wace? kamar ban waye ta ba?" Uncle Haroon yai murmushi yana jinjina halin Yaa Sheikh. Abba Hakimi ya ce "Amma kasan Rugar Bello? Ka kuma san Arɗon rugar ka gane abin ya faru,ka kuma shaida zoben hannunta?" Yaa Sheikh ya ɗan kallin kyakkyawan hannun Danejo wanda yake maƙale da zoben da yake so har ransa nan take ransa ya ɓaci, a lokacin ya tuna everything ya shanye mmkin kamannin da yake gani a fuskar yarinyar, shi kam a rayuwa ko zai so mace ai banda ƴar cikinsa wannan gwaliliyyar yarinyar bata shige raino ba, ita za a kalla ace wai matarsa? Shi kam ya zai yi da mata biyu ba?. Yai shiru yaƙi bada damar da za a karanci halin da zuciyarsa ke ciki. Uncle Bashir ya ce "Da alama ya fahimta" Abba Hakimi ya ce "Halisa maza je aikyan yayar taki kada taga kin daɗe" ta miƙe da sauri domin daman a takure take Yaa Sheikh duk ya firgitar da ita. Abba Hakimi ya ce. "Ba wasa muka zauna yi ba, jibi zaka shige Madina kafin nan kana son yarinyar nan ko baka son ta?" Yaa Sheikh yai shiru ya kasa fahimtar abin da suke nufi dashi, shi kam duk ranar da ya ce yana son mace ai sai ya yi azumin kaffara shi ya sa har abada ba zai taɓa cewa yana son wata ba. Ya girgiza kai a hankali "Baka son ta?" Cewar Uncle Haroon. Bai kalli Uncle Haroon ba ya kalli Abba Hakimi. Abba Hakimi ya gyara zama yana sakin murmushi ya ce "Ka shirya sakinta? baka san me gobe zata haifar ba?" Yaa Sheikh ya riƙe hannunsa da kyau yana girgiza kansa harshen shi na harɗewa ya ɗan motsa ƙafarsa ɗaya cikin In-ina ya ce "Ha...hhh...har... Har abada ba ba ba zan zan so ta ba" _IDAN BA KE it's paid book ₦500 via 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman fidelity bank shaidar biya 08119237616..... Isn't free if you read for free🤷🏾‍♀️_ Yaa Sheikh ya faɗi hakan kai tsaye. Abba Hakimi ya ce "To kafin nan muyi wata game mana, idan kaci ni kuma nayi al'ƙawarin raba aurenku har abada, ka zauna kai ɗaya da ita Zahrah tunda ba a son Ƴar fillo" Mother ta juya ta kalli Yaa Sheikh kafin ta ce. "Yanzu meye laifin yarinyar? ba tafi wacce aka haɗaka da ita ba? to a karo na farko zan faɗa maka zama da wannan babu fashi a wajanka Aliyu" Uncle Haroon ya ce "A'a Barrister labarin aure baza kici haka ba, ana yin aure dan farin ciki da kwanciyar hankali,idan ba yajin yarinyar a ran shi bai kamata a takura masa wajan zama da ita ba, zai iya amincewa bisa takurar kuma ya cutar da ita, a dai bi komai a hankali" Mother ta girgiza kai ta ce "Uncle Haroon ka rabu da Aliyu, tunda ya amince dana Zahrah zai amince da wannan ɗin ma sai ya tattara su tafi can Madina su ƙarata" Yaya Halima ta kalle su baki ɗaya kafin ta ce "duk ba Wannan ba, na tambayi Zahrah a sigar wasa cewa wannan ƙanwarta ce? Sai ta ce mini wai ƴar aiki aka samu mata, That's the position of a maid in Aliyu's house" Dr A'isha tai murmushi ta ce "Matar gida ko ƴar aiki? dama a ɗauke ni aikin gidan Aliyu naga yadda zaman zai kasance" Yaa Sheikh ya ɗaga kansa a hankali kamar zai kalli Dr A'isha sai kuma ya fasa ya mai da kan ƙasa. Sai a lokacin Uncle Bashir ya ce "Ya kamata kada ita Zahrah tasan cewa itama yarinyar matar Yaa Sheikh, a barta ta tafi da ita a matsayin ƴar aikin kamar yadda tazo da ita da manufar hakan" "I also agree with this decision, she took it as her worker" cewar Dr A'isha. Abba Hakimi ya sauke numfashi yana duba lokaci,bayan nazartar maganganun sauran ya ce. "Na amince baka son ƴar fillo, suma sun yarda da hakan, zaka tafi da ita can gidanka dake Madina matsayin matar ka kuma ƴar aikin matar ka, zaka iya zuba idanu matar ka ta zama baiwa a cikin gidan aurenta, ra'ayinka ne, Ni bance kaji tausayin ta ba, kawai ina son ka riƙe mini ita a wajanka na tsayin shekara ɗaya ciff, ka sata makaranta, ni bance ko sau ɗaya kayiwa Halisa Danejo kallon matar ka ba, ita ɗin kamar ajjiya ce na baka, ka dawo mini da ita shekara guda, kada naga wani sauyi a tare da ita, ka tabbatar yadda take budurwa a haka ka dawo mini da ita, nayi maka al'ƙawarin shekara nayi zan raba auren naku rabawa ta har abada" gaba ɗaya mutanan parlourn suka zubawa Abba Hakimi idanu, su basu ga dabarar haka ba, sun san ko shekarar biyar aka bawa Yaa Sheikh there is nothing he will do, there will never be any change from him, balle ya furta da bakin shi ya ce yana son ta,That will never happen. Abba Hakimi ya gyara zama sosai idanunsa akan Yaa Sheikh ya ce "Amma Wallahi Wallahi Allah kenan Aliyu ban taɓa rantsuwa akan ka kamar haka ba, shekara guda tayi ka dawo mini da yarinyar nan saɓanin yadda nai tunani zaka sha mamakina, kai ba yaro bane ka fahimci mai nake son faɗa maka, babu dalilin da zai sanya ka lalata budurcin yarinya kuma ba son ta kake ba, This is a deal" Uncle Bashir ya ce "Amma Abba Hakimi wannan deal ɗin bai tsauri ga Malam ba?" Abba Hakimi ya ce "Ba kaji kai ma kace Malam ba? Yaa Sheikh zai iya ɗaukan wannan game ɗin" Murmushi Uncle Haroon ya yi kai tsaye ya yarda da abin da Abba Hakimi ya zartar cikin fara'a ya ce "To idan haka ne ina tsagin uwar gidan Halisa, za muje matsayin masu aikin gida kawai" Uncle Bashir ma ya ce "Ni ma dai ina team ɗin uwar gida" yaya Halima tai murmushi ta ce "Ikon Allah, to ina team ɗin Aliyu koma mai zai faru ya faru she is his wife matar shi ce babu laifi" Dr A'isha ta ce "Ni dai ba zan zaɓi team tun yanzu ba, sai naje Madina naga yadda zaman zai kasance" Idanun Yaa Sheikh ya yi jajir shi kam a rayuwa mai Abba Hakimi ya mai da shi? Ina ruwan shi da wata ƴar fillo balle har yaje gareta matsayin miji mai buƙatar hakƙin shi wajan matarsa? Zai bawa kowa mamaki. Miƙewa ya yi a hankali zai bar wajan Abba Hakimi ya ce "No tayaya ka taɓa ganin anyi deal ba saka hannu, maza saka hannu a wannan dairy ɗin" Yaa Sheikh ya kalli Abba Hakimi da kyau, shi kam Abba Hakimi ya ɗauke kan shi alamar bai gane meke nufi ba. Cikin sauri ya saka hannu tare da saka suna da date da kuma time. Yana gamawa ya juya jiri na ɗaukan shi sbd ciwon kai ya nufi Part ɗin shi. Abba Hakimi yabi bayan shi da kallo a zuciyarsa ya ce "let's see ko Aliyuna waliyyi ne" Wajan ya yi shiru kowa da abin da yake tunani a ran shi, Mother na tunaninsu yadda zata cusa Halisa a zuciyar Yaa Sheikh, kallo ɗaya ta yi wa yarinyar hankalinta ya kwanta da ita, kawai dai ta fahimci bakin yarinyar babu control kamar ba a gasa mata shi ba. Yaya Halima kam gani take kamar Yaa Sheikh ba zai iya tsallake wannan gasar ba, lura da yanayin Halisa da komai sai tafi Zahrah jan hankalin ɗa namiji kowa zaman zai kaya ohhu! "Kada a bari Jadda da Engineer su san maganar auren wannan yarinyar Halisa da Yaa Sheikh, mu bari muga abin da hali zai aga yanayin zaman maybe a samu sauyin ra'ayi game da Yaa Sheikh akan yarinyar" cewar Uncle Haroon. Abba Hakimi ya miƙe tsaye haka Uncle Haroon da Uncle Bashir sukai wa Mother sallama. Bayan tafiyar su yaya Halima ta kalli Mother ta ce "Yanzu me zaki Barrister?" Mother ta girgiza kanta idanunta akan wayarta tana neman contact ɗin wata mata ta ce "me zan yi kowa yaya? ga Abban Sheikh nan ya gama magana" ta faɗi hakan tana danna call. "Tun ɗazo da nace ki kawo mini bottle water ina kika tsaya?" Zahrah ta tambayi Halisa tana zare mata idanu. Ta turo baki gaba ita tsakani ga Allah take son faɗawa Zahrah abin da ta fahimta wajansu Abba Hakimi. Zahrah ta ce "ba dake nake ba dan ubanki?" Da sauri Halisa ta kalli Zahrah bakinta na rawa ta ce "Baffana kika zaga? Ya mutu fa?" Wani tsaki Zahrah taja ta ce "Idan ya mutu ni na mutu? Waye shi da ba za a zage shi ba" Halisa ta jima tana kallon Zahrah idanunta ya yi jajir ga abin masifa babu halin yi sbd ka shaidin Dada a gareta. "Matsa ki bani waje ai dama har uwar suka haɗu suka mutu Kinga baki da sauran wani gata kiyi mini aiki hankali kwance" Halisa ta juya da gudu tare da fashewa da kuka hannunta a fuskarta tana karewa. karo suka ci da Maimoon data ɗakko warmers ɗin lunch wanda akace ta kaiwa Zahrah, Maimoon ta ja baya da sauri tana faɗin "Subuhanallah ya akai kike kuka haka ke dawa?" Halisa ta kasa kuka sai shassheƙa da zata iya ita gida kawai zata gudu wallahi. Maimoon ta ce "Ok ya isa daina kukan jirani a nan wajan kinji?" Ta ɗaga kai a nutse alamar "to". Zahrah na kwance waya a hannunta suna vedio call da Deen wanda gaba ɗaya ba vedion Allah da Annabi bane, ita dai Maimoon taji wani sauti kamar gurnani da sauri Zahrah taja duguwar rigarta zuwa ƙasa tana rufe wajan data buɗe. She pretended not to notice what she had done. Tana ajjiye warmers zata juya Zahrah ta ce "Hey you" Maimoon tai banza kamar ba taji ba. "Ina magana" Maimoon ta juya kaɗan suka haɗa idanu ta ce "dani kike?" Ta ce "to waye a ɗaki?" Maimoon ta ce "Huh na ɗauka kina magana da wayar hannun ki ce" Zahrah ta sakko daga kan gadon ta ce "what the do you mean by that?" Maimoon tai shiru can Zahrah ta ce "What's your name?" "Maimoon" ta bata amsa Zahrah ta ce "Ok At least you have to respect me ni matar yayanki ce, kin shigo bedroom without my permission da muna tare Yaa Sheikh fa?" Maimoon ta ware idanu sosai ta ce "Yaa Lee a bedrooms ɗinki? Shhhh" tana faɗin hakan tai waje da sauri. "Kan uba wannan yarinyar sai na saita mata zama kalli Yadda take mayar mini da matar tani?" Waya ta ɗauka ta shiga kiran Surry. Maimoon ta kalli Halisa wacce ke zaune a ƙasan carpet ta ce "Sister tasu muje part ɗin mu" Halisa ta girgiza kai Maimoon ta ce "Anty Zahrah ta ce mu tafi tare zuwa dare sai ki dawo" ta miƙe tana faɗin "Ita ta ce haka?" Maimoon ta ce "ita ce mana" hannunta ta kama suna zuwa Main parlour El-bashir na tashi tare da ɗaga waya ya nufi ƙofa, Halisa ta bi bayan shi da kallo ta ɗauka Balarabe ne. Maimoon taja hannunta har zuwa part ɗin su, Zeefa da auta Fattoumah suna zaune ganin Halisa yasa Auta Fattoumah faɗin "Wow yaya Moon wannan kyakkyawa ce She's very beautiful she looks like bro El" Maimoon ta ce "to sarkin surutu" ta zaunar da Halisa ta shiga ɗakko mata su ice cream da chocolate amma sam Halisa taƙi ce sbd bata saba dasu ba, ta ɗago kai a hankali ta ce "bana cin irin wannan" Nazeefa ta ce "To sai me?" A hankali kanta a ƙasa ta ce "Kindirmo nake shu" a tare suka zare idanu tare da faɗin "what?" Tai shiru tana kallon su can Maimoon ta ce "Zeefa haɗa mata ruwan wanka a bathroom bari na kawo mata kindirmon" tana faɗin hakan tai waje har lokacin Maimoon ta kasa mance abin da idanunta ya gani a bedroom ɗin Zahrah. Cikin sauri Zeefa ta haɗa mata ruwan wanka tare da nuna mata komai a toilet ɗin da yadda ake amfani da su. Suna bakin toilet ɗin suka ji ana knocking "Halisa duba kiga waye?" Kamar ba zata ba sai ta nufi ƙofar jiki a sanyaye zagin da Zahrah tayi mata har yanzu damun zuciyarta yake. Halisa ta tsaya bakin ƙofa ta rasa me za ta ce can dai ta ce "waye?" Ta faɗa cikin ƙasa da murya. El-bashir ya gyara tsaiwa hannunsa riƙe da waya da kuma chocolate ya ce "Buɗe ki gani mana?" Halisa ta murguɗa baki tana ƙoƙarin buɗe ƙofar Zeefa ta ce "jeki kiyi wankan bari na buɗe ƙila Maimoon ce" Halisa ta juya zuwa bathroom ba tare da ta ce komai ba, Zeefa na buɗe ƙofar taga El-bashir tsaye fuska ɗaure ta ce "Yaya El" ya wurga mata harara ya ce "wace take tambayar waye?" Zeefa ta juya ta kalli ƙofar bathroom ta ce "Laa Halisa ce bata sanka bane" ya ce "I'll break her legs" chocolate ya bawa Zeefa ya juya yana faɗin "Kira mini Fattoumah" ya nufi Main parlour Mother dake zaune ta ce "Yau zaka shige ne?" Ya ce "I don't think so.. sai abin da Mai martaba ya ce" ta ce "Ohh abokin Mai martaba". Washegari Zahrah na zaune ta caɓa ado cikin wata atamfa mai kyau ruwan ƙwai ta yafa mayafi babba kamar ta Allah. A hankali ta fito zuwa Main ta samu Mother zaune ita da Jadda suna hira sai Maimoon Zeefa da Auta Fattoumah suna makaranta. Zahrah ta durƙusa ta ce "Ina yini Mother?" Mother ta ce "kina lafiya ya kwanan baƙunta?" Zahrah ta ƙara sunkuyar da kai alamar kunya ta ce "Allahamdulillah, daman cewa nayi bari nazo idan da aiki nayi" Jadda da bakinta ke rawa ta ce "Allah ya yi gutsi gutsi da maƙaryaci" Zahrah taƙi kallon Jadda. Mother ta ce "Ayyah jeki ki huta ba aiki" Zahrah dai ta kasa riƙe abin da yake ranta ta ce "Yaa Sheikh fa? daman ina son gaishe shi ne" da hannu Mother ta nuna mata wani part ta ce "zaki iya samun shi can" ta miƙe da sauri ba kunya ta nufi Part ɗin Yaa Sheikh. Mother ta ce "Maimoon kira mini Halisa yanzu" Maimoon ta nufi part ɗin Zahrah ta samu Halisa sai zuba kayan Zahrah take cikin trolley bag tayi saurin riƙe hannunta ta ce "Kizo Mother na kiranki" Halisa ta ce "Bari na ƙarasa aikin Anty" Maimoon ta ɗaga ta tsaye ba tare da ta ce komai ba ta jata zuwa waje. Bata samu Mother a parlour ba sai suka shige bedroom ɗinta tana zaune bakin gado. Mother ta ce "shigo Halisa, Maimoon jeki ko" Maimoon ta juya Halisa ta shiga kanta a ƙasa haka kunyar Mother tai mata nauyi taji kunyarta ta ce "Saki jekin ki zo nan" ta kama hannunta tare da zaunar da ita bakin gado ta ce "Yaya sunanki ma?" A hankali ta ce "Halisa Danejo Rome" Mother ta jinjina kai ta ce "Ok Zahrah ƴar uwar ki ce?" Ta girgiza kai ta ce "A'a wai aikatau zan mata" ta faɗi haka a taƙaice. Mother ta jinjina kai sosai ta ce "Saurare ni da kyau, Zahrah matar Yaa Sheikh ce Wannan babban mutumin da kika gani fari dashi?" Halisa ta ce "Balarabe?" Mother ta ce "Yawwa shi" haka kurum idanun Halisa ya cika da ruwa Mother ta ce "Shi ne mijin Zahrah kuma kema mijinki ne, dan haka ke ba ƴar aiki bace matar shi ce ke, kamar yadda Zahrah take matar shi haka kema kike matar sa" Halisa tai ta kallon Mother har lokacin idanunta cike yake da hawaye da gaske Balarabe shi ne mijin Zahrah?. Mother ta katse mata tunani da faɗin. "Kece uwar gida, aurenki aka fara ɗaurawa sannan na Zahrah, na kira ki muyi magana sbd Yaa Sheikh ya ce baya son ki" da sauri Halisa ta miƙe tsaye hawaye na zubu mata bakinta na rawa ta ce "Amma ni ina son shi ai..... Ni ina team Yaa Sheikh ku fa? 08119237616 Paid book ₦500 "Kin san shi ne da kike son shi?" Mother tayi tambayar idanunta akan Halisa wacce hawaye ya gama cika mata idanu. Ta kasa cewa komai amma bakinta bai bar rawa ba, ganin yanayin ta ya sanya Mother sassauta murya ta ce "Kina da ƴan uwa a garin nan?" Ta girgiza ta ce "Aradu babu" "Ok to ki Saurare ni da kyau, listening to me..." Tsayawa tai da maganar idan ma tayi ta san a banza, Halisa does not speak English, let alone understand what is being said. Ganin bata da wani option wanda ya shige tayi magana da harshen da Halisa zata gane ya sanya Mother tattara nutsuwarta ta ce "Ki ɗauke ni matsayin uwa kafin ki koma gida, zan riƙe ƙo kamar ƴar dana tsuguna na haifa, da farko ki yarda cewa ke matar Yaa Sheikh ce Balarabenki kamar yadda kika ce ɗin, Kinga zoben hannunki shi ne sadakinki, abu na biyu kada ki kuskura koda wasa ki faɗawa Zahra kema matar Yaa Sheikh ce, duk aikin data saki kiyi zaki samu lada albarkacin igiyar auren dake kanki, duk abin da Yaa Sheikh zai ce kiyi just do it ina nufin kiyi kai tsaye, ba zai cutar dake ba, infact ai kin riga da kin san shi ko?" Halisa ta ɗaga kai da sauri kuma ta ce "Kuma ina son shi ai, ina ganin shi idanuna idan ina barci" Mouth ta ce "Good, a kullum yana tashi tun ƙarfe 4 na dare baya komawa barci sai ƙarfe 12 sbd ƙarfe 8 yake zuwa wajan ɗaliban shi, duk inda 12 tayi ya dawo gida, bai damu da abinci ba sosai ba zai taɓa cewa yana jin yunwa ba, tsakanin azahar da asr yana barci idan bai ba, ciwon kai yake sosai, sannan baya rabo da black tea da zuma a ciki, duk ranar Alhamis da Litinin azumi yake, yana son ƙosai sosai" Halisa ta saki murmushi tare da riƙe hannun Mother ta ce "Innalillahi ƙoshai aradu daɗi akwai burudi to? Wayyo Allah zanci ƙoshai na mure" dariya Mother zatai ko takaici bata son duk wannan shirman a wajan Halisa.. "Zaki samu abin da yafi ƙosai ba, amma can idan kina shirme gidan yankan kai suke kai mutum, ki zama a nutse, bayan haka yana son abincin gargajiya tuwo, dambu da sauran su dai, ki tabbata kina wanka sau biyu zuwa uku a rana, idan ba haka ba Yaa Sheikh kurarki zai yi daga gidan shi, kuma kishiyarki ta rabaki da mijinki har abada" Idanun Halisa ya sauya kala jin abin da Mother ta ce. Bayani Mother taci gaba dayi mata cike da ƙwarewa ta ɗora da faɗin. "Kina jin alamun ya dawo, ko babu abin da zai miki kije wajan shi kice kanki ke ciwo ko ya koya miki karatu, zan zuba miki kayan amfani masu kyau ki tabbatar kina using dasu amfani kinji?" "Zan yi ai, amma dai ba zata ƙwace mijina ba ko?" Mother ta haɗiye dryar data zo mata ta ce "Akan me? Idan kina yin abin da nace bata isa ta ƙwace miji ba, amma idan bakya yi uhm ko ganin shi kin dai na yi, yawwa sai gaisuwa kullum da safe kije ki gaishe sa, da yamma haka da kuma daddare, akwai lokacin da yake ciwon kai bai azabar zafi ganin shi har ɗauke yake ya zama kamar makaho, zan faɗa miki abin da za ki yi idan ciwon ya tashi, yanzu maza jeki gama aikin ki za kuje a gyara miki wannan gashin kan" Halisa ta miƙe tsaye kanta a ƙasa ta ce. "Na gode" "is nothing jeki daughter" sai da taje bakin ƙofa ta juya a hankali ta kalli Mother idanunta ya yi raurau da hawaye ta ce. "To yaushe zan faɗawa ina da miji? kuma yaushe zan fara dama masa fura" a ranta Mother ta ce "na shiga uku, wannan za ayi sirri da ita kam?" A file ta ce "zan faɗa miki ranar jeki" ta juya ta fita tana ayyana cewa da gaske dai Balarabe mijinta ne. Kai tsaye ɗakin Zahrah ta koma taci gaba da shirya mata kayan da zata tafi Madina dasu, zuciyarta cike da tunanin maganganun da Mother ta faɗa mata. Ta sauke ajjiyar zuciya a fili ta ce "Wallahi kyakkyawa da shi, Allah ya sa na zama kamar shi" ta faɗa tana taɓa fuskarta sai kuma ta miƙe da sauri tana nufar inda mirror yake, a hankali ta shiga ƙarewa kanta kallo, bata hango nata kyan zallar kyan da Rabbil izzati ya yi wa Yaa Sheikh idanunta ke hangowa. Tsaye tayi a bakin ƙofar da zata kaita parlourn Yaa Sheikh tun a nan kuma ta gane Yaa Sheikh daban yake a gidan, tsarin shi da yadda yake tafiyar da rayuwar shi, bata taɓa shakkar tsayawa gaban namiji ba, amma a yanzu tsoro da fargabar tsayawa gaban Yaa Sheikh da yadda kaifin idanun shi ke tasiri a zuciyarta sun gama cika Zahrah. "No Zahrah Aliyu mijinki ne, ki koyi zama da shi kafin ki fara juya rayuwar shi tamkar waina a tanda, dole ragamar rayuwar shi ta dawo tafin hannunki" wata zuciyar ta shiga gargaɗin haka, jikinta ta kalla tsaf duk da kasancewar ciki ne jikinta amma ƙirjinta yana kwance ya manne da fata, ita kalar halittar ce ko kuma garin yawan ta zubar aka gama lalata halittar da Ubangiji ya yi mata wacce kuma iskancin kawai ta sani sam bata san tsaunin da zata hau tabi ba, zuwa tubalin da zai gyara mata garkuwar jikinta. Ta tura ƙofar a hankali ƙamshin air-con da wani air freshener sune suka daki hancinta, shigar ta parlourn ya yi daidai da sautin karatun Yaa Sheikh dake ratsa cikin wajan har ya kawowa kunnenta farmaki. Yana zaune saman kujera ya ɗora farar ƙafarsa akan table idanunsa rufe a haka yake motsa bakinsa yana karatun cikin baiwar da Ubangiji ya bashi ya sahale masa yin karatun ba tare da harɗewar harshe ba.. Zahrah ta bi farar Jallabiyar dake jikinsa da kyau da kyau, zuwa kansa dake rufe hirami hannunsa guda ɗaya riƙe da carbi yana ja. Ta nemi wajan a kujerar dake kusa da shi ta zauna tana fari da idanu tare da juya jiki amma ta kasa yi masa magana balle gaisuwa. A jikinsa yaji ana kallon shi bambancin ƙamshin turaren da bai taɓa ji a gidan yasa ya fahimci ko waye ba ɗan gidan bane. Zahrah ta gyara murya ta ce. "My Excellency" "Shhhh" Yaa Sheikh ya furta a ran shi gaba ɗaya murya ko a maza bai taɓa jin mai amonta ba. Ganin ya yi shiru ta ɗauka ko bai ji mai tace bane?. "Daman nace bari nazo muga juna muyi hirar ku mintuna biyar ne kafin mu tafi gidanmu" still shiru ya yi mata, ta miƙe tsaye cike da kwarkwasa ta ƙarasa har zuwa inda yake tare da zama kan armchair ta saka hannu ta shafi fuskar shi kaɗan zuwa dugun gemun shi ta ce. "You're just quiet, but I know you hear what I'm saying" a wannan lokacin Yaa Sheikh ya ɗauka gangar jikinsa zata ƙaryata zuciyarsa, amma sai yaga abin ya zama diro, ya ƙara tabbatarwa lallai to da gaske bashi da cikakkiyar lafiya irin ta cikakkun maza, mace ƴar 32 tazo har inda take suyi very close da juna amma ko tsigar jikin shi bai ji ta motsa ba, balle ya yi zaton zai ji abin da Khalil ke masa surutu akai. Zahrah ta kai hannu zata ƙara jan gemun shi ya buɗe narkakkun idanunsa na mai kama da mai jin barci. He didn't give her a full look, because looking at people is not his style. Bai sake kallonta ba ya miƙe tsaye yana goya hannunsa a baya, ya nufi bedroom ɗinsa, Zahrah ta ce "Amma dai ni matarka ce ka sani?" Ya tsaya cak ba tare daya juya zuwa gare ta ba, kamar zai magana sai kuma ya fasa ya shige cikin bedroom ɗin, Zahrah tabi bayan shi da kallo me hakan yake nufi? Ta ɗauka zuwanta gare shi zai nuna wata buƙuwa ta miji ga matar shi sai kuma taga saɓanin haka. Ta juya ta sauri Dr A'isha dake Main parlour tabi Zahrah da kallo wato halitta kala-kala ce, ita bayan shekaru da zubin halittar jikinta har wani tumbi take dashi kamar namiji?. A fili Dr A'isha ta ce "Allah ya kyauta" tana faɗin hakan ta miƙe zuwa bedroom ɗin Mother itama a yau take son shigewa gidan mijinta. Zahrah na shiga bedroom ɗinta ta saka ƙafa ta murje yatsun Halisa cikin faɗa ta ce "ke kam wacce jakar yarinya ce? kina ganin mutum ba zaki matsa daga hanya ba?" Halisa da idanunta yayi jaa sbd zafin da yatsun suke mata, ta kalli Zahrah ta ce "Kiyi haƙuri" ta saka hannu ta ɗauke Halisa da mari ta ce "haƙurin uwarki? Ni dai na shiga ban ɗauka fulani mahaukatan gaske bane sai yanzu" gigicewar da Halisa tayi yasa ko gabanta bata iya gani, ba a taɓa yi mata mari da tafkeken hannu kamar na maza irin wannan ba. Ruɗewar da tayi yasa ta nufi wata ƙofa a tunaninta part ɗin su Maimoon ne, tana fita taci karo da mutum a hanyar zuwa swimming pool. El-bashir yaja baya da sauri yana kallon farar kyakkyawar yarinyar data fito hannunta a fuska tana shassheƙar kuka, ya taɓe baki yana ƙoƙarin shigewa Halisa tayi saurin kama hannunsa cikin matsanancin kuka ta ce. "Hamma fuskata zata cire wayyo Dadata fuskata ka taimaka mini" sai murza fuskar take da hannunta guda ɗaya, ɗaya kuma ta riƙe hannun El-bashir da shi. Hannunsa ya sanya zuwa hannunta dake fuskarta cikin ƙasa da murya ya ce "Sorry" ya faɗi hakan yana ɗauke hannunta. Cikin daƙiƙo ya nemi ji da ganinsa ya rasa, tunaninsa ya tsaya cak, ya zama kamar wani stateu yana ganin tarin kamanni amma bai taɓa cin karo da zallar kama irin ta yau ba. Hannunsa na rawa ya kama fuskar Halisa da kyau yana ƙare wa hukuncin Rabbil izzati ido, ita dai kuka take sosai ba ƙaramin gigita marin ya yi ba. El-bashir ya sauke numfashi yana daidaita nutsuwarsa tare da haɗiye mamakinsa, ko ita ce yarinyar da Khalil ke bashi labari?. Ya shiga goge mata hawayen fuska tare da faɗin "ke dawa? Wace ke? Mene sunanki?" Ya jera mata tambayoyin. Halisa ta marairaice fuska tare da shagwaɓewa ta zama wata narkakkiyya hannunta cikin baki alamar shagwaɓarta a zahirance take bata ɓoyewa. "Uhm magana nake" tai saurin ɗaga kanta zuwa fuskar shi, baki da hanci ta saka ta kasa cewa komai El-bashir ya ƙifta mata idanu tare da ware su ya ce "Keee. "Wallahi kama muke, kai ma kasanni ya naga fuskarmu iya ɗaya?" Ta ƙare maganar tana ƙoƙarin taɓa fuskar shi domin tabbatarwa. El-bashir ya haɗe fuska ya ce "Bani amsa? Wace ke?" Ta tura baki gaba ta ce "Sunana Halisa Danejo Rome, kuma ni matar Balarabe ce" El-bashir ya ware idanu ya ce "What are you married? Waye Balarabe?" Ta ce "Ace kada na faɗawa kowa sai lokaci ya yi amma dai ni zan dinga yiwa Matar Yaa Sheikh aiki, kuma ance jibi zamu tafi ko'ina ne, haka.....," "Heyyy will you shut up your mouth caaaaa haba" ta tura baki gaba fuska duk a shagwaɓe taƙi cewa komai. Ya gyara tsaiwa ya ce "Oh Halisa, dake Yaa Sheikh zai tafi ko?" Tayi saurin kallon shi ta ce "Eh" ya ce "Ok good, daman shi ya aike ni yanzu, kuma ke ya ce na bawa aikin domin ya yarda da hankalinki" tamkar wacce bata yarda da maganar El-bashir ba haka take kallon shi, wanne aike? daman yana sane da ita kenan yana son ta shi ma?.. "Riƙe wannan, ya ce ki ɓoye wajanki har sai kunje Madina, maganin shi ne, zaki zuba masa a cikin shayi ko abinci, kada ki bar kowa yasan da abin a wajanki, idan ba haka ba zai kureki daga gidan shi kinji?" Ta ɗaga kai ta ce "Amma bari na bawa Mother ajjiya ko?" Ta faɗa zata juya ya yi saurin riƙe hannunta ya ce.. "Ai har Mother ba a so tasan da maganin a wajanki, ki zama mace mai sirri ki tabbatar kin zuba masa, idan ba haka mutuwa zai gaba ɗaya" ta shiga girgiza kai tsoro da fargabar abin da El-bashir ɗin ke faɗa suka firgitar da Halisa ta ce "Wallahi ba zai mutu ba, ba zan barshi ya mutu ba, ni da kai na zan zuba masa maganin" wani irin kyakkyawan murmushi mara sauti El-bashir ya yi kafin ya ce "Good girl" ganin ya yi gaba ta ce. "Kai ya sunanka to?" "Ki ce El" ya faɗa a taƙaice tayi saurin faɗi "Ban iya faɗa ba, tunda muna kama ɗaya zan dinga cewa Hamma ka yarda?" Ya tsaya tare da juyawa wani abu nayi masa yawo akan abubuwa da yawa, kalmar kamannin data faɗa suka ƙara dagula masa lissafi. Ya jinjina mata kai tare sakar mata murmushi. Halisa bata da riƙo lokaci guda ta mance marin da Zahrah tayi mata. Cikin sauri ta ɓoye maganin da El-bashir ya bata tare da juyawa tabar wajan. Barinta wajan ya sanya Yaa Sheikh sauke numfashi tare da zame idanun shi daga saitin wajan da Halisa da El-bashir suka tsaya, yana mai ɗan girgiza kai tare da ya motsa fuska. Father ya kalli Yaa Sheikh ya ce "Kaje ka duba visa ɗin Zahrah da Yarinyar da zatai mata aikin" Yaa Sheikh ya jinjina kai alamar "to" tare da miƙewa sai da ya je bakin ƙofa Father ya ce "Ka shiga part ɗin nata, da kanka ba aike ba kace ta shirya kuje tare, matarka ce saɓa mata tamkar zaɓa mini ne, kai ne mai auren amma ni ne mai zartar da hukunci ko da wasa ka sake Zahrah ta kawo ƙararka za kaga yarda za mu yi dakai Aliyu, kaji tsoran Allah kai Malami ne kasan hakƙin aure da sauke nauyin miji ga mata, kada ka yarda saboda baka son ta kace zaka tauye hakƙinta wallahi wallahi Allah Aliyu akan aurenka da Zahrah sai nayi maka baki" Yaa Sheikh ya juya da sauri ya kalli Father kalmar shi ta ƙarshe ta daki zuciyar Yaa Sheikh, kansa a ƙasa ya nufi wajan Father yana zuwa ya zube a wajan ƙafafuwan Father, cikin ƙasa da murya mai tarin nutsuwa da Ilham yana mai ɓoye abin da yake ransa a kame ya ce. "Kada ka aibata ni Abbi, zan riƙeta, ka saka albarka a kai na a karo na farko na rayuwata Father" Father ya kalli Yaa Sheikh kafin ya ce "Kaje Allah ya yi maka Albarka" Yaa Sheikh ya kifa kansa a ƙafar Father farin ciki ko baƙin ciki zai ji? Yau Father ya saka masa albarka dalilin Zahrah?. "Ka tashi kaje nace, kuɗi ne kama fini shi me zan maka? Ko akwai abin da ka ke buƙata?" Yaa Sheikh ya yi shiru can kuma ya miƙe tsaye tare da yin waje. A hankali ya haɗu da Maimoon da Halisa shi sam ba zai ce yaga Halisa ba domin direct idanunsa ya sauka akan Maimoon ɗin. Part ɗin Zahrah ya nufa lokaci wata farar riga ce a jikinta iya gwiwa waya riƙe a hannunta ta ce "No Deen ka bari muyi 1week a Madina sai ka zo ɗin? I will arrange a day when we can meet, I don't want to be recognized....," Ƙamshin Roja da hancinta ya shaƙa yasa tayi saurin ajjiye wayar tana duban door way, idanunta ya sauka akan Yaa Sheikh dake tsaye bakin ƙofar yaƙi shigowa ciki. Zahrah duk ga ruɗe bata tsammaci ganin shi a yanzu ba, ta sakko tana yin murmushi tare da girgiza jiki ta ƙarasu tana faɗin "My Excellency" Yaa Sheikh ya duba ta da kyau, har zai larabci ya tuna ba lallai tana ji ba, shi kuma he's not interested akan english. "Ki saman waje, mota" ya faɗa a taƙaice cikin rarrabe murya. Bai aune ba yaji Zahrah ta shige jikinsa tare da rungome shi. Bakinsa na rawa cikin rashin ya ce "Asstagafirullah, Allah na tuba" ya faɗa yana zame jikinsa tare da barin part ɗin da sauri. Yana zaune a bayan mota idanun shi rufe yana ta Asstagafirullah akan rungumar da zara tai masa, ba wani sauyi a jikinsa amma that is forbidden. Umar-khan ya ɓoyewa Zahrah bayan mota har zata shiga sai kuma ta tsaya ganin kamar maca ce a gaban motar, ta tsaya tana faɗin "Umar-khan wace wannan a gaban motar mijina?" Umar-khan ya kalli Halisa wacce take sanye da wata Marron ɗin turkish Abaya wacce Mother ta bata, Maimoon kuma tai mata rolling vail ɗin abaya a fuskarta, ƙaramar round face ta fito sosai farinta ya ƙara bayyana, gashin idanun nan lub zara-zara dasu idan ba magana tai ba, ba zaka taɓa cewa ƴat fillon Rugar Rome bace, ta kame kanta sosai bisa gargaɗin Mother. Umar-khan ya danne dariyar dake cin sa ya ce "Motar mijinku dai" "me kace?" Cewar Zahrah ya ce "cewa nayi baki gane wace ba?" Ta girgiza ta ce "Idan na gane wace mene amfanin tambayar?" Yaa Sheikh dai duk abin da suke cewa yana jinsu bai magana ba. Umar-khan ya ce "Ikon Allah, Ƴar fillo ce fa? Mai aikinki ina nufin Halisa ce a gaban motar garkuwarta" wani irin bugawa ƙirjin Zahrah tayi ta ƙara leƙa motar Halisa ta sakar mata wani cute smile ta ce "Laa Anti ni ce fa, mai aikin ki Halisa Danejo Rome" wani jiri ya ɗebi Zahrah tayi saurin riƙe motar a cikin ranta ta ce "Da sake wallahi ba zai yiwu ba.... _IDAN BA KE it's paid book... ₦500 via 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman fidelity bank shaidar biya 08119237616. If you read for free😂🤷🏾‍♀️_ Umar-khan ya katse mata tunani da faɗin "Ki shiga muje" Zahrah ta ɗan basar tare da faɗin "Dake ban kula da kyau bane, amma ita me za ta je yi?" Ta tambaya idanunta akan Halisa wacce wayar Umar-khan ke hannunta sai latsa ko'ina take ba tare data san ta kanta ba. Umar-khan ya ce "Ayya ko kin manta Glasses ɗin naki ne, ita za ai mata visa ne" baƙin cikin maganar da umar-khan ya yarfa mata ya sanya ta kasa cewa komai ta shiga cikin motar tana sauke numfashi sbd ƙamshin Roja data shaƙa ga daddaɗan freshener dake tashi a motar. Tana shiga Umar-khan shi ma ya shiga a hankali ya yi wa motar key sbd Yaa Sheikh baya son gudu da yawa, gatekeeper ya buɗe gate suka nufi wajan da za ai photo a haɗa musu visa. Bayan sun yi nisa akan titi Umar-khan ya juya ya kalli Halisa ya ce "Madam idan kika latata mini waya mijinki zai biya" Zahrah ta ɗago kai tare da duban saitin Umar-khan, bata fahimcin zancen ba domin ita ta ɗauka waya yake. Halisa ta buɗe fararen daidaiton haƙoranta masu kyau ta ce "To ai baya da kuɗi" "Injiwa?" Umar-khan ya tambaya idanunsa akan titi, ta ɗan turo baki tare da watsa hannu alamar bata sani ba, ya girgiza kai ya ce "Shi ke da kuɗi, hakan ne ma ya sa ban ƙwace wayata ba, albarkacin ki sai a siya mini iphone 13max pro Matar Malam na makka da madina" taja lulu eye's ɗinta lumshe wanda hakan ya zama jiki a gareta, magana zarar bunu cikin rashin sani da kuma sabo da surutu yasa Halisa faɗin. "Kai ma kasan ayi mini aure ne? Ko na faɗa maka yanzu" Umar-khan ya tuntsire da dariya sosai yana faɗin "Ina zan sani ƴar fillo? Kuma......," Yaa Sheikh da tun ɗazo idanunsa yake a rufe ya buɗe su a hankali kai tsaye ganinsa ya sauka akan ƙaramin bakinta wanda yake motsawa a hankali ta cikin madubin motar. Yaa Sheikh ya ɗauke idanunsa da sauri yana mai ɗan dafe kai cikin nutsuwa da kamewa wacce ta zauna a jikinsa ya buɗe baki da ƙyar ya ce. "Ka kula, Umar-khan" "Ok Yaa Lee" cewar Umar-khan with so much respect. Zahrah ta matsa kaɗan kusa da Yaa Sheikh tare da ɗora hannunta a saman na shi. "Asstagafirullah, Allah na tuba" ya furta cikin ranshi a zahiri bai motsa ba, sai ma rufe idanunsa da ya yi kamar mai barci. Zahrah taja gemunsa wanda yake matuƙar ɗaukan hankalinta ta ce "I love you My Excellency" baki ta miƙa zata sumbaci gefen fuskar shi, tari ya turnuƙe Halisa a kiɗime Umar-khan ya ƙara slow da driving ɗin ya ce. "Sannu mene ya sameki, are you sick? Baki da lafiya ne?" Ganin tarin ya kasa tsayawa yasa Umar-khan faɗin "Yaa Sheikh ko zaka taimaka mata da ruwan wajanka, babu raguwar a motar" bai ɗago ba, ba kuma zakai tunanin da shi ake maganar ba.. "Sannu, sannu" ya ƙara jerawa Halisa cike da tausayi. Yana driving ya kalli Yaa Sheikh ta madubi da kuma Zahrah wacce takaicin Halisa ya cika ta duk ta hana su sakat tasu a lokaci na farko ta bawa Yaa Sheikh ɗin kyakkyawar sumbata wacce zata ruguza shi tun yanzu, tasan ba lallai ya iya riƙe kansa ba, dole ya zo gareta. Umar ya ɗauke idanunsa yana faɗin "Yaa Sheikh Please ta wahala da yawa" ya ajjiye carbin hannunsa tare da ɗago kansa kamar mai nazari ya shiga kallon Umar-khan, not looking at her place ya kame kansa murya kamar anyi forcing nasa na magana ya ce.. "Stop the car" Yasan idan har Yaa Sheikh ya buɗe baki ya yi magana to yana nufin abin da ya faɗa ne har cikin ran shi a hankali ya yi parking motar zuwa gefen titi. Zahrah ta kalli Yaa Sheikh ta ce "Daman bai kamata mu shiga mota ɗaya dasu ba, ga wannan shegiyar yarinyar ƴar fillo, kawai su nemi abin hawa i can drive us kaji My Excellency" ya ɗan kalleta kaɗan ta wani kashe masa idanu tana shirin kama hannun shi ya fita daga cikin motar, yana fitowa ya shiga takawa a gefen titin hannunsa goye a bayansa, ganin yadda ya tsaya waje guda kansa a ƙasa yada Umar-khan fita yana tunanin ko lafiya? Ya nufi wajan shi tare da faɗin "Yaa Lee lafiya?" Ya ɗago kai ya kalli Umar-khan, mamaki ya kama Umar ganin yadda goshin Yaa Sheikh yake fitar da zufa ya jiƙe sosai da gumi. Bai magana ba ya miƙa hannunsa tare da amsar key car ɗin hannun Umar-khan, da hannu ya nunawa Umar-khan bayan motar alamar ya shiga ciki ya zauna, mamaki ya kashe Umar a tsaye yau Yaa Sheikh zai yi driving ɗin mutane a mota bana shi ɗaya ba? Me hakan yake nufi. Zahrah dake bayan mota tana jiran ace Halisa ta fita ita kuma ta dawo gaba ita da mijinta su tafi iya su biyu sai gani tayi Umar-khan ya buɗe bayan motar ya shigo, mamakin sauyin al'amarin cikin ƙaramin lokaci ya hanata magana. Yaa Sheikh ya sanya tattausan farin hannunsa mai ɗauke da suma lub ya buɗe murfin gaban motar, ƙafarsa ta hannun dama ya fara shigarwa kana ya shiga ya zauna baki ɗaya. "Ban gane wani ƙaton namijin ya zauna dani ba, bayan ina matarka?" Babu wanda ya bata amsa sai ji tayi ya yi wa motar key. Murmushi kawai Umar ya yi yana ayyana wani abu a ran shi.. Yaa Sheikh ya yi tunanin zata cika shi da surutu kamar yadda ta cika Umar-khan da hayaniya mara tushe, amma sai yaga saɓanin haka bawai kallonta ya yi ba, ya fahimci hakanne ta madubin motar. Kanta a ƙasa idanunta ya yi masifar jaaa jikinta na ɗan rawa a hankali, saukar sautin ƙira'ar daya cika motar har ya kawo zuwa kunnenta yasa ta sauke numfashi mai ƙarfi jikinta ya saki kafin su ƙarasa barci ya ɗauke ta sai ajjiyar zuciya take saukewa. Bayan magrib Mother na zaune a parlour ita da Jadda. Jadda ta kaɗa ƙafa ta ce "Amma dai Allah ya isa, an munafurce ni ko waye kuma yaje shi da Allah, shi yasa yadda zai yi dashi danni ba zan iya komai ba" "lafiya dai Jadda?" A fusace Jadda ta ce "Ina batun lafiya Maryam? Ashe haka aka haɗawa Uwar matar can lefe hadda na Allah ya isa fa? Ni dai babu ruwana na kusa zare hannuna daga al'amarin Aliyu ko na ɗaga masa nonon kawai tun da nayi niyya" Mother tai murmushi kawai tana jiran zuwan Maimoon. Zahrah ta ƙarasu parlourn sanye da ƙaton hijabi irin ta Allah ɗin nan nace, ta zauna tana faɗin "Sannu da hutawa Mother" a taƙaice ta ce "Yawwa" ta juya kan Jadda wacce ta haɗe rai sosai ta ce "Barka da gida" Jadda tai mitsi mitsi da idanu ta ce "Allah ya isa, Allah ya isa wallahi ban yafe ba" Jadda ta faɗa tana kallon Mother tare da fashewa da kuka ta ce "To me nayi mata da zata gaishe ni? Sbd Allah ina ruwanta dani ko nace ina buƙatar gaisuwarta" Zahrah bata ƙara bi takan Jadda ba ta kalli Mother tana sunkuyar da kanta ƙasa ta ce "Daman zan mayar da Yarinyar nan ne gida" Mother ta kalli Maimoon dake shigowa tana faɗin "Wacce yarinya?" Zahrah cike da nuna cewa tafi kowa iya ladabi ta ce "Ƴar fillo, zan tura ta gida" Jadda ta miƙe ta ce "Wannan farar yarinyar kyakkyawa mai zubin labarawa kamar ita tai kanta? Idan kin isa Allah ya tsine" Mother tai murmushi ta ce "Me ya sa?" Zahrah tai ƙasa da kai ta ce "Daman Mimi tace na dawo da ita gida, da ƙyar aka yarda aka bani ita kuma tana karatu" Mother ta karkaɗa ƙafa ba tare da ta ce komai ba ta danna wayarta babu jimawa aka ɗaga wayar ta ce "Umar-khan, kayi waya da mutananku na can Madina, a fara nemawa Halisa gurbin karatu a matakin ajin farko na secondary" gaban Zahrah ya faɗi, ganin how smart she had. Bayan gama wayar Mother ta ce "kada ki damu Zahrah, I'll talk to your mom, ki fara shirye-shiryen tafiya" ta miƙe tana faɗin "Na gode Mother" da sauri ta shige part ɗinta. Tana zuwa ta rufe ƙofa tare da cire hijabin jikinta inners ne kawai a jikinta cikin faɗa ta ɗaga wayarta ta ce "haba Deen wai kai wanne irin maye ne?" Deen dake cikin wayar ya ce "Muna vedio call kika tafi kin barni cikin wani hali Beb" cikin ɗaga murya ta ce "Jarbabbe duk kai ka koya mini jaraba kwana nake bana barci, nifa batun tafiya da yarinyar nan ne na fasa,ina hangowa kai na matsala gaba ɗaya ji nake kamar wani abu zai faru idan na tafi da ita" Deen ya numfasa ta wayar yana faɗin. "Ya kukai kuma me kike so ayi?" Ta faɗa masa duk yadda sukai da Mother ya ce "Uhm Sirikarki Educated ce kuma Barrister, ta fiki tunani da hankali idan kina wannan haukan da wuri za a gano shirinmu, dole ki yafe ɗan cikin ki a gidan Yaa Sheikh, shi ne zai bamu damar cimma burinmu ya zama dole ki samu kusanci dashi ina nufin ki samu mu'amalar aure da shi, hakan shi ne hanyar farko, ai ana haihuwa bakwaini ki san duk yadda kikai kina zuwa Madina ku samu daidaito Zahrah, kece madafin cimma burina na faɗa miki irin cin amana da zaluntar da akai mini" ta sauke numfashi tare da ta ce. "It's ok Deen, na maka al'ƙawarin ƙwato maka hakƙin ka, ina son ka, burina ka tsaya dani banda wata macen" ya yi murmushi ta wayar ya ce. "Zahrah kenan, kina so na kullum kike cewa, amma son da kikewa Yaa Sheikh yafi son da ki ke mini, duk da hakan me ya sa kika amince zaki cutar da shi bayan kina son shi?". Zahrah ta ce "kada ka damu wannan sirri na ne, sunna or later zaka sani, Yaa Sheikh manufa ne, kai kuma makami ko wanne nada amfani, amma dole muyi wani abu akan Halisa" ya ja tsaki a ran shi sam bai ga abin damuwa akan wata Halisa ba. "A kashe ta? Ko kuma a haukata ta?". Zahrah ta ce "Hauka kuma, zan yi tunani akan haka, muje vedio call na nuna maka wani abu mai yaji" dry ya yi ya ce "Zahrah bana son ganin wannan shafaffen ƙirjin naki, wanda yake kwance har ciki serious tun kafin Yaa Sheikh yasan wace ke ya kamata ki nemi magani" maganar Deen ta daki zuciyar Zahrah ta kashe wayar rai ɓace. Khalil ya ce "Mother daman zuwa nayi nai miki sallama, yanzu zamu tafi airport" ta ce "To sai yaushe kuma" ya shafa kai ya ce "Ina tunanin sai bikin Maimoon ko idan matar Yaa Sheikh ta haihu". "Ikon Allah daga aure sai haihuwa, Maimoon kam ai da sauran ta" ya ƙara shafa kai idanunsa akan Maimoon dake tura masa baki. "To Allah ya tsare, a gaida Oum Juwairah" ya miƙe yana faɗin "za taji ai tana gidan Abba Hakimi" kafin Mother tai magana idanun Khalil ya sauka akan yatsun Halisa da mmkin yake kallon Zoben dake maƙale a yatsar zai magana El ya ce "Zan tafi ni dai" ya ce "kafi jirgin sama tashi" Halisa ta kalli El suka haɗa idanu sun jima suna kallon juna kafin tai ƙasa da kanta, tun jiya da suka je visa ta daina walwala taƙi kula kowa surutun ya rago sosai. El-bashir ya fita Khalil ya ce "Ƴar tsuhuwa Maimunatu zo ki kaiwa Matar Yaa Sheikh gift ɗinta" ta miƙe kafin ta ƙarasa yayi waje, tana zuwa corridor taji an jawota zuwa jikin mutum, a tsorace ta buɗe baki zatai ihu Khalil ya yi saurin rufe bakin ya ce "Haba Amaryata yaushe za mu yi auren ne?" Ta ce "Allah ya sauwaƙe na auri me mata ni ban so" ya ce "Ni kuma na miki al'ƙawarin wallahi sai kin aureni na haɗa mata biyu a cikin masarauta" tai masa shiru, tun Maimoon na ƙarama yake mutuwar son yarinyar. Ya ɗan ƙara matseta a jikinsa daidai kunnanta ya ce "I love you" yana faɗin hakan ya saketa yana damƙa wani box ya ce "For our In-law, and this na ki ne" ya ƙara damƙa mata wani box ɗin ya juya da sauri tare da ficewa. Washegari gari da safe Yaa Sheikh ne yake fitowa a hankali daga part ɗin sa, yana sanye da jallabiya fara tas ƙafarsa sanye cikin slippers, hannunsa goye a bayansa ya ɗan tsaya a parlourn sbd shiru da yaji juyawa ya yi idanunsa ya sauka akanta tana ƙawance akan duguwar kujera ta kifa kanta a hannunta kamar mai barci, jar rigar dake jikinta ta ƙara fidda tsarin jikinta, madaidaitan hips ɗinta sun bayyana a fili ya ɗauke idanu yana ya mutsa fuska, remote ya ɗauka tare da kunna karatun Alkur'ani ya danna ƙara ya cika gidan. A firgice Halisa ta miƙe tsaye jikinta duk rawa yake, jajayen idanun da kusan kwana biyu suka ƙi dawowa dade ta buɗe su akan Yaa Sheikh dake zaune akan kujera yana ɗan jan gemunsa. Ba tare da ta ce komai ba sbd kanta dake juyawa da sauri ta nufi hanyar da zata fitar da ita daga cikin parlourn wacce kai tsaye kuma zata kaita har waje bakin hanya, Allah Allah take ta fita sbd karatun dake gigita mata lissafi kamar zai fasa kanta. Tana zuwa daidai inda yake zata gilma ta shige ya sanya farin hannunsa mai laushi ya damƙota tare da dawo da ita baya... Paid book It's 500 Via 08119237616 Dawo da ita baya ya yi tare da zaunar da ita a ƙasa wajan ƙafafuwansa, yana mai sakin hannunta da sauri. Tamkar wacce take gane abin da shirun nasa yake nufi haka ta zauna waje guda taƙi yarda ta ɗago kanta kamar yadda yasu sbd ya fahimci abin da yake tunani. Yasan har abada indai tana cikin wannan yanayin to ba zata taɓa kallon cikin ƙwayar idanun shi ba, sai dai idan marasa kunya ne suke tattare da ita.. hannunsa daya riƙe nata ya dunƙule waje guda a haka Mother ta fito sanye da duguwar riga ganin Yaa Sheikh a main parlour da sassafe ya bata mamaki, idanunta akan shi kana ta zame zuwa kan Halisa dake zaune kusa da ƙafar shi ta dama. Da mmki tana zama ta ce "lafiya dai Haydar? fitowa da safiya, Halisa fa?" Ta tambaya tana kallon Halisa elxty yadda Yaa Sheikh yake abu lokacin yana yaro haka yanzu Halisa tayi. Ya buɗe idanun shi yana ajjiye carbin hannunsa cikin kamilalliyyar muryarsa ya ce. "Mun tashi lafiya Mother?" Ta saki murmushi tana faɗin "Allahamdulillah Haydar, Halisa fa?" Ya ƙara ware idanu yana kwaɓe fuska alamar tambayar batai masa ba, kamar zai share ya numfasa kaɗan ya ce. "Wafa?" Mother ta ce "Meya fito da Halisa da wannan safiyar kuma gata kusa dakai kamar bata da lafiya?" Ya jima yana tunanin amsar da zai bawa Mother baya ƙarya baya kuma faɗin abin da bashi da tabbacin sai ya yi shiru Mother ta miƙe tsaye tana faɗin. "Black tea ko? Bari na kawo maka,ka jira ina son magana dakai" ya jinjina kai. Mother na tafiya ya juya kansa zuwa inda Halisa take zaune a hankali ya miƙa tattausan farin hannunsa mai taushi ya ɗora saman goshinta. Zabura tayi zata gudu ya riƙe kan da kyau, sosai yaji kanta ya ɗauki zafi yana harbawa. Ya jima riƙe da kan yana ɗan murza babban yatsar shi a tsakiyar goshinta kafin yaji taja duguwar ajjiyar zuciya tare buɗe idanu. Ya zame hannun shi daga kan, itama ta kasa kallon shi ta kuma kasa motsawa. Kamar wacce aka tsikara haka ta miƙe jiri na ɗaukanta ta nufi part ɗin su Maimoon domin anan ne take kwana yanzu. Barin ta parlourn ya yi daidai da dawowar Mother daga kitchen, bayan ta zauna tare da tsiyayawa Yaa Sheikh black tea ɗin tare da 2 spoon na honey yana tiriri ta miƙa masa. A nutse yake sha ganin ya kusa shanyewa ta kalle shi ta ce "You need more? with chips or kunnu?" Ya jinjina kai alamar "Eh" kitchen ta shiga not too long ta dawo ɗauke da tray, Spoon ɗin ya ɗauka ya fara cakar chips yana taunawa a hankali, haka kawai jikin shi ya bashi ana kallon shi gently ya ɗago kai da sauri ta koma ciki tana dafe ƙirji, ya girgiza kai domin idanunsa sun riga da sun ganta tuni. Mamakin cin abincin na Yaa Sheikh yau ya kama Mother tana zaune tasan ko tayi magana ba zai fahimta ba, sai da ya goge baki da tissue kana ya zaro Aswaq daga cikin aljihu ya fara yi. "Ina son yin magana da kai ta fahimta Aliyu" ya maida hankali sosai akan Mother ta gyara zama ta ce. "Halisa bata da kowa, bata da wanda kareta ya kuma ja ragamar rayuwar ta, ko da baka san yaya akai tazo gidan nan ba, amma ka tuna cewa matar kace, ban damu da kai mata kallon mata ba, wannan deal kai da Abbanka, amma ka zama garkuwa a gare ta don Allah don Annabi ba danni ba Aliyu" ta haɗe hannaye biyu alamar roƙo a gare shi, a taushashe ya kama hannun Mother duk biyun, ya jima kafin ya ce. "Fiye da yadda kike zato, al'ƙawari ne" tai murmushi ta ce "Allah ya yi maka Albarka Malam, tare da matanka, kayi ƙoƙarin sauke hakƙin ko wacce mace a cikinsu, kada ka tauye na wani ko fifitawa" ya jinjina mata kai yana miƙewa tsaye. Kai tsaye bedroom ɗinsa ya nufa tare da ɗaukan system ya shige Library ɗinsa, wasu muhimman ayyuka ne dashi gashi yana son tattara komai wajan Saif-wazir tunda da Umar-khan zasu koma, ɗalibai na can suna jiran shi da gidan marayunsa. Misalin 10 kowa yana zaune akan dinning ana dinner Father ya ajjiye Spoon ɗin hannunsa ya kalli Zahrah ya ce "Aliyu ya faɗa miki 12 jirginku zai tashi ko?" Ganin Idanun Mother yasa Zahrah faɗin "Eh Father, nama gama shirya kayana" Jadda ta fashe da kuka tana share majina da gefen zani ta ce "Ubangiji ya bawa Malam haƙuri, an haɗa shi da wacce tafi ƙarfin shi, na rantse uwata ta haifan ban taɓa ganin ƙatuwa budurwa irinta ba, an bashi sa'ar babar shi da kaɗan fa na girme mata, gaskiya dole Malam ya ƙara aure zan nemi Hakimi da kai na ai shela a sama masa mata ko cikin masarauta ne" gaban Zahrah ya faɗi sosai kishiya za ayi mata? To ai Yaa Sheikh shi da wata mace har abada,da ita zai ta rayuwa da daɗi ba daɗi,idan har tana raye babu wacce ta isa ta shigo cikin gidanta, ba zata taɓa haɗa Mijinta da wata ƴa mace ba. Father ya ce "Bayan auren da yake dashi?" Jadda ta ce "A'a zan maka Allah ya isa Aliyu, tun nazo gidanka kaji na kulaka? Nifa ba zan yarda Malam ya zauna da ɗirkekiyyar mace kamar durunar ruwa ba, ko ni bata ban sha'awa ba balle namiji, kana kallon ƙirjin kamar an zuba kwalta a titin gwammaja, dole ya auri ƴar ƙarama wacce zai mure ƙuruciyarta ai Alsulhu khair" bakin Halisa na rawa ta ce "To ai nima matar shi ce kuma ƴar ƙarama ce ni....," Kafin ta ƙarasa maganar Mother tayi saurin rufe mata baki, faɗan da Jadda kewa Father yasa babu wanda yaji maganar sai Maimoon. Baƙin ciki ya cika Zahrah jin daɗinta ɗaya babu Yaa Sheikh a wajan. Cikin makirci Zahrah ta fashe da kuka tana zubewa gaban Jadda ta ce "Don Allah kiyi haƙuri Jadda, kada ki rabani da mijina yana so na, ina son shi" Jadda tai mitsi mitsi da idanu tana riƙe haɓa ta ce "Mai ƙarya aƙona shi a wuta, nifa na rarrashi Malam na bashi baki akan ya aureki da ƙyar sai dana zubar da hawaye, nace zanbi duniya kawai idan bai yarda da aurenki ba, shi ne zaki ce yana son ki?" Da sauri Zahrah ta nufi part ɗin ta, sbd gab take da yiwa Jadda rashin mutuncin wallahi. Jadda ta ce "To ai kaga nayi mata bayani cikin sauƙi,ta fahimta da faɗa nai mata sai ta ƙulla ce ni, ai Alsulhu khair" "Ai kam dai munga Sulhu, bamu sani ba ko zai zama alheri" cewar Auta Fattoumah. Jadda ta ce "A'a kowa ya yi ta kansa, bana shiga abin da bai shafan ba, amma fa na girgiza a bawa mutum auren sa'ar uwar shi?" Halisa ta ajjiye Spoon ɗin hannunta idanunta ya yi jajir kalmar.. _“Yana so na, ina son shi”_ ya shiga yi mata yawo a cikin kunne. Ta miƙe a hankali tare da nufar ɗakin su Maimoon. Tana zuwa Mother ta biyu bayanta.. Ta kasa kallon Mother bakinta kuma ya ƙiyin shiru ta ce. "To yaushe zan faɗawa kowa ina da aure kuma Malam ne mijina?" Mother ta girgiza kai ta ce "Ba yanzu ba, inda kika faɗawa wani to mun ɓata kuma zance Yaa Sheikh kada ya saki makaranta" Da sauri tana zare ido ta ce "A'a ba zan faɗa ba, amma zan dinga ce masa mijina ko? ko Baffa?" Mother ta rasa me zata ce, surutun yarinyar baya sarrafuwa idan har ya fito to dole ta furta.. "duk yadda kika gani, amma idan kika ce miji ai Zahrah zata gane, kice Abba Sheikh" bayani ta ƙara yi mata cike da hikima na zaman rayuwa, da kuma wasu muhimman abubuwa akan Yaa Sheikh ɗin. "Maza ta shi kije Maimoon ta ƙara yi miki saloon" ta miƙe tana cewa "To" sai da taje bakin ƙofa zata fita ta tsaya tare da kallon Mother ta ce. "Amma idan naje can Madina zan iya faɗawa kowa ayi mini aure ina da miji?" Mother ta tafe kai tare da faɗin "Na shiga uku".. Zahrah ce ke waya da Surry ta ce "Wallahi Surry ko da wasa aka bawa Yaa Sheikh auren wata sai na kasheta, ina da tsananin kishi akan abin da nake so, balle mutum kamar Yaa Sheikh wanda banyi tunanin zan same shi matsayin miji ba" Surry ta ce "Tab, sai ki san yadda ki kai kika tare da mijinki idan kuka tara zuri'a babu mai rabaki da shi ai" Zahrah ta ce "You're right jirginmu zai tashi, yama sunan maganin dake saka mutum feelings in 5 minutes?" Surry ta faɗa mata sunan maganin ta ɗora da faɗin "Amma dole Yaa Sheikh ya gane bake bace" murmushin mugunta Zahrah tayi tana girgiza kai ta ce "Idan kuma yana cikin maye fa?" Surry ta zare ido ta cikin wayar ta ce "Bugar dashi zaki? Kada ki cutar da ƴar mutane yafi ƙarfin ta ba" "Surayyerh kenan, na shige duk tunaninki, kada ki manta Zahrah Farouk nake, ita kuwa Zahrah ba mahaukaciya bace ta san me take, Ƴar fillo data gama aikinta zan aiwatar da burina a kanta gudun matsala" Zahrah tai wa Surry ba zata, gashi bata da hanyar da zata taiwa Halisa magana. "Do you want to just leave me alone now? these past few days have been a bother" "Okay bey" cewar Zahrah. Tana gama wayar Halisa ta shigo tai tsaye fuska a haɗe. "Oh su ƴar fillo an samu duniya, bari muje wannan farin na jikin ki sai na ɓatar da shi" ta tura baki gaba cikin surutu ta ce. "Ai farin daga Allah ne" Zahrah ta ce "magana ki kai?" Tai shiru ta kalleta da kyau ta ce.. "Ki gane baki da haɗi da dangin mijina, ke ƴar aikina ce, ki daina cusa kanki inda baki da mazauni ba zaki taɓa samun karɓuwa ba, saura ki faɗawa wani ke ba ƴar uwata bace kamar yadda nace" "Sai dai kishiya ba ƴar uwa ba" da sauri Zahrah ta ce "kika ce me?" Ta girgiza kai ta ce "Salati nayi" Ta ja tsaki tare da cewa "Get out jakar kawai" 11:00 Yaa Sheikh ya fito cikin wata haɗaɗɗiyar Alkyabba mai kyau da tsari, ya naɗa rawani wanda ya ƙara fidda haibarsa da cikar kamalar da yake da ita, fuska kame. Hannu goye abaya tare da carbi yana ja. Banda ƙamshin Roja babu abin da ke tashi a main parlour. "Allahu Akbar Allah ya baka haƙurin zama da uwar mata Malam, ni tsoro na ɗaya kada a dinga nunaka da baki ana ka mijin sa'ar babar shi" Zahrah data ƙarasu parlourn tai tsaye a gefen Yaa Sheikh ba tare data kula Jadda ba ta ce. "You look good My Excellency". A can bedroom Kuka sosai Halisa take sai rigima take ita kawai wajan Dada zata, da ƙyar Mother ta rarrasheta, ta zuba mata komai na buƙata cikin torelly bag ba tare da sanin Zahrah ba. Maimoon ta ce "Matar Yaa Lee ga gift inji Yarima Khalil" Mother ta ce "Gift?" "Eh, shi ya bani wai na bawa matar Yaa Sheikh, ni kuma kawai zan bawa Halisa" Mother ta amshi box ɗin ta buɗe, wani gold ring ne mai kyau sai ƙyalli yake, ta ce "Zan ajjiye waje na, hannunta akwai ring har biyu ya isa, Allah ya tsare ya ki yaye sai na kira waya Daughter" Halisa ta kalli Maimoon tana mata gwalo ta ce. "Yarinya na tafi gidan mijina, duk abin da ya faru zan ajjiye miki labari ko na dinga faɗawa Mother tana gaya miki" Mother ta ce "A'a na shiga uku bani a nan" Yaa Sheikh tuni ya shiga mota, shi kaɗai ne a baya Saif-wazir na driving.. Zahrah a motar Ishaq-Hakim ita da Halisa da Maimoon. Mother ta ce ba zai taje rakiya ba. Kai tsaye gidan Abba Hakimi suka nufa. Yaa Sheikh ne kawai ya shiga sbd babu lokaci, ya shige jikin Abba Hakimi yana sauke numfashi, rauninsa ya bayyana kasancewar yana jikin Abban nasa, a karo na farko ya riƙe Abban da kyau murya bata fita ya ce. "Ba zan iya ba Abba" Abba Hakimi bai fahimta dan haka ya ce "Kai mutum ne mai tsoran Allah da gudun hakƙin wani, balle matarka kada ka damu, ita Halisa ƴar riƙo ce shekara nayi zan amshi abata" ya zare jikinsa yana sauke numfashi tare da yin sallama. Daga nan suka ɗauki Umar-khan kai tsaye suka shige Airport inda jirgi ke jira. Tunda daga jirgin hankalinta ya tashi amma bata nuna ba, ta riƙe hannunta da kyau, Umar-khan na gaba sai Zahrah Halisa na biye da ita a haka suka shiga cikin jirgin, suna shiga Halisa ta riƙe kanta sbd tsoro, Umar-khan ya kalli Zahrah ya ce "Wajenku na cikin vip" Zahrah ta kalle shi ta ce "Yana ciki ne?" Umar na zama a mazauninsa ya ce "Gaskiya ban sani ba, ku shiga ku gani" ba tare da Zahrah ta ce komai ba ta nufi vip ɗin, jin takun tafiya a bayanta yasa ta tsaya tare da kallon Halisa ta ce "Ke kuma lafiya kike boye ni? Na manta ba a saba ba, Umar nuna mata wajan zama"bai ɗago kai ba ya ce "Wajan zamanku ɗaya ne ai duk vip" Zahrah ta riƙe ƙugu ta ce "kan uba, tayaya haka ya kasance kana nufin tare zan zauna da ita ga mijina kuma?" Sai a lokacin ya ɗaga kansa tare da kallonta ya ce "To ai suna ɗaya kuka amsa, matsayi ɗaya" "Kamar yaya suna ɗaya? Umar ya kamata kasan me zaka ce dani, ka gane" ya haɗe hannaye waje guda ya ce. "A'a ranki ya daɗe, mai da wuƙar mijin naki shi ne ya bada umarnin haka" ta haɗiye yawun takaici tare da shigewa vip, daman ita Halisa ta jima da shigewa, dan haka Zahrah na shiga ta samu Halisa zaune ta sunkuyar da kanta ƙasa, wajan ya haɗu sosai akwai duguwar kujera wacce Halisa take zaune akai, sai kujera mai guda biyu, tunanin Zahrah ya bata mai guda biyun ita ce wacce zasu zauna ita da Yaa Sheikh, ta nemi waje ta zauna idanunta akan Halisa ta ce. "Ina mijina?" Tai shiru taƙi cewa komai. "Ba magana nake miki ba, na lura kin fara ganin wajan barcina?" Ta ɗago lulu eye's ɗinta wanda suke sheƙi kamar an tara musu ruwa sbd yadda hawaye ya kwanta cikinsu. A tsiwa ta ce. "Ina mijina?" Zahrah ta zare ido tare sakin baki da jin abin da Halisa ta ce. Ƴar fillo tai murmushi kawai tare da girgiza kai ta ce "nifa kamar haka naji kince Anti shi ne nake ƙara tambaya, to a haka naga wajan kam" Zahrah ta ɗaga hannu zata ɗauke Halisa da mari suka ji gyaran murya. Gaba ɗaya suka ɗaga kai a tare daga Uwar gidan har amarya Zahrah, basu yake kallo ba wayarsa yake sakawa a airplane mode. Yaa Sheikh ya riƙe ya saba akan duguwar kujera yake zama, sbd yana ɗan samun hutu yayi barci kafin ya isa inda zashi, kai tsaye ba tare daya lura da Halisa ba ya nufi duguwar kujera tare da zama dab da ita. Numfashin Halisa ya kusa ɗaukewa sbd wani mugun shaƙar ƙamshin Roja da tayi, gashi Yaa Sheikh ya zama ƙato babba sosai har kafaɗar shi na rufe kanta. A karo na farko zuciyar Zahrah ta shiga bugawa gabanta ya faɗi,ta juya ta kalli Halisa wacce ta kafe Yaa Sheikh da idanu, a hankali kuma ta kalli Yaa Sheikh wanda ya nuna kamar bai san da mutane a wajan ba. Ta kasa magana ta rasa a wanne ma'auni zata saka haka, anya bata hau tsaunin da zai kaita zuwa ga hallaka ba?. A zahiri Yaa Sheikh ya mance ya taho da matayen nasa har biyu, da uwar mata da kuma ƴar rainon shi. A hankali aka fara sanarwar a ɗaura blet, Zahrah ta ɗaura Halisa kuma ta rasa me ake cewa sbd cikin harshen turanci ake maganar, sai faɗa computer take tana ƙara sanarwa. A nutse ya ware rawani kansa domin duk a zaton shi, shi kaɗai ne a cikin vip ɗin, kyakkyawar sumar shi ta bayyana abin mamaki ilahirin sumar kan shi daga gaba jajir take tamkar wanda ya fara furfura, daga baya kuma baƙaƙirin tai luff har wuyan shi. Ya sauke hannunsa akan Alkyabbar jikinsa ya ɗan buɗe gaban kaɗan sbd nauyi da tayi masa, yana kammalawa yaja blet, daidai lokacin aka fara sanarwar a shirya jirgi zai tashi, Halisa ta razana ta ƙanƙame jikinta, kanta ya shiga juyawa sai tayi nan luu tayi nan luu, lokacin da jirgi ya ɗaga zuwa sama Yaa Sheikh ya lumshe idanunsa ba zato ba tsammani yaji an fasa wata gigitacciyar ƙara kafin ya buɗe idanu ta faɗo kan cinyarsa babu numfashi.... Paid It's 500 08119237616 Da fararen idanunsa masu tsari yake bin ta da idanu da mamaki, ganin da gaske bata mutsi tsoran da ya yi mata yawa ya sanya numfashinta ya ɗauke, hannunsa basu taushi ya sanya akan fuskarta kamar mai jin tsoran gently ya shiga bubbuga kumatunta amma ko motsi ba tayi ba, ya ɓata fuska ganin tun ba a je ko'ina ba, yarinyar zata fara bashi wahala. Yatsun hannunta biyu ya kama yaja da ƙarfi yana buga tsakiyar kanta ajjiyar zuciya ta sauke da ƙarfi tana jan numfashi, sai kuma ta fashe da kuka tana riƙe wanda taji kusa da ita sosai cikin fillatanci take faɗin. "Don Allah ku sakko dani ƙasa zan mutu wayyo Dada wajanki zan dawo" saukar numfashin da yaji yana sauka a fuskarta da ƙamshin da ba zata manta da shi ba ya sanya ta buɗe idanunta wanda ta rufe su saboda tsoro, wanda ta gani take jikinsa ya bata mamaki numfashinta ya kusan ɗaukewa, sbd yadda ya yi mata kwarjini a idanu ga Alkyabbar jikinsa duk ta rufe mata jiki, a jikinsa yaji shi take kallo bai kalleta ba, ya sanya hannu tare da riƙo kafaɗunta da kyau yana zaunar da ita akan kujerar sosai. Yana daga inda yake ya ranƙwafa sosai tare da miƙa hannu zuwa inda blet ɗin take, kwantaccen sajansa ya shafi fuskarta ta sauke numfashi mai zafi wanda ya sanya Yaa Sheikh daka tawa da kama blet ya jima kafin ya zaro blet ɗin da sauri ya maƙala mata, yana ƙoƙarin janye jikinsa ta ɗora hannunta a tsakiyar tafin hannun shi.. "Uhmmm" ya ce a ransa yana ɗaga idanunsa zuwa gareta ya kalli cikin idanunta ba tare da ya ce komai ba, Halisa ta sake damƙe hannunsa da kyau cikin rawar murya ta ce. "Usako miyetti masin" idanu kawai ya lumshe mata tare da matsawa waje guda. A fusace Zahrah ta kunce blet ɗin jikinta tare da tashi tayi kan Halisa tana kumfar baki ta ce. "Ke dan uwarki mijina sa'anki ne da har zaki faɗa kansa da ƙazamin jikinki? Shegiya mara ƴan ci" Halisa ta kalli Zahrah ta ce "To Anti godiya nayi masa fa, kuma dana faɗa ƙasa naji ciwi ba ƙwara na faɗa kan shi ba, kuma ai ban masa nauyi ba ko kaji ciwo?" Ta faɗa tana juyawa tare da kallon Yaa Sheikh, shi gaba ɗaya hankalinsa baya kansu hannunsa riƙe da darija yana dubawa, tuni ya mayar da hiramin kansa baya buƙatar kowa yaga wani sashe na jikinsa. "Kauuu!!" Zahrah ta ɗauke Halisa da mari tare da nuna ta hannu ta ce "zanci uwar data haifi babarki" ƙarfi da girman zagin yasa Yaa Sheikh kallon Zahrah a zuciyarsa yana Istigifari bai ɗauka wani zai iya zagin ba, ba a taɓa zagi a gaban shi ba, hakan ya zama abu sabo a gare shi. Bai ce komai ya ɗauke kai tare daci gaba da duba jaridar hannunsa, zafin marin yasa Halisa fashewa da kuka sosai tana kifa kanta a cinyarta, kuka take sosai wanda rabin kukan baƙin cikin zagin da Zahrah tayi mata ne. Yaa Sheikh kukan yake ji har tsakiyar kansa jin kukan na neman tarwatsa masa kai yasa ya miƙe tsaye tare da buɗe wata ƙofa ya shiga. Zahrah ta kasa haɗiye mamakin yadda Yaa Sheikh ya nuna kulawa ga Halisa, haushin abin da ya yi yasa ta huce akan Halisa ɗin. Sun yi nisa da tafiya sosai wata maid ta shigo cikin wajan tana tambayar Zahrah me za a kawo musu, Zahrah ta karɓi abin hannun matar ta duba, kana ta zaɓi abin da take so. "Nace ko zaki iya sauyawa wannan yarinyar waje?"Flight attendant ta ce. "Her name please?" Zahrah ta ɗan kwaɓe fuska ta ce "Something Halisa.." ta ɗan danna wani abu a jikinta tare da yin magana bayan ta gama ta ce. "I think ita ce Halisa Sheikh Aliyu haydar Aliyu right Maah?" Zahrah ta ce "No, bana tunanin ita ce her name is Halisa Danejo Rome" Flight attendant ta sunkuyar da kanta ƙasa ta ce "Sorry Maah babu da wani suna a jerin wanda za su yi tafiya yau, Halisa Sheikh Aliyu haydar Aliyu shi ne" A fili Zahrah ta ce "Kan uba" sai yanzu ta tuna sunan Yaa Sheikh kenan, da sunansa akai mata visa kenan?. "Oh maybe she's the one, zaki iya sauya mata wajan zama?" Matar ta ce "Yes Maa, daman yanzu na duba ta samu sauyin wajan zama tuni" Zahrah tai murmushin jin daɗi matar ta kalli Halisa wacce ko inda suke bata kalla ba sai Ajjiyar zuciya take saukewa. "Can you follow me please?" Zahrah ta ce "ki mata hausa maybe she understand you" matar tai murmushi ganin yadda Zahrah take kwaɓe fuska ta ce "But she's your daughter?" Wata uwar harara Zahrah taiwa matar ta ce "Kinga alamar ina da ƴar ne?" Ita ma tai murmushi ta ce "Ai babu mmki idan nace miki a tunani zaki haifi yara biyar ma" Zahrah ta kalli jikinta da kyau ta kasa cewa komai, sbd baƙin cikin Flight attendant. "Halisa biyo ni kinji" a sanyaye duk da tsoran jirgin da take tabi bayan matar har zuwa champer 2 na jirgin. Nan ma dai kujeru biyu ce kawai a wajan ba kowa, ta nemi waje ta zauna cike da tsoro. Not too long da zamanta ya shigo tare da zama kan kujera da sauri ta sunkuyar da kanta domin a tunaninta faɗa zai mata, sai taga mai kulata ba ƙafarsa kawai ya miƙe. Tana zaune aka turo basket na abinci, zallar fruits ne sai gorar ruwa, aka ajjiye a gaban Yaa Sheikh ita kuma aka ajjiye mata chips da egg sai haɗin salad da ruwa. A hankali ya ɗauki orange ya saka bakinsa ya shiga taunawa cikin nutsuwa, Halisa ta kalle shi bakinta na rawa ta ce. "Amma wannan abin yabann sha'awa ɗan sammani" ya jita sarai amma yai mata banza sai da orange ya ɗin ya rage guda uku ya ɗauki guda ɗaya zai ƙara sakawa a bakinsa tayi saurin riƙe hannun shi, bai zaici haka ba ya kalli hannunta tare da kallon gefen fuskarta ta langwaɓar da kanta gefe ta ce "Ayya ka sammin bana, ni ma idan kaga abuna zan maka naga kana ta haka da idanu" yabi idanunta da kallo yadda ta lumshe su tare da buɗewa tana gwada masa yadda yake, ta kwance na hannunsa tare da kawai bakinta, ta ɗauka wani daɗi ne a orange ɗin. Ya sauke numfashi ganin hannunta na neman taɓa dugun gemun shi cikin ƙasa da murya mai sanyi ya ce. "Ci kani" ta yi saurin saƙona tana komawa wajanta, bai ƙara taɓa komai ba a kayan sai ruwa daya sha sosai. Misalin 10 na dare jirginsu ya sauka a Prince Muhammad bin Abdul'aziz International airport, sai nasarwa ake kowa ya saka blet jirgi zai sauka, ganin bata fahimci me ake cewa ba ya kalleta da kyau, ya riƙa ya saka blet a jikinsa ba damar cirewa kuma sun ɗan bada tazara, a hankali jirgi ya fara girgiza yana rawa Halisa ta rikice daga tai nan sai tayi nan, shuuuuu jirgin ya yo ƙasa tai gaba luuu zata kifa shiru tayi jin an riƙo kafaɗar ta, ya haɗa da gefen ƙirjinsa tare da riƙeta. Ƙuri tayi masa da idanu ganin nasa idon a rufe ta kasa motsawa shima kuma bai saketa ba, tunda har lokacin jirgin bai gama daidaita ba, balle ya samu damar sauka a titinsa. Ɓangaren Zahrah sosai taji daɗin ganin an ɗauke Halisa yanzu zata samu damar kasancewa da mijinta hankali kwance, sai dai tun tana jiran dawowar shi amma shiru gashi bata da ikon tambayar wani, bisa dole tai shiru. Bata tsammaci abin haka ba, sai ji tayi ana faɗin sun ƙarasu Madina tuni ai. A hankali ta saka blet tasan dai dole tare zasu tafi gida. Jirgi na yin parking ya saketa da sauri kafin ta buɗe ido ya fice daga cikin wajan, ta shiga zare idanu yanzu idan guduwa sukai yaya zatai?. Tana wannan tunanin Umar-khan ya shigo yana murmushi ya ce "Matar Malam tasu muje" ta miƙe tana kallon Umar-khan ta ce "To kai gida kaje ka dawo ne?" Yai dare ya ce "Hhhhhh ai kam na koma Nigeria na dawo" tabi bayansa da sauri ta ce "Kasan me" ya ce "sai kin faɗa" ta lumshe idanun ta buɗe ta ce "A ciki da abin ya tashi sama kawai na faɗa kan Malam na ɗauka zai dukeni kamar yadda anti da dake ni, sai naga kawai ya lumshe idanu ni kam nace masa na gode" "Uhm" kawai Umar-khan ya ce domin bashi data cewa a wanann batun, suna fitowa Zahrah na fitowa suka kalli juna da Halisa kowa ya ɗauke kai. Bayan sun sauka daga jirgin Zahrah ta kalli motar dake gabansu ta ce "Ina My Excellency?" Ya ce "Yana da meeting ne, sai zuwa 12 zai dawo" Zahrah ta ce "meeting da wannan daren?" Umar-khan ya ce "Manyan mutane daman sai dare suke meeting, muje kada mu ɓata lokaci" Zahrah ta shiga bayan mota Halisa ba haka, Umar-khan na gaba shi da driver. Wata haɗaɗɗiyar area suka nufa gaba ɗaya mazauna wajan larabawa ne, gidan dake kusa da na Yaa Sheikh sune hausawa, faɗar kyau da tsarin gidan Yaa Sheikh ɓata baki ne, flat gida na zamani, motoci birjik a harabar gidan ga tarin flowers da ɓangaren swimming pool, ga Wajan tsuntsayen shi kusan duk rubutun gidan da rabci ne, yana da ɓangare na Musamman da yake bawa manyan mutane darasi. Zahrah ta dubi haɗaɗɗan parlourn mai ɗauke da wasu ƙawatattun kujeru, sai ƙamshi yake, ga wasu fitito masu kyau iya haɗuwa ya haɗu. Umar-khan ya kammala shigo da kayansu ya ce. "Ɓangare uku ne a gidan, wancan ɓangaren Yaa Sheikh na tsakiyar kenan, na gefen dama babu na kowa na hango ma babu kowa, ya ce ki zaɓi wanda kike so, ɗayar ki bawa mai aikin naki" Zahrah ta kalli part ɗin hannun hango taga bayan na Yaa Sheikh yafi kyau dan haka ta ce "Na ɗauki na ɓangaren hango ka shigo mini da kayana ciki" tana faɗin haka ya miƙa mata key ɗin ɓangaren ta amsa hana shigewa ciki. Ya kalli Halisa ya ce. "Daman girman kine shiga ɓangaren damar" murmushi kawai tayi, Umar-khan ya riga yasan da ɓangaren Yaa Sheikh da wanda Halisa zata zauna a manne suke, domin akwai ƙofa kai tsaye daga ɗakin Yaa Sheikh wacce zata kawo shi ɓangaren Halisa ɗin. Ya ja mata kayan zuwa jiki, ya yi mata bayanin komai da kitchen da banɗaki komai dai, kana ya nuna mata yadda ake amfani da kayan kallon ɓangaren ta.. "Sai da safe Matar Malam" ta jinjina masa kai. Zahrah ma ya kai mata kayan kana ya nufi nasa gidan. Misalin 1:30 motar Yaa Sheikh tai parking driver ya buɗe masa ƙofa, a hankali ya fito ya ɗan tsaya yana duba ko wanne ɓangare yana yin addu'a sbd ya saba, ganin hadari a garin kuma yasa duk ya rufe Windows na gidan. Ya nufi ɓangaren shi, wanka ya yi ya ɗora jallabiya mai kyau a jikinsa, black tea yake son sha amma bai san yarda zai ba, gashi kuma yasa a sallami masu aikin shi. Haka dole ya zame jallabiyar ya saka kayan barci yana buƙatar hutawa sosai, sbd ya samu peace of mind kwana biyu yana stressed kansa da yawa. Kiran sallar farko a kunan Yaa Sheikh da Halisa domin zamanta wajan mother ta saba da tashin asuba, a hankali ya nufi bathroom tare da sakarwa kansa ruwa mai zafi kana ya yi alwala tare da yin brush, cikin zafin nama ya shirya cikin kyakkyawar shigar shi wacce ya saba, farar jallabiya ya ɗora hirami a kan shi, bakinsa ɗauke da aswaƙ ya nufi Masjid Malik wanda shi ke gabatar da jam'i a can, bayan idar da Sallah ya yi karatu wa jama'a kamar yadda ya saba. 7:00 ya shigo gidan da mmki yake jin parlour ƙamshi mai daɗi, yana ƙoƙarin shigewa part ɗin shi ta ce "Jamɓanduna?" Jin fillatanci yasa ya fahimci ba Zahrah bace amanar shi ce kuma ƴar riƙonsa, ya juya tare da kallon ta, tana cikin wata duguwar riga mai kyau plush pink sai baby hijab a kanta, kai ya ɗauke ta ce. "Anti Zahrah ba ta shi ba, ni tun ɗazo na tashi ina ta kallo" shi dai bai ce komai ba ya shige part ɗinsa tabi bayan shi da kallo kafin ta juya zuwa kollon girke-girken da ta keyi. Yana shiga part ɗin sa ya zauna saman kujera, tare da kiran number Umar-khan babu jimawa ya ɗauka a nutse ya ce "Ka yi komai, kada ya shige kwana biyu a nemi gurbin karatun" yana faɗin hakan ya kashe wayar, tare da kiran wata number mgn ɗaya ya yi ya kashe.. Halisa na zaune taji telephone line na ƙara ta miƙe sauri daman Umar-khan ya faɗa mata yadda ake amfani da ita, tana ɗagawa taji ance "Mrng maaa, the breakfast is ready Yaa Sheikh na jira" Halisa ta ce "Kika ce me?" Ta ce "Abincin Yaa Sheikh ya kammala kina magana da ɓangaren kitchen, yanzu maid zata kawo" Halisa ta taɓe baki tare da komawa ta zauna, babu jimawa wata mata mai fararen kaya ta shigo ɗauke da tray da butar shayi ta ce "Mrng Maa ga shi Yaa Sheikh na jira" Halisa ta amsa tana miƙewa tsaye Zahrah ta fito cikin kayan barci da alama ko sallar ba tai ba, ta kalli matar ta ce "lafiya?" Tai mata bayani ta ya mutsa fuska ta ce "Ok daman ita ce mai aiki bata ta kai, ki sama mini breakfast mai kyau yanzu" matar ta juya Halisa ta riƙe tray Zahrah ta ce "Sai ki fara aikin ki tun yanzu, kije ki kai masa breakfast ɗin ki dawo ki shirya mini kayana a wardrobe" Halisa ba ta ce komai ta juyawa zuwa inda taga Yaa Sheikh ya nufa, bakinta ɗauke da sallama bata sani ba ko ya amsa ko bai amsa ba, yana zaune kan kujera ta ƙarasu har inda yake ta tsuguna ta ce "Ga shi wai" ya gyara zama yana tsiyaya tea ɗin tare da kaiwa bakinsa. "To kai iya wannan kake sha ne? Ko nayi maka abinci?" Da idanu kawai yake bin gefen fuskarta da kallo ta gyara zama ta ce "Mother ta ce kai mijina ne" ya ware idanu da sauri yana binta da idanu, ta buɗe baki zata sake magana caraf ya saka hannu tare da kame bakin..... 08119237616 Paid book Not edited "Shiru" ya ce yana sakin bakin tare da mai da Idanunsa kan glass cup ɗin da ya tsiyaya tea aciki. Ta tura baki gaba ba tace komai ba duk da irin ƙaiƙayin da bakin yake mata, haka nan taji kamar ana mintsininta akan Halisa yi magana cikin sauri ta ce. "Nima ina jin yunwa na sha shayin naka?" Cak ya ajjiye tea ɗin daga hannunsa yana ɗaukan tissue tare da goge bakinsa, ta ɗauki shayin daya rage zata kai bakinta ta ji ance "A'a" ta ajjiye cup tana miƙewa tare da bin bayansa, sahun tafiya da yaji a bayansa yasa ya tsaya, tayi saurin dawowa gabansa suna haɗa ido ya ware mata manyan idanunsa masu kaifi ta tura baki ta ce "Na sake magana banga ka riƙe bakin ba ai" Yaa Sheikh ya girgiza kai kawai tare da shigewa bedroom ɗinsa yana ɓoye yanayin fuskar shi. Ta kalli inda ya shiga sai kuma ta juya tana kwashe tray ɗin. A main parlour ta samu Zahrah zaune tana breakfast ga wata maid nayi mata tausa a ƙafa. "Ke zonan" cewar Zahrah Halisa ta dawo ta zauna tana ɗauke kai gefe guda, saboda har yanzu bata mance mari da zagin da Zahran tai mata ba, Zahrah ta ajjiye spoon ɗin hannunta wanda take shan tea da shi ta ce. "Kai breakfast ɗin sai yanzu? Ko bai ta shi bane" Halisa ta kalle ta sai kuma ta ɗauke kai tana faɗin. "Shi ya ce na tsaya" Zahrah ta ce "Shi Yaa Sheikh ɗin?" Tai shiru ba tare da ta ce komai, tasan indai zatai magana to zata saki layi ne, Maid ɗin ta kalli Halisa da sauri, ai ko ita da tayi shekara da shekaru tana aiki a gidan Yaa Sheikh magana bata taɓa haɗa su ba, infact ko parlourn shi bata san ya yake ba, Ummul ce kawai take kai masa breakfast ita ma iya dining room, sai ya gama yabar wajan take zuwa ta kwashe, idan kuma yini gida zai yi a ranar basa taɓa zuwa part ɗin, Umar-khan ne ke kai masa dinner, bai fiya cin lunch ba sai dinner, anytime yana tare da butar shayi kamar buzu. Mamaki ya cika Maid ɗin jin abin da Halisa ta faɗa wai shi ya ce ta jira? Who is she to him?.... "Whatever, Ke yama kika ce sunanki?" Maid ɗin ta ce "Bara'at" Zahrah ta ce "Ok, duk wani aiki na part ɗin nan, zuwa part ɗin Yaa Sheikh ya dawo hannun wannan yarinyar, idan kun kammala abinci na Yaa Sheikh ita zata dinga kai masa, bana son na dinga ganin wani abu na ba daidai ba, bana son surutu da hayaniya yana saka mini ciwon kai, ko a gidan ubana ban taɓa sanin hanyar kitchen ba, to a nan ba zan fara saninsa ba, kuna gama girki ki bata ta kawo mini nawa" daga Halisa har Bara'at kallon Zahrah suke, suna mamakin ƙarfin ikon nata, duk da cewa Bara'at bata san matsayin Zahrah ba, amma tasan dole da akwai abin da ta taka a gidan... Zahrah ta kaɗa ƙafa tana faɗin "Ku ɗauke idanunku daga kan mijina, daga nesa kuka ganshi ku sauya hanya, duk abin da kuke nema ni zaku faɗawa, koda abin cin gidan ne ya ƙare" Bara'at ta ce "Ok, amma kula da abincin gidan yana wajan Ummul" It's your problem, I just finished planning what I want" ta juya kan Halisa tana faɗin.. "Jeki breakfast ki saman a bedroom" tana faɗin hakan ta shige part ɗinta, Halisa ta bita da kallo a zuciyarta tana mmkin halin Zahrah. Miƙewa Bara'at tayi Halisa ma haka, tabi bayanta har zuwa sashen kitchen, ma'aikata ta gani mata da yawa ko wanne da abin da suke a kitchen ɗin. Da sauri Bara'at ta nufi wajan Ummul tana ce wa "Yau naga abin mamaki Ummul" kyakkyawar matashiyar matar wacce zata iya shekaru 50 zuwa sama ta kalli Bara'at ta ce. "Da akai me Ukkuti Bara'at?" Bara'at ta sauke numfashi ta ce "Wata mata na gani, mai iko da isa, wallahi na tsorata da yanayinta" Ummul tai murmushi tana ajjiye abin hannunta ta ce "Faɗimatul-zahrah bin Umar Farouk, matar Yaa Sheikh" a tare duk suka ce "Matar Yaa Sheikh?" Ummul ta kallesu ta ce "Na manta ban shaida muku bane, sai a haƙuri da juna ko?" Idanunta ya sauka akan Halisa wacce take dube dube duk abin da suke faɗa tana ji amma hirar bata gabanta, Ummul ta girgiza kai kawai, tana mai jin wani abu a ranta, yarinyar tana nan dai babu sauyi a tare da ita kamar yadda yake nuna mata ita a waya. Hawaye ya sakkowa Ummul ko yanzu ta mutu ta yi farin ciki, Aliyu ya samu gefen rayuwar shi kamar yadda yake faɗa mata a koda yaushe. Bara'at ta ce "Ummul wace ita kuma wannan?" Ummul ta ce "Masu gidan ce" "Masu gidan kuma?" Cewar Suhaima Ummul ta ce "Ina nufin mai aikin Zahrah ce" ta kalli Halisa da kyau tana mai sakin murmushi ta ce "Sunanta Halisa, ƴar uwar Zahrah ce an bawa Yaa Sheikh riƙon ta amana ne, zatai amfani da sunan Halisa bin Sheikh Aliyu haydar Aliyu" Halisa ta ƙarasu wajan Ummul da sauri fuskarta ɗauke da kyakkyawan murmushi ta kama hannun Ummul ta ce "Laa kema kin sanni ashe, kuma kin san anyi...." Ummul tayi saurin rufe bakin nata tana cewa "Ba'a yin surutu a ɗakin girki, Bara'at akwai tray tana shirya breakfast ki bawa halisa" Bara'at ta ɗakko tray ta bawa Halisa ita kuma ta ce a kitchen ɗin zata zauna ta ci. Bayan ta gama cin abincin Ummul ta miƙa mata farar madara mai ɗauke da zuma a ciki, batai musu ba ta amsa "Nima ina son na iya girki sosai, ina son yi wa Yaa Sheikh girki mai daɗi" Ummul tayi kamar bata ji zancen na Halisa ba, taci gaba dayin aikin gabanta tana son a akai gidan ciyarwa Yaa Sheikh abincin akan lokaci. Zahrah na tsaye a gaban mirrow anci uwar kwalliya sai ƙarinin mai take, wayarta dake ringing ta ɗauka ganin sunan Deen ta ce "Uhm maye daman nasan babu mai kirana sai kai" daga cikin wayar ya ce "Ba wannan zaki tambaya ba, fara duba number" da sauri Zahrah ta duba number da mmkin take kallon number ta Saudiya ce,what does that means? Ya katse mata tunani da faɗin "Ki daina mamaki na riga ki sauka a Madina, ke kawai nake jira, don't make any mistakes nazo da maganin da ki ke buƙata, ina son ganinki" The surprise of his behavior prevented Zahrah from speaking. "Wallahi ki san yadda akai ki ka zo, ko ki ganni a gidanki" yana faɗin haka ya kashe wayar babu jimawa ya tura mata address ɗin inda yake, Zahrah ta dafa kai da sauri kuma ta juyawa zuwa ɗaya bedroom ɗin nata a nan ta samu Halisa tana shirya mata kaya a wardrobe, zama tayi ta ce "Ke kin fara menstrual?" Halisa ta ɗauka gyaran kayan take nufi kai tsaye ta ɗaga mata kai alamar eh. Juyawa tayi ta nufi part ɗin Yaa Sheikh. Fitowar shi kenan daga Library room ɗinsa, ya zauna sanye da wata tattausar Jallabiya a jikinsa hannunsa cikin sumar kansa, cikin nutsuwa ya gyara zama akan duguwar kujerar da yake kai hannunsa riƙe da Cup yana shan green tea wanda Ummul ta kawo masa da kanta, speaking calmly ya ce da Khalil. "Uhm surutu dai" Ta cikin waya Khalil ya saki dariya ya ce "Ya muke da matarka? Allah ya nuna mini ranar da zata barbabaɗa tana ɗauke da cikin Yaa Sheikh, koda yake kace baka son ta ai, auren dole akai maka" Yaa Sheikh yaja idanu ya rufe yana jinsa fresh sbd barcin da ya yi, cikin son dakatar da Khalil ya ce. "Wallahi ba auren dole bane, ni na zaɓi matata It was completely my plan..." Katse wayar ya yi jin yana faɗin abin da mai shirya ba, tare da rufe kansa. Tsaye ya ganta a kansa babu sallama ya ɗauke kai kawai yana ci-gaba da danna waya tare da duba abubuwan da Umar-khan ya tura masa. Ta zauna kusa da shi tana cewa "My Excellency baka fito ba har yanzu hope lafiya?" Kai kawai ya jinjina mata ba tare daya kalleta ba, ta haɗe jikinta da nashi tana cewa "Daman nace ina neman permission zamu shopping da ƴar fillo" har lokacin idanunsa yana kan waya bai ce komai ba. Ta shafi fuskar shi tare da cewa "Ba jimawa za mu yi ba kaji My Excellency" Jotter ya ɗauka da pen ya yi rubutu kana ya ajjiye mata a gefenta haka kurum yaji harshensa ya harɗe baya jin yin maganar. Ganin ƙoƙarin rungome shi take son yi ya ɗan miƙe tsaye, yasan cewa hakƙinta take nema, kuma yasan girma da ƙarfin hakƙi amma ya zai? He's not interested at all, baya son Ubangiji ya kama shi da wannan laifin. Tabi bayan shi da kallo, tana ji a ranta dole ne ma tayi gaggawar aiwatar da burin dake ranta, Yaa Sheikh ya dawo hannunta sai yadda tai da shi tayi imani da Allah idan ya zo hannunta shi da wata ƴar mace kuma har abada, ba zai iya kallon kowa a matsayin mace ba dole sai ita, What is the solution? where will she start and what will she do now. "You can go, Ina buƙatar gyaran part, With food" shi ne abin da ya rubuta mata a jikin Jotter ɗin, ta duba kenan dole mutum ɗaya ya tsaya, ita gasky ba wani gyaran ɗaki da zata iya, bayanta ciwo yake idan ta yi,kuma bata saba ba. Fita tayi ta samu Halisa a main parlour a kwance barci ya ɗauke ta tunda ta farka da asuba bata koma ba, gashi tai aiki ta gaji sosai bata san barcin ya ɗauketa bama sbd kallo take. Tana zuwa ta fisgo ƙafar Halisa zuwa ƙasa ta faɗo daga kan kujerar, a tsorace ta ce "Hande en boni me na yi Anti?" Zahrah ta ce "Ai hutu kika samu kenan? Ai babu ranar da zaki huta, zaki ta wahala har abada, kije ki gyara part ɗin Yaa Sheikh, ki kai masa lunch zan fita unguwa" kanta a ƙasa ta kasa cewa komai, tana zaune a parlourn Zahrah ta fito cikin wata duguwar riga ta yana mayafi hannunta riƙe da hand bag, kamar yadda Zahrah bata kulata ba itama bata kula ta ba. A compound ta ci karo da Umar-khan yana fitowa daga mota hannunsa riƙe da takarda. Ya ce "Evening" ta share sa, ta nufi wajan wani da alama shi ne drivern gidan. Kai tsaye Umar-khan gidan ya shige ya samu Halisa zaune kanta a ƙasa tana gyangyaɗi ya ce "Matar Malam" tai saurin jan mayafin abayar ta ɗora a kanta tana yi masa murmushi ta ce "Ina yini?" "Lafiya, barci a nan kuma? Yaa Sheikh ɗin yana ciki?" Ta ce "Ban sani ba" ya jinjina kai ya ce "Ok bari na duba, kije ki kwanta mana" ita dai ba tace komai ba ya nufi Part ɗin Yaa Sheikh barci yaci ƙarfinta, ta kwanta nan ƙasan carpet. Umar-khan ya zauna bayan ya gaida Yaa Sheikh ya ce "Na cike komai na makarantar, gobe aka bada izinin ta fara zuwa, Mother ta ce komai cikin gaggawa take buƙata" ya miƙawa Yaa Sheikh file ɗin takardun Halisa bai amsa ba, sai tsare Umar ɗin da idanu da ya yi, Umar yana fahimtar shirun na Yaa Sheikh hakan ya sa ya ce. "Al Aqeeq International School for Girls, Safiya Opens 7:30 ita ce makarantar" Yaa Sheikh ya jinjina kansa tare da miƙewa ya shigewa ɗaki. Wajan mintuna goma suka fito tare da Umar-khan wata Milk ɗin jallabiya ce a jikinsa, sai golden ɗin Alkyabba daya ɗora a kan jallabiyar, ya fito a babban malaminsa sai ƙamshin Roja yake bazawa, yana fitowa idanunsa ya sauka akan Halisa wacce ta cure waje guda tana barci, ya tsaya cak tare da kallon Umar-khan, Umar ya nufi ɓangaren Ummul babu jimawa suka dawo tare, Ummul ta kallesa ta ce "Malam za a fita ne? Ba kaci abincin kirki ba?" Ya ɗan ɗauke kai zuwa hanyar fita yana faɗin. "Sanyi zai illata ta, a sauya mata waje" sai a lokacin Ummul ta lura da Halisa. "Tom babu damuwa, Allah ya tsare" ta nufi wajan Halisa ta shiga tashinta tare da faɗin "Matar Malam, matar Malam" ta buɗe ido tana kallon Ummul ta ce "Maza ta shi ki koma ɗaki, a kwai sanyi zai kama jikin ki" ta buɗe ido sosai ta ce "Anti Zahrah ta dawo ne?" Ummul ta ce. "Fita tayi ne? ta shi lokacin sallah ma ya yi ai muje ko" har part ɗin Halisa Ummul ta shiga, akan idanunta Halisa tai alwala kana tai Sallah. Ummul ta ce "ƙarfe biyar kizo ɗakina, zan nuna miki yadda ake cikakkiyar sallah, na fara karanta miki Alkur'ani, yanzu ki kwanta wajan ƙarfe 4:30 ki tashi ki wanka ki wanke baki, ki sauya komai na jikin ki, kinji ko?" Ta tura baki sosai ta ce "To wannan duk na mene Ummul" Ummul ta ce "zaki sani ne" ta fice daga ɗakin. Yaa na fita kai tsaye Al Masjid an Nabawi ya nufa sbd wani karatu da yake dashi na musamman, kuma acan yake son yi Sallah ma, da kuma zaman tattaunawa da za su yi da mahukunta kula da Masallaci harami ana son naɗa Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu matsayin limamin masallacin Haramin wanda zai jagorancin sallar Taraweeh da Tahajjud, gaba ɗaya azumi saura wata guda ya rage a fara. Tamkar uwa mahaifiyya haka Yaa Sheikh ya ɗauki Ummul yana ɗaukan minti goma yana magana da ita, tasan kusan komai nasa kuma tasan da yawa abin da Mother bata sani ba, tunda yafi rayuwa a Madina fiye da Nigeria. Sai bayan sallar issha Zahrah ta shigo a gajiye tana tafiya da ƙyar idanunta ya yi jaa, Halisa ta bita da idanu ganin yadda take tafiya kamar yaron da akaiwa shayi. Duk yadda Halisa tasu taga dawowar Yaa Sheikh bata gani ba, barci ya ɗauketa a Main parlour. Ƙarfe 12:30 ya shigo gidan shi kansa a gajiye yake sosai, ganinta a parlourn ya sanya ya tsaya yana binta da idanu, a hankali ya dubi lokaci sai kuma ya shige part ɗinsa. Kiran sallar asuba ya farkar da ita, da mmki take bin makeken gadon da take kai da kallo, an rufe ta da wani haɗaɗɗan duvet mai ƙamshi ga laushi an kuma rage ƙarfin a.cn ɗakin, ita dai tasan a parlour ta kwanta waya kawota nan? Ko ita ta shigo da kanta. Ta miƙe ta nufi toilet yadda Ummul ta koya mata haka tayi, tai wanka da ruwan zafi ta shafe jikinta da Vaseline Intensive Care Cocoa Glow Body Lotion. Shiryawa cikin Abaya ta ɗora hijab a nutse take duba littafan da Ummul ta bata, Ubangiji ya bata fikirar hadda ce, da yawan lokaci ita abu a kanta yake zama, duk wani abu mai muhimmanci bata wasa da shi. Tana zaune taji saukar muryarsa a kunnanta yana data kabbarar sallah, shiru tai bata taɓa tunani muryar shi takai daɗin haka ba sai yanzu. Sallah ta gabatar sannan ta nufi ɓangaren kitchen ta samu tuni sun Bara'at sun fito. 6:30 Ummul ta ce tayi sauri ta shirya za a kaita makaranta, wani tsalle tayi ta rungume Ummul daɗi ya kamata jin za a kaita makaranta abin da take buri a rayuwarta. Ta shirya ta fito tsaf a cikakkiyar ƴar fillonta Ummul na ganinta tai murmushi tana cewa "Kije ki gaida Abban naki" Halisa ta ce "Abba kuma Ummul" ta ce "Eh, uban riƙon ka ai uba ne jeki maza" hannunta ɗauke da yam balls ta nufi ɓangaren shi. Cikin siririyar murya tai sallama tare da shiga tsaye ta gan shi cikin kyakkyawar shiga mai ɗan kauri sbd sanyin garin da aka tashi da shi, hannunsa goye a bayansa ta ƙarasa cikin da sauri tana durƙusawa har wajan ƙafafuwan shi ta ce. "Jamɓanduna, Noi sare,Noi kuɗe" ta jera hausuwar ma'ana _“Ina kwana, ya ya gida, ya ayyuka”_ ya ware gajiyayyun Idanunsa a kanta, yana bin shigar makarantar nata, ta ɗaga kai ta gan shi tsaye ta miƙe tana kallonsa, ya dubi yam balls ɗin hannunta da raguwar na gefen bakinta. "Jiya nai barci baka dawo ba, yanzu kuma wai makaranta za a kai ni inji Ummul" ya jinjina mata alamar _"Eh"_ yana ƙoƙarin juyawa tayi saurin riƙe ƙugunsa da hannu ɗaya ta ce "Miyetti masin, Allah ya ƙara arziƙi" Ɗan ƙaramin bakin maganar kawai yake bi da kallo, gumi na tsastsafo masa ta goshinsa ta saki kyakkyawan murmushi ta ce "Mijina" da sauri ya kalli cikin idanunta ta ɗauke nata idanun sai murmushi take sbd daɗin zata makaranta. A hankali ta buɗe baki a taushashe kuma cikin ƙasa da murya ya ce "Matar m......" Maganar ta tsaya sbd yam balls data tura masa a cikin baki ta dinga tsalle tana cewa "Nayi maka wayyo daman ance baka cin abinci" ya lumshe fararen idanunsa tare da nufar kujera har lokacin tana riƙe da shi. Yana zama ta zauna a ƙasa Yaa Sheikh sai mai da numfashi yake sam bai niyyar cin komai ba, bisa dole ya shiga tauna yam balls ɗin bakinsa yana goge zufar dake goshinsa, wanda kuma shi kansa ya san zufar ta mece ce. Ya ɗauki bottle water tare da tsiyayawa a cup bayan ya sha ruwan ya mai da numfashi. Halisa ta ce "nace Ummul tayi maka wani na cinye gaba ɗaya tas" gently ya buɗe idanun a kanta ganin yadda yake bin fuskarta da kallo sosai yasa tai masa kyakkyawar murmushi tana lumshe idanu tare da buɗewa kamar yadda yai, a hankali ya ɗan ranƙwafa daidai kanta ya sanya fararen tafukan hannayensa tare da kama fuskarta da kyau babban hannunsa yasa yaja kumatunta numfashinsa na sauka a fuskarta ya ce. "Zaki fasa mini kai da surutu Matar Malam, shiru kan na ɗinke bakin...... Not edited Paid book ₦500 08119237616 Sarautar marubuta. _Ubangiji ya haɗamu da alkairan da suke cikin jumma'h. Mu haɗu Monday🥰❤‍🔥_ _I unite you with the greatness of God a daina fitar mini da littafin IDAN BA KE. What you want will not be difficult for you to buy. This is not appropriate at all.🫰🏿har zuwa ake a nuna mini wai an samu book ɗin Idan ba ke as free irin ga masifaffiyar nan bari nai ta ihu a media😂 I love my book lovers wherever they are. Amma don Allah a daina fitar da book ɗin... It's 500 via 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman fidelity bank shaidar biya 08119237616_ Kasa ƙarasa maganar ya yi sbd gemunsa data kama tana cewa "Yasunan wannan abun? Kuma da gaske ni matar malam ce, naje na faɗawa Ummul nace kace mini matar malam?" Ya lumshe idanunsa na wani lokaci kafin ya buɗe su a kanta tare da ɗora hannunsa akan nata data riƙe gemunsa ya zare yana girgiza mata kai. Zata sake yin magana ya miƙe tsaye yana nufar hanyar bedroom ɗinsa dole sai ya sauya kaya gaba ɗaya ta goge masa maiƙon hannunta a jiki, da sauri ta biyo bayansa ta ce "To baka faɗa mini sunan wannan dugun abin ba, kuma waye zai kaini makarantar ina son zama babbar mace" ya juya tare da kallonta a nutse yana mai mamakin surutun ta, yana da masaniyya akan yadda take amma bai ɗaukan surutun ya yi girma da tsayin haka ba. Bai ce mata komai ba ya juya yana mai sakin murmushi shirmanta a karo na farko da suka kasance tare domin sauran duk baɗini yake ganinsu. Ummul na kitchen Halisa ta dawo ta kalleta cikin kyakkyawan lafazi ta ce "Ba dai haka kika je da hannunki ba?" Ta kalli hannun kuma ta kalli Ummul ta dafe ƙirji ta ce "Wallahi na goge masa" Ummul tai shiru daman tasan za a rina, kuma sam ba tayi mamakin hakan ba. Maid Suhaima ta ce "Wa kika gogewa?" Da sauri Halisa ta ce "Malam, nikam ya sunan wannan dugun abin na fuskar shi? naji yana da laushi aradu" Ummul ta dafe kai da sauri kuma ta miƙe tsaye tana kama hannun Halisa suka nufi can part ɗin Ummul ɗin. Bayan sun shiga Ummul ta kalli Halisa sai kawai tai murmushi kafin ta ce "jeki wanke hannun ko?" A sanyaye ta ce "To" ta nufi bathroom ta wanke tas tare da wanke bakin ta fito har lokacin Ummul na zaune tai shiru tana kallon hanyar toilet ɗin, ganin yadda Ummul tai shiru yasa Halisa faɗin "Ummul" ta buɗe idanu ta ce "Kin gama? Lokaci na tafiya zaki buƙaci abinci a can, lunch box naki yana cikin mota" suka fita Main parlour daidai nan Zahrah ta fito da kayan barci da alama ko sallah ba tayi ba, balle ashirin zancan wanka tabi Ummul da kallo ta ce. "Wace ke? daga ina bana hana ana shigowa kai tsaye ba, ba tare da permission ba, ke kuma jeki gyara mini bed ki haɗa mini ruwan wanka" Halisa ta ce "makaranta za a kai ni, idan na dawo zan haɗa miki sai Kiyi wankan" Ummul ta danne dryar data zo mata. Da mamaki sosai Zahrah ta ce "School? Da izinin waye kuma? babu wata makaranta da zaki, baki zo gidan nan dan kije makaranta ba" ta faɗa tana fisgo hannun Halisa daga kusa da Ummul. "Ke kuma da kika tsaya kina ƙwalala mini idanu da alama kina da masaniyya, tell me waye zai kai ta makarantar" "Ni ne" ya faɗa a taushashe yana mai fitowa daga inda yake tsaye, yana sanye da sabbin shiga saɓanin ta ɗazo, farar dakakkiyar shadda ya sanya mai jamper da babbar riga, ya ɗora hirami ɗaya a kansa ɗaya kuma a kafaɗa.. Ta saki Halisa ta nufi inda yake ta ce "My Excellency amma daga zuwa sai batun makaranta, kuma ya kamata a faɗa mini, ni bani da ra'ayin yarinyar nan tai makaranta" Halisa ta tura baki tana mai jin haushin yadda Zahrah ta wani matsa kusa da Yaa Sheikh haka kawai taji zuciyarta ta cunkushe, amma hakan bai hanata cewa. "Amma ai Dada tana da niyya ko Anti, da izinin zani makaranta ta baki...." Cikin rawar murya Zahrah ta ce "Oh ok it's ok you can go, but waye zai kai ta?" Sai a lokacin Ummul ta ce. "Umar-khan, kafin driver ya fara kai ta, Aliyu yana da lecture da ɗaliban shi, zai iya magana" Ummul ta faɗi haka ne domin Zahrah ta bawa Yaa Sheikh hanya. Haka kurum Zahrah taji sha'awar kasancewa da mijinta ya bijiro mata, musamman da ƙamshin Roja ke ƙara narkar da zuciyarta, Yaa Sheikh na musamman ne, idan zaka kalli cikin idanun shi yayin magana to ba zaka taɓa yi masa ƙarya ba, ɗaya daga cikin baiwar shi kenan. Babu kunya ta rungome shi a gaban Ummul tana faɗin "Am going to miss you My Excellency back soon please" gani sukai Halisa ta juya da sauri zuwa part ɗin ta, Ummul ba tai magana ba. A hankali ya zame jikinsa daga na Zahrah ta ce "Bari naje nai wanka da Sallah bye" Ummul ta kalli lokacin 7 harta gota ba dai sallar asuba ba, sai dai walaha. Bayan shigewar Zahrah Yaa Sheikh numfasa yana mai gyara murya a kasalance ya ce. "Mun kwana lafiya, Ummul?" Ummul ta ce "lafiya lou, kaga ƴar rigima ko? kamar kuka naga ta nayi?" Ya saki fuska daga kamewar da ya yi shima yana duba lokaci a diamond rolex watch ɗinsa. "Aje a duba, kin san hali tun ba yau ba" tai murmushi ta ce "Wallahi fa" ta nufi part ɗin Halisa shi kuma ya goya hannunsa a baya tare da tsaiwa a tsakiyar parlourn. Kwance Ummul ta samu Halisa ta cire baby hijab ɗin jikinta sai kuka take kamar ranta zai fita. Ummul ta zauna cikin sakin fuska ta ce "Matar Malam lafiya? Wani abun ne? ko wani gurin ke miki ciwo?" Kuka kawai take taƙi magana tamkar zata shiɗe haka take kukan. "Faɗa mini mene? ke dawa" ta miƙe zaune cikin shassheƙar kuka ta ce "Ummul Dada zani, ni na fasa zaman wajan Dadata zani ki saka a bayar dani" Ummul ta ware idanu da kaɗuwa sosai ta ce. "Yanzu Matar Malam ina ke ina zuwa gida, keda kika zo bautar Ubangiji? Maza tashi akai ki makarantar ga shi can yana zuwa kin san kuma akwai inda zashi" idanunta ya yi jajir hawaye na zuba daga cikinsu ta ce "banso, na fasa makarantar ni rugarmu zan koma" yin duniya taƙi yarda Ummul ta ce "To dai na kukan bari na faɗa masa" ta juya tana mmkin sauyin da yarinyar ta samu lokacin gudu, me akai mata me kuma ya sauya mata tunaninta daga sha'awar zuwa makarantar. A tsaye Ummul ta same shi, bai kalleta ba amma tunaninsa da hankalinsa na kanta ta ce. "Kuka take sosai, wai bata son makarantar kuma a bayar da ita can ruga" maimakon ya fita sai ya juya zuwa part ɗin shi ba tare daya amsa maganar ta Ummul ba. Ta gane yaran kuraman nashi dan haka ta ƙarasa juyawa zuwa sashin na Halisa. kanta kife idanunta data rufe su take hango rungumar da Zahrah taiwa Yaa Sheikh, kuma bata manta maganar da Maimoon ta faɗa mata ba, idan kana son mutum da zarar wata macen ta raɓesa zaka ji kishinsa, ita a yanzu ta kasa fahimtar me ya sa taji komai ya dameta zuciyarta babu daɗi ne? Da wannan tunanin Ummul ta dawo ɗakin tare da ce mata "Ki saka hijab ɗin, kije Abban naki yana kira zai mayar dake" ta kalli Ummul sosai amma bata ce komai ba, hijabin a hannu ta nufi part ɗinsa. Ummul ta girgiza kai tana sakin murmushi kawo yanzu ta gama gane abin da ke damun Halisarta ta fahimci zallar rigima da shagwaɓa ce ke damunta akan dalili mara toshe. Yana zaune hannunsa riƙe da azkar yana dubawa yaji saukar siririyar muryarta tayi sallama, amsata ya yi a rai, yana mai ɗago kansa tsaye ya ganta taƙi ƙarasuwa sai cukurkuɗe hijab ɗin hannunta take. Shi bai fiya son yin surutu ba kwana biyu kuma tana neman sashi, gashi kamar ciwon kanshi na neman ta shi. Ajjiye azkar ɗin hannunsa ya yi, tare da miƙa mata hannunsa alamar tazo, kanta a ƙasa ta matsa inda yake zata zame a ƙasan ƙafafuwansa ta zauna a ƙasa ya kamo hannuna tare da zaunar da ita a gefen shi yana kafeta da idanunsa. Kafin ya ce komai ta fashe da kuka sosai tana jan numfashi, ya tallafo haɓarta da hannunsa mai taushi idanunsa na yawo a fuskarta. "Ya akai? Ke dawa?" Ya faɗa yana mai sauke numfashi tare da jan jikinsa zuwa jikin kujerar. Muryata na rawa ta ce "Abba gida zani, ni Dadata zan koma" ya lumshe ido kana ya buɗe a sauƙaƙe cikin son dakatar da kukan dake neman fasa masa kai ya ce. "Karatun fa? Ban son rigima" ta girgiza suna haɗa ido ta tura masa baki ta ce "Shi ma banso, kuma..." Sai kuma tai shiru tana ɗauke kai. Kallon yadda fuskarta tai jajir ya yi sosai duk ta birgita kanta sbd rigima, he's still holding her face ya fesar da iska ya ce. "Gida kike so? Ta ɗaga masa sai kuma ta ce "Eh wajan Dada zaka kaini kaji Abba" "Baki son Malam?" Ya tambaya kai tsaye domin shawo kan rigimar tata, ta riƙe hannunsa ta ce "Ina so bana, to ba naga Anti Zahrah ta rungomeka ba, shi ne naji kawai kuka yazo mini kaga gwanda na tafi gida" ya miƙe da sauri tare da shigewa bedroom ɗinsa not too long ya dawo fuska a kame, a tsaye ya sameta kallon da yake masa yasa ta saka hijab ɗin. Kana tabi bayansa babu kowa a main parlour dan haka ya nufi compound direct. Yana zuwa Umar-khan na fitowa daga mota tare da faɗin. "Good Mrng Yaa Lee" kai ya ɗaga masa ya shiga bayan mota, itama Halisa ta shiga bayan motar gatekeeper ya buɗe musu fita. Sun jima da tafiya amma abin mamaki Halisa bata ce komai ba, ko Umar-khan bata gaisar ba, a haka suka ƙarasa Al Aqeeq International School. Umar-khan ya yi parking a harabar makarantar tare da fita yabar musu motar, ƙoƙarin buɗe motar take ta fita taji ya kamo hannunta taƙi yarda ta kallesa alamar dai She's still angry with him. Wani sirrin baƙin zare ya ɗaura mata a hannunta, ya riƙo hannun da kyau ta yadda dole ne ta matso kusa dashi idan taji an jawota, sukai kusa da juna. "Ƴar fillo" ya ce a hankali da sauri ta kallesa sai taga ba ita yake kallo ba, ta ce "gidan zaka bayar dani?" Sai a lokacin ya juya gaba ɗaya zuwa gareta a hankali numfashinsa ke sauka cikin murya ta yanayin gajiya da kasala ya ce. "Anti ba zata sake ba, Amma idan Anti bata rungome Malam ba waye zai rungome shi?" Bakinta na rawa ta ce "Ni matar malam zanyi" ya buɗe ido sosai da sosai yana mmkin ƙarfin halinta. "Da gaske ni kullum sai na rungome ka nace maka mijina" bashi da wani option wanda ya shige bin bakin mganar da kallo ya daɗe yana kallonta kafin ya ce. "Uhm" da sauri bakinta na rawa ta ce "Ai na iya bari ka gani" kafin ya yi magana ko wani yunƙuri yaji gaba ɗaya ta zagaye hannuwanta tare da rungome shi, ta ɗora kanta a ƙirjinsa, ya buɗe idanu da sauri cikin In-inar data zo masa ya ce. "Su...su... Subuhanallah Ya Allah.... Ta saki dry sosai ta ce "Abba Allah na iya kaji ai?" He was completely lost for words and just shook his head. Bayan wasu giftawar seconds ya nuna mata ƙofa da hannu ta buɗe ƙofa tare da fita, a hankali shima ya buɗe ƙofa ya fita tare da fitowa yana ƙara covering jikinsa da kyakkyawar shigar dake jikinsa. Umar-khan na ganin fitowar Yaa Sheikh ya ƙarasu wajan yana mai sakin murmushi,kai tsaye office ɗin headmaster school ɗin Yaa Sheikh ya nufa, gaba ɗaya teachers na school mmkin ganin Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu a cikin makarantarsu ya kama su, kowa sai durƙusawa yake yana miƙa gaisuwa a nutse cike da kamala nutsuwa yake ɗaga musu hannu yana ƙara kame kansa wanda yake fidda kwarjinin shi. Cikin mutunci Headmaster ɗin mai suna Ayyan ya miƙe yana gaida Yaa Sheikh. Umar-khan ya ce "you did the interview for her, then you look at the one class that is suitable for her" Headmaster ɗin ya kalli Halisa cike da birgewa ya ce. "What's your name?" Tai ƙasa da kanta sam bata ji me yace ba, balle ta fahimci me yake cewa. Ya ɗauka bata gane english sai ya juya zuwa cewa. "ma asmuk? kam eumarka?" Nan ma tai shiru Ayyan ya kalli Yaa Sheikh cike da martabawa ya ce "سنضعها في الصف الأول حتى تتمكن من أخذ الدروس" _“Zamu sakata a matakin farko domin ta fara darasin”_ cewar Ayyan Yaa Sheikh ya numfasa ba dai ce komai ba. Ayyan ɗin ya ce. "Zata samu gogewa cikin ƙaramin lokaci Insha Allah, kuma a nemata mai darasi a gida,that will help her study more" Umar-khan ya yi murmushi ya ce "How long do you think she can take the time before she can learn everything, and get experience" Ayyan ya ɗan kalli Halisa yana karantar how smart she's kafin ya ce "I can't say how long it will take,But she will get good academic training" Umar-khan ya ce "that's good, amma matar...." Gyaran Muryar da Yaa Sheikh ya yi ya hana Umar-khan faɗin abin da ya ke shirin faɗa ɗin. Yaa Sheikh ne ya fara miƙewa yana kallon lokaci a nutse ya ce. "A kula, banda wasa" ta miƙe tsaye tana shirin yin magana ya yi waje abinsa domin yasan zata iya faɗin abin da ba shikenan ba, bai shirya ɗaukan abin kunyarta cikin mutane Yanzu ba. Idanunta ya cika da hawaye sosai tana neman yin kuka a haka Headmaster ɗin ya kaita Jss 1. Akan idanunta kuma motar Abban nata da Umar-khan ta fita waje. Ita ɗaya ce a table nata, gaba ɗaya class ɗin basu da yawa dukkansu farare dasu gwanin sha'awa, itama ta saje dasu sbd farin da take dashi mai tsari. Shiru tayi tana kallon kowa da idanu kowa na ajin harkar gabansa yake a haka Headmaster ya gabatar da ita ya fita. Babu jimawa wani kyakkyawan balarabe ya shigo cikin jallabiya ash ya ɗora half ɗin hula a kansa, bai tsaya jiran gaisuwarsu ba. Ya nufi blackboard inda suke duba kamar computer haka ya shiga latsa abubuwa sai ga sunan subject ya fito _Social studies_ A ƙasa kuma aka rubuta _MEANING, SCOPE AND NATURE OF SOCIAL STUDIES_ Matashin ya kalli students ɗin dake gabansa, har lokacin idanunsa bai kai inda Halisa take ba, cikin kamala ya ce. "Alhmd, yau zamu fara da meaning na social studies, please who can tell me the full meaning of Social studies?" Duk sukai shiru ya ce. "It's okay" ya ɗan duba abu kaɗan kana ya mai da attention nasa ga ɗaliban ya ce. _“Social studies can be defined as the study of man and his environment. Social studies can also be defined as the totality of man’s physical and social environment”_ daga nan ya yi musu explanation yadda zasu fahimta ya saka english ya saka Larabci maybe they can understand very well. Yana ƙoƙarin yin magana yaji ance. "To aradu nidai tunda ka fara magana ban san me kace ba, idan zaka faɗa da hausa kawai ka faɗa ko kayi shiru" ya juya gaba ɗaya zuwa direction ɗin da daddaɗar muryar dake tashi, yana juya a ƙaramin bakinta idanunsa ya sauka, magana take sosai ko haɗiyar yawo ba tayi. AZAAN ya ware fararen idanunsa akanta da kyau, da alama ita ɗin new student ce, yasan magana take amma baya gane me take cewa sosai, ya dai san hausa take. Ya ɗauke bai tankata ba ya ce. _“SCOPE OF SOCIAL STUDIES”_ _The word “man” in the definition given above connotes human beings while man’s environment has a huge influence on mankind in all spheres of life. Man’s environment affect their language, dressing, food and every other thing one can think of in the society,_ _Man also interacts with two environments which are:_ Physical environment (Natural) Social environment (Artificial)". "Tab ni dai dama ba wannan makarantar aka sani ba, malamin ba babu abin da ya iya" Azaan ya dubi Halisa ya ce "What's your name" ta tura ƙaramin bakinta ta ce "Me kace?" Wata wacce ba zata shige age mate ɗin Halisa ba mai suna ABIR ta ce "Ya ce ya ya sunanki?" Halisa ta ƙaramin murmushi kawai cikin siririyar murya ta ce "Halisa Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu" Azaan ya buɗe idanu da kyau cike da mamakin jin sunan data alaƙanta kanta dashi, Yaa Sheikh take nufi ko wanne? Dama yana da yarinya yaushe ma ya yi aure har ya samu yarinya kamarta?. Azaan ya ce. "Abir make her understand, explain to her" Abir ta ce "Okey Sir" mai Hali baya fasawa domin Azaan na shirin fita ta ce "Kuma na manta na faɗa maka ina da aure" Azaan ya kalleta sai kawai ya fice dan ya lura bama tasan shi kansa auren ba har take cewa haka. Ya tafi cike da sha'awar surutunta wanda ya birgesa lokaci guda. Abir taiwa Halisa bayanin komai na topic ɗin cikin harshen hausa, ta ce amma ta rage surutu da yawa a haka ta ƙare zaman makarantar wani karatun ta gane wani a'a, Umar-khan da kansa yazo ɗaukanta sbd Yaa Sheikh yana can wajan lecture ba zai samu dama ba. Sarki Ahmad Nuran Kingdom. Da sauri yake tafiya hannunsa zube cikin aljihu cikin yanayin kaɗuwa da kuma tashi hankali, saukarsa kenan ƙasar kullum cikin tafiye-tafiye yake, kana kallon fuskarsa kasan baya cikin nutsuwa da walwala. Ko'ina ya gilma acikin gidan sarautar bayi da kuyangi ke zubewa suna gaida shi, amma kallon arziƙi basa samu daga gare shi. Kai tsaye sashin Fulani Atine ya nufa, wata kuyanga ta sanar da Fulani Atine zuwan yarima cikin jin daɗi ta bashi izinin shigowa bayan ta sallami hadiman nata. Tsaye ya yi yana kallonta kafin ta ce. "Meke faruwa da kai El-bashir? Yaushe ka tafi da har zaka dawo?" Yaƙi magana sai huce yake tamkar zakin dake neman abinci bai samu ba. "Wannan ɓacin ran na mene What is the reason for bringing you back to this country now?" Ya ɗauke idanunsa cikin ɗaga murya ya ce "Idan ina raye sai naga bayan Yaa Sheikh hankalina zai kwanta, sai na tabbatar ya wahala a rayuwa kamar yadda ya wahalar dani, zan tirkesa na musguna masa kamar yadda ya sanya ni cikin damuwa da ƙonar zuciya na tsayin shekaru, sanyi amfani da uniform ɗin dake jikina na police na jasa zuciya hanyar da zata ɓata suna da martabar da yake iko da su, ba zan taɓa farin ciki ba muddin ina ganin gilmar Yaa Sheikh a duniya" Fulani Atine tayi murmushi tana mmkin zafin zuciyar da El-bashir yake da ita, a hankali ta ce "El-bashir duk bai kai wannan extent ɗin ba, pls i want u to calm down" cikin zafin zuciya El-bashir ya ce "Ya kai har ya shige extent ɗin da da kike faɗa, a wannan karan dole nayi gaba da gaba da Yaa Sheikh dole nai amfani da mutum mafi kusanci da shi wajan ruguza rayuwarsa data ahhalinsa" Fulani Atine ta ce "Kana da hujja kenan? kana da shaidar da zaka iya kurfanar da Yaa Sheikh a court? Kada ka manta lokacin da al'amarin nan ya faru Yaa Sheikh baya ƙasar bare ka zurfafa cewa shi ya aikata, kada ka tirke kanka maimakon Aliyu, nice shaidarka akan idanuna komai ya faru" El-bashir ya riƙe hannun Fulani Atine ya ce "Ki taimaka mini na ɗauki revenge akan Yaa Sheikh, ba zan iya ba, na kasa haƙura na kasa jurewa Fulani, ya rabani da jin daɗina" Fulani Atine ta ce "Kafin ɗaukan fansa, dole ka nemi kusanci da Yaa Sheikh, dole ka nemi gurbi a zuciyar ƴar fillon da ake magana, kasan yadda kayi ta fifitaka akan shi" El-bashir yai shiru for some minutes kafin ya ce "Mene amfanin saka ƴar fillo cikin al'amarin nan?" Fulani tai murmushi yaro yaro ne, daman ance daka na gaba ake gane zurfin ruwa, ta ce "Idan ka taɓa ƴar fillo kamar ka taɓa zuciyar dake sarrafa tunani Yaa Sheikh ne, nasan abin da kai baka sani ba, kayi hakan" ya shiga safa da marwa He was completely at a loss, unable to understand what she was saying to him. "Nayi masa da baibayi ta ko'ina ina da investigator a cikin ma'aikatan dake aiki a can gidansa na Madina" yana faɗin hakan ya fice rai ɓace. "Well-done El-bashir Ahmad Nuran Sarki, kana yin komai bisa tsari kamar yadda aka shirya" Fulani Atine ta faɗa tana bin bayansa da kallo. Ma martaba Ahmad Sarki ne ke tafiya shi da Khalil yana yi masa bayanin sauyawar da El-bashir ya yi cikin kwana biyu. Mai martaba na ƙoƙarin yin magana El-bashir yazo ya shige ta gabansu tamkar zai ta shi sama, meke damun El? Kamar wanda ya zauce ko wani abu ya taɓa tunaninsa? "That's what am going to tell you, El ya sauya ko dai akwai abin da yake faruwa ne?" Mai martaba ya numfasa bai ce komai ba ya shige babban sashinsa, Khalil kuma ya nufi wajan Oum Juwairah. Halisa na zaune tana duba Assignment ɗin da aka bata juya littafin kawai take amma ta rasa ta ina zata fara. Tunda ta dawo gida bata ji motsin Yaa Sheikh ba, ko taji Ummul ta ce akai masa abinci. Ta miƙe tsaye jikinta sanye da wata riga mai kyau wacce tazo mata iya gwiwa wandon jikinta 3gauter ne. Zahrah data fito daga ɗakinta zuwa parlour hannunta riƙe da plate ɗin da aka soya masa ƙwai ta kalli Halisa ta ce. "Ke ubanwa ya ce kina saka wannan kayan a cikin gidan nan?" Halisa ta kalleta ta ɗauke kai ita bata ita take ba "Kan uba? Ke dan ƙaniyarki ni sa'ar ta ruga ce ina magana kina jina?" Halisa ta murguɗa baki cikin tsiwa ta ce "Ban ɗauka magana ki ke ba" hannu ta ɗaga zata wanka mata mari taji an riƙe hannu, ƙamshin Roja daya cika parlourn ya gama shaida mata wanda ya riƙe ta. Ta juya da sauri har lokacin yana riƙe da hannunta ta ce. "My Excellency yarinyar ta fara raina ni ne, ka barni naci.." wata kyakkyawar tsawa ya daka mata wacce bata taɓa jin irinta ba, Halisa ta firgita da tsawar ga Yaa Sheikh ta kwasa da gudu zuwa part ɗin Ummul tana haki. Zahrah ta ce "Tsawa kai mini akan wannan mara gata da ƴancin ƴar aiki na ce ita ga Yaa Sheikh?" Ya saki hannunta fuska kame yana gyara yanayinsa ya ce. "Ba a kanta ba, Akan zagin da ki ke mana, idan zaki ki bari kije waje" ya faɗa a taƙaice kwarjininsa yasa Zahrah kasa tanka masa a ranta kuma ta ɗauki niyyar cin uban Halisa. Cike da kissa da buƙatar mijinta kusa da ita, cikin dake jikinta ya ƙara sanya mata son kasancewa da namiji ƙwarai da gaske. Ta rungome Yaa Sheikh tana shassheƙar kuka ta ce "Amma kasan ni ba sa'ar ta bace, kawai zan mayar da ita, tunda akwai masu aiki a gidan" ya yi mata shiru shi dai bai kuma hanata rungome shi ba, kallo ɗayan da ya yi mata ya karanci yanayinta. Ganin abin da take ƙoƙarin yin yasa Yaa Sheikh faɗin. "Asstagafirullah Allah" Zahrah ta tsaya tana kallon shi kafin ta ce "what do you mean by that? Am your wife exit?" Ya zameta daga jikinsa tare da juyawa zuwa part ɗinsa sai da ya kusa shigewa ya ce "Lokacin Sallah, akwai alwala tare dani" tai murmushin jin daɗin ganin ya juya da alama alwalar da yake riritawa ta lalace dalilin rungumar shi da tayi. "Shikenan, anjima zan zo" ta juya zuwa nata part ɗin. Ummul ta kalli Halisa dana cewa "Wannan hakin fa? yana da kyau ki nutsu sosai matar malam" Halisa ta dafe ƙirji ta ce "Wallahi na tsorata sosai Ummul, Allah yasa ba dokan Anti Zahrah ba" Ummul ta dubeta ta ce "Doka wanne iri, ni wannan Assignment ɗin naki ba Abin da na gane, kije wajan Abban naki" ta kwanta cinyar Ummul tunanin Dadarta ya faɗo mata a rai. Tai shiru can kuma ta ce "Ummul Abba mijina ne ko?" "Me ya sa kike tambaya matar malam?" Cewar Ummul. Halisa ta miƙe zaune zance na cinta ta ce "Ummul naji baya ce mini matar shi, kuma ni bana son naga Anti Zahrah..." Wayar Ummul tai ƙara hakan ya hana Halisa ƙarasa maganar. Bayan kammala wayar Ummul ta ce "kije ya duba littafin naki,ko a buge ki a makaranta" Halisa ta ɓata fuska ta ce "haka kurum ya dakeni, zaro ido naga ya yi fa?" "Ko zai daki kowa, Ai banda matar malam, kawai baya son taurin kai ne, kuma na lura kina da shi tun ba yau ba" Halisa zata sake magana Ummul ta ce "Tashi kije, sai ki dawo kici dinner muyi karatu" ta miƙe tana ɗora hula akanta tana tafe tana waƙa da fillatanci. A hanya taci karo da Bara'at tai mata murmushi. A hankali ta shiga parlourn dake part ɗinsa, gaba ɗaya baya cikin parlourn sai kyakkyawan ƙamshin daya bari wanda yake tashi a hankali, tabi ƙofofin dake parlourn da kallo ta rasa wanne Kofar bedroom ɗinsa, a hankali take tafiya kamar mara gasky tana raɓewa jikin bango ta shiga leƙa wani ɗaki tsarin bedroom kaɗai ya tabbatar mata shi ne. Ji tayi an tsaya a bayanta ta juya da sauri taci karo dashi tsaye towel a hannunsa yana tsane gashin kansa daya kwanto, ganin ruwa na zuba a jikinsa tasan wanka yayi, maimakon taji kunya a matsayinta cikakkiyar bafullatana sai ta zubawa wani waje a jikinsa ido. Ya tsare ta da idanu. "Abba" ta faɗa dimple ɗinta na lomawa ya ɗauke kai ya ce. "Me kike leƙe? Kin yi ajjiya ne?" Ya tambaya yana bata hanya ta tura baki fuska a narke sai juya bakinta take ta ce "Ummul ta ce ka koyan karatu, ni ba kai nake nema ba" ya dubi bakin maganar da kyau, ya ɗauke kai wato fushi take har yanzu. Ganin yaƙi bata amsa ta saki kuka tana juyawa zata bar wajan, ya damƙi hannunta ya dawo da ita gabansa. Cikin kula da tausasa harshe ƙamshin shower gel yana fita daga cikinsa ya saka hannu tare da tallafo haɓarta ɗaya hannun ya dafa kanta dashi, tayi saurin riƙe ƙugunsa da duk hannunta biyu. "Abba" ta ƙara faɗa idanun na cika da hawaye wanda suka ƙarawa idanunta sheƙi. "Rigima dai matar malam, nayi busy banje makaranta ba" ta tsora masa idanu masa idanu tana ƙara riƙe ƙugunsa ta ce "To darasi zaka duba mini, Abba kuma me ya sa Anti Zahrah take riƙe ka" ya saki fuskar yana dafe kai ta saki kuka zata juya ta fita ya saka hannu ya ɗaga ta cak tare da yin bedroom ɗinsa da ita... If you read for free🤷🏾‍♀️ it's 500 via 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman fidelity bank shaidar biya 08119237616. Ta saki dry sosai ta ce "Abba Allah na iya kaji ai?" He was completely lost for words and just shook his head. Bayan wasu giftawar seconds ya nuna mata ƙofa da hannu ta buɗe ƙofa tare da fita, a hankali shima ya buɗe ƙofa ya fita tare da fitowa yana ƙara covering jikinsa da kyakkyawar shigar dake jikinsa. Umar-khan na ganin fitowar Yaa Sheikh ya ƙarasu wajan yana mai sakin murmushi,kai tsaye office ɗin headmaster school ɗin Yaa Sheikh ya nufa, gaba ɗaya teachers na school mmkin ganin Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu a cikin makarantarsu ya kama su, kowa sai durƙusawa yake yana miƙa gaisuwa a nutse cike da kamala nutsuwa yake ɗaga musu hannu yana ƙara kame kansa wanda yake fidda kwarjinin shi. Cikin mutunci Headmaster ɗin mai suna Ayyan ya miƙe yana gaida Yaa Sheikh. Umar-khan ya ce "you did the interview for her, then you look at the one class that is suitable for her" Headmaster ɗin ya kalli Halisa cike da birgewa ya ce. "What's your name?" Tai ƙasa da kanta sam bata ji me yace ba, balle ta fahimci me yake cewa. Ya ɗauka bata gane english sai ya juya zuwa cewa. "ma asmuk? kam eumarka?" Nan ma tai shiru Ayyan ya kalli Yaa Sheikh cike da martabawa ya ce "سنضعها في الصف الأول حتى تتمكن من أخذ الدروس" _“Zamu sakata a matakin farko domin ta fara darasin”_ cewar Ayyan Yaa Sheikh ya numfasa ba dai ce komai ba. Ayyan ɗin ya ce. "Zata samu gogewa cikin ƙaramin lokaci Insha Allah, kuma a nemata mai darasi a gida,that will help her study more" Umar-khan ya yi murmushi ya ce "How long do you think she can take the time before she can learn everything, and get experience" Ayyan ya ɗan kalli Halisa yana karantar how smart she's kafin ya ce "I can't say how long it will take,But she will get good academic training" Umar-khan ya ce "that's good, amma matar...." Gyaran Muryar da Yaa Sheikh ya yi ya hana Umar-khan faɗin abin da ya ke shirin faɗa ɗin. Yaa Sheikh ne ya fara miƙewa yana kallon lokaci a nutse ya ce. "A kula, banda wasa" ta miƙe tsaye tana shirin yin magana ya yi waje abinsa domin yasan zata iya faɗin abin da ba shikenan ba, bai shirya ɗaukan abin kunyarta cikin mutane Yanzu ba. Idanunta ya cika da hawaye sosai tana neman yin kuka a haka Headmaster ɗin ya kaita Jss 1. Akan idanunta kuma motar Abban nata da Umar-khan ta fita waje. Ita ɗaya ce a table nata, gaba ɗaya class ɗin basu da yawa dukkansu farare dasu gwanin sha'awa, itama ta saje dasu sbd farin da take dashi mai tsari. Shiru tayi tana kallon kowa da idanu kowa na ajin harkar gabansa yake a haka Headmaster ya gabatar da ita ya fita. Babu jimawa wani kyakkyawan balarabe ya shigo cikin jallabiya ash ya ɗora half ɗin hula a kansa, bai tsaya jiran gaisuwarsu ba. Ya nufi blackboard inda suke duba kamar computer haka ya shiga latsa abubuwa sai ga sunan subject ya fito _Social studies_ A ƙasa kuma aka rubuta _MEANING, SCOPE AND NATURE OF SOCIAL STUDIES_ Matashin ya kalli students ɗin dake gabansa, har lokacin idanunsa bai kai inda Halisa take ba, cikin kamala ya ce. "Alhmd, yau zamu fara da meaning na social studies, please who can tell me the full meaning of Social studies?" Duk sukai shiru ya ce. "It's okay" ya ɗan duba abu kaɗan kana ya mai da attention nasa ga ɗaliban ya ce. _“Social studies can be defined as the study of man and his environment. Social studies can also be defined as the totality of man’s physical and social environment”_ daga nan ya yi musu explanation yadda zasu fahimta ya saka english ya saka Larabci maybe they can understand very well. Yana ƙoƙarin yin magana yaji ance. "To aradu nidai tunda ka fara magana ban san me kace ba, idan zaka faɗa da hausa kawai ka faɗa ko kayi shiru" ya juya gaba ɗaya zuwa direction ɗin da daddaɗar muryar dake tashi, yana juya a ƙaramin bakinta idanunsa ya sauka, magana take sosai ko haɗiyar yawo ba tayi. AZAAN ya ware fararen idanunsa akanta da kyau, da alama ita ɗin new student ce, yasan magana take amma baya gane me take cewa sosai, ya dai san hausa take. Ya ɗauke bai tankata ba ya ce. _“SCOPE OF SOCIAL STUDIES”_ _The word “man” in the definition given above connotes human beings while man’s environment has a huge influence on mankind in all spheres of life. Man’s environment affect their language, dressing, food and every other thing one can think of in the society,_ _Man also interacts with two environments which are:_ Physical environment (Natural) Social environment (Artificial)". "Tab ni dai dama ba wannan makarantar aka sani ba, malamin ba babu abin da ya iya" Azaan ya dubi Halisa ya ce "What's your name" ta tura ƙaramin bakinta ta ce "Me kace?" Wata wacce ba zata shige age mate ɗin Halisa ba mai suna ABIR ta ce "Ya ce ya ya sunanki?" Halisa ta ƙaramin murmushi kawai cikin siririyar murya ta ce "Halisa Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu" Azaan ya buɗe idanu da kyau cike da mamakin jin sunan data alaƙanta kanta dashi, Yaa Sheikh take nufi ko wanne? Dama yana da yarinya yaushe ma ya yi aure har ya samu yarinya kamarta?. Azaan ya ce. "Abir make her understand, explain to her" Abir ta ce "Okey Sir" mai Hali baya fasawa domin Azaan na shirin fita ta ce "Kuma na manta na faɗa maka ina da aure" Azaan ya kalleta sai kawai ya fice dan ya lura bama tasan shi kansa auren ba har take cewa haka. Ya tafi cike da sha'awar surutunta wanda ya birgesa lokaci guda. Abir taiwa Halisa bayanin komai na topic ɗin cikin harshen hausa, ta ce amma ta rage surutu da yawa a haka ta ƙare zaman makarantar wani karatun ta gane wani a'a, Umar-khan da kansa yazo ɗaukanta sbd Yaa Sheikh yana can wajan lecture ba zai samu dama ba. Sarki Ahmad Nuran Kingdom. Da sauri yake tafiya hannunsa zube cikin aljihu cikin yanayin kaɗuwa da kuma tashi hankali, saukarsa kenan ƙasar kullum cikin tafiye-tafiye yake, kana kallon fuskarsa kasan baya cikin nutsuwa da walwala. Ko'ina ya gilma acikin gidan sarautar bayi da kuyangi ke zubewa suna gaida shi, amma kallon arziƙi basa samu daga gare shi. Kai tsaye sashin Fulani Atine ya nufa, wata kuyanga ta sanar da Fulani Atine zuwan yarima cikin jin daɗi ta bashi izinin shigowa bayan ta sallami hadiman nata. Tsaye ya yi yana kallonta kafin ta ce. "Meke faruwa da kai El-bashir? Yaushe ka tafi da har zaka dawo?" Yaƙi magana sai huce yake tamkar zakin dake neman abinci bai samu ba. "Wannan ɓacin ran na mene What is the reason for bringing you back to this country now?" Ya ɗauke idanunsa cikin ɗaga murya ya ce "Idan ina raye sai naga bayan Yaa Sheikh hankalina zai kwanta, sai na tabbatar ya wahala a rayuwa kamar yadda ya wahalar dani, zan tirkesa na musguna masa kamar yadda ya sanya ni cikin damuwa da ƙonar zuciya na tsayin shekaru, sanyi amfani da uniform ɗin dake jikina na police na jasa zuciya hanyar da zata ɓata suna da martabar da yake iko da su, ba zan taɓa farin ciki ba muddin ina ganin gilmar Yaa Sheikh a duniya" Fulani Atine tayi murmushi tana mmkin zafin zuciyar da El-bashir yake da ita, a hankali ta ce "El-bashir duk bai kai wannan extent ɗin ba, pls i want u to calm down" cikin zafin zuciya El-bashir ya ce "Ya kai har ya shige extent ɗin da da kike faɗa, a wannan karan dole nayi gaba da gaba da Yaa Sheikh dole nai amfani da mutum mafi kusanci da shi wajan ruguza rayuwarsa data ahhalinsa" Fulani Atine ta ce "Kana da hujja kenan? kana da shaidar da zaka iya kurfanar da Yaa Sheikh a court? Kada ka manta lokacin da al'amarin nan ya faru Yaa Sheikh baya ƙasar bare ka zurfafa cewa shi ya aikata, kada ka tirke kanka maimakon Aliyu, nice shaidarka akan idanuna komai ya faru" El-bashir ya riƙe hannun Fulani Atine ya ce "Ki taimaka mini na ɗauki revenge akan Yaa Sheikh, ba zan iya ba, na kasa haƙura na kasa jurewa Fulani, ya rabani da jin daɗina" Fulani Atine ta ce "Kafin ɗaukan fansa, dole ka nemi kusanci da Yaa Sheikh, dole ka nemi gurbi a zuciyar ƴar fillon da ake magana, kasan yadda kayi ta fifitaka akan shi" El-bashir yai shiru for some minutes kafin ya ce "Mene amfanin saka ƴar fillo cikin al'amarin nan?" Fulani tai murmushi yaro yaro ne, daman ance daka na gaba ake gane zurfin ruwa, ta ce "Idan ka taɓa ƴar fillo kamar ka taɓa zuciyar dake sarrafa tunani Yaa Sheikh ne, nasan abin da kai baka sani ba, kayi hakan" ya shiga safa da marwa He was completely at a loss, unable to understand what she was saying to him. "Nayi masa da baibayi ta ko'ina ina da investigator a cikin ma'aikatan dake aiki a can gidansa na Madina" yana faɗin hakan ya fice rai ɓace. "Well-done El-bashir Ahmad Nuran Sarki, kana yin komai bisa tsari kamar yadda aka shirya" Fulani Atine ta faɗa tana bin bayansa da kallo. Ma martaba Ahmad Sarki ne ke tafiya shi da Khalil yana yi masa bayanin sauyawar da El-bashir ya yi cikin kwana biyu. Mai martaba na ƙoƙarin yin magana El-bashir yazo ya shige ta gabansu tamkar zai ta shi sama, meke damun El? Kamar wanda ya zauce ko wani abu ya taɓa tunaninsa? "That's what am going to tell you, El ya sauya ko dai akwai abin da yake faruwa ne?" Mai martaba ya numfasa bai ce komai ba ya shige babban sashinsa, Khalil kuma ya nufi wajan Oum Juwairah. Halisa na zaune tana duba Assignment ɗin da aka bata juya littafin kawai take amma ta rasa ta ina zata fara. Tunda ta dawo gida bata ji motsin Yaa Sheikh ba, ko taji Ummul ta ce akai masa abinci. Ta miƙe tsaye jikinta sanye da wata riga mai kyau wacce tazo mata iya gwiwa wandon jikinta 3gauter ne. Zahrah data fito daga ɗakinta zuwa parlour hannunta riƙe da plate ɗin da aka soya masa ƙwai ta kalli Halisa ta ce. "Ke ubanwa ya ce kina saka wannan kayan a cikin gidan nan?" Halisa ta kalleta ta ɗauke kai ita bata ita take ba "Kan uba? Ke dan ƙaniyarki ni sa'ar ta ruga ce ina magana kina jina?" Halisa ta murguɗa baki cikin tsiwa ta ce "Ban ɗauka magana ki ke ba" hannu ta ɗaga zata wanka mata mari taji an riƙe hannu, ƙamshin Roja daya cika parlourn ya gama shaida mata wanda ya riƙe ta. Ta juya da sauri har lokacin yana riƙe da hannunta ta ce. "My Excellency yarinyar ta fara raina ni ne, ka barni naci.." wata kyakkyawar tsawa ya daka mata wacce bata taɓa jin irinta ba, Halisa ta firgita da tsawar ga Yaa Sheikh ta kwasa da gudu zuwa part ɗin Ummul tana haki. Zahrah ta ce "Tsawa kai mini akan wannan mara gata da ƴancin ƴar aiki na ce ita ga Yaa Sheikh?" Ya saki hannunta fuska kame yana gyara yanayinsa ya ce. "Ba a kanta ba, Akan zagin da ki ke mana, idan zaki ki bari kije waje" ya faɗa a taƙaice kwarjininsa yasa Zahrah kasa tanka masa a ranta kuma ta ɗauki niyyar cin uban Halisa. Cike da kissa da buƙatar mijinta kusa da ita, cikin dake jikinta ya ƙara sanya mata son kasancewa da namiji ƙwarai da gaske. Ta rungome Yaa Sheikh tana shassheƙar kuka ta ce "Amma kasan ni ba sa'ar ta bace, kawai zan mayar da ita, tunda akwai masu aiki a gidan" ya yi mata shiru shi dai bai kuma hanata rungome shi ba, kallo ɗayan da ya yi mata ya karanci yanayinta. Ganin abin da take ƙoƙarin yin yasa Yaa Sheikh faɗin. "Asstagafirullah Allah" Zahrah ta tsaya tana kallon shi kafin ta ce "what do you mean by that? Am your wife exit?" Ya zameta daga jikinsa tare da juyawa zuwa part ɗinsa sai da ya kusa shigewa ya ce "Lokacin Sallah, akwai alwala tare dani" tai murmushin jin daɗin ganin ya juya da alama alwalar da yake riritawa ta lalace dalilin rungumar shi da tayi. "Shikenan, anjima zan zo" ta juya zuwa nata part ɗin. Ummul ta kalli Halisa dana cewa "Wannan hakin fa? yana da kyau ki nutsu sosai matar malam" Halisa ta dafe ƙirji ta ce "Wallahi na tsorata sosai Ummul, Allah yasa ba dokan Anti Zahrah ba" Ummul ta dubeta ta ce "Doka wanne iri, ni wannan Assignment ɗin naki ba Abin da na gane, kije wajan Abban naki" ta kwanta cinyar Ummul tunanin Dadarta ya faɗo mata a rai. Tai shiru can kuma ta ce "Ummul Abba mijina ne ko?" "Me ya sa kike tambaya matar malam?" Cewar Ummul. Halisa ta miƙe zaune zance na cinta ta ce "Ummul naji baya ce mini matar shi, kuma ni bana son naga Anti Zahrah..." Wayar Ummul tai ƙara hakan ya hana Halisa ƙarasa maganar. Bayan kammala wayar Ummul ta ce "kije ya duba littafin naki,ko a buge ki a makaranta" Halisa ta ɓata fuska ta ce "haka kurum ya dakeni, zaro ido naga ya yi fa?" "Ko zai daki kowa, Ai banda matar malam, kawai baya son taurin kai ne, kuma na lura kina da shi tun ba yau ba" Halisa zata sake magana Ummul ta ce "Tashi kije, sai ki dawo kici dinner muyi karatu" ta miƙe tana ɗora hula akanta tana tafe tana waƙa da fillatanci. A hanya taci karo da Bara'at tai mata murmushi. A hankali ta shiga parlourn dake part ɗinsa, gaba ɗaya baya cikin parlourn sai kyakkyawan ƙamshin daya bari wanda yake tashi a hankali, tabi ƙofofin dake parlourn da kallo ta rasa wanne Kofar bedroom ɗinsa, a hankali take tafiya kamar mara gasky tana raɓewa jikin bango ta shiga leƙa wani ɗaki tsarin bedroom kaɗai ya tabbatar mata shi ne. Ji tayi an tsaya a bayanta ta juya da sauri taci karo dashi tsaye towel a hannunsa yana tsane gashin kansa daya kwanto, ganin ruwa na zuba a jikinsa tasan wanka yayi, maimakon taji kunya a matsayinta cikakkiyar bafullatana sai ta zubawa wani waje a jikinsa ido. Ya tsare ta da idanu. "Abba" ta faɗa dimple ɗinta na lomawa ya ɗauke kai ya ce. "Me kike leƙe? Kin yi ajjiya ne?" Ya tambaya yana bata hanya ta tura baki fuska a narke sai juya bakinta take ta ce "Ummul ta ce ka koyan karatu, ni ba kai nake nema ba" ya dubi bakin maganar da kyau, ya ɗauke kai wato fushi take har yanzu. Ganin yaƙi bata amsa ta saki kuka tana juyawa zata bar wajan, ya damƙi hannunta ya dawo da ita gabansa. Cikin kula da tausasa harshe ƙamshin shower gel yana fita daga cikinsa ya saka hannu tare da tallafo haɓarta ɗaya hannun ya dafa kanta dashi, tayi saurin riƙe ƙugunsa da duk hannunta biyu. "Abba" ta ƙara faɗa idanun na cika da hawaye wanda suka ƙarawa idanunta sheƙi. "Rigima dai matar malam, nayi busy banje makaranta ba" ta tsora masa idanu masa idanu tana ƙara riƙe ƙugunsa ta ce "To darasi zaka duba mini, Abba kuma me ya sa Anti Zahrah take riƙe ka" ya saki fuskar yana dafe kai ta saki kuka zata juya ta fita ya saka hannu ya ɗaga ta cak tare da yin bedroom ɗinsa da ita... If you read for free🤷🏾‍♀️ it's 500 via 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman fidelity bank shaidar biya 08119237616. Kokawar ƙwace kanta take amma ta kasa ya sauke ta saman kujerar dake kusa da bed ɗin ɗakin nasa, bai kula ta ba ya nufi deep freezer ya ɗauki Apple guda ɗaya wacce tai sanyi. Cikin nutsuwarsa da son kame kansa daga yanayin da yake ciki ya nemi waje saman gado ya zauna, kyakkyawan numfashi ya sauke yana ƙara daidaita kansa a karo na babu adadi. Ya ɗago kai yana duban direction ɗin da take, dole sai ta sanya ma gantu ya miƙa hannu cikin taushin murya ya ce.. "Zonan naji, rigimar me ce?" kanta a ƙasa ta ƙarasa inda yake domin bata iya bijirewa umarninsa. Ya dubeta da kyau amma taƙi yarda ta kallesa cikin son jin meke faruwa ya kamo hannunta zuwa inda yake zaune muryarsa har kullum a taushashe ya ce. "Ya akai matar malam? waye?" Hawaye na sakko mata ta ce "Abba kai ne, Mother ta ce kai miji na ne, me ya sa kake bari Anti Zahrah take taɓa ka" ya dafe kansa cike da mmkin kaifin bakin Halisa ya ce "Ba zaki bar mganar mijin nan ba? You're too young to understand that" "Abba ina son ka ai" Ya girgiza kai ya lura rigima take ji kuma ta shirya bashi kunya a Idanun kowa. Yana mamakin yadda maganar miji ta zauna a bakinta raɗau kamar wacce akewa bita akan hakan. Ya dubeta yana dawo da ita gefensa tare da riƙe hannunta ya ce "Matar Malam ki bar mganar mijin nan, ba zaki gane ba, ki dai bar Anti ta faɗa ok?" Ta maƙale ka faɗa alamar bata amince da zancan ba kaifin ta ce "Abba...." Sai kuma tai shiru ya ɗago kanta tare da tallafo haɓarta yana duba cikin idanunta da hawaye ya kwanta. "Matar malam" ta marairaice fuska tare da faɗin "Abba yaushe zan zama matar malam ɗin? Kuma yaushe zan zama kamar Anti Zahrah nima na dinga rungomeka?" Ya kau da fuska tare da lumshe idanunsa a hankali ya ce "Baki son Antin naki tana haka? Ni kuma fa" ya ƙare maganar yana ƙara riƙe fuskarta a hannunsa da kyau, gaba ɗaya ta marairaice fuska ita a dole bata son abin da Zahrah ke masa, haka kurum ranta ke ɓaci taji kuka yazo mata ta ce "Abba zanna yi maka, da safe da rana, da daddare" ya shafa kanta cikin nutsuwa ya ce. "Kada mu fara haka, ki tsaya a ƴar rainonki" ta langwaɓe kai ta ce "Abba ni ban son rainon Ummul ta ce kayi mini karatu" bai biyewa surutun nata ba, ya amshi littafin nata duk dan a rabu lafiya, burinsa kuma bai shige ta tafi part ɗinsa ba, ko zata barshi ya samu salama daga surutun nata mara dalili da toshe. Cikin sauƙin harshen yake mata bayani akan Social studies ɗin, da kuma muhimmancinsa. Ya kama hannunta ya ɗora saman littafin a hankali ya ɗora nasa hannun akan nata ya fara nuna mata yadda zatai rubutu, yana lura da ƙwazonta ko dan akwai son karatun a ranta duk abin da ya nuna mata ɗauke shi take. Ta ɗago kai ta kallesa taga hankalinsa baya kanta gaba ɗaya ya tattara nutsuwarsa zuwa ga abin da yake nuna mata. "Abba" Halisa ta faɗa tana ƙarewa fuskar shi kallon yaƙi kulata ta leƙa fuskar shi ta ƙara cewa "Abba kana da kyau sosai, kaga gobe idan naje makaranta zance mijina ne ya yi mini aikin ko?" Nan ma bai kulata ba amma tsat yake ɗauke zancan nata a zuciyarsa tasbihi kawai yake. Taja gemunsa cikin sauri ya miƙe tsaye yana damƙa mata littafin tare da janta zuwa bakin ƙofa kamar an masa dole ya ce. "Ki kula, akwai sanyi" ta ɗaga kai tana faɗin "To Abba" har ta juya zata fita ta dawo da sauri zuwa bedroom ɗin Yaa Sheikh kuma a lokacin ya juya hannunsa ɗauke da azkar na dare yana dubawa.. Kyakkyawar rungumar data bashi da baya ya sanya Azkar ɗin suɓuce masa cikin In-inar data zo masa a lokacin zufa na yanko daga goshinsa ya ce. "Yaaa....yaaaa... Allahu ya ya... Ya Rahman, Yasubuhanallah" ta saki dry tana riƙesa ta ce "Abba kaga nayi maka ta dare sai da safe" kasa magana ya yi tana sakinsa ya buɗe ƙofar bathroom ya shige ciki... Cikin farin ciki da murna yau itama tayi abin da Anti Zahrah keyi ta nufi part ɗin Ummul. Ummul ta kalleta ta ce "Kin dai gane karatun ko?" Ta ɗaga mata kai kawai tana jan plate ɗin da Ummul ke mata, tana cikin cin abincin ta ce "Ummul kin same?" Ummul ta girgiza kai ta ce "Sai kin faɗa matar malam" Halisa ta ture abincin dan ba wata yunwa ta keji ba ta ce. "Me ya sa gumi ke fitowa a goshin Abba? Kuma naga wani abu a jikinsa ba, duk sanda na gani kaina juyawa yake" Ummul a zuciyarta addu'a take Allah ya sa ba wata maganar da zata bata Kunya zatai ba, ko wani abu ne ya faru tsakaninta da Yaa Sheikh ɗin take son faɗa, duk tai mamakin haƙurinsa, daya kawo har yanzu, ta riga tasan waye Yaa Sheikh da kuma yadda ya ɗauki al'amarin Halisa da girma ko yana jin tsoran yanayin rigima da ƙuruciyarta ne?. Halisa ta dawo da Ummul daga tunanin data tafi ta hanyar faɗin "Ummul ni ina son Abbana" Ummul ta ce "Kina iya bakinki, ba dan abinci kawai Ubangiji ya bamu ciki ba, hadda ɓoye maganar da bata da ikon a faɗa da riƙe sirri, ki nutsu idan kina wannan shirman Abban naki ba zai so ki ba" Halisa ta kwanta tana juyawa Ummul baya ta ce "to naga mijina ne, kuma ina son sa" kamar wacce aka tsikara ta miƙe da sauri domin abu biyu ne ya faɗo mata a wannan lokacin, da maganin da El-bashir ya bata, wanda take tunanin shi ne ya sanya Abban nata Yaa Sheikh yake fitar da zufar goshinsa, sai kuma tuna Dada da tayi. Ummul tabi bayanta da kallo sai kawai ta girgiza kai ta ce "Ubangiji ga Danejo ka shirya mana ita, Allah ka kawo zama na har abada tsakaninta da Aliyu, ita ce farin ciki Aliyu, Aliyu shi ne garkuwarta" Halisa na fita ta nufi part ɗin Zahrah lokacin tana tsaye gaban madubi sai turare take fesawa ajikinta, ta sanya wasu kaya kamar zata gasar rawa a club Halisa ta ce "Anti" ta juya ta kalleta ta ce "wai ke wacce daƙiƙiya ce ne? Ko acikin ƴan fulani ke daban kike, kawai ki faɗo ɗaki kamar wata dabba?" Halisa taji zagin har ƙasan zuciyarta ta kalli Zahrah ta ce "me ya sa kike haɗani da dabba? Bayan ni mutum ce kamar ke?" Zahrah ta tsaki ta ce "baki da wani suna da ya shige haka, and you'll never be like me never" ta goge hawayen idanunta ta ce "Yaushe zan miki aikin ki? Ina son ki mayar dani rugarmu, ban san haka kike ba kinyi al'ƙawarin kula dani da kuma Dadata" Zahrah tai wata dry ta ce "Aikin kin kusa gabatar da shi, dan kin gama zan mayar dake nima zamanki bai mini ba, yanzu bani da lokacin zani wajan mijina" Halisa ta kalleta da sauri zuciyarta har ɗagawa yake sbd jin zata wajan Yaa Sheikh. Ta juya idanunta fal hawaye tare da barin ɗakin. Zahrah ta nufi part ɗin Yaa Sheikh ko'ina na part ɗin gwanin sha'awa ne, ko wacce kusurwa an kafe kalmar sunan Allah, a hankali sautin ƙira'ar Alkur'ani ke tashi, amma ta nemi ƙofar bathroom ɗin nasa ta rasa. Ta juya da sauri zuwa sashin Ummul ta sameta tare da Bara'at daga tsaye ta ce "Naje part ɗin Yaa Sheikh na rasa ina ne bedroom ɗinsa, ina buƙatar sani sbd ina son kasancewa da mijina" "Amma shi mijin na son kasancewa dake?" Cewar Ummul. Zahrah ta ce "Ni matarsa ce, dole ya buƙace ni" Ummul tai murmushi ta ce "Zahrah ki zauna muyi magana mai muhimmanci, maybe ki gane sosai" Zahrah ta ce "ki riƙe maganarki mijina nake tambaya" Ummul ta ce "Malam yana kan rabuta Alkur'ani yanzu, kafin azumi yake son kammala rubutun, ba zai iya ganin kowa ba" Zahrah ta juya rai ɓace gashi masifa ke cinta kamar taci babu. Ummul bata da zaɓi wanda ya shige faɗin hakan, tasan ba lallai Zahrah ta samu abin da take so ba. Washegari tun da Halisa ta tashi bata da wani karsha shi ta wakana da tunanin ko Zahrah ta je wajan Abbanta? Tai sallah Asuba tare da Azkar ɗin da Ummul ta bata, 6:30 ta nufi kitchen tasan a nan zata samu Ummul ɗin, Tana zuwa Bara'at ta ce "Sannu da zuwa Halisa" Suhaima ta ce "Baki zo da wuri ba" tai murmushi kawai ta ce "Ina kwana Ummul?" Cike da farin ciki Ummul ta ce "Allhmd. Sanyi bai ka maki ba?" Ta ɗaga kai tana taya Bara'at aiki tare da ita suka kammala breakfast. Ummul ta bata shayin Yaa Sheikh ta kai masa bayan ta shirya zuwa kayan makaranta. Ta amshi shayin ta mufi part ɗinsa kai tsaye. Fitowar sa kenan sbd barcin da bai samu ba jiya, kana kallon yanayinsa da sauyin idanunsa kasan akwai matsala. Yana zama kan kujera ta shigo bakinta ɗauke da sallama ta ajjiya tray ɗin tana zubewa wajan ƙafafuwansa ta ce. "Abba ina kwana?" Ya jinjina tare da zuba black tea ɗin ya shiga sha a hankali ta gyara zama ta ce "Abba" ya ware ido a kanta ba tare daya tanka ta ba. Ta ce "Anti Zahrah ta zo jiya?" Hawaye ya cika idanunta ganin ya kasa cewa komai, zai gumi dake tsastsafo masa ta goshinsa jijiyoyin kansa sun ta shi. Ya ajjiye mug ɗin hannunta bayan ya gama shan tea ɗin tare da miƙewa tsaye, ta miƙe da sauri ta ce "Abba baka da lafiya?" Sai a lokacin sauke numfashi yana jin kansa kamar zai rabe yana ɗan yin gaba ya ce. "Ki kula,ba wasa" ranta bai mata daɗi ba, shi kansa ya kasa riƙe sauyin nasa gudun kada wani ya ankare baya son kuma Ummul ta san halin da ake ciki... Ta fita tana jin kamar kada taje makarantar. Har ta yini a makaranta cir bata da wata walwala haka kurum ta tsinci kanta cikin sukuni, Abir tai ƙoƙari sosai wajan fahimtar da ita duk subjects ɗin da sukai attending. Har suka taɓa hira sai lokacin ma Halisa ta saki jikinta jin Abir itama asalinta ƴar Nigeria ce. Yau ma Umar-khan ya dawo da ita ya lura da sauyin nata bai kulata ba, tunda ba huruminsa bane yin magana da matar malam ɗin. Tana shigowa gidan bata nufi part ɗin Ummul ɗin ba, ta nufi Main parlour zata shige part ɗin ta Zahrah ta ce. "Yawwa ke nake jira dama, ki shirya zamu asibiti" Halisa ta kalleta tana mmkin waye babu lfy kuma? Sai kuma gabanta ya faɗi ko dai Abbanta ne bashi da lfy, ta rikice rikicewar da Zahrah taso ta ɗaure mata kai ta ce. "Bana son shirme mene haka kuma? Kije kafin mu tafi ki gyara mini ɗaki kizo ki ɗan danna mini ƙafata" Halisa ta tsurawa cikin Zahrah idanu har bata ji abin da Zahran ta faɗa ba, tayi saurin jan riga ta rufe cikin da ya ƙara girma fiye da ko yaushe. Ta juya tare da shigewa part ɗin nata, duk ta gigice tana shiga kuma ta fara duba maganin da El-bashir ya bata, ƙila shi ne maganin da Abban nata yake sha bata sani ba. "Kayi haƙuri Abba, laifi na ne" ta faɗa a sanyaye idanunta na cika da hawaye. Zahrah ta miƙe tare da shigewa ɓangarenta, kai tsaye wayarta ta ɗauka tare da kiran number Deen, kamar wanda yake jiran kiran nata yai picking call ɗin ta ce "Akwai matsala Deen" ta cikin wayar ya ce. "Yanzu muka fara samun matsala idan har ba zaki abin da ya dace ba, yanzu mene?" Ta ce "Cikin nan girma yake, yau ƴar fillon nan ta gani amma kamar bata gane ba, kasan kamar shirme ya yi mata yawa, shi ya sa na zaɓi nayi aikin nan da ita" Deen dake zaune idanunsa sauke akan wata Balarabiyya dake ɗakinsa ya ce. "Kada ki damu da wannan ƴar fillon na yanke shawarar abin da za mu yi mata, kawai ki tabbatar Yaa Sheikh ya samu kusanci da Halisa, ki daure ko a tea ne ki zuba maganin feeling ɗin, yana da ƙarfi sosai" Zahrah ta sauke numfashi ta ce "Amma kada a raunata ƴar mutane, nice daidai da Yaa Sheikh mai zai hana ni naje gareja bana tunanin zai gane bani da budurci" Deen yaja tsaki sosai ya ce "Kina da matsala Zahrah,ki fito kice bana gamsar dake mijinki kike buƙata tunda naga alamar ba sanya a wannan ɓangaren ba, listing to me Zahrah nasan waye Yaa Sheikh, nasan shi sanin da zaki mamaki, duk yadda kike tunanin basirarsa ya shige nan, duk abin da zai same shi yana ji a jikinsa, ki tura yarinyar kawai babu damu da duk irin abin da zai mata ba" ɓoyayyan numfashi ta sauke tare da shafa cikinta wanda ya fara motsawa alamar yana cikin ƙosashiyar lafiya ta ce "Deen what's your plan?" Ya ce "ban gane ba? Ina tare dake muke tsara plan ɗin? Are you doubting me?" Ta kasa cewa komai sai kashe wayar da tayi. Ta shiga zirga-zirga a bedroom ɗin duk ranar da Yaa Sheikh ya kusanci Halisa maybe ita kuma zuciyarta ta buga, a ƴan kwanakin nan wata sabuwar Soyayyar Yaa Sheikh ta wanzu a zuciyarta, duk da bai bata wata dama ta Kasancewa dashi ba, amma kullum da soyayyar shi take kwana a rai. A hankali Halisa ke tafiya cikin wasu kayan shan iska sbd sanyin garin ya lafa, ta sauke numfashi ganin Zahrah bata parlour kai tsaye ta nufi part ɗin Yaa Sheikh, ta shiga bakinta ɗauke da sallama Umar-khan dake yiwa Yaa Sheikh bayani ya ɗago kansa tare da kallon Halisa, da sauri ya ɗauke kai ganin kayan dake jikinta, Yaa Sheikh dake jingine jikin kujera sanye da Jallabiya sabuwa kamar ko yaushe ya miƙe tsaye tare da amsar ducoment ɗin da Umar ke basa, Umar ya ce "Ban gama yi maka bayani ba" Yaa Sheikh shiru da Umar ganin haka yasa Umar miƙewa yana ɗauke idanunsa daga kan Halisa, Ta ce "Umar-khan teacher ya ce gobe ka same shi a officer" ganin kamar bai jita ba yasa ta sake cewa "Umar-khan, Umar-khan" ta faɗa tana ƙoƙarin bin bayansa cak taji anyi sama da ita tare da nufar bedroom da ita..... Ya direta gabansa yana binta da gajiyayyun Idanunsa masu kaifi, ya shiga ƙarewa kayan jikinta kallo can dai ya juya zuwa wani ƙaramin bedroom dake jikin wanda suke ciki, ya dawo hannunsa riƙe da hawaya bai ce mata komai ba, sai hannunta daya kama zuwa bakin gado ya nemi waje ya zauna tare da zaunar da ita a gefensa. "Kina son Allah ya kama ki ne matar malam?" Ta marairaice tana narke fuska ta ce "Abba me na yi? Kuma wai baka da lfy naji Anti ta ce wai na shirya zamu asibiti" ya dubeta da kyau tare da kawar da batun Antin ya ce. "Baki san me ki kai ba? Ki nutsu ƴar fillo" ta tura baki zata ta shi ya tsare ta da idanu sosai kafin ya yi magana wayarsa ta fara ringing ganin sunan Abba Hakimi yasa Yaa Sheikh ya danna wayar a handsfree. "Malam, ina ajjiyata ne?" Halisa tai murmushi jin muryar Abba Hakimi, kafin Yaa Sheikh ya ce wani abu ta ce "Jon wuro" Abba Hakimi ya saki murmushi ta waya ya ce "To matar ni dai ban iya yaran nan ba, dama dai Abban naki ne" ta juya tare da kallon Yaa Sheikh taga idanunsa a rufe amma kamar mai jin zafi duk zufa ta gama rufe masa fuska sai gemunsa yake shafawa. "Jon wuro Abba ya iya fillatanci ne?" Abba Hakimi ya ce "Eh sosai, fiye da ke ɗin, baki taɓa ji ya yi bane?" Ta ce "Jon wuro ai baya nunawa yaji me nace ko da fulde nai magana, to Bafullatani ne Abban nawa?" Abba Hakimi ya ce "Matar baga ki kusa dashi ba? Ki tambaye shi, ni dai nasan duk wani motsi na Fulani a idanunsa yake" tai murmushi kawai har lokacin kallon Yaa Sheikh take shi kuma yaƙi yarda ya buɗe idanu, amma yana jin idanunta na yawo a jikinsa. Abba Hakimi da yaji shiru ya ce "Abban naki yana kula dake? kuma yana kusa yanzu" da sauri ta ce "Ai shi ya ɗauke....." Tattausan hannunsa da taji a bakinta yasa tayi saurin zaro ido suna haɗa idanu ya ware mata ido yana ya mutsa fuska gaba ɗaya yanayinsa ya sauya jin tunan asirin da take shirin yi masa. Ya miƙe baki ɗaya yana daidaita zamansa ya zagaya hannunsa ɗaya ɓangaren nata. "Shhhh" ya ce yana tare da yi mata alamar tai shiru. Abba Hakimi ya saki murmushi daga wayar kafin ya ce "Da alama kinyi nisan kiwo, ki bawa Abban naki" ta sauke numfashi bayan Yaa Sheikh ya zare hannunsa daga bakinta cikin ƙasa da murya ta ce. "Jon wuro Abba ya ce nai shiru kada nace ya ɗauke ni" tamkar Yaa Sheikh ya ce ya shiga uku haka yaji shi kam tayaya zai fara nuna mata illar surutun nan? Abba Hakimi ya yi kamar bai ji ba ya ce. "Me kika ce, ntwrk na rawa" Yaa Sheikh ya zare wayar tare da kashe handsfree ɗin a hankali ya manna wayar a kunnansa ya ce. "Abba" ya faɗa tamkar baya son maganar. "Aliyu" Abba Hakimi ya kira sunan cike da girmama kamar yadda yawancin lokaci yake ambatar sunan kai tsaye. Yaa Sheikh ya ce "Uhm". "Ina fatan baka mance deal namu ba, ka watsa mini ƙasa a idanu, kai tsaye na nuna buƙatar ka zauna da yarinyar nan, amma ka ce baka sonta? acikin shekara munci sati ko sama da haka, kamar yau Ubangiji zai nuna mini cikar shekarar. Wallahi Aliyu naga saɓanin yadda muka ajjiye yarjejeniyar zaka san bani da kirki zaka san waye Ostman-zannur" Yaa Sheikh ya juya tare da kallon ƴar rainon da ake kafa masa sharuɗa akanta cikin lafazi mai kyau ya ce. "Abba zan dawo da ita" "Alfarmar riƙon nata ne ba zaka iya ba?" Yaa Sheikh ya ɗan ya mutsa fuska kaɗan ya ce "Ramadan zai zo Abba, ba lokaci ba zan iya ba" sautin murmushin Abba Hakimi ya ratsa kunnan Yaa Sheikh ya ce "Kai kaɗai ne a gidan? da wasa ka bari Matarka taci zalin Halisa wallahi sai nayi maganinku duk" kafin Yaa Sheikh ya sake cewa komai Halisa ta miƙe tare da zama kan ƙafafuwansa tare da zagaya hannunta ta riƙesa da kyau ta ce. "Ina son ka Abbana, kuma...." Ƙitt Yaa Sheikh ya kashe wayar baki ɗaya yana rufe idanu tare da dafe kansa da hannu. Tuni Abba Hakimi yaji abin da Halisa ta faɗa kafin Yaa Sheikh ya kashe wayar. Halisa ita bata ɗauka wani abu tai ba ta ce "Abbana, ni ma kace kana so na" ya sanya hannu ya share zufar dake binsa kafin ya buɗe ido ya kalleta a hankali ya ɗagata da kyau ya zaunar da ita saman cinyarsa ya kifa fuskarsa daidai nata numfashinsa na sauka a hankali saman nata ya jima yana sauke Afra kafin ya ce. "Me... Me.. me..." Innalillahi wa'inna ilahir raji'un! In-ina ta dawo sabuwa a lokacin da bai zato ba, kuma daman tuni tuni jikinsa ya bashi hakan zai iya faruwa. Ta zuba masa idanu ganin yadda yake ɗan karkatar da kai yana damƙe hannunsa. "Abba kayi haƙuri ban sakewa ka yafe mini" ya girgiza idanunsa sukai jajir cikin son nuna mata kuskuren kaifin bakinta ya tallafo haɓarta sai kuma ya saka ya riƙe hannuwanta da kyau ya ƙanƙame, yana buga ƙafa duk don maganarsa tazo amma abu ya gagara. Ta zuba masa idanunta wanda ya cika da ƙwalla sosai tsoron da tausayin Abban nata ya ɗarsu a zuciyarta. A hankali ya zame hannunsa zuwa rigarta ya riƙe gaban rigar da kyau yana cukurkuɗata ba tare da sanin cewa gaba ɗaya rigar ya tattare ba, ya jawota kusa da shi sosai ba tare daya haɗe jininsu ba, wasu hawaye suka kwanta a idanunsa na zallar asabar fitar maganar. Tamkar wanda zai shaƙeta haka ya rirriƙe gaban rigarta ƙwayar idanunsa kwance cikin nata, cikin Muryar In-inar ya buga ya ce. "Ma...mama.... Mata ma matar maaa ma malam...." Ya faɗa yana buga ƙafa Halisa ta saki kuka bana shaƙar da ya yi mata, na tausayin Abban nata na, da yanayin da taga ya shiga ta ɗauka duk rashin lafiyar ce. A hankali ya saketa tayi sauri ta zame jikinta tare da shigewa cikin jikinta ta rungomesa cikin kuka ta ce. "Abbana" ya dubeta kana ya ɗauke yana shafa kanta a nutse. Ganin kuka take da gaske ya ƙara tallafo fuskarta tare da kama hannunta ya ɗora a ƙirjinsa, wani irin bugawa sosai taji saitin zuciyar shi nayi kamar zata tsago ƙirjin shi ta fito. "Shhhhh" kalmar ta ƙwace masa yana mai lumshe idanunsa tare da buɗewa ya zareta a jikinsa ta ƙwace ta koma tana ƙara riƙesa. "Abbana ka barni" ta faɗa a tsorace shi kifa kansa kawai ya yi a wuyanta sbd tsananin yanayin dake hura wutar abin da yake ji, ya jiƙe sharkaf da gumi. Ya goga hancinsa a wuyanta tayi saurin kallonsa ta ce "Modibbo" ma'ana Malam ko malami, ya cireta a jikinsa yana miƙewa tsaye itama ta miƙe da sauri wata Jotter ya ɗauka da pen ya shiga yin rubutu cikin good handwriting. Yana jin hakan da ya yi shi ne mafita, idan akwai divorced tsakanin su dole Abba Hakimi ya daina tunanin wani ba. Bayan ya gama rubutun ya naɗe tare da sakawa cikin envelope. "Abbana mene wannan" ya dubeta tare da tsugunawa daidai da ita a hankali ya ɗaga ta ya ɗora saman ƙafarsa ɗaya a taushashe ba tare da rauni ko yanayinsa ya sauya ba. Cikin sakin harshe saɓanin ɗazo ya ce "Matsayinki ne a nan Matar Malam, ki yafe mini kinji?" Bata gane ba dan haka tai murmushi ta ce "Abba nima ka yafe mini naji tsoro" ya shafa kanta kana yaja ƙaramin sirrin hancin ya ce. "Ga Malaminki ba tsoro, kina ji ni ba mijinki bane zanci gaba da riƙeƙi matsayin ƴa" ya ɗan yi shiru yana sauke numfashi ya ce. "Ba zaki gane karatun ba yanzu, ki riƙe wannan a wajanki zuwa shekara guda, yanzu ke ƙawata ce ki cire miji a bakin ki" tai murmushi bata fahimta amma haka kurum jikinta ya yi sanyi, duk wata mace da aka saka dole ta samu wannan raunin. Ya miƙe yana cewa "Muje muyi darasi" Zahrah ce gaban likita tana jin abin da yake faɗa ta ce "Da zan baki shawara ku bar cikin jikinki yana cikin ƙoshin lafiya sosai" Zahrah ta kalli Deen dake kusa da ita ta ce "Dr akwai matsala ne, ko nawa ne zan iya baka, ayi duk yadda za ai cikin nan ya kwanta zuwa wasu watanni" Dr ya ce "Ki fahimta wannan ganganci ne" Deen ya gyara zama fuskarsa da face mars ya ce "Daga miliyan 5 zuwa sama ka faɗi abin da kake so, ka yi mata scanning da sai nuna cuta ce a cikinta harta kumbura, za ai mata aiki zuwa watanni huɗu ko biyar" likitan ya yi murmushi ya ce "Wannan ba damuwa bane, ka bada kuɗin duk sanda kuka shirya sai kuzo" Deen ya ce "Your Account number, zan kiraka idan zata zo, ya zama sirri bana lamuntar ha'inci da cin amana, zan iya ɓatar da mutum" Zahrah ta ce "Dr macan da bata fara al'ada ba, zata iya ɗaukan ciki?" Ya girgiza mata kai ya ce. "Al'ada Ita ce hanyar dake nuna cewa mace ta shirya amsar namiji, kuma zata iya amsar dukkan wasu ƙwayaye da zai zuba mata, sai dai bisa tsari ƙwan ɗaya ke nasarar samu shiga cikin wani gurbi na mahaifa, idan ƙwan namiji guda biyu ya samu damar shiga cikin mahaifar mace lokaci guda, shi ne ake iya samun twins, twins ɗin da suke a mahaifa guda sune ake kira da identical twins, masu tsananin kama da juna, wanda suka zo a mahaifa daban daban suna iya kama amma ba can ba, mahaifa na buɗewa ne lokacin da mace ta fara al'ada magana ya gaskiya babu yadda za ai mace ta samu ciki ba tare data fara al'ada ba, wannan shi ne" Zahrah ta sauke nauyin jin daɗi kana ta miƙe daga nan Hotel ta nufa, tana murna plan ɗinta zai cika cikin ƙaramin lokaci. Daman dai fargaba kada ace Halisa ta samu ciki a mu'amalar da zatai da mijinta, amma yanzu ta samu nutsuwar zuciya. Washegari bayan Halisa ta tafi makarantar Yaa Sheikh na gida sbd baƙin da zai masu ɗaukan tafsir da ake sakawa a Channel. Ummul ta kallesa ta ce. "Ka tafka babban kuskure Aliyu, mene amfanin abin da kayi? Idan zaka rabu da ita mene yasa ka aureta tun farko?" Kansa a ƙasa domin yana martaba Ummul ƙwarai da gaske. Ya kalleta yana miƙewa tsaye ya ce "Ƙaddara Ummul, ƙila ba rabon zama Inuwa ɗaya, mganar ya tsaya iya mu" Ummul ta goge hawayen idanunta ta ce "Malam kada ka manta kai da kanka ka zaɓa mata suna Halisa, kai ne kayi mata huɗu ba, kai me ka reneta meye duk wannan wanne irin abu ne? Zaka yanke hukunci ba shawara" ya juya kawai ba tare da ya ce komai ba, sbd kansa dake juyawa sosai. A haka ya nufi Part ɗinsa. Yau da murna Halisa ta dawo sbd yaba mata da Ayyan ya yi harda gift ya bata bayan ya ce tana da kyau. Wanka tayi tai sallah ya shirya cikin wasu english wears masu kyau. Bata nufi wajan Ummul ba, kai tsaye wajan Abban nata ta nufa lokaci yana kwance akan bed ya yi rigingine. "Abba, Abbana" ta hango shi can bed kallon da ya yi mata yasa ta juya tare da dawowa ta ce "Assalamu alaika" ya amsa a ransa. Ta matsa kan gadon tare da hayewa saman gadon, kai tsaye ta yi wa kanta masauki a bayansa, ta zauna a bayan ta ce "Abba yau nayi ƙoƙari sosai, Teacher Ayyan ya ce ina da kyau kuma yana so na" ya mirgina tare da dawo da ita saman cikinsa ya riƙe hannunta ya ce "Uhm" ta shafa fuskarsa tana wasa da gemunsa ta ce. "Amma Abbana nake so shi ne mijina" ya ƙurawa bakin indo yadda take juyawa babu sassauta zan can. A hankali ya mirginata, ta koma ƙasan bed ɗin, shi kuma ya yi mata rumfa. "Abba" ta faɗa tana kallon idanunsa tamkar ba na Abbanta ba. Ya kame bakin surutun a hannunsa ya ce. "Kina buƙatar darasi Matar Malam" ya shinshina wuyanta sak irin turaren daya siyawa su Maimoon da mother. Ta ce "Abba ai na san darasin" ya buɗe ido ya ce "Za dai ki sani" kamar yadda ya yi mata haka itama ta riƙe bakinsa, ya rufe ido yana janye jiki tare da jan duvet ya rufe jikinsa baki ɗaya har kansa, gaba ɗaya jikinsa rawa da karkarwa yake kamar mazari. Ta miƙe a rikice tana faɗin "Abba, Modibbona, Abba" da sauri ta fita wajan Ummul ta amsa black tea kana tayi ɗakinta maganin wajan El-bashir ta buɗe tana zubawa a tea ɗin, ta juya shayin da sauri ta nufi bedroom ɗin, har lokacin yana kwance ta ce "Abba ga shayi kasha kaji" yai mata banza har zata janye duvet ɗin sai kuma ta tsaya a fili ta ce "Bari muji ko babu ɗaci shayin" ta ɗauki cup ɗin shayin tare da kaiwa bakin, tai karɓa ɗaya biyu har zuwa uku samun kanta tayi da shanye shayin baki ɗaya..... Zuciyar Yaa Sheikh tai kyakkyawan bugawa a duk lokacin da ya shiga wannan yanayin yasan akwai mummunan abun da zai faru da rayuwar shi. Ya akan iya gani a mafarki ko jikinsa ya shaida masa hakan ta hanyar sauyawa. Ya zame duvet ɗin jikinsa a hankali ya mirgina zuwa gefen ya rufe ido yana sauke numfashi bakinsa ɗauke da addu'a. A hankali ya sakkowa daga kan bed ɗin zai shige bathroom idanunsa ya sauka a kanta tare da cup ɗin shayi. Kansa ya sara a nutse ya nufeta tare da durƙusawa daidai inda yake, yanayinta ya nuna sam ba lafiya ta kifa kanta a gefen gadon ta kifa kamar zata faɗi. A taushashe ya ce. "Kee!" Shiru bata amsa ba abu ne mai wahala Halisa ta nutsu haka dole akwai wani abu. Ya riƙe numfashi ya ce "Ƴan matan Abba" nan ma shiru ya ɗora hannunsa tare da girgizata gaba ɗaya tayi baya zata faɗi ƙasa ya yi saurin taro ta zuwa cinyarsa. Wani irin zafi yaji fatar jikinta ɗauka sosai tsoro ya kama Yaa Sheikh amma ya riƙe kansa ya riƙota tare da bubbuga kumatunta ya ce "Ƴar fillo, ƴar fillo!" Ta buɗe idanu da ƙyar yana kallon fuskarsa amma ta kasa cewa komai sai hawaye dake fita daga gefen idanunta yana gangaruwa fuskarta. Yaa Sheikh ya juya idanunsa ya sauka akan cup ɗin shayin ya ɗauka da sauri ya jima yana kallon cup ɗin. Da sauri ya ajjiye ya riƙota gabaɗaya ya ce. "Ina ki ka samu wannan? Waye baki?" Gaba ɗaya ya nemi rasa nutsuwata duk yadda yasu ya kame kansa daga shiga firgice ya kasa. Ya jawota sosai muryata na rawa ta ce "Abbana" ya shafa kanta ya ce "Yes, Amanata. Me ya sa? Zaki kassara rayuwarki akai na?" Ta riƙe hannunsa jikinta na rawa na tsananin azabar da take ji, domin ji take kamar ana hura mata wuta a naman jikinta idanunta ya kasa tsayawa sai lumshewa take tana buɗewa ta ƙara riƙe sa ta ce. "Kashe mini kai za ayi Abbana? Me ya sa? Me kayi don Allah kada a kashe mini kai" wani irin hawaye na zubuwa daga idanunta. "Amanata why? Guba ki ka sha tayaya Abbanki zai jure?" Ta girgiza kai ta ce "Na san maganin mutuwa ne Abba, amma ni babu abin da zai mini, Abba ka ɗaukeni jikina bafii ciwo Abbana" ta saki numfasa, sanyi kawai take buƙatar ji zafin jikinta ya tsananta azaba da raɗaɗi kawai take ji, ta gwammace taji azabar da ace Abban nata yaji, ba zai iya ɗauka ba. "Nothing... Nothing will happen Amanata" ta ƙara buɗe idanunta daya fara sanyawa ta ce "Modibbona" "Na'am ta Malam?" Ta kallesa da kyau ta ce "Modibbo bafii ina jin ciwo" tausayinta ya kama shi a zahiri ya yi mugun rikicewa, amma dake ya iya riƙe kansa fiye da kima ya girgiza kai kawa tare da ɗaukanta zuwa kan bed ɗin da ya kwantar. Telephone line ɗinsa ya ɗauka ya kira wata number, babu jimawa akan ɗauka. A nutse ya yi bayani wanda aka kira ya ce. "Blood poison ne, wanda yake ƙona jinin mutum cikin ƙaramin lokacin, am on my way" Yaa Sheikh ya yi shiru tunani kala-kala a ransa yana ƙara maimaita kalmar _“Blood poison?”_ waye? Daga ina? Akan wanne dalili?. Dr ɗin ya ce "Ka bata taimakon gaggawa kafin nazo, zaka iya yin body connection da ita sbd ta samu zafin jikinta ya ragu a jikinta, ma'ana dai sanyin jikinka ya shiga nata, zafin jakinta ya shiga naka....," Yaa Sheikh bai tsaya jiran jin abin da Dr ɗin zai ƙarasa faɗa ba ya ajjiye wayar tare da nufar bathroom, gaba ɗaya ya zare sutturar jikinsa ya rage daga shi sai farar singlet da trouser a karo na farko wani zaiga jikinsa kuma waninma ƴar rainonsa. Ya sakarwa kansa shower da ruwa mai mugun sanyi, bai taɓa wanka da ruwan sanyi ba sai warm water amma yau shi ne tsaye shower na dokan tsakiyar kansa, sai daya jiƙe sosai sai ko'ina na jikinsa ɗiga yake kafin ya fito daga bathroom ɗin. Direct bed ɗin ya nufa tana kwance ba zaka taɓa ɗauka tana da rai ba, sbd ita kaɗai ta san abin da take jin bakinta wani irin ɗaci ya yi idanunta ya fara yin fari sosai, da hanzari ya hau kan gadon yana ɗaukanta tare da zaunar da ita saman cinyarsa, ta buɗe ido tare da zuba masa su alamar "Me zakai Abba?". Ya saka hannu ya shiga ɓalle gaban rigar ta, ita dai kallonsa kawai take ya zame rigar tare da yin cilli da ita ya rage daga ita sai farar vest da White Padded bra sai under wear. Ya saka hannu zai zare vest ɗin yaji ta riƙe hannun, yana ɗago kai suka haɗa ido, ta rufe ido ta buɗe kai tsaye ya fahimci me take nufi. Ya ɗora hannunsa akan ta yana shafa sumar kanta a taushashe ya ce. "Abbanki ne amanata, ki nutsu" lokacin daya zare vest ɗin ta rufe idanu a hankali ya kwanta, tare da ɗorata saman shi, wata iriyar ajjiyar zuciya ta sauke mai nauyi tana ɗana zabura sbd sanyin daya ratsa fatar jikinta, wani irin daɗi ya kamata zafi da raɗaɗin na raguwa, Yaa Sheikh ya rufe ido tasbihi kawai yake a ran shi. A hankali zafin jikin Halisa ke shigewa nasa, sai da jikinsa ya ɗauki zafi sosai ya zameta a hankali tare da miƙewa ya koma bathroom ya ƙara sakarwa kansa shower ɗin. A wannan karan ƙanƙame shi tayi sosai sbd samun sassaucin da take kallo ɗaya zakai mata kasan ta jigata. Yaa Sheikh addu'a yake yana tofa mata hannunsa zagaye da bayanta ki sau ɗaya bai tsaya ya sauke idanunsa akanta ba. Ringing ɗin telephone da yaji yasa ya kwantar da ita yana miƙewa tsaye ya san Dr ne. Ya zura jallabiya da hirami tare da nufar ƙofar part ɗinsa ta baya yana zuwa ya samu Dr da Umar-khan. Yaa Sheikh ya kalli Umar-khan gane abin da yake nufi yasa kai tsaye ya nufi sashin Ummul. Yaa Sheikh ya juya zuwa ciki Dr ya biyo bayansa, cikin sauri ya shiga buɗe dukkan wasu abun gwaje-gwaje da zai tabbatar da zargin da Yaa Sheikh yake. Gwajin farko ya nuna guba bace mai ƙarfin gaske ba wacce zata kashe mutum lokaci guda ba, a hankali zata dinga ƙona jinin mutum har ya ƙare cikin watanni biyu ko uku ya mutu. Ya kalleta yaga kamar barci ya ɗauketa sbd yadda numfashinta ke sauka, Dr zaiwa Halisa allura ya ɗaura mata drip tare da saka mata wani abu acikin baki, Yaa Sheikh ya yi gyaran murya ya ce. "Kada a manta am a doctor, zaka iya tafiya" Dr ya ce. "Allah ya ƙara sauƙi da afuwa" fitar Dr ya yi daidai da shigowar Ummul a rikice ta ce. "Poison a gidan nan? Kuma wajan Halisa Aliyu? A ina aka samu guba?" Ya sauke numfashi a ɓoye yana ɗauke kansa, da kansa ya saka mata drip tare da yi mata Injection. "Kaga abin da nake faɗa? ba za a barka ba Malam Wannan shirun naka bashi da amfani, nasan kasan masu nufinka da haka, abin tambaya ya akai Halisa ta samu guba?" Ya zauna saman kujera ya jima kafin ya ce. "Maganar ta tsaya iya mu Ummul, a nemi abin cewa" ta ce "Shikenan amma na fara gajiya ba zan iya zuba idanu mu rasaka ba, kalli halin da yarinyar nan ta shiga" Sai a lokacin Umar-khan ya ce "Abin tambaya ne ina ta samu poison?" Yaa Sheikh ya miƙe tsam yana buƙatar hutu da nutsuwar Zuciya ko zai samu ya yi cikakken tunani mai kyau. "Zan huta, ina buƙatar kyakkyawan lokaci Ummul, a nemi wacce tayi shayin nan" yana faɗin haka ya shige ɗakin dage gefen bedroom ɗin.... Basu da wani zaɓi wanda ya shige fita. Ummul ta nufi kitchen gaba ɗaya ta kira ma'aikatan ta ce "Waya haɗa shayin Yaa Sheikh?" Duk sukai shiru domin sun san babu wanda ya kewa Yaa Sheikh abincin bayan Ummul. Suhaima ta ce "Ummul ina tunanin ke kika haɗa fa? Ko kin manta ne?" Ummul ta ce "Ko ɗaya dole an sauya" Bara'at da tun ɗazo ba tai magana ba taja duguwar ajjiyar zuciya ta ce "Wanni abin ne?" "A'a. Daman ya ce ya masa yadda yake so, an zuba suger ya yi yawa, wanda ya ɓata ɗanɗanon. Kuma saƙon daɗin yaje har ƙwaƙwalwar shi, wacce aka bawa kwangilar tana buƙatar a bata tukucin kai goran albishir" Ummul ta juya rai ɓace, gabaɗaya suka bi bayanta da kallo tare tunanin ko dai wani abun ya faru ne?. Tunda Ummul ta shiga ɓangarenta ta rasa yadda zatai da ranta, ko dai iyayen Yaa Sheikh zata kira ta faɗa musu abin da yake faruwa su sani? Kada a wayi gari da gawar Yaa Sheikh ya zatai?. Ta nemi waje ta zauna tare da faɗin. "Ubangiji kamar yadda ka bawa Yaa tsayin shekarun daya ɗauka yana kula da Halisa tun tana ciki, har kawo haihuwar ta, Ubangiji ka ƙara masa wasu shekarun da zai tabbatar da mauradinsa ta zama cikakkiyar mata a garesa, Ya Allah Ya Rahmanu ka nufi Yaa Sheikh da mayar da wannan taɓargazar da ya yi, Yadda take ƴar raino a garesa Allah kasa ta zama mata a gare shi har abada" Ta goge hawayen daya sakko mata, tana son komawa taji yadda jikin nata yake amma tasan taga Yaa Sheikh tasan riƙe kansa yake amma baya jin daɗi, ko zazzaɓin Halisa baya jurewa yanzu zai zo yana cewa. "Ummul ƴar fillona" balle yanzu data sha poison ason kare rayuwar Abban nata. A daddafe Yaa Sheikh ya gabatar da Sallar Issha a masallacin da yake ɗaukan su jam'i. Bai tsaya yi musu karatu ba, ya dawo gidan ma'aikatan dake kula da dukkan wasu abubuwa daka waje ya shiga bi da idanu gabaɗaya suka sha jinin jikinsu wannan shi ne karo na farko daya kallesu har haka. Zahrah na ganin shigowar Yaa Sheikh ta miƙe da sauri tare da rungomesa ta ce. "My Excellency yau duk ban ganka ba, sai yaushe zamu kasance tare?" Ya zareta daga jikinsa ta ce. "Na fara gajiya, matarka ce ni amma kana nunawa sam baka damu dani ba, ina da hakki a kanka kasan ni macace mai rai wacce jini ke gudana a jikinta kuma....," Kaifin idanunsa daya sauka cikin nata ya hanata ƙarasa maganar duk rashin kunyarta bata isa taiwa Yaa Sheikh. "Me kike so? uhm kada ki damu shekaru biyu ne kawai na baki" maganar ta tsaya mata a zuciya, wato kada ta damu ko dan tai masa rashin kunya?! Ta tsiri kukan ƙarya idanunta rufe ta ƙara rungomesa ta ce. "Ina buƙatar My Excellency, ina son kasancewa da mijina" Yai mata shiru ta riƙesa sosai ta shiga yi masa wani abu, amma ko gizau bai ba, al'amarin daya bawa Zahrah matuƙar mmki kenan. Sumbatar shi zatai daidai lokacin kuma ɗan dake cikin cikinta ya yi wani kyakkyawan juyawa tare da harba ƙafa wanda ya a sanya taji mararta ta ɗaure tana da tabbacin Yaa Sheikh yaji juyawar ɗan dake cikin nata.. Ya ɗauke kai tare da shigewa abinsa. A ruɗe Zahrah ta nufi bedroom ɗinta tana kiran number Surry gaba ɗaya ta fara rasa mafita tashin hankali ya bayyana akan fuskarta. Tun daga bakin ƙofa Yaa Sheikh ya fara jiyo numfashinta tana kwance jikinta zai rawa yake kumfa na fita daga cikin bakinta, tuni ta fisge drip ɗin hannunta. Ya ƙarasa da sauri yana zama kan bed ɗin tare da ɗagota, ko magana ya kasa jinta jikin mutum yasa ta ƙanƙame Yaa Sheikh tana ɓoye kanta kwantar da ita ya yi tare da kama hannunta ya shiga murzawa da sauri da sauri, ya daɗe yana murza hannunta kafin ta ja numfashi ta sauke jikinta ya saki sai hawaye dake bin fuskarta. Ɓoyayyiyar Ajjiyar zuciya shi ma sauke yana janye drip ɗin ta buɗe ido tana kallon Yaa Sheikh ta ce. "Modibbo zan mutu kai ni Dadata" duk yadda yasu kame kansa da riƙe yanayin kasawa ya yi, ya jawota jikinsa tare da yi mata masauki da kyakkyawan ƙirjinsa ya rufeta ruf ya yi mata rungumar da rabon da ya yi mata tun tana shekara biyar a duniya. Ta sauke numfashi tai luff a jikinsa ƙamshin Roja na ratsa zuciyarta a hankali ta ce. "Abbana" ya dubeta bai ce komai ta ce "Abbana me ya sa zasu kashe mini kai? Su waye mai kayi musu zan basu haƙuri ni su kashe ni kaji?" Ya ɗora hannunsa a bakin nata "Shhhhh" ya ce yana ƙara matseta a jikinsa. "Modibbo, Abbana kada ka mutu kaji?" Idanunsa da suka gama juyawa ya buɗe tare da kwanto da ita saman hannayensa ya kifa kansa a fuskarta suka kalli juna muryarsa bata bita sosai ya ce.. "Rayuwa, mutuwa na hannun lillahi wahidul ƙahhar, ban son hawayen" A hankali Halisa ta fara tunanin vedion data gani a wayar Anti Zahrah komai ya dawo cikin tunaninta ita kanta Zahrah bata san Halisa taga wannan vedion ba. Yaa Sheikh yana ƙoƙarin zame fuskarsa daga kan ta Halisa kamar a mafarki, kamar gilmar tunani cikin ƙwaƙwalwar mutum haka yaji saukar bakinta cikin nasa..... Paid book It's 500 08119237616 "Ya subuhanallah, wa...wa wa'auzubillah" sune kalmomin da suka samu fita daga cikin bakin Yaa Sheikh wanda suka kasance iya zuwa. Ya riƙe kanta da kyau yana ƙara ware idanunsa akan ta, mmkin ya cika shi yaushe matar malam ƴar amanar shi tasan duk wannan? ya ɗauke numfashi yana ƙoƙarin sauya yanayin yaji ta ƙara riƙe bakinsa da kyau idanunta rufe, al'amarin da bai taɓa ji ba shi yake neman bijiro masa. Ilahirin jiyoyin kansa sun fito tare da yin kwance a saman goshinsa. Ya zare bakinsa da ƙyar ba dan ta daina abin da take ba, Halisa ta marairaice fuska idanunta na cikowa da hawaye ta ce "Abbana" ya goga fuskarsa a wuyanta yana tura dukkan hannunsa cikin sumar kanta ta sauke numfashi tana bin fuskar shi da kallo tare da kama gemunsa tana ja.. Cikin wata kalar raunatacciyyar murya wacce shi kaɗai yasan ma'anar ta ya ce _"Ta fuɗɗu ko a wawata famtugo nder majuum"_ karo na farko da taji fillatanci a bakinsa wanda ya zauna raɗau kai kace harshen shi ne na Iyaye. Ta ce "Abba zan iya gane darasin da gaske" "Uhm" ya ce kawai dan bakinsa ya yi nauyi sosai, yarinyar ta shayar da shi mmki. "Sallah zaki" ta ce "Abba ba zan iya tashi ba, kuma zanyi fitsari" ya miƙe da ita tsaye tare da nufar bathroom. Suna zuwa ya sauketa tare da ƙoƙarin juyawa tayi saurin maƙale kafaɗa ta ce. "Ka tsayani, tsoro ina" ya kalleta sai kawai ya tsaya tare da juyawa mata baya. Bayan ta kammala ya yi mata alwala da kansa a taushashe ya ce. "Walk" bata gane zaran zancan nasa ba da hannu ya nuna mata ƙofa ta shagwaɓe fuska sosai kamar yadda take masa a shekarun baya amma duk ta mance. "Ni ka ɗaukeni ba zan iya tafiya ba" ya girgiza kai tare da sunkuya ya ɗauketa ta saƙalo wuyansa. A jingine a jikinsa a haka ta gabatar da Sallar duk yana kallon ta, saura kaɗan gabar ya kassara mata jiki gabaɗaya bata da kuzari duk babu kazar kazar ɗin. ganin tana lumshe idanu ya ce "Gajiya? Jikin? Yunwa?" Ya faɗa a taƙaice ta girgiza kai ta ce. "Abba Dadata yaushe zan ganta? Ni goyani take idan bani da lafiya" ya ware manyan idanunsa yana hango zallar rigima dake kwance a nata idanun. "Abba ka goyani" ya dubeta a dole sai ta saka ya magantu ya ce. "Ki rufa mini asiri, goyo tun shekarun baya baki mance ba?" ta saki kuka da gaske domin ita har zuciyarta take son a goyatan ƴar rigima ce, idan abin ya motsa bata ji bata gani. Ta saka kuka sosai ya ɗauketa gabaɗaya tare da jijjigata ya ce "Kina son rikitani Amanata, ki tauyasawa Abbanki" ta maƙale kafaɗa daidai kunnanta ya shiga yin wasu baitotoci na waƙar larabci na addini. Tai shiru tana tunani kamar tasan waƙar, Yaa Sheikh yasan dole ta haka zai shawo kan rigimar ta ce "Abba kai ma ka iya?" Ya zauna bakin gado yana ɗorata akan cinyarsa ya ɗan kalli time yaga goma ta kusa. "Kin taɓa ji ne?" Ta ɗaga masa kai ta ce "Kamar dai" tai shiru alamar tunani da sauri ta ce "Abba na tuna, wani na manta sunan mai rufe fuska shi ne yake yi mini a Rugar Rome" ya ɗauke kai yana mai sassauta fuska kamar wanda murmushi zai ƙwacewa. Ya gyara mata zama tare da zagaye bayanta ya ɗora kansa a wuyanta tattausan gemunsa na gogar fatar wuyanta ya ce. "Duba can?" Ya nuna mata direction da hannu idanunta ya sauka akan wani photo a prame photon baby girl ne zata iya yin 10 mnts da haihuwa, idanunta rufe sumar kanta har gaban goshi. Anyi wani rubutu kala biyu ɗaya da hausa ɗaya da turanci. _“Angel my world”_ shi ne abin da aka rubuta da turanci da larabci kuma aka saka _“Ƴar Aljanna Mrs Aliyu haydar Aliyu”_ yanayin yadda aka tsara photon zaka san cewa ana matuƙar ji da shi, ta juya ta ce "Abba wace?" Ya shafa kanta da hannunsa har lokacin fuskarsa na kifa a wuyanta yana murza mata sajansa mai laushi ya ce. "Zaɓin Allah, matar ƙwarai, hasken zuciya" nan da nan yanayinta ya sauya ta ce "Abba nifa? Da gaske baka so na?" Ya ware bakinsa kamar zai magana sai kuma ya fasa Halisa tau saurin sauke numfashi jin tongue ɗinsa a skin na wuyanta yana yawo. "Baka so na Abba?" Ya buɗe ido tare da ɗagowa baki ɗaya. "Kina so a soki ne?" Ta ɗaga masa kai ya numfasa tare da kwantar da ita yana sauke mata numfashi ya ce. "Ban son ina kwana, every morning come and Peck my cheeks, left and right, shi ne gaisuwar" ta ɗaga masa kai. Duk sukai shiru can ya miƙe ya bisa da idanu. Kai tsaye sashin Ummul ya nufa Ummul na ganinsa ta miƙe tsaye ita kanta kwarjinin Yaa Sheikh rikita ta yake haibarsa da kamala har sun yi yawa. "Ya jikin nata? da sauƙi dai? ta faɗa maka wanda ya bata gubar" Ya juya yana yin wace ya ce. "Allhmd. Ba buƙata" daga nan ya nufi Library ɗinsa, yaci gaba da rubutun Alkur'anin da yake da ka, wanda yake son ya zama cikakken kafin zuwan Ramadan da shi zai amfani wajan yin tafsir. 1:00 ya tashi bayan ya tabbatar komai lafiya yake, ya watsa ruwa tare da yin alwala. Sallah ya gabatar sosai ya zauna zaman azkar sai 2:30 ya shirya cikin fararen kayan barci ya fesa turare ya nufi duguwar kujera tare da duvet ya kwanta, daga ina yanke ya hangota sai barci take numfashi na sauka a hankali gabaɗaya ta kwaɓe fuska. "Rigimammiyata" ya furta a fili yana rufe idanu. Cikin dare sanyin zazzaɓi ya takura mata da wani irin ciwon kai sosai kuma duk yana cikin matsalar da gubar ya haddasa mata, ta yayar bargon da take ciki kai tsaye idanunta ya sauka akan Abban nata ta nufi kujerar tare da hayewa saman shi ta zagaye hannuwanta ta riƙesa sosai kanta a ƙirji nan take barci ya sake ɗauketa. Ba barci yake ba yana jinta kuma dama ya san dole zata ta shi yaja bargon ya rufesu tas sai a lokacin barci ya ɗauke shi. Duk yadda ya makara a kwanciya hakan bai hana shi tashi tun kiran sallar farko ba. Ya buɗe bakinsa ɗauke da addu'a a hankali ya yunƙura zai tashi yaji an ƙanƙamesa, ya kai idanunsa zuwa jikinsa ya sauke numfashi tare da komawa ya kwanta gaba ɗaya ya manta a jikinsa ta kwana, gently ya miƙe da ita yana ji tana riƙesa tsoran kada ta faɗi a haka ya kwantar da ita saman bed tare da rufeta da duvet yana matsawa ta mirgina tare da cire duvet ɗin a haka taci gaba da barcin. Cikakken wanka ya yi tare da ɗaura alwala ya shirya cikin embrodiery Islamic jallabiya jikinsa sai fidda ƙamshin Nivea Men Active Clean Shower Gel, ƙafarsa sanye cikin Scuff faux-shearling slippers ya nufi fita daga gidan zuwa Masjid sai baza ƙamshi Roja yake. Sai da ya gabatar da raka'atul fjr kana yaja jam'i cikin daddaɗar muryarsa cikin makarijul huruf da fidda hakƙin tajwid yake karatun. Ana idarwa ya fara gabatar da karatu wanda ya kasance da mutane da yawa, ya ɗago kai tare da kallon mutanan kana ya bayar zuwa ga littafin dake gabansa a taushashe ya ce. _“ Babin da yake bayani akan tilasta mace zuwa ga shimfiɗa bada yarda ta ba, a turance kuma Sexual violence”_ ya gyara zama sosai gaba ɗaya larabawan wajan sukai shiru suna sauraran abin da zai ce. A hankali ya ce. 7:00 ya shigo gidan bayan ya biya ta wajan tsuntsayensa, daman yasan ba zai samu kowa a main parlour ba. Kai tsaye part ɗinsa ya nufa da mmki yake dubanta tana kwance saman prayer kar sai gyangyaɗi take. Ya nufeta bai ce komai ba taji an ɗagata sama tayi saurin buɗe idanu suka kalli juna sai kawai tai murmushi mai kyau tana kwantar da kanta. Bayan ya sauketa saman bed ya ce. "Sanyi sai kama ki, a daina kwanciya ƙasa" ta ɗaga masa kai tare da faɗin "To Abba makaranta fa?" Ya tsare ta da idanu kafin yai magana wayar shi ta gida ta fara ringing ya miƙe tsaye a hankali ya manna wayar a kunnansa. Umar-khan dake kan layi ya ce. "Barka da safiya Yaa Lee, ya mai jiki? Ummul na neman iso na shigowa sashin naka" "Uhm" ya ce yana ajjiye wayar. Babu jimawa Ummul ta shigo hannunta ɗauke da babban tray. "Barka da safiya, ya jikin nata?" Yana zama kan kujera tare da naɗe ƙafarsa ya ce. "Mun tashi lafiya?" Ta ce "Allahamdulillah, Ya jikin ƴar Abba" Halisa tana daga kwancan ta ce "Naji sauƙi Ummul, tambayi Abba kiji shi ne ya ɗaukeni yanzu kuma a jikinsa na kwana" kamar ƙasa ta tsage ta shiga haka Ummul taji kunyar Yaa Sheikh ta kamata Halisa ta ƙara cewa. "Ummul Abbana ɗan gayo ne ba kiji bakinsa ba..." "Ya isa haka, yau naga takai ne ni Ummul" Halisa ta juya za taiwa Yaa Sheikh magana amma ko inuwarsa babu a bedroom da alama ya daɗe ta ficewa tun da yaji abin kunyar da take neman haɗa shi da ita. Ummul sam batai wani mmki ba, ita juriya da haƙurin Yaa Sheikh kawai take gani. "Ƴar Abba ba komai ake faɗa ba, shi aure sirri ne, duk abin ya faru ki barshi a ranki, kinji?" Ta ɗaga mata ta ce "maza sha tea kinji?" Ta maƙale kafaɗa ta ce "Modibbona zai ban kije kawai Ummul, kuma me ya sa ki ka daina cewa matar malam?" Ummul ta ce. "Because he's no longer your husband" tana faɗin haka ta fita. Ita kuma Halisa sam bata gane ba. Tana fita Yaa Sheikh ya fito daga bathroom suna haɗa ido da Halisa ya watsa mata harara ita dry ya bata ma. Zahrah na tsaye ta kafe Ummul da idanu tana tirketa da manyan tambayoyi. "Ina ƴar aikina take, ya zama last question da zan miki" Ummul ta ce. "Bata jin daɗi, a part ɗina ta kwana" Zahrah tai shiru sai kuma ta ce "Muje akwai aikin da za tayi mini yanzu?" Ummul ta ce "Bata lafiya fa?" A fusace Zahrah ta ce "And so what? Ke rashin lafiyarta ya dama" Ummul ta ɗauke ta ce. "To Umar-khan ya tafi kai ta asibiti" yaja tsaki tare da juyawa ta ce "Bari naje wajan Yaa Sheikh ɗin naji wanda ya bada lasisin yiwa ƴar fillo abu ba tare da izinina ba" Ummul tai bedroom ɗinta da sauri ta kira Umar-khan ta ce. "Ka kira Yaa Sheikh yanzu ga matarsa Zahrah nan zuwa, kasan Halisa na wajansa" tana faɗin hakan ta kashe kiran. Kiran telephone line ya tsayar da Zahrah daga tafiya part ɗin Yaa Sheikh, ta ɗaga kiran tare da cewa "Hello" Jadda dake bisa layi ta ce "Waye ne za a fasa mini kunne kamar yaƙi?" Zahrah taja tsaki a ranta ta ce "Matar Aliyu mana?" Jadda ta zabga Salati ta ce "Yaushe Gadanga ya yi aure kuma?" Zahrah ranta ya ɓaci ta ce "matarsa Zahrah" Jadda ta ce "Uban meye kuma Zahra? A to Allah ya isa ban yafe ba maganar da nayi dake, maza maza mutum nake nema bake ba don Allah, kije kiji da Iyaye abu a kwance kamar tawul ɗin wankan mai jego" wani kyakkyawan tsaki Zahrah ta ja. Tamkar Jadda ta fasa wayar haka tayi ta ce "Uwarki ki kaiwa tsaki, ai sai yanzu na tabbatar Gadanga bai aure mace ba, mai siffa irin ta fir'auna da ƙaruna, baki kamar maliya tayi ambaliya" kashe wayar Zahrah tayi baki ɗaya tsanar mata ya ƙara zama daram a zuciyarta. Ko sallama ba tayi ba a haka ta shiga part ɗin Yaa Sheikh, a tsaye ta gansa ya baza Alkyabba sai ƙamshi yake zabgawa wani irin kyau ya yi mata wanda bata taɓa ganinsa ba, ya ƙara girma da faɗi. Ta sauya tafiya tana kaɗa jiki cike da kissa ta nufesa tana zuwa ta ce. "My Excellency, you look good kayi kyau sosai" ta rungumesa ta ce "I love you husband" ya buɗe ido yasan daman babu gaisuwa a tsarinta. "Yaushe zaka bani damar zuwa sashinka na tayaka barci? Na fara gajiya kawaici na ya ƙare ina buƙatar mijina" sai a lokacin ya kalleta sosai a hankali ya ce "Sanda ki ka shirya" zata sumbaci bakinsa taji kamar wani abu yana yi mata yawo a jiki ta ɗan motsa ta ce "Uhm daman nace a daina fita da ƴar aikina ba tare dana sani ba, kuma idan da hali ta kwashe kayan zuwa sashen masu aikin gidan nan" ta zabura sbd abin da yake ƙara bin jikinta gudun kada ta bata kanta a gaban Yaa Sheikh tayi saurin cewa "I'll be back" ya lumshe idanun tare da buɗewa tai saurin ficewa. Wani irin fisgar numfashi ya yi jin yadda ta riƙesa sosai ta baya, gaba ɗaya ta jiƙa masa bayan riga ta bakinta. Ya saka tattausan hannunsa tare da fito da ita waje daga cikin Alkyabbar jikinsa. Ya dubeta ya kalli hannunta brush ne wanda ta wanke baki ta tura baki ta ce. "Ji nayi tana cewa zata kwana dakai fa Abba shi ya sa" wato ita ta kuri Zahrah?. Ya juya zuwa bedroom har lokacin jikinta baƙwari sosai suna zuwa taga ya jawo Injection yana zuƙar ruwa gabanta ya faɗi sosai. "Allah sarki Abbana waye babu lafiya kuma?" Da ace dry halinsa ne babu abin da zai hana shi yi ya juya ya ce. "Ƴar fillo" ta haɗiye yawo ta ce "A'a wallahi lafiya nake,don girman Allah Abba kada kayi mini don soyayyarka da Annabi wlh banso" ganin ta gaske yi mata zai ta kwasa zata gudu ya damƙota tare da zama da ita akan cinyarsa ya ce. "Shhhhh, ina gaisuwata?" Ya faɗa yana ajjiye allurar gefe ɗaya. Ta sauke numfashi ta ce "Naji tsoro ashe bani za aiwa ba" ya dai bita da idanu a hankali ta saƙalo wuyansa tare da ɗora bakinsa a kumatunsa, ta sakar masa kiss ya saka hannunsa a bayanta tare da yin ƙasa da trousers ɗin jikinta, idanunsa cikin nata a haka ya ɗauki Injection. Halisa tai murmushi tana ƙara yi masa kiss a kumatu shi kuma ya saita Injection ɗin a jikinta. A hankali ta dawo bakinsa sai kuma ta fasa ta ɗaga idanu tare da kallon Yaa Sheikh ta ce "Abbana ina son ka" a karo na farko ya sakar mata murmushi wanda yasa ta zuba masa idanu kamar bata taɓa ganinsa ba, ya sumbaci goshinta ya ce. "I na... Ina.." tai dry ta ce "Yawwa Modibbona ni ma kace kana so na" ya ɗora tsinin allurar sosai a jikinta ya ce "Ina.. ina son" bai ƙarasa ba ta ce "Ina son k....," wani ihu ta fasa daidai lokacin daya tsira mata tana ƙoƙarin sakin kuka ya kame bakin kukan da nasa bakin ya rungometa sosai a jikinsa... Paid book 500 08119237616 Allah ya nuna mana Monday ai weekend lfy🥱