*SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *SHAFI NA ƊAYA* Sanin cewar a kwai banbanci a cikin duniyar da Allah subuhanahu wata ala ya halitta masu ɗauke da halittu mabanbanta jinsi,bayan ya halicci duniyar mutane, da kuma waɗanda ba'a ji ko gani gare su sai dai duk wanda ya yi imani,ya na da yaƙinin samuwarsu a cikin duniyar da muke cikinta,da sauran halittu na dabbobi.Allah gwani wanda ba shi da abokin tarayya a cikin gwanintar halintunsa,ya halicci mutane ya kuma nuna babu wani banbanci a tsaƙanin su,sai wanda ya fi wani tsoron kiyaye abin da ya sharaɗa game da bautarsa,tabbas wannan haka ya ke a gurin Allah,amma kuma yayin da jinsi na bil'adama suka ɗauki sabanin haka,sun ɗora mizanin hankalin su suna auna banbanci na jinsi ta hanyar duba ga mulki,kuɗi ko kyawu na halitta.Su na kallon waɗanda suka mallaki waɗannan ababen na more rayuwa ga mafi ƙololuwar more rayuwa,wanda duniya ta yi maraba da zuwan sa kuma su ke kurɓan ruwan mafi ƙololuwar ɗaɗi a cikin ta. Haka ta kasance ga wannan matashi mai cike da kyawu da kuɗi da kuma baiwar ilmi da Allah ya azurta shi dashi,ya na ji da kansa da kuma kalar rayuwar da ya tsinci kansa a cikin ta,bai san a kwai wani ƙunci ko wani ƙalubale da Allah ya ke jarabtar bayin sa,waɗanda suka yi imani domin ya gwada ƙarfin imanin su da shi. Tabbas duniya ta na gara masa ƙwallo yadda ya ke so,domin ya fito daga cikin farin jadawali na tsarin rayuwarsa don ya yi gam da katar da bai fito daga cikin baƙin jadawali ba!Waɗanda da duniya ta ke musu kamun kazar kuku, su shiga halin ƙaƙa na iya tare da tunanin makomar rayuwar su. Sanye ya ke cikin shadda ruwan bula gizina,sai ɗaukar ido da sheƙi take ga wani daddaɗan ƙamshi da ke tashi a jikin sa wanda ya ke sanyaya zuciyar duk wanda ya shaƙi ƙamshin. Tuƙi ya ke cikin gwanance wa da kuma yanga,dan yadda yake jan motar ya ke kamar mai jin bacci ya na lumshe idanunsa masu kama da mai jin bacci.Gefen sa amininsa wato Ak ya ke zaune a kujerar mai zaman banza da wayarsa riƙe a hannunsa ya na dannawa.Jefi-jefi su na taɓa hira duk da hirar ta su,ba ta wuce na 'yan daƙiƙa yayin da shuru yafi yawa a tsakanin su,kasancewar ta kowannen su ya na ji da kansa, dan sun haɗu ta ko ina ga kyau kuɗi da kuma wayewa da tsantsar ilmi. Wani irin ƙara motar ta yi ya ja birki ya tsaya cikin tashin hankali ganin wani tsoho ya shige masa gaba har ya buge shi da motar.Ya tsaya ya na kallon gurin da takaici,ganin yadda tsohon ya ke son ɓata mishi lokaci. Da sauri ya kuma buɗe murfin ƙoofar zai fita ya na faɗin"Wannan wawan mutumin zai ɓata min lokaci,an gaya mishi bani da aikin yi ne?" Ya fice ba tare da ya kula Ak da yake mishi magana ba,da sauri Ak shima ya fito sanin halin shi sai dai kafin ya ƙara sa Am ya wanka ma wannan tsohon mari har guda biyu. "Ba ka da hankali ne da wannan banzan ƙarfen na ka zaka ɓata min lokaci?Shashasha kawai!" 'Dan tsohon ya yi taga-taga ya faɗi har ya na fasa baki,da sauri Ak ya kama hannunsa ya mike sai kawai ya fashe da kuka,don shi kaɗai yasan halin da yake ciki. "Haba A.m ya zaka mari wanda ya haifeka rashin mutincin na ka ya kai haka?Dubi halin da yake ciki amma baka tausaya mishi ba." Harara ya watsa mishi kamar ba zai ce komai ba,har ya fara taku zuwa motar shi sai kuma ya buɗe baki ya ce, "Kai baka ganin abin da ya yi min?Jiya na fara hawa motar nan amma ya ƙuje min mota.Nasan kaf zuriyarsa babu wanda zai iya siyan ko da tayar motar ce."A.k ya yi shuru ya na kallonsa cikin takaicin halin sa,na rashin daraja talaka da nuna tsantsar tsana da hantara,amma shi a ganin sa ya kama ta ya dinga kawaici saboda yasan waye Ak kuma waye asalinsa. "Da izinin Allah sai ka sami dai-dai da kai ya faɗa ya na jin tsoro kasancewarta yasan waye shi ɗa ne ga Alhaji Muhammad Turaki,waye bai san wannan family masu ji da kuɗi da ilmi da wayewa.Cikin sa'a sai A.m bai ji abin da ya faɗi ba don ya juya ya nufi motarsa ya na tsaki. A.k ya zaro kuɗi masu yawa ya miƙa mishi ya na ce wa." Gashi Baba ka yi haƙuri don Allah ka je asibiti a duba ka." Ya faɗa ganin duk ya ƙuje a hannunsa.Da sauri ya karɓe ya na godiya,ganin kuɗ'in da ya ba shi dan shi gaba ta kai shi ,dama ya fito zai je ya saida kekensa gashi kuma ya sami wannan kuɗi. 'Dan tsohon ya dinga saka mishi albarka ya na hawaye kamar zai yi mishi sujjada, juyawa ya yi ya nufin motar da A.m yake ƙoƙarin tayar wa,sai kuma ya tsaya ya na kallon titin da alamun abin hawa yake nema a ransa ya na jin kawai ya haƙura da abokantakansu don ya sama ma zuciyar sa salama,da irin cin kashin da A.m yake yi wa talaka a gaban sa. A.m ya kashe motar ya fito ya na mishi maganar ya shigo,amma ko kallon inda yake bai yi ba sai ma juyar da kansa da ya yi,ya na kallon titi fuskar sa kamar an aiko mishi da mala'ikan mutuwa. "Well." Ya ce tare da ɗaga kafaɗunsa ya juya ya na faɗin"Shike nan tun da baza ka taho muje ba ni na tafi,sai mun haɗu a ofis ka taho min da fayal ɗin da mukai maganar dakai,sannan ka shirya gobe ne tafiyar mu". Ya ta da motar ya bar gurin A.k na kallon motarsa har ta ɓace wa ganinsa,ya ja numfashi mai zafi ya fesar ya riƙe habbar shi ya na jiran ɗan acaba,sai kuma ya fasa hawa mashin ya fara taku ahankali ya na jiran adaidaita.Tafiya kaɗan ya yi ransa a jagule ya na jin zafin yadda yake nuna tsanar talaka karara baya kawaici a gabansa,yasan cewar bazai taɓa iya canza aminin nasa ba don tsanar talaka a jinisa yake kasancewar duk family d'insu basa son talaka ya rabe su,shi kansa don Allah ya bashi tarin baiwar ilmin kasancewar Allah ya yi mishi baiwa da samin na'ura mai ƙwaƙwalwa,kuma saida suka mai da shi wani don yanzu ya na jin kansa a cikin jerin masu hannu da shuni. Murmushi ya so ya suɓuce mishi sai kuma ya dake,ya kauda kansa tamkar bai ga motar A.m da ta yi ribas ta dawo ba,da ma yasan dole ya dawo kamar yadda suka saba duk sanda suka yi faɗa a tsakaninsu, wanda ba ya wuce sati don A.m bashi da haƙuri ko kaɗan gidan su da gurin aiki duk sun san haka,shi kuma A.k ba ya ɗaukar raini mafi yawancin lokuta mutane su na mamakin yadda abokantakarsu ta yi ƙarko a haka don kullum cikin faɗa suke kamar wasu yara Daddy shi ne ɗan sasanci,sam baya gajiya kasancewar ya na ji da shi saboda irin ci gaba da ya ke kawo mishi a cikin kampanin sa,ya sani cewar in har babu A.k to kampaninsa bazai ci ga ba. A.k ya kauda kansa bai tanka mishi ba sai wayar sa da ya ciro da nufin ya kira direban sa ya zo ya ɗauke shi,don ya fasa shiga cikin a daidaita."Ganin ya taho kamar zai buge shi da motar amma bai kula ba,sai ɗauke kansa da ya na kallon gefe don cike yake dashi. A.m ya leƙo ta tagar motar sa ya ce ya na murmushi mugunta,don daga ganin yadda ya yi ya san ya gaji matuƙa."Don Allah ka zo mu tafi kasan dole na dawo,Daddy ya kira ni ya na son ganin mu". Banza ya yi da shi ya ci gaba da tafiya,ganin haka ya fito tare da kashe motar sai kawai ya kama shi da kokuwa zai tura shi cikin motar,kamar dai yadda suka saba duk lokacin da suka yi fad'a. Bai wani ja ba ya shige cikin motar ransa a haɗe,dariya sosai A.m yake mishi don ya na matuƙar son aminin nasa saboda riƙo da gaskiya, kuma bashi da shishshigi a lamuran sa. Tun da suka shiga cikin motar babu wanda ya yi ko tari a cikin su,da ma ɗabi'ar su ce shirin basu cika magana ba kasancewar kowa naji da kansa. Wayar A.k ta yi ƙara alamun ana kira amma sai A.m ya kai hannunsa ya kashe wayar baki ɗaya,don yasan mai kiran taɓe bakinsa ya yi ya ci gaba da tuƙi cikin kwanciyar hankali.A k ya ja fasali tare da buɗe baki da nufin ya yi magana,amma da ya kula rigima yake ji sai kawai ya kauda kanshi bai ce ƙala ba don har yanzu ransa a ɓace yake da abin da A.m ya yi ma mutumim da ya haife shi. Ko da suka ƙaraso tangamemem get ɗin gidan mai gadi ya buɗe musu get,A.m ya yi parking bai kula da gaisuwar da maigadin yake mishi ba ya shige cikin gidan,yayin da A.k yabi bayan sa kasancewar ba'a yi mishi shamaki da cikin gidan ba. ******* Juwairiya zaune a gefen ƙanin ta Ibrahim ta zuba mishi idanu, ya yin da hawaye suke gasar turarreniya a fuskarta,ji ta ke kamar ta yi hauka tsabar damuwa ta na jin wani irin baƙin cikin halin da suka tsinci kansu. Zura hannunta ta yi a cikin kofin ruwa ta shafi fuskar Ibrahim da yake kwance rai kwakwai mutu kwakwai,sai kuma ta kama shi ganin yadda ya zaburat amkar zai shiɗe. Mama da ke tsaye a bakin ƙofa fuskarta ɗauke da tsananin damuwa da ƙunci ta janye tagumin da ta yi tare da ajiyan zuciya mai ƙarfi."Anty Juwairiya mutuwa zan yi ga shi Baba ya ƙi dawowa." Ya faɗa da wata irin murya da yake ƙoƙarin haɗa kalmomin da su."Baza ka mutu ba Ibrahim ciwo ba ya kisa."Mama ta ce cikin tausayin sa. Juwairiya kuwa ta kasa magana sai kuka ganin gudan jinin na ta ƙanin ta tilo na cikin wani mawuyacin hali, ji take da ma ace ciwon a jikinta yake.Sun jima suna tsaye a kansa da numfashin sa yake baraxanar ɗauke wa,hankalin su a tashe sai shafa masa ruwa suke yi suna kuka gunun ban tausayi. Juwairiya ce ta miƙe ta na faɗin"Mama bai kama ta mu zuba mishi ido mu na kallon sa a cikin wannan halin ba,tunna Baba bai dawo ba zan fita na samo abin da za'a kaishi asibiti.Ta ce cikin kuka Mama ta kasa ce mata komai duk da ta na tunanin in da za ta samo kuɗin,amma har ta na shirin fita ba ce komai ba."Juwairiya na shiga uku!Ya sume."Ta ji muryar Mama cikin ƙaraji dai-dai lokacin da ta fice da ga gidan. *Follow,read,comment,share.* *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *SHAFI NA BIYU* Da sauri Juwairiya ta dawo ta rungumshi da hannunta ɗaya,ɗayan kuma ta na shafa mishi ruwa, ajiyan zuciya ta sauke mai ƙarfi ganin ya buɗe ido,don hankalin su ya tashi maƙura gani suke kamar mutuwa zai yi ganin yadda idanunsa suka ƙaƙƙafe. Juwariya ta miƙe ta na faɗin."Tun da ya farfaɗo bari na je na naimo mishi magani."Miƙewa ta yi ba ta jira amsar da Mama zata ba ta ba ta fice da ga cikin gidan ta na sharar hawaye. A hankali ta ƙarasa shiga cikin shagon na sa ganin yadda ya haɗe rai tun da ya hangeta ta na tahowa,tamkar an aiko masa da mala'ikan mutuwa ya haɗe ransa babu wani walwala.Jikin ta ya yi sanyi sai ta tsaya a bakin ƙofar ta kasa mishi magana kuma ta ƙi ta tafi duk da kallon kora da hali yake mata. "Lafiya ki ka yi min tsaye kofar shago kamar na saki ki?Ya faɗa ransa a ɓace"Don Allah ka taimake ni Bala kasan mai ya kawo ni a karo na biyu,wallahi suna cikin wani hali na rantse maka wannan karon zan naimi kuɗin ka na baka."Ta faɗa da muryar kuka fuskarta bayyane da damuwar halin da take ciki. "Ni ina ruwana na gaji da baki bashi kuma ba kawo min kike ba,sannan na nuna miki hanyar da zaki bi mafi ɓulluwa kin nuna a'a wai ke ustaziya,to sai kije can amma ko maganin biyar ba zan baki ba."Tamkar zai kai mata duka yake magana ganin haka sai kawai ta juya,dan ta saka a ranta yau bazai bata ba. "A'a Juwairiya tafiya zaki yi."Ya faɗa da sanyin murya ganin ta kama hanyar fita,sai kuma ya ƙara matso da fuskarsa gurin ta yace."Kin cika kafiya ki yadda ki amince ko sau ɗaya ne,Allah zan baki duk abinda kike so.Kin san ina son ki Juwairiya na san babu yadda za'ai na same ki,wannna dalilin ya sa nake so ki amince min kar soyayyata ta faɗi a banza." Ƙarashe fita ta yi da ga shagon dan abin da yake so bazai samu ba.Mahaifiyarta kullum ta na mata nasihar ta tsare kanta da ga aikata zunubi mai girma wanda Allah yake fushi da wanda ya aikata,kuma ya yi hani ga bayinsa muminai na ƙwarai. Gidan ƙawarta Mariya ta wuce ta same ta zaune akan tabarma a cikin falo ta na gugan kayan ta da dutsen guga na gawayi,sallama kawai ta yi ta zauna a kan tabarma ji take kamar zatai hauka."Juwairiya lafiya kike mai ya faru?"Mariya ta jera mata tambayoyin da ta kasa ba ta amsa ba,sai ta janye hannunta da Mariya ta kama tare da share hawayen da ya gangaro mata. Mariya ta ƙarashe share mata sauran hawayen ji take ita ma kamar ta saka kuka,ta ɗago idanunta da suka kaɗa suka yi ja ganin ƙawar ta ta na kuka tace."Ki yi min magana Juwariya!Kin san ba na jure ganin ki a cikin wannan hali,abin da ya sa naƙi dawowa kin san halin Baba Sani na rasa yadda akai ya takurawa rayuwar ki baya son kowa ya raɓe ki,dan haushin koron da yake yi nake ji irin kullen da yake miki ko fa yaran sa baya yi mawa,lamarin sa akwai ayar tambaya ,dan ina tunanin akwai lauje cikin naɗi!"Ta ja fasali ta na kallon Juwairiya da kukan ta ya tsananta,tuna yadda ya tsane ta yake azabtar da rayuwarta.Mariya ta ci gaba da magana cikin ɓacin rai ta na cewa. "Ina jin takaicin halin da kike ciki amma ki sani bawa bai isa ya canza ma wani rayuwar sa ba,kin ga da Baba Sani baya miki kulle sai na sama miki aikatau ni bashi nake yi ba hankalina kwance. Juwairiya ta sauke ajiyar zuciya duk da baƙin cikin da take ji na ƙin barta ta yi aikatau,wanda mahaifinta ma ya amince amma ƙememe ya hana ta da ta na yi ƙila da basu shiga cikin uƙubar rayuwa ba,gashi tun da ta gama sakandiri ya hana ta karatu amma yaran sa duk sun yi. Duk da lamarin na ci mata tuwo a ƙwarya amma ba ta ce ƙala ba,sai dai zuciyar ta cinkushe take da damuwa tare da tunani iri-iri. Mikewa Mariya ta yi ta shiga kicin ta zuba tuwo da miyar kuɓewa ta kawo mata ta na faɗin."Gashi tun ɗazu na so na kawo muku amma ina tunanin wannan Baban naki,kuma Auwal tun da ya tafi islamiya bai dawo ba balle na bashi ya kawo miki."Ta miƙa mata tare da kwance ƙullin zaninta ta ciro naira ɗari biyu ta miƙa mata. Tsabar murna sai kawai ta rungumeta tare da fashewa da kukan murna,Mariya na taimakon ta ƙwarai ta na fatan Allah ya bata ta taimaka mata. Rako ta ta yi ta siya magani sannan ta kaita dai-dai kwanar lungun gidansu.Da sauri Mariya ta saki hannunta ta na faɗin."Na shiga uku wallahi gashi nan duk da ƙin kaiki gida da na yi amma ya na nan ya na sa ido ya san ki fita,ke Juwairiya wannan ko mijin ki ne sai haka."Ta ruga da gudu har ta na tuntuɓe bayan ta gama maganar don Allah ya saka mata tsoron shi,bashi da mutunci in dai akan Juwairiya ne. Juwairiya da jikinta ya fara rawa ji ta yi kamar ƙasa baza ta iya ɗaukar halintar ta ba,ta tsorata iya tsorata zabura ta yi kamar zata ruga sai kuma ta fasa ta na karanta wallahu galibun ala amrih ganin ya tunkaro ta. Ya ƙaraso ya na mata wani irin kallo da shi kaɗai yasan ma'anarsa."Ina kika je?"Ya tambayeta da murya kakkausa tare da saka ƙafafunsa ya take mata 'yan yatsun kafar,ta rintse ido ta na jin wani iri madarar azaba ya na taso wa daga kan 'yan yatsun na ta ya na zagaye ilahirin jikinta,taso ta matsa domin akoda yaushe ya tsaya kusa da ita ta na ƙalubantar yadda yake matsowa daf da jikinta.Amma hakan ya ci tura ganin yadda ya take kafarta ya hana motsinta. "Bana hana ki yawon maula da uwarki ta koya miki,bayan Yayana bai rage ku da komai ba."Ya faɗa ya na ƙara kusanci da ita fiye da na ɗazu. "Don Allah kayi haƙuri bani ta yi wallahi ban roƙe ta ba,kuma Ibrahim zan bawa."Tace yayin da taƙi shaƙar numfashi ba ta son ta shaƙi iskar hucin bakin sa da take jin sa a fuskarta.Ya ɗa ga kafafun na ta ya na ƙare mata kallo hakan ya bata damar shirin arcewa ko takalminta bata ɗauka ba,dan ya zame lokacin da ya take ƙafarta. Da gudu ta ruga amma sai ta faɗi ƙasa yayin da miyar tuwon ya zube,amma duk da zafin da take ji bai saka ta yadda tuwon ya zube ba,ta zabura ta miƙe hanyar gida dai dai sanda ta ji ya na faɗin."Ni da kene a duniyar na baza ki taɓa jin daɗi ba matuƙar ina raye,haka kawai na yi sakaci har tunanina ya faru mu zu ba mu gani Juwairiya na shiga cikin ɗaki ta fashe da kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro,a ranta ta na jin baƙin cikin halinsa bata san mai ta tsare mishi ba,amma ya saka ma rayuwarta ƙahon zuƙa. Koda ta shigo Mama ba tace komai ba har ta sha kukanta ta ƙoshi don tasan mai ya faru,tunna babu abin da za ta iya shi yasa bata tanka mata ba,sai ta jawo kwanon tuwon ta ba Ibrahim sannan ta bashi magani ragowar taci ta ragewa Juwairiya duk da babu miya kuma ta ji ƙasa-ƙasa a tuwon. Bayan ta gama kukan taji sanyi a zuciyar ta dama kukan shi ke sanyaya mata zuciya,duk lokacin da ya yi mata hakan don babu wanda yake ko tari a cikin iyayenta,su kansu tsoron sa suke yi duk da mahaifinta shine babba. Miƙewa ta yi ta ɗauro alwala ta yi magariba sai ta yi zamanta ta na jan carbi yayin da hawaye ke zuba fuskarta,wani gefe na zuciyarta ta na hasaso mata lamura sosai game da Baba Sani. Baba Sani ya yi tsaye a gurin bayan tafiyar ta ya na tunani sannan ya ƙarasa dakalin ƙofar gidan ya zauna ya na gadin masu zuwa gurinta,ko da ka kira sallar isha'i ya yi sannan ya dawo ƙofar gidan ya ci gaba da gadin gurin. Sai misalin tara na dare mahaifin Juwairiya ya yi sallama ya shigo da ƙullin leda mai ɗauke da garin rogo gwangwani biyu da siga.Mama ce ta amsa sallamar ta ƙarbi ledan tare da shinfiɗa mashi tabarma,lokacin har baccin wahala ya fara ɗaukar ta don yunwa take ji matuƙa kuma kamar zazzaɓi yake son kama ta. Jin sallamar ya sa ta buɗe idanu ganin leda a hannun Mama ya sa ta miƙe tare da ƙarban ledar bayan ta yi mishi sannu da zuwa ta fice dan ta jiƙa garin.Ya kalli Ibrahim dake kwance ya na bacci ya shafa fuskarsa ya na faɗin." Ya jikinsa?Ina can amma hankalina ya na nan kin san jiya ƙafarsa ta bani tsoro."Yace ya na lasar bushashshen bakinsa dan rabon sa da abinci tun jiya da yamma da suka girka taliya leda ɗaya gashi ya wuni ya na faskare. "Da sauki amma ya kama ta a maida shi asibiti gaskiya,yau ya bani tsoro ina ki kamar zan rasa Ibrahim saboda halin talaucin da muke ciki."Tace sai kuma ta rushe da kuka ta na fyace majina. A sanyaye Juwairiya ta ije garin da ta jiƙa ganin Mama ta na kuka ta koma gefe ta zauna ta na jin zafin Baba Sani dan ita gani take shi ya takurawa rayuwarsu da ya hana ta naimi aiki,in da ace ta na aiki rayuwar su ba ta yi muni haka ba,ga Mariya da take aikin suna jin daɗi kuma matar ta na taimaka musu. "Ki bar kuka dan Allah da kin san halin da na wuni da kin tausaya min!Na dage tuƙuru ina faskare sai da na gama Malam Aminu yace bashi da kuɗi sai gobe,daƙyar na samu ya bani naira ɗari biyu wai shima kwana biyu ba cinikin iccen. Shuru sukai cikin jimamin rayuwar su kowa ya na takaicin yadda suke tsotsan tsamiya,ganin Baba ya dawo Juwairiya ta miƙe tare da yi musu sai da safe ta tafi ɗakin da take kwana. Washegari da safe misalin bakwai da rabi ta shafa addu'a,sannna ta miƙe ta nufi waje dan wanki zatai da aka kawo musu da safe kuma ana so anjima,murna sosai ta yi dan aka wo kuɗin wankin za su sami su yi girki. Da sauri ta ƙarasa ta na faɗin."La Mama har kin fara."Bata ce mata komai ba sai botiki da ta miƙa mata ta ibo ruwa a randa. Basu gama wankin ba har misalin tara da rabi bayan sun gama Juwairiya ta fita tayo musu cefanen taliya suka dafa da mai da yaji.Bayan ya dawo daga sallar asuba ya kwanta don ji yake ko ina na jikin sa ya na ciwo,bai tashi ba sai da aka gama girki shi ma sai da Juwairiya ta tashe shi,dan tasan yunwa ce ke damunsa. Bayan yaci abincin ya miƙe tare da fita ya na son ya ga kanin nasa,akan maganar komawa da Ibrahim asibitin da kamar yadda likitocin suka faɗa. Ya na ƙoƙarin shiga shashinsa suka yi kicibis saura kaɗan su yi karo,Baba Sani ya matsa ya na kallon ɗan'uwan nasa ya ce."Lafiya yaya baka da lafiya ne?Ji yadda ka koma kamar wanda ake iban shi ana miya."Yace da maganar shi ta izgilanci ya na karkaɗe jakar zuwa aikin shi,dariya kawai ya yi mai kama da yaƙe yace."A irin wannan rayuwar ka na sane da halin da nake ciki ni da iyalina,yanzu ko taimakon da kake yi min ka daina."Ya ƙarashe magana da takaicin yadda ɗan'uwan nasa ya daina taimaka mishi tun tsawon shekaru da irin butulcin da ya yi mishi. Hannun shi ya watsa ya kalleshi ya na kallon agogo."Sauri nake yi yaya kaga na yi latti kuma kasan yanayin aiki na,yi sauri ka faɗi abinda ke tafe da kai.Kuma da kake maganar ba na taimaka maka nauyi ne ya yi min yawa kowa ya ji da kansa." "Haka ne Allah ya shige mana gaba,amma ya kama ta ka duba rayuwar Juwairiya kaga ni bani da shi da zan saka ta a makaranta,kuma kace ba aure zakai mata ba baka da ƙuɗin auren da ita." "Haka na ce don ni yanzu ba ta aure nake ba,sabon gidana nake son na kammala.Ya bashi amsa a taƙaice sannan ya ɗora da ce wa."Kuma da kake maganar na saka ta a makaranta baka ga yadda take mara kamun kai ba can zata dinga watsewa da mutane,ka na sane da irin ƙorafin da nake maka a kanta ni nasan halinta da nake zaman gida." Shuru ya yi ya na takaicin abinda ya faɗa ransa ya yi zafi,shi dai yasan kawai ya tsaneta ne amma yasan wacece 'yarsa wani irin hali take dashi. "Yaya na fa gaya maka aiki zan tafi amma ka tasa ni gaba kana ta wasiƙar jaki,ina sauri ne in kima baka da abin faɗe na tafi imna dawo saimu tattauna."Ya ce dashi ya na ƙoƙarin fita da sauri ya tare shi sannan ya ce."A kan maganar komawa da Ibrahim asibiti ne,kuma gashi bani da kuɗi dan Allah ka taimaka...." "Haba yaya kasan fa bani da ƙuɗi nima hidima tayi min yawa kowa yaji da kansa,amma ga dubu ɗaya kuje Allah ya ba da lafiya."Ya miƙa mishi 'yan ɗari biyar guda biyu ya fice ya barshi a tsaye kamar sanda ya na tunanin butulci irin na ƙanin nasa. A sanyaye ya shigo cikin sasan sa ya zauna akan turmi kamar babu laka a jikinsa,bai ce komai ba har zuwa wani lokaci sannan ya ja numfashi ya na kallon Mama dake ninke kayan da suka wanke har sun fara bushewa. "Lailai ɗan adam butulu ne."Yace cikin raunanniyar murya sannna ya ɗora da cewa."Wai yau ni Sani yake wulaƙanta wa kan kuɗi ya manta yadda na wahala dashi dan ya sami ingantacciyar rayuwa.Mama ba tace mishi komai ba sai gyaran murya da ta yi,dan babu wani abu sabo a cikin halinsa duka sananne ne a gurinta. Juwairiya na kwance bayan ta tashi ta yi sallar nafila ta yi addu'a ta koma ta kwanta,idanunta babu alamun bacci sai juyi take yi ganin haka sai kawai ta janyo carbi ta na ja,idanunta a rintse zuciyar ta na fatan samun maslaha a rayuwar su tunannin ta inda za'a sami kuɗi a mai shi asibiti,don likitocin suna tunanni aiki za'ai mishi a ƙafar. Kawai sai ta ji ana ƙoƙarin buɗe ƙofar ɗakinta tsoro ya kama ta,tunawa da ta yi ta manta bata saka sakata ba da ta fita zuwa alwala.Tsananin tsoro ya kama ta ta rintse idanunta ta na tunani ta ya ya kai wani ya shigo cikon gidan su,dan Baba Sani ya gyara gidan kuma akwai ƙofa na masu kuɗi mai ƙarfi gidan. Ba ta gama wannan tunanin ba ta ji mutum ya shigo ya nufi makwancinta,ta buɗe baki da nufin ta yi ƙara sai kawai taji an toshe mata baki da wata irin murya da nufin a ɓatar da tunanin mutum ga sanin mamallakin muryar aka ce."In kika yi ihu saina kashe ki?Ya faɗa tare da soka zungureriyar wuƙa dai dai cikinta,amma ta yadda bazai cutar da ita ba. Wani irin tsoro da tashin hankali ya ziyar ce ta taji tamƙar numfashinta zai yi balaguro zuwa wata duniyar wacce take da banbanci da wacce take rayuwa a cikinta."Da gaske abin da sautin amon kunnnuwana suke gaya min muryar Baba Sani take amo a cikin dodon kunnuwana?To mai ya shigo dashi cikin ɗakina a wannan sulusin daren?"Irin tarin tambayoyin da suke ta bijiro mata a cikin zuciyar ta wacce ba ta samu ko da amsar ɗaya ba. _Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Mu haɗu a shafi na uku dan har yanzu shinfiɗa ne har ba'a fara ba.Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku man da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. *FOLLOW, READ, COMMENT, SHARE* *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *SHAFI NA UKU* Hannun Baba Sani ya sauka a ƙirjin Juwairiya tare da wasu tagwayen hawaye masu tsananin zafi da ƙuna a fuska.Ta jin wani irin tsananin tashin hankali a zuciyarta yayin da take ji a cikin zuciyar ta tamkar za ta haɗiye zuciya ta mutu."Da ma burin sa kenan a kai na ya hana rayuwata samun sukuni,kullum ya na bibiyata tare da daƙile farin cikina?Me na yi masa wanda ba zai iya ɗauke mugayen idanunsa a kaina ba,a matsayina na ƴar wansa wanda suka fito ciki ɗaya?Wayyo Allah ina ma ace ranar mutuwa ta ce aka nuna min ba wannan ranar mai baƙin gani da muni a cikin zuciya ta ba.Ihu ya kama ta na yi ya kashe ni kamar yadda yace ko na yi shiru ya ɓata min rayuwa?"Ta tambayi kan ta cikin tsananin ruɗani dai-dai lokacin da ta ji saukar hannun sa a hurumin da ba na shi ba.Sai ta rufe idanunta ta na kiran sunan Allah tare da karanto duk addu'ar ta da fito daga cikin bakin ta. Da sauri Baba Sani ya janye hannun sa daga ƙirjin ta tare da fasa abin da ya yi ninya,jin motsi daga waje."Sannu Malam ka yi a hankali jikin ka babu ƙarfi."Suka ji muryar mahaifiyar Juwairiya ta na magana cikin tausayi. Hankalin Baba Sani ya tashi sosai ya daɗe ya na dakon wannan ranar tun lokacin da Juwairiya ta fara girma ya saka kwaɗayin sa a kanta,gashi ya sami dama amma kuma kamar hakonsa bai cimma ruwa ba. Dai-dai saitin kunninta ya saita tare da raɗa ma ta."In kika yi magana sai na kashe ki."Hakan ya sa Juwairiya kame bakin ta ta yi shuru sai hawaye dake zuba a fuskarta. Ya tsorata iya tsorata ganin sun shige cikin bayin ya buɗe kofar ya fice cikin sanɗa,Juwairiya ta fashe da kuka tare da fita daga cikin ɗakin a ranta ta ƙudirta ba za ta ƙara kwana a cikin sa ba.Fitowar ta ya dai-dai da lokacin da suka fito daga cikin bayin.Faɗawa kan jikin Mama ta yi ta fashe da kuka ta na wani irin kuka mai ƙarfi da ta da hankali ba ta damu da daren da ya tsula ba.Cikin tashin hankali da tsoro Mama ta rungume ta ta na faɗin."Lafiyar ki ɗaya Juwairiya dare ne fa?Ko kin yi gamo ne."Irin tarin tambayoyin da take mata amma ba ta kula ta ba sai kuka da take yi mai ɗaukar hankali,ganin kukan na ta ba na ƙarewa bane Mama ta ja hannunta suka shiga cikin ɗaki lokacin Baba har ya shige ya kwanta,saboda gudawa da yake fama da shi ya kasa tsaya wa ya tambayi abin da ke faruwa. "Mai ya same ki lafiya?"Mama tace don zuwa yanzu kukan ya fara ba ta tsoro ta na ganin kamar Juwairiya gamo ta yi,yayin da ta wani gefen ta fara ba ta haushi bacci ne sosai a idanunta. Juwairiya ta kasa magana sai kuka haka Mama ta yi ta gaji ta koma ta kwanta yayin da ta barta zaune tamkar ta haɗiye zuciya ta mutu. Washegari da safe Mama duk lallashin da ta yi mata akan ta gaya mata abin da ya faru,amma taƙi ƙarshe sai dai ta yi mata ƙaryar mafarki mara kyau ta yi.Mama ba don ta yadda ba ta ƙyaleta amma zuciyar ta ta na gaya mata a kwai ɓoyayyen lamari,kasancewar Juwairiya ba ta taɓa kasa kwana ita kaɗai ba.Hankalinta ya tashi musamman da Juwairiya tace mata ba za ta ƙara kwana a ɗakin ita kaɗai ba,sai dai a haɗa ta da Ibrahim wanda Mamma bata iya kwana sai da shi saboda ciwon sa,gashi ta na da mugun bacci.Duk da jikin Baba da ya kwana babu daɗi amma haka nan ya shirya ya fita bayan ya sha magani. Wunin ranar Mama ta kasa gane kan Juwairiya duk irin tarin tambayoyin da take mata,don ko ruwan koko da ta dama taƙi sha daga ƙarshe wani ƙarya sake yi mata tace ba ta da lafiya. ****** Gidan cike yake da mutane kai da gani kasan ana farin ciki a dalilin bikin ƴaƴan gata, ga kayan abinci da na tsotse-tsotse da a ke ta fita da shi.Bikin na yaran manya ne waɗanda duniya take hannun su kuma ta yi na'am da zuwan su duniyar,suke rayuwa a yadda suka tsara kuma suke ƙurɓar ruwan daɗi a cikin ta. Naira ta na tsala kuka tare da nai man taimakon agaji da son ɓoyeta domin ta adana kanta ga masu buƙatar ta.Ruwan kuɗi kawai yake tashi da jerin gwanon motoci wanda ba zasu irgu ba.Wannan biki ne wanda ya amsa sunan sa kuma ya buƙaci a buga a jarida,wato bikin Muhammad Dawood Turaki da amaryar sa Zainab Abubakar mai shadda.Waye bai san waɗaɗnan hamshaƙan masu kuɗi da samu rayuwa mafi ƙololuwar daɗi a gare su ba. Muhammad Dawood ɗa ne ga wani hamshaƙin mai kuɗi daga cikin turaki Family,wanda duniya ta san shi har da ƙasashen waje don ma yafi gudanar da harkokin sa a can.Tsarin rayuwar su irin na turawa da zallar boko.Gida ne na ƴanci da rayuwa babu taƙurawa da samun kwanciyar hankali.Suna da matuƙar kyau da asali mahaifin sa haifaffen garin Zariya ne.Ya gina katafaren gidan sa mai kyau a unguwar Zangon shanu,gida mai kyau na bene da tsari.Matan sa biyu Hajiya Khadija wato mahaifiyar A.m sai amarya Hajiya Binta Yaran sa bakwai Muhammad shi ne na farko wanda aka fi sani da A.m,sai kanin sa na miji sauran mata ne guda biyu sai kuma bangaren amarya ta na da uku.Suna zaman su lafiya kuma kan su a haɗe yake. A.m mutum ne mara daɗin sha'ani ga rashin haƙuri ga saurin ƙulewa,ba ka taɓa gane in da ya sa gaba shi kullum mutum a gurin sa bai iya ba kuma ba a yi mishi gwanin ta ba.Kannin sa suna shan faɗa shi ya sa basa ƙaunar ya zauna a gida in kayi magana,yace ka faye surutu in kayi shuru yace ya na magana an raina shi.Shi komai a gurin sa laifi ne sannan ba shi da fara'a ko wasa ba ya yi dasu.Faɗin halin A.m abu ne mai wuya domin ya na da murɗaɗɗen hali baka gane in da yasa gaba,wannan dalilin ne ya sa ba shi da wasu abokan sai A k wanda ya jure halin sa duk da wani lokacin shi ma hutsu ne,amma ya san yadda yake tafiyar da shi.Muhammad ɗan gata ne a gurin mahaifin sa ga shi fari kyakykyawa dogo mai aji da tsafta.Wan mahaifin sa Alhaji Sama'ila ya na matuƙar ji da shi domin a hannun sa,ya tashi ya ma fi Daddy sa kuɗi sai dai shi Allah bai ba shi haihuwa ba. Ya na matuƙar son yaga ya haihu saboda ya samu magaji har ƙasar waje ya kai matan sa uku a ka yi musu dashen kwai,amma Allah bai nufa cikin zai tashi ba,ƙarshe daga baya kan dole ya fauwala ma Allah lamuran sa ya na addu'ar Allah ya sa ya na da rabon haihuwa a duniya. Tun kafin a haifi A.m mahaifin sa ya yi ma Yayan sa alƙawarin ba shi duk abin da ya haifa,saboda haka ana yaye shi aka miƙa ma matarsa Karime.A.m ya taso cikin gata da shagwaba bai san damuwa ko a kasin haka ba.Duk karatun sa a ƙasar waje ya yi in da ya karanci (Economis)bayan ya kammala ya dawo gida Nigeria amma ba ya wata yake fita waje. Family ɗin Turaki mutane ne da ba ruwan su da harkan talaka ba sa hurɗa dasu,kuma ba sa shiga sha'anin su.A.m da ya tashi ɗauko tsanar talaka sai yafi kowa a cikin Family ɗin na su,don shi tunanin sa laifin sa ne da yaƙi tashi ya nema ya tsaya lalaci.Saboda mugun tunanin sa akan talaka ya sa ya tsani ma'aikatan gidan su kullum cikin hantara da mari yake musu laifi kaɗan zai kai duka,musamman masu aikin cikin gida. Zainab Abubakar ƴar gidan wani ɗan majalisa ne da yake tashe a yanzu kuma hamshaƙin ɗan kasuwa.Yarinya mai tashen kyau da ƙuruciya ta na ji da kanta tare da alfahari da kyan da Allah ya yi mata,ga ɗagawa da son nuna ita ma wata ce mai ilmi da kuma nera.Sannan ra'ayin ta yazo ɗaya da A.m na ƙin talaka ba ta da kirki sosai,amma in baka shiga sabgar ta ba ba zaka gane hakan ba.Zainab likita ta karanta a ƙasar indiya.Mahaifinta ya na ji da ita don ita kaɗai ya haifa,sukai hatsarin mota ya samu naƙasa ba zai ƙara haihuwa ba. Saboda haka yake ji da ita ba ya son ya ga ɓacin ranta komai take so shi take yi,gara mahaifinta ya na ɗan jan ido akan lamuran ta musamman shigar ta da ya tsana,amma mahaifiyar ta Hajiya Mariya ba ta barin ya tsawa ta mata a cewar ta in basu ba ta gata ba wa zasu ba. Zainab mace ƴar ƙwalisa da gayu ga ƙamshi a kwai son turare masu tsada da kamshi,ga son kwalliya ta na ɓata lokacin ta akan kwalliya ita rayuwar ta tafi ba ta hamimmanci akan kwalliya da charting,sai ta wuni ta na kalle-kalle a waya ko ɗaukar hoto.Kullum rana na duniya Zainab ta yi wanka sai ta ɗauki hoto ta yi posting ɗin shi ko da wankan kwanciya ta yi.Bayan kwalliya da take so a rayuwar ta sai waya ko da yaushe wayar ta ya na hannun ta. Wani lokacin mahaifin ta ya na tonon ta ya na kiran ta suna mai aljanar hoto ta na son ɗaukar hoto ta tura a Social Media a yi mata comment da liking a na zuzuta kyawun ta,ko ta ɗora a tiktok. Zainab mace ce mai son jiki da hutu duk da ba ta da ƙiba sai dai jiki na mata,amma a kwai son jiki ko waya a kace ta ɗauko sai tace wash!Ta miƙo ta na ya mutsa fuska ko alamar gajiya. A taƙaice ba ta cas ko as ɗakin ta kullum mai aiki za ta shi ga ta share,sannan mai wanki ta kwashi kayan ta hatta innerwears ɗinta,mai aiki take wanke wa ko al'ada ta yi sai dai mai aiki ta kwashe abin a bayi ta zubar sannna ta wanke.Ta na matuƙar alfahari da gatan da iyayen ta suka bata tare da yi musu addu'a.Mace sangartacciya mai son jiki da hutu da zallar wayewa mai ƴanci wacce rayuwarta a cikin fararen fata ta yi. Zainab ta na da kyua na nuna wa tare da mannata a hoton irin matan nanne waɗanda ka na ganin su kaga hutu,ko kai mace in ka hansu sai ka yaba.Doguwa fara ga gashi da kyan diri sannan ta na ƙara zuzuta kyanta da mayuka na gyara gashi da fata da kuma sabulai masu tsada.Ita dai ta yadda ta bautawa jikinta ko da za ta karar da wunin ranar ne,shi yasa in ka kalleta dole ka ƙara. Ta na da girman kai a gurin samari ga ta da farin jini,amma duk saurayin da yazo za tace bai yi mata ba.Mahaifinta ya na matuƙar son yaga ya yi mata aure don ta haifa mishi jikoki,shi yasa kullum yake lallashin ta akan ta fidda miji daga cikin yaran masu da shi da alhazawan da suke neman ta,amma taƙi ita ganin ta aure taƙurawa rayuwar tane.Tafi son rayuwar hutu da jin daɗi sannan ba ta son taƙura da shishshigi ga lamarin ta. Abin da ƙara tsoratar da ita ganin ƙawarta Nihal da ta yi aure shekara ɗaya da ya wuce.Ta na da kyau da gayu,amma tun da ta yi aure ta haihu ta zama ƙatuwa ga tumbi da ta yi,sannan ƙirjinta ya zube,kullum cikin aikin yara ko a gurin aiki ta rage ƙokari,ga takurawa ɗan tiktok ɗin da take yi mijinta ya hana. Wannan dalilin yasa ta ƙara tsanar aure ta na gani kamar koma baya ne a rayuwar ta,ganin mahaifinta na da kuɗi kuma ita ma ta tara kuɗin da za ta ɗauki nauyin kanta.Ta saka ma ranta ba za ta yi aure ba,in ma dole sai ta yi aure to ba za ta yadda ta haihu ba kawai za ta yi rayuwar hutu ne don gani take kamar tara yara wahala ce gata likita kuma bata son jikin ta ya canza. Duk mazan da suke zuwa gun ta kullum cikin kushe su take yi ta na yi musu wulakanci,kuma in auren za ta yi tana son namji mai kyau wanda ya fita gayu da tsafta.Ba ta taɓa jin soyayyar wani a cikin zuciyar ta ba,shi ya sa take wulaƙanta duk wanda ya zo gurin ta. Kwasam!Ta haɗu A.m a ranar wata daren alhamis da misalin ƙarfe shidda saura kwata agogon birnin a ƙasar London,ta raka yar gidan ƙanwar mahaifiyar ta siyo kaya.Suna zaune a cikin jirgin za su dawo A.m ya shigo hannunsa riƙe da waya da cingam a bakinsa ya na taunawa a yangace.A.m na son cin cingam kamar mace hakan ya samo asali ga matar Alhaji Sama'ila da ta rike shi ta na son cin cingam.Hausawa sun ce zama da maɗaukin ƙanwa shi ke kawo farin kai.Aiko haka ta kasance A.m ya koya cin cingam a gurin ta duk lokacin da ya ci abinci ko ransa yake a ɓace,sai ya huce a kan cingam ɗin. Ran shi a ɓace yake akan taron da suka yi da safe a companin su,sam yadda yaso taron ba haka ya kasance ba,wannna dalilin ya saka shi baro London bai kammalla abin da ya kawo shi ba. Ya shigo cikin jirgin fuskar sa kamar an yi mishi mutuwa,bai kalli kowa ba sai kujerar sa da ya nufa ya na murza tafin hannun sa tare da tauna cingam ɗin da ƙarfi saboda fushin sa ya ragu. Wani irin kallo ya watsa mata ganin ta zauna masa a kujerar sa,da fari ya ɗauka makauniya ce saboda kowa da numbar kujerar sa amma ganin ta na riƙe da waya sai ya daka mata tsawa da ƙarfi yace."Za ki iya tashi a ƙujerata ki nemi taƙi tunna baki je makaranta balle kin san yadda ake irga numbobi." A hatsale ta miƙe tare da faɗin."What."Ita sai yanzu ta kula ba'a gurin ta ta zauna ba,saboda hankalin ta na kan wayar ta sanda ta shigo.Ranta ya ɓace jin kalaman sa sai kawai ta ɗaga hannunta da nufin ta wanka ma mutumim da ya kira ta jahila mari,sai ya banbance waye ke da jahilcin atsakanin shi da tunna idanunsa sun kasa gane mishi wayayya mace mai a aji da class,wacce take tashe a tiktok. Zainab ta sauke hannunta a hankali jikinta ya yi sanyi matuƙa ganin matashin saurayin da ya kafa mata manyan idanunsa ya na kallonta,cikin zafin rai a yadda idanun sa suka nuna jira yake ta mare shi ƙila ball zai yi da ita yadda ya haɗe fuska. Ta shiga in ina ta na ƙoƙarin matsawa daga gurin ya tureta ya na faɗin."Matsalar ƴan matan bahaushe kenan daga sunga sun fita waje su dinga nuna isa.Da kin mare ni wallahi sai na yanke duk yatsun ki na kai ma karan gidan mu nan gaba sai na ga da wane hannun zaki yi mari."Ya ja tsaki tare da zama ya maƙala earpis a kunninsa tare da harɗe hannun sa duka a ƙirji,zuwa can ya cire earpis ɗin ya lumshe idanunsa. Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Mu haɗu a shafi na huɗu dan har yanzu shinfiɗa ne har ba'a fara ba.Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. *FOLLOW, READ, COMMENT, SHARE* *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *SHAFI NA HUƊU* Jiki a sanyaye ta koma kujera ta zauna ta na jin wani shauki ya na ratsa bargon jikinta,hannu ta sa ta share zufan goshin ta tare da jingina kan ta da bayan kujera ta na kallon sa cikin wani irin yanayi.Ganin halin da ta shiga Imsal ya matso dai-dai kunninta tace."Gaskiya gayen ya na da kyau sosai." Zainab ta ƙara lumshe idanunta ta na kallon shi ba tare da tace mata komai ba,amma ta na jin wani girmar lamari a tare da shi,zuciyar ta ta na bugawa da sauri-sauri haka bugun ƙirjinta. A lokacin da jirgin ya fara tafiya Zainab ji take kamar ta je gurin sa ta yi mishi magana,ji take komai na ta ya sukurkuce,amma ganin yadda ya ɗaure fuska idanunsa na rufe ya sa taji karayar zuciya. Wayarta ta ciro ba tare da ya sani ba ta dinga ɗaukar sa hoto,ta na turawa ma ƙawayen ta da ta yi saurayi.Ko da suka iso Nigeria bai kalli in da take ba,ya na janye da troley ɗin sa hankalin sa na kan A.k da yazo ɗaukar sa. Da sauri ta ƙarasa gurin sa tare da shan gabansa saura kaɗan ta faɗi,amma ba ta kula ba ta tsaya ta na mishi murmushi mai ɗaukar hankali. A.m ya juya bayan sa ya na kallo a tunanin sa wani take ma murmushi a bayan sa,don shi sam ba yarinyar ba ta yi mishi ba,saboda tsiwarta sannan shi a wannan lokacin babu so a tsarinsa,bai shirya aure ba duk da burin iyayen sa kenan. Kallo ya bita da shi tun daga saman ta har ƙasa ta na da kyau shi ma ya san haka,amma hakan bai wani dame shi ba kasancewar ya sha haɗuwa da mata kala-kala. Wani ƙarin murmushi ta ƙara saka mishi tare da bin sa da sauri ganin ya fara tafiya."Don Allah ka tsaya ina son magana da kai,in ba damuwa ina son mu ƙulla abota."Ta faɗa tare da miƙa masa hannunta . Wani ban zan kallo ya yi mata mai kama da ya ga kashi yaci gaba da tafiyar sa ba tare da yace mata uffan ba.Jikinta ya yi sanyi ta na tsaye ta na kallon shi har ya shige cikin motarsa,wanda A.k ya tuƙo don ya ɗauke sa.Da idanunta da suka canza kamar za ta zubda ƙwalla ta kalli bayan motar. TURAKI FAMILY Abin da taga an rubuta keman a bayan motar wani irin farin ciki ta ji ganin A.m ko ɗan waye,sai murna ya kama ta sosai tasha jin mahaifin ta na waya da wani daga cikin family ɗin.Ba ta son wulakanci sannan ta sha wulaƙanta maneman ta,amma wannan karan ta na ji ranta sa samu kalan mijin da take so. Ko da ta isa gida tunanin wannan kyakykyawan saurayin ya tsaya mata a zuci,da ta rufe idanunta kyakykyawar fuskarsa take hangowa.Tun kafin Abban ta ya dawo ta kira tare da bashi labarin saurayin da ta haɗu da shi,kuma ya tafi da imanin ta. Dariya ya yi sosai kin yadda ta ruɗe akan shi ta na mishi shagwaba da ƙyar ya samu ya lallasheta,ta kashe wayar ta bayan ya yi mata alƙawarin gane ko waye daga cikin family Turaki saboda ya san Alhaji Sama'ila abokin cinikayyar sa ne. Ko da ya dawo gida haka ta sa shi a gaba ta na ta yi mi shi magiya,har ya gaji da ƙorafin ta ya kira Alhaji Sama'ila. Bayan ya gaya mi shi dalilin kiran sa dariya sosai tare da farin ciki ya yi,a ransa ya na roƙon Allah ya sa A.m ya so Zainab ko ba komai ya yi dacen mace,sannan zumuncin kasueancin su zai ƙara ƙarfi. Duk yadda Abba ya yi da ita kan ta haƙura da numbar A.m da ta kafe sai an turo mata,amma taki daga ƙarshe kan dole ya ƙara kiran Alhaji Sama'ila ya turo mi mi shi da numbar. Da gudu ta ruga cikin ɗakin ta da wayar ta a hannunta bayan ta kwashe numbar a wayarta.Kan gadon ta ta faɗa ta na ajiyar zuciya mai ƙarfin gaske ,tare da ƙanƙame filo a ƙirjinta. Ran ta ya fara ɓaci ganin ta yi kira ya kai sau biyar ba'a ɗaga wayar ba,da ga ƙarshe sai ta ji an kashe wayar jifa ta yi da wayar ta ta zauna akan gadon ranta a jagule. Ko da Alhaji Sama'ila ya tare shi da zancen yarinyar da suka haɗu a jirgi,nuna ya yi bai gane ba in ma ya haɗu da ita ya manta.Ganin kauce-kaucen da yake mi shi sai ya yi masa umurni da yaje ya ganta ya na son ya nemi aurem ta. Babu yadda A.m zai yi ba tare da ya so ba ya amince duk da a wannan lokacin ya fara tunanin lokaci ya yi, da zai yi aure ya huta da damun da iyayen sa suke mi shi a kan ya yi aure sannan ya na buƙaƙar ya ga yaransa ga ƙaninsa ya na da biyu. Da wannan tunanin A.m ya amince ya je gidan su Zainab tamkar za ta yi hauka haka take ji a ranta,da ta gan shi ruɗewa don Allah ya saka mata son shi a birnin zuciyar ta. Tun ya na share ta har ya bada kai bori ya hau.Zainab ba ta a cikin matan da namiji zai wulaƙanta ita kanta ta na alfahari da hakan.Haka suke shan soyayyar su kullum suna maƙale da waya ana ga ya ma juna kalamai so. A hankali A.m ya fara jin tsanar wasu daga cikin halayan Zainab,musamman yanayin shigar ta da tsabon son jikinta,sannan shi namiji ne mai son mace wacce ta iya girki amma tunkafin su yi aure ta gaya mi shi ita ko ƙafar kicin ba ta shiga. Dariya ya yi kawai don ya yi tunanin tsokanar shi take yi ganin ta wayayya mai aji,ya san babu yadda za'a ta bari ƴar aiki na yi mi shi girki,ko a gidan su Amminsa take mi shi abinci. Haka dai aka dinga cin soyayya har Allah ya kai si ga aure.Bayan an gama shagali amarya ta tare a ɗakin mijinta.Shi kaɗai ya shigo bai nemi rakiyar kowa ba,ko A.k daga kofar gida ya tafi ya na ta mishi dariya. Da gudu ta taso ta rungumshi ya janye ta jikinsa,kasancewa wannan ne karon farko da mace ta rungume shi,idanunsa ya kafa mata duk rashin kunyar ta sai ta ji ta kasa haɗa ido da shi ta sunkuyar da kanta. Bayan sun yi sallah sun ci kayan daɗi da ya siyo musu,suka tsunduma kogin soyayya.Wani irin tarairayan juna suke yi ma junansu A.m bai san ya kamu da soyayar Zainab ba sai da ya aure ta yake jinta a zuciyar sa.Koda yaushe suna maƙale da juna in ba shi a gida suna kan waya.Ya na matuƙar ji da ita ba ya son ɓacin ranta. Abu ɗaya da ya fara kawo musu cikas yadda Zainab take son jiki komai suka yi amfani da shi,a nan za ta barshi sai in shi ya ɗauke da fari abin bai dame shi ba,amma daga bisani sai ya ji ya na taɓa zuciyar sa. Kusan shi yake ɗan wasu aikace-aikace na gidan.Sati biyu da auren su mahaifiyarta ta kawo mata masu aiki mata guda biyu.Da fari A.m yaƙi amincewa amma daga kan dole ya haƙura,saboda yadda shaƙar numfashin gidan yake son ya fi ƙarfin sa.Hankalinta kwance ta ci tasha ta tafi gurin aiki.Hakan bai wani dame shi ba saboda ya na matuƙar sonta. Kamar yadda Zainab ta tsara ba tare da ya tsani ba take shan maganin ha na ɗaukar ciki a ɓoye,ba ta damu da mai zai faru ba duk da ta san illar sa musamman da take likita,amma yadda A.m yake yaba halintar ta ya sa take shan maganin don ba ta son canjin jikinta.Kuma mafiyawancin family ɗin su suna da ƙiba. Tsaye yake a gaban madubi ransa a jagule ya na kallon kansa a madubi,zuciyar sa babu daɗi.Matuƙar yunwa yake damun shi amma ba ya son cin abincin masu aiki,saboda daɗin shi bai kai na amminsa ba ya na jin kunyar zuwa ƙarɓo musu abinci,wanda ita Ammin da kanta tace ya kama ta su fara girki saboda ta gama kawo musu na amarci,in bai manta ba rabonsa da abinci tun daren jiya da ya ci a gidan A.k. Ya ɗauki kum cikin ɓacin rai ya na tunanin bayan ya na matuƙar kiahin Zainab,sannan ita ba ta da kiahin kanta don ko masu aikinta mata yadda take fito musu kamar tsirara ya na bashi haushi amma ita ko a jikinta.Da namiji zai ɗauko kuku ya dinga mishi girki. A hankali ya ji an turo ƙofa an shigo wani ɗan murmushi dole ya yi mata ya na jiran ta ƙaraso,amma sai ya ji an yi shuru kamar ba'a shigo ba idanunsa ya ɗaga da nufin ya kalleta yau yangar ce ta motsa. Sai ya ga mai aikin su wacce bai ma san sunan ta ba tsaye ta na kallon ƙirjinsa ta na lashe baki,idanunsa ya kai kan jikinsa tare da jin kunya don daga shi sai ɗan tawul iya gwiwarsa."Ke!Uban me kike kallo ƙazama kawai?"Yace da ita ran shi a ɓace ganin yadda take kallonsa kamar wata mayya. Da sauri ta matsa cikin tsoro muryar ta na rawa tace."Madam ce ta bani umurnin na shigo na share ɗakin."Ta ba shi amsa tana jin wani lamari dangane da shi. "Tunna kin ga da mutum ba sai ki fita ba,banza mayya kawai."Yace da ita bayan ya ƙara daka mata wani tsawan,da sauri ta fice har ta na buge kanta da ƙofa. Ya zama dole na ɗauki mataki ba zan lamun ce da waɗannan ƙazaman arna suna shigo mim ɗaki ba,gajerun wandunan sa ya kwashe ya saka a sif ɗin sa ya na takaici don ya san masu aiki suka wanke. Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Mu haɗu a shafi na huɗu dan har yanzu shinfiɗa ne har ba'a fara ba.Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. *FOLLOW, READ, COMMENT, SHARE* *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *SHAFI NA BIYAR* Juwairiya zaune a gefen Mama ta na yi mata kitso,Ibrahim ya na zaune a gefenta ya na wasa.Baba ya buɗe labulen ɗaki ya fito dai-dai lokacin da Baba Sani ya kwaɗa sallama daga nesa da su.Ganin sa Juwairiya ta zabura kamar za ta gudu,tun lokacin abin ya faru ta ƙara matuƙar tsoron shi ganin shi take kamar kumurci. Baba Sani ya kalle ta da wani irin kallo wanda shi kaɗai ya san ma'anar sa,sannan ya miƙa ma Baba takadda yace."Gashi na gaji da biyan kuɗin wuta ni kaɗai,yau za su zo ka biya ko kuma a yanke na ka."Ya faɗa ya na kallon bangaren Juwairiya da ta rintse idanunta tun bayan da lamarin ya faru ta yi katanga da shi,ko ina ba ta zuwa islamiya ma ta haƙura gara ta din ga zama a gida da ta gan shi. Baba ya yi kasaƙe ya na kallon sa na tsawon lokaci sannan yace."Ka sa su yanke nawa in dai baza ka iya biya ba,bani da shi kuma na ga ko waya babu wanda yake da shi a cikin mu hasken kawai muke amfani da shi." " Oho ko ma me zaka ce kace na gaji da wahala."Ya sa kai ya fice ya na bambami. " Ikon Allah na rasa me ke damun shi ya canza gabaki ɗaya.Allah ya ganar da shi."Yace sannan ya ɗauki gatarin sa ya fita.Juwairiya ta yi shiru ta na tunani a ranta zuwa can ta miƙe tare da shiga bayi ta saka kuka. Mama ba tace komai ba illa baƙin cikin halin da yake nuna musu,wanda ta san tsananin ƙiyaryarta ya sa yake nuna musu hakan.Idanunta suka kawo ruwa amma sai ta yi ƙoƙarin sharewa,ba tare da Ibrahim ya gani ba. Juwairiya ba ta fito ba sai da ta sha kukanta ta ƙoshi sannan ta wanke fuskarta ta fito,a ranta ita kaɗai ta san halin da zuciyarta take ciki.Duk da Mama ta gane kuka ta yi ba tace mata komai ba,domin ita ma da za ta samu dama kuka za ta yi ko zuciyarta ta rage raɗaɗin damuwar da take ciki. Yanayin rayuwar da Juwairiya take ciki babu daɗi ji take kamar ta na rayuwa a gidan kurkuku!Kusan kullum sai ta yi kuka ta na matuƙar bakin cikin halin da iyayenta suke ciki,burinta bai wuce ace ta samu aiki ta na taimaka ma iyayenta ba. Tsakanin ta da Baba Sani tun faruwar lamarin take jin wani tsanar sa mai tsanani ya na ƙara shiga cikin ranta,ko muryar shi ta ji sai ta yi ta'awizi a cikin ranta tsananin mamakin mugun halin sa take. Duk yadda ta so ta taimaka wa iyayenta abin ya ci tura har takai su kwana basu ci ba,tashin hankalinta yadda Ibrahim yake yi,amma ƙiri-ƙiri Baba Sani ya hana matar sa basu abinci. Ganin halin da suke ciki wani lokacin ta yi kuka kamar numfashin ta zai rabu da gangar jikinta. Mahaifin Juwairiya na tsaye ya rataye gatarin sa a kafaɗa hankalinsa baya jikinsa,tunani yake sosai a cikin ransa ga wata irin yunwa dake ƙwaƙularsar.Tunani fal a cikin ransa ya na tunanin kuɗin aikin da za'a yi ma Ibrahim aiki a ƙafar sa. Ya daɗe a tsaye ya na tunanin mafita daga bisani yaci gaba da saran iccen da yake yi cikin rashin kuzari,tare da rashin madafa sai tsaƙa da warwara yake a cikin zuciyar sa. Ya ɗaga gatarin sa a sama ya na can ya na tunani bai ankara ba sai ji ya yi gatarin ya dawo tsakiyar kansa! "Innalillahi wa inna ilaihir ra ju'un."Iya abin da yace kenan ya zube a ƙasa a sume jini na ta zuba kamar famfo! Hankalin Malam Audi dake gefen icce ya na bayar da iccen ya fahimci abin da ke faruwa, da sauri ya iso garesa ya na salati cikin tsananin razana tamkar zai fasa ihu ganin halin da yake cikin. Mutanen dake gurin suka yo kansa suna salati ganin abin da ke faruwa,kama shi suka yi aka saka shi a cikin mota suka nufi a sibiti da shi. Lokacin da labari ya riske Juwairiya hannunta saka a ka sai kuma ta yi ƙoƙarin daƙile zuciyar ta da take ninyar kwarma ihu,ta fara salati ta na faɗin."Inna lillahi wa inna ailaihir raji'un."Sai hawaye bayan ta yi nasarar faɗin haka ta yi koyi da faɗe na ubangiji da ya umurci bayin sa da su faɗi haka duk lokacin da wata musiba ta same su. "Wayyo Allah rayuwa ta me ya sa daga wannan sai wannan?"Ta tambayi kanta cikin tsananin ruɗani.Gabaki ɗayan su sun ruɗe ganin halin da yake ciki kai ya kumbura kamannin sa ya canza,sannan an ɗaure kansa da bandeji duk ya ɓace da jini. A lokacin da suka je ko magana baya yi idanunsa a rufe ba ya iya ko buɗe idanunsa,daga ganinsa ya na cikin wani hali babu alamun numfashi tare da shi sai bugun numfashin sa da yake sauka a hankali a cikin tsananin wahala. Rintse idanunta ta yi a jikinta take jin kwatankwacin zafin ciwon dake jikin Baba,ta kasa kuka sai hawaye da yake gasar sauka a ƙuncinta ba tare da sanin ta ba. Suna zaune har tsawon wani lokaci amma bai farka da ga baccin da yake ba,saboda allurar baccin da aka yi masa.Har misalin tara na dare sai a lokacin Baba Sani ya shigo ya na ta zare ido,a cewar sa yanzu ya dawo gida ya ji labari. "Ni na rasa wannan lamari na ka Yaya kamar wani mai bakin uwa,kullum rayuwarka ƙara taɓarɓarewa take.Haba wannan wane irin musifa ne! Tun ba yau ba nake maka maganar kabar yin faskare amma kaƙi ga shi nan abin da ka jawa kanka." Ire-iren kalaman da yake faɗi kenan ba tare da nuna tausayi a fuskarsa ba,sai dai nuna rashin damuwa da faɗin maganganu mara tsari.Juwairiya da ta kifa kanta da akan gadon asibitin ta na wani irin kuka. Hankalin su ya yi matuƙar tashi ganin halin da yake ciki,Juwairiya kamar ta mutu haka take ji,ƙiri-ƙiri in aka buƙaci kuɗi Baba Sani yake ƙin bayar ba kullum da uzurin sa da yake faɗi. Da ga baya Baba Sani yake zuwa ya na kwana da Baba.Baba Sani tsaye akan Yayan na sa da misalin ƙarfe ɗaya na dare,kallon sa yake da mugun nufi a ransa.Filo ya janyo tare da danne masa kai. Allah Sarki bawon Allah da yake kwance a cikin mawuyacin hali ya fara mutsu- mutsu da ƙafafun sa,bai jima ba ya yi dip alamun babu numfashi a jikinsa. " Gara ka mutu kowa ya huta kullum cikin wahala nake da kai da iyalan ka,sannan ɗan buƙata ta da nake son na biya na rasa.Kaje kawai Allah ya haɗa mu a kiyama!Abin da yace kenan ya kwanta da ninyar da safe ya fasa ihun ya mutu. Washegari da safe Juwairiya tun da asuba take azalzala wa Mama da su je asibiti,irin mugayen mafarkin da take yi akan mahaifinta ya sa hankalinta ya tashi sosai.Mama ce ta ɗan ƙarfafata har suka dama koko suka sha,duk da dai Juwairiya ƙurɓar kokon take wanda ko siga babu hankalinta na gurin mahaifinta. Ko wanka ba ta yi ba ta ɗauki ruwan kokon ta na addu'ar Allah ya sa ya iya sha,Mama dai ba tace mata komai ba duk da ranta babu daɗi.Ko da suka isa asibitin gaban Juwairiya ya yanke ya faɗi ras!Sai ta kira sunan Allah ta riƙe kofin kokon ta na wani irin tafiya zuwa ɗakin da yake tamkar wacce ƙwai ya fashe mata a ciki. Gabaki ɗayan su suka yi mutuwar tsaye ganin Baba Sani tsaye, a ɗakin ya ɗora hannu a kansa ya na ƙwala ihu, da kuruwa tamkar yadda jahilan farko suke yi yayin da wata musiba ta afkawa ɗayan su. Sautin kukan sa yake tafiya tare da bugun zuciyarta,ta rintse idanunta ta na addu'ar kar Allah ya sa mafarkinta ya zama gaskiya!In kuma da gaske ne ya za suyi da rayuwar su a duniya bayan ba mahaifin su? Sai kawai ta fara ja da baya ta na girgiza kanta tare da nuna mahaifinta, ta na faɗin dai-dai lokacin da Mama ta saka kuka domin ta tabbata ya riga mu gidan gaskiya."A'a bai rasu ba wallahi mafarki ne!Don Allah kar kuce min mafarkina ya zama gaskiya.Mahaifina ya na raye bai mutu ba." Sai ta ruga za ta fita waje tashin hankalin ta ta ya ya mahaifinta zai mutu ya bar ta da azzalimi!Mutuwar sa na nufin ya yi nasara akan ta zai cika mummunan nufin sa kenan? Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Mu haɗu a shafi na shidda dan har yanzu shinfiɗa ne har ba'a fara ba.Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. *FOLLOW, READ, COMMENT, SHARE* *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *SHAFI NA SHIDDA* Duk yadda Juwairiya ta so ta kwantar da hankalinta akan mutuwar mahaifinta, abin ya ci tura!Da ta tuna mugun nufin Baba Sani sai ta ƙara rikicewa,irin yadda ta nuna na rashin tawakkali ya so ya fara tunzura Mama tun ta na ba ta haƙuri, ta taushe tashin hankalinta domin Juwairiya ta natsu amma ta kasa,sai uhu take ta na furta sunan Baba. Ganin irin abin da take yi sai Mama ranta ya ɓace matuƙa,ta saki hannun Juwairiya dake son a kyaleta ta fita da gudu kamar wata kamun aljanu tace."Ku kyaleta ta yi duk abin da ta ga dama,ban san baki da tawakkali ba sai yanzu Juwairiya!Na ɗauka saboda ƙarfin imanin ki ni zaki din ga ba ma haƙuri,tare da jawo min aya akan na ɗauki haƙuri domin duk mai rai mamaci ne." Juwairiya ta duƙa tare da ƙara sakin wani kuka dai-dai lokacin da Baba Sani ya ƙaraso gun ta ya na mata wani kallo,mai kama da tausayi ko akasin haka tare da sausauta murya yace."Ku kyaleta rashin mahaifi abu ne mai ciwo na tausaya miki matuƙa,domin hakan da kika yi sai kika tuna min lokacin da mahaifin mu ya mutu ina kuka mahaifinki Yaya Ahmed shi ya dinga lallashina!" Sai ya saka kuka ya na faɗin."Allah Sarki!Allah ya jiƙan ka Yaya."Ya nufo Juwairiya dake kuka tamkar ranta zai fita,da nufin zai riƙe ta ya lallasheta. Da sauri ta matsa ta na wani irin kuka kamar za ta shiɗe,ja da baya take kamar ta ga dodo.Ganin haka sai ya kyaleta a ran sa kuwa murmushin mugunta yake mata.Bayan an gama cuku-cuku aka ba su gawar Baba da har ta fara sandarewa. Hankalin Juwairiya bai ƙara tashi ba sai da suka dawo gida ta ga inda yake kwanciya,wani ƙarin abin tausayi tun da Ibrahim ya ji mutuwar mahaifinsa ya ɗauke numfashi ko motsi ba ya yi.Lamarin sai ya jagule ma Mama ta rasa in da za ta sa kanta ta ji sanyi,ga wani irin kuka da Juwairiya take yi taƙi ta yi shiru. Bayan an yi wa Baba sallah aka kai shi gidan gaskiya gidan da ko wane bawa yake da gadon sa domin ba'a wahala gurin mallakar sa.Cikin dare Juwairiya ta na kwance ta kasa bacci!A ranta ji take kamar mahaifinta kashe shi aka yi musamman yadda ta ga Baba Sani bai nuna tashin hankali game da mutuwar sa ba. Ta na lura da shi har shinkafa ya siyo a dafa ma ƴan zaman makoki,wanda ko mutuwa za su yi ba zai taimaka musu da shi ba. Kwana ishirin da rasuwar Baba amma har yau sun kasa manta shi a kullum ta ranar duniya sai sun yi kukan rashin sa,musamman Juwairiya da yake sokanar ta duk san da zai fita ya na cewa Allah ya nuna mi shi ranar auren ta,a she ba shi da rabon gani. A lokacin da Baba ya yi arba'in Juwairiya ta saka ma ran ta za ta yi fito na fito da Baba Sani duk abin da ya shirya a shirye take ita ma.Tun lokacin da Baba ya rasu bai ƙara shiga sabgar ta ba,duk da cewar ba ganin ta yake ba don ba ta fita ko ina. Ganin ba su da cin yau bare na gobe sannan Mama ita ma kwana biyu ba lafiya take da shi ba,ya sa za ta gaya ma Mariya ta nema mata aiki ta din ga yi don da yunwa ya kashe ta gara dukan Baba Sani ya kasheta ita kaɗai.Ta san ya na hana su abinci ne don kawai ya cutar da rayuwar su ko ya samu biyan buƙatar sa,amma ba wai don ba shi da kuɗi ba tunna aikin gwannati yake yi. Ranar da Baba ya yi arba'in sun sha kuka bayan sun yi mishi saukar alkur'ani suka haƙura da kukan suna mishi addu'ar Allah ya jiƙan shi. Cikin sa'a bayan kwana biyu da gaya ma Mariya ta nema mata aikatau,ta zo da murnar ta an samu saboda ta na samun aikatau da dama kusan ita dillaliyar masu aiki ne. Tafiyar da Baba Sani ya yi sai hakan ya ba Juwairiya damar ta fara aikin ta cikin kwanciyar hankali ba tare da kowa ya sani ba.Duk da ita Mama taso ta bari ya dawo su tambaye shi amatsayin sa na mahaifi,amma taƙi ta kafe daga karke wasu irin maganganu ta jefa ma Mama wanda yasa ta ji babu daɗi,a yadda take gaya mishi magana duk da ta san dama ba sa shiri,amma ko ba komai yanzu shi yake da matsayin mahaifinta kuma ko aure za ta yi shi yake da alhakin komai. Faɗa sosai ta yi mata don ganin ta a maganganunta har da rashin kunya,wanda hakan bai dace ba musamman shi da yake da matsayi mai girma a ranta.Juwairiya ta ji maganganunta amma yadda ta faɗe su haka ta watsar da su a gurin a ranta take faɗin."Ta ya ya za'ai na mutunta mutumim da yake da burin ɓata min rayuwa,ko da mahaifina ne ya bijiro da wannan iyakan abin da zai yi mishi kenan Mama,domin babu biyayya ga abokin sabon halitta!Kema da zaki ji abin da yake so a gareni sai kin yi mishi fiye da nawa." Matar da Juwairya za ta yi ma aiki likita ce a shika ta na da yara uku,a kwai wata mace tsohuwa wacce take mata girki ita kuma Juwairiya aikin ta kula da yaranta mata biyu da namiji ɗaya,in da za ta din ga mata aiki ta na tafiya har islamiya ta saka su tare da yaranta.Ranar da kuma take da aikin kwana za ta kwana da yaranta da safe ta shirya su ta tafi makaranta,wanda ta ba ta zaɓi in ta gama shirya su za ta tafi gida duk da ita matar makaranta ta ba Juwairiya zaɓi ta koma ta zana jarrabawar fita sakandiri. Juwairiya ta ji matuƙar daɗi na samun aikin duk da ta na jin tsoron abin da Baba Sani zai yi mata in ya fahimci ta na aikin.Taƙi amince mata kan shawarar da ta ba ta da ta koma makaranta,duk da ita ma ta na da buƙatar haka amma ta san Baba Sani ba zai bar ta ba. Sai dai cewar da matar ta yi za ta dinga kwana da yaranta in ta na aiki ya so ya ɗan tsorata ta,amma da ta gaya mata a kwai Baba tsohuwa sai hankalinta ya kwanta don ta yi tunanin tare za su din ga kwana. Juwairiya ta ƙara son ta yi aikin jin an ambaci kuɗi mai tsoka,sannan da suka tashi za su tafi sai ta ba ta kayan abinci da kuɗi naira dubu ta sallami Mariya da tsoka,saboda ta yaba da hankalinta musammam da ta ganta ba ta da ƙazanta. Mama da ta ji aikin har da kwana sai ta fara yiwa Juwairiya faɗa kuma tace sam ba za ta yi aikin ba,ta na ta faɗa in da take shiga ba nan take fita ba.Ganin hakan sai ta saka kuka ta miƙe domin ta yi sallar magariba."Ba gara na zauna a gidan Anty Naja ba tunna na ji Mariya tace mijinta ustazi ne me gamu,akan ƙanin mahaifina dake son ya ɓata min rayuwa. Juwairiya ta yi tunanin za ta shawo hankalin Mama,amma sai ta ga ta kafe a dokin naƙi in da ta ƙara mata da cewar sam ata fau ba za ta yi aikin ba. A ranar da suka shirya da Anty Naja za ta fara aikin,Mama ta kafe ko da Mariya tazo suka lallashi Mama shi ma bai yi wani tasiri ba ganin haka sai ta haƙura,akan ta nema mata wani kawai wanda ba za'a din ga kwana ba. Da maraice ta na zaune akan kujera ta na wanke-wanke sai suka ji sallamar Mariya da wata a bayan ta,da sauri ta ɗaga kanta duk da cewar ba ta yi ma Anty Naja kallon kirki a ranar ba,amma ta sheda ta. A kunyace ta amsa mata sallama tare da yi mata jagora zuwa ɗaki,ta ibo mata ruwa a kofi ta ije mata sannan ta fice daga ɗakin ta na jan numfashi ta riƙe turaren Anty Naja da ya baɗe ɗakin na su,wanda Juwairiya ta so ya dauwama a ɗakin saboda daddaɗar ƙamshin sa. "Ba ki sanni ba ko Mama?"Anty Naja tace bayan ta ɗauki ruwan da Juwairiya ta kawo mata cikin sakin fuska,kuma ta sha ruwan sosai ba tare da nuna ƙyanƙyani ko tafi ƙarfin shan ruwan randa,wanda hakan sai ya yi matuƙar burge Mama wani ƙarin burgewa ta baje akan tabarma har ta na cire hijabin ta da ɗankwalinta. Hakan ya yi matuƙar ƙara burge Mama sai ta ƙara jin ta saki jiki da ita tace."Bam ma sanki ba yarinya,amma da na ganki da Mariya ƴar maƙocin mu na gane kece wacce aka yi maganar aiki da Juwairiya..." "Ni ce Mama tabbas ni ce ina ta jiran ta ba ta zo ba,sai da ga ba ya Mariya ta zo tace min kin hana ta "Tace tare da ƙatse Mama ba tare da ta kai aya ba. "Haka ne gaskiya aikin nan ki nemi wata kawai."Mama tace ta ɗan canza fuska kaɗan,ganin haka sai jikin Anty Naja ya yi sanyi amma saboda ya ba hankalin da ta yi na Juwairiya ta kasa haƙuri tace."Don Allah Mama karki hana ta wallahi ba ni da matsala da ga ni har mijina,kuma in kina tunanin kwanan da za ta yi ne mijina ba zama yake ba wani lokacin ni kai na sai na yi bacci yake dawowa." Ta matsa kusa da Mama tare da riƙe hannunta ta yi rau-rau tace."Don Allah Mama kar kice a'a ban ɗauki Juwairiya a matsayin me aiki ba ƙanwa ce a gareni,kuma duk ranar da kika ga wani abu ya faru mara daɗi a tsakanin mu ki hana ta zuwa." Ta yi shiru ko Mama za ta ce wani abu amma sai ta ga ta kauda kanta ta na tunanin wanda ba za ta iya cewa ta yanke ta barta ko a'a."Kin ji Mama ki amince don Allah!Na yi masu aiki da dama amma basa iya riƙe min amana,bayan haka sace-sace suke min." Duk maganganun da take yi ba ta ce mata komai ba,aranta ta na tunanin karta amince a za a sami matsala da Baba Sani duk da shi ma ya na da laifi,in da ace ya na taimaka musu da ba za ta yi aiki ba. 'Ki na ji Mama da ban so na gaya miki wani sirrina ba,amma nuna amincewar ki ya zama dole na sanar miki domin ki taimakeni ki ceci aurena.Mai aikina mijina ya kama ta da yarana tana basu kirjinta suna tsotsa ita kuma ta na saka musu hannu a gabansu.Hankalinsa ya tashi ƙwarai ba yan ya miƙa ta ga hukuma ya kawo su asibitin da nake aiki,hankalina ya tashi ƙwarai na yi kuka kuma mun yi rikici da shi daga ba ya yace dole na bar aiki ko mu rabu.Ina son aikina saboda da shi nake taimaka iyayena,sannan ina son aurena na yi-na yi a dai na saka ni aikin kwana amma ba zai yiwu ba. Mijina ya bani zaɓin na bar aiki na kula mishi da yaransa ko ya rabu da ni,domin yaƙi barin na ƙara ɗaukar me aiki.Mun yi rikici da shi sosai daga baya ya haƙura na samu mai aiki amma daga wannan ya kama ta da wani matsala zai rabu da ni."Tace cikin hawaye ta ja numfashi sannan ta ɗora da cewa. "Mariya ita ta ja ra'ayina akan Juwairiya saboda ta gaya min ta na da hankali,da ƙyar na amince da na ganta na yadda da maganar Mariya ki taimake ni Mama in har kika amince zan zama tamkar ƴarki,zan taimaka ma rayuwar ku." Jikin Mama ya yi sanyi sosai har ba ta san sanda ta amince ba jin aure na shirin mutuwa,duk da watarana ita ma aure za ta yi."Na amince Allah ya kyuata amma ƴar nan ya kamata ku din ga kiyaye wa,ni ma matsalar ba daga gareni ba ne a kwai ƙanin mahaifinta ba lai-lai ba ne ya amince amma ta fara mu gani." Sosai ta ji daɗi ta buɗe jakarta ta ciro dubu ishirin da biyar tace."Ga kuɗin ta na wata biyu dubu ishirin sai ki fara koda sana'a ne,sannan dubu biyar na baki kyauta kuma gobe in Allah ya sa tazo za ta taho da tsaƙo." Mama ta ji daɗin kuɗin da ta bata ta na ta murna da saka mata albarka har ta yi mata sallama,ta kama hannun Juwairiya tace."Sis sai kin zo gobe ko?Don Allah ki zo da wuri ƙanninki suna ta maganarki."Tace tare da shafa kanta. "Gaskiya ta na da kirki sosai."Mama tace ta na juya kuɗin da ta bata,sai kuma ta aje kuɗin ta kalleta tace "Kin san me ba zan taɓa kuɗin nan ba sai mun ji me Baban ku Sani zai ce."Da sauri ta miƙe kawai ta na faɗin."Ki ba ni naje na yo miki sare-sare ki fara sana'a ni fa ko me zai yi sana yi aikin nan,tunna shi ba taimakon mu yake yi ba don haka ba shi hurumin da zai hana mu." Ta yi maza ta fice daga ɗakin kafin Mama tace komai sam ba ta jin tsoron abin da zai ce in dai ba kasheta zai yi ba ta rantse sai ta yi aikin. Kamar yadda ta gaya mata mijinta ba mazauni bane haka kuwa ta gani,don tun da ta fara aiki ba ta gan shi ba sai tanƙamemen hoton su da yake manne a falon wanda tun da taje ranar da Mariya ta kaita ta gan shi a hoto,wannan dalilin ya sa hankalin ta ya kwanta ko da ta ga Baba me aiki aikin ta take yi ta tafi ba ta kwana. Ta na aikin ta cikin kwanciyar hankali ga abinci da take ci kullum taci mai kyau ta sha mai kyau,don Anty Naja ba ta da rowa ko nama taci sai ta rage mata saboda yadda Juwairiya take kula da yaranta ga ta da tsafta ko ina na gidanta tsaf ya na tashin ƙamshi. Kusan sati biyu ta na aiki cikin jin daɗi kuma har zuwa wannan lokacin Baba Sani be dawo ba,kullum in dai za ta dawo Anty Naja na sawa a yi girki da su ta saka mata a kula kuma da yawa,don haka ba sa matsalar abinci ga ɗanye da take badawa a kai ma Mama in dai za ta yi aikin kwana. Ranar Juma'a da safe bayan ta gama aikin ta ta shirya musu abincin karyawa ta ibi nasu kamar yadda ta yi mata umurni,kasancewar ta gama aikin kwana za ta yi hutu har ta bawa Juwairiya hutun kwana biyu. A hanya Juwariya ta na tafe ta na ta yi mata addu'a don tsakanin su Allah ne kawai zai biya ta,saboda irin kyautata mata da take yi fara aikin ta ta bata kaya masu kyau sosai da abin alheri ko hijabi kala biyar ta bata,sannan ko baƙi ta yi bata ce mata me aiki sai dai tace ƴar'uwanta ta na da matuƙar kirki sam bata nuna wani abu ko rashin mutunci. A dai-dai ƙofar gidan su ta tsaya cikin firgici ganin Baba Sani ya ɗare kan motar sa ya na riƙe da ƙatuwar bulala,sai juya ta yake ya na zare ido ransa a ɓace da ga ganin yadda ya ɗaure fuska alamun ba mutunci. Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Mu haɗu a shafi na bakwai.Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. *FOLLOW, READ, COMMENT, SHARE* *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *SHAFI NA BAKWAI* Tsananin mamaki ya kama shi ganin yadda Juwairiya ta gan shi amma sai ta yi tsaye ta na kallon shi, ba tare da nuna wani tashin hankali a fuskar ta ba ko tsoro. Ya ɗan ƙare mata kallo cikin mugun nufin sa amma sai ya ga duk da ramar da ta yi,ta ƙara mishi kyau ɗan tafiyar da ya yi. Juwairiya da tsaya ko zai ce wani abu amma ganin ya yi shiru,ya sa ta nufi hanyar shiga ƙofar gida za ta shige.Da dauri ya sha gaban ta a ransa ya na mamakin dai na tsoron shi da ta yi,tun ranar da ya nemi haɗa jiki da ita. "Da ga gidan uban wa kike?" Ya tambayeta da fuskar shanu y na zare mata idanunsa da suka kaɗa suka yi ja,saboda tsabar fitina da ya saka ma kansa.Ta ɗan ja ta tsaya tare da matsawa nesa da shi ganin yadda ya matso daf da ita. "Ba na hanaki yawon maula ba,shi ne don kin ga ba na nan kika mai da shi sana'ar ki?"Ya tambayeta tamkar zai kai mata bugu. "Ni ba maula naje yi ba,aikatau na samu nake yi domin na ciyar da kammu."Ta faɗa mishi ba tare da jin tsoro ko shakku a ranta ba. Wani irin azababben mari ya wanka mata wanda ya sa ta yi taga-taga za ta faɗi,amma ta dake duk da azabar da ta ji kamar za tai fitsari a tsaye sai ba ta nuna mishi ba,don a shirye take ta shirya tsaf!Ko kasheta zai yi. Matuƙar mamaki ya kama shi wai yaushe ya yi sake har ta raina shi haka,amma sai ya ƙara ɗaure fuska yace."Na ga kwana biyu kin raina ni Juwairiya saboda na nuna miki manufa ta a kanki,to wallahi har yanzu ina kan baka na saina cika muradina gara ma ki amince ki sami maslaha a rayuwarki." A wannan lokacin ta ji wasu tagwayen hawaye sun cika mata fuska,zuciyarta ta amince da lai-lai shi ba mutum bane don ta yi tunanin rasuwar mahaifinta zai saka ya haƙura da ƙudirin sa. "Ka sani ko mutuwa zan yi ba zan lamunce ka biya buƙatar ka a kaina ba!Ina matuƙar kaico a rayuwata da ka fito a matsayin ƙanin mahaifina.Ko mutuwa zan yi sai dai na mutu."Tace mishi ta na ƙoƙarin shigewa gida. Sororo ya yi lai-lai ya yi sake tunna har taga wallar shi ta na faɗa mishi mugayen kalamai,masu tsauri a cikin idanunsa ba tare da shakku ko shakkar sa ba. "Tun da kika ce haka mu zuba ni dake,bari na tuna miki akan ki zan iya komai tun da kika girma na ɗora kwaɗayina akanki Ki kuka da kanki zan iya komai don na cimma manufata." Ta buɗe baki za ta yi magana wani irin takaici ya toƙare mata maƙogaro,sai hawaye da suka fara turereniya a fuskarta da ta tuna ƙanin mahaifinta yake mata wannnan halin,sai ta ruga a guje ta shige cikin gida ta na kuka. Mama dake ƙoƙarin hura wuta a murhun gawayi idanunta duk sun yi ja, suna zubar hawaye saboda wutar taƙi kamawa sai saka leda take yi.Sai ganin ta ta yi ta shigo da kuka ta shige cikin ɗaki ta buɗe baki da nufin ta yi magana,duk da cewa ta san dalilin kukan saboda ta ji dirin motar sa sanda ya dawo sai kuma ga shi ya shigo. "Saboda ba na nan shi yasa kika saka ta ta na yawon maula ta samo muku abinci ko?Na rasa wani hali kike so ki koya mata shi yasa na tsaneki saboda mugun halinki." Ta yi shiru ba tace komai ba dama ɗabi'ar ta kenan duk sanda zai yi mata rashin mutunci ba za ta tanka ba,haka ma yanzu mutuwar Yayan sa bai saka ta canza ba. Har ya gama bambamin sa ya fice bata ce ƙala ba,amma ta na jin gara su haƙura kawai da tashin hankalin da zai jawo musu.Bayan ta gama kukan ta ta share kamar kullum don Mama ba za ta taɓa lallashinta ba. "Juwairiya ina ganin a haƙura da aikin nan kawai."Tace cikin ƙunar zuciya ta na kallon ta."Gaskiya Mama sai dai kiyi haƙuri,amma ba zan haƙura tunna shi ba taimaka ma na yake ba." "Amma kina ganin tijarar da yake mana ko?Kin san halin shi ba shi da kirki,ni fa bana son tashin hankali ya dinga jibgar ki a banza." Juwairiya shiru kawai ta yi a ranta ta saka komai zai faru sai dai ya faru,amma aikin Anty Naja yanzu ta fara.Hankalin Mama ya tashi da safen ranar da ta gama hutun ta bayan Juwairiya ta yi sallah ta tafi aikin ta,ba ta kula da kiran da Mama take ƙwala mata ba. Da yamma da ta dawo Baba Sani ya shigo da bulalarsa ya yi mata duka,har bata iya tashi amma ba hana washegari ta koma aikin ta ba.Ganin irin dukan da yake mata Mama ta hana ta aikin,sai dai wannan karan ta bijire ma umurnin ta don ta rantse ko kashe ta zai yi ba za ta bar aikin ba. Tsakanin ta da mijin Anty Naja ba ruwanta da shi tun da ta fara aikin so uku ta gan shi,duk sanda ya shigo ya ga yaran a kusa da ita sai ya fara musu faɗa ya kora su cikin ɗaki ya na harararta ya na mazurai,a yadda yake mata ta lura ya matuƙar tsorata da halin masu aiki. Ganin haka ta ƙara kame kanta ta na mamakin yaran duk da suna zuwa islamiya amma ba su wani iya karatu ba,don ko babban dake da shekaru tara ko alhamdu bai iya cikakka bare ya damu da sallah ba,sai kallon catoon da suke yi kullum ba ƙauƙautawa,ganin haka ta dage da koya musu da saka su su yi salla,abin da ya ƙara saka Anty Naja son ta a cikin zuciyar ta. Ganin ƴan canjin da yaransa suke samu abin ya burge shi har yake amsa gaisuwar ta a sake,wani lokacin har kyauta yake mata na kuɗi yace ta kaiwa mahaifiyarta don Anty Naja ta gaya mishi mahaifinta ya mutu. Kusan kullum Juwairiya ta dawo sai taci na jaki a gurin Baba Sani jikin ta duk shatin duka ne,amma hakan bai saka ta karaya ba ta ci gaba da aiki don yanzu suna ci ga Mama dake sana'ar ta rayuwar su ta na tafiya cikin rufin asirin Allah sai dai takurawar da Baba Sani yake mata,wanda hakan ya na damin Mama ga shi taƙi ta dai na aikin. A haka rayuwa take gara musu yau fari gobe tsumma,yayin da kullum burin Baba Sani ya cika burinsa amma Allah bai ba shi damar ida mugun nufin sa a kanta ba.Ganin haka sai ya ɓullo mata da nuna mata kuɗi ya na jan ra'ayin ta akan ta amince mishi ko sau ɗaya ne,amma taƙi duk ta gan shi sai ta nemi tsari da sharrin sa don ganin sa take kamar wani sheɗani. Ta ɗauki tsawon shekaru biyu ta na aiki a gidan Anty Naja,a lokacin ta girma ta ƙara wayewa ga hankali da natsuwa kullum cikin hijabi take bata cirewa sai in mutanen gidan ba sa nan,ko ita Anty Naja ba za ta ce ga yanayin jikin ta ba,don tun kafin takai haka da Baba Sani ya saka mata ido ta yi tunanin ko jikinta yake ruɗarsa,bare yaanzu da ta zama ƴan mata ta cika ta batse ga Anty Naja da take ba ta kaya masu kyau kuma ta ba cin me kyau,har mai na shafawa da na wanke kai take siyar mata. Maza da dama sun sha bayyana soyaryarsu gurin ta wasu kuma suje gurin Baba Sani,amma sai ya taƙarƙare yace Juwairiya ƴar mace ce sannan ba ta da kamun kai har kwana take a waje.Ya faɗi mugun abu da ba ta mata suna ya gaya musu,wasu suna jin haka za su tafi wasu in suka nace ya yi musu korar kare don ya rantse,in har ba ta amince mishi ba to ita da aure sai dai ta ga ana yi ko kuma in ya mutu. Juwariya yarinya mai kimanin shekaru sha tara.Ta na da haske amma ba can ba,fuskarta mai kyau irin zagayayen fuska gareta,da dogon hancin ta haƙoran ta masu kyau ga ƴar wushiryar ta a tsakiya,wanda in ta yi dariya yake ƙara ma kyau matuƙa!Da dimful ɗinta.Bata da jiki amma a kwai shafe sannan doguwa ce ba can ba,amma ta na da tsawo wanda yake ƙara mata kyau. Ƙirar jikinta me kyau ne ko ita ta na alfahari da hakan wato irin jikin nan ne mai ɗaukar hankali waɗanda ko wane namiji yake burin samu mace mai irin sa.Wannan dalilin ya sa kullum take cikin hijabi do ko ƙawayenta suka shigo suka gan ta ba hijabi,sai su yi ta zuzuta ta su na yaba kyawun jikinta. A wata ranar litinin da safe bayan mutanen gidan sun gama karyawa suka wuce gun aiki,kasancewar da garin a kwai zafi sannan Anty Naja ta tura mata da tsako a cikin wayarta me botira da ta siyar mata,don ta din ga kiran ta ko kuma in ta tafi aiki da wuri ta gaya mata abin da za ayi,don yanzu girkin su ya dawo hannunta saboda Baban Abnaj yafi son girkinta. Waina da miyan karas za'a yi da farfesun rago,ganin ta na da aiki ya sa ta zage damtse ta na yi tun ta na cikin hijabi har ta cire ta na ta aikin ta,ta kunna wayarta ta na sauraron karatun kur'ani cikin suratul ma'ida.Ta shafa'a ta na ta aikin ta sai ƙanwar Abnaj mai suna Ibtihal ta danna remote ta ɓata saitin tibin,Abnaj ɗan shagwaba ya saka kuka ya zo ya na sanar da Juwairiya akan ta zo ta gyara musu. Hannunsa ta kama suka nufi falon da nufin ta gyara mishi,ta na tsaye a gaban tibi ta na ta ƙoƙarin yadda za ta gyara amma ta kasa gashi ita ba ta san yadda ake yi ba,sannan gashi har sun fara kuka akan a gyara musu. A hankali ya buɗe ƙofar ya shigo da sallama a bakinsa,Juwairiya da hankalin ta ke kan tibi ba ta san ya shigo ba,ko in ce dukan su sai bayan ya ɗauki tsawon lokaci ya na kallonta cikin mamaki a ransa ya na mamakin dama a kwai wannan halittar a gidan sa?Don shi zai rantse bai taɓa mata kallo ko na sakan bane ya san dai ta na da kyau a fuska. "Oyoyo Daddy!"Abin da yaran suka ce kenan wanda ya ɗauki hankalinta ta miƙe a razane ta yi diri-diri,tamkar za ta shige cikin ƙasa yayin da wani irin kunya ya lulluɓeta. Ganin yadda ta diririce sai ya shige ɗakin sa akan ya ɗauko abin da ya saka shi ya dawo saboda mantuwa da ya yi,wato wasu fayal da ya ije da nufin ya tafi dasu sai gashi ya manta da su kuma ana buƙatar su.Ashe da rabon ya yi gam da katar!Don shi ya ga matar aure dama tuni ya yaba da hankalinta. Ko da ya shiga cikin ɗakin wani irin kasala ya ji y rufe shi ya faɗa kan gadon shi ya na jin wani irin shauki na ta ya na zagaye ilahirin jikin shi.Ko da ya shiga ɗakin faɗa kan gadon sa ya daɗe ya na jin wani girmar lamari har na tsawon lokaci,sannan daga bisani ya miƙe ya ɗauki fayal ɗin ya fito. Kawai sai ya tsinci kansa da bin hanyar kicin ɗin ya ɗan tsaya nesa da kicin ɗin zuciyar sa na bugu da ƙarfi,take yake jin lamura suna sauya mishi har ya fara dana sanin dawowar sa gida gashi komai na son ya canza musamman akan yarinyar da take ba shi girma "Abnaj fito na gyara muku tibin ku barta ta yi aikin ta,kun dame ta da surutu."Yace da yaransa da suke kicin ɗin suna ta zuba da Anty Juwairiya kaza,ita kuma ta na ta yi musu dariya ba yan ta basu kwan da ta soya musu. Yaran suka bi shi suna murnar zai gyara musu tibi,bayan tafiyar sa ziciyar Juwairiya ya buga dam!Da ta kalli ƙwayar idanunsa cikin rashin sani ganin yadda ya kafa mata idanu lokaci guda,abin da ta hango ya matuƙar tsorata ta wanda bai yi kama da so ba sai tsantsar sha'a warta da ta hango.In ko haka ne abincin ta ya ƙare a gidan. Bayan fitar sa ta ɗaga labule ta na kallon farfajiyar harabar gidan,sai kawai ta ji hawaye ya na sauka a kan ƙuncinta bai yi kama da mutumim banza ba saboda ya na da dattako.To me ƙwayar idanunsa suke nuna mata?Ita kuma irin na ta jarrabawar kenan? Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Mu haɗu a shafi na takwai.Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. *FOLLOW, READ, COMMENT, SHARE* *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *SHAFI NA TAKWAS* Tun daga wannan ranar Juwairiya ta ga canji a tattare da shi,ya sakin mata sosai kuma ya na matuƙar kyautata mata,ko hira yake da matar shi sai kiji ya tsoma ta ciki yace"Wai haka aka yi Juwairiya ita za ta faɗi gaskiya." Ranar da ya fara mata hakan ta yi matuƙar razana ta kalli Anty Naja ta ga ko me za tace amma sai taga sai dariya take ta na jin daɗi har ta na ƙara tambayar Juwairiya,wani tsabar takaici kaɗa kanta kawai ta yi ta shige kicin ɗin wanda dama shi ya ƙwala mata kira don kawai ya tambaye ta. Bayan sati ɗaya sai gashi ya dawo gidan da wuri da yake a ranar matar sa na gurin akin ta na night duty acan za ta kwana.Bayan ya yi sallar magariba ya kulle ko ina na gidan ya shigo,tun da taga ya dawo da motar sa ya wuce masallacin kofar gidan sa gabanta ya faɗi hankalinta ya tashi,domin ita canjin da ta gani a gurin sa ya na tsorata. Bai fito ba ya na karatun kur'ani har kiran sallar isha ya tafi masallaci,sannan bayan ya yi sallah ya dawo ya zauna a falo shi da yaransa suna kallo shi kuma ya na aiki a laptop ɗin sa. "Abnaj je ka kira min Antyn ka Juwairiya kace ta zo ta bani abinci."Yace mishi ba tare da ya kalle shi ba,burin sa ya ganta ya san ta ɓoye kanta a ɗaki don kar ya ganta. Yaron ya ruga da gudu zuwa can ya dawo yace."Ga ta nan zuwa."Ya ci gaba da kallon sa bata jima ba ta fito da dogon hijabin ta har ƙasa.Ita sai yanzu dake matuƙar dana sanin gadin mijin wata da yaran ta da take,don a a kwai haramcin haka a cikin addini mace baliga da namiji ba muharramai ba dama na ukun su sheɗan ne. Nesa da shi ta tsaya kamar za ta yi mishi magana sai kuma ta juya ta shige kicin ta ɗauko abincin shi ta ije mishi za ta juya."Ba kiji ba Juwairiya."Yace da ita ganin za ta shige ɗakin da take kwana har ta na haɗawa da gudu-dugu. Tsayawa ta yi bata re da ta juyo ba ta na watsa da yatsun hannunta gani take kamar zai haiƙe mata kamar yadda ƙanin mahaifinta ya yi mata,amma sai ta ga ya ƙaraso ya tsaya ɗan nesa da ita ya miƙa mata sabuwar waya mai kyau a kwali ya ɗan daure fuska."Ga shi na ji Antynki tace Abnaj ya saka miki waya a ruwa ta lalace shine na hutar da kuɗin ta,amma fa ki kiyaye ki dai na basu don nan gaba in kika bari suka lalata sai na haɗa da bulala kafin na canza miki wata."Yace ya na kashe mata ido. Zare ido ta yi ganin wayar da ya siya mata irin wanda take gani a hannun su masu kyau da tsada,ina ita ina wannan wayar ta na ƴar gidan Malam Shehu kuma me za ta ce ma Anty Naja." Kamar ya san me take tunani sai ya kaɗa kansa yace."Karki damu na san me kike tunani zan yi mata bayani.Kuma ba ni da nufin na cutar dake alkhairi ne zuciyata,don Allah ki karɓa kin san babu kyau mai da hannun kyauta baya."Yace da ita ya na wani marairaice fuska sai kace maraya. "Gaskiya ka bar shi bana so ina gani a matsayina na ƴar aiki bai kama ta na riƙe irin wayar nan ba,don daga ganin ta na san za ta yi tsada kuma in Anty Naja ta gani me zan ce mata?"Sai ta tsinci kanta da furta hakan yayin da takai aya ta tsare shi da ido ta na tambayarsa. Shi ma ya ɗan razana jin tambayar da ta yi mishi kansa ya ɗan sosa ya kafe ta da idanunsa yace."Haba Juwairiya kina abu kamar ba mace ba,kice mata saurayin ki ya baki mana." "Ka yi haƙuri don Allah ba na son kyakykyawar alaƙar mu da matarka ya ɓace,kai sheda ne mace ce na ƙwarai kuma ta yi min halacci."Tace dashi da murya raunanniya yayin da hawaye suka fara turereniya a fuskarta. Ganin haka sai jikinsa ya yi sanyi ya ɗan yi shiru ya na nazarin maganar ta zuwa can ya ja numfashi yace."Laifi ne don nace ina sonki ni fa bani da nufin na cutar dake,kawai ina son ki zamo uwar ƴaƴana ne."Tsananin tsoron da ta nuna ta na me gwalo ido sai abin ya ba shi dariya. Tafe take cikin sauri bayan ta tashi daga aikin zuciyarta tunanin sabon halin da mijin madan ɗin ta ya fito dashi,yake damun ta har ta fara tunanin ko ta aje aikin ƙila in Anty Naja ta gane ba lalle-lalle ne ta fahimce ta ba.Kallon tsadaddiyar wayar dake riƙe a hannunta da ya bata take kallo wanda ya rantse ya maya in har ba ta ɗauka ba to zai ba wa Antynna ta da take tsoron sani ta bata da kanta. Abin mamaki dai-dai za ta shiga gida ta ji an dameta da hon,kamar ba za ta juya ba sai kuma ta juya in da ta ga mijin Anty Naja a cikin mota ya na ɗaga mata hannu,wato biyo ta ya yi ba tare da sanin ta ba ya ga gidan su.Tsabar takaici ba ta kula shi ba ta shige cikin gida. Koda ta gaya ma Mama abin da ke faruwa hankalin Mama ya tashi ƙwarai ta yi shuru kawai ta na jinjina abin a ranta,ta ɗauki tsawon lokaci ba tare da tace komai ba zuwa can ta nisa tace."Ina ga ko haƙura da aikin nan tunna mun sami jari Juwairiya,ni nafi son kiyi aure shine mutuncin ki.Kin san maza basu da ta ido zai iya furtawa hakan ya jawo miki matsala gara mu yi rabuwar mutunci,in ban da shi ma ina ke ina kishi da Anty Naja mace me mutunci." "Nima haka na gani Mama hankalina ya tashi ƙwarai."Tace da ita ta na juya wayar da ya ba ta."Kinga gobe ki mayar mishi da wayar shi,kice ni na ce ki mayar masa na tabbata ya tsorata ki ne amma ba zai yi gigin bata wayar ta baki ba,in dai ba ya na so ya kira ma kansa ruwa bane." "To Mama in sha Allahu zan mayar masa,ni ma bana son na riƙe irin wayar nan don Allah kaɗai ya san abin da Baba Sani zai faɗawa jama'a." "Haka ne Allah ya fishi."Ta bata amsa tare da miƙewa don ɗauro alwalar kiran sallar magariba da ke ta kwaɗawa masallacin kusa dasu. Washegari da ta je gidan bayan fitar matarsa ya dawo kamar yadda ƴan kwanakin yake mata,ta na ganin shi ta ƙara tamke fuska kamar ba ta ganshi ba ta ji gaba da aikin ta. Ta yi tunanin zai yi mata magana amma sai ta ji shiru na tsawon lokaci,da sauri ta waigo sai ta ga ita yake kallo kamar bai taɓa ganin ta ba.Miƙa masa wayar ta yi tace."Mahaifiyata tace na dawo dashi,kuma don Allah ka yi min rai ka fita sabgata domin ba za ta amince aci amanar Anty Naja ba." "Ni kuma sai na shiga wani hali ko?Wannan dalilin ya sa kika ƙi ɗaukar wayata jiya da daddare sai ma kika kashe wayar.Dama masoyi ya na zama maƙiyi Juwairiya?"Ya ƙarashe maganar da sigan tambaya,a yadda ya furta maganar sai ta ji ranta babu daɗi,ganin namiji mai natsuwa ya na mata magiya akan ta so shi. Wani irin abu ta ji a ranta in da ace matarsa ba ta shiga tsakani ba,babu yadda za'ai taƙi auren shi sai dai ba za ta zama butulu ba.Ganin taƙi kallon sa bare ya saka ran za ta yi magana,sai ma hawaye da ta soma ganin haka ya ɗauki wayar da ta ije mishi ya fice ya san ta na sonshi,amma tsoro ne ya cika mata zuciya in ko haka ne zai je har gida ya nemi aurenta. Kwana biyu haka suke wasar ƴar ɓuya ganin haka sai ya dena shiga sabgar ta ko dawowa gida ya dai na,ya na shirye-shiryen zuwa gidan su ya nemi auren ta. Ranar wata yammacin talata ta tashi daga aiki kasancewar an yi rana sosa,da yake lokaci ne na damina garin ya fara haɗa hadari.Juwairiya sauri take ta isa gida saboda ta kauce ma baƙin hadarin da yake tasowa ya na canza garin da yake duhu sosai. Hon ta ji an danna mata ta waiga sai ta ga Daddyn Abnaj ne ya na mata murmushi yace."Maza shigo na kaiki gida kar ruwa ya zane min masoyiyata."Ta yi kamar ba za ta shiga ba amma ganin har an fara iskar hadari ya sa ta buɗe gidan baya ta shige,tare da haɗe girar sama da ƙasa don karya tambayeta dalili Hakan sai ya ba shi dariya sosai bai ce komai ba suka fara tafiya, sai ya sai ta madubin motarsa dai-dai in da take zaune."Wato na zama direban ki ko."Ya jefa mata tambaya dai-dai lokacin da ya fara tafiya. "Ina wuni."Tace ba tare da ta amsa mishi tambayar ba. "Ba zan amsa ba ina fushi."Yace ya na kallonta ta gilashin motar. Ba tace mishi komai ganin hakan ya sa ya fara magana da murya mai taushi."Matsalar ƴan mata kenan da kun ga namiji ya na ƙaunarku,shikenan kun samu zaren ja amma babu komai nima lokacina ya na nan zuwa,don na fara hango sona a cikin ƙwayar idanunki." Ta ɗan saki ranta saboda ta fara sabawa da shi ya wan janta da ɗawainiya da yake musu ta ja numfashi ta sauke ta fara magana da cewa."Ku kuma maza ba amana ka san kusancin dake tsaƙanina da matar ka,amma ka bijiro da wannan lamari haba kai ma ka auna ka gani bai dace ba." "Kija min aya da ya hana hakan ko hadisi."Ya faɗa a raunane kuma a taƙaice.Babu amma Bahaushe ya na girmama al'adarsa hakan ya saɓa ma al'adar Bahaushe."Sitiyarin motar ya buga da ƙarfi yace "Kin ji ko in da karatun naki ya tafi ina miki zan can addini kina yi min wata magana can,kawai na gane bakya sona ki ce na haƙura kina da wani hakan zai sa na bawa zuciyata haƙuri duk da na san za ta shiga wani hali." Yanayin da ya yi maganar sai ya bata tausayi amma ta san abin da yake so ba mai yiwuwa ba ne.Murfin motar ta ɓalle za ta fita ganin sun ƙaraso gida ya yi parking,sunan ta ya ƙira da wata irin murya.Ta waigo ba tare da tace ƙala ba,sai ƙasa da kanta da ta yi wato alamun ta na sauraren sa. "Ki yi tunani zuwa ƙarshen sati nan nake so na turo magabata na,ina ganin za ki dakata da akin nan kafin kizo a matsayin ƙanwa kin ga sai ki ɗora daga in da kika tsaya ki na samun lada rututu! Ɓalle motar ta yi ta fice dai-dai lokacin da ya miƙa mata ƴan rafar ɗari biyar kusan kimanin dubu ishirin ba tare da ta karɓa ba ta fice,musamman da ta ga Baba Sani tsaye a ƙofar gida shi da wani mutum ya zura mata ido. Ganin jikinta ya soma rawa ya kalli in da take kallo,sai hakan ya yi mishi daɗi domin faɗuwa tazo dai-dai da zama,ya buɗe murfin motar ya fito ya nufi su Baba Sani dake kallon Juwairiya kamar ya shaƙe ta. Da sauri ta matsa za ta bi ta bayansa ta shige cikin gidan da ya bake ƙofar,amma sai ya daka mata tsawa tare da jan hijabinta."Ina zaki ƴar iska maza dawo,iskancin naki ya kai har a kawo ki gida a mota.Kawai sai ya saka salati da ƙarfin sa ya ci gaba da cewa."Inna lillahi gara da ka mutu Yaya Ahmed in da ka na raye Juwairiya ita za ta ƙashe ka.Karuwa kika zama fa ke ko kunya duniya ba za ki jiba tunna baki ji na Allah ba." "Ashsha!Subuhanallahi haba Malam ya za ka dinga jifan ta da waɗannan muggan kalamai?Iya sani na Juwairiya yarinyar kirki ne ta ɗaɗe ta na tare damu ta na mana aiki.Yanzu haka mun daidaita ne nake son ka bani auren ta,ma'ana na yaba da hankalinta ina sonta." Wayyo Allah faɗin haka da ya yi wato ya na son Juwairiya ji Baba Sani ya yi kamar ya watsa mishi fetur ya kyasta ashana domin baƙin cikin sa biyu ne a kan maganar.Na farko ta ya ya za 'ai mutum me hannu da shuni yace ya na sonta,sannan kuma baƙin kishinta ya taso ya lulluɓe mishi zuciyarsa kawai sai ya ƙara kuka ya na faɗin ma abokin da suke hira cewar."Kaji ko wai na ba shi aurenta bayan ya gama iskanci da ita ni nasan ya na naɗe tabarmar kunya ne.Amma ta ya ya zai auri mazinaciya!Ba Juwairiya dake tsaye ta na kuka ba har ta Daddyn Abnaj sai da yaji wani irin abu ya soke shi ya rintse idanunsa ya na jin kamar ya shaƙo wuyar Baba Sani,take ya fahimci wani abu wato na zaman ƙunci da suke yi iya zaman su da ita bata taɓa basu labari ba,duk da ya san cewa ba lai-lai bane ta gaya musu kasancewar ta na da zurfin ciki. Ya kalli Juwairiya da ta ƙara sautin kukan ta ganin mutane sun fara taruwa Baba Sani yaci gaba da magana da ƙarfi ya na nanatawa,sai ta ruga da gudu dai-dai lokacin da Baba Sani ya kai mata bugu a bayanta. Ba ta san ya suka ƙare ba ya dai shigo gida ya na ta faɗa tare da ja mata jifa'i kala-kala, Juwairiya ta so ta tanka saboda abin da ya yi mata a gaban mutumim da yake girmama lamarin ta,amma Mama ta hana duk san da ya gaya mata baƙa ta buɗe baki za ta yi magana Mama za ta hana ta,har ya gaji da rashin mutuncinsa ya fice. A ranar Juwairiya ta ci kuka sosai ta ji ta ƙara mugun tsanar shi a ranta. Washegari ganin taƙi shiryawa taje aiki Mama ta shigo ɗakin ta tsaya ta na kallonta tace."Juwairiya ba zaki je aiki bane naga rana ta yi." "Na haƙura da aikin Mama gara na zauna a gida dama kin san mun yanke shawarar na daina zuwa,sai ga abin da Baba Sani ya yi min a gaban shi Allah kunya nake ji matuƙa.Karuwa ya kira ni."Sai kawai ta saka kuka ta na jin zafin kalmar da ya danganta ta da ita." Mama a ranta har tafi Juwairiya damuwa amma sai ta ɗan gyara murya tace."Ki yi haƙuri komai lokaci ne watarana sai ya yi dana sani,amma da kin daure kije kila ma ya shafa miki lafiya don na tabbata ba zai ƙara miki maganar soyayya ba,ganin yadda ya tozar taki." "To Mama shikenan a haka rayuwata za ta ƙare duk wanda ya fito neman aurena sai Baba Sani ya ɓata lamarin gaskiya na gaji."Tace cikin hawaye yayin da ta tuna katoɓarar da ta yi na faɗin hakan,kamar ta nuna ta na son auren kenan sai ta zari hijabinta da sauri ta fice zuwa aiki. Ko da ta isa bata sami Anty Naja ba duk da ta san dama abu ne me wuya ta same ta,abin mamaki ta yi sallama ta shiga fuskarta babu walwala,sai ta same shi zaune akan one siter ya zuba tagumi ya na kallon hanya,ganin ta ya saka shi sakin ajiyar zuciya mai ƙarfin gaske. "Shigo mana Juwairiya hankalina ya tashi matuƙa na yi zaton wannan mara kirkin Baban nan naki ya hanaki zuwa "Yace da ita ganin ta dogare a bakin ƙofa,ta ɗan tsaya ta na kallon shi sai kuma ta ƙara haɗe fuska haushin sa take ji don shi ya yi shishshigi a lamarinta,har ya saka Bab Sani ya yi mata wannan tozarcin. "Gaskiya ban ji daɗin abin da ya faru ba!Haba sai kace ba ƙanin mahaifinki ba.Lamarinsa ya tsoratani baƙin cikina yadda yaƙi yadda da maganata akan ina sonki da aure.Kawai ki gaya min dangin ku naje can na nemi aurenki." Yace da ita ya na kare mata kallo don ya fahimci a wani hali take,takaici ya kamata jin abin da ya faɗa sai ta miƙe hanyar kicin ba tare da tace mishi komai ba. Gabanta ya sha tare da riƙe mata hijabi yace."Na fa fara ƙosawa da halin ko in kula da kike min haba waike dutse ne a ƙirjin ki ba zuciya ba!Ki ji tausayina ko don halin da kike ciki ki zaɓe ni a matsayin mijin ki hatta mahaifiyarki ba za ta zauna a wannan gida ba. Takai hannu da nufin ta ƙwace hijabinta sai ya riƙe hannun cikin kalar tausayi ya na jin kamar ya yi mata kuka,ganin sam ba ta da rangwame akan soyayya.Baki ta buɗe da nufin ta yi magana sai suka ji sallamar Anty Naja ta shigo da sauri da alamun gajiya tare da ita. Da sauri ya saki hannunta ya matsa gefe ya na zare ido,ita ma cikin tashin hankali ta tsaya ta kasa haɗa ido da ita ta na jiran tashi n hankalin da za ta fuskanta. Amma sai dukansu ta basu mamaki ta faɗa kan kujera ta na lumshe ido "Wash Allah! Na gaji matuƙa Juwairiya bani ruwa don Allah."Tace cikin sakin fuska ba tare da ta fahimci komai ba." Da sauri Juwairiya ta shige kicin ta na mamakin sokanci irin nata haba ta ya ya za'ai tace bata fahimci komai ba.Bayan ta kawo mata ruwan ta haɗo har da abin motsa baki,ta shige kicin ta ci gaba da aiyukan ta can sai ga shi ya shigo yace."Ina jiranki in kin gama zaki tafi ina hanyar da nake tsayawa sai mu ƙarashe tautaunawar. Ganin ba zai saduda ba Mama tace ta haƙura da aikin in ta bata kuɗin aikin ta na wata haka kuwa aka yi,bayan ta yi mata albashi ta ƙara mata harda zannuwa masu kyau biyu nata sai ɗaya Mama ta ɗinka,kasancewar suna da biki a family ɗin su kuma tare da Juwairiya za su tafi garin Kano. Hankalin Anty Naja ya tashi matuƙa ganin ba ta zo aiki ba,ta shiga ruɗani ta din ga tunanin ko ta yi mata wani abu amma bata gano ba.Shi ma hankalinsa ya tashi sosai duk da yaso sai sun gama daidaitawa a tsakanin su sai tabar aikin,amma ta yi sauri gashi ya na son yaje gidan ya na tsoron tijararren ƙanin mahaifinta Sai ya azalzala ma Anty Naja ta shirya ya kaita har ya na mata barazana da ya na nan akan bakan sa in dai ba Juwairiya ba sai dai ta bar aikin,ai kuwa ba shiri ta shirya suka taho ya ijeta a kofar gidan ta shiga ciki ya zauna da yaransa ya na jiran ta fito,burin sa ya ga Juwairiya. Juwairiya na tsakar ta na girki Mama ta na zaune ta na jan carbi ta yi sallama ta shigo,da sauri Juwairiya ta saka hannu ta rufe fuskarta ta na dariya. Anty Naja ta harareta ta na kallon Mama tace."Da ma Mama haka Juwairiya take bata da kirki? Kawai ta guje mu ba tare da mun yi mata wani abu ba,hankalina ya tashi ƙwarai Mama gaskiya ba ta kyauta ba." Ta ƙarashe maganar ta na kallon Juwairiya sannan ta ɗora da cewa "Ko mun yi miki wani abu ne?Ai gaya mana ya kamata ki yi ba ki ɗauke kafafunki ba.Ni da yara da Daddyn su Abnaj duk hankalin mu ya tashi." Mama ita ba tace komai ba tace komai ba sai dariyar yaƙe take mata,bayan sun shiga ɗaki suka yi gaisuwa a tsakanin su sanann shiru ya biyo baya.Sannan Anty Naja ta katse shirun tace."Me ya faru Mama kwana biyu bata zo aiki ba na yi tunanin ko wani ba lafiya,amma da nazo naga kowa lafiya.Ko na yi laifi ne Mama." Matuƙar kunya sai ya lulluɓe Mam ta ji kamar ta nitse ta rasa yadda za ta fara mata bayani,har Juwairiya ta yi sallama ta shigo,ganin Mama ta kasa mata bayani ta kalli Juwairiya tace."To ko auren ne ya zo,in kuma wannan ne Mama ai ni ce me haɗo kayan ɗaki ko?"Ta ƙarashe maganar ta na me tsigar tambaya. I ta dai Juwairiya ba tace komai ba ta na ta wasa da yatsunta,Mama ta daure tace."Ba shi bane ban san dai yadda zaki ɗauki zancen bane shi yasa na kasa sanar miki,amma ranar wanka ba'a ɓoyan ciji." Gaban Anty Naja ya faɗi daram!Sai ta ji zuciyar ta ta raya mata lai-lai a kwai abin da suke ɓoye mata,duk da bata san ko menene ba amma taji ta firgita Allah ya sa ba wani lamari me girma ya faru ba. Ganin ta yi shiru ba tace komai ba jikinta ya yi sanyi Mama dai ta daure tace."Dama mijinki ya bijiro da wata magana ya na son auren Juwairiya har ya shigo da maganar gida,mu kuma muka ga rashin dacewar haka saboda irin halaccin da kika yi mana shi yasa nace ta dakata da aikin kawai ki nemi wani."Tace ta na karantar fuskarta. Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Mu haɗu a shafi na Tara.Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakaƙuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. *FOLLOW, READ, COMMENT, SHARE* *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *SHAFI NA TARA* Abin mamaki da yake macece wayayyiya sai bata nuna komai ba duk da irin tarin luguden da zuciyar ta take mata,ta na jin kamar ta fita ta shaƙo shi munafiki kawai haba ya kamata a ce ta ɗago tuntuni saboda yadda yake yabon ta da kalamai magana ɗaya biyu ya sako sunanta,amma da yake ba ta da wayo sai ba ta ɗago ba ta danganta kular da yake bata a dalilin ta na kular mishi da yara,sam ba ta yi tunanin zai ce ya na sonta ba ganin basu da komai ƴar Malam Shehu. Wayancewa ta yi ta na dariyar yaƙe tace."Haba Mama ni na yi tunanin wani lamari ne me girma yasa kika hana ta,amma akan wannan ɗan ƙaramin abin zaki hana ta,in dai a kan wannan ne karku damu ai gara ya auro wacce na sani da ya ɗauko min wata.Kuma karku manta shi fa mijin mata huɗu ne,don Allah karku ce zaku hana mishi aurenta." Yanayin yadda take maganar ya nuna da ƙarfin hali kawai take yi,amma ta na ƙoƙarin ƙaƙalo dariya. "Haba ƴar nan ai ana barin halas don kunya kawai ya nemi wata,amma Juwairiya ba tsarar auren sa bane." Anty Naja ta dage ta riƙe kishinta ta na ba ma Mama baki akan ta haƙura ta yadda ayi auren,sannan ta ɗora da ko ba zasu bashi ba don Allah Juwairiya ta dawo aiki. Daga ƙarshe ta yi ma Mama sallama ta fita har ta na tonon Juwairiya ta fito tare suke da angon ta yazo biko,ita dai ba tace komai ba a ranta take mamakin wani irin hali take dashi.Bayan ta jaddadawa Juwairiya tazo aiki ta yi musu sallama ta fita. Bayan ta fita ta buɗe murfin mota ta shige tare da haɗe girar sama da ƙasa a ranta ta na mamakin raina mata wayo da ya yi wato ya turo ta ta yi mishi bikon budurwar shi,bayan ta sheda Juwairiya yarinyar kirki ne sai tace amanarta suke ci. A yadda ya ga yadda ta fito sai hankalinsa ya tashi don bai yi tunanin za su gaya mata abin da ke tsakanin sa da ita ba,sai ya yi dana sani da tuntuni ya tare ta da maganar. Bayan sun fara tafiya ya kalleta yadda ta ƙara cin magani fuskarta ba rahama yace cikin ƙarfin hali ya yi mata tambayar."Ya take ko ba ta jin daɗi ne?" Haba kamar jira take ya yi tambayar lokacin da take kallon waje ta fara bala'i in da take shiga ba nan take fita ba tace."Munafiki da zamu taho ai da ka gaya min biko zan je na yi maka.Da ma amanata kuke ci kai da ita da ta amince ƙila sai dai in ji ta tare a gidana ko." Nan ta ɓalle ta na gaya mishi kalamai zafafa mara sa daɗin ji,in da take shiga ba ta nan take fita ba a hanya ta zage shi tatas! Ta yi mishi wankin babban bargo.Shi dai shiru ya yi mata don ya san ya ibo ruwan dafa kansa kuskuren shi ɗaya da bai sanar mata ba,kuma bai ɗauka su Juwairiya za su yi suɓul da baka su gaya mata ba. A haka suka kwana sam ba ta barshi ya rintsa ba,shi kan shi bai san ta iya rikici ba,sai ayau ya san ta na da zafi mata da kishi humh ba'a magana. Washegari Juwairiya ta na zaune ba ta da ninyar zuwa aiki amma Mama ta matsa mata akan taje.Sai dai yadda ta ga gidan ta san ba su kwana lafiya ba. Tun daga falon take kallon yadda ya hargitse ko ina an birkita shi sai gabanta ya fara faɗi ta san cewa a kwai wani girman lamari da ya faru. "Munafuka kema me ya kawo ki gida!Maza fita matsiyaciya me kwacen miji kawai,in banda ke jahila kina ƴar talaka za kiyi tunannin mijina zai aureki."Anty Naja take magana cikin zafi sannan ta ɗora da cewa."Fita kar na ƙara ganin ki a gidana,sai abi wani sarkin amma mijina yafi ƙarfin ki. Ko da ta dawo ta sanar ma Mama tace."To shikenan Allah ya sa haka yafi alkhairi.Hankalin Baba Sani ya kwanta ganin Juwairiya ta bar aiki kullum ta na gida,hakan sai ya yi masa daɗi musamman da yake tunanin yanzu komai zai kwaɓe musu. Juwairiya ta yi tunanin Baban Abnaj zai biyo bayan ta,amma shiru kake ji Malam yaci shurwa wato matarsa taci ƙarfinsa.Ganin haka sai suka kama sana'a sosai da kuɗin da Baban Abnaj yake basu,yanzu har abincin siyarwa suke yi Ibrahim ya na kai wa ƙofar gida.Kuma suna samu ba laifi don da shi suke cin abinci. ********* Kimanin shekaru huɗu da auren su suna zama cikin so da ƙaunar juna,sai ƴan saɓanin da ba'a rasa ba a tsakanin ma'aurata.Kullum A.m ya yi kasaƙe ya ji Zainab tace mishi ta na da ciki amma hankalinta ba shi a gurin tunna ba ta taɓa yi mishi maganar baby ba. Lamarin sai ya fara damunsa musamaman da ƙannin shi da sa'annin shi suna da yara,amma shi matarsa ko ɓatan wata ba ta taɓa yi ba. Sai kuma Allah ya ɗauki son ƴara ya ɗora mishi in ya gan su kamar ze zare.Ya na matuƙar son yara kullum ya na hanyar gidan ƴan'uwan shi ya na manne da yaransa.Daddy ɗin shi ya fara ƙorafi ya na tsoron kar A.m ya ɗauko rashin haihuwa sai ya fara mishi ƙorafi sosai kullum ya na kiran waya akan suje likita ya duba su. Ganin yadda ya ɗauki son yara ya ɗora ma kansa sai Zainab ta yi gum da bakinta ba ta taɓa suɓutar baki ta nuna mishi ita ce ba ta son ta haihu take shan ƙwayoyi ba. Sun ɗan fara samun saɓani yadda yake kwaso yaran ƴan'uwan shi ya kawo gidan ya siyo musu kayan wasa.Ranta ɓaci yake sosai ta na ganin hakan kamar takuratawa rayuwarta ne,duk yaran da ze kwaso ba ta musu komai sai masu aiki.Gaskiya Allah ya jarabce shi da son yara sosai. Wataranar Alhamis Zainab ta tashi da ciwon ciki kamar za ta mutu,hankalin A.m ya tashi matuƙa ganin a sume ya ɗauke ta ya saka a mota suka nufi asibiti. Bayan an karɓe ta aka yi mata ƴan gwaje-gwaje tare da turata ɗakin hoto,duk abin da ake ta na kwance kamar gawa ba ta san in da kanta yake ba.Likita ya gano mahaifarta ce ta samu matsala sakamakon tarin ƙwayoyi da ta din ga ɗinkira ma kanta masu ƙarfi na hana haihuwa.Wanda sakamakon haka mahaifar na gabda ruɓewa in da likitan ya ba A.m shawarar ayi mata aiki a cire mahaifar. Tsananin tashin hankali A.m ya shige shi ya din ga kallon likitan kamar ƙarya ya yi mishi."Me yasa Zainab za ta aikata hakan?Hakan na nufin ba ta son shi ne har take shan maganin hana ɗaukar ciki don kar ta haihu?" Irin tarin tambayoyin da yake yi ma kansa kenan amma ba shi da amsarta,daga bisani ƙeƙeshe zuciyarsa ya yi kan ƙaryata likitan ya san Zainab ba za ta aikata hakan ba,musamman yadda ta ga Daddyn shi ya mutu akan ya ga ya haihu,sannan yadda yake nuna mata ya na son ta haifa mishi baby ta na nuna masa Allaha ne be kawo ba.To hakan na nufin yaudararsa take. Sai ya yi zuru ya na kallonta da take saukar da numfashi cikin rashin haiyaci ta na bacci,sakamakon allurar baccin da likita ya yi mata.Sai ya shafi fuskarta ya na me tausaya mata halin da ta shiga. "Gaskiya ban yadda da maganar likita ba ina ta ya ya zan rayu ba tare da na ga ɗan cikina ba,duk da na san Allah ya ba jarabtar bayinsa amma gara wata jarrabawar ba wannan ba.Ya na ganin halin da Daddy ɗin shi yake shiga saboda rashin ɗa duk dukiyar da ya tara ya tafi a banza.In in haka ne ya zan yi da shares ɗin da na saka ma yarana tun kafin su zo duniya a ƙasashen waje. Nan take zuciyarsa taƙi amincewa da abin da likitan ya faɗa duk da ya san asibitin su ƙwararru ne. Kusan awa ɗaya ta na baccin wahala sannan ta buɗe idanunta.Da sauri ya riƙe mata hannu ya na shafar kanta."Kin tashi babyna sannu. Yace ya na ƙoƙarin temaka mata tashi ta zauna. Bayan ya haɗa mata tea ya ba ta tasha ta lumshe idanunta ta na ji har yanzu wani abu ya na karta mata a cikinta,ita kaɗai ta san irin tarin azaba da raɗaɗin da take kwankwaɗa. "Ya jikin sannu kin ji abin da likita yace game da ciwon ki?"Ya tambayeta da murya mai sanyi ya na gyara mata ɗaurin ɗankwalin ta da yake son ya warware.Ba tare da tunanin komai ba tace."A'a hubbina."A taƙaice ta ba shi amsar don ba ta son dogon surutu. Ya ɗan ja numfashi ya fesar ya jinjina girman lamarin baya so ya gaya mata,bai san yadda za ta karɓi lamarin ba cewar ba ta haihuwa mahaifarta ya fara ruɓewa wanda dole sai an yi mata aiki.To amma ya na son ya gane shin da gaske ita tasha maganin hana ɗaukar ciki har ta illanta musu kanta,ba yan haka da ya bari sai ta warke. "Likita yace ba zaki taɓa haihuwa ba yanzu ma mahaifarki za'a yi miki aiki a cire."Yace da ita ya na son yaga yadda za ta ƙarɓi lamarin. "Inna lillahi.Tace tare da bayyano wani tashin hankali a fuskarta nan take fuskarta ta sauya sai hawaye,ta yi ƙasa da kanta ta na son ta yi magana amma ta kasa sai hawaye dake ta gasar sauka a fuskarta.A zuciyar ta kuwa illa tarin nadama da faɗin"Na cuci kaina!" "Ina son na sani da gaske ke kika illan ta mahaifar ki Zeey sabosa bakya son ki haihu da ni,ko dama ba kya sona ne ko a kwai wani ƙudiri a ranki."Yace bayan ya yi ƙasa da kan shi dai-dai da kunninta saboda baya son aji me yake faɗi. Ta dago ta kalle shi fuskarta cike da hawaye ganin yadda fuskarsa ya bayyana da tashin hankali,don in ba ta yi ƙarya ba har hawaye ta gani a fuskarta. "Na shiga uku yanzu in yace ya na son ya haihu ga shi ni bana haihuwa ya zan yi?Kuma wallahi ba zan taɓa iya lamun ce na gan shi da wata mace ba.Gara ma ace na ga ranar mutuwata!Tace a zuciyarta ta na kukan nadama. "Ka yi haƙuri hubbi ka yafe min na san na yi wa rayuwata illa ba zan taɓa haihuwa ba!Girman lamarin ya yi wa zuciyata girma.Duk akan sonka ne ina son karka juya min baya inna fara haihuwa na saki sanann jikina ya canza,kuma na sha jin kana faɗin baka son jikina ya canza kafi son na kasance yadda nake.Kuma a wannan lokacin ban shirya haihuwa ba gani nake yara kamar takurane a gareni duba ga irin yanayin aikina."Sai ta fashe da kuka ta na ƙarawa taci gaba da cewa."Wallahi ba zan iya buɗe idanuna na ga wata mace a matsayin muharramar ka!In kuwa ranar ta kasance to kasa a ranka zan kashe kai na na kasheta sannan na kasheka.In taƙaice maka mutuwar kasko za muyi,don ina sonka ba zan juri wata a kusa dakai ba." Tsananin tashin hankali ya shige shi tare da nadamar furta mata waɗannan kalamai da yake na baya son yanayin ta ya canza,duk da be yi tunanin za su yi tasiri a gareta ba har ta aikata wannan abu su yi dana sani. Ya zura hannun sa a aljihun wandon sa ya na kallon yadda fuskarta ya canza zuwa tsabar tashin hankali,ita kanta ya san ta yi nadama amma kuma mara amfani. Ganin be ce mata komai ba ya na tunanin wanda shi kansa be san tunanin da yake ba,sai ta ci gaba da cewa."ko ma me ya faru duk akan sonka ne A.m ina kishin ka zan iya komai a kanka,son da nake maka ya sa na lalata mahaifata." Ta kalle shi idanunta ya na zubar hawaye ta kama hannunsa ta haɗa da nasa tare da kai bakinta dai-dai saitin kunninsa."Don Allah ka yi min wani alƙawari,ka amince za ka yi min sannan gaya maka." Ya damƙe hannunta ƙaƙam ya na hawaye matuƙar tausayinta ya kama shi ganin duk akan son shi ta shiga cikin wannan halin domin ta burge shi. "Na yi miki alƙawari amma wa ya gaya miki in mace ta haihu mijinta ya na tsanar ta ni fa ina yaba miki kyawun halittar ki amma ba wai ba na son ki haihu ba.Yanzu ya zan yi da iyayena da suka ɗora idanunsu akaina suna son suga jikar su?" a tambayeta ya na ganin tsananin wautar ta da ta aikata hakan,ita ma da ma wannan kan gabar take so yazo sai ta ƙara damƙe hannunsa tace." Ka yi min alƙawari ba zaka taɓa juya min baya ba kuma wannan ya zama sirri tsakanin mu cewar nice ba na haihuwa,sannan ka gaya ma dangin ka cewar matsalar da ga gareka take.Bayan haka ba za ka taɓa yi min kishiya ba,in kuma ka yi to lai-lai nice ajalinmu baki ɗaya." Ta faɗa da farko da son ya ɗauki alƙawarin muryarta a shaƙe ta na murza hannunsa,amma daga ƙarshen maganarta sai ta ƙarashe da murya kamar wacce take ba shi umurni ko tsoratarwa. Rungumeta ya yi ya na jin matuƙar tausayin ta duk da girman lamarin amma sai be ga wata illa a ciki ba,musamman da ya ga duk akan sa lamarin ya faru don haka zai amince ya gaya wa iyayensa da hakan, dama shi a duniya be ga wata mace wacce za ta haɗa kanta da Zey ɗin sa ba ita kaɗai ya ji ta burge shi kuma zai ci gaba da son ta ba tare da ya haɗa ta da wata ƴa mace ba don babu ita a duniya. "In dai akan wannan ne karki damu na miki alƙawari,zan shirya mana viza zuwa ƙasar indiya a duba min ke don ban yadda cewar ba zaki taɓa haihuwa ba.Ƙara ruƙunƙume shi ta yi ta na faɗin."I love you nureel ƙalbi.!" Loakacin da suka ji Zainab ba lafiya hankalin su ya tashi take a ka cika asibitin domin sun ɗauka ko ciki ta samu.Mahaifinta da ba shi ƙasar ya na jin ta na asibiti ya biyo jirgi ya dawo,ya na ta addu'ar Allah ya sa ta samu juna biyu,saboda ya na tsoron kar ita ma ba ta haihuwa kamar Mominta,duk da ya so ya ƙara aure ta yi ruwa ta yi tsaƙi ta hana. Wani irin gata suke nuna mata sosai musamman gidan su A.m duk tunanin su ya sami ɗa ne,saboda tunanin su ya sa suke yi mata abinci irin na masu ciki suna kawo mata. Hakan sai ya sa jikin A.m ya yi sanyi ya na tausayin su don haka ya shirya musu biza suka wuce Indiya domin a duba lafiyarta. Kwanan su biyu suka huta sannan suka fara ganin likita,sai dai gwajin farko da suka yi mata aikin gaggawa suka sa aka shigar da ita tiyata,saboda mahaifar ta fara ruɓewa ta na narkewa a jikinta wanda hakan zai iya kawo mata matsala.A.m ya shiga tsananin tashin hankali duk yadda yake cikin tashin hankali sai ya kwantar da na sa ya na lallashinta ganin ta na son ta yi ƙaramin hauka. Be baro ƙasar ba sai da ya tabbatar ta warke garau babu wanda ze ce an yi mata aiki.Sannan suka wuce zuwa yawon shaƙatawa don ya kwantar mata da hankali. Zainab ta yi kuka har ta ba uku lada daga ƙarshe suka tattaro suka dawo cike da alhini. A lokacin da A.m ya sanar ma family ɗin sa sun shiga cikin tsananin tashin hankali barim ma Daddy da har sai da ya yi kuka,ya rungume A.m ya na shafa bayan sa da tsabar tausayi da ya cika mishi zuciya." Yanzu son kai ma ba zaka ga ƙwanka a duniya ba.Allah Sarki ni da kai ne kawai ba mu da rabon haihuwa."Sai ya ci gaba da sharara hawaye. Mahaifin shi ya jinjina lamarin tsananin tausayin ɗan na sa ya kama shi."Ni yanzu nafi tunanin matarsa an ya anyi mata adalci ina ga ka bata zaɓi kawai,domin na tabbata da ita ne ke da matsalar aure zaka ƙara in kuma ta amince za ta zauna dakai kaga ba'a shiga haƙƙin ta ba."Yace ya ba kallon ɗan nasa cikin tausaya wa. A.m ya ji matuƙar tausayin iyayen nasa ganin yadda suka tashi hankalin su,suna jimami da alhini anya ya kyuata musu kuwa.Sun ba shi tausayi matuƙa wanda ya sanyaya jikinsa amma ko ma menene ya riga ya yi mata alƙawari. "Haka ne Baba nima na bata zaɓi,amma tace ba za ta iya rayuwa ba ni ba."Ya ba shi amsa kansa duƙe." To shikenan Allah ya kyauta ai faɗan likita ba na Allah ba ne,sai kaga Allah ya canza lamuransa "Sun yi matuƙar jimami suka fauwala ma Allah lamuran sa ƴan'uwan shi suna ta yi mishi tayin ya karɓi yara daga cikin ƴaƴan su,duk da ya na son hakan sai dai ya san Zey ɗin shi ba za ta yarda ba. Zaman nasu sai yaƙi jituwa tun daga lokacin sai suke samun saɓani da ya fara mata faɗa, sai ta saka kuka tana faɗa masa don ya ga ba ta haihuwa ne. Tun ya na haƙuri har ya fara kai su gaban iyaye mahaifin shi kullum haƙuri yake ba shi ya na nuna mishi halin mata,dama tunna baya haihuwa ya shirya karɓan fiye da haka a gurinta. Rashin zaman ta a gidan shi yake ƙara damun sa kullum ya dawo aiki ba ze sameta a gida ba sai tarin ƙazaman ƴan aiki masu kama da mayu a gurin kallo.Shi ya manta rabon da yaci abinci me daɗi in dai ba gida yaje ba ko,gidan amininshi A.k.Kullum ba ta da gurin zuwa sai ƙawa ta gayyace ta bikin ƙawarta ana birthday ɗin ƴar ƙawarta aikin ta ne kullum yadda ka san ana tsikarin ta in ta zauna a gida mace kamar me aljanun fita yawo. Ya dawo da misalin karfe huɗu da rabi rabi na yamma yanayin garin hadari yake haɗawa ya canza iskar garin ta na bada wani iska mai sanyi-sanyi babu abin da yake so ya sha ruwan tea me ƙamshi ya shige cikin bargo ya yi bacci shi da ƴar matar shi. Sai dai abin takaici ya na shigo da motarsa ya ga ba nata motar tsaki yaja ya yi parking ɗin motar a kasale ya fito be kula sannu da ma'aikan gidan suke mishi ba ya shige ɗaki. Sharab!Ya zauna a falon sa ya na jin wani irin ƙunci ya saka yatsu biyu ya tallabe gemunsa ya lumshe ido da takaici,burinsa ya buɗe idanunsa ya sauke su akan kyakykyawar matar shi amma sai ya yi tozali da mero me aiki da tiren abinci ta kawo mishi tsaye ta na kallonsa. "Ke!Uban wa kike kallo."Ya daka mata tsawar da yasa ta watsar da tiren abincin za ta ruga,sai kuma ta dawo da sauri ta tsaya ta na ƙoƙarin gyara gurin ganin iri n aika-aikar da ta yi. " Anty ce tace na kawo maka abinci in ka dawo."Tace da shi bakinta na rawa ta na ci gaba da kallonsa.Ji ya yi tamkar ya shaƙeta ya miƙe kamar ze kai mata duka da gudu ta ruga.. "Zainab kina bani tarin matsala na gaji da kwashe-kwashe da kike min gaskiya."Ya faɗa idanunsa suka ƙara rinewa saboda tarin damuwar da yake ciki. Bata dawo gidan ba sai zuwa ƙarfe tara na dare ta shigo da gudu saboda ruwan da ake yi tamkar da bakin ƙwarya,a lokacin A.m na zaune akan kujera two seater ya matsu ta shigo yau sai ta gane kuranta. Ba ta kula da shi da yake zaune da waya a hannunsa ya na dubawa ba,ta tsaya a falon ta na ƙoƙarin cire kayanta da ruwa ya soma jiƙata saboda tafiyar da ta yi zuwa cikin gidan. Gyaran murya ya yi wanda yasa ta fahimci ya na falon gaban ta ya ɗan faɗi,amma ta dake bata ce komai ba sai ƙoƙarin ta na cire doguwar rigar da ya matseta kamar za ta yi amai,ta na ƙwala ma Mero kira. Wani ƙarin haushi ya turniƙe shi ita sam ba ta kishin jikinta ganin shigar da ta yi,sannan ta na cire kayanta amma take kiran me aiki tazo kai Zainab lamarinta a kwai gyara. Bayan ta cire rigar ta umurci Mero ta ɗauko mata wani wani kayan ta saka,sannan ta nufi gurin sa da yake zaune saboda tsaban takaici be kalleta ba bare ya tanka mata,sai kallon agogon hannunsa yake. Ba tare da nuna damuwa ba taja tiren abincin da ya saka Mero ta kwashe wan can ta kawo mishi,saboda tsabar yunwa da yake ji amma ya kasa cin abincin sam babu tes jira yake a gama ruwan ya ya yi take away. Fara ci ta yi ta kalle shi tace."Habibi ba ka ci abinci ba lafiya."Banza ya yi da ita yaci gaba da kallon wayarsa ya na danne-danne a cikinta. Kai hannu ta yi ta taɓa wuyan shi ko ta ji da zafi a tunaninta ba shi da lafiya,amma sai ta ji jikinsa normal.Taɓe bakinta ta yi ta ci gaba da cin abincin a ranta ta na faɗin."Miskilancinne ya motsa bari na kama kaina." Kusan minti talatin ya na kwance be tanka mata ba har ta gaji da zama yaƙi kunna kallo ta san ta na kunnawa, ze taso mata tunna dama a yadda ta gan shi jira yake ta taɓo mishi,sai ta miƙe sif za ta shige ɗakinta ta hau charting. Idanunsa a lumshe ba tare da ya buɗe ba yace."Da ga ina kike?"Yace a cikin wata irin murya me kama da da baya son maganar. Dawowa ta yi ta zauna ta duburbuce ta fara in ina.Ya ƙara jeho mata wasu tambayoyin da cewa."Sai yanzu kika dawo ba na hana ki dawo min gida da daddare ba?Me yasa baki wuce gidan kuba.Kuma da izinin uban wa kika fita?" Gabaki ɗaya ta tsorata ta kuma ruɗe ganin yadda yake jeho mata tambayoyin da ta kasa amsa koda ɗaya ne. Miƙewa ya yi ya matso kusa da ita ya na kallon kayan da tasa ya ɗauka ya na kallonta a wulaƙance."Ba na hanaki saka irin kayan nan ba wai ke me yasa bakya kishin kanki yanzu fa a gaban ƴar aiki kika canza kaya,sam bakya kishin sirrina Zainab hauka kike son na yi a kanki na fara gajiya da halinki." Duk cikin maganganunsa ba wanda ta ji haushi sai tambayar ta daga ina take da ɗan yi jim ta kuma dake ta ba shi amsa da cewa."Ina tunanin mun gama magana akan fita ba sai na tambaye ka ba saboda gaskiya ban ga a na wannan takurar a gidan mu ba.Kuma fa gidan ƙawar Anty Usaina muka je yau ake birthday ɗin ɗanta."Ta ƙarashe maganar ta na son ta ja hankalin shi ya sausauta fushin da ya ɗauka. Ya ƙara jan tsaki me ƙarfi dama ya san tatsuniyar gizo ba ta wuce ta ƙoƙi. Tsawa ya daka mata yace "Malama karki raina min wayo na gaji da waɗannan banzan bidi'oin da kika saka a ranki.Kin raina ni matuƙa Zainab baki ɗauke ni da daraja ba a matsayina na mijinki,watakila haka kika ga ana yi a aure a matsayinki na matar aure ba zaki shigo gidana ba sai tara da mintina." Kaɗa kansa ya yi ya miƙe yaci gaba da cewa."Kin san nace miki in har kika fita ba da izinina ba,ban yafe miki ba kuma mala'ikun rahama suna tsine miki harki dawo sai ki kiyaye." Hararan shi ta yi tace cikin gunaguni."Taɓ ni ai na gaya maka ba zan amince a takurawa rayuwata ba.Haka kawai to meye amfanin ilmina na lura so kake ka mai dani irin gidahuman matan nan marasa ilmi,waɗanda suke bari namiji na raina su wai duk in da zani saina tambayeka Allah ya kyauta." Da takaicin yadda ta raina shi bata shakkar shi yace."Ba ma fita ba na hanaki driving sai dai duk in da zaki a yi driving ɗin ki."Ya na faɗin haka ya fara taka matakalan bene ze haye. A sukwane ta jawo rigar shi ta baya cikin fushi tace."Wallahi ba za ta saɓu ba wai bindiga a ruwa Ka mata ni zan yadda wani shashashan direba ya tuƙa ni,karka manta kusan motocina daga gidanmu na zo da shi bare ka yi min iko,in ma akan wace ka siya min ne ba zan ƙara hawa ba amma ba wanda ya isa ya kafa min dokoki." Nu na ta da yatsa ya yi ya na cewa."Ba na hana ki kuma na yi miki warning akan riƙe min riga da kike yi ba,to wannan ya zama na ƙarshe da zaki ƙara wannan gangancin.Kuma kika kuskura kika zage ni sai kin raina kanki,don jikin ki ze gaya miki." Dariya ta yi me sauti ta ba shi amsa da faɗin."A lai-lai da ka tabbata ɗan ƙwaya kamar ni zaka buga aiko ruwan sama se inna so bare wani gardi can.Duk mutanen gidan ku kuwa sai an koya musu hankali ai ban yi kalar matar duka ba.Ko ka manta matsayin uba na."Ta numfasa sanann ta ɗora ta na kallon shi da tsananin ɓacin rai ya sa shi tsaye ya na kallonta. " Kuma da kake faɗin karna zage ka inna zage ka me za ka yi?"Tace mishi cikin zallar rashin kunya ta na karkaɗa ƙugunta.A.m ya yi ƙuta yace. " To ki kwatanta ki gani fitsararriya kawai." Baki ta turo mishi tare da murguɗawa." Ni ba fitsararriya ba ce banza mara m....". Wani irin mari ya gaura mata wanda yasa ta ɗauke lokaci guda ta yi taga-taga za ta faɗi amma ta dake tare da kwarma wani uban ihu,abin ka da farar fata lokaci guda fuskarta ta sunduma domin marin ya gigitata sosai. Amma saboda taurin zuciyarta ta cakume shi ta na ihu ta na zagin sa shi kansa ya yi mamakin kafiyarta,ture ta ya yi ya shige ɗakinsa tare da bugo ƙofar kai tsaye bayi ya wuce ya sakar ma kan shi ruwa,domin ta haɗa mishi zafi kwanyar shi har wani tafasa take yi. Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Mu haɗu a shafi na goma.Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. *FOLLOW, READ, COMMENT, SHARE* *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *SHAFI NA GOMA* Bayan ya fito da ga wankan ya na jin yadda sautin kukanta yake tashi ya na mishi kuwwa a kunninsa,sai ya ji be kyauta ba da ya mari rabin ransa take ya zira doguwar riga ya fita don ya rarrasheta. Ɗakin ta ya shiga ya ganta ta na ta kuka ta na haɗa kayanta tare da ƙoƙarin kira a wayarta,sai dai da alamu ba ta samu wanda take kira ba.Wayar ya fisge tare da rungumeta cikin tsigar rarrashi. Dukan sa ta fara a ƙirjinsa ta na ƙoƙarin raba jikinta da na sa,da kyar ya samu ta sausauta kukan ta ɗan yi shiru ta na sheshsheƙar kuka cike da shagwaɓa. Da ƙyar ta ya samu ta yi shiru amma ta rantse mishi duk ranar da ya ƙara kai hannunsa jikinta sai ta haɗa shi da Daddy ɗin ta,shi dai aikin lallashi yake ya na gaya mata maganganu masu daɗi har da kama kunninsa ya na faɗin ya tuba. Bayan sun shirya suka kwanta cikin ƙaunar junan su kamar babu abin da ya shiga tsakanin su.Yanayin garin sai ya basu damar yin bacci cikin shauki suna maƙale da junan su. Washegari suka tashi kamar babu wani abin da ya shiga tsakanin su na saɓani.Bayan ya yi wanka ya fice gidan amininsa ita ma ta gallah wanka ta fice aiki. Parking ɗin motarsa ya fito ya caɓe Anwar ɗan gidan A.k da ake goyo don yanzu ya iya tafiya. Juya shi ya yi ya na dariya tare da ɗauko tsarabar sa ya ba shi wanda duk ze zo sai ya kawo musu,sannan suka shiga cikin gidan sai ga ƴayarsa ita ma ta rugo da gudu ya ɗauketa haka dai ya shiririce ya na musu wasa har ya ɗauki tsawon lokaci. " Yau kai ne a gari in ji maƙi baƙo ka ga angon Zainab to sannu da zuwa."Matar A.k tace ta na dariya bayan ta kawo mishi ruwa. Shafa kansa ya yi ya na dariya yace."Gaskiya kince wani abu irin wannan kirari haka,kin san ƙawar taki bata da dama ba ta bari na naje ko ina gaskiya kin cancanci tukwici." Dariya ta yi tace."Gaskiya makka da madina nake so a kai ni."Tace da shi."Duk kin je sai sai in kina buƙatar zuwa sai na saka sunan ki a cikin jerin masu zuwa."Dariya suka yi duka. Sannan ta wuce ta na gyara dinning domin cin abincin rana.Bayan A.k ya fito daga ɗakin baccin sa ya ba shi hannu suka tafa tare da tsokanar junan su A.k yace."Ina madam Zey."Ya shafa gemun sa ya ɗan canza murya yace ƴar rigima za ka ce min na san yanzu ta wuce gurin aiki." Dariya ya yi shima ya na kallon shi."Ai hali ne ya zo ɗaya an haɗu ne da an dace."Su kai dariya tare da ƙara tafawa."Madam ta gama shirya abinci ka zo muci."A.k yace da shi yamutsa fuskarsa ya yi ya na kallon shi, nan take sai hankalin A.k ya tashi musamman da ya ga ya maida kan shi a jikin kujera ya na kallon shi.Nan take ya fahimci amininna sa ya na cikin damuwa. " Ya dai aboki a kwai matsala ko yanayin ka ya nuna a kwai abin da ke damun ka." Ya kauda kansa gefe ya na faɗin."Kai ma ka san matsalar a kan Zainab ce ta na ba ni ciwon kai lamarin ta a kwai gyara.Na rasa yadda zan ɓullo mata ga kafiya da taurin kai." A.k ya watsa hannun shi in akan wannan ne be wani dame shi ba yadda ka san auren dole a ka yi musu kullum cikin faɗa."In dai akan wannan ne ba ni da matsala daku kai ba haƙuri ita kuma kafiya ni lamarin ki ya na bani mamaki.Kun fi kusa kun san yadda zaku sasanta kan ku." Ya faɗa ba tare da wata damuwa ba don ba yau ya saba kawo mishi ƙarar ta ba,kuma ko yaje ba saurarsa take ba gashi shi baya iya haƙuri da fushin ta haka kawai su yi ta sa maka ɓacin rai. "Ko zamu keɓe ina da wata magana da zan ɗan tautauna a tsakanin mu kuma sirri ce."A.m yace da muryar raɗa ya na kallon gefen matarsa don ya yadda da aminin na sa ba zai gaya mata ba. "Ki kawo mana abincin falona."Yace sannan suka shge cikin ƙaton falonsa da ya sha gyara ya na ta ƙamshi.Bayan sun ci abinci sun natsa har sai da suka yi salar azahar sannan suka natsa tare da taɓa hirar kasuwancin su. A.m ya gyara zama ya na kallonsa cikin fuskar tausayi ya fara magana duk da wani gefe na zuciyarsa ta na masa gargaɗin karya faɗa masa amma ya fara magana da cewa. " A kwai wani sirri da na ɓoye a raina na san zaka fahimce ni kuma ka ba ni shawara me kyai kamar yadda ka saba,ina ganin kamar na yi wa iyayena rashin adalci da na ɓoye musu cewar ni ne ba na haihuwa bayan ba haka lamarin yake ba. "Na yi wa Zainab alƙawarin ba zan yi mata kishiya ba kuma ba zan taɓa gaya ma iyayena cewar ba ta haihuwa ba,amma na yi tunanin za ta canza halayenta mu yi zaman lafiya amma kullum ƙara bijiro da abin da zai saka mu samu saɓani,jiya duk ruwan da ake ta na waje wai sun je fati kamar ba matar aure ba,gabaki ɗaya ba ta damuwa da halin da zan shiga in ta ɓata min." Ya yi shiru ko zai ce wani abu amma be tsinka shi ba sai kallon shi da yake yi ganin haka sai ya ɗora da cewa." Jiya ta kai fagen da na mareta wanda daga baya na yi dana sani.Ka ba ni shawara kar Zainab ta haukani." A yanayin yadda ya yi maganar sai ya ba shi tausayi,sai dai ya na mamakin wai Zainab ɗin ce bata haihuwa kuma ya yi mata alƙawarin va ze gaya ma iyayen shi ba,sannan ba ya yi mata alƙawarin ba ze ƙara aure ba to wane irin shawara yake son ya ba shi don ya san be wuce yace ya ƙara aure ya samu matar da za ta ba shi yaro ba. "Gaskiya ka yi wauta kana tunanin in kai ne ba ka haihuwa za ta yadda ta zauna da kai?Kuma ka cuci iyayenka kullum muka haɗu da Daddy sai ya yi min ƙorafin rashin haihuwar ka ya na tausaya maka,ga kuma masoyinka da yake ɓatar da kuɗin shi gurin yi maka sadaka da neman maka magani." Ya numfasa ya na kallon shi a tsanake yaci gaba da cewa."Wace shawara kake son na ba ka bayan ka yi mata alƙawarin ba zaka ƙara aure ba kasan dai zuriya ta hanyar aure ake samun su,don haka Baban soyayya kaje kuci gaba da soyewa kawai shine shawarar da zan baka." Abin da A.k yace mishi kenan ya miƙe don ransa ya gama ɓaci.A.m shima miƙewa ya yi don ba shi da abin da ze ce kan shi ya ɗau zafi,shi dai ya san koma mene ne ba zai karya alƙawarin da ya yi mata ba. Bayan sun fito ya kalli matar A.k da take tattara gurin da yara suka ci abinci ya na dariya."To ni madan zan wuce."Dariya ita ma ta yi "Wato an gama gulmar mu ko ba komai nima ina nan zuwa gidana musha namu." A.m ya ƙara dariya yana cewa."Baku da dama ne shi yasa musamman mutuniyar ki.A.k ya ja hannun shi ya na faɗin.Muje ka ji in ka biye mata sai ta ɓata maka lokaci da surutun ta suka fice. ****** Juwairiya ta ƙara samun aiki a gidan wata mata mai suna Hajiya Binta,matar ta na da kirki matuƙar gaske yaranta bakwai.Kusan dukkan aikin gidan Juwairiya take yi,saboda yawan yaranta take wahala a gidan sai dai amma babu laifi suna ƙaruwa da ita.Matsalar ta ɗaya mafaɗaciya ce sam ba ta da haƙuri kamar zawo take,duk yadda take taka tsan-tsan amma sai ta rori abin da za ta yi mata faɗa. Saboda ba ta saba da irin aikin ba sai yake ba ta wahala ƙwarai,in ta dawo aiki ba ta iya taɓuka wani aikin watarana ma sai tasha maganin ciwon jiki. Ganin irin wahalar da take sha Mama ta ba ta shawarar ta haƙura da aikin,amma ta nace sai ta yi musamman da ta ga kuɗin aikin na ta da tsoka. Yaran matar kwata-kwata basu da mutunci ga rashin kunya abu kaɗan za su hauta da zagi suna ci mata mutunci,mahaifiyarsu kuma ba ta son ganin laifin ɗanta hakan ya sa ba ta kula su. Abin da ya ƙara tsorata ta ganin sun girme mata ƙaramar cikin su ita ce take tunanin za su zo tsara da juna. Hatta wankin su ita take yi musu don tsabar rashin mutunci harda pant da breziya suke ba ta wanki,amma ta yi haƙuri ta jure burinta ta samu abin da za su dinga ci. Sai dai rashin mutuncin da suke mata da ta fahimci ba me ƙarewa bane ta yi tsalle ta fara nuna musu sam ba za ta ɗauka ba. Hakan ya saka suka ƙara saka mata ƙahon zuƙa,domin zuciyar su tsabar hassada ce suna ƙyashin kyan da Allah ya yi mata musamman da suka ga sun ɓata jikinsu da mayukan bilicin. Abin da Hajiya Binta ta tsira ya sa Juwairiya ta ji aikin ya fita a ranta,saboda kullum ta zo sai ta tuhumeta da cewar ta yi mata sata.Hakan ya tinzira ta ta saka a ranta duk ranar da ta ƙara za ta bar mata aikin ta. Haka kuwa aka yi taƙi zuwa aikin bayan kwana biyu da barin aikin sai ga motar ƴan sanda da Hajiya Binta akan Juwairiya ta sace mata sarƙar gwal ɗin ta. Juwairiya ta shiga cikin tsananin tashin hankali ganin yadda ɗan sandan yake ƙoƙarin tasa ta zuwa ofis ɗinsu,hankalinta ya tashi matuƙa ya dinga kuka tana rantsuwar ba ta ɗauka ba.Tsananin tashin hankalin da Mama ta shiga ba'a magana duk da ta san halinta,amma sai ta shiga ruɗu ta din ga tamabayarta da in ta san inda yake ta fito mata da shi,hakan ya saka Juwairiya cikin tashin hankali ta dinga wani irin kuka gani take kamar Mama ba ta yadda da ita ba. Baba Sani ya sami abin da yake so don haka ya ƙara zuga Hajiya Binta kan ta tafi da ita ofishin ɗan sanda,burinsa ya cika dama tintuni yake addu'ar Allah ya sa haka ya faru. Mama na gani aka tafi da Juwairiya ta na wani irin kuka gani take kamar dukan ta zasu ta yi har sai ta amsa laifin da ba ta aikata ba.Ganin an tafi da ita Mama ta nufi hanyar shiga cikin gida ranta na wani irin suya,hango halin da Juwairiya take ciki da yadda take kuka ta na kiran sunan ta,sai kawai gani akai ta yanke jiki ta faɗi ƙasa. Hankalin Mariya ya tashi matuƙa wacce take zaune a ƙasa ta na kuka sosai,gani take kamar ita ta saka ta a cikin wannan hali saboda hanyar aikin da ta yi mata. Ita da mahaifiyar ta suka kama Mama suka shigar da ita gida,sai dai daga baya kan dole suka kwasheta zuwa asibiti ganin numfashinta na ɗaukewa gashi ta na aman jini! Baba Sani ya yi matuƙar jin daɗin faruwar lamarin duk da ba shi da shiri akan hakan sai dai ya na ganin yanzu ne burinsa zai cika akanta,don ya tabbata basu da wanda zai yi belin ta hakan zai ba shi damar ɗora mata sharaɗin zai yi belinta amma sai ta amince za ta yadda da buƙatarsa,don haka ma yaƙi zuwa ogishin da nufin sai sun yi mata dukan kawo wuƙa ta galabaita saboda ya san ta a kwai kafiya. Juwairiya na zaune a cikin cell ɗin ta ƙudundune kanta a cikin jikinta tun da suka kawota take kuka,tunanin halin da Mama take ciki yake damunta wani irin sauro da yake damunta da ihu da cizo,yasa take ta zubar jawaye ga yunwa dake ƙwaƙularta."Rabbi inni lima anzalta ilayya min khairin faƙir."Abin da bakinta yake faɗi kenan cikin tsananin tashin hankali. Tun da Hajiya Binta ta kawota ba ta ƙara zuwa ba sai washegari da safe lokacin ta matuƙar galabaita,bayan sun tuhumeta amma taƙi amsa laifinta dukan tsiya suka yi mata sannan aka maida ta. Da rana sai ga Baba Sani ya shigo ofishin ya na zare ido,gurinta yazo ya na kallonta." Kin ga abin da kika jawo ma kanki kosaboda shegen taurin ranki.'Yace ya na kallonta duk da ita ba shi take kallo ba saboda taƙi ta kalleshi wani irin tsanar sa take ji matuƙa. " Har yanzu kina da dama zan iya fitar dake amma sai kin amince za ki yadda da buƙatata."Yace da ita ya na kashe murya. Wani irin kallo ta watsa mishi " Allah ya yi min tsari da mugun nufin ka,da na amince gara na tabbata a gurin nan ko ya zamo shine ajalina." "Ok haka kika ce ko?To ai shikenan kuɗina ya huta tunna kin zaɓi rayuwar zuwa gidan mutane kina sata."Yace tare da watsa mata harara ya fice daga ofishin,kuka ta saka tare da cigaba da addu'ar ta ta na roƙon Allah ya kawo mata mafita. Kwanan ta uku a gurin ranar da Hajiya binta ta shigo ta buƙaci a saki Juwairiya taga sarƙarta,duk da cewa ƙazafi aka yi mata amma ko haƙuri basu bata ba.Ita dai da gudu ta dawo gida tasan yaran Hajiya Binta suka ƙulla mata wannan ƙullalliyar amma Allah ya fisu kuma addu'a takobin mumini. Ƙarin tashin hankali da ta zo Mama ba ta a gida Ibrahim ne yake sanar da ita ciwon Mama,wani kukan ta saka ta fita zuwa gidan su Mariya domin Mariya bata gaya mata Mama ba lafiya ba. Yadda ta ga Mama hankalinta ya tashi ƙwarai rungume Mama ta yi ta na kuka sosai.Mama ce ta buɗe ido jin muryar Juwairiya hankalinta ya ɗan kwanta ganin ta fito,don ba ta san halin da take ciki ba shi ya sa jikinta yake rikicewa. Likita ne ya shigo ya miƙa ma Mariya takadda yace."Gashi ki siyo wannan maganin ya kamata ku din ga kwantar mata da hankali, domin ta na da hawan jini ga ciwon zuciya, matuƙar ana ɓata mata rai to watarana zuciyar za ta buga!" Wani ƙarin tashin hankali Juwairiya ta shiga jin Mama na da waɗannan ciwuka rungumeta ta yi tana kuka."Mama kema mutuwa za kiyi?Don Allah karki mutu ki barni!Rayuwata za ta shiga cikin garari.Allah na gode maka ka bani ikon cin jarrabawa,amma karka ɗauke min mahaifiyata ka barni da azzalimi." Mariya ta kama ta ta rungume ta na buga bayanta hawaye ya na kwaranya a fuskarta tsananin tausayi ya cika mata zuciya ganin halin da take ciki."Kin ga ni Mama za ta barni ko!Wai me ya sa rayuwata tazo a baƙin jadawali ne?Nake kurɓar ruwan bakin ciki mafi zafi da ƙuna a zuciya."Tace cikin kuka." A'a Juwairiya karki faɗi haka!Kada ki kasa cinye jarrabawarki kin san Allah ya na jarraba mutum dai-dai imaninsa.Kar zuciya ta sa ki yi saɓo.Ina ji a jikina zaki ji daɗi a rayuwarki.Allah zai ba Mama lafiya."Ta gaya mata ta na shafa bayanta. Daƙyar Juwairiya ta daina kuka sai ajiyar zuciya hannun Mama ta kama ta riƙe ta na kallonta.Duk wani hidima na asibitin su Mariya da mahaifinta suka yi har kuka ta yi ta na gode musu domin Allah ne zai biya su. Bayan Mama ta samu sauƙi aka sallame su akan Mama za ta din ga zuwa ganin likita ta na karɓar magani,hankalin Juwairiya ya tashi ta na tunanin ina za ta din ga samun kuɗin da Mama za ta din ga zuwa ganin likita. Kan dole ta ƙara saka Mariya ta nema mata wani aikin don sana'ar da suke yi sun cinye tsugune kawai suke,da fari Mama taƙi yadda ta ƙara yin wani aikin amma daga ƙarshe dole ta haƙura ganin yunwa na so ta yi musu tabo. Kwasam ta haɗu da wani matashin saurayi mai suna Mas'ud Allah ya jarabci Juwairiya da son shi yaro ɗan gata da sanyin rai ga kyautatawa.Shigowarsa rayuwarsu ya sa sun samu canji sosai,duk da ya ga ita yar talaka ce amma be saka yaƙi sonta ba don da Allah yake sonta.Mas'ud ya na temaka musu sosai ya na aiki a Jami'ar Ahamdu Bello a library kuma ɗan samaru ne iyayen sa sun rasu sun bar mishi dukiya sosai,sannan ɗan kasuwa ne. Juwairiya ba ta taɓa jin ta na son mutum ba sai akan sa, gabaki ɗaya ta ji ta na son ta aure shi sai dai tasan hakan ba me yiyuwa bane,don babu yadda za'ai Baba Sani ya barta ta aure shi sai dai akan yadda take jin sonsa, za ta iya fito na fito a tsakanin su ko gidan me unguwa za ta iya kai shi. Haba tunna ya ga ya na zuwa gurinta ya saka tashin hankali yayin da shi ma Mas'ud ya kafe,ganin shi ma ɗan zamani ne sai yace bai tashi uren Juwairiya ba don bashi da kuɗi,nan take yace mishi kar ya damu ya amince zai yi mata komai. Ranar da Mas'ud ya kira Juwairiya ya gaya mata Baba Sani ya amince da auren su har ya ba shi izini ya turo magabatansa,kawai jin sa Juwairiya ta yi amma ba ta yadda da abin da yace mata ba.Ganin haka sai ya ƙyaleta kawai in ta ga zahiri ta yadda. Da misalin huɗu da kwata ɗan Baba Sani ya yi sallama ya shigo ya yi kiran Juwairiya taje shashin Baba Sani ya na kiranta a ɗakin matarsa. Gabanta ya faɗi amma sai ta saka hijabinta ta nufi ɗakin ganin a kwai baƙi ya sa ta ji a ranta a kwai abin da ke faruwa sai ta tsaya daga kofa ta na sallama."Yauwa Juwairiya shigo." Baba Sani ya faɗa da murya sanyaya a hankali ta yaye labulen ta shigo tare da tsaya daga nesa ta na kallon mutane jikinta ya bata dangin Mas'ud ne. Miƙo mata alkur'ani ya yi tare da canza fuska kalar tausayi yace." Dangin yaron nan Mas'ud suka zo neman auren ki,amma ni bazan cuce su ba sun yi min tambayar kina da tarbiya nace gara suji a bakin ki, don nasan ke ƴar mace ce sannan kin yi yawon aiki gidajen masu kuɗi,duk mazan gidan sun sanki a matsayin ƴa mace ga abin kunya na satar da kika yi,har aka kulle amma ga kur'ani ki rantse musu hakan be faru ba " Taɓ ji ta yi ƙasa ta gaza ɗaukarta ta ji wani irin hajijiya ya kamata." Inna lillahi wa inna ilaihir raju'un." Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Mu haɗu a shafi na goma sha ɗaya.Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. *FOLLOW, READ, COMMENT, SHARE* Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/G0J8rS0cxTtCCC38iwA3B9*SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *SHAFI NA GOMA SHA ƊAYA* Ganin taƙi karɓar kur'anin hawaye ya na zuba ƙuncinta ya yi murmushin mugunta,ya juyo ya na kallonsu sannan ya ƙara saka kuka har da hawaye share-share yace." Kun ga abin da na gaya muku ya zama gaskiya? A matsayina na ƙanin mahaifinta babu yadda ban yi da ita ba akan ta zama macen ƙwarai, amma taƙi jin maganata!" Juwairiya da take cikin wani yanayi na tashin hankali mara misaltuwa,ta rintse idanunta ta na jin wani irin ƙaton abu ya taso daga ƙirjinta ya tokare mata kirji ya kuma ƙi wucewa. Tana son ta ji saukar hawaye akan ƙuncinta ko ya rage mata raɗaɗin da zuciyarta take ciki.Kunnuwanta ba za ta iya jure jin kalamai da yake yi ba,ya na aibanta ta ita da mahaifiyarta. Ta muzanta iya muzanta da ƙyar ta yi nasarar jan jikinta ta fita zuwa shashin su,ta bar shi da bayin Allah da suka yi zuru suna kallon shi,yanayin su bai nuna sun yadda da maganar da yake musu ko akasin haka. Da gudu ta faɗa ɗakin tare da ƙanƙamre Mama ta na wani irin kuka." Mama duniya ta min zafi! Ina jin wani irin baƙin ciki a cikin zuciyata,wallahi nafi buƙatar mutuwa fiye da rayuwata! Wai me na yi wa Baba Sani ya tsane ni haka!Gara ya kashe ni da ɗacin da yake saka ma rayuwata." Mama ta rungumeta ta na shafa bayan ta don gani take kamar hauka ta yi." Lafiyar ki ɗaya kuwa?Ki yi shiru ki yi min bayanin yadda zan fahimta." Kusan minti goma ta na kuka ganin ta kasa magana sai ajiyar zuciya take,a ranta ta na jin baƙin cikin rabuwa da masoyinta,don ta san yadda ya aibata ta babu yadda za'ai su yadda ɗan su ya aureta. Da ƙyar Mama ta samu ta daina kukan sannan ta yi mata bayani.Ran Mama ya ɓace sosai ba ta san sanda ta ji jawaye ya na zuba a ƙuncin ta ba." Na gaji da halin da yake min! Zuciyata ta fara gajiya amma ba komai Allah ya fi shi da ikon Allah sai ya yi nadama,akan halin da yake miki." Sosai Juwairiya take kuka koda Mas'ud iyayensa suka koma gida suka sanar mishi a abin da ya faru,hankalinsa ya tashi matuƙa duk ƙoƙarinsa na ya fahimtar da su,amma sun ƙi ƙarshe wan mahaifinsa ya gyara zama yace." Ko da a ce yarinyar ba halinta bane,to ƙanin mahaifinta ba ya son ya baka ita ka kyale musu yarinya ga ƴan'uwan ka nan sai ka zaɓa a cikin su." Ransa ya ɓace matuƙa da ma ya ba shi izinin ya turo dangin sa saboda ya faɗa musu haka. Motarsa ya ɗauka sallama ya yi bai ko tsaya Mama ta amsa ba ya faɗa gidan,a yadda ta gan shi ta san ba shi cikin hayyacin sa. Da sauri Juwairiya ta ruga da gudu don ta saka hijabi ganin ya shigo." Mama ya Baba Sani zai yi haka? Juwairiya ya aiba ta a gaban iyayena. Wai me kuka yi mi shi ya tsane ku?"Ya faɗa yayin da idanunsa suka kawo ruwa. Cikin jimamin lamarin Mama ta share hawaye ta kalli Mas'ud da ya haɗa kansa da gwiya hawaye na zuba a fuskarsa,sai ya ba ta matuƙar tausayi ta san yadda yake son Juawairiya duk da iyayensa suna da shi amma a haka yake son ta. Ka yi haƙuri ka san matar mutum kabarin sa Allah be nufi Juwairiya matar ka bace,ka bi zaɓin iyayen ka ni na san duk korar mata masoya da yake in har lokacin ta ya yi bai isa ya hana ba." " Gaskiya Mama ba zan iya jure rashin Juwairiya ba zan je na sami Baba Sani duk abin da za'a yi sai dai ayi haka kawai ya din ga cusgunawa rayuwarku.Ya katse ta da faɗin hakan ransa a ɓace tare da miƙewa. " Zo Mas'ud don Allah karka je a yadda ranka yake a ɓace za'ayi ɓatatta,ka san halin shi ba shi da haƙuri ni ce na haifi Juwairiya ina me baka haƙuri ka haƙura da ita,shi kaɗai ne wanda take gani a matsayin na ta in har aka ɓata mishi wa za ta riƙe?Ka yi haƙuri Allah be nufa za ka aure ta ba." Kawai sai gani ta yi ya saka kuka ya na kallon Juwairiya da ita ma take kuka na tausayin halin da suke ciki." Juwairiya zuciyata za ta shiga cikin wani hali na rashin ki.Ki yi min addu'a Allah ya ba ni mace me irin halin ki,ni na san ke wace ce ko idanunki mutum ya kalla ya san kina da tarbiya da natsuwa.Ina sonki zan haƙura da auren ki saboda umurnin Mama." Fita ya yi har da gudun sa ya na sharen hawaye Juwairiya ta miƙe da gudu ta shige ɗaki tare da saka kuka.Sam ita ba ta ga dalilin da Mama za ta hana shi ba,ba ta san me Baba Sani yake nufi da ita ba shi ya sa take girmama shi,abin da ya sa taƙi ga ya mata ta san duk ranar fa ta gaya mata ƙudirin sa akan ta, ƙila zuciyarta za ta buga domin abin ya yi muni. Tun daga wannan ranar ba ta ƙara gani Mas'ud ba ko wayar da ya siya mata Mama ƙwacewa ta yi ta ije,don a yadda ta ga take-taken ta za ta iya kiran shi kuma shi ma haka.Tun ta na saka ran ze dawo har ta cire sai dai ta wahala kafin ta cire son shi a ran ta,sannan da ga baya taci gaba da al'amuranta. Mariya ta sami miji za ta yi aure anan kusa da layin su za ta yi auren don haka su Juwairiya su ne ƴan mata.Su Juwairiya an sha gayu da lalli an yi kyau sosa,ana ta hidimar biki don ba zama an saci ɗan ɓarawo. Zaune suke ana hirar ƴan mata Juwairiya ta kalli Mariya yadda ta sha kyau yace."Su amarsu kin ganki kuwa,dama komai munin amarya ranar bikinta sai ta haska." Fari ta yi musu ta na dariya tace." Ku zauna kuna rungume filo ni dai Allah ya hutashshe ni na shige daga ciki,ku tsaya kuna ruwan ida kwayi kwantai." Wani irin dundu Juwairiya ta duma mata ta nafaɗin." Ji min ƴar baƙin fata wato fatan da kike mana kenan tunna kin shige daga ciki ko? To in sha Allah muna bayan ki."Sauran ƴan matan suka taso mata ita dai Mariya dariya take musu,sannan tace." Ai ke Juwairiya Baba Sani ya hana ki aure da tuni kin haihu ma.Amma ba komai Allah ya na tare dake lokacin ki ne kawai ba yi ba." Shiru ta yi sai hawaye yayin da mutanen ɗakin suke ta ba ta baki. A haka suka sha bikin Mariya aka kaita ɗakin ganin Juwairiya za ta tafi ta kama ta tare da saka kuka.Sai kuma ta ba Juwairiya tausayi ta rungumeta ta na share mata hawaye. Mariya ta share hawaye tace." Maganar da mukai dake akan aikin nan kije Allah za kiji daɗi kin ga ni na yi aiki da su."Juwairiya tace." Ke ni raba ni da aikin nan don na yisu amma ban ji da daɗi ba." " Allah ki gwada wannan kin ga yanayin halin da kuke ciki,ga shan maganin Mama dole kina buƙatar kuɗi." " To zan shawarci Mama duk abin da tace sai na je."Da wannan Juwairiya ta tafi gida cike da kewar ƙawarta wacce ta temaka mata. Koda ta yi ma Mama magana shiru ta yi zuwa can tace." An ya zan barki kiyi aikin nan nifa tsoro nake yi kina ganin rashin mutuncin da Hajiya Binta ta yi miki,amma tuna kin ce Mariya tace ta na da mutunci sai ki je Allah ya tsare ki." Numfashi ta saki tace." To bari na gwada mu gani." Juwairiya ta fara aikin cikin jin daɗi ga karatu da take samu ake yi wa yaran lesson da islamiya matar ma ba ruwanta. Watan ta biyu a gidan ranar ta kammal aikin ta za ta tafi matar tace." Don Allah Juwairiya ki tsaya zamu je gidan biki ni da yarana,zuwa yamma zamu dawo sai ki tafi in kuma na yi dare zan kaiki a mota." Duk a ranta ba ta so ba amma sai ta amsa da." To." Ta koma ta zauna yayin da ita kuma ta shirya da yaranta suka fita. Tun da suka tafi har aka kira sallah ba ta dawo ba,ranta ya fara ɓaci don ba ta son ta yi dare kar Baba Sani ya dawo ya kuma ƙara mata wani sharrin. Jin ƙarar mota sai ta yi maza ta leƙa ta windo ta na tunanin ita ce,sai dai cikin takaici ta koma ta zauna ganin mijinta ne ya dawo. Ya shigo da sallama ya amsa ya na kallonta." Juwairiya har yanzu ba ki tafi ba?"Ya tambayeta ya na kallonta." Eh tunna ka dawo bari na tafi " " No ki kira ta nima ƙara fita zan yi." Don takaici ko amsa mishi ba ta yi ba to me ya dawo da shi koma wa ta yi ta zauna. Ya shiga cikin ɗakin sa mintina biyar ya fito sai kawai Juwairiya taga ya yi kanta gadan-gadan! Da sauri ta miƙe tare da saka salati dai-dai lokacin da ya fisgota ya haɗa ta da jikin sa da ƙarfi. Kasancewar shi namiji me jiki da ƙarfi ya yi nasarar kayar da ita ƙasa tare da yi mata rumfa,yayin da dabbe ya kaure ko kaɗan ba ta yi tsammanin ya na da wannan halin ba.Kuka ta saka ta na rokon shi,amma bai kula ta ba yaci gaba da ƙoƙarin ida nufin shi. " Inna lillahi Faruk!Me zan gani dama amanata kuke ci?"Ta furta cikin ƙaraji! yayin da ta yo kan juwairiya ta hau ta da bugu. Juwairiya ta yi kuka ta yi ihu ji take kamar numfashinta zai fita domin kanta ta hau ga ta da ƙiba,da ƙyar ya samu ya ɓamɓare Juwairiya ta samu ta gudu. Da ƙyar ta samu ta isa gida ta na kuka a ranar ta rantse ba za ta ƙara yin aiki ba,ko da mutuwa za su yi yadda ta shigo Mama ta tsorata. Bayan ta yi mata bayani tana kuka Mama sai da ta zubar mata da hawaye ganin halin da take ciki.A ƙalla sai da ta yi sati ta na jinyar jikinta don har sai da ta kwanta ciwo. Haka rayuwa take tafiya musu yau baƙi gobe tsummma ga ciwon Mama ya yi tsanani.Wani abin ƙarin tashin hankali Ibrahim da dama can ba lafiyayye bane,saboda sikila ne shi jikin sa da ya yi sauki amma a cikin kwana biyun nan jikin ya tashi. Ciwon shi sai yake son ya danne na Mama amma duk wanda ya ganta ya san ta na cikin tsananin ciwo.Ga kuma Baba Sani da ya sanar da Juwairiya ya yi mata miji wato Alhaji Tanimu. A ranar da Baba Sani ya gaya mata sumewa ƙau ta yi don ya tabbata Baba Sani ba ya ƙaunarta,don ita da ya aura mata shi gara ta zauna ba aure ko ace mutuwa ta yi. Waye a faɗin garin be san Alhaji Tanimu ba wanda ya mai da mace tamkar rigar sawan shi.Mutum ne mara addini ga shi kamar wani hor.Kusan duk shekara yake sakin mace ya ƙara aure bayan ya tabbatar sun sami ciki,don baya son haihuwa a tunanin ta shi kan shi be san iya yawan yaran shi ba,duk da wasu ya na ba ma iyayensu mata kyauta wasu kuma ya kai su almajiranci. Sannan an sha kama shi ƴara ƙanana ya na musu ya lalata musu rayuwa irin mutumin da Baba Sani yake son ya zama mijinta kenan.Ai Juwairiya ƙaramin hauka ta yi don gara yace ta shiga duniya. Shiko Alhaji Tanimu se ɗinkirama Baba Sani kuɗi yake yi hankalinsa kwance ganin zai mallaki wannnan zuƙeƙiyar,shi ya sa be damu ba ko sanda ya zo zance taƙi fitowa tallar ta fa aka kawo mishi har gida. Rayuwa a wannan karan tafi yi wa su Juwairiya illah ga aba abinci sannan dukkanin su ba lafiya,ga Baba Sani da yake ta shirye-shiryen bikin ta don har an kawo kayan sa rana watan gobe biki. Mama ta shiga tashin hankalin ciwonta ya ninku ga yunwa har takai sai su wuni ba su saka komai a bakin su ba. Juwairiya ta tsara ma kanta ta gudu amma in ta ga halin da su Mama suke ciki sai ta ji kamar ta kashe kanta ta huta,ita kanta ba lafiya take da shi ba don ta na ganin har tafi su Mama jigatuwa saboda zuciyarta da take ji kamar za ta fashe. Ganin yunwa zai kashe su sannan duk kuɗin da Baba Sani yake karɓa bai ta ba ba su koda na sabulu ba,ta je gurin Mariya ta ara mata naira dubu biyu ta fara jarin gyada.Da wannan suke samun abinci. ******* Zaune yake cikin damuwa sai kuma ya miƙe don a yau jin sa yake duk shawarar da amininsa ya ba shi zai iya ɗauka saboda halin da yake ciki.Makullin motar shi ya ɗauka ya nufi gidan A.k. Sai dai cikin rashin sa'a ba ya nan don haka bayan sun gaisa ya fice daga gidan ya samu wani guri mara hayaniya ya tsaya,tare da ciro waya ya kira A.k. Ba'a fi minti goma ba sai ga A.k akan mashin ya sauka ya buɗe gaban motar ya shiga ya na share zufa."Am sorry aboki motar da ka siya min na kai ta service ba'a gama ba kan dole na baro motar na hawo mashin.Are you under the weather?"Ya tambayi aminnin nasa ganin yanayin sa. Yace ya na kallonsa bai tanka ba illa ajiyar zuciya da ya yi ya kauda kansa gefe guda,ganin yadda aminin na sa yake ya san yauma ba lafiya to ko dame yazo oho don ya san dai zancen. Suka ɗan yi shiru ba tare sun ce uffan ba na tsawon lokaci sannan A.k ya katse shirun da cewa." Lafiya na gan ka wani iri in ce ba mutuniyar bace ta haɗa maka zafi." "Akan maganar da na nemi shawarar ka yau ma na ƙara bijiro maka da ita.I really need your advise pleese help me out."A.k ya kalle shi yadda idanunsa suka kaɗa suk yi ja ga mamakin sa sai ya ga hawaye ya na sauka da ga ƙuncinsa. Ya kama hannunsa ya haɗa da nasa ya riƙe sosai ya na kallonsa ya ci ga ba da cewa."I know my wife she is a woman of raging jealousy.Bazan iya haɗa ta da wata mace ba kuma ba yan haka na yi mata alƙawari,amma ina jin zafin rashin yaro da ba ni da shi wanda hakan in ban ɗauki mataki ba zai iya taɓa lafiya ta,domin a yanzu ya kai matsayin da ba na iya bacci. Tun da ya fara magana A.m ya yi shiru ya na kallon sa a ransa tunani yake to ko amininasa ya ci kai ne ko kuma rashin haihuwar ya taɓa tunanin sa, kamar yadda yace shi dai ya san ta aure ake samun haihuwa ya ba, shi shawara yaƙi bi saboda wani alƙawari na shi na banza to amma bari ya ji me yake tafe da shi. Ganin ya yi shiru ya dafa kafaɗarsa ya na cewa."Try to be patient ka san zuriya kake buƙata kuma dole a aure za ka same shi,ba zaka so ka sami ɗanka ta zina ba wanda na san ba halinka bane,amma ni banga dalilin da zai sa kaƙi ƙara aure ba bai ita ta ɓata mahaifinta da kanta ba?"Ya ɗan faɗa da zafi kuma da tsigar tambaya. " Haka ne." Ya ba shi amsa sannan ya ci gaba da cewa." Duk akai na ne ta samu wannan matsalar gaskiya i can't make up my mind ko zan iya cin amanarta." Ƙarin takaici maganganunsa suka ƙara ba shi gani yake ba shi da tsayuwa a gidan sa,amma shi bai ga yadda matar shi zai ta da hankalin shi ba,don kawai zai ƙara aure kuma duk laifin tane. Ya kaɗa kafaɗunsa yace."It is up to you ni dai na gama baka shawara."Yace amma sai kuma ya ga hankalin aminin nasa ba shi a gurinsa wataƙila ma be san me yace ba. A hankali ya bi gurin da yake kallo shima Juwairiya ce da tiren gyaɗa a kanta da ga ganinta ka san ta na cikin wani hali, kusan ma ta na tafe ta na share hawaye saboda har Alhaji Tanimu ya kawo kayan auren ta na jin gara ta haƙura ta aure shi,wataƙila shi Allah ya tsara ya zamo mijinta ta san bawa ba ya wuce abin da Allah ya tsara mata,sai dai yanayin halin da Mama da Ibrahim suke ciki ya sa ta zagaya wa da gyaɗar da yau ba ciniki ta haɗa da kuɗin da Mariya ta ba ta ta kai su asibiti. A.m da ya zuba mata ido ya na kallonta bai taɓa ganin mace me sanyi da wani irin shauki a tare da ita ba sau,haka kawai ya ji ta kwanta mishi a rai ba wai son ya na son ta ba irin zai iya magana da ita har ya ba ta lokaci su yi wasa da dariya,kuma ya nemi shawarar ta kuma zai iya yin komai don ta yi farin ciki,zai iya cewa yau ne rana ta farko da ya ga wata mace bayan Zainab har ya na jin zai iya mata magana. Wato in ya fahimci zuciyar shi ƙawa yake son ya mai da ita ko ƙanwa." To amma duk tsanar talaka da na yi sai ace na yi ƙawa da ƴar talaka kuma ƙasƙantacciya ƴar talla kai an ya da wuya.". Yace a zuciyar a cikin zuciyarsa ya na me ƙoƙarin kauda idanun sa daga gareta don jin hakan bai dace ba ace duk matsayin shi.Sai-dai idanunsa sun kasa ɗauke kan su daga kallonta ya na ƙara zaƙulo kyawunta. Ta na tafe cike da damuwa har tazo ta gaban su za ta wuce." Me gyaɗa." Kalmar da bakinsa ya furta ba tare da ya ba shi umurni ko tunanin hakan ba. Juwairiya ta ji wani irin sansanyar murya mai kama da sarewa ta kira ta ta na son ta juya amma sai ta daƙile kanta da juyawar,don ƙila in ta ga mamallakin wannan muryar ba ta san halin da za ta shiga ba sai kawai ta ci gaba da tafiya yayin da aranta take addu'ar Allah ya sa karya ƙara kiranta, don ta san in ya ƙara kiran ta ba za ta iya tursasa zuciyar ta da ƙin juyawa ba. A.m ransa ya matuƙar ɓaci ƙazama da ita ta na talaka zai kira ta taƙi waigowa ya so yaje ya yi watsi da kayan tallar,ya ga uban wa take taƙama da shi taƙi amsa kiransa amma da ya yi tunanin ko kurma ce sai ƙara kiran ta a karo na biyu. Cak! ta tsaya amma ba ta wai go ba ta na addu'a a cikin ranta yayin da idanuwanta suka zaƙu da suga wannan mamallakin muryar.A hankali ta tako ta iso gun motar su ta tsaya ta kasa magana kuma ta kasa ɗaga ido ta kalle shi. Kusan minti goma ta na tsaye ba tare da ya kalleta ba me ya gani oho ganin ita ma ba ta da ninyar ta yi mishi magana kuma ba ta tafi ba A.k dai ya na zaune ya na kallon ikon Allah. A.m ya buɗe motar da nufin ya yi mata wulaƙanci dai-dai lokacin da idanuwan su suka tsarƙe da na juna. Kyansa yanayin jikinsa idanuwansa da yadda yake kallonta suka ruɗa ta ta yi kamar za ta faɗi, amma sai ta dafa jikin motar sa ta na kallon shi cikin wani irin shauki,lokaci guda ta ji abu me kama da guduma ya sauka akanta! Yayin da wani irin shokin na soyaryarsa suka dinga ɗana mata son shi a cikin ranta,har ta ji za ta iya mutuwa in ba ta same shi ba. Idanun su da suka tsarƙe da juna sai ya tsinci kansa da kasa mata rashin mutuncin da ya yi ninya a yatsine yace."Nawa-nawa gyaɗar." Ta zuba mishi idanunta sai kuma ta janye ta lumshe su tare da kauda ganin ta gare shi ahankali da sanyaryar murya tace.Hamsin gwagwani ɗaya." Ya ɗan ƙura mata ido haka kawai kyawunta da muryarta yake ruɗan shi a kanta."Duka buhun nake so nawa."Yace tare da barin kallonta lokacin da ta ɗora idanunta akan sa. Zare ido ta yi " kwai yawa fa kusan na dubu uku da ɗari biyar ne.Tace mishi hakan sai ya burge shi ya tsinci kansa da yin murmushi. "Ok bari in ci Allah ya sa da daɗi."Da sauri ta saka hannunta da baya rabo da lalli ta miƙa mishi ta na faɗin." A kwai daɗi kaci kaji." Yabi hannunta da kallo ya karɓi gyaɗar ya ɓare tare da taunawa,lumshe idanunsa ya yi yace da ita."Gaskiya a kwai daɗi zuba min a leda sauran kiyi sadaka da shi." Da sauri ta zuba mishi sannan ta kalli gefen A k da ya yi mutuwar zaune saboda tun tarihin rayuwarsa da A.m yau ce rana ta farko da ya siyi abu a gurin masu talla,sai ya yi lakato ya na kallon A.m da ke cin gyaɗa har ya na faɗin ta ƙara mishi ya yi daɗi. " Yayana kai fa ba ya cine."Ta kalle shi sai kuma ta mai da maganar da tsigar tambaya ta na kallon A.m,kaɗa kafaɗunsa ya yi ya na kallon shi ya ma manta da shi yace."Ba ya ci." Juwairiya tace " Ka tambaye shi ne?"Sai kuma ta kalli A.k tace."Wai haka Yayana?" "Yes Am ok."Yace da ita ya na kallonta. Zuba gyaɗar ta yi ta miƙa mishi ta na faɗin."Kaci a kwai daɗi."Ya ƙarɓa tare da faɗin."Thanks sis." A.m ya zaro kuɗi da yawa ya miƙa mata. Gashi sis ki cire kuɗin ki sauran ki ƙara jari."Zare kuɗin ta ta yi tace."Siyan da ka yi na gode." Hakan sa ya yi matuƙar birge shi ya na ta kallonta har ta yi nisa ya leƙo ta cikin murfin motar yace." Manene sunan ki." Ya ɗan ɗaga muryarsa yadda za ta ji don ta yi nisa,waigowa ta yi ta kalle shi tare da sakar masa murmushi ta tabbata wannan kyakykywa gayen ya yi mata sata mafi girman abu a rayuwarta,wanda ta san ba zai dawo mata da shi ba kawai za ta ci gaba da renon giɓin rashin abin da ya ɗauke mata har iya tsawon rayuwarta! " Sunana Juwairiya Ahmad."Tace tare da ƙoƙarin ɓullewa a ranta ba ta son ta ƙara haɗuwa da shi don ta san babban goro sai magogin ƙarfe. A hankali ya kwantar da kan shi akan jikin kujerar da ya saukar da kansa ya na murmushi ya furta.Juwairaaah! Da wata irin murya ya ja sunan ya yi mishi wasali sosai." Ta na da kyau haka kawai sai na ji ta burge ni." Ba tare da wani shakku ba A m yace."Bayan kyau a kwai hankali da natsuwa .Rayuwarta a kwai tarin tausayi ka aureta kawai ta haifa maka yara. Da sauri A.m ya buɗe idonsa ya ɗora akansa wani irin ɓacin rai da takaici ta ya ya zai haɗa shi da ita ƴar talaka me talla ita yake nufin ta haifa mi shi yara!Ina imposible wasa yake yi. Ya buɗe baki zai yi magana sai kuma ya figi motar tamkar zai zubar da su,A.k dai bai ce komai ba koma kashe su zai yi, ya yi amma iyakan shawarar da zai iya ba shi kenan kuma in dai bai ɗauka ba to ba zai ƙara kula shi akan damuwar sa. Ƙofar gidansa ya ije shi ba tare da yace komai ba bayan ya fito daga motar ya leƙa ta tagar motar yace.Allah ya bamu alkhairi ka yi tunani shawarar da aka yanke ina sauraranka." Ba tare da ya tanka mishi ba ya ja motar a guje dariya ya saki tare da girgiza kan shi ya shige gidan sa. A.m da ya koma gida sai yaji wani tashin hankali game da maganar da ya yi mishi,amma ya kasa amincewa wanka ya yi ya kwanta don baya so ya yi tunani akan maganar,sai dai bayan baccin ya kwashe shi sai ya yi mafarkin ga Juwairiya ta na kuka ta miƙo mishi yara guda biyu shi kuma ya na cikin ƙaton rami ya fito da ninyar ya ƙarɓa sai ta ɓace ta na wani irin ihu,ihun da ya fargar da shi ya miƙe a zabur! Ya na salati don har yanzu bai daina jin sautin kukan a cikin kunninsa ba. " Ita za ta haifa min yara amafarkin da na gani kenan amma a kwai matsala.Tabbas matsala babba don ko ni auren ta zan yi cikin sirri ba tare da sanin kowa ba wato auren wucin gadi,na ƴanta mata rayuwa na ba ta jin daɗi amma mu yi aure na tsawon shekara ɗaya tazo a matsayin me aikin gidana bayan ta samu ciki, na ɗauke ta na kai ta wani gurin in ta haihu na biyata na karbi yarona na kawoma matata masoyiya Zainab." Tofa masu karatu kun ji A.m abin da yake so. *Hakan zai yiwu? *Ta ya ya A.k zai karɓi lamarin shin zai bashi goyan baya kuwa? *Wani irin aure yake son yi? *Shin ya zai yi da Baba Sani da ba shi da buri sai dai rayuwar Juwairiya ta wulaƙanta,zai amince mutum me daraja da matsayi ya aureta? *In ma ya amince taya za'ai Juwairiya ta yi rayuwa a gidansa a ɓoye a matsayin matarsa amma kuma azahiri ƴar aiki? *Ta ya ya za ayi auren sirri ba tare da sanin Mama ba? Ku dai biyo ni a shafi na gaba"SAKACINA KO HALIN MAZA" NAGA RUWAN COMMENT IN ANA SO NA CI GABA.😘😘😘😘😉😉TAKU JAMILA LAWAL ZANGO💔💔💔💔❤❤ Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/G0J8rS0cxTtCCC38iwA3B9 *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *SHAFI NA GOMA SHA BIYU* Juwairiya ta na ɓacewa ganin sa ta tsaya ta tsuguna tare da sakin wani gigitaccen kuka sosai wanda ba ta san dalilin yin hakan ba,sai bayan tasha kuka sosai zuciyarta ta fara jera mata tarin tambayoyi." Me ya sa nake kuka ga mutumim da na san ba zan taɓa samun shi a cikin rayuwata,na sa ni cewar dariya ba so ba ne.! Maganar da ya yi min ba ya nufin zai iya sona a cikin ransa,sannan na tabbata ya yi aure har ma da iyali saboda kamalar shi ta nuna na cikakken mutum me iyali." Ta tallabe fuskarta da hannunta wani sashi na gefen zuciyarta,ya na ƙara jaddada mata da cewar ko da ya nuna ya na sonta Baba Sani ba zai taɓa ba shi auren ta ba,mutane wanda ba su kai shi matsayi ba sun nemi auren ta amma ya hana bare shi da ga ganinsa kasan ya jiƙu da nera,da duk wani ababen more rayuwa. Sai ta share hawayenta tare da ɗaukar tiren jiri na jiri ya na iban ta ta na ji kamar ta haɗiye zuciya ta mutu in ta tuna wannan tsohon ze mallaki jikinta. Gizo-gizon hoton sa da murmushin da ya yi mata lokacin da ya tabbayi sunan ta idanuwanta suke hasko mata,ta rintse idanunta da ƙarfi ta na son su daƙile mata ganin ta ga mutumim da take jin kamar ya saka ta a aljihun sa su yi ta yawo. Bayan ta dawo gida ta na zaune jingine da bangon ɗakin su idanunta a sama ta na aikin tunanin da ta ɗaura ɗamara da shi tun lokacin da idanunta suka yi tozali da shi. Mama dake tsaye ta na karantar yanayin ta tun da ta kawo mata kuɗi tace wani mutum ya siye,ta zauna a gurin ta na kallon sama sai hakan ya tabbatar mata da a kwai lauje cikin naɗi. " Juwairiya lafiyar ki kuwa."Mama ta kalleta lokacin da ta dafa kafaɗarta,amma ba ta ji ta ba har sai da ta maimaita sau biyar ba ta ji ba sai ta juyo da fuskarta. Ga mamakin ta sai ta ga ta juyo tare da saka hannunta ta rungumeta ta fashe da kuka,hankalin Mama ya ƙara tashi dama tun safe take jin wani irin zafi-zafi a ƙirjin tare da sauke wani irin ajiyar zuciya mai kama da zai tafi da rayuwarta. Yaƙe me kama da murmushi ta yi tace." Akan maganar auren ki ko Juwairiya ya za mu yi da ƙaddarar ubangiji,komai kika ga ya faru Allah ne ya ƙaddara." Ta sauke irin wannan ajiyar zuciyar da ke barazanar ɗauke numfashin ta sai kuma hawaye suka fara turereniya a kan ƙuncinta. Ta buɗe baki da nufin ta yi magana amma ta kasa sai ta rufe bakin tare da sakin kuka wanda ya fi na Juwairiya sauti. Hankalin Juawairiya ya tashi matuƙa!Tun da lamarin ke faruwa Mama ita take kwantar mata da hankali amma yau haƙurin ta ya gaza. " Don Allah ki de na kuka wallahi na haƙura ba zan ƙara nuna damuwata ba,in dai akan auren nan ne kin san yanayin ciwon ki. Ta faɗa ta na share hawayen ta don ta na tsoron kar ciwon Mama ya tashi,ga shi aure za ta yi babu wanda zai kula da ita sai Ibrahim wanda ba cikakkiyar lafiya gare shi ba,don har ɗingishi yake yi kafar sa ɗaya ba lafiya. Mama ta miƙe ba tare da tace komai ba ta fice daga ɗakin ta na jin matuƙar tausayin ta kasancewar ba ta sami bango abin jingina ba.Tanimu ba mutumim aure ba ne ita kuma mace ta na zama zinariya ce in har ta samu miji na gari,ta fauwala ma Allah lamuran sa saboda Allah na iya can za lamuran sa iya addu'ar da take yi wa Juwairiya rayuwar ta ba za ta taɓe ba. Buta ta ɗauka ta shiga bayi ta tsarkake kanta ta fara kai kukan ta ga Allah Sarki gwani gagara misali! Ganin haka Juwairiya ta miƙe tare da sakin kuka ta toshe bakin ta bayi ta shige ta saki bakinta ta na kuka mai tsuma zuciyar me sauraro." Me ya sa ka shigo rayuwata a lokacin da nake jin duniya ba ta da muradina a cikin ta gyambo biyu kake so na yi ta jinya a cikin rayuwata! Na rashin ka da auren mutumim da na tsana a rayuwata!"Kuka sosai ta yi sannan ta fito ta yi alwala tabi sahun Mama. Wunin ranar ta yi shi ne a suku-suku tamkar wacce ba ta da lakka a jikinta,ta kasa cire shi a ranta.Da daddare ta na kwance sai mutsu-mutsu take ta na jin Mama na ajiyar zuciya ƙut!Ƙut! Wanda hankalinta ya tashi kwarai ba ta rintsa ba sai kusan asuba ta ji ɓarawo bacci ya kwashe ta. Da asuba bayan ta yi sallah ta na karatun alkur'ani ta yi mamakin da Mama ba ta tashi ta yi sallah ba,sai ta miƙe dai-dai lokacin da Ibrahim ya shigo ya dawo daga masallacin dake kusa da su. " Mama ki tashi ki yi sallah." Amma shiru ba ta amsa mata ba da sauri ta ƙara jijjigata sai dai ta ga Mama idanunta sun ƙanƙance jikinta ya saki da ƙyar take janyo numfashin dake barazanar kuɓucewa gangar jikin ta. " A'a Mama don Allah karki mutu ki bar mu kin ji Mama!"Kuka take sosai ta na girgiza Mama da ta ƙasa buɗe idanun ta saboda nauyin da sukai mata,a jikin ta ta na jin wani irin zafi me kama da rushi ya na zagaye ilahirin jikinta don har huci yake ya na fitar da tiriri me zafin gaske! Jin ihun Juwairiya ya sa matar Baba Sani ta shigo wanda hankalinta ya tashi matuƙa ta na tausayin su sosai,sai dai ta san halin tijararren mijinta zai iya shuka mata rashin mutunci koma ya sake ta bare yanzu da yake mata rashin mutunci zai ƙara aure. Kuɗi ta miƙa ma Juwairiya ta saka yaron ta ya nemo me keke napep aka saka Mama a ciki zuwa asibiti. ********* Bayan A.m ya fita gidan iyayen shi ya nufa don ya ɗan kwana biyu be leƙa su ba,ya na shiga ya ga ana ta murnar matar ƙaninsa ta haifi ƴan biyu gidan ya cika sai murna ake,saboda daga asibiti nan aka wuto da ita. Jikinsa ya yi sanyi ya irga yaransa yanzu huɗu kenan sai kawai ya ji zuciyar sa na bugawa,bai ƙara shiga cikin tashin hankali ba sai da aka ɗora masa yaran masu kama da larabawa a kan cinyarsa. Gidan gabaki ɗaya sun ruɗe suna ta ɗaukar yaran waya kamar zasu ƙarar da jikin su saboda ɗaukar hoton,har sai da ya tsawatar da su bari sannan suka dena suna ta kallon yaran. Hawaye yaji suna bin ƙuncinsa ya kasa ɗaukar yaran ya na kallon su gunun sha'awa kamar ya kwace yace ƙwansa ne shine ya haife su. Ganin ya na hawaye sai dukannin su jikin su ya yi sanyi suka koma suna rarrashin sa,amma ya kasa tsaida hawayen da ke kwaranya kamar an buɗe famfo. " Zainab an ya kin yi wa rayuta adalci kuwa?" Ya tamabayi kansa dai-dai lokacin da mahaifiyar sa ta dafa kafaɗun sa ta na rarrashin sa.Bayan ya sawa yaran albarka ya fice daga gidan kai tsaye kampanin su ya wuce tare da jiran A k su haɗu da shi farfajiyar kamfanin. A.k ya sanar mishi ya na kampanin in ya iso ya kira shi kawai,amma sai A.m ya nuna ya fito kawai ya jira shi saboda yanayin da yake ba zai iya ƙara kiran waya ba. Ya na isowa ya same shi tsaye da waya a hannun sa da alama waya yake sai kuma ganin shi ya sa ya kashe wayar,tare da maida ta cikin gabar rigar sa ya ƙarasa gurin da A.m ya yi parking ɗin motar sa. Ina ga muje farfajiyar da Daddy yake hutawa abin zai fi ko a bisa mu yi magana don nima ina da maganar da nake son mu tautauna akai."A.k yace da shi bayan ya nufi hanyar gurin ba tare da ya ji amsar da ya ba shi ba. Ganin haka sai shi ma ya bi bayan sa ba tare da yace komai ba.Bayan sun zauna shirun na su na ƴan mintoci ya biyo baya wanda sai da nabi dindigi na gano dalilin shirun na su a duk lokacin da suka haɗu kafin su fara maganar da ta kawo su,wanda suna yi ne don su sami natsuwa tare da nazarin maganar da zasu tautauna a tsakanin su. A.k ya buɗe baki da nufin zai fara magana amma sai A.m ya hana shi ta hanyar taran numfashin sa tare da gyara zama yace."Abokina ka fara bani dama na yi magana domin na samo mafita a kan damuwata,na yi tunani sosai kan maganar da muka yi da kai na Juwairaah.Tabbas yarinyar ta kwanta min a rai kuma na yaba da hankalin ta amma saboda alƙawarin da na yi wa Zainab,kuma ita kaɗai nake son takasance matata zan auri Juwairaah mu yi auren kwangila da ita shekara ɗaya,kamar yadda ka bani labarin ƙanin mahaifinta ni kuma zan siya shi da ruwan kuɗi ya fasa auren da zai yi mata da wannan tsohon." Ya numfasa ya na kallon sa ko zai fahimci yadda ya karɓi zancen,amma sa ya ga ya na mishi kallo kamar irin amma ka zare ko! Bai damu ba ya ƙaɗa kansa yaci gaba da cewa."Tunna ka gaya min ta yawon aikatau sai mu ɗauketa akan za ta koya wa matata girki da kula na tsawon shekara guda,kaga a wannan lakacin in ta samu ciki zan ɗauke ta daga gidan na kai ta wani guri,na san yadda zan tsara Zainab ta amince ta karɓi ɗan burina na ga ɗana kafin na mutu. "Amma baka da hankali ko na ɗauka alkhairi ya sa ka kira ni nan,ashe ka je ka bugu ne ka zo ka ɓata min lokaci."A.k yace tare da miƙewa yayin kamar zai fice daga gurin bayan ya miƙe sai ya dawo ya ƙara zama ya na kallon sa yace." Aikin banza kawai na ɗauka auren ta za ka yi na ɓata lokaci na gurin sanin tarihin rayuwarta! Abin takaici sai ga shi kazo ka na min maganar banza. Shin baka da zuciya ne a ƙirjinka har ka kasa tausayawa rayuwarta na halin ƙuncin rayuwar da take ciki? Ko ƙyamar talaka da kake yi ne ya sa kake son ka cutar da zuciyar ta. Ya ƙara miƙewa don ji yake kamar ze rufe shi da duka ya na jin zai iya gaya mishi duk maganar da ta zo bakinsa,saboda tun jiya da ya ji halin da take ciki Allah ya saka mata tsananin tausayinta a ranta. A.m hannun sa ya kama shi ma sai hawaye ya na faɗin." A tsakanina da ita waye yafi kusanci da kai ina cikin wani hali bani da nufin na cutar da Juwairaah wallahi tsananin son ganin ɗana ya sa nake jin zan iya komai.In har ka amince ka bani goyan baya mukai auren sirri da ita na yi maka alƙawari rayuwar Juwairaah sai ya canza daga talauci zuwa mafi ƙololuwar jin daɗi na rayuwa.Kuma ko banza aurena zai zamo katanga a tsakanin da tsohon mutumim nan,ƙanin mahaifinta da yake takurawa rayuwarta duk haɗuwana da ita zai saka ya dena saka mata ƙahon zuƙa." " Rufe min baki nace! Shashasha!Kawai ka san yadda zuciyar mace take da rauni kan soyayya.Kai fa namiji ne da ko wace mace za ta yi mafarkin samu,ka na tunanin in ka auri Juwairiya za ta iya haƙuri da rashin ka ne,a kan maganar soyayya kuɗi ba ya tasiri mace za ta iya baka rayuwarta kuma ta sadaukar da rayuwarta duka gabaki ɗaya in har ta na sonka,ba za ta taɓa damuwa da halin rashi ko baƙin cikin da za ka saka taɓa." Ya saukar da zazzafan huci ya ja numfashi sannan ya kalle shi da idanunsa da suka kaɗa suka yi jajur." Ina tunanin yaudarar Zainab kake da kake faɗin ka na sonta don da ka san yadda soyayya take tasiri da baka buƙaci auren Juwairiya na wucin gadi ba, don na tabbata kafin ku rabu sai Juwairiya ta faɗa kogin son ka koda yankan namar jikinta kake yi ɗanye,bare kuma za ka raba ta da abu mafi girma a rayuwarta kawai za ka rabu da gangar jikinta ne amma zuciyar da da ruhinta duk za ka raba ta da shi.Ba ka san yadda uwa take zama akan yaron ta ba,saboda ba ka haihu ba shi ya sa baka san soyayyar da Allah ya saka tsakanin ɗa da mahaifi b..." "Ya ishe ka! Rufe min baki nace banza mara mutunci! Har ni za ka yi ma gorin haihuwa na rantse tunna ka yi min gori sai na aureta kuma na raba ta da yaran na kai ma matata,na yi alƙawarin sai kaga ƙwaina a duniya." Ya matso tare da taɓa ƙirjin shi da ɗan yatsa yace." Saboda nace zan aure ta ka wani tada jijiyar wuya'duk na gane kauce-kaucen ka don ta na talaka ba ka son na aureta.To siyan ta zan yi da kuɗina kai ma ka san in ka yi tunanin zan aure ta na yi rayuwar har abada ka yaudari kan ka, me zan yi da ƴar talaka wanda basu da komai sai tsiya,kuma ka sani ko ban aure ta ba ina da kuɗin da inna ce zan auri ƴan mata waɗanda suka fi ta kyawu da ɗaukaka zan iya auren goma in ana yi." "To kaje ka auri ƴan matan duniya duka in kana son ɗan ƙaruna amma ba zan haɗa hannu da kai na saka rayuwar ta a cikin matsala." Ya faɗa tare da ƙoƙarin barin gurin rigar sa ya jawo ya juyo da shi gaban sa ." Ko ka sa min hannu ko ka ƙi sai na aure ta ita kaɗai ce na ji zan iya rayuwar aure da ita ba yan masoyiyata Zainab,don haka in dai kuɗi na aiki ka ba ni sati biyu za ka gan ta a gidana kuma a matsayin me aikin matata za ta shigo gidan." Ran sa ya ƙara ɓaci da ya tuna ya sha zuwa gidan ya ga Zainab ta daki me aiki,hakan ya na nufin in ranta ya ɓace za ta dake ta kenan aiko in dai haka ne a kwai zalinci. " Ai kin banza kawai sai dai in zaka ɗauki numfashina ma'ana ba ni a raye,amma ni da kai na zan tona asirin ka kuma na ga uban da zai karɓar maka auren tunna ba ƴar tsana ba ce,sai da waliyin ka za'a baka.Yace a fusace. " Ok haka kace ko zan nuna maka true color ɗina dama duk abin da aka haɗa da jaki sai ya ci kara,ka haɗa hulɗa da talaka matsiyaci da be da komai sai tsiya na yi dana sanin tarayyata da kai don bi amfana min komai ba,duk halaccin dana yi maka ni da dangina muka ƴanta rayuwarka shi ne zaka saka min da haka!" To fa ran A.k ya ɓace matuƙa kawai sai hawaye ya kalli A.m da yake ta ga ya mishi maganganu mara sa daɗi da baƙan ta rai,don shi in dai ran shi ya ɓace bai iya magana ba." " A she haka kake dama na daɗe ina tunanin wannan ranar za ta zo,saboda a gaba na kasha wulaƙanta talawa irin na na gode in sha Allahu daga yau ba ni bakai,ba zan ƙara hulɗa da kai ba kuma na bar muku aikin ku ka sana ni ba jahili ba ne ko yau na yanke alaƙa da ku sai kun yi jimamin rashina."Yace ya na me tabbatar da hakan a ran sa. Kai ɗin me kai ɗin banza me kake da shi kaje a kwai waɗanda suka fika ilmi da zasu buƙaci gurbin ka.". Lamarin fa ya yi tsamari gabaki ɗayan su kowa ya hau dokin zuciya duk da zo mu saɓa zo mu zauna,amma ba su taɓa samun saɓani irin na yau ba. Ko da A.k ya nufi hanyar fita A.m jawo kwalar rigar sa ya yi tare da dawo da shi ya hau shi,da dambe don gani yake ya ma rai na mishi wayo ya na karkashin sa,sai ya manta abokantakar su ya dawo kan matsayi. Aiko A.k a zuciye ya kai mishi mari ya kauce shi ma ya kai mishi suka rikice da dambe kici-kici.Me ba ma fulawa ruwa ya zo ya gan su da gudu ya ruga ya yi kiran mutane,su raba don ba zai yi gigin shiga tsakiyar su ba su bar shi da jinya yadda suke ji da karfi. Da ƙyar mutane suka raba su sai huci suke tamkar wasu zakuna.Faruwar lamarin sai ya yi matuƙar bawa mutane mamaki,tuna yadda suka shaƙu kamar wasu ƴan'uwa suna ta jimamin lamarin me ya haɗu ko ma dai mene ne lamarin me girma ne,amma da suka tuna tsakanin harshe da haƙori ana saɓawa sai suka ba su haƙuri tare da ɗauko musu ruwan sanyi,domin ya sanyaya zuƙatan su saboda sheɗan da ya yi nasara haddasa fitina a tsakani aminnan ko nace ƴan'uwa. A.k da ran sa ya ɓace ko jiran wanda ya nufi zuwa cikin kampanin ya ɗauko musu ruwa bai yi ba ya fice ya na jin a ran sa ya tafi na har abada. Ko da a ka ɓalle murfin gorar ruwa aka zuba mishi ruwan wurgi ya yi da kofin tangaras ɗin ya nufi motar sa,ya shige tare da figar ta kamar zai tashi sama. Ko da ya iso kofar gidan ya shiga sakin hon ba ƙauƙautawa.Allah Sarki Audi direba dake cikin bayi da cikin sa ya murɗa ya shiga kenan ya ji hon wanda ya tabbata matar gidan ne me shegen yawon tsiya,amma da ya tuna ya ga ta fito ɗazu sai ya yi maza ya fito ba tare da ya gama abin da yake ba sai dai hon ɗin da ake saki na rashin hankali. Ya na wangale get ɗin sai yaga megidan sa ne yake ta zuba wannan hon,hankalin sa ya tashi kwarai don a tunanin sa ba lafiya ba. Ya na shiga ko parking bai yi ba ya fito ya ƙarasa gurin Audi direba dake mishi sannu ya na son ya kulle get ɗin ya ruga bayi,don har lokacin cikin sa bai dai na murɗawa ba. Mari ya zabga mishi." Kai wane irin banza ne matsiyaci kawai gidan ubanka ne da zan ɗauki lokaci ina hon baka amsa min ba? Ko kuɗin da nake biyan ka da shi haƙo su nake!" "Allah ya baka haƙuri ina bayi ne cikina ya lalace." Bai saurare shi ba ya shige cikin gidan falo ya shiga gibbiyar ta na kwance a doguwar kujera me cin mutum uku da remote a hannunta ta na kallo. Ba tare da kallon in da take ba ya shige cikin ɗakinsa ruwa me sanyi ya dinga kwankwaɗa har sai da ya cika cikin sa,amma bai ji zuciyar sa ta dai na tafarfasa ba don ji yake kamar za ta fito. Ya yi cilli da robar ruwan dai-dai lokacin da ta shigo ta na mishi kallon ko ya taɓu ne? Tsaki ta yi kawai ta fice ta san in ta tambaye shi zai iya gaya mata baƙa ita kuma sai ta rama,don haka ba ta tanka mishi ba ta ɗauki wayar ta dake kan gado ta fice a ran ta ta na faɗin." To wa kuma ya taɓo wannan kububuwan?Ba zan yi mishi magana ba ya ƙare a kaina bari na bari ya huce."Ta koma ta yi kwanciyar ta ta na kallo. Tofa masu karatu kun dai jin yadda ta kaya game da waɗannan aminan juna.Ku ci gaba da bibiyata na gode da yaba lintafina da kuke. ƊUBBIN GAISUWA GARE KU SABODA COMMENT ƊIN KU YA NA SAKA NI NISHAƊI. MAMAN SUDAIS AISHATU MINNA FATIMA ZARA JOS SAHURA NURA RABIN RAINA NABILA MAMAN SAFWAN HAMDIYA UMMU ABDULHAKIM Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Mu haɗu a shafi noma sha uku.Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 13* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM A.k ya na tuki ya na jin zuciyar sa na wani irin tafasa sai dukan sitiyarin yake ya na tsaki ji yake kamar ya je ya shaƙe shi,ya na ji a ran sa ba zai ƙara hulɗa da shi ba don ya tabbata ba shi da mutunci kuma yau zai mayar mishi da motar da ya siya musu a tare da suka je Dubai. Da sauri ya taka burki ganin ya na son ya buge wani yaro dake sai da rake a tire,ya yi ƙoƙarin janyo natsuwa don ya samu ya isa gida lafiya saboda da ƙyar yake gani. Matarsa na zaune ita da yaranta suna assigment sai ganin sa ta yi ya shigo kamar an jeho shi,bai amsa sannu da zuwa da suke mishi ba ya shige ɗakinsa wanda ya ɗaga hankalin ta ta miƙe ba shiri ta bi bayan sa. Ganin yadda ya haɗe kai da gwiwa ta ɗauka rasuwa a kai don haka jikinta a mace ta ƙarasa gun sa tare da dafa shi. " Lafiya Baban Najwa in ce ba wani abu mummuna ya faru ba?" Ta faɗa cikin tsoro ganin yadda idanun sa suka canza sannan ta ƙara cewa." Ka yi haƙuri dama haka duniya take ni dai fatana ba mutuwa akai ba,ko wani mummunan lamari ya faru! Don Allah ka yi magana." Bai amsa mata ko ɗaya ba ya ɗauki ruwa ya na sha.Ganin haka sai ta janyo jikinta bayan ta ƙara A.c ɗakin ta janyo mishi kofa a ran ta ta na addu'ar Allah ya sa lafiya. Kimanin rabin awa ya ɗauka a cikin ɗakin sannan ya yi wanka ya fito da duguwar farar jallabiya a jikin sa,gefen ta ya samu guri ya zauna ya na kallon ta da ɗan murmushi a fuskarsa. Sai hakan ya sanyaya zuciyarta da take ta bugawa ta na tunanin ko wani abu me girma ne ya faru. Ido ya zura mata bai ce mata komai ba hannunsa ta kama tare da ɗora kanta a kafaɗan sa." Zuciyata ta ku san bugawa da na ga ka shigo a cikin wannan halin." Shafa gashin kan ta ya yi yace a hankali da muryar da har yanzu a kwai ɗan ɓacin rai a cikin ta." Mun yi faɗa ne da A.m kuma me zafi don har na bar mishi aikin sa,zan kuma mayar mishi da duk wani abu da ya mallaka min." Ya faɗa ya na furzar da wani irin huci mai zafin gaske. Kallon sa take da irin ba za ku taɓa canzawa ba duk cewar ta san suna faɗa amma wannan karan da alamar faɗan ya yi tsamari ganin yadda ransa ya ɓace. " Me kuma ya ƙara haɗa ku?" Miƙewa ya yi ya ɗauki wayar sa zai koma ɗaki jin tambayar da ta yi mishi wanda ya ɗaukar ma kan sa wargaza shirin,amma kuma bai gaya mata ba sai yace." Wanann kuma sirri ne a tsakaninmu." Ya ƙarashe shigewa bayan ya riƙe hannun Farha dake ta nacin ya ɗauke ta tun da ya fito daga ɗaki,ya bar ta a tsaye ta na jinjina wane irin rikicine ya faru a tsakanin su har ya yanke barin aikin. " Ko ma mene ne su suka sani haba! Suna girma suna cin ƙasa." Tace cike da takaicin halin su sai kuma ta yanke shawarar ta kira Zainab ta tambaye ta sai da wayar ta yi ringin sau ku,sannan ta ɗauka tare da sakin wawan ajiyar zuciya. " Hello sahiba ki yi haƙuri ina falo na bar wayar a cikin na manta da ita,sai da Atine me aiki ta kawo min.Ina yarana?" Ajiyar zuciya ta yi tace " Ba komai wallahi suna lafiya dama na kira ki na tambaye ki ko A.m ya na nan,na ga aminin na sa ya shigo kamar sun sami saɓani hankalina a tashe yake." Tsaki ta yi ta taɓe baki." Humh ke kika kula shi ni nawa da ya shigo ko kallon sa ban yi ba,na kyale shi don ba na son ya haɗa min zafi saboda ni ma a cike na ke da wata da ta yi min rashin mutunci a tiktok."Ta ba ta amsa ta yamutsa fuska. "Zainab!Wai ke ba zaki dai na yin rawa a tiktok ba! A da baki aure amma yanzu ke matar aure ce hakan bai dace dake ba,kin ci sa'a shi A.m sam ba ya yin tiktok amma in Allah ya so ya kama ki sai kiga wani ya tura mishi kuma ba zai ji daɗi ba." " Umh ke ni kyale ni lokacina ne kin san iya yawan adadin mutanen da suke bibiyata,so kike na yi asaran mutanen da suke zuzuta kyawuna?Ai in kika ga na dai na ƙila na mutu ne." " To Allah ya shirye ki da masu hali irin naki a matsayin ki na matar aure ji je kina bayyana surar ki ɗora waƙa ki nabi don kawai ki yi suna ko burge mutane,ba yan kin san haramun ne a addini kuma bayan haka malamin ahalari yace.Wal mar'atu kulliha aurati ma adal wajha wal kaffaini.Wato ita mace dukkannin ta al'aura ce sai dai fuska da tafukan hannaye. Gaskiya ya..." " Wash Allah na! Wallahi Maman Najwa kin cika cika mutum wannan dalilin ya sa ban cika zuwa gidan ki ba.Ke kullum sai kin yi ma mutum wa'azi,ke da uztazi kika aura sai kin addabi mutum da wa'azi ina ga ko sallah mutum ya yi zaki ce ba dai-dai bane." Ta ɗan numfasa ko za ta ce wani abu sai ta ɗora da cewa jin ta yi shiru ajiyar zuciya ta sauke. "In kin kira ni ne ki yi min wa'azi ba ni da buƙata matar liman sai kije masallaci ko in da ake buƙata.Ni ya maganar mu na fara yin sana'ar zuwa waje kin yi mishi bayani."Ta canza maganar don ta gundire ta ita ba ta da wani aki sai na yin wa'azi ita kam ba za ta iya ba,ita dai da ta ga za ta iya kashe rayuwar ta da kuruciyar ta sai ta yi Allah ya ba ta sa'a. Dariya ta yi jin ta canza maganar tace." Na gaya miki tun ranar ni ba zai barni na fita zuwa wata ƙasa saro kaya ba,gara mu dinga basu kuɗin ko mu yi oder kin san yanzu komai a sauƙaƙe yake." "Taɓ kin yi makaranta amma kamar baki waye ba ok da ma kina jira ya amince miki ne? Dama ba sana'ar kike so ki fara ba,ai koni da kika ji nace zan yi ba zan gaya mishi ba,sai ya ji na fara ke ranar da na ɗan sako mishi maganar Yayyina suna zuwa waje yin business,bai kalle ni ba yace ai da yake mazan na su mahaukata ne basu san mahimancin iyali ba.Shiru na yi bance komai ba ai sai dai ya ga na ɗaware inna dawo koma me zai faru ya faru Am ready for the conseqeuncy." A ranta ta na girmama irin halin Zainab wacce sab ba ta tsoron miji ga shi Allah ya yi mijinta da son girma,sai dai bai samu macen da za ta ba shi wannan girma ba aiko za'a sha daru don shi ma ba daga baya ba. " To shike nan Allah ya sa ki gane ni dai ba zan baki kuɗina ba kar mijin ki ya ji na baki,ni ina daraja aurena ke na lalata miki na ki gara na ba shi ya yi min oder hankalina kwance,sannan ki je ki rarrashe shi ki ji abin da ya haɗa su ko ma bai gaya miki ba don Allah ki ba shi kula kina sakaci da mijinki fa kar wata ta yi miki kwace." Ta faɗa da tsigar tsokana duk da ta san Zainab yanzu za ta harzuƙo mata da shegen baƙin kishinta amma ta kasa kula da shi. " Kinga ni ko zamu fara Allah babu wata matsiyaciyar mace da za ta shigo min gida,na kuma riga na gaya miki in ta yi wannan kuskuren to ta tabbata ni ce ajalin ta.Kuma hankalina kwance yake ya yi min alƙawari,wace mace za ta aure shi baya haihuwa ko ni haƙuri nake." Faɗin likita ba Allah bane Zainab in Allah ya so sai ya haihu domin ubangiji yudabbirul amri ne ya na jujjuya lamaruran sa,don haka ban ji daɗin abin da kika faɗi haka kuma kinga ya na iyakan ƙoƙarin sa. Zainab sai ta ji wani iri a ranta ta na fatan hakan don yanzu yadda A.m yake son ya haihu har yake zubar da hawaye ta na son ko ɗaya ne ta haifa mishi ita fa ba ta son tara yara. " Ina fatan haka Allah ya amshi addu'armu sannan da kike cewa na je na rarrashe shi Allah ya sauwaƙe haka kawai kema kin faɗa min don ki tsokane ni ne ko?A kan maganar fita waje ai dama ban miki dole ba.Ni na gaji da wayar nan don takaici kike ƙara min zan shigo gidan ki kawai mu tautauna ki gashe min da yara." Ta maza ta datse wayar ta na baƙin cikin halin da ƙawarta ta ɗaukar ma kanta saboda ta yi aure sai ta hana ci gaba a rayuwar ta?Tsaki ta yi ta ɗauki wayarta ta ta shige ɗaki zuwa can ta fito ta ci ado kamar wacce za ta gasar kyau,ta ɗauki key ɗin motarta da wayarta ta fice ta na ba za ƙamshi mai sanyaya zuciyar duk wanda ya yi katarin shaƙar shi. A.m riƙe da waya a hannunsa a cikin haɗaɗɗen ofishin sa sai ya duba numbar A.k da nufin ya kira sai kuma ya yi cilli da wayar a kan duguwar kujerar da ke cikin ofishin. Ya yi haka yafi sau a ƙirga gabaki ɗaya abubuwa sun rikice mishi a kampanin wanda har Daddy ya fara ƙorafi,ya sani A k wani jigo ne a cikin kampanin amma ransa ya ɓace ya je ya gaya mishi maganganu mara sa daɗi ga shi tun ba'a je ko ina ba ya fara dana sani. " An ya Juwairaah auren ki alkhairi ne?"Ya faɗa da tsigar tambayar kansa saboda ganin da ya yi kan maganar auren ta kawai ya bata da aminin na sa wanda suka zama kamar ƴan'uwa. Miƙewa ya yi ya tsaya a windon dake ofishinsa ya na kallon waje ganin Daddy ne da ƙaninsa yake tuƙa shi,ya yi maza ya fice daga ofishin tare da shigewa cikin wani ofis wanda ya san ba za su neme shi acan ba ya kulle kansa. " Wayyo Allah na! Ya zan yi na san Daddy ya biyo ni ne ganin na ƙi ɗaukar wayarsa ga shi kwana biyu A.k bai zo ba abubuwa duk sun caɓe. Sai ya yi shahadar kiran wayarsa duk da ya san ba dole ba ne ya ɗauka saboda ya yi fushi tunna mai tsanani da shi. ilai kuwa wayar ba ta shiga wanda ya tabbatar mishi da ya yi blocking ɗin layin ne,ɗaga wayar ya yi zai yi jifa da ita sai ya fasa ganin kira ya shigo a ransa ya na addu'ar Allah ya saka shi ne,duk da ya san abu ne mai wuya ya kira shi Ganin kiran Daddy sai hankalinsa ya tashi ya kai hannu zai kashe bai san sadda hannunsa saboda ruɗewa ya danna masa amsa kira ba har kuma ya saka a amsa kuwa. "Son lafiyar ka kuwa wai me ke faruwa ne?Rejecting ɗin wayana kake yi are you alright kuwa? Ina A.k wayarsa ba ta shiga lafiya yake mai ya faru tsakanin ku mutane suna ta kirana suna complaining tun shekaranjiya na ɗauka ko bai jin daɗi.Gashi gobe ne tafiyar ku chaina. Daddy ya fara magana ya na jero mishi tambayoyi cikin tsananin damuwa wanda ya ƙara ta da hankalinsa to mai zai cewa Daddy shi kam ya yi nadama sosai ya san ya na da saurin fushi amma nan da nan yake sauka. "A.k ya yi fushi sosai dama haka yake da ɗaukar abu gaskiya na shiga ruɗani kawai na haƙura da auren bani da rabon haihuwa ne don ba zan iya karya alƙawarin da na yi ma Zainab ba,ba zan iya rabuwa da ita ba don ina son ta na tabbata duk ranar da na kawo wata mace Zainab za ta yi kisa in kuma ba ta yi ba za ta kashe kanta ko ta rabu da ni,ni kuma ina sonki bazan iya rabuwa dake ba." Sai kawai ya rintse idanunsa ya na jin wani gululun baƙin ciki ya tokare shi a maƙogaron sa ya duka ƙasa don jin shi yake zai faɗi."Hello ka na ji na a kwai abin da kake ɓoyewa son ban yarda yadda yake girmamani,zai daina zuwa aiki ba maza ka shirya muje gidan sa duk in da kake ka dawo ina jiranka ga shi nazo ofis ɗin ka baka nan." Muryar Daddy ya katse mishi tunanin sa ya firgita lokacin da ya faɗi haka dama ya san babu wanda zai yi gigin gaya masa sun samu saɓani ne in ba so suke su rasa aikin suba. " Um um Daddy ba ni kusa na fita a mashin zan karɓo tsako bari na dawo sai muje." " Ok duk ma in da kake yanzu ka yi maza ka dawo." Daddy ya ba shi umurni tare da katse wayar sa ya bi wayar da kallo ya san dai a kwai abin da ya haɗa su,amma haka kawai A.k ba zai ƙi zuwa gurin aiki ba sanin sa mai ƙwazo da kiyaye halalin sa. Kamar an ce ɗaga labule sai ya hangi A.m ya zura da gudu ya na sanɗa ya fice daga kampanin kamar wani ɓarawo,kamar yadda mutane suka tsaya suna mamakin haka tare da tunanin lafiyarsa kuwa Daddy sai abin ya ba shi dariya ya kira Mudassir ya nuna mishi shi,dai-dai lokacin da ya fice da gudu har ya na buge kai da get. Dariya suka ƙara kwashewa da shi." Wai me ke damun son ne ya canza kwana biyu."Daddy yace ya na kallon Mudassir shiru ya yi kawai don ba za'a ji mutuwar Sarki bakin shi ba. Yafi kusan rabin awa in yakai hannu zai ƙwaƙwasa gidan sai ya janye ya kai ma iska naushi ya na jin tsananin nadamar abin da ya yi masa. " A'a yallaɓai kai ne a tsaye." Megadin gidan da ya fito da ninyar ya siyo abu a shago ya gansa tsaye.Jikinsa ya hau rawa don shi bai ji ya ƙwanƙwasa kofar ba ya san zai sha faɗa." Don Allah ka yi haƙuri wallahi ban ji ja ba kuma ba bacci nake ba." Ganin ya gigice sai ya buɗe baki a wahalce yace." Karka damu yanzu na zo."A taƙaice ya haɗa kalmomin don baya son magana. " To shigo zan ɗan siyo a bu a shago ne." Yace ya na waigen in da yabar motarsa amma ganin bai gan ta ba ya wuce abin sa. A hankali yake taku zuwa cikin gidan ya na isa kofar shiga falo ya ga an buɗe ƙoda tun kafin ya ƙwanƙwasa,matar A.k ne ta na dariya." Hangoka na yi na Zey."Tace masa da masa. " Uhumh kawai yace ya ƙara sa ciki ya zauna."Ina mijin ki na yi mishi laifi don Allah ki ba shi haƙuri tun kafin ya fito duk da na san ba dole ba ne ya fito."Yace mata cikin damuwa. " Oh wannan tsakanin ku ne ya dai kama ta ku din ga haƙuri kun girma fa shi ma tun da lamarin ya faru yake ta huci na ba shi haƙuri amma yaƙi." Tace sannan ta miƙe ta nufi ɗakinsa ba ta jima ba ta dawo fuskarta babu walwala na ƙin zuwa da ya yi duk irin haɗa shi da Allah da ta yi kan ya gane kuran sa.Bayan fitar ta ne A.k ya rintse idanun sa ya na jin ɗacin abin da ya faru tsakaninsu shi da Allah yake son shi ba wai don kuɗin sa ba,amma haka A.m ya rufe idanunsa ya na gaya masa baƙaƙen maganganu kuma sab ba zai goya mishi baya akan abin da yake so ba. A.m ya canza fuska tun da ta gaya mishi bai ce da ita komai ba idanunsa a rintse ya miƙe tamkar wanda ƙwai ya fashe mawa a ciki ya fice ba tare da yace komai ba,abin da ya sa ya zo tsoro yake kar A.k ya gaya ma Daddy abin da ke faruwa kawai ya haƙura,amma tun da yaƙi fitowa bari ya ɗauko Daddy koma me zai faru ya faru. Da ya koma hankalin Daddy ya tashi ganin yadda ya ɗan faɗa tsakanin kwana biyu,dafa kafaɗarsa ya yi." Ka na cikin damuwa lafiya wai me faruwa ne?Ina A.k ɗin?" Ya jera masa tarin tambayoyi a tare ya shaƙi numfashi ya fesar sai kawai ya kwanta akan kafaɗar Daddy cikin muryar kuka ya na hawaye yace." Daddy A.k ya yi fushi da ni mun ɗan sami saɓani ne saboda wata ƴar matsala kuma na je gidan sa na ba shi haƙuri,ni na janye wannan maganar amma yaƙi saurarata har ya ije aiki.Daddy shi ne ya ɓata min rai na kasa riƙe kaina na faɗa mishi baƙaƙen maganganu, amma na yi nadama sai dai ya datse layina layika na ba ya son magana da ni." Sai ya sa kuka kawai hankalin Daddy ya ƙara tashi yau shagwabar ta tashi kenan. Miƙewa ya yi." Oya tashi muje gidan na sa amma ba ka kyauta ba duk da tsaƙanin harshe da haƙori ana saɓawa,nan gaba ka kiyayye ba'a ɓata ma wanda yake kusanci da kai sosai in ma hakan ta faru ƙoƙari ake a riƙe fushi don dole zaku ne mi juna." Daddy yace ya na shafa bayan sa." Gaskiya ne Daddy na ba shi haƙuri fa kuma na yi nadama. A lokacin da suka isa gidan da matar shi ta shiga da nufin ta gaya masa,har ya ji muryar Daddy a falo da sauri ya zo ya durkusa ya na faɗin." Da kan ka Daddy ai da ka sanar min ni zan zo." " Ta ina zan sanar maka bayan ka kashe wayarka.Son ya yi laifi a yafe mishi don kawai kun samu saɓani za ka dai na zuwa aiki, in ka ƙara hakan zan hukuntaka ta hanyar turaka ƙasar waje ka yi wata biyu ba tare da ka dawo gurin iyalin ka ba,saboda ka ɓata min rai kuma na yi fushi da kai." Jin abin da ya faɗa da sauri maman Najwa ta miƙe tare da ficewa ko gaisuwar da ta tsaya ta yi ma Daddy ba ta yi ba,don ya ba ta kunya duk da ta san in ya yi hakan ya cutar da rayuwar masoya. " Ka yi haƙuri Daddy na yi nadama hakan ba zai ƙara faruwa ba! Da ma A.m ɗin ne ya...." " Daddy ya yi haƙuri kawai ya koma aikin sa ni nama haƙura akan maganar da muka yi na fasa na janye." Yace da sauri ya na kallon A.k don ya tsorata ya ɗauka gaya ma Daddy zai yi.Daddy ya kalle su duka kamar a kwai abin da suke ɓoye mishi wanda shi ne ya kawo musabbabin faɗan. " To wai me ya kawo rikicin?" Ai kafin ya rufe bakinsa A.m yace."Daddy ba komai ai mun shirya ya wuce." A.k dai bai ce komai ba Daddy ya kama hannunsa ya haɗa." Kar na ƙara jin kun yi faɗa ku yi min alƙawari." "Hakan ba zai ƙara faruwa ba Daddy komai ya wuce."Kamar sun haɗa baki don a tare suka faɗa. " Ok ka shirya ka taho aiki dama ina son na ƙara maka girma." A ranar dai ba wata magana na amininai da ya shiga tsakanin su,amma tare suka fita zuwa aikin sai dai A.k ko zuwa su tafi cin abinci kamar yadda suka saba bai yi ba,don har yanzu ya na jin haushin abin da ya yi mishi hakan ya sa yake yin azumi don ya rage mishi fushinsa tunna ko Allah muna mishi laifi kuma ya yafe,amma shi mutum ne wanda ya san mahimmancin kansa. Ƙin zuwa su je suci abinci hakan ya tabbatar ma A.m bai huce ba sai da ya daidaici ya gama tarin aiyukansa da ya jibga ma kansa,ya shiga ya na zaune a kan kujerar ofishin ya rintse idanun shi wataƙila bacci yake. Shigar shi ya farkar da shi ya tashi ya zauna." Don Allah ka yi haƙuri haba na san ina da fushi,amma ba ni da riƙo na lura kafi son Juwairiya da ni na haƙura da haihuwar don ni ba zan aure ta ba don na rayu da ita har abada,amma tunna ba ka so mu manta da zancen. Ga mamakinsa sai A.k ya bugi bayan sa ya na dariya yace." Haba na manta da wannan kuma akan maganar Juwariya na yadda ka aure ta Allah zan ba ka gudummuwa in har Daddy zai amince ya nema maka auren ta a sirri." Ya ɗan kalle shi ko ya yi tunanin wasa yake masa amma bai ga alamun haka ba sai ya rungume shi ya na faɗin." Na ji daɗin amincewar ka yamzu mu tafi gurin ƙanin mahaifin ta." Tofa masu karatu kun dai jin yadda ta kaya game da waɗannan aminan juna,Baba Sani zai yadda ya basu auren ta.Ku ci gaba da bibiyata na gode da yaba lintafina da kuke. ƊUBBIN GAISUWA GARE KU SABODA COMMENT ƊIN KU YA NA SAKA NI NISHAƊI. MAMAN SUDAIS AISHATU MINNA FATIMA ZARA JOS SAHURA NURA RABIN RAINA NABILA MAMAN SAFWAN HAMDIYA UMMU ABDULHAKIM Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Mu haɗu a shafi noma sha huɗu.Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 14* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM Sakamakon aiki da ya yi musu yawa sai hakan ya hana su zuwa kamar yadda suka shirya a ranar,saboda ba su tashi daga gurin aiki ba sai bayan sun yi sallar magariba daga nan kowa ya nufi gidan sa. A.m ya ji daɗi sosai ranar kasa bacci ya yi gani yake kamar ya auri Juwairah ya gama musamman da aminin sa ya amince,duk da a cikin zuciyar sa har yanzu ya na tunanin mai ya saka A.k ya sauko har ya amince duk da dokin naƙi da ya hau daga farko. A haka dai ya yi ta saƙe-saƙen shi amma ya rasa gano komai daga ƙarshe ya janyo bargon da Zainab ta rufe jikinta da shi ta na bacci,ya rufa da shi tare da juyawa dai-dai fuskarta ya rungumeta ya na shaƙar daddaɗar ƙamshi daga gareta,yayin da hankalin sa yake kwance kamar ya yi baƙo ya mutu a ransa duk ya ƙosa gari ya waye su ji yadda za su kaya da ƙanin mahaifin Juwairah. A.k kuwa ko da ya koma gida hankalinsa a tashe gani yake kamar ya aikata zunubi me girma akan amince masa da ya yi,amma da ya auna a mizanin hankali sai ya ga da ta auri wannan tsohon rayuwar ta ta shiga garari gara A.m da ko ba komai za su samu ci gaba a rayuwa,duk kuma abin da zai faru wannan kuma ya bar ma Allah lamuran sa shi yake da iko akan komai,kawai abin da zai yi shi ne ya gaya ma Juwairiya kar ta yadda zuciyarta ta fara son A.m. Ya daɗe sosai ya na shawara kafin ya furta ya amince da auren musamman da ya ji mahaifiyarta ba da lafiya,a taƙaice dai tsotsan tsamiya suke yi a rayuwar su tare da alhini. Washegari da safe A.m ya yi mishi dirar mikiya ko karyawa a gidan sa ya yi,wanda Maman Najwa ta yi mamakin sammakon sa amma sai ta yi tunanin ko ya na son A.k ya manta komai. Bayan sun gama karyawa suka nufi gidan su Juwairiya. Baba Sani ya na ƙoƙarin fita gurin aiki da ƴar ƙaƙuran motarsa da yake riƙe da makullin ta a hannun sa ya na karkaɗawa. Ganin su a kofar gidan sai ya yi turus ya na tunanin mai ya kawo waɗannan larabawan kofar gidan ko sun yi makuwa ne,saboda ya na da ɗagawa sai ya ɗauke kansa zai shige cikin motar sa ba tare da ya kalli in da suke ba,duk da tunani ya cika ran shi ganin sun tunkaro sa. "Assalamu alaika Malam barka gurin ka muka zo,don Allah ko zaka ba mu lokacin ka duk da ba ka san da zuwanmu ba,amma in ka bamu ƴan mintuna zamu tafi musammam in ka yi ma abin da ke tafe damu kyakykyawar fahimta." Yace da shi da murya mai sanyi duk ƙoƙarin sa ya tabbatar masa da baƙin sa ne saboda fuskar sa ta nuna kokwanton ko sun yi makuwa ne,duk da ya san ya na da ƴan mata amma ko kaɗan bai yi tunanin za su zo neman ɗaya da ga cikin su. Ya kalli A.m da ya ɗaure fuskar sa kuma bai ce komai ba ya lura wamda ya yi mishi magana ya fi shi sakin fuska,sai ya mai da hankalinsa ga A.m yace a cike da shakku don shi har yanzu bai yadda gurin sa suka zo ba. " An ya gurina kuka zo ko kuma kun yi makuwa ne wataƙila tambaya ce da ku." " Ka na shakkun mun zo gurin ka ne mu ba mutane ba ne? Ko aljanu ka gani." A.m ya ce mishi ba tare da ya kalle shi ba hankalin sa na gurin wayar sa dake hannun sa ya na daddannawa. Baba Sani nan take ya ji ran shi ya ɓace ya kalle sa a ran sa ya na faɗin." Ba ka sanni ba kenan amma bari na ji da wanne kuka zo." " Gashi kuma sauri nake zan tafi aiki sai fai ku dawo wani lokacin." Ya ce fuskar sa a ɗaure ganin A.m ya zo da rainin wayo.Am ya buɗe baki zai yi magana sai A.k ya watsa mishi kallo kuma aka ci sa'a ya yi shiru ya ci gaba da kallon wayar sa. " Don Allah ka yi haƙuri ka bamu ƴan mintina kamar yadda na buƙata da farko ka saurari abin da yake tafe da mu." A.k ya ce cikin marairaicewar fuska ya kuma haɗa hannun sa biyu ya na roƙon sa.A.m kuwa kofar gidan ya din ga bi da kallo ya na jin wani tsigar jikin shi na tashi,wai shi zai haɗa jini da ƴar wannan wulaƙantaccen gidan mai kama da bola,duk da Baba Sani ya na ƙoƙarin gyarawa amma abincin wani gubar wani. " Ok to muje in har zaku taƙaita maganar da ta kawo ku a cikin lokacin da kuka iba." " In sha Allahu." A.k ya bashi amsa a lokacin da suka shiga cikin gidan zuwa ɗakin Baba Sani A.m ya na ta wulƙita ido ko zai ga Juwairah don shi yanzu ma ya manta da kamannin ta. "Maza ku gaya min mai yake tafe daku da farko ina fatan ba laifi na yi ba kuka zo kama ni."Ya faɗa kamar kuma ya ji tsoro a fuskar sa. Hakan ya sa A.k ya murmusa shi ko A.m ko kallon sa bai yi ba.A.k ya gyara zama ya kalli Baba Sani ya ma rasa yadda zai fara ya na son ya ce A.m ya faɗi buƙatar da ta kawo su,amma ya san dunƙula maganar zai yi ta yadda ma ba zai fahimce shi ba ya lalata abin,bayan dai in ina da ya yi,ya kuma shiga ƙumbiya-ƙumbiya daga ƙarshe ya faɗi abin da ya kawo su don barin kashi a ciki baya maganin yunwa. Alokacin da Baba Sani ya ji maganar da A.k ya faɗa sai ya ji kamar bai fahimci maganar ba kuma har ga Allah a cikin zuciyar sa ya gasgata hakan da bai ji ba. " Ikon Allah bayin Allah don Allah ka ƙara maganar wallahi ban ji me ka ce ba yadda ka san ciwon kurumta ya kamani,a lokacin da ka yi maganar sake faɗi kamar yadda ka faɗa kuma da Hausa don Allah ba turanci ba. A.k ya so ya yi dariya jin ya ce ya yi magana da Hausa ƙila in ya ƙara maganar da larabci zai ce ya yi mishi,A.m ya mai da wayar sa a aljihun rigar sa shi bai ga dalilin da A.k zai tsaya ya na ɗan waken zagaye ba,ya san a ran shi irin abin da suka zo mishi da shi bai isa ya hana auren Juwairah ba " Auren Juwairiya kuka zo nema!" Ya maimaita hakan ya fi sau ba adadi daga bisani ya miƙe zubbur ya na faɗin." Haba dama na yi tunanin a lokacin da na ganku irin yaran manya ne da suke shaye-shaye su yi ɓatan kai su dami mutane,kun ga tunanina ya zama gaskiya ga ku kamar mutanen kirki ta waje amma ta ciki ba hali." Ya numfasa sannan ya ci gaba da cewa ba tare da ya ba su ikon koda jan numfashi ba." Wallahi na ɗauka wani abin ya kawo ku ko ba sa rana akan Juwairiya a bazan taɓa yadda ta auri wani daga cikin ku ba,bare na ba da Juwairiya yanzu haka bikinta saura sati ɗaya don haka ku wuce ki bani guri ƴan ƙwaya kawai." A.m ya harzuƙo ya na faɗin." Wa kake ce ma ƴan ƙwaya kai ne mugun ɗan ƙwaya da ka kasa gane mutanen kirki da na banza,ba giya muke sha ko kuma kamfanin ƙwayar muke haɗiya." "A.m ya kamata ka saukar da fushin ka kasan me muka zo nema." A.k ya ce mishi tare da kama shi ya zaunar ya na dafa kirjin sa. " A'a ka barshi ya yi min rashin kunya ya biyo ni har gida zai gaya min magana,a ɗakina fa kake.To bari kaji ko mutuwa za kai sai dai ka mutu, kai ko maka mutu ne aka fito da kai a ƙabari,a ka ce na baka auren Juwairiya numfashin ka zai dawo wallahi sai dai a turbuɗaka a cikin ƙasa ta rufe maka ido." " Wai tsaya kun ma san me kuka zo min da shi?Juwairiya da na tsana a rayuwata shi ne zaka kazo ka na da kuɗi ka aura taɓ wallahi ina." Da aka kai wannan gabar sai A.m bai ce komai ba ya rintse idanun shi kawai don aikin A.k ne.Amma sai ya ji A k ya yi shiru ya na kallon Baba Sani da yake faɗin ƙiri-ƙiri ba ya son ƴar wansa ta ƙaru,kai wannan wane irin mutum ne an ya a kwai zumunci a duniya saboda son duniya ko ya ce son kai,mutane sun manta zumunci bayan Allah ya gaya mana zamu tsallaka siraɗi mara zumunci ba zai sha ba. A.m ya buɗe baki zai yi magana ganin A.k yaƙi magana dai-dai lokacin da Baba Sani ya sausauta murya ko me tuna ya sa ya yi sanyi ya ce." To kai in ban da ku me za ku yi da mace irin Juwairiya yarinyar da ta gama zagaye duniya ta na yawon aikatau kuma duk mazan gidan sun san ta,sam ba ta da hali mahaifiyarta ta koya mata bin maza har sata take yi ka tambaya har kulle ta a ka yi a prison." Ya ƙara sausauta murya ya matsa kusa da A.k don ya fi A.m sauƙi ya fara magana kamar zai yi mishi raɗa amma A.m ya na jin me yake faɗi." Ina da yara sun yi karatu na boko in kuma so Juwairiya ba ta san komai ba har talla yi take yi,ai da ka aure ta gara na yi maka fatan ka mutu ba aure. " Juwairah nake so kuma zan aureta ko da ace duk mazan duniya sun san ta a matsayin ƴa mace."A.m ya ce ransa a ɓace. " To ba zan ba da ba kuma kamar maganar ta ita matar wani ne na rantse,a yau zan ɗaura mata aure ba sai an jima ba don ina zargin ku za ku iya sace ta.To ni sai in ce kamar an yi maka baki kamar ka mai zai saka ka auri Juwairiya uban ta har ya mutu faskare yake yi, a gurin faskaren ya sara ma kansa ya mutu shi ne za ka ce ka na sonta. " Nima ba son ta nake ba ban taɓa jin ina son wata ƴa mace bayan matata ba,kai ma in ka furta ina sonta ka yaudari kan ka don duk faɗin unguwarku ban ga macen da zan ji ina son ta ba." Kawai sai ya yi galala ya na kallon shi a ransa tunani yake to uban me zai yi da ita,koma dai mene ne ba za ba shi ba in ma ya na son ya yaudare shi ne ya ba shi aurenta,yadda ya rantse Juwariya ba ta ba jin daɗi a duniya tun da ta kange kwaɗinsa a kan ta gara ya ba ma wannan tsohon ya wulaƙanta rayuwar ta. " Ku faɗi ko me za ku ce ni ba yaro ba ne kuma ba zan baku auren ta ba yanzu ma zan ɗaura mata aure don haka ku cire wanann tunanin." A.k ya karkace ya zaro makullin mota ya ije masa a gaban sa sannan ya janyo cek da ga aljihun sa ya ije na kimanin miliyan biyar. Wayyo Allah zo ka ga ido sai ya zare ido can kuma ya fara mitsinan kansa ya gane ko mafarki yake." Ka bar cutar da kanka ta hanyar mintsnin kanka ba mafarki ba ne a zahirin gaskiya lamarin ke faruwa,in har ka bamu haɗin kai har gida zan canza maka rayuwar ka ta dawo sabuwa in har zaka ba ni auren ta." A.m ya ce da shi ya na kallon sa yadda ya ruɗe kamar zai zare." Ikon Allah don Allah in mafarki nake ku dake ni sai na farka wai ni ne zaku ba wannan kuɗin don ku auri Juwairiya an ya ku ba ƴan cin kai ba ne?" Ya faɗa ya na ƙarewa A.m kallo tunanin sa shi ne babba a wurin cin kai saboda ya fi A.k jiki da faɗi."Ko ma duniya muke ci ba ruwan ka in mun cinye ta tunna ba ƙaunarta kake ba." A.k ya ba shi amsa amma kuma sai A.m ya kalle shi ya ce. "Ka daina danganta mu da wannan mu mutane ƙwarai ne kawai fatanmu ka amince da buƙatarmu." Ga mamakin su sai suka ga ya tattara kuɗin ya saka a aljihun wandon sa har da makullin motar ya fara zare ido. " Duk da cewar na tsane ki saboda wani ƙudiri na wa ba na fatar in da za ya huta ta ji daɗin aure,amma ba zan bari wannan damar ta wuce ni ba Juwairiya sai dai wallahi ina tsananin baƙin cikin faruwar lamarin da na ɗaya daga cikin ƴata kuka nema Allah bari na kira ta sai dai Juwairiya ta nuna mata kyawun halitta amma ta na da hali." Miƙewa ya yi sai A.k ya kamo hannunsa ya zaunar da shi." Ka barshi ba buƙata ita dai Juwairiyar ya gani yake son ya aura na wucin gadi,shekara ɗaya tak za ta yi zai rabu da ita don a cikin sirri za' a ɗaura auren." Ya ɗan kalle su a fakaice ya tabbatar da gaske suke yi ko fim suke son shirya wa suka yaudare shi haka." Tabbas haka maganar abokina yake ni zan aureta na shekara ɗaya matata ce ba ta haihuwa,shi ne nake son ka aura min ita bayan ta haihu zan ɗauke ɗana na sake ta ita ma zan biya ta kamar yadda da na yi maka." Wani irin daɗi ya cika mishi rai ya kama hannun A k ya riƙe ya na faɗin." Kasan Allah ko auren kwana ɗaya kake son yi da ita zan baka, kai duk abin da za ka yi da rayuwar ta ba nida matsala in har za ka bani kuɗi sai dai da sharaɗin komai ya din ga biyo wa ta hannuna." " Wannan kuma ba zai yiwu ba za mu baka duk jin daɗi na rayuwa,amma Juwairiya na cikin wani hali a yanzu ina da labarin mahaifiyarta da ba lafiya kuma za 'ayi mata aikin zuciya kaƙi ka taimaka,ga ƙaninta da yake da matsala tun mahaifinta na raye yake da burin a yi mishi aiki don haka zamu fitar da shi da mahaifiyarta,ita ma mu saya mata gida,sannan ba su da cin yau bare na gobe ka ga ya dole mu inganta rayuwarta wanda da shi zamu ci ƙarfin ta har ta amince da auren." Baba Sani take ya haɗe rai jin baza a ba shi na Juwairiya ba da ya rantse ba zai ba ta da yawa ba,amma sai ya ɗan saki fuska ya na ce wa." Ni ma ki yi min uzuri ba ni da shi ne da na taimaka mata,wannan aikin wahala kawai nake yi ai nima abin a taimaka min ne." A.k tsaya wa ya yi ya na mamakin sa ya sani ce wa a kwai mutane masu son kuɗi amma wannan ya wuce tunanin sa an ya na da imani kuwa. Yauwa a matsayin ƴar aikin gidana za ta zo wanda za ka gaya ma mahaifiyarta za ta aiki na tsawon shekara ɗaya ta koya wa matata girki,wanann dalilin ya sa na ingamta rayuwar ta haka."Ba ka da matsala in ma a matsayi ƴar gadi za ta zo ai wallahi sai an yi auren,na san yadda zan yi da su duka hatta mahaifiyar ta tunna ka ba ni kuɗi ba ka da matsala. Yace ya na tare da zaro makullin motar ya kalla sai kuma ya maza ya mayar lokacin da A.m ya miƙe a tunanin sa ƙwacewa zai yi don ya ga ba shi da kirkin ɗaya. " Oh Juwairiya ban sani ba a she ke jarina ne mahaifin ki ya mutu ya bar min dukiya nima na yi kuɗi!Ai wallahi ƴan mata biyu zan gallo a rana ɗaya wayyo Allah!Ashe dama zan yi kuɗi Wallahi mutane za su ga rashin mutunci ehe." " Yauwa ina motata kuma a ina gidan yake sannan kamar yadda ba ka son matar ka ta sani haka iyayenka kenan ni ne waliyin ku duka ba matsala in ma ka na son a ɗaura yanzu ba matsala." Tsabar takaici ya sa A k yaƙi ce wa komai don ya fahimci jahili ne ku kuma son kuɗin ne ya rufe mishi ido yake faɗin ya zama waliyin su duka,sai shi ma ya miƙe ba tare da ya ce mishi komai ba A.m ne ya miƙa mishi takadda ya ce ga shi duk abin da kake son ka sani ya na ciki. Zai fita A.k ya kalle shi ya ce " Ai ya kama ta a kira Juwairiya mu gaya mata ko in ce ka yi mata bayani ka san waƙa a bakin me ita tafi daɗi." A.k ya ce mishi cikin gatsali shi har ya fara jin kunyar ta tun kafin ta fito haka kawai daga haɗuwa sau ɗaya sai su zo mata da wanann tatsuniyar. " Baku da matsalar ga ya mata ita ɗin banza ai gaba ta kai ta."Ya ɗan matso ya na cewa." Dama wannan ɗan iskar tsohon ba ya bani wasu kuɗin kirki yau zan mayar mishi da kayan tsiyar shi,ana harkar kuɗi me za' ayi da tsiya ai ni mutuwar mahaifin ki gaba ta kai ni gobarar Titi a Jos." " Ga ra dai ka kira ta shi ya sanar mata."A.k ya ce shi dai A.m bai ce komai ba sai dai ya ji wani iri lokacin da Baba Sani ya fita daga ɗakin ya na faɗin bari na dubo ta shegen yawo ne da ita ai kai da zama za ka yi da ita sai ince baka dace mata ba." Juwairiya ta na duƙune a murhun gawayi ta hira wutan yafi sau ba adadi amma da ta hura sai ya mutu muɗis,kusan kuka take son ta yi don har ta fara hawaye ganin wutar ta taƙi kamawa ta miƙe tsaye tare da zura mata ido,ji take kamar ta ɗora hannu aka ta yi ta ihu. Ta takaici ta kalli ledar taliyar da take son ta dafa ma Mama ba ta jima da dawowa daga asibiti ba take son ta ɗora musu abinci da ruwan zafi ta kai musu. Kawai sai ta ki muryar Baba Sani ya na magana tare da ƙoƙarin shigowa duk da ba ta ji me yake faɗi ba,amma ta tsorata matuƙa gani take kamar zai ce ta dafa taliyar ya ɗaura aurenta. " Juwairiya ina kike ashe dama ke jarina ne?Oh ikon Allah dare ɗaya Allah kan yi bature."Oya maza biyo ni kika abin mamaki aike kin samo mana can jin rayuwa Juwairiya yarinya ɗiyar albarka." Cikin rashin hayyaci ta tsaya ta na kallon shi sam taka sa fahimtar wai yau Baba Sani yake ce mata ƴar albarka,sai ta fara shakkun ko ya zare ne jikinta ya fara rawa ta matsa nesa da shi,ta na karanto duk addu'ar da ta fito bakinta. " Ke ban san hauka maza wuce kina da baƙi a falona kuma wallahi in kai min hauka,zan iya ajalin ki kin san bani da wasa akan kuɗi gara ma ki kiyaye!Maza wuce." Da sauri ta ruga zuwa shashinsa jikinta na kyarma haka kawai jikinta ya ba ta Alhaji Taminu ne ya zo,sai ta rintse idanunta ba ta son ganin shi a haka ta faɗa ɗakin tare da sallama wanda na yi tsammanin a zuciya ta yi,don ko ita kanta ba na tunanin ta ji. Tsayawa ta yi a ɗakin ta kasa buɗe idanunta sam ba ta son ganin fuskar sa mai kama da biri. Wani ƙamshi wanda ta shaƙe shi a rayuwarta wanda ba za ta taɓa manta mamallakin ƙamshin, ba har iya tsawon rayuwarta,tun daga ranar da ta shaƙe shi take jin ƙamshin a jikinta har zuwa yau da ta haƙiƙance ma kanta lai-lai wannan mamallakin ƙamshin,mai sanyaya zuciya da kawo nishaɗi ga duk wanda ya shaƙesa ya na kusa da ita,musamman da ta ji sautin da zuciyarta take ta na bugawa da ƙarfi kamar za ta fito fat!Fat!!Har sai da ta dafe gurin. A hankali ta sauke idanunta da suka kaɗa sukai jajur saboda wahalar hura wuta da tasha,duk da taji an kira sunan ta wanda ta gane ba muryar sa ba ne saboda ko tari ya yi za ta gane muryarsa,amma sai ta tsinci kanta da ɗora idanunta a kansa yayin da idanunnata sukai rau-rau sun canza kala suna ba da wani tarwatsi a cikin su. A.m da ya ji shigowar ta duk da ba ta yi sallama ba amma ya ji an buɗe kofa an shigo,sanann kiran sunan ta da A.k ya yi sai ya kasa ɗaga idanunsa ya kalleta,duk da ya na son ya kalli wacce yake so ta zamo ɗa ga abu ɗaya tal mafi soyuwa a gareshi don ko sun rabu aba' a sake ma tuwo suna. "Ya ilahi! Allah na roƙe ka ka farkar da ni daga mafarkinsa da nake,kuma wanann ya zama na ƙarshe tunna na kusa zama matar wani."Ta faɗa aranta ta na ƙoƙarin mai da hawayen da suke son bayyana ɓoyayyaen lamarin da ke cikin zuciyarta. " Juwairiya ki zauna mana." A.k ya ce ganin hankalinta ya tafi wani gurin ga mamakinsa sai ya ga ta nemi ƙasa ta zauna tare da saukar da kanta ƙasa. Gaishe su take son yi amma ji take kamar babu harshenta a cikin bakinta ta ƙara buɗe bakinta amma ta kasa. Ganin sun yi shiru duka sai ta ƙara ƙasa da kanta ta na kallon kafen ɗin dake ɗakin tamkar ta na son ta gano ko an maguɗi gurin yin sa. A.k ya miƙe ya kalli A.m da yake ta danna wayarsa amma a zahirin gaskiya bai san me yake dannawa ba, tunanin sa ta ina zai fara kuma ta fahimce shi,shirun da ya yi ya na son ko A.k zai yi mata bayani amma sai ya ga ya miƙe. " Bari in jira ka a mota in kun gama tautaunawar ina mota." Ya fice ya na girmama lamarin da suka zo da shi. " Juwairaah! Babu gaisuwa wataƙila kin manta ni ko."Ya faɗa don rashin sanin ta in da zai fara. Ta ɗago idanunta ta zuba mishi amma ba ta ce mishi komai ba,sai dai a ranta ta ce." Ta ya ya za'ai na manta da kai bayan ka tafi da zuciya da ruhu gangar jikina kawai ka barmin,amma to mai ya kawo shi gidammu wanda har Baba Sani ya yadda na zo gurin sa.Aurena yake son yi?". Ta tambayi kanta sai ta yi saurin kawar da wannan bahagon tunanin ta ce " Kai ina wutsiyar raƙumi ta yi nesa da ƙasa." "Wai ni kurma kika zama bayan rabuwarmu?Ko kina mamakin ganina ne" Ya ɗan tambaye da hasala a ranshi ganin yadda take basar da shi kuma ya tsani hakan. " A'a ai ba'a mamaki da ikon Allah." Iya abin da ta ce kenan ta ƙara naɗe bakinta ta yi shiru tanani fal a zuciyarta. Ganin ta tafi wani tunanin daban sai ya ce " Haka ne ba'a mamaki da ikon Allah don haka kar ki yi mamakin na zo nai man aurenki amma fa na kwangila auren shekara ɗaya nake son mu yi dake kuma cikin sirri." Juwairiya ta ɗago kanta da sauri ta kalle shi a wannan karan ba tare da ta ji nauyin sa ba." Aurena zai yi amma na kwangila mai hakan yake nufi?Sannan kuma cikin sirri to suwa ye ba' a son su san auren?" Tambayar da ta yi ma kanta kenan a cikin zuciyarta wanda ba ta san maganar ciki ta fito fili ba.Ya gyara gilashin idanun sa ya miƙe tare da juwa mata baya. " Yes abin da kika ji hakan nake nufi kin san ke ba sa'ar aurena ba ne,na tabbata kina tunanin me ya sa zan aure ki?Kamana ɗan gayu kuma ɗan masu da shi yayin da ke kina talaka kucaka dake.Ki kalle ni mai aji kama na ban yi kama da wanda zai aure ki ba." Ya numfasa ya juyo ya na kallonta ganin yadda ta saki baki hanci ido ma'ana ta yi galala ta na jin tatsuniyar da yazo mata da shi. " Matata Zainab wacce nake so fiye da komai rayuwata mace mai aji yarinya ƴar babban gida,Allah bai nufe ta da haihuwa ba ni kuma bazan iya haɗa ta da wata ƴa ɓace ba don na yi mata alƙawarin bazan yi mata kishiya ba,ga shi ina son na ga ƙwaina a duniya shi ya sa nake son na aure ki a sirri ki haifa min ɗa ɗaya na ba ta amma a gidana zaki zauna amatsayin ƴar aikin ta." Wani irin hajijiya ta ji ya ibeta sai ga shi a gabansa ta zare ido jin a bin da ya faɗa,take ta ji wani hajijiya zai yarda ita ƙasa ta rintse idanunta,hawaye suka fara turereniya a kan fuskarta da ta shiga da tashin hankali. " Allah na roƙe ka ka farkar da ni daga wannan mummunar mafarkin na farka ba tare da na gan shi kamar yadda yake tsaye a gabana! Ya Allah ka ɗauke ganina da shi na har abada da kunnuwana su ƙara ji min abin da yake faɗi ba,Ai gara na auri Alhaji Tanimu da na amince na auri mutumin da nake jin,bayan shi babu wani ɗa namiji a duniya shi ne yake son na yi rayuwa a gidan shi a matsayin ƴar aikin matarsa. Wayyo Alla!gara na ga ranar mutuwata don zan fi samun maslaha a cikin ƙabarina da na amince da buƙatarsa. Tofa ga dai Baba Sani ya amince shin Juwairiya za ta amince ya auren zai kaya?Ku dai ci gaba da bibiyar lintafin SAKACINA KO HALIN MAZA. ƊUBBIN GAISUWA GARE KU SABODA COMMENT ƊIN KU YA NA SAKA NI NISHAƊI. MAMAN SUDAIS AISHATU MINNA FATIMA ZARA JOS SAHURA NURA RABIN RAINA NABILA MAMAN SAFWAN HAMDIYA UMMU ABDULHAKIM Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Mu haɗu a shafi noma sha huɗu.Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 15* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM A karo na biyu ta ƙara gwalalo idanunta." Ina hakan ba zai taɓa yuwu ba!Gara na rayu a cikin talauci na kuma mutu a cikin sa.Anya ya san me yake faɗi kuwa. Sai kawai ta nufi hanyar fita ba tare da tace mishi komai ba. Juwairaah!" Ya kira sunan ta da sauri tare ƙofar ya kama hannunta wani irin hajijiya ya kama ta wani abu mai kama da shokin,ya na zagaye jikinta yayin da yake fitowa daga gurin da ya riƙe ta ya na ƙara wutar sonsa a cikin zuciyar ta. " Don Allah ka cika ni ba zan iya abin da kake faɗi ba,hakan ya tabbatar min da ka tsane ni ba ka son ganin farin cikina dama na san ni ba'a sa'ar auren ka ba ne, to amma kaje ka auri mata masu aji irin matarka ta yadda za ka samu ƴara daga gidan kuɗi,ba irina wanda mahaifina ya mutu bai bar min komai ba. Ta faɗa tare da fisge hannunta da sauri ya sha gabanta ya toƙare kofar da take son ta fice, jikinsa ya yi sanyi ganin kamar ba za ta yarda ba,amma kuma ya zama dole ya san yadda zai yi ya shawo kanta,saboda amincewar ta ne kawai zai sa ka ta jure duk wani abu da za ta gani a gidan. " Nima na so haka na sami mace mai aji kama ta, amma kin san babu wata mace mai aji wanda zan nema ta yadda da hakan.Kasancewa ta ɗa namiji da kowa ce mace za ta yi burin samu shi ya sa naƙi nai mar me aji iri na, don na san ba za a kwashe dai-dai da ita ba,kuma kema fa so nake na ceci rayuwarki daga ƙangin talaucin da kike ciki. Ya ƙarashe maganar da murya na salon yaudarar shi ya na son ta amince. Hawaye suka ƙara turereniya a fuskarta ta kalleshi da nufin ta saka wani mugun tsanar shi a cikin ranta,amma sai ta ji wani madarar son sa ya na ƙara shiga cikin bargon jikinta a duk sanda ta yi kuskuren haɗa ido da shi. " Sai ni talaka ko?Ni da Allah bai saka min zuciya na so ba.Ko naƙasun talauci ya na yin tasiri a zuciya duk lokacin da ta ke son wani?Shi ya sa za ka zo ka cuci rayuwata ta ɗa na kake son na haifa na ba wata mace na har abada?Don Allah ka fita daga cikin rayuwata na roƙe ka na san ba za ka samu matsala da ƙanin mahaifina ba,amma ni ba zan amince da mugun nufin ka a kaina ba.A yau na yi burin dama ban taɓa sanin ka a cikin rayuwata ba." " Ke ya ishe ki ƴar talaka kawai zaki zo ki na jera min wasu maganganu kamar wani ɗan ki!Dama ban yi miki dole ba." Ya faɗa tare da kaucewa ya ba ta hanya ganin hakan ya sa ta zura da gudu za ta fita,dai-dai lokacin da Baba Sani ya yi gyaran murya."Ya kamata ka wuce abokin ka ya na jira,kawai ka nemo waliyin ka a duk sanda kake son a ɗaura auren kar ka damu da ita ko amincewar ta" Da ido ya kalleta ya na gasgata abin da yake faɗi." Kin ji da kunninki abin da kwaɗayayyen ƙanin mahaifin ki yake cewa?Don haka ina tambayar ki ne don kar ayi ba tare da yaddar ki ba kizo ki ɓata komai." Ya zaro waya mai kyau da tsada ya ije mata." Ga shi zan wuce na gaji da wannan kukan nan naki da kika tasa ni da shi.Fisabilillahi sai kace na zo gidan ta'aziya,duk abin da kika yanke zan kira sai ko gaya min." Ya miƙa mata kuɗi masu yawa." Ga shi ki je ki yi ma marasa lafiya siyayya.Ina ƙara gaya miki ɗa ɗaya kawai nake son ki siyar min bayan nan zaki iya auren namiji wanda ya fini,domin zan ƴanta rayuwarki zan gina ma mahaifiyarki gida na ba su duk wani jin daɗi na rayuwa. Shekara ɗaya ne fa kawai za ki yi kina ma masoyiyata aiki in ma kin sami ciki, da wuri zan ɗauke ki daga gidan kin ga kin huta kenan,sannan ki iya takun ki ba da sani ta zan yi komai ba." Ya numfasa ya na kallon ta yadda ta yi zuru ta na kallon shi,yayin da zuciyarta ta ci gaba da bugu cikin tashin hankali. "kamar yadda na gaya miki haka za ki yi don haka ko kallona kar ki yi in dai ta na kusa da ni.Kasancewarta ba mai zaman gida ba ne kinga haka zai bamu damar aurenmu ya tafi cikin sirri." Ya ce da ita sannan ya fice ya barta a tsaye tamkar gunki sai da ta ɗauki tsawon lokaci sannan ta yi zaman ƴan bori a ƙasa tare da fashewa da kuka. " Don Allah karfa ku yi min ƙarya ku dawo fa in ba haka ba wallahi sai na nemo ku duk in da kuke don ba zan ga samu na ga rashi ba. Motar su na ɓacewa ya ruga da gudu ya shige ɗakinsa alokacin Juwairiya har ta miƙe ta share hawayenta za ta fice." Ƴar albarka Juwairiya zo mai ya baki." Sai kuma ya hangi damin kuɗin da ko ta kan shi ba ta bi ba, ai da sauri ya dafe ya na washe baki sannan ya miƙa mata dubu biyar ya ce." Gashi maza ki tafi Juwairiya ya gaya miki komai ko?Ai Allah ya tarfa ma garin ki nono kin huta da auren wannan mutumin,dama ɗan iskan tun da ya ga na ba shi auren ki ya dai na bani komai,duk da na yi baƙin ciki amma ko ba komai ai na samu ta sanadin ki rayuwata za ta shiga cikin jerin masu da shi." Juwairiya ba ta ce komai ba har ta kai ƙofa za ta fita, sai kuma ta dawo ta ce." Ni fa ba zan aure shi ba haba Baba ka ji tausayina mana!Wallahi in..." "Rufe min baki banza shashasha!Don ma kin samu zai aure ki wallahi da bai zuba uban kuɗin nan ba, to ko megadin gidansa yake son ki yi masa ba zan bari ba,ai ke gaba ta kai ki ko banza a shekara ɗaya zaki rayu cikin daula,ko banza za'a sha zaƙi da maiƙo a rabu da tuwo wanda shima ba kullum ake samu ba." Da sauri ta fice jin maganar da yake mata wanda duk cin fuska ce. Juwairiya ta shiga cikin tsananin hankali tun lokacin da ta fito da ga ɗakin Baba Sani ta kife kanta ta na wani irin kuka mai tsuma zuciyar mai saurare. Yayin da tausayin kanta ya rufe ta ganin mutumin da take matuƙar so ya zo neman ta akan auren kwangila."Yanzu inna auresa shekara ɗaya za mu yi? Shima tsakanin mu tamkar mage da ɓera tunna matarsa ta yi katanga a tsakanin." Abin da take ta faɗi a ranta kenan sai kuma ta share hawayen da damuwa cike a zuciyarta,don ta rasa yadda za ta kwatanta wannan auren da yake son su yi,amma a ranta ta ƙudira koma me zai faru sai dai ya faru don ba za ta aure shi ba,ai gara ya barta a cikin tsananin talauci saboda in talaucin bai kashe ta ba,tsananin son da take mishi da kishin matarsa zai kai ta lahira! Ko da ta isa asibiti ba yan ta gama girki abin mamaki sai ta ga Baba Sani zaune a can,ya dage sai zuba ruwan surutu yake yi tamkar wani aku. Sai Juwairiya ta kasa shiga ta tsaya ta na kallon shi da mamaki ganin yadda yake ta magana har da dariya ga uban leda da ya siyo musu abu. Mama shiru ta yi ta na kallon shi da mamaki."Oh ikon Allah duniya juyi-juyi!" Abin da ta ce kenan cikin tsananin mamakin sa. "Ƙaraso mana Juwairiya kin ga har na riga ki ai daga gurin aiki sai na taho,ban san kina gida ba." A sanyaye ta shigo tare da ije abincin dai-dai lokacin da Baba Sani ya tashi tare da yi musu sallama ya tafi. Da sauri Juwairiya ta bi bayan sa ya na ƙoƙarin shiga motar sa ta riƙe murfin motar idanunta na zubar hawaye " Ba zan aure shi ba gara ya barni a halin da muke ciki,amma ba zan yi aure ba wanda mahaifiyata ma ba'a son ta sani!Tun wuri ka mai da masa da kuɗin sa ni zuciyata ba irin naka ba ne!Na san mutuncina ai talauci ba hauka ba ne " Kau ya gaura mata mari " Baki da hankali kina wasa da ni ke baki san halina,ni murucin kan dutse ne! In har kika ce ba za ki yi wannan auren ba,kin ji na rantse miki Juwairiya zan iya kashe ki har da mahaifiyar ki.Don haka in baki bi umurnina ba ki kuka da kanki." Ya ja motar sa ya barta a nan tsaye cikin tashin hankali sai kawai ta rushe da kuka,sai da ta yi mai isar ta sannan ta yi shuru ta wanke fuskarta ta shiga cikin ɗakin da Mama suke. " Ikon Allah abin duniya ba ya ƙarewa kin ga abin mamaki ko.Ai addu'a takobin mumuni ne." Juwairiya ta ce."Umh Mama."Sannan ta ɗauki filet ta zuba mata abinci. "Juwairiya bayan fitar ki likita ya zo ya ce in dawo ki je ki same shi,sannan ya ba da takadda kamar na magani ne." Ta ce cikin damuwa da murya ƙasa-ƙasa kai da ga ji ka san ta na cikin jinya mai tsanani. " To Mama bari na je na same shi." Ta miƙa mata abincin sannan ta fita zuwa ofishin likitan. "Ok zauna" Ya ce da ita bayan ta ƙwanƙwasa ta shigo a hankali ta zauna cikin tsoro-tsoro don ba ta san dalilin da likitan ya kira ta ba. Ga sakamakon gwajin da muka yi ma mahaifiyar ki nan gaskiya ta na cikin matsala ya kama ta a canza mata asibiti,saboda zuciyar ta ta kumbura dole a yi mata aiki. Da sauri Juwairiya ta miƙe tare da zare idanun ta jin abin da likitan ya faɗa." Na shga uku Allah ka kawo min ɗauki!Mama za'a yi wa aiki!" Sai hawaye shar-shar a fuskarta ta koma ta zauna kamar yadda likitan ya umurce ta ganin ta tada hankalinta. " Ki yi haƙuri! Jarrabawa ce amma kar ki yadda ta ji lalurar da take da shi wannan dalilin ya sa na so namiji ya zo na gaya mishi,amma sai ta nuna ke ɗin dai zan gaya ma wa." Da sauri ta miƙe tare da ficewa daga ofishin har ta kai ƙofar ɗakin da Mama ke kwance, sai kuma ta ja da baya ta tsaya kamar wata zararra!Tuna likita ya ce kar ta gaya ma Mama komawa ta yi wani guri ta na son ta yi kukan amma ba hawaye sai tuƙuƙi da zuciyarta take yi mata. Ta ɗauki tsawon lokaci sannan ta koma cikin ɗakin.Da daddare Juwairiya ta kasa bacci sai juye-juye take,abin duniya ya haɗu ya yi mata yawa ji take kamar ta ɓace a cikin duniyar. Kwana biyu kuma sai Ibrahim ya fara ciwon ƙafa wanda in ya na yi yake fita cikin hayyacin sa,don har tsuma yake na tsawon lokaci bai farfaɗo ba.Abin duniya ya yi mata yawa ga tunanin A.m da yake son ta baƙunci kabarin ta kafin mutuwarta,duk ta yi fari ta rame kamar wacce ba ta da jini a jikinta sai ƙashi da ya zama ado a jikin ta. Zaune take a gefen Mama ta zura mata ido ta na tausayin halin da suke ciki,don ko wannen su da jinyar da yake yi.Hannu ta sa ta yarfe zufan dake goshin ta,wanda yake tsatstsafo mata duk sanda ta tuna da A.m. " Inna lillahi." Ta ce tare da miƙewa ta tsaya bakin windo sai hawaye." Wai dama haka ciwon so yake?Allah na roƙe ka ka cire min soyayyar son maso wani a cikin rayuwata,yayin da nake tsananin son sa shi haɗuwar mu ya zama dama a gare shi ya faranta ma masoyiyar sa rai. Likitan ne ya yi sallama ya shigo wanda ya saka Juwairiya ta juyo da hawayen dake zuba a fuskarta,ya tausaya mata sosai amma sai ya miƙa mata takadda ya ce." Ga shi Juwairiya an baku sallama duk da jikin mahaifiyar ki bai warke ba,amma baku da kuɗi kuma mai asibitin ya na buƙatar kuɗi." Juwairiya da ta ji ta daskare amma sai ta kai hannu ta ƙarɓa jikinta a sanyaye ba tare da tace mishi komai ba,ita zuwa yanzu hawaye sun ƙare da ga fuskarta sai wani azaban raɗaɗin baƙin ciki da take kurɓar ruwan sa mara daɗi a cikin zuciyarta wanda yafi na guba illah. Sai ta fara haɗa kaya dai-dai lokacin da likitan ya fice daga cikin ɗakin. Kwana biyu da dawowar su jikin Mama ya rikice Juwairiya a daren ranar ta ɗauka ba za ta kwana ba,da safe ta sami Baba Sani ta na kuka ya taimaka ma Mama da ranta yake tsakanin mutuwa da rayuwa. "Kin ji na rantse miki Juwairiya ko mutuwa za ta yi sai dai ta yi matuƙar ba za ki amince da auren A.m ba.Ya faɗa ya na zare ido sannan ya ɗora da ce wa."Ai dama ba son ta kike ba in banda ƙashin tsiya ne dake Juwairiya irin A.m ko auren kwana ɗaya yace ki yi,ai na ɗauka jikinki na rawa za ki amince." Haka ta dawo jiki a sanyaye ta zauna ta tare da zuba ma Mama ido ta na hawaye.Sai ta ji ɗakin ya ɗauka da wani irin abu kamar na vibration,da sauri ta miƙe don ita tsoro ta ji sai da ga baya ta koma ta zauna tuna wa da ta yi A.m ya ba ta waya,wace tun ranar ta ije ta amma abin mamaki cajin bai ƙare ba. Sau uku ana kira amma ba ta tashi ba ta na kallon Mama dake bancin wahala,sakamakon rashin baccin da ba ta samu ba daren jiya,yayin da kiran ya ci gaba da shigo wa sai hakan ya ƙular da Juwairiya ta miƙe da sauri ganin Mama ta fara mutsu-mutsu za ta farka. Waje ta yi da wayar ta kai hannu da nufin ta kashe don ta tabbata shi yake kiranta sai kuma ta fasa tuna da halin Mama take ciki,ta saki nauyayyar ajiyar zuciya. Wata gefe na zuciyar ta ta bijiro mata da ta amince da auren A.m don ta ceci rayuwar mahaifiyarta duk da ta san ba ta yi ba Mama adalci ba,amma halin da suke ciki zai saka ta amince ba tare da ta yi tunanin komai ba. Sannan ko ba komai ai auren sa ya yi mata katanga da auren tsoho a lokacin da suka rabu,ta na matsayin bazawara ba wanda ya isa ya yi mata karan tsaye a rayuwarta. Sai dai da ta tuna tsananin son shi da take da kuma ɗanta da za ta ba ma matarsa,wacce take jin yanzu bayan mutuwarta babu abin da ta tsana fiye da ita. Ta na wannan tunanin ne ta ji muryarsa ta daki dodon kunninta ya na faɗin." Hello Juwairaah ki na ji na?" Bata san ta danna wayar ba ashe ta amsa kiran da sauri ta kanga wayar a kunninta ba tare da ta yi shirin hakan ba,jin daddaɗar muryarsa da ya saka ta manta komai ta ji kamar ta zuƙo shi ta wayar saboda wani irin ƙaiƙayi na son ganin sa da idanuwanta suke mata. " Ina jinka." Ta ce jin ya maimaita maganar har sau uku.Ba tare da ya yi wata doguwar magana ba ya ce." Ya maganar mu kin yanke shawara? Saboda zan yi tafi zuwa India kin ga sai na gama komai kafin na tafi." A hankali ta sauke ajiyar zuciya ta sauke cikin baƙin cikin daina magana da ya yi,saboda jin muryarsa take kamar ana busa mata sarewa. Sai kuma ta fara sheshsheƙar kuka ta buɗe baki za ta yi magana sai kuma ta fasa tare da kecewa da kuka. " Oh my God! Ni fa ba na son mace mai saurin kuka haka kawai ki dinga kuka,in dai kuka za ki dinga min zamu tsamu matsala dake." Ya numfasa ko za ta ce wani abu sai ya ji ta yi shiru sai ɗan sautin kukan dake tashi a ajiyar zuciyar da take yi. " Na amince!" Ta furta tare da ƙara sakin sabon kukan duk da gargaɗin da ya yi mata ya shiga jikinta don umurnin sa kamar yankan wuƙa ne,sai da ta kasa hana kuka a ranta ta na tunanin yadda za su yi a tsakanin su ba a lokacin da aka ɗaura auren. Ta ƙara buɗe bakinta da ƙyar ta ce " Don Allah ka kawo ma mahaifiyata ɗauki ta na cikin wani hali diɓ!."Ta kashe wayar tare da tsugunawa a gurin ta na jin wani hali wanda duk ƙwaƙwana na kasa gane halin da take ciki domin ita kaɗai ta san halin raɗaɗin da take ciki. A.m ya ji wani sanyi a zuciyarsa waya ya ɗauka ya kira A.k nan take ya fara shirye-shiryen yi ma Mama biza. A lokacin da aka fita da Mama ba ta san halin da take ciki ba Juwairiya har ta cire ran zai kawo ma Mama agaji,saboda da ta ga kwana uku da maganar su bai kira ta ba wanda hankalinta ya tashi sosai. A ranar na uku Baba Sani ya sanar ma Juwairiya su fara shiri har sujjada shukuriya sai da ta yi gani take kamar Mama mutuwa za ta yi. Ba ƙaramin mamaki ta ji ba lokacin da Baba Sani yake gaya mata har da Ibrahim za'ayi tafiyar,zuciyarta ta haƙiƙance mata Allah ya kawo mata A.m a cikin rayuwarta don ya fitar da su halin da take ciki,sai dai in ta tuna son shi da ya mamaye mata zuciya ta na jin tausayin ranar da za su rabu wataƙila shine sanadin ta. Su Juwairiya na ƙasar waje A.m da A.k suka shirya zuwa gidan Daddy domin su shawo kansa ya amince ya ƙarɓar mishi auren Juwairiya. Gabansa ne yake faɗi ras! Har suka isa gidan maigadi ya wangale musu get,A.k da shi yake tuƙi ya shigar da motan. Daddy ya na falonsa ya na ganin A.m ya tashi ya rungume shi tare da jawo A.m suka zauna a kujera me cin mutum biyu." Na yi kewar ka son ya kuka dawo? Wannan mutumim ya kirani don Allah son ka rage zuciya ka san harkan kasuwanci sai an yi haƙuri." Sumar kan shi ya shafa tare da sakin murmushi duk da mutumim ya ɓata mishi rai matuƙa,amma yanzu ba shi ya kawo su ba. Bayan sun ci abinci wanda A.m bai so ya ci ba amma Daddy ya matsa mishi,duk yadda yake da hope a kan sa sai gashi ya kasa sanar mishi ya na ta tunanin yadda zai fara magana. A.k kuma ya yi banza da shi ya na ta kwasar girki shi ko tun da ya kai loma biyu wanda ya ci ne saboda takurawar da da Daddy ya yi mishi. " Am Daddy don Alah a kwai abin da yake tafe damu,amma muna roƙon ka ka fahimci abin da ya kawo mu don Allah Daddy." Ya yi ƙundumbalar faɗi da fuskar tausayi ya na hararar A k da ya manta da shi ya na ta aikawa cikin sa bayani,kamar da ma abin da ya kawo su kenan. " Ina jin ka son dama har a kwai abin da za ka kasa sanar da ni?" " Aure nake ne ma amma a kwai ƴar matsala."Ya ce ya na kallon Daddy ya ga yadda zai karɓi zancen. Daddy kuwa tsananin tausayin shi ya kama shi da ya tuna shi ma haka ya din ga aure-aure don ya samu ɗa,amma kuma shi ne ba ya haihuwa ba matarsa ba me ya sa yake son ya ƙara aure. " Son mata biyu anya za ka iya zama da su kai da baka da haƙuri,ɗayar ma ya ka cika bare ka tara fiye da ita.Amma tunna zaka iya faɗa min ƴar wacece kuma su waye ahalin ta?" Wannan karan A.k ne ya ce." Ba ƴar kowa ba ce asalima mahaifinta ya mutu ƙanin mahaifin su yake riƙe da su." " Son ƴar talaka matsiyata kake son aure ka manta Zainab ko ƴar wace ce ita?" Ya miƙe tsaye tare da furta hakan ya na mamakin A.m da ya canza duk yadda yake nuna tsanar talaka sai ga shi ya jajibo auren ta. Ya shafa kansa ya na faɗin." Karka damu Daddy auren nawa na wucin gadi ne,sannan saboda ita Zainab ɗin zan ƙara aure."Take ya kwashe komai ya gaya masa. Sosai yake kallon sa ya na mamakin wai Zainab ce ba ta haihuwa amma ya ce shi ne baya haihuwa.Lai-lai ya tabbata ya na shaye- shaye. " Ka yaudare mu Abdurrahman an ya ka yi m kanka adalci ka n ganin in kai ne ba ka haihuwa za ta yadda ta zauna dakai?Ka san ciwon rashin ɗa har yau kuka nake kan ban taɓa haihuwa ba duk da mahaifin ka ya ba ni kyautar ka.Wallahi da sake dole kowa ya sani sannan ka canza mata ba ƴar talaka ba don ba ma haɗa dangi da matsiyata!" Ya ce tare da miƙewa zai fice ga mamakin sa sai ya ga A.m ya yi sauri ya kama ƙafafunsa ya riƙe ya saka kuka kamar wani ƙaramin yaro ya na roƙon sa,wanda magana uku ya yi masa har ya saka ya zauna jikin sa sharɓar da zufa ya na kallon su. " Daddy ka tuna Zainab ƴar amininka ne kuma a saboda ni ta kamu da wannan ciwon,Zainab ta rantse in har na haɗa ta da wata mace za ta rabu dani,rayuwata ba za ta yiwu ba in babu Zainab ina sonta raina fansa ne akan duk abin da take so." Waɗan nan kalamai ya gaya masa ya na kuka wanda hakan ya sa ya zauna don ya saurare su." Na ji to yanzu ya kuke son ayi ni fa ba mahaukaci ba ne kuma ni soyayya ba ta mai da ni zautacce ba,kar na zo na biye maka mu aika ta hakan lamari ya caɓe mu rasa yadda za mu yi." Ya tambaye shi ganin A.k ya miƙe ya ba su guri saboda yadda Daddy yake kallon sa kamar ya na buƙatar hakan. " Saboda haka ya sa na zaɓi ƴar talaka wanda ba su da komai ka ga ta gurin ta hankalinmu ba zai tashi ba,kuma ni na tallafi rayuwar ta.Matsiyata ne basu da komai sai talauci da garari a rayuwa sannan ƙanin mahaifinta wani irin mugun me son kuɗi ne ya kuma tsane ta don haka kar ka damu."Ya ce ya na kallon shi don duk wani kalamai da zai gaya mishi ya ƙare shi dai burin shi ya amince. " Kai ku tashi ku tafi kai son ka je ka yi tunani na baka nan da sati biyu,in baka sanar da mahaifin ku gaskiyar lamari ba to ni zan fasa ƙwai maza tashi ka wuce! Hankalin A.m ya tashi matuƙa ko kaɗan bai yi tunanin zai yi kafiya akan lamarin ba,saboda yadda ya ga baya son ya ga ɓacin ransa,ƙara riƙe ƙafar sa ya yi ya na kuka da roƙon sa,amma haka Daddy ya janye ƙafarsa ya shige ɗakin sa duk da kukan shalelensa na yi masa ƙuna sai dai lamarin da ya kawo mai girma ne. A mota suna tafe babu mai yi wa juna magana A.m tunanin kuɗin da ya kashe take yi,sai ya ji ya ƙara samun ƙarfi wanda washegari Daddy na fitowa daga masallci ya gan su a tsugune. A ƙalla sun ɗauki tsawon wata suna jerangiya amma Daddy ya hau dokin naƙi,cikin ikon Allah A.m har ya haƙura sai ga kiran shi ya sanar masa su shirya yau zai je a ɗaura aure. Haka kuwa aka yi bayan an idar da sallah aka ɗaura auren Juwairiya Ahmad da Abdurrahman Dawood akan sadaki naira dubu ɗari biyar wanda Baba Sani ya dage hakan zai ba da,ba tare da damuwa ba ya amsa wanda Daddy ne ya biya kuɗin. Tofa masu karatu ga shi Allah ya kawo mu an ɗaura aure kuci gaba da bibiyar lintafin domin mu ji yadda za ta kaya. SHIN JUWAIRIYA ZA TA IYA DANNE SON DA TAKE MASA TA ZAUNA DA SHI KAMAR YADDA YA BUƘATA?NI DAI NASAN SON GASKIYA BA YA ƁUYA WAƊANDA SUKE CIKIN SO SUNE KAWAI ZASU AMSA AMIN TAMBAYAR NAN. TAKU JAMILA LAWAL ZANGO ƊUBBIN GAISUWA GARE KU SABODA COMMENT ƊIN KU YA NA SAKA NI NISHAƊI. MAMAN SUDAIS AISHATU MINNA FATIMA ZARA JOS SAHURA NURA RABIN RAINA NABILA MAMAN SAFWAN HAMDIYA UMMU ABDULHAKIM Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Mu haɗu a shafi noma sha shidda.Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 16* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM Jikin Baba Sani ya na rawa ya dawo gida don murnar kuɗin da Daddy ya biya a matsayin sadakin Juwairiya,da ga gurin ɗaurin auren ɗakinsa ya wuce sai da ya yi fasalin kuɗin ya cire kuɗi kaɗan da nufin zai bawa Juwairiya sadakinta,wan da sauran ya saka su a aljihunsa murna cike a zuciyarsa, ganin irin yadda rayuwarsa ta canza lokaci guda kuma duk a saboda Juwairiya. Ya yi kiran Juwairiya da take girki duk da damuwar da yake ranta amma ta na jin daɗin yadda Mama ta samu sauƙi jikinta ya yi sauki,ga kuma Ibrahim da shi ma an yi masa aikin a ƙafar sa ya samu sauƙi sai wani daɗi ya mamaye mata zuciya har take girkin da kula ta na son Mama ta ci abincin sosai. Kiran da Baba Sani ya ƙwala mata ya sa ta ji gabanta ya faɗi ras!Don ta san yanzu in dai zai kira ta to akan maganar auren ne.Cikin saiɓin jiki ta amsa tare da saurin zuwa gurin sa. " Amaryar shekara ɗaya yaufa an ɗaura auren ki da A.m ɗazu."Ya faɗa tare da miƙa mata kuɗi. Wani irin zufa ya keto mata da sauri ta dafe ƙirjinta." Na shiga uku."A bin da ta ce kenan sai hawaye suka fara turereniya a ƙuncinta. Miƙa mata kuɗin ya yi amma sai ta ƙi amsa tare da shigewa cikin gida hankalinta ya tashi sosai ganin da ga yau ta zama matar A.m. Tun da ya gaya mata maganar ɗaurin aurenta ta shiga cikin wani hali na rashin natsuwa gabaki ɗaya ta ruɗe,ta na cikin waswasin tunani sai ga kiran sa ya shigo da ta tuna yau a matsayin mijinta ya kira ta kuma ba ta san me zai ce mata ba sai ta ƙara ruɗewa. Daga bisani kashe wayar ta yi gabaki ɗayan ta ta kai ta ɗakin ta in da take ɓoyewa kar Mama ta gani.Ta koma gurin girkin ta da take tunanin kar ya ƙone. Sam ta manta ta saka gishiri a girkin ba tare da ta tuna ba kawai ta ɗauki gishirin da nufin ta zuba ba,ta sai ta gishirin a tukunya wanda hannunta ya zame ta juye shi duka sannan kuma a lokacin ta tuna ta riga ta saka gishiri. Kawai sai ta fashe da kukan da ta kasa gane saboda juye gishirin ne take kuka,ko kuma a kan maganar da Baba Sani ya gaya mata ne oho. Mama da ke falo ta na shan magungunan ta sai ta ji kukan Juwairiya da ƙarfi ta na rera shi kamar wata ƙaramar yarinya duk da jikinta ba ƙarfi, amma hakan nan ta daure ta fito ta na dafe bango a ranta ta na mamakin mai ya saka ta kuka haka. "Lafiyar ki kuwa?" Ta ce a lokacin da ta ƙaraso gurin sai ta yi turus! Don ita hankalinta ya tashi ta ɗauka ƙone wa ta yi,amma ganin lafiyarta ƙalau sai hankalinta ya kwanta Ganin ba ta amsa mata tambayar da ta yi mata ba. Kama ta ta yi ta riƙe tare da shigar da ita cikin ɗaki saboda kukan da take yi ya tsorata ta." Ki yi shiru don Allah ki dai na kuka kin san abin da likita ya gaya min,yanzu haka dalilin kukan ki ba ki ji yadda zuciyata take bugawa ba."Ta faɗa tare da dafe ƙirjinta da yake harbawa da ƙarfin gaske. Ganin haka hankalinta ya tashi da sauri ta share fuskarta duk duk yadda ta so ta ƙaƙaro murmushi a fuskarta,amma hakan ya faskara wasu sabbin hawayen da suka ƙara yin matsuguni a fuskarta. " Mama don Allah kar ki saka damuwa a ran ki.Girkin ne ya bani haushi saboda na manta na zuba gishiri kuma na zo na ƙara shi ne hannuna ya goce na juye duka." Dariya Mama ta yi ta ce." Juwairiya wacce ta iya girki komai auna wa ake shi ne yau ta yi juye lailai yau hannu ya ƙwace kenan.To ai ni ban ga abin kuka ba sai dai in a kwai abin da kike ɓoyewa." Gaban Juwairiya ya faɗi jin Mama ta na so ta ɗago ta sai ta yi sauri ta tsaida hawayen ba shiri."Iya kan abin da ke damuna Mama kenan haba dole na yi kuka bayan tsawon jinya da kika sha a ƙasar waje,yau za ki ci girkina ga shi hannu ya ƙwace min." Mama ta koma ta zauna ta ce " To ba sai ki ɗora wani ba."Ai da sauri ta miƙe tare da faɗin."To." ganin yadda Mama ta kafe ta da ido haka kawai sai wani irin kunya ya lulluɓeta har ta ji ta kasa haɗa ido da ita. " Ok bara na je na ɗora na san yunwa kuke ji."Ta faɗa ta na shafa kan Ibrahim da ke zaune ba ya tafiya saboda likita ya ba shi lokacin da zai fara tafiya. "Juwairiya dawo magana zan yi dake."Mama ta faɗa tare da lumshe idanunta da su kai mata nauyi. "Mama don Allah bari na gama girkin kar yunwa ta dame ku ga Ibrahim har ya fara yaushi." Ta ce cikin in ina ta na son ta kauce ma idanun Mama." Kar ki damu da dawo kawai akan mutumim nan bawon Allah da ya ke taimakonmu,na ke son mu yi magana ni fa kullum tunanin sa nake yi ga shi ya ƙi bayyana kan shi,bare mu yi masa godiya an ya saboda Allah yake mana ni fa na fara shakku a raina.". Juwairiya ta firgita da maganar da Mama ta yi mata ta san da ma dole ta yi mata waɗannan tarin tambayoyin game da kuɗin da A.m yake kashe musu ya wuce misali. Ganin Mama ta fara zargi a zuciyarta sai ta daure ta kauda duk wani tsoro da shakku a ranta,ta kalli Mama da natsuwa ta koma ta zauna ta ce." Mama ki yi masa kyakykyawar fahimta kin san irin tarin kuɗin da suke da shi,sannan da zai cuce mu kuɗin ba zai biyo ta hannun Baba Sani ba.Don Allah ki kauda komai a ranki kuma in ma sabon gidan da ya gidan da ya siya mana ne ba kya so sai a mayar masa." Da ƙwarin gwiyarta take magana saboda ta yi tunanin yanzu ita ace za ta din ga buga ƙwallon a raga kuma in ba ta jajirce ba Mama za ta ɗago ta wanda hakan zai ɓata shirin su. "Lamarin duniya a kwai tsoro ke yarinya ce amma ba zaki gane ba kuma da kike maganar Baba Sani ai duk kanwar ja ce,ke sheda ce akan halin sa kin san irin halaccin da mahaifin ku ya yi mishi amma ya manta ya kasa tallafar rayuwarmu,shirun da kika ga na yi hakan ya samo asali ne saboda alƙawarin da na yi ma mahaifin ki wanda ya tilasta min na yi masa daga baya na zo ina dana sani,amma wallahi kin ji na rantse da ban yi ma mahaifin ki alƙawari ba da na ɗauki mataki akan yadda ya hana rayuwarmu saƙat." Ta ce ta na kallon Juwairiya da ta firfito da idanunta ganin yadda Mama take magana, saboda tsawon rayuwarta fa ita ba ta taɓa jin ta ɗaga harshe ba,sai yau lamarin ya matuƙar razana ta har ta fara dana sanin amincewarta don da wuya shirin su ya tafi ga shi A.m ya kashe kuɗin sa. Mama ce taci gaba da magana ganin ta yi shiru ta na zare ido sai ta ce." Wa ya sani ko kuɗin kammu muke ci." Yayin da tsoro ya ƙara kamata tuna yanzu duniya ba gaskiya. " Da ma Baba Sani zai yi miki bayani Mama ni ne na ce ya bari ki ƙara samun sauƙi Wato shi mutumim da yake taimaka mana ya auri matarsa wacce ƴar majalisa ce. To gabaki ɗaya rayuwarta ƙasar waje ta yi karatu,ta samu gata sosai wanda hakan yake saka suna samun saɓani ga shi ba ta iya girki ba komai ba ta yi." Ta yi shiru ta na son ta ji ko me Mama za ta ce amma sai ta ga ta tsaya ta harɗe hannunta a ƙirjinta ta na sauraren wannan tatsuniyar ita tunanin ta to meye haɗin ta da wannan dogon labarin wanda take ganin ina ruwan ta da labarin sa. Juwairiya ta rasa in da za ta kama ta ci gaba da zancen a wannan lokacin ji take kamar ta ɗora hannu ta yi ta kuka ganin yadda Mama ta kafe ta da ido. " To saboda wannan ne ya na son a koya mata abubuwa da girki yake son ya s..."Juwairiya da ta ci gaba da magana sai kuma ta tsaya tare da sakin kuka wanda hakan ya ta da hankalin Mama, amma sai ta yi shiru ta na kallonta yadda take kuka mai sauti. " Shi ne yake son mace wacce za ta zauna a gidan shi na shekara ɗaya ta koya ma matarsa girki da yadda ake kula da gida,na tsawon shekara ɗaya kuma duk wacce ta amince za ta yi zai tallafa ma rayuwar su,ban san tsinannen da ya gaya masa halin da kuke ciki ba har ya zaɓi Juwairiya a matsayin wacce za ta yi,don wallahi da na sani ba zan bari ba ai gara na saka ƴata."Muryar Baba Sani suka ji ya na magana a bakin ƙofa. Mama ta ji wani irin juwa ya kamata murna za ta yi ko farin ciki amma kuma Juwairiya ta din ga yawon aikatau kenan?Juwairiya a yanzu ya kama ta ace ta na ɗakinta,sai dai kuma mutumim ya yi hidima ga rayuwar su wanda wani ɗan'uwan ka ba zai iya haka ba. Ta buɗe baki da nufin ta nuna rashin amincewarta amma sai ta kasa saboda ya yi musu halacci haka kawai sai ta ji ba za ta iya musawa ba,amma ranta ta saka dole in Juwairiya ta gama aikin ta za ta yi aure da irin mijin da take so ko da hakan zai saka ta karya alƙawarin da ta yi ma marigayin mijinta ne don za su raba abin faɗi ƙila kutu za ta raba su,saboda haƙurin abin da yake mata wanda sakamakon hakan ya sa zuciyarta ta buga. Juwairiya ta shiga tsananin mamaki gani Mama ba ta ƙara ce mata komai ba ta takure gefe zuciyarta cike da tashin hankali,wani irin zazzaɓi ya rufe ta sai makyarkyata take hawaye ya na zuba a ƙuncin ta. Mama ta yi jim da kofi a hannunta bayan ta ba ta magani tasha." Ni fa hankalina ya tashi Juwairiya ke ma kin yi gangancin karɓar wannan kwangilar duk da hakan ya tseratar da ke da ga auren wannan tsohon,amma kin manta irin wulaƙancin da dukan da kika sha a dalilin aikatau." Juwairiya ba ta ce komai ba sai hawaye da suke shatata fuskarta. Mama tace ta rasa wani irin tunani za ta yi akan maganar aikin Juwairiyar da za ta yi,kuma da ta nemi sanin waye hatta ita Juwairiyar ba ta gaya mata ba sai wani lulluɓin biri suke yi wa kare an ya? Akwa lauje cikin naɗi!Ta faɗi a zuciyarta cike da shakku. Ta zauna a gefen gadon da take kwance tare da janyo mata bargo." Allah ya baki lafiya."Ta ce tare da zabga tagumi. Wa su irin zafafan hawaye suka wanke mata fuska sai ta canza kwanciyarta saboda ta juya ma Mama baya." Ki yafe min Mama na san ban yi miki adalci ba,amma na yi hakan ne saboda na ceci rayuwar ku duk da hakan ni zai kai ni kushewata saboda ƙara kusanci da na yi da shi,shi zai jagoranci ruhina zuwa mutuwa.Allah na roƙe ka ka cire min son sa a cikin zuciyata." ***** A.m zaune a tanƙamemen falon sa da remote a hannun sa gefe kuma Zainab ce take aiki da computa da ta ɗora a cinyarta,saboda gwanancewa da aiki da ita da ta yi ba tare da ta kalle abin da take daddannawa ba take aikin ta,yayin da hankalinta ya na kan A.m da yake ta jan tsaki ya na juyi a kujerar. Talatu mai aiki wacce take sabuwar ƴar aikin da Mominta ta kawo mata saboda halinta sam ba ta daɗewa da me aiki.Ita ce ta yi sallama ta shigo idanunta akan A.m saura ƙiris ta yi ɓari amma sai ta ije ta ci gaba da kallon shi. A.m wanda da ma hanya yake jira miƙewa ya yi ya kwasa mata mari ya ce." Wai ke wace irin mayyar yarinya ce ba na hanaki kallona ba!Banza ƙatuwa da ke maza fice min daga falo! Kuma yau zaki bar gidan nan." Da sauri ta ruga ta na shafa gurin da ya mare ta don ta ji zafi sosai jikinta har rawa yake saboda ita duk ta gan shi,sai ta ji ta na son ya kula ta duk da ta san shi ba san ta bane amma ya na da kyan da duk mace za ta yi mafarkin samun shi. Zainab kuwa tsaki ta yi a ranta ta ce." Haka kawai duk ka tsani ƴan aiki kullum cikin canza masu aiki muke wannan karan sai dai ka yi haƙuri amma ba zan canza ba." Juya wa ya yi ya kalli Zey da ta daina aikin da take yi ta na kallon shi ya ce." Allah na tsani yarinyar nan ke duk masu aikin ki dangin mayu kike ɗauko wa,gaskiya ki sallame ta ni sam ma abincin ta ba ya min daɗi." "To ni ya kake son na yi ko ni kake son na dun ga yi maka girkin?"Ta ɗan saki dariya ta ci gaba da magana ta na ce wa." In haka kake tunani gara ma ka cire har na yi aure ban taɓa shiga kicin da nufin na yi girki kai ko ruwan zafi ban iya dafawa ba,ka ga ya zama dole ka ci na ta in ba so kake ka ɗauko kuku namiji ba wanda da ma kafiyarka na tsiya da baƙin kishi ya hana ka,amma ni ban ga dalilin da ya sa ka za ka ƙi ɗaukar kuku namiji ba a gidammu su suke girki ni kai na na gaji da cin abincin masu aiki." Wani kallo ya watsa mata ya ce." Zainab ki kiyaye ni da maganar kuku a haka yadda kike zama kusan naked ne zan ɗauko kuku,matan ma da suke kallon ki ni na san baƙin cikin halin da nake shiga sai dai na lura shashasha ce ke kin ɗauki rayuwar yahudu da nasara ba ki san darajar kan ki ba." "To aiko ka na ruwa wallahi tunna duk yawon duniya da ka yi baka waye ba ni ban ga dalilin da zai saka kasa na din ga ɓoye kai na ba kamar wata ƙonannniya." Ta ba shi amsa cike da gatsali ta na girgiza ƙafa. " Ƙaryar iskanci kike tunna kin nuna ba za ki canza ta ba sai dai ki zaɓa ko aikin ko ki zauna ki rinƙa dafa min abincin da kanki,tun da na tashi na ga iyayena suna girki a gidammu amma ke saboda sakarci ki ce ba ki iya ba.Ki na ganin ƙannina duk sun iya girki ke na rasa wani irin tarbiya kika samu. " Ta katse ta hanyar ɗaga masa hannu ta ce."Ka dakata kar abin ya zama cin fuska kuma da kake wannan maganar ai ka san wacce kake aure da matsayin ubana." "Dallah rufe min baki ke ma kin san sai dai ki yi min gori na mahaifin ki ya riƙe muƙami,amma ba wai ko kun fi mu kuɗi ba iya tarbiya ne kawai da muka hora su da shi, saboda arzikin da muke da shi bai saka ya sa mun yi watsi da al'adarmu ta yi ma miji girki." Tsaki ta saki ta ci gaba da aikinta ta na faɗin." Ai sai ka yi ba ka da aiki ne ni ina da abin yi kamar yadda ka gani."Ta ɗan ƙara sakin ƙaramin tsaƙi a hankali ta ce." Jarababbe kawai." Ya kalle ta ya na baƙin cikin halin ta don shi bai yi tunanin halinta haka yake ba."Mu zuba da ni dake tunna baki da mutunci kuma da ga yau in kika ƙara zuwa wani guri bayan akin ki Allah y...." Da sauri ta tashi ta waurgar da ƴar mini system ɗin dake hannunta tare da faɗawa jikin shi ta rufe bakin shi jin zai kafa mata dokar fita,in ta bari hakan ya faru ita kuwa ya za ta yi da zuwa pati da yawaon da suke da ƙawayen ta. " Haba mai sanyina don Allah ka yi haƙuri karka faɗi haka kai ma ka san wallahi ban saba zaman gida ba,in ka hanani fita ya zan yi kuma ka san kai ma zaka saka Allah ya yi fushi da ni ne,amma na riga na saba da yawo ba zan iya zama guri ɗaya ba ko da ka rantse." Ya kalleta da mamakin abin da ta ce ba yan Allah ya jarabce shi da sonta ya riga ya rufe mishi ido da sai ya ce bai yi dacen macen ƙwarai ba,amma so makoho har zuciyarsa ta sauko ya kalleta da shauki ya haɗa hannunta duka ya na murxawa da hannunsa don ya na ganin damar sa ne yanzu ya ce. " Na lura don kin ga ina son ki shi ya sa kike wahalar da zuciyata Zey amma ba komai ina fatan Allah ya saka miki irin son, da nake miki a zuciyarki nawa zaki gane halin da na ke ciki."Ya faɗa ga mamakin ta sai ta ga yana hawaye. Hankalinta ya tashi ta ƙara maƙalƙalewa a jikinsa ta na share masa hawaye saboda jikinta ya mutu murus da son sa. " Ni ma fa ina sonka hubby kai ɗin ne ka cika faɗa ba ka min uzuri duk da ƙoƙorina da nake kuma ka san yanayin aikina. Janye hannunta ya yi akan fuskarsa aran sa ya na faɗin." Na sani amma kuma hakan bai hana ki fita ba." A fili kuwa sai ya saki ɗan murmushi kamar ba shi ya gama hawayen baƙin cikin Juwairiya za ta shigo duniyar auren su ba wanda ya ɗora laifin duk akan Zainab amma sai ya ce. " To ki canza me aiki ni bana son wancan yarinyar k..." Ta ƙatse shi ta na faɗin ."Na ji zan canza amma kuma Momi ta ce in dai muka kori wannan ba za ta ƙara ne mo mana mai aiki ba tunna ba ni da haƙuri." " Kar ki damu dama tuntuni nake son na tambaye ki na yi ma Atine mai aikin gidammu ta kawo mana macce matashiya wacce ta iya girki sosai,in kin bani dama sai na gaya mata ta nemo mana kuma ba za'a daɗe ba, za ki ga ta kawo mana tunnna ita ma ta na irin kawo su kusan family mu ita take kawo musu masu aiki." Ya ce tare da rungumeta ya na goga fuskar shi a na ta."Ok ba komai sai ta kawo mana amma ba za mu kore ta ba sai an kawo mana wata." A.m hamkalinsa ya kwanta ganin bai sha wahalar samun haɗin kanta ba miƙewa ya yi ya shige ɗakin sa,ya gallah wanka ya fice kai tsaye gidan su ya wuce ya sami Atine mai aiki ya ce." Ina son in kika tashi zamu fita da ke zuwa wata unguwa amma ya zama sirri a tsakanimmu in kika yi min hakan zaki samu alkhairi." "Ka faɗi ko mene ne in sha Allahu zan yi maka." Ta ce cikin mamakin in da za su kuɗi ya zaro masu yawa ya ba ta.Atine jikinta na rawa ta karɓa ta na kallon shi." Wata yarinya nake son na nuna miki ki kaiwa Zainab a matsayin ƴar aiki.Shikenan buƙata ta kuma ba na son kowa ya sani kawai ki bar shi a matsayin ke kika kawota." Duk da mamakin maganar da ta yi amma tunanin ta bai kai ko ina ba,ta amince masa akan sai ya zo daga ƙarshe watsar da tunanin ta yi don ta san ya wuce ƙarfin ya kula ƴar aiki ,kasancewar yadda ta ga ya na hantarar su bare ma ta yi tunanin wani abin. ******** A ranar da Juwairiya za ta tafi hankalinta ya tashi matuƙa wanda da Mama ta so taƙi kan ta din ga kwana duk da a kwai nisa sosai ta so Juwairiyar ta din ga zuwa ta na kwana har shekara ɗayan ta yi,amma sai Baba Sani ya kafe dole sai dai ta din ga kwana tunna kuɗi ya biya. TO MASU KARATU GA DAI AMARYA JUWAIRIYA ZA TA TAFI GIDAN ANGONTA KO YA ZAMAN SU ZAI KAYA ?SAI KU CI GABA DA BIBIYAR LINTAFIN SAKACI KO HALIN MAZA. TAKU JAMILA LAWAL ZANGO ƊUBBIN GAISUWA GARE KU SABODA COMMENT ƊIN KU YA NA SAKA NI NISHAƊI. MAMAN SUDAIS AISHATU MINNA FATIMA ZARA JOS SAHURA NURA RABIN RAINA NABILA MAMAN SAFWAN HAMDIYA UMMU ABDULHAKIM Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Mu haɗu a shafi noma sha shidda.Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 17* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM Juwairiya ta yi tsuru da jakarta ta na kallon Mama da ke tsaye a gefen ta riƙe da hijabin ta a hannu ta na ƙoƙarin saka wa a kanta sai ta ji hawaye sun ƙara wanke mata fuska,ta share da sauri domin Mama tun ɗazu take mata ƙorafin kuka yanzu ma da taga ta na hawaye sai ta yi tsaki ta ce." Gaskiya kukan nan na ki ya fara siƙe ni Juwairiya na ga ke da Baba Sani kuka shirya hakan,amma kin bi kin dame ni da kuka in da kin san ba za ki iya ba uban wa ya ce ki amince." Sai ta rungume Mama ta ƙara fashewa da kuka ta na jin wani irin baƙin ciki da fargaba ga gabanta da yake faɗuwa a kai akai don ji take kamar ta ce a ta fasa. "Mama akan ki sami lafiya na amince amma ki yafe min in na ɓata miki na ga kamar ran ki ba ya son na tafi."Ta ce da ita cikin hawaye fuskarta ta tura shi a jikinta. " Ki na ganin in da bai yi wa rayuwarmu halacci ba wallahi Baba Sani bai isa ya saka ki ƙara wani aikatau ba,don kullum na yi sallah sai na roƙi Allah ya raba ki da shi saboda irin cin mutuncin da kika fuskan ta." Share hawayenta ta yi ba ta ce komai ba ta shafa kan Ibrahim tare da riƙe hannun sa suka fito tare. " Mama ji nake kamar kar na tafi sai kun tare a sabon gida."Ta faɗa tare da fuska. Mama ta kalle ta ta ce " Gara ki tafi Juwairiya saboda yau aka yi zaki tafi kuma kin ga mutumim nan ya yi ma rayuwarmu hallaci wanda dalilin haka ina matuƙar girmama shi." " Humh." Ta ce a cikin zuciyarta sannan ta ɗora da ce aranta jin abin da Mama ta ce." Da kin san abin da ya ƙulla da ba ki girmama shi ba,shi ɗin macuci ne sosai ya fiye son kan sa da rayuwar matar sa da kin san dalilin da ya sa ya yi mana wannan abubuwan da kin tsane shi har iya ƙarshen rayuwar ki." A lokacin da suka yi nisa mama ta kama hannunta ta riƙe sai hawaye ta ce." Juwairiya ki riƙe mutuncin kan ki a duk in da kike kuma, duk abin da ki kai kin san Allah ya na kallon ki mutunci na ƴa mace shi ne zai zama ado a rayuwarki,ba wai ina zargin ki ba ne a' a ina miki nasiha a matsayina na uwa wacce ƴarta za ta yi nesa da ita,sannan ya zama dole na saki a hanyar daidai don kar ki ga mutum zai aikata abu a ɓoye,ya na tunanin ya kauce idon mutane bayan ya manta mahaliccin sa ya na ganin duk abin da ke" Jikin Juwairiya ya ƙara sanyi kamar ƙanƙara haka kawai sai ta ji ta fara tsarguwa yadda Mama take ta mata wasu irin maganganu, wanda take shan jinin jikinta don in ta yi mata irin waɗannan maganganun ko kallonta ba ta iya wa. Yanzu haka ta kasance ta yi ƙasa da idanunta ta ce."Mama an ya ba zan." Katse mata hanzari ta yi tare da taran ɗan mashin ta karɓi jakarta da ta riƙe da ta yi tsumu ta ɗora a kan mashin ɗin sannan ta kalle ta ta ce." Ma za ki tafi Allah ya tsare da kin sami lokaci ki leƙo." Juwairiya ta haye mashin jikinta babu karsashi hawayen fuskarta sun ci gaba da kwaranya yayin da ɗan mashin ɗin ya fara tafiya a kan titi. Wani ƙarin abin da ya ƙara zubar hawayenta cikin ƙunar rai da ta tuna yau gidan mijinta za ta akan mashin da ƙullin kaya a jaka, ba tare da an kawo mota kamar yadda ko wace mace mai gata wacce mijinta yake son ta ake mata,duk lokacin da ta tuna wannan sai ta ƙara sakin kuka har ɗan mashin ɗin ya juyo ya kalle ta ya na faɗin." Lafiya Hajiya?" Amma ba ta kula shi ba kuka sosai take har suka isa gidan Atine,a lokacin da ta isa ba ta nan sai da ta jira ta sannan ta dawo sallah ta yi suka kama hanya. Wani irin faɗuwar gaba take yi har sai da ta dafe ƙirjinta.Kasancewar a kwai tazara sosai da gidan Atine sai da suka hau nafe. A lokacin da suka iso ƙofar gidan da Juwairiya ta saka a ranta na A.m ne hankalinta ya yi matuƙar tashi matuƙa gaya.Kawai sai ta ji ƙasa ba za ta iya ɗaukar ta ba ta sani A.m suna da kuɗi amma ko kaɗan ba ta taɓa tunanin haka gidan sa yake ba. " Dole ka ce baka sona kuma ba zaka taɓa sona ba saboda ba mu dace ba ni kai na sheda ne." Ta furta cikin karayar zuci don ta san ya fi ƙarfinta na har abada.Gaskiya fasalta gidan sa abu ne da zai ɗau lokaci saboda gida ne mai matuƙar girma, da tsari ga shukoki masu kyau waɗanda suka ƙara ƙawata gidan,don haka mai karatu na bar maka aikin tsara fasalta iya tsaruwan gidan,A.m a hannun ka don in na ce zan yi zan ɗauki lokaci ni dai na yi wa gidan suna da aljarnar duniya. Lokacin da suka shiga cikin falon Juwairiya ku san neman numfashinta ta yi ta rasa, don barazanar shiɗewa yake yi saboda tsaruwar falon da ke ɗauke da ku san set huɗu na kujeru mabambanta. Duk lokacin da ta ƙara taku a cikin falon zuciyarta karaya take da son A.m da ya shige zuciyarta saboda ta haƙiƙance ma kanta da yaudarar kanta take yi A.m babu abin da zai yi da ita. A ƙasar kafet ɗin dake zagaye a tayas ɗin da ya sha guga ya na ta ƙyalli da ɗaukar ido ta zauna tare da rintse idanunta,hakan ta ji ba ta son idanuwarta su yi tozali da matar A.m don ta san zuciyarta za ta buga. Atine ta zaro wayar ta ta yi kiranta sai dai cikin takaici ta ije wayar ta kalli Juwairiya ta ce." Ba ta dawo aiki ba amma ta ce mi jira ta za ta duba patient ta dawo." Sai Juwairiya ta sauke idanunta daga kallon Atine saboda kiran sunan ta da ta yi,ta ci gaba da kallon ƙasa yayin da zuciyarta yake bugawa tamkar za ta fito. Kusan waya biyu suka shafe suna zaune a falon sai kowa shiru jefi-jefi Atine take sakin tsaki,amma Juwairiya iya tsawon lokacin ko tari ba ta yi ba sai sautin bugun zuciyarta da yake ta ƙara tsanantuwa. Ƙwas!Ƙwas!!Ƙwas!!! Suka ji sautin takalmi wanda Juwairiya ta sadaƙar da matar gidan ce ta dawo,bayan iya tsawon lokacin da ta ɗauka ta shanya su zaman jiran ta kamar wasu dussa. Bugun takalmin Zainab ya na tafiya tare da bugun zuciyar Juwairiya da take jin tamkar za ta fito,ta rintse idanunta ta na burin a ce ba Zainab ɗin ba ne take ƙoƙarin shigowa,domin tsoro ya bayyana a fuskarta sai take ganin kamar za ta gane dalilin shigowar ta gidan. Koda ta shigo waya take yi zama ta yi ba tare da ta ce musu komai ba ta ci gaba da wayar ta. Juwairiya ta kasa ɗago idanunta ta ga matar mijinta na wucin gadi wanda take cikin zuciyar sa yake fifita ta fiye da komai har ya zaɓi ya cutar da rayuwarta duk akan ya farnta mata. Amma idanuwanta sun kasa haɗa ido da ita hasalima ko ɗagowa ba ta yi ba, duk da ta fahimci ta gama wayar da take yi bayan ta ɗauki rabin awa. " Am Atine na ɓata miki lokaci ko?" Tambayar da ta yi mata kenan ta na kallon matar da ta kusa jika da ita a yatsine. " Ba komai Hajiya dama me aikin ne da muka yi magana da megidan ki na kawo miki."Ta ce mata ta na kallonta. " Ok." Abin da tace kenan ta janyo wayarta ta kunna data yayin da tsaƙwanni suke ta shigowa ta na duba wayar har na tsawon lokaci,daga bisani ta kashe ta kalle su duka daidai lokacin da Juwairiya ta yi sa'ar yaƙar idanunta, na tsoron haɗa ido da ita da suke ta kalle ta, don ta ga wannan mace mai ji da kanta da wulaƙan ta mutane. Karab idanun su duka suka haɗu da juna Juwairiya da ƙyar ta yi nasarar daƙile gangar jikinta da yake shirin tashi da zura da gudu ganin kalar matar da A.m yake aure. " An ya ƴar Nigeriya ce?" Ta tambayi kanta cikin tsananin mamaki domin yanayin ta da kyanta surar ta gabaki ɗaya ya tsorata ta,saboda hasken ta har wani kashe ido yake yi sosai da ta yi duba ga kalar fatar jikinta sai ta ga ta yi baƙa wuluk kamar gawayi,duk da ya ba kyan fatarta da ƙawayenta suke yi. Zainab kuwa wani irin tsanar ta ya shiga ranta haka kawai sai ta ji ba ta kwanta mata ba,ba wai kuma kyan da ta gani ba ne ya tsorata ta a'a ita sheda ne akan A.m ko ƴan mata larabawa za ta kawo mishi ba zai yi dubi garesu ba, duba ga yadda ta sha wahala kafin ya amince da ita sannan tun da su kai aure ba ta taɓa jin ya yi maganar wata ko wata ta kira shi ba. Amma sam Juwairiya ba ta yi mata ba saboda daga ganin ta za ta yi munafunci ganin yadda take duƙar da kanta ƙasa-ƙasa. " Atine an ya wannan ƴarinyar kina ganin ta yi?Kin san A.m a kwai shi da ƙyanƙyani ji yanayin shigar ta da wani zumbulelen hijabi kin san ya na da tsafta, kar ta zo ta na ma na girki ya na shiga sannan wallahi zubin ta bai yi min ba don ni na daina ɗaukar ƴan aiki gidahumai ƙauyawa,bai gaya miki ɗakin sa da komai na shi ita za ta din ga gyarawa ba?A can zo wata kawai." Juwairiya ta yi ƙasa da kanta jin abin da ta faɗa duk da ranta ya ɓace,amma ta yi tunanin fiye da hakan a gurin ta saboda ta karance ta tsaf mace ce mai ɗagawa da nuna ta isa,musamman ga talakawa ƙasƙantu irin ta. Sai kuma ta ji daɗin abin da ta ce ranta ya yi fari ko banza ba za ta zauna agidan wannan mai kama da canis ba sai ya zo ya san yadda zai yi da ita,ai dama abin da ya shirya a yi mata kenan shi ya sa ya aure ta ya kawo ta kuma ita ta sai ma kanta don in da ƙwaɗayi a kwai wulaƙanci! Atine ta ji jikinta ya yi sanyi sosai har ta fara tunanin in da za ta samu kuɗin A.m ta mayar masa don ya na ba ta ta kai ma mai kujeru akan bikin ƴarta marainiya wanda mijinta ya mutu ya bar mata. Sai ta ji kamar ta ce ai mijin ta ne ma ya buƙaci ta kawo ta,amma da ta yi tunanin ba ta san dalilin da ya sa ka shi ya buƙaci hakan ba sai ta kama bakinta ta guntse ta ce." Ai Hajiya Juwairiya a kwai aiki da tsafta sosai ta yi aiki da dama shi ya sa na kawo ta,kuma za ki ya ba sosai sai kin gode min,amma ki gwada ta in ba ta yi miki ba sai a kawo wata.Kin sai an gwada akan san na ƙwarai. " In ko haka ne ta na buƙatar gyara don sai na canza mata tufafi ba za din ga mana girki da shi ba,ni ban san daƙiƙanci da rashin wayewa." Ta ce ta na kallon Atine da ta yi hamdala a ranta jin ta amince da ita,sai kuma ta kalli Juwairiya ta na mata kallon tsaf irin na ciki da waje har mutum ya gano munin ka. " Ina yini" Juwairiya ta ce mata ganin ta na mata kallon ke ba kya gaisuwa ne. Ɗauke idanunta ta yi ba tare da ta amsa gaisuwar ba duk da ta tabbata ta ji gaisuwar da ta yi mata. Sai ta miƙe ta kalli Atine ta ce."Wash na gaji ba ri na shiga ciki."Har ta fara tafiya sai ta tsaya. " Ina fatan Atine ta yi miki bayanin aikin da za ki din ga yi a gidan nan? Ina da da tsohuwa da take share-share da ƴan abin da ba'a rasa ba.So ke aikin ki kula da ɗakina da na mijina da wankin underwears ɗin mu da girki.Kasancewar ba zama nake ba don yanzu waje zan fara fita na baki amanar gidana, da mijina duk sanda ba na nan ki rinƙa kula da abincin sa ruwan wankan shi kayan sawan shi da wanda ko ina nan ke zaki kula da wannan." Ta ɗan numfasa ta ɗora da ce wa " Game da kayan sawar shi irin wanda yake so ina fatan ke ba daƙiƙiya ba ce kuma ba' a yi asaran tara ba na yi mishi time table a ɗakin sa na kayan da yake saka wa sai ki din ga dubawa ki na cire masa." Wani iri Juwairiya ta kanta ya yi mata take wani irin zafin kishin mijinta A.m ya taso ya mamaye zuciyarta,har ya hana ta jin abin da Zainab take ce wa sai kuma tausayin sa ya kamata matuƙa jin irin ballagar mace da yake aure. Ta ƙara rintse idanunta ta na jin kishin iya adadin masu aikin da Zainab ta yi waɗan da suka gama kallon mata miji,kuma a haka yake iƙirarin ya na sonta lallai ta yadda so halitta ce kuma makaho ne. " Ki na ji na ina magana kin yi banza da ni!" Zainab ta daka mata tsawa ganin ta tafi duniyar tunani. " Yi haƙuri ina sauraren ki ne." To ba na son shashanci in ina magana duƙar da kunnin ki saitina za ki yi kuma duk na yi magana ki ɗaga kanki." Ta ce sannna ta ci gaba da tafiya ta na faɗin." Atine ba ri na ɗauko miki abu." " Kut! Na shiga uku A.m ya san halin matar sa ya kawo ni cikin gidan nan." Ta faɗi ta na jinjina kanta tare da tunanin irin zaman da za su yi da ita .A jiyar zuciya ta saki mai ƙarfi jin sakacin da Zainab ta yi da mijinta. Kuɗi masu yawa ta miƙa ma Atine wacce ta sandare da jiranta,saboda har wanka ta yi ta saka kaya shara-shara wanda al'dar ta ce zama da irin wannan kayan a gida. A lokacin Juwairiya ta gaji har ta fara gyangyaɗi ga yunwa dake ta ƙwaƙwular cikinta. " Kin ga na jima ban dawo ba ruwa na watsa ga shi ki yi haƙuri." Ta ce da Atine sannan ta kalli Juwairiya ." Ke ki tashi ki fara aiki kuma na manta ban gaya miki ba! Ba na son raini da ƙazanta." Sai kuma ta ƙwala ma Baba mai aikinta kira da gudu sai ga shi ta ƙaraso mari ta zabga mata.Banza daƙiƙiya ba na ce miki za'a yi sabuwar mai aiki ba? Da kika gan su sai ki fara nuna mata aikin gidan ko sun yi miki kama da irin baƙin da zan yi ne?"Ta tambayeta ta cikin zafin rai. "Ki yi haƙuri Hajiya ai ba ki bani umurnin haka ba kuma..." " Rufe min baki banza maza ki je ki nuna mata." " Allah ya huci zuciyar ki." Ta ce tare da kallon Juwairiya sannan ta ce ." Mu je na nuna miki aikin." Juwairiya da ta yi mutuwar tsaye ta dafe ƙuncinta don gani take kamar ita ta mara.Zainab ciki ta koma tare da ɗaukar wayarta ta yi kiran rabin ranta. Tsananin tashin hankali Juwairiya ta shige shi ji ta yi tamkar ba za ta iya rayuwa a cikin gidan ba,a tare suka share hawaye da Baba suka kuma kalli juna. " Ki yi haƙuri Baba haka matar gidan take miki?Gaskiya ba ta da mutunci a matsayin ki na wanda kika haife ta.Wai mai masu da shi suka ɗauki talaka shi ba mutum ba ne don kawai ya na nema a ƙarƙashin wani sai wulaƙanci." Baba ta share hawayenta ta kama hannun Juwairiya ta ce " Humh ba zaki gane ba ne!Hajiya Zainab ta wuce tunanin ki ina tausaya miki wallahi Allah ya sa kin iya girki." Ta ɗan ƙara matsowa kamar ta na tunanin Zainab za ta yi musu laɓe ta ce." Ina gaya miki wacce ta kora ta kawo ki da ta yi abinci juye mata ta yi a jikinta,ta rufe ta da duka wai mijinta ya ce ba ta iya girki ba.Ni fa ban taɓa ganin mutum irin maigidan nan ba,ya tsane mu sai dai shi baya duka." Duk da Juwairiya ta san matsayinta a gidan amma sai da gaban ta ya faɗi ras!Shiru ta yi ba tare da ta ce komai ba. Da Juwairiya suka shiga kicin kusan ruɗewa ta yi kamar za tai hauka,irin dukiyar da aka narka da kayan na'ura,duk da ta yi aikatau gidan masu kuɗi ta san yadda ake sarrafa na'ura amma a ranar yar ƙauye ta dawo. Abinci mai rai da lafiya Juwairiya ta shirya sannan ta shiga ɗakin da aka ba ta wanda Zainab ta yi mata umurnin duk ta yi girki ta yi wanka. Juwairiya ta da fari kasa amfani da kayan bayin ta yi sai daga baya a hankali ta fara gane yadda ake amfani da shi bayam ta ɓata lokaci ta na ƙauyanci. Juwairiya ta yi mamakin irin kayan da ta jibga mata da sunan ta dun ga amfani da shi,haka dai ta shirya ta na ta tunani barkatai a ranta yayin da kewar su Mama ya kamata, matuƙa har ta ji hawaye na zuba a ƙuncinta. Juwairiya na zaune a ɗakin da ya zama mallakinta bayan ta idar da salla sai kuma ta miƙe da sauri jin kamar Zainab na kiran ta. Ta na baƙin ƙofar fita daga ɗakin suka yi kicibis da ita za ta shigo." Ke kurma ne ina kira kin yi banza dani." Ta faɗa cikin ɗaga murya." Ki yi haƙuri ban ji ki ba ne." Ta ce ta na kallonta amma kuma a tsorace take saboda kar ta kai mata mari.Tsaki ta yi." Maza ki je ki shirya dinning za mu ci abinci mijina yanzu zai shigo.Kuma ki cire wannan ƙazamin hijabin na ki don na san ina ya gani ba zai iya cin abincin ba." Juwairiya ta ji jikinta ya yi sanyi jin umurnin da ta ba ta domin ba za ta iya fita a haka ba,amma sai ba ta ce komai ba ta saɓule hijabin ta koma ciki. Hankalinta ya kwanta da ta tuna a kayanta a kwai hijabi wanda bai kai wancan tsawo ba,da sauri ta ɗauko ta saka a jikinta bayan ta saka turare kamar yadda ta murceta. Juwairiya na gyara dinning ta ji dirin mota alamun an shigo da mota,gaban ta ne ya faɗi ras! Don jikinta ya ba ta masoyin ta ne ya dawo haka kawai sai ta ji gaban ta na faɗi. Da sauri take shirya dinnnig ɗin saboda ta gama ta kauce ma ganin sa,amma sai kafin ta gama ya riga ya shigo ya na takun sa da sarsarfa irin na ingarmar namiji mai jini a jika. Shigowar sa ya yi daidai da fitowar Zainab daga cikin ɗakinta cikin wata irin shiga ta alfarma,amma fa a gurin sa wanda kuma Juwairiya ta ga bai kamata ta fito da irin wannan shigar ba,sanin a kwai ta a cikin gidan don har tafi shigar ɗazu rashin kyan tsari. Da gudu ta faɗa jikin sa ta na dariya cikin farin ciki. Shigowar sa ya sa Juwairiya ta gane ashe tafiya ya yi saboda direban sa da yake janye da troley ɗin sa guda biyu kuma masu girma. Duka suke dariya sannan suka faɗa kan kujera suna bayyana iya kewar da sukai ma junan su. A hankali A.m ya zura ma Juwairiya ido shi har ya manta sun yi da Atine yau za ta kawo ta.Ya ɗauke idanun sa da sauri ganin Zainab ta bi in da yake kallo. " Hubbina sabuwar mai aikin da Atine ta kawo mana ne,Allah ya sa ta yi maka sai dai na ganta kamar gidahuma ce ko ina yawo da hijabi,amma haka zamu yi haƙuri da ita don gaskiya na gaji da ɗaukar masu aiki." A hankali Juwairiya ta ɗago idanunta ta ɗara su akan A.m duk da ba ta son hakan,amma ta na son ta ji mai zai ce mata. Ga mamakinta sai ta ga ya taɓe bakin sa ya kalle ta kamar ya ga kashi ya ce." Uhm na gan ta sai dai ki yi mata magana ta kiyaye sosai in kuma taƙi dole ki canza wata don kin san halina."Ya ce a taƙaice sai kuma ya canza maganar ya na kallon Zainab ya ce." Na yi missing ɗin ki babyna sati ɗaya da na yi kamar na yi shekara,yanzu haka ma ban gama abin da na ke yi ba na baro A.k a can na dawo na ga kyakykyawar fuskar ki." Ya faɗa kamar zai yi mata kuka yayin da idanunsa suka bayyana hakan ga Zainab da take kallon sa da wani irin murmushi ta na kashe masa ido. " Allah ko zauji ka san ni da kai kamar hanta da jini ne ɗazu ina ma wani operation, ka san Allah saura kaɗan na yanka sa ba in da ya kamata ba kuma fa kai na ke tunani." Dariya suka yi duka ya riƙe hannunta ya ce." Na san za ki yi fiye da hakan akai na amma ki kula rai ya wuce wasa." " Ke banza wawiya!Ba ki da tarbiya ko?Ko baki ko ya a gida ba in ma'aurata suna magana ki ba su wuri maza wuce daga nan stupid kawai!" Juwairiya da ta yi mutuwar tsaye tun lokacin da A.m ya shige ta nemi hankalinta ta rasa ji take kamar ta ruga da gudu ta faɗa jikinsa. Gabaki ɗaya ta manta a wace duniyar take wasu irin zafafan hawaye ta ji ya wanke mata fuska, saboda tsananin son da take masa wani irin kishin sa ya tokare mata maƙogaronta, har ta ji ta na son ta yi aman sa don ta na jin ɗacin sa ya na hawowa bakinta. Muryar Zainab da ta daka mata tsawa ya fargar da ita halin da take cikin da sauri ta ruga da gudu,ta shige ɗakinta har ta na bugewa da bango ƙum!Amma ba ta kula ba don tsoron Zainab take yi sosai a ranta. Ta na shiga cikin ɗakinta ta fasa kuka sai kuma ta toshe bakinta tuna ko a ina take daga ƙarshe toleit ta shige, ta kulle ta ƙara sakin kuka ta na buga kanta a bango amma ba ta kula ba ko kaɗan. " Na shiga uku a haka zan rayu a gidan nan? Na tabbata zuciyata ta kusan kamuwa da hawan jini!Allah na roƙe ka ka yafe min laifin da na yi maka ka haɗa ni da A.m wanda da ma burin sa ya kawo ni gidan sa kishin sa ya yi ajalina!" TO FA JUWAIRIYA AN YA DAI? GARA DAI KI TSAYA A MATSAYIN KI KISAN KE FA AUREN GWANGILA CE AKAN KI AMMA BA MATAR SO BA.INA JIRAN COMMENT TSAKANIN FANS ƊIN ZAINAB DA JUWAIRIYA. TAKU JAMILA LAWAL ZANGO ƊUBBIN GAISUWA GARE KU SABODA COMMENT ƊIN KU YA NA SAKA NI NISHAƊI. MAMAN SUDAIS AISHATU MINNA FATIMA ZARA JOS SAHURA NURA RABIN RAINA NABILA MAMAN SAFWAN HAMDIYA UMMU ABDULHAKIM Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Mu haɗu a shafi noma sha shidda.Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 18* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM Tun daga wannan ranar Juwairiya ba ta ƙara saka shi a idonta ba wanda hakan ya tabbatar mata da tafiya ya yi tafiya, ita ma kan ta mai gidan ba zama take ba tun safe in ta fita sai dare za ta dawo,ta kwashi abincin da Juwairiya ta dafa,wanda tun daga ranar farko ta yi amanna da abincinta mai shigen daɗin tsiya,don ko A.m da ya ci ya yaba sosai ji ya yi abincinta ya yi kama da wanda yake ci a gidan iyayen sa. Rashin zaman mutanen gidan haka ya ba Juwairiya damar sakewa a gidan kamar na ta ba ta da wani matsalar takura. Juwairiya a ɗan zaman da suka yi da Zainab ta gane ko ita wace ce mace mai son hutu da gata,ga shi ta tsani zaman gida ko da ace mijinta na nan ga ta da shegen son ƙwalama kullum ta na yawon siyo kayan daɗi da ciye-ciye. Juwairiya ta ɗauki tsawon wata ɗaya a gidan a cikin wata ɗaya ta ƙara kyau da kuma irin mai da cimar da take yi,ita kanta in ta kalli kanta a madubi sai ta ƙara juyawa ta kalli kanta cikin jin daɗin yadda ta sauya,wanda har take zolayar kanta da in ta je gida Mama ba za ta gane ta ba. Juwairiya ba ta da son jiki ku san duk wani aikin gidan ta ɗauke shi shi ya sa kullum gidan ya ke cikin tsananin tsafta da ƙamshi, ita kan ta Zainab kullum yabawa take sai dai tsabar girman kanta ba ta taɓa nunawa ba. Aiki ɗaya da yake ɓata ranta shi ne gyaran ɗakin A.m wanda kullum ta shiga sai ta yi kuka sosai,musamman da Zainab komai ba ta ɗaukewa sai ita take gyarawa cikin kuka da zafin kishi. Ganin yadda Juwairiya take da hankali da natsuwa ga shi mijinta ya yaba kuma har ya yi tafiya bai ce komai ba,sai Zainab ta ɗan saki jiki da Juwairiya kaɗan duk da ta san rabuwa za su yi saboda ta isa aure,don haka ta yanke shawarar za ta ɗauko yarinya ta haɗa ta da Juwairiya ta din ga koya mata girki da yadda take gyaran gidan,saboda ko baƙi ta yi sai sun ya ba gidanta. Ta na tsaye a kicin ta na tunanin abin da za ta dafa sai ta ji Zainab ta ƙwala mata kira,da sauri ta ruga kamar yadda ta buƙata duk lokacin da ta yi kiran ta. Ba tare da ta kalle ta ba ta na riƙe da jaka ta ci uwar gayu ta ce " Fi ta zan yi yau zauji ya na hanya don haka ina son ki shirya abinci masu daɗi."Fita ta yi ba tare da ta ji mai ta ce ba. Kwan biyu da dawowar shi da rana ta na shirya abinci a falon cikin sauri take son ta yi ta kammala kafin ya fito,wanda ta yanke shawarar haka ya dace ta din ga kauce mishi ƙila zuciyarta ta huta da raɗaɗin son da take mishi. Ta na cikin shirya abinci kan dinning ta ji ƙarar kiran waya ya shigo sai ta shiga dube-dube a tunanin ta wayar Zainab ce ta manta fa ita,don sam ba ta kula da A.m da yake bacci ta bayan ta akan doguwar kujera. Sai dai jin ƙarar wayar ya sa ta gane ba ta Zainab ba ce, wanda kuma haka ya ba ta damar fahimtar a kwai mutum a cikin falon. Kiran wayar ya sa shi juyawa da nufin ya kashe wayar saboda a gajiye yake matuƙa! Kwanan nan sam bai samu ya huta ba,ya laluba wayar sa da nufin ya janyo wayar ya kashe bai jita in da yake tsammani ba,tunawa ya yi da jifa da ita da ya yi lokacin da ya shigo cikin falon. Sai ya buɗe idanun sa a wahalce ya na waigen in da yake jin ƙarar ta amma tsabar gajiya ya saka shi kasa motsa jikin sa ya ɗauko wayar. Ganin haka sai ta nufi in da wayar take ta na neman agaji ta ɗauko masa tare da miƙa masa,yayin da idanunta suke cikin na sa kuma ta kasa ɗauke ƙwayar idanunta ga barin kallon sa. Idanu suka zuba ma junan su na tsawon lokaci wanda hakan ya sa Juwairiya ta rasa natsuwarta,shi ya fara ɗauke idanun sa ya lumshe su. A hankali Juwairiya ta tako ta miƙa masa wayar da ta ƙara rurin neman agaji. Idanun shi ya ƙara maida wa kanta ya na mata kallo ƙasa-ƙasa ya na son ya gano halittarta,don shi zai iya rantsewa bai taɓa yi mata kallon cikakke ya san ya take ba,shi dai ya san ya yaba da ita har ya ji zai iya aurenta matsayin matar da zai iya aure na kwangila ta haifa mishi yaro. Wayar da ta miƙo masa ya kai hannun sa zai ƙarɓa ya haɗa har da hannunta ya na ƙare mata kallo tun daga sama har ƙasa,da sauri Juwairiya ta janye hannun tare da fara tafiya a hankali da nufin tabar gurin don jin wani irin tsau da ta ji jikinta ya yi,yayin da take jin wani ƙarin saƙo daga zuciyarsa ya na aika mata cikin zuciyarta. " Juwairaah." Ya kira sunanta ba tare da ya miƙe ba cak tsayawa ta yi ba tare da ta jiyo ba,haka shi ma ya na kwance ya na kallonta kusan tsawon minti biyu,sai ta jiyo gabanta ne ya buga ras! Da sauri ta ruga zuwa ɗakinta tare da faɗawa kan gado ta saki gwauron numfashi idanunta ta rufe cikin wata irin murya ta ce."Allah na roƙe ka kasa na zama jaruma na gama kwangilata na bar gidan nan kamar yadda na saka ma raina." Ta nisa tare da ƙara juyawa ta kuma ce wa." Haka kawai ka shigo cikin rayuwata ka hana zuciyata sukuni." Idanunta ta buɗe suka tsarƙe a na A.m da yake tsaye a gefenta ya na jin abin da take faɗi,ya kai hannu ya fi sau uku da nufin ya riƙe ta amma sai ya kai ma iska nushi don ya na ganin in ya taɓa wata ƴa mace bai yi wa Zainab halacci ba. Ganin ta buɗe ido sai ya ja baya ya haɗe rai hakan sai ya ɗan tsorata har sai da ta ja da baya ta na kallon shi don ba ta san ya shigo cikin ɗakin ba. " Ji nan Juwairaah! Ko kaɗan kar ki saka a ranki zan iya rayuwa dake kin ga matata kuma iya ɗan zaman ki a cikin gidan nan,kin ga irin tsananin son da nake mata don bai kamata sai na gaya miki zaki fahimta ba,don na faranta mata na aure ki don haka ki kiyaye duk wani abin da zai sa ki yaudari kan ki,don kin san haka ba mai yuwu wa ba ne sanin kan ki ne ruwa ba tsaran kwando ba ne?" A hankali ta ɗaga mishi kai ganin ya tsare ta da ido ya na son ya ji amsar tambayar sa. " Sannan kar ki ɗauka ko na manta dalilin da ya saka na aure ki ne.". Ya juyo ya na kallonta ya ce da ita." Wallahi na rasa yadda za' yi na fara ɗaukar ki a matsayin matata don ba mu dace ba,ni sai yanzu nake dana sanin da idona da ya rufe na yadda na aure ki,amma duk da hakan zan daure na aiwatar da shirina da zarar kin sami ciki na kai ki wani gurin ki haihu na karɓi yarona mu shafe babin rayuwarmu." Ya na kai nan ya fice ba tare da ya lura da kukan da take yi ba na baƙin cikin tsanar ta da ya yi,sai dai kuma daga ba ya ta dai na jin haushin kalaman da ya faɗi saboda duk abin da ya faɗa gaskiya ne,ita ma ta karɓi auren sa ne saboda ta ta ceci ran mahaifiyarta da ɗan'uwanta. Washegari da safe Juwairiya na kwance hayaniyar masu gidan ya tashe su wanda ta kasa gane ko menene,amma ta tabbata ba lafiya ba jin yadda suke magana sama-sama musamman muryar Zainab wacce har kukanta ta ji. Matuƙar tsoro ya kamata ji ta yi ta ƙara mugun tsoron A.m don ba ta san haka yake da tsiya ba. Ta na zaune a ɗakinta ta yi tsumu so take ta haɗa abin karyawa amma ba zata iya fita ba jin yadda suke ta ɗaga murya kamar za su dambace. Mamaki ya kama ta sosai wai masoya ne suke irin wannan faɗar,ganin sun ƙi yin shiru da sauri ta shige kicin ba tare da sun gan ta ba,ta fara ɗora abinci jikinta na rawa gani take kamar a kanta faɗan zai ƙare. Ta na shirya a binci a dinning ta ga A.m da ƙatuwar troley ɗin sa ya na ja, ransa kamar an aiko masa da mala'kan mutuwa, ba tare da ya kalle ta ba ya fice daga gidan. Ba'a jima ba sai ga Zainab da na ta jakar ta na waya bayan ta gama wayar ta kalli Juwairiya ta ce " Ke wai me sunan ki baki gaya min ba?Ko ki na jiran na tambayeki ƙila uwar ki zan ci da sunan." A hankali Juwairiya ta furta." Juwairiya sunana."Yayin da hawaye suka fara turereniya a fuskarta. Tsaki ta saki." ko ma mene ne ni tafiya zan yi kuma ƙasar zan bari, ban ce kije ko ina ba kar a kwashi kayana akai gidan matsiyata,ki kula min da gidana duk abin da kike so ga waya ki kira ni in da matsala." Jefa mata wayar ta yi a jikinta ta fice ba tare da ta yi tunanin za ta iya fashewa ba. Tsananin mamaki ya kama Juwairiya yanzu ne ta gane musabbabin faɗar su.Da sauri ta leƙa ta windo don idanunta su fita da shakkun kayan da ta saka za ta ƙetare wata ƙasa a matsayin ta na matar aure. Haka ta wuni sukuku daga kallo sai kwanciya tunna ba masu gidan da za ta yi musu girki.Da daddare sai ta kasa bacci saboda ita kaɗai ne sai masu gadi,Baba in ta gama ayyukanta gida take tafiya saboda ba ta da nisa sosai da gidan. Kasa bacci ta yi ta na ta juye-juye girman gidan yake matuƙar tsorata ta, sai take ganin kamar wani zai shigo ga ihun karnikan gidan da suka hana kunninta saƙat! Da ga ƙarshe ma tashi ta yi ta ɗauro alwala ta yi sallah sannan ta ɗauki alkur'ani ta na karatun suratul Ali imran don ta samu ta yi bacci. A ƙalla mutane gidan sai da suka yi sati biyu ba su dawo ba.A.m ya fara dawowa ranar talata da rana dama tun da safe Zainab ta kira Juwairiya ta gaya mata zai dawo ,don haka ta shirya abinci wanda Zainab ta saka direba ya siyo duk kayan buƙata na girki. Misalin biyu da rabi ya shigo da jakar shi rataye a kafaɗar sa,sai dai kamar mahaukaci ya shigo saboda zargin sa da yake na Zainab ta yi tafiya zuwa Dubai saro kaya duk da ya hana ta. Duk da cewa ta ji shigowar shi sai ba ta fita ba ta yi zaman ta a ɗaki ta na jan carbi,domin ta sama ma kanta natsuwa. " Ina Zainab?" Muryar sa ta ji lokacin da ya banko ƙofa ya shigo da sauri ta matsa ganin kamar zai kai mata duka lokacin da yake tambayarta. Ba ta ba shi amsa ba amma yanayin da take kallon sa ya tabbatar masa da Zainab ta tafi duk da gargaɗin ta da ya yi,cikin ɓacin rai ya lailayo ashar zai yi ko me ya tuna sai ya fasa ya fita cikin ɗakin da sauri. Juwairiya da sauri ta bi bayan sa saboda tashin hankalin da ta ga ya shiga,abincin da ta girka masa ya yi jifa da kwanonin da suke jere a dinning ɗin,ya zaro wayar sa ya kira ta sai dai har ta gama ringing ba ta ɗauka ba. Jifa ya yi da wayar ta faɗi a kan tayas ta fashe ya dunƙule hannun sa guri ɗaya ya furta." Zainab ki na son sa min hawan jini sai dai wannan karan ba zan ɗauki wannan iskancin ba,ina mijin ki ki tsallake ki tafi wata ƙasa hakan ba zai yiwu ba. Idanun Juwairiya suka kawo ruwa sai hawaye ganin ita kuma haka Allah ya ƙaddara rayuwar ta su dun ga sauke fushin su akan ta. " Ke!" Ya daka mata tsawar da ya firgita ta sannan ya ci gaba da magana da ce wa." Wallahi yanzu jikin ki zai gaya miki dukan ki na yi zaki saka min kuka bayan na gaya miki na tsani kuka a rayuwata,maza fice ki ba ni guri sannan ki ƙara min wani abincin. Hakan ya ƙara saka ta sakin wani kukan tuna yadda ta sha wahalar girkin ya zubar kuma yake buƙatar ta ƙara yi masa. Da sauri ta wuce kicin ta bar shi a falon ya kai gwauro ya kai mari da ga ƙarshe wayar sa ya ɗauka da nufin ya kira A.k,sai dai kuma ya ga aika-aikar da ya yi tsaki ya yi da nufi ɗaki don ya ɗauko wata. Bai jima ba ya fito bayan ya yi wanka ya canza kaya ko kallon abincin da ta girka bai yi ba ya fice daga gidan. A haka suke ta zama na rashin daɗi duk da A.m na buƙatar ya kawo ƙarshen zamanta a gidan amma ya kasa,haka dai yau ya daure da nufin zai yaƙi zuciyar sa don ta bar mishi gidan sa saboda ba ya son ganin ta a ciki. Da misalin biyar da rabi ya dawo gida Juwairiya na falo ta na kallo da ƙaton hijabin ta,ya na hango ta ya tsaki wawan tsaƙi saboda shi haushin hijaban da take sawa yake yi bayan ta san ko shi wanene a gurin ta. " Wawiya ƙazamiya a haka yadda kike ɓoye jikin ki ko uban me take ɓoyewa shi bai ga abin sha'awa a jikin ta ba." Ganin sa ya sa ta miƙe da sauri za ta shige cikin ɗakin ta. "Ke." Tsayawa ta yi ba tare da ta kalle shi ba don ta san wani wulaƙancin zai yi mata. Hararar ta ya yi ya zauna akan kujera tare da ɗaukar remote ya canza tasha,sannan ya kalle ta ya ce " Gidan uban wa za ki saboda dodo ya dawo ko?Wai haka kika ga matan aure suna rayuwa a gidan mazajen su kullum cikin hijabi ke sam baki da wayewa ne?" Juwairiya ta yi sororo ta na kallon shi jin wani sabon salon da ya fito da shi,amma ba ta ce masa komai ba sai kallon shi da take tamkar baƙo a gare ta. " Maza ki je ki kawo min abinci." Ya ce ganin ta kafe shi da ido ba ta san shi ma ransa a ɓace yake maganar ba saboda tsanar ta da yake ji kuma wai ta na matsayin matar sa. Juwairiya ta so ta bi umurni n shi ta cire hijabin sai dai ina sam ba za ta iya ba,don tsananin kunyar shi take da ke,don haka ta ƙi cire hijabin ta ɗauko abincin ta na ije mishi ta ruga zuwa ɗaki. Bayan ya ci abinci ya na zaune a falon har aka kira magariba ya yi sallah bai dawo ba sai da aka kira isha'i,sannan ya dawo gida ya rufe gidan duk da ran sa a ɓace yake akan Zainab kuma ya rantse in ta dawo sai ta ga abin da zai yi mata,amma sai ya daure ya ɗauki wayar sa ya shiga ɗakin. " Ki biyo ni ɗakina kin san ba zan iya kwana a ɗakin ƙasƙantu ƴan aiki ba." Ya fice kallon sa kawai ta yi amma ba ta ce mishi komai ba har ya fita ta gyara kwanciyar ta tare da karanto addu'ar bacci ta janyo bargo ta kwanta. " Wataƙila maganar Baba Sani ta yi tasiri a zuciyar sa ya yadda ba ni da kamun kai ne har yake tunanin na bi shi ɗakin sa a she zai bushe da jira na. Washegari da safe bai ci ko abincin karyawar da ta yi masa ba ya fice daga gidan, don ko da ta gaishe shi harara ya banka mata. Sai abin ya ba ta dariya kawai ta ruga da sauri ta laɓe a ƙofar falon ta na kallon sa har ya fice saboda wankan da ya yi ya tafi da imanin ta. Sakin labulen ta yi ta zauna a falo tare da ɗaukar filo ta rungume a ƙirjinta ta na jin wani irin nishaɗi, don ko kaɗan ba ta yi tunanin rayuwa tare da shi ba ko da kuwa a matsayin matar sa kuma ƴar aikin matar sa. Bai shigo gidan ba sai da daddare tare da A.k suka shigo suna ta hira abin su. A.k na ta baza ido ya gan ta bai gan ta ba musamman da ya ga Zainab ba ta nan,kallon A.m ya yi da yake ta aika ma cikin sa abinci saboda tun zuwan Juwairiya gidan hankalin sa ya kwanta na rashin samun abinci. " Kai wai ina maryar ka ne ?Tun na yanzu madam ba ta nan na san ƙila an samu baby?" Ya faɗa ya na kallon shi ya na dariya tare da kai mishi duka a kafaɗan sa.Taɓe baki ya yi ya ce.Ina zan sani kai kyale ni da wani amarci Juwairiya muguwar bagidajiya ce kullum cikin hijabi ka san kuma ba haka Zainab take min ba." Ya ɗan kalli A.k da ya daina cin abincin ya na sauraron sa ya ce."Jiya da na kira ta ɗakina ƙin zuwa ta yi ban san tunanin ta a kai na ba." " To kai in ban da abin ka A.m ai kai za ka bi ta kuma kuma mace take Hausa dole ta ji kunya." A k ya ce da shi ya na kallon sa.A.m ya ƙara taɓe bakin sa ya ce." Ok ka manta abin da ƙanin mahaifinta ya ce a kan ta ni ban ga abin kunya ba." "A haba A.m ka san halin sa kar ka yadda da maganar sa kuma koma mene ne kai ka amince za ka aure ta sai ka ba da azama mu sami baby.". Dariya suka yi duka daga bisani A.k ya matsa mishi ya kira ta su gaisa ya na zaune ya ƙwala mata kira ba ta jima ba sai ga shi ta fito,kamar dama laɓe take musu ta na jin maganar da suke yi. A.m tashi ya yi ya nufi ɗakin sa zai ɗauko tsaƙon da A.k ya biyo shi ya karɓa ba tare da ya kalle ta ba. Da ladabi ta gaishe shi ya amsa ya na ta tsokanar ta dai murmushi take masa. " Na so mu haɗu kafin ayi auren ki da shi sai dai kuma Allah bai nufa ba ko Juwairiya?" Ya faɗa tare da mai da maganar ta tsigar tambaya.Ɗaga masa kan ta ta yi ta na kallon shi " Ok ba komai da ma na so na ɗan miki wata magana ne Juwairiya don Allah duk yadda zuciyar ki za tai ki karki yadda ki saka son A.m a ran ki kawai ki sama ran ki zaki ci arziki ki tafi ne.Ki ɗauke ni a matsayin Yayan ki duk lokacin da wata matsala ta haɗa ku ki sanar da ni." Ya yi maza ya ƙarashe maganar jin takun A.m daga matakalar bene.Kallon sa ta yi sai kuma ta ji ya burge ta sosai yadda bai ɗauki rayuwar sa da zafi ba. Ɗaga masa kanta ta yi alamun ta ji amma kuma a cikin zuciyarta sai ta ce. " Ka makaro A.k da ce wa ka yi na yaƙi zuciyata da take son sa ƙila da na karɓi shawarar ,amma na riga na daɗe da shiga cikin kogin son sa." Sai da A.m ya yi masa rakiya sannan ya dawo ya tsaya ya na kallon Juwairiya da ta kasa tashi ta na ta tunani a ranta." Me hawayen banza maza ki tashi ki gyara min ɗakina saboda yau haushina da kike ji sai kika huce akan ɗakin,sam gyaran bai yi kuma ki ƙara wanke bayi." Ya faɗa tare da zama a falon kamar ya na son ta gama sai ya shigo. Wucewa cikin ɗakin ta yi ba tare da ta ce masa komai ba amma ya faɗi son ransa ne kawai duba ga yadda take ba da dukkan lokacin ta in ta je ɗakin sa gyara. A.m ya na ganin ta shige ya bi ta tare da tura ƙofar a hankali ganin ya shigo ta tsaya dama tun da ta shigo ta rasa mai za ta gyara saboda ɗakin ya na tsaftace da kyan sa. " Ki zo mu kwanta a gadon da baki taɓa hawa ba amma albarkacin aurena zai saka ki din ga moresa in matar so ba ta nan." Hawaye suka wanke mata fuska ba ta ce mishi komai ba kuma ba ta motsa ba bare ya saka ran za ta hawo,asalima gaban ta ne ya faɗi ras! Hannunta ya jawo ya na faɗin." Na lura kuka shi ne farin cikin ki to ki sani ba zan taɓa buɗe bakina rarrashe ki ba,ko na ɗauki hannuna na share miki hawaye da su. Yanayin da suka shiga a ranar yanayi ne mara fasaltuwa da bayyanuwa a gare su musamman Juwairiya da ta sha kuka har ta gode ma Allah,domin kwana ta yi ta na kuka ko kaɗan ba ta bar shi ya rintsa ba,wanda in ta tuna dalilin kukan na ta biyu ne sai ta ƙara sakin wani kuka. A.m da bacci ya fara ɗaukar sa a hankali bayan wata sabuwar duniya da ya shiga kuma ya kasa fahimtar wace duniya yake ciki,kukan da take yi ya na ɗaga masa hankali ya yi maganar duniya taƙi yin shiru,har ya gaji ya ƙyaleta ya rintse idanun sa da ƙarfi ya na son bacci ya ɗauke sa. Ganin taƙi dai na kukan ya janye bargon da ya ƙudundune kan sa da shi ya kunna fitilar ɗakin." Ke wai ke." Sai kuma ya yi shiru daga ninyar faɗar da yake ya yi mata ya ɗan sausauta murya ganin dare ne ya ce." Ko fa wace mace da kika gan ta a gidan mijinta da haka ta fara.Kuma idan bakya son haka ba sai ki gaya min ki gode ma Allah auren kwangila muka yi so ba daɗe wa za ki yi da ni ba." Hakan sai ya saka Juwairiya ta ƙara fashewa da kuka ganin ta ba ma mutumim da ya tsane ta rayuwarta,ga shi bai san mahimmancin ta ba bayan wahalar da ta sha yake gaya mata waɗannan kalamai. Bakinta ta murguɗa a ranta ta ce." Mugu kawai azzalimi."sai kuma ta ci gaba da kukanta wanda A.m ya lura harda shagwaɓa don shi ya gama fahimtar ta shegen shagwaɓa ne da ita shi ya sa da an yi magana sai kuka. Wani irin walƙiya a ka saki lokaci guda aka fara tsawa nan ne A.m ya fahimci garin hadari ne ya taso,da sauri ya sauka don ya duba ko windina a kulle ne kawai sai ya tsinci kan shi da jin daɗin ya na yin garin har ya buɗe labule ya na shaƙar iskar gurin. Iskar ya ƙara ma Juwairiya zazzaɓin da ta ji ya saukar mata ganin haka sai ya rufe windon ya na addu'ar Allah ya sa ta yi shiru kenan,jin ta sassauta sautin kukan da take yi sai ya koma ya zauna. Wayar sa ta fara ruri da sauri ya ɗauka don gabansa ya faɗi ya na tunanin waye da daddare zai kira shi,ganin numbar masoyiyar sa ya sa shi miƙewa da sauri take ɓacin rai ya bayyana a fuskar sa. A wannan lokacin da yake duba wayar sa aka tsuge da ruwa sosai kamar da bakin ƙwarya. Zubbur ya miƙe ganin numbar Zainab ce ya yi kamar ba zai ɗauka ba,saboda tun da ya gaya mata zai dawo ta de na ɗaukar wayar sa ashe mara mutuncin tafiya ta yi tabar ƙasar.Sai kuma ya kanga wayara a kunnin cikin tsanani ɓacin rai a ransa ya na tunanin Allah kawai zai raba ta da shi. " Hello zauji don Allah gani a airport ka zo ka ɗauke ni kuma na samu ƴar matsala da kayana har mutumim ya na min barazana.Ga kuma ruwa da ake yi kazo ka ji zauji." Wani irin tashin hankali ya ziyarce shi ya kalli Juwairiya da take cikin wani hali don shi kan sa ya san ya wuce gona da iri,kuma ba tare da sanin haka ba ya kuma kalli kansa da har yanzu ya kasa tantance duniyar da yake ci. Tunani ya fara yi ko Zainab ta hauka ce ne da za ta dawo da tsakar dare sai ya ɗauki wayarsa da nufin ya duba lokaci, ai wallahi ba zai fita yanzu ba sai dai koma mene ne ya faru musamman da ta ɓata masa rai ta yi tafiya ba tare da izinin sa ba. Tsananin mamaki ya kama sa da agogon wayar sa ya nuna mishi ƙarfe biyar da mintuna,ya na cikin kokwanton ko wayar sa ce saitin ta ya goce sai ya ji ladani ya kwaɗa kiran sallah. Da sauri ya yaye labulen ɗakin don ya ƙara tabbatar ma kansa take kuwa ya ga har hasken alfijir ya keto gari ya fara wayewa.. Sai hankalin shi ya ƙara tashi musamamn da Zainab ta turo masa tsaƙon ba sai ya zo ba,don sun daidaita da mutumim yanzu haka ma suna hanyar gida,saboda mijin Anti Fati ya turo direba ya ɗauke su kuma duka za suzo gidan. TO FA JUWAIRIYA GASKIYA NA TAUSAYA MIKI DA RANAR KI TA KASANCE A HAKA KOMAI DAI MENENE ALLAH YA BAKI HAƘURI DA JURIYA.KUCI GABA DA BIBIYAR LINTAFIN SAKACINA KO HALIN MAZA NAƘI YIN TYPING DA YAWA SABODA GASKIYA FANS BA KWA RUWAN COMMENT SAI DAI KU YI TA BIYO NI TA PC KUNA FAƊIN ALLAH YA ƘARA FASAHA INA GODIYA AMMA NI NA FI SON NA GA RUWAN COMMENT YA NA TASHI DON GAKA IN KUNA SON NAADIN GA TYPING DA TSAWO KU DIN GA COMMENT. TAKU JAMILA LAWAL ZANGO ƊUBBIN GAISUWA GARE KU SABODA COMMENT ƊIN KU YA NA SAKA NI NISHAƊI. MAMAN SUDAIS AISHATU MINNA FATIMA ZARA JOS SAHURA NURA RABIN RAINA NABILA MAMAN SAFWAN HAMDIYA UMMU ABDULHAKIM Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Mu haɗu a shafi noma sha shidda.Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 19* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM A.m ya shiga cikin tsananin tashin hankali ya juya ya kalli Juwairiya da take jin duk abin da yake faruwa,ga jikinta sai kyarma take yi har ta fara haɗa haƙori kar-kar! Sai tashin hankalin sa ya nunku ya kuma rasa tunanin da zai yi.Hannunsa ya sa ya tallafe kan sa can kuma ya shiga shafa sumar kan sa ya na tunanin mafita,don shi babban tashin hankalin shi da Zainab ba ita kaɗan za ta dawo ba ya san ce wa ta ce su zo ne su rarrashe shi. Wayarsa ya zaro ya yi kiranta ringing ɗaya ta ɗauka ta na kashe murya ta ce." Hello Habibina ai mun kusa ƙarasowa gidan..." Wata uwar tsawa ya daka mata da ya firgita ta ya ce." Ni ko Zainab wallahi in kika shigo gidana na da waɗannan dabbobin sai na yi miki mugun rashin mutunci,don haka ki ce musu ko wace banziya ta kama gabanta tunna su mahaukata ne.Kuma zaki dawo zaki ga abin da zai faru! Allah ya sa su yi gangancin shigowa gidan." Da fushi yake magana tamkar ta na gaban shi don iya abin da zai yi kenan ya hana su shigowa cikin gidan. Zainab ta yi shiru da waya sororo a hannunta, ta rasa ya za ta yi ga shi ta gama koɗa kanta ta isa da shi,don sun nuna ƙin zuwa saboda sun san halinsa ba kamar mazajen su yake ba. " Kai direba tsaya wallahi Zauji yau rashin mutunci yake ji kun ji abin da ya ce." Ta faɗa a kunya ce ta na kallon su. "Mai ya ce ɗan rashin mutuncin?" Anty Fati ta tamabaya don ta san za'a rina sanin hali."Gaskiya ko wace mace ta tafi gidan ta ku sauke ni anan kawai ina ga ƴan iskan ƴan uwansa sun zuga shi ne,amma da amincewar sa na tafi Dubai yanzu ya na faɗa min kar ku zo mishi gida ." Ta faɗa a kunyace don ya ba ta kunya ga shi ta gama zuga musu ƙarya." Kar ki yadda Zey ya haɗa ki fita kin ga dai irin ribar da muka samu,ki nuna mishi turjewar ki." Anty Fati ta faɗi cikin maganar zuga ta na son ta ƙara zuga ta don ta shirya duk abin da yake ji. " Ke ma kin san halina kawai ba na son ya wulaƙanta ku ne ku je kawai ni wallahi akan sana'ta zan iya haƙura da aikin gwannati bare kuma ya ce zai kawo min cikas." Anty Maryam da ba ta ce komai ba ita ma ta na tunanin abin da za ta tarar,in ta koma sai yanzu ta yi magana ta ce." To ki rabu da shi mana yadda kike da kyan nan ai kin san ki na fita za'a wawushe." Wani mugun kallo ta yi mata tamkar za ta kai mata duka ta ce." Ka ji Anty Maryam da maganar banza ni da Hubbi ai mutu ka raba takalmin kaza! So kike na kashe aurena na je na auri mai mata ko wanda zai yi min kishiya nan gaba,hakan ma ba zai yiwu ba don ni da kishiya ko a lahira ba na fata kuma zan iya yin komai a kanta ni da ita yaƙi ne tsakaninmu." "To ki tafi mana ga shi har yanzu ana yayyafi kuma kin buɗe mota kin tsaya ki na zuba,don kawai an miki maganar kishiya duk da family ɗin mu ba'a mana kishiya, amma Zey ki rage kishin ki to ke da mijinki ba ya haihuwa wace mace za ta zauna da shi ai sai ke ƴar wahala." Dariya ta yi ta na ɗaga musu hannu ta ce da ƙarfi ta yadda za su ji ta don motar su ta fara tafiya." A huta gajiya a haka nake son abina kuma sai mutuwa za ta raba mu.Kayana zan shigo na karɓa." Sannan ta juya da nufin ta shiga gida yayin da gabanta yake dukan tara!Tara!! Don ta san ba za su kwase da sauƙi ba. A.m ya juya da nufin ya yi ma Juwairiya magana amma sai ya ga ba ta a cikin ɗakin har ya fara taku zai bita sai kuma ya dawo,jikinsa na rawa da shi kan sa ya kasa gane kansa ya na jin wani canji a jikinsa. Sai kawai ya nufi cikin bayi don ya tsarkake kan shi ya yi salla amma sa ya fasa jin ana buɗe gida da alamun Zainab ce ta shigo,da sauri ya ƴarasa gurin windo ya buɗe ilai kuwa ita ce ta shigo da gudu saboda ruwa da yake dukanta. Girgiza kan shi ya wuce cikin bayi da sauri don ya san in Zainab ta same shi a haka za ta fahimci wani abu,kuma rashin mutunci yake son ya yi mata sai dai yanayin da yake ciki na rashin ƙarfi ba zai ba shi damar yin hakan ba. Ya jima a cikin bayi duk da kiran da Zainab take kwaɗa masa bayan ta shigo ganin ba ta gan shi ba,amma hakan bai sa ya ko ɗaga kan sa ba ya na ta tunanin da shi kansa in aka tsare shi ba zai ce ga dalilin tunanin ba. Ikon Allah dama Baba Sani ƙarya yake yi wa Juwairiya mace ce mai nagarta da kamun kai?Haka kawai sai ya ji tsanar mutumim ya kama shi har ya na jin zai iya komai don ya taimaki rayuwarta. Ko da ya fito faga ɗakin bai ga Zainab ba wacce ya tabbata ta ga ji da zaman jiran shi ƙila ita ma ta na bayi ta yi wanka. Sallah ya yi da sauri don yau ne karon farko da ya rasa jam'i shi lokacin ne ya wuce gani yake yau gari ya yi saurin wayewa. " Hubbyna oyoyo zuciya ta yi kewar ka da gangar jiki." Ta faɗa lokacin da ta buɗe ƙofa duk da cikin tsoro take amma sai ta daure ta kauda tsoronta ta furta hakan,don ita a shirye take koma mai zai faru ya faru in dai akan fita ne saboda ta ji daɗin fitan sosai. Wani irin mummunan kallo ya watsa mata wanda ya sa ta firgita ta tsaya tare da fasa rungume shi da ta yi ninya. A.m da yake a zucuye da ita ya miƙe tare da fasa shafa addu'ar ya gaura mata mari ji kake kau! " Banza mara mutunci ni zaki maida ɗan tasha ki tafi wata ƙasa ba tare da sanina ba ki dawo ki na min ilinbo ko.To wallahi sai dai ki zaɓa ko ni ko fita zuwa waje." Zainab ta saka kuka iya ƙarfinta kamar yadda ta san ya tsani kuka tare da watsi da kayan shafar shi da suke jere a madubi ta ce. " Ai wallahi ka mari auren ka ba sai na zaɓa ba dama na sha gaya maka duk ranar da ka ƙara marina sai na bar maka gidan ka!Don kawai na fita zuwa waje saboda ba ka wayewa ba za ka mare ni,da ka zo nai man aurena da ka yi bincike ba'a gaya maka Momina ta na fita zuwa waje saro kaya ba,ai kai ma ka san dole na yi sana'ar ta kuma in baka manta ba har jari Daddy ya ba ni lokacin da za'a kawo ni gidanka." Da takaici ya kalleta ganin ɓarnar da tayi mishi ya matsa kusa da ita daidai lokacin da ta ruga za ta fita don ganin yanayin sa ta san dukan ta zai yi,amma sai ya yi nasarar kamota ya riƙeta kamar zai ɓallata. " Zainab ba cin son ki da nake yi da rabuwa zan yi dake saboda baki da tarbiya ni kaina na yi kuskure da ban yi bincike ba,saboda mun ga Daddyna na tare da mahaifin ki ashe ƴar mace na aura.To bari kiji wallahi ba zan zauna dake a haka ba maza ki fice min daga gida mara mutunci kawai."Ya ce zuciyar sa na tafasa kamar za ta fito. Ya saketa cikin rashin tsoro ta tsaya ta kuma kauda duk tsoron da take ji na sa tuna huɗubar da Yayyinta,suka yi mata cewar su ma duk sai da suka sha artabu da mazajen su sannan suka haƙura suka bar su. " Na gode da cin mutuncin da kake yi ma uwata amma ka sani yadda ba ka daraja mahaifiyata ba ni ba babu wani da banza da zan daraja, kuma Daddyna zan kira na gaya mishi dukana kake yi mugu azzalimi mai dukan mace."Ta ce ta na kuka da ƙarfinta. Wani marin ya kawo mata ya na faɗin ." Ok haka kika ce to bari na ƙara miki sai kiji daɗin faɗin kashe ki na yi,kuma yanzu zaki bar min gidana ba sai an jima ba ki je can ki sami shashasha irin ki ki aura,amma ni ba zan bar mace mafi soyuwa a gare ni ta na cuɗanya da wasu mazan ba ke ko kishin kan ki ba ƙya yi ...." Katse shi ta yi ta na faɗin."Babu in da za ni wallahi ai nasan ɓaɓatun banza kake yi,amma ba zaka iya rabuwa da ni ba." A.m ya zaro bell ɗin shi ya na kallonta ya ce " Tunna haka kika ce zan nuna miki halina baki san wane ne ni ba,amma sai kin tafi gidan ku in ya so in iyayenki suna son ki yi zaman auren sa hana ki tunna ni kin raina ni." Zainab ta yi mamaki sosai ganin duk abin da za ta yi mishi ta yi amma ya kafe kan dole ta tafi,hankalinta ya tashi sosai domin in har ta tafi ƴan'uwanta za su din ga mata dariyar a she dama ba ta fi ƙarfin mijinta ba. Sai dabara ta faɗo mata lokacin da ya janyo mata akwatinta ya tura mata ta ɗauki waya za ta kira Daddynta, sai ta canza shawara ta kira Daddyn A.m ta fashe da kuka ta ce. " Daddy A.m zai kashe ni da duka mun samu saɓani na kuma bashi haƙuri,amma kuma yaƙi dukana yake sosai.Don Allah Daddy ka zo ka taimake ni!Ga shi nan da bell ya nifo ni."Ta ce tare da saka sabon kuka ta saki ƙara ganin A.m ya yo kanta don ko kaɗan bai yi tunanin Daddy za ta kira ba." " Baki da hankali ko mahaifina zaki kira uban me ya sa baki kira naki ba?"Ya ce tare da doka wayar a ƙasa. Hakalin Daddy ya tashi matuƙar gaske jin wayar ta mutu wanda ya zargi A.m ya karɓe wayar,sai ya shiga safa da marwa don ya san halin ɗan na sa ba shi da haƙuri sam! Har ya danna numbar ainihin mahaifinsa da nufin ya kira sa sai kuma ya fasa ya kira numbar A.m,wace ta yi ta ringing bai ɗaga ba duk da ya na kallon wayar. A karo na ba adadi A.m ya ɗauki wayar tare da kanga ta a kunninsa cikin fushi ya ce. " Hello Daddy." "Abdurrahman ba da hankali ko! Ƴar mutane kake duka wa ya ce maka ana dukar mace in ka saba mata da haka,kafiya za ta din ga mata ita mace ai ƴar lallashi ne.Ka taɓa ganin wani ya duka matarsa a cikinmu irin tarbiyar da na baja kenan?" Daddy ya tambaye sa cikin zafi ba tare da ya tsaya jin mai zai ce ba." Wallahi Zainab ta rai na ni nina san halin da take min!Daddy wata ƙasa ta sallake ta tafi saro kaya har zuwa Dubai bayan na hana ta.Shin Daddy na gaza ɗaukar ɗawainiyar ta ne?" Shi ma ya furta cikin ɓacin rai da kuma murya mai sauti don ya manta da Daddy yake magana. Daddy ya ji maganar wani iri tabbas ya ji ba ta kyauta ba,amma shi A.m har yau ya kasa gane wace irin mace yake aure kuma ƴar waye. Jin Daddy bai ce komai ba sai ya yi ƙuta ya ce." Na rantse dole ta bar min gidana tunna ba ta da tarbiya ni ba zan yadda ta mai da ni namijin tace ba." Ya ce ya na huci don Zainab ta ba shi haushi matuƙar gaske shi ya sa dama ya ɗauki alƙwarin in ta dawo ba za su kwashe ta daɗi ba,sai ta gane shi baya ɗaukar raini shi ya sa ya ɓoye sonta a wani guri na zuciyarsa don kar ya han shi ɗaukar mataki. " Abdurrahman dama ka auri ƴar abokina ne saboda ka tozarta ni, ka nuna ban isa dakai ba saboda ba ni na haife ka ba ko?Ka na son ka tada min da taɓon ba na haihuwa ko?" Daddy ya faɗa a raunane wanda hankalin A.m ya tashi da jin abin da ya faɗa don ji ya yi kamar kuka yake yi. " No Daddy don Allah kar ka ce haka wallahi kai ɗin kafi mahaifina don zan iya bijire masa,amma ban da maganarka ka yafe min." Ya ce hankalinsa a tashe ya na ma mata mugun kallo saboda yau ne rana ta farko da Daddy ya yi mishi irin wannan maganar. "To ina baka haƙuri tabbas ba ta kyauta ba karka ƙara dukan matarka ta sunna yanzu gani nan zuwa gidan,zan yi mata faɗa kuma dole ta daina tunna baka so ai kai kake da iko da ita." Daddy ya ce masa cikin muryar taushi da lallashi ya na son ya kwantar da hankalinsa,ya san zai iya yin ɓatatta. " To sai ka zo." Ya kashe wayar ya na huci kamar mesa daga ƙarshe ficewa ya yi a ɗakin ya bar ta ya koma farfajiyar gidan ya na jiran Daddy,don har yanzu bai huce ba dole Zainab ta zaɓi ɗaya duk da ya san barazana kawai yake mata amma ba zai iya rabuwa da ita ba. Zainab kuwa ba yan fitarsa ta yi tsaki tare da saka makulli a ɗakin ta na shafa ƙuncinta da ya sha mari ta ɗauki wayarta da ya fasa ta ce.Wahalalle kawai ka gama jarabarka sai ka siyar min wata wayar kuma ba zan fasa sana'a ta ba ƙarshen da zarar na samu lokaci wata ƙasar zan koma.Sai dai in hauka za ka yi ka yi." Ya na tsaye a farfajiyar gidan ya ji hon wanda ya tabbata Daddy ne ya zo,mai gadi ya buɗe masa get ya shigo. Da sauri A.m ya ruga kamar wani ƙaramin yaro ya faɗa jikin Daddy ya na magana kamar zai yi kuka.Dariya ya yi ya shafa bayan shi suka shiga ciki. Faɗa sosai Daddy ya yi ma Zainab wacce ta ɗauke shi a matsayin son kai kuma ya tursasa mata ta ba A.m haƙuri,sannan ƙar ya ƙara jin ta fita ko unguwa ba wata ƙasa ba in dai ba da izinin sa ba. Ya kuma ƙara da ce wa." Tunna A.m ba ya so ta dai na zuwa in ya so ko shi zai iya yi mata oder. A kasale ta miƙe ta na ganin kamar son kai Daddy ya yi mata,amma ta rantse ko sama da ƙasa za ta haɗe ba wanda ya isa ya hana ta fita waje,don har ta fara saka kanta a cikin matan da za'a fara irgawa suna da kuɗi a cikin Nigeriya, so ba wani ƙwaro da zai hana ta fita. Amma a fili sai ta ƙara sakin kuka ta ce " Na yi nadaama kuma na ba shi haƙuri Amma ya ƙi haƙura." " Shikenan Daddy ya wuce amma kar ta ƙara." Ya faɗa cikin ɓacin rai sannan ya miƙe ganin Daddy ya miƙe." Ok Allah ya kyauta ku yi haƙuri dama aure ɗan haƙuri ne ni zan tafi." A.m ya shafa kan shi ya na murmushi ya ce." Daddy ya zo gidan son amma ko ruwa ba'a kawo mishi ba,ka yi haƙuri Daddy ni kaina haƙuri nake da ƴar taku komai ba ta iya ba sai shegen yawon tsiya da rai na miji,Allah Daddy ko ruwan zafi ban taɓa sha ba wanda Zainab ta dafa,asalima ce wa ta yi ba ta iya ba.Shi ya sa nake tunanin ta rako mata ne kawai. Daddy ya saki dariya ya na faɗin daidai lokacin da ya nufi ƙofa." Ah ah wanan to magana ake yada min ba haƙuri ake ba ni ba,amma kuma a haka ka ga ƴar tamu ka kace in ba ita ba sai rijiya." Tsaki ya yi ya na hararar ta ya ce " Shigo shigo ciki akai min ban san halin ta ba na ba ta amanar zuciyata." Zainab kuwa mai da mishi da harar da yake mata ta yi ta ce." Ba wani nan wahala ce na ce ba zan yi ba ai ko addini bai ce dole sai na yi ba,kuma yanzu ai baka da matsalar abinci tunna ga Juwairiya nan mai aiki." A.m ya watsa mata wani kallo wanda shi ya sa ma'anar sa jin ta ambaci Juwariya. Ganin Daddy zai fice sai Zainab ta ce." Daddy bari na yi kiran Juwairiya ta kawo maka abinci,na san yanzu haka ta na kicin kuma zaka yaba don ta na da zaƙinn hannu." Wani irin tashin hankali A.m ya ji ganin ta nufi kicin ɗin har ya na dana sanin maganar da ya yi gashi ƙilu zai jawo mishi bau! Ya buɗe baki da nufin ya yi maganar da bai san me bakinsa zai ce ba sai ya ji Daddy ya ce. " Karki damu ƴata kin san bana karyawa sai sha ɗaya bari na tafi Allah ya yi muku albarka,kuma don Allah ku din ga haƙuri da junan ku."Sai ta dawo ta fasa ta na murmushi. Wani irin wawan ajiyar zuciya ya saki wanda ya sa har sai da Zainab ta juyo ta kalle shi,ya watsa mata harara,ya shige sama da sauri ya nufi ɗakinsa ya kwashi zanin gadon da ya saka a warshing mashine ya kunna da sauri har ya na sheƙa ruwa a ƙasa garin ya zuba a ciki. Zainab ce ta shigo ta zauna a kan gadon ta na ƙare ma ɗakin kallo ganin ya na bayi sai kwanta ta na jiran sa,amma sai yaƙi fitowa ya tsaya kamar me tunanin wa ni abu da ya manta. A hankali Zainab ta taso ta tsaya ta bayansa ta huging ɗinsa da sauri ya ture hannunta ya koma gado ya kwanta tare da rufe idanunsa ya janyo bargo ya lulluɓa da shi. Ganin haka ita ma ta hau ta ɗaga bargon ta shige tare da rungume shi,ya sa ka hannunsa ya ture ta ta faɗi ƙasa don har yanzu haushinta yake ji,haka kawai ta ba ma wata mace damar shigowa rayuwarsa ga shi ya na jin wani abu da ba zai iya ce wa ga shi ba,don har yanzu jikinsa babu ƙarfi. Da takaici ya isheta sai kawai ta fashe da kuka don ta bugu sosai ta miƙe ta na share hawaye ta ce." Bari na fita tunna baka buƙatar son ganina! Haba ko Allah muna yi mishi laifi ya yafe mana." Ta saka takalmi ta kuma ce wa." Dama yunwa nake ji bari naje na ci abinci." Haba da sauri ya diro a kan gadon da ya ƙudundune kansa da bargo ya janyo ta da ƙarfi ta faɗa kan gadon ya na zare ido. " Ke ce kika ban haushi matuƙa amma na haƙura tunna kin ce ba zaki ƙara ba." Ya ce da ita ya na murmushin dole ya saka hannun shi ya tallabeta ganin ta na murmushi ya ci gaba da ce wa." Baki san tashin hankalin da na shiga ba da baki nan kin san duk yawon ki ba ki taɓa bari mun raba shinfiɗa ba.Tun lokacin da na ce miki mun iso kika kashe waya na tsargu." Ya ƙura mata ido ya na kallonta ya kai bakinsa kusa da kunninta ya na mamakin abin da zai ce mata." Ko dafa da na dawo na ga baƙya nan sai wancan wa take da suna ta bani abinci wurgi da shi na yi,a hotel na zauna saboda gidan ya yi min baƙi na kasa bacci ni kaɗai gabaki ɗaya kewanki ya dame ni,gaskiya ina son ki matuƙa." Ya numfasa ya na mata wani tsadadden kallo da murmushi ya ci gaba da ce wa." Ina masallaci na ga kiranki duk da fushi nake dake har na fito cikin hotel ɗin da nufin na ɗauki mota na ɗauko ki,sai ga shi kin kira ni in bar shi mijin Fati ya turo muku direba shi ya sa na karyo mota na dawo gidan tunna matar gidan ta dawo." Ya faɗa ya na kaida kansa gefe shi kansa ya na mamakin kansa. Zainab murmushinta ya ƙaru ta na jin wani irin girman kai da alfahari da mijinta da take yi,sai ta kama shi ta rungume ta na faɗin."Ina sonka Habibina ni na san ba za ka iya rabuwa da ni ba,ko ce wa da ka yi na bar maka gidan ka kana faɗi ne kawai amma ni da kai mutu ka raba." " Tabbas Zainab maganarki dutse da sai dai ki taho asibiti jinya."Ya faɗa Dariya suka yi duka ya rufe su da bargo ya kasheta da soyaryar shi sannan ya sa ta baccin dole,saboda ya sakin mata nauyin shi wai dole sai ta kwanta sun yi bacci,duk da ba shi take ji ba. Kallonsa take yi yadda yake saukar da numfashinsa a hankali,daga gani baccin na kai mishi karo ita kuwa ta kasa baccin saboda wani irin yunwa dake ƙwaƙwularta,saboda rabonta da abinci tun daren jiya ta kasa ci ta na fargabar yadda za su kwashe da shi. Shafa fuskarsa ta yi da yake ta sheƙi da kyau ta na mamakin mai ya hana shi bacci,sai kuma ta danganta hakan da ce mata da ya yi ba'a gida yake kwana ba ƙila ya kasa bacci ne. A.m da fari baccin ƙarya yake yi ya saka mata nauyin jikinsa don kar ta ce za ta buƙaci abinci, ta je gurin Juwairiya don ya san a halin da take ciki ba yadda za'a yi ta iya wani aiki a gidan,amma kuma daga ba ya saboda rashin baccin da bai yi ma wannan mai kukan tsiyar da ta hana shi bacci sai bacci ya kwashe shi. Da Zaina b ta gaji da juyi a gado ta bubbuga shi ya ɗan buɗe ido ya na kallonta. " Gaskiya ka tashi ni fa na gaji da baccin nan yunwa na son ta yi min lahani." Ta faɗa ta na jan shi ya sauko shahada ya yi ya sauka tare da miƙa da salati,ya shige bayi ganin haka ita ma ta sai ta wuce ɗakinta ta shiga bayi wanka ta yi ta zira duguwar riga,suka fito falo suna taku a jere sai kace ba su suke ta faɗa ba. ************ Juwairiya kuwa bayan ta gama jin wayar da A.m yake yi da Zainab ta shiga tashin hankali matuƙa! A wannan lokaci ji take kamar ta buɗe ido ta ga ba ta a doron ƙasa kuka take yi sosai na rashin abu mafi girma a rayuwarta,wanda Baba Sani ya so ya yi galabar raba ta da shi dama mutane da dama amma ta yi yaƙi tukuru,ta ada na abin ta sai ga shi yau ta siyar da shi saboda kuɗi ta na shan wulaƙanci ba tare da an daraja ta ba. Ta rintse idanunta ta na jin wani irin ciwo mai raɗaɗi a zuciyarta yayin da wasu tarin hawaye suka ci gaba da turereniya a fuskarta. Cije bakinta ta yi lokacin da ta miƙe ta na jin wani irin azabar raɗaɗi ya na zagaye duk ilahirin jikinta. A hankali ta fice daga ɗakin ba tare da ya sani ba jin matar so ta dawo yayin da hankalinta ya tashi,amma ta wani gefen ta na jin ina ma ace Zainab ta riske su a wannan yanayi koma mai zai faru ya faru,don ta gaji da tarin raɗaɗin azabar da take kurɓar ruwan baƙin cikinsa a cikin rayuwarta. Ta na shiga ɗaki sai ta fashe da kuka sosai har ta yi mai isar ta sannan ta rarrafa ta shiga bayi ta gana ma kanta,azaba da ruwan zafi don ta rage ma kanta ciwo da nauyin da jikinta ya yi. Bayan ta yi wanka ta fito ta yi sallah a zaune sai bacci mai haɗe da zazzaɓi ya kama ta wanda faɗan su ya tashe ta,ba wai don ta gaji da baccon ba tunna duka yaushe ta kwanta sai dai ta ji daɗin baccin don ya ɗan rage mata wani ƙunci daga cikin damuwarta. Ta din ga jin hayaniyar su da kukan Zainab har da saukar marin da ya yi mata. Ta saka hannunta ta toshe kunnin ta amma sai ta ji sun sauko ƙasa suna ta faɗa sosai,ya faɗa ta faɗa sam babu tsari a rayuwar auren su don ba sa daraja juna. Gabaki ɗaya sai ta ɗauki laifin ta ɗora akan A.m wanda yanzu take jin haushin sa fiye da komai a rayuwarta,ga wani irin kishinsa da ya ƙara ninkuwa a ranta mai girma wanda take jin kamar ta illata duk wadda ta raɓe shi. Ta na jin suna faɗa daga bisani ta ji shiru sai muryar namiji ta ji ya na sasanci,wanda daga baya ta game mahaifin A.m ne. Sasancin da aka yi a tsakanin su suka koma ciki shi ya ba ta damar yin baccin wahala,duk da ta san ya kamata ta shirya ma mutanen gidan abinci,sai dai ba za ta iya ba saboda jikinta da ko ina yake mata ciwo. A tare suka sauko ƙasar sun ci gayu sosai an sha kyau. Zainab ta tsaya ta na kallon dinning cike da mamaki ganin ba komai wayam. Ta kalli A.m ta na faɗin." Ina wannan wawiyar take ba ta shirya min abinci ba duk da na kira ta ba ɗauka ba na tura mata da text." A.m ya da gaban sa ya faɗi amma sai ya taɓe bakin sa ya ce. " Ina zan sani ko kin bani ajiyar ta ne?Ni da ba'a gida nake kwana ba." Ya faɗa ya na wani cin magani har da ɗan harara yake sakin mata. Ƙwala mata kira ta yi sau uku sai ga Juwairiya ta fito a wani yanayi ta na jan ƙafarta. Da masifa Juwairiya ta kalle ta ta fara magana da ce wa." Ina abinci na kuma gidan uban wa kika shiga na kira wayar ki na gaya miki zan dawo amma baki ɗauka ba." Ta faɗa tare da tsare Juwairiya da ido kamar ta na son ta gano dalilin ƙin ɗaga wayar da ta yi. Juwairiya ta saci kallon A.m da yake zaune a ɗaya daga cikin kujerun dinning ya na danna waya,kamar bai san da mutane a gurin ba amma kuma a zahirin gaskiya hankalin sa na gurin su ya na son ya ji mai za ta ce,yayin da gaban sa yake faɗi duk a tsorace yake sai dai ya yi ta maza ya dake. Juwairiya ta mai da kanta ƙasa hawaye na bin fuskarta jikinta har kyarma yake yi,saboda har yanzu zazzaɓi take ji,ita kanta ba za ta ce ga in da wayarta take ba don rabon ta ita tun jiya da ya ce ta gyara masa ɗakinsa. " Ki yi haƙuri wayata ba caji na gaya ma maigadi ya kunna jannareto don ba wuta,amma ya ƙi tashi sannan na so na kunna sola sai dai ban iya ba ina gudun kar na ɓata na haƙura k....." " Rufe min baki nɓbanza daƙiƙiya jahila solar ce kika kasa kunnawa abu a rubuce ba na tunanin kin yi firamari,ni tsoro nake karki din ga ƙona min kayan wuta ko ki ta da gobara ai dai yi asarar kuɗin tara wallahi.To uban me ya hana ki yin abinci." Zainab ta ce ta na hararar ta don ranta ya ɓace ta so ta samu abincinta da ta yi rashin sa na kwana biyu mai daɗi da,shi ya sa taƙi sakin jikinta ta ci abinci da za ta taho. Wannan karon A.m ya yi tsubbul da bakinsa ya ce." Wa za ta dafa ma abincin ni da na gaya miki a hotel na ke kwana ita da masu aiki ne kawai ƙila sun yi sun ci,tunna ba ta san za ki dawo ba." Ya ce cikin sauri ya na tsoron kar ta yi katoɓara don ganin ta fara kuka. Juwairiya kuwa gwalalo idanunta ta yi ta na kallon sa jin ƙaryar da ya shirya mata. Karab! Kuwa suka haɗa ido kowa ya yi saurin ɗauke kansa. A.m sai da ya sakin mata harara sannan ya ɗauke kansa,Juwairiya kuwa wani irin kunyarsa ya kama ta ta rintse idanunta da sauri. " Ke." Ta daka mata tsawar da ya firgita ta." To uban wa kike ma kuka daga tambayarki?Maza ki je ki ɗora min abinci yunwa nake ji kuma ki kawo min abun da zan iya ci kafin ki ɗora girkin." Sai hawayen Juwairiya ya ƙara zarya a fuskarata ta kalli Zainab ta ce " Don Allah ki yi haƙuri bani da lafiya zazzaɓi nake ji,ba zan iya girki ba." Ta faɗa cikin muryar da ta bayyana irin kukan da ta sha tun daren jiya. Zainab ta harare ta ta ce." Allah ya sa mutuwa za ki yi amma sai kin yi min abinci kin san yunwar da nake ji maza wuce.Kuma ki kawo min abin da zamu taɓa ni da zauji." Ta zauna tare da ɗaukar remote ta kunna kallo ta na karkaɗa ƙafa ta na jan A.m da hira wanda ya kasa ko da tari ne ya na ta kallon fuskar wayarsa,da ya kasa ɗauke idanunsa a kanta bayan babu abin da yake yi. Juwairiya na shiga ta haɗa kanta da bangon kicin ɗin ta na kuka sosai take jin jikinta ba daɗi. Ta daɗe a haka sannan ta soya dankalin turawa da ƙwai ta kuma haɗa musu da tea mai kauri ta kai musu,ta na tafiya tamkar wacce ƙwai ya fashe mawa a cikin ta. " Ok maza ki je ki haɗa mai nauyi don wannan ba zai ƙosar da ni ba." Ta ce mata ba yan ta ije mata ba tare da ta kalle ta ba. "Anty Zainab ki yi haƙuri ba ni da lafiya don Allah sa..." Mari ta wanka mata a fuskarta da take jiƙe da hawaye ta ce. " Ban san lokacin da kika raina ni ba har kike musayan yawu da ni banza dangin matsiyata!Maza wuce ki yi abin da na saki." A.m ya tashi da sauri ya na faɗin " Haba Zainab ta ce miki ba ta da lafiya ba ki da tausayi ne.." Katse shi ta yi ta ce." Ba da kai nake yi ba ba ta da lafiya ta sha magani,uban wa take son ya yi mana girkin meye amfanin ta a gidan?Ko ubanta yake neman ma na kuɗin da za mu biya ta?" SAUKAR MARIN YA SA NA FIRGITA AMMA NA CI GABA DA RUBUTU SAI DAI KUMA TAUSAYIN JUWAIRIYA YA HANANI ƘARASAWA,DON NA KASA GANE MAI NAKE RUBUTA AN YA ZAINAB KIN KYAUTA KUWA. KUCI GABA DA BIBIYAR LINTAFIN BARI NA ƘARA TUNA MUKU DA SUNAN LINTAFIN SAKACINA KO HALIN MAZA TAKU JAMILA LAWAL ZANGO TUNATARWA DON ALLAH ƳAN'UWANA MATA KADA KARATUN LINTAFI YA ƊAUKE HANKULANMU MU MANTA DA BAUTAR UBANGIJI,KU TUNA ALLAH YA HALICCE MU DON MU BAUTA MASA NE. GOBE JUMA'A KAR A MANTA KARATUN SURATUL KAHAFI ALLAH YA BA MU ALKAIRUN DA KE CIKINTA AMIN Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Mu haɗu a shafi noma sha shidda.Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 20* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM A.m har ya buɗe baki zai ƙara magana sai kuma ya fasa,ya ɗauki wayar sa ya haye sama ba tare da ya ƙara kallon ɗaya daga cikin su ba. Juwairiya ta dafe ƙuncinta hawaye na zarya a fuskarta da ma ta san dole watarana Zainab za ta dake,ta tun da halinta ne sai dai yadda ta ji saukar marin ta ji sam ba za ta iya ɗauka ba,domin da ya zo neman aurenta bai gaya mata har da duka a ciki ba. Hawaye ta share ta juya ta nufi kicin saboda rashin ƙarfin da take ji,tsayuwa ma wahala take mata don haka ba ta ƙara ce wa komai ba ta shige kicin ɗin. Jingina ta yi da slinder na gas ɗin kicin ta saki kuka duk da ta na jin cewar,lokaci ya yi da za ta dai na asarar hawayen a banza akan su saboda ta fahimci bayan damuwar da suke saka mata,har da na auren su da suke faɗa kamar kaji su hana ƙwaƙwalwarta sukuni. Da ƙyar ta samu ta kammala girkin da taimakon Baba da ta dameta da tambayar mai ke damunta,ganin ta ƙi tanka mata sai ta kalle ta ta ce bayan ta gama kwashe abinci ta saka a kula. "Ƴar nan ya kama ta ki naimi maganin basir saboda shi yake damun ki,ji yadda kike cije baki ki na tafiya da ƙyar." Da takaicin maganar da ta yi mata ɗaki ta wuce ba tare da ta tanka mata ba. Tun daga wannan ranar Juwairiya ta kame kanta ba ta barin ko haɗuwa da shi su yi,saboda wani irin kunyar sa da take ji kamar ta nitse in ta gan shi,don ko gyaran muryar shi ta ji sai jikinta ya kama rawa kamar za ta ruga. Kwana biyu Zainab ta takura kanta ta hana zuciyarta fita don ta faranta masa,saboda ta ga canji kwana biyu ya na wani shareta,da ta yi masa magana zai hayayyaƙo mata kamar zai cinye ta. Sai ta danne zuciyarta ta ƙi fita ko ina daga aiki sai gida ta na ba shi kulawa,wanda da ƙyar ta samu ya sauko suka koma rayuwar su kamar da. Juwairiya kullum za ta yi musu abinci mai rai da lafiya su ci suna yabawa a zuci,don girkinta ya na matuƙar ƙayatar da su duk da babu wanda ya taɓa yabawa,amma har ɗan ƙiba sai da suka ƙara kaɗan. Sai dai fa mai hali ba ya fasa halin sa Zainab a daddafe ta yi ƴan kwanaki a gidan, wadda take jin kamar ta na gidan yari duk da irin kayan alatun dake gidan amma saboda ta saba fita sam komai ba ya burgeta. Zaune take a ɗaki ta kulle kamar yadda ta saba duk lokacin da za ta yi rawa ta tura. Tasha ado da wasu riga da wanda na ƴan kanti masu kyau kalar pink,wandon bai kai ƙasa ba. Gyara gashinta ta yi ta fara rawa cike da ƙwarewa ta tura ta na murmushi don ta san yanzu za ta ga ruwan comment da like. Ilai kuwa ta na turawa aka fara liking ta na kallo ta na murmushi,ta na shirin sauka wata numba da kullum take mata sallama a facebook,ta ƙara yi duk da ba amsa wa take ba amma ba ta gaji ba,ku san kullum sai ta yi mata sallama. Tsaki ta yi ta sauka da ga online gabaki ɗaya ta na mamakin wannnan numba da take damunta,saboda ita in dai ba ta san mutum ba ba ta magana online,sanin cewar ita tauraruwa ce a yanar gizo so ba ta da lokacin da za ta tsaya ta na kula su,amma a ranta ta ji ta na son ta amsa sallamar don ta ji mai ke tafe da ita,saboda ta duba profile ɗinta ta ga ita ma ba ƙaramar mace ba ce,don da Barrister Mardiyya take bearing. Murmushi ta saki tare da ije wayar da sauri daidai lokacin da A.m ya murɗa ƙofar ya shigo,sai ta kama hannunsa ta riƙe ta na dariya tare da kashe murya ta ce. "Barka da dawowa yanzu na ji ƙarar shigowar ka, ina wanka ne shi ya sa ban fito ba." Dafe kan sa ya yi ya janye jikin sa ya zauna akan gefen gadon ya na kallonta tare da ƙoƙarin rage kayan jikin shi. "Babyna na gaji matuƙa kamar kai na ciwo yake son ya yi,yunwa nake ji kawo min abinci in ci anan bacci nake son na yi." Ya faɗa tare da kwantawa ya miƙewa a kan gadon don jikin sa ko ina ciwo yake masa. Zainab ta ɗan canza fuska ta ce " Na ɗauka za ka ci abincin a dinning ne fita nake son na yi,kuma Juwairiya ta riga ta shirya abinci meye sai ka wahalar da mutum gurin ɗaukowa." Ta ƙarashe maganar cikin yauƙi da yanga tare da ɗaukar wayarta,da take kusa da shi don ta tuna kamar ba ta sauka a online ba,sai dai kuma da ta tuna ba ta taɓa ganin ya ɗauki wayarta da sunan ya duba ba,ko kuma ya ce zai yi wani abu. Gaban sa ya faɗi da ta ambaci sunan Juwairiya ba zai ce ya manta da ita ba,amma sam ba ya son ya ji sunan sai ya ji haka kawai gaban sa ya faɗi. " Zainab ba na son rainin wayo ni da gidana da kuma matata ba ni da ikon na ce ga in da zan ci abinci?Kuma da kika ce wancan za ta kawo min,to ba ita nake so ba matata wacce nake da iko da ita nake son ta kawo min,kuma ki je ki dawo bacci nake son mu yi babu in da za ki." A ɗan kausashe ya faɗa ya na harararta wanda ya zamar masa ƙa'ida,kamar wani mace in dai aka gaya mishi ba daidai ba, sai ya yi harara. Yarfe hannunta ta yi ta ije wayarta tare da fara ƙorafi ta na ce wa." Haba Hubbi kai ma ka san na yi ƙoƙari ban je ko ina ba,na baka lokacina na tsawon kwanaki. Ta ɗan matsa kusa da shi ta ce." Yau fa bikin ƙanwar ƙawar Anty Fati ake yi,ka ga ai ya zama dole na je ko?"Ta tambaye shi tare da tsare shi da ido. Kallonta ya yi bai ce komai ba sai ya miƙe ya kunna tangamemen tibin da ke ɗakin ya riƙe remote ya ce. " Dole ki je mana gayyar soɗi ni dai na gama magana ba in da zaki,ke ko kishina ba kya yi ki ta sa ƴan aiki suna kawo min abinci,ko tunanin in canza miki ba kya yi." Kusa da shi ta zauna ta na faɗin." Yarda da kai ne Hubbi Allah in za a ban kur'ani zan iya rantse wa a kan ka,sam ba ni da haufi ko da ba ka yi min alƙawarin ba za ka yi min kishiya ba,hankalina ba zai tashi ba saboda ban taɓa jin ka yaba wata mace ba." Ta ɗan kalle shi da murmushin yadda a fuskarta ta ci gaba da ce wa." Kuma duk abin da nake yi ai ba na zuwa da ƙawayena waɗanda ba su da aure gidana saboda tsaro." Dariya ya yi jin abin da ta ce ya miƙar da ita ya na faɗin." Ok Babyna ina godiya sosai da yardar da kika yi min,kuma ke ɗin zazzafa ce ta ko'ina ga kyau ga ilmi da da tarin baiwa kala-kala,ina gaya miki ba wata sai ke a nan." Ya nuna mata ƙirjin shi da da babbar yatsar shi dariya suka yi ta yi huggin ɗin sa,sannan ta ba manna masa kis ta ruga da sauri don ta ɗauko masa abincin,duk da ranta bai so haka ba amma fitar ta ta rantse sai ta fita. Don haka ko da ta dawo haka ta ci gaba da lallaɓar sa har ya amince saboda ta dame shi,kuma bacci yake son ya yi da sauri ta ɗauki ɗan gyalen ta ta fice daga gidan. Bayan ya ci abinci ya ɗan miƙe tare da ba da tazara kafin ya kwanta,saboda abincin da ya ci sannan ya kwanta bacci. Juwairiya ta warke sumul bayan ɗan ciwon kwana biyu da ta yi ta zage ta na ta aikinta,cikin ƙosawa a ranta ta na addu'ar Allah ya sa ta samu cikin ya ɗauke ta daga gidan,ganin yadda Zainab ta mai da ita baiwa,shi kuwa daga ranar bai ƙara neman ta ba. Ta na falo aiki take yi goge su tibi da abin da ya kama ta a goge a falon take yi. Sosai ta mai da hankalinta a kan aikin da take yi ta na son ta gama ta ɗora girkin abinci. Ya fito daga ɗakin sa ya na sanye cikin doguwar riga na jallabiya mai ruwan madara,wayar sa riƙe a hannun sa sam fuskar sa babu fara'a. Juwairiya ta saki ɗan ƙaramin tawul ɗin da take goge tibin da shi za ta ruga ganin ya fito, amma sai ya yi maza ya riƙe mata hannu tare da kiran sunan ta. Tsayawa kan dole ta yi tare da juya masa baya cikin tsananin kunyar sa. Juyo da ita ya yi da murya mai sanyi ya fara magana. " Ban san tunanin ki in da ya tafi ba tun daga ranar kin ɗauke wuta kin mai da ni kamar wani dodo,bayan kin san wannan kamar sharan fage ne akan tsarinmu har zuwa randa zamu cimma haƙar mu,kowa ya huta da wahalar da kan sa mu samu maslaha a rayuwar mu." Ta na son ta yi mishi magana irin ya faɗa ta amsa mishi ko da maganar da ya yi mata babu daɗi,amma kuma ta na matuƙar jin nauyin sa wanda ko haɗa ido a bisa kuskure take yi. Sai ta kauda fuskarta a ranta ta na faɗin." Kai ne kake son ka cimma haƙar ka,amma ni ina son na kasance da kai har abada A.m ina sonka burina ka ɗauke ni daga gidan ka nima ka sama min ƴanci na rayu da kai duniya ta san mijina ne kai." Amma a fili sai ta yi ƙasa da kanta ta na kallon ƙafafun sa suke da kyau da sha'awa. " Ke ni fa ba na ɗaukar rainin wayo na yi ta miki magana kina sharewa,ki buɗe baki ki yi min magana kuma ni ban ce ki yi min kuka ba." Ya faɗa ganin ta yi rau-rau idanunta sun kawo ruwa. Kamar umurni ya ba ta sai ta yi ƙoƙarin mayarwa ta na son kallon sa. A.m ya saka hannun sa ya shammace ta kawai ya cire mata hijabin jikinta ya na faɗin. "Ni fa yanzu ban ga abin ɓoye-ɓoye a tsakaninmu ba bayan kin san ke ɗin matata ce,wanda aure ya ba ni damar mallakarki a gurin makwaɗaicin ƙanin mahaifinki." Ta kauda kanta ba ta ce komai ba sai kuma ta saka kuka. Dunƙule hijabin ya yi ya jefar ya ci gaba da faɗin."Anyway yanzu dai ni maigida na ba da umurnin in dai daga ni sai ke ne a gidan,to amaryar wucin gadi ƙar ta ƙara saka hijabi ki bari sai in wanda kike jin kunya ta dawo sai ki saka abinki,amma ni da ke ai ba kunya tsakaninmu ko." Ya gama maganar ya na tambayarta ya na wani irin murmushi mai kama da na mugunta ko ya na son shirya wani ƙeta. Juwairiya ta ji wani irin sanyi a ranta karan farko haɗuwara da A.m yau ne rana ta farko da ya yi mata murmushi,duk da murmushin na sa da wata manufa ya yi amma hakan ya ba ta matuƙar citta a ranta. Ta matsa daga kusa da shi ganin irin ƙare ma jikinta kallo da yake ta fara tafiya a hankali. "Juwairaah." Ta tsaya cak daga tafiyar da take yi amma ba ta jiyo ba,shi ya taho har in da take ya matsa kuda da kunninta ya ce " Ina zaki matar wucin gadi ai ban gama magana ba,kin san ya kamata a ɗora daga in da aka tsaya ko." Banza da shi ta yi tana mamakin wai haka yake mai ya sa yau ya ƙara zuwa da salo ne? " To shikenan tun da kin ƙi magana da ma zan yi godiya ne na ranar nan gaskiya na ya ba sosai,wannan daren momerable and remarkable ne a gurina,Allah shi zai saka miki saboda ai ba ta ki da ƙanin mahaifin ki ya yi." Ya faɗa ba tare da kunya ba kuma ya na kallon ƙwayar idanunta. Juwairiya ta ɗago ta kalle shi ba tare da ta shirya ba ta ji ta sakar mishi wani lalausar murmushin,har dimple ɗinta suka losa ta ruga da gudu ta shige ɗaki tare da rufo ƙofar. A.m ya saki dariya don kunyarta ta na matuƙar burge shi matuƙar gaske,saboda ya na son mace mai kunya juyawa ya yi zuwa waje jin shigowar motar Zainab,ya saki duk wani wulaƙanci da yake son yi mata da tsanar ta da yake ji zai more abin sa kafin zuwa ranar rabuwar su,saboda tsakani da Allah ya ji wani girmanta a ranshi tun ranar da ya mallake ta,tsananin talaucin da take ciki bai saka ta zubar da mutuncin kanta ba. Ƴa ƴan'uwana mata don Allah mu kama darajarmu domin shine mutuncinki, don Allah ƴan mata ka da son abin duniya ko jinkirin aure ya sa ki zubar da mutunci,don ki na tunanin kin daɗe ba ki yi aure ba ba zaki yi ba,ki tuna lokacin ki ne bai yi ba,kuma duk daren daɗewa in da kina raye za ki yi,yayin da ki ka yi aure wulaƙanci shi ne abin da za ki girba har ƙarshen rayuwarki. Kuma ƴar'uwa da ki yi saurin aure ki fito gara ki daɗe ba ki yi ba,ki daure har ki samu wanda zai kula da ke emotionally,phisically financially,and mentally.Shawara ce. Juwairiya gado ta faɗa tare da ɗaukar filo ta rufe fuskarta da shi. " Mai ya sa yake min irin waɗannan kalamai ne wai dama ba shi da kunya haka?Kai na rasa gane wa wallahi gabaki ɗaya ya canza dariya fa ya yi min." Sai ta saki murmushi ta mirgina wani gefen ta na jin wani irin nishaɗi a cikin zuciyarta. " To ko ya fara sona ne?" Da sauri ta kori wannan tunanin a cikin zuciyar ta amma kuma ta na fatan haka ta kasance,da sai ta ce tafi kowace mace sa'ar miji duniya,don A.m wuta ne gurin kyau da tsari. Washegari Juwairiya ta na kicin abinci take haɗawa hankalinta kwance cikin jin daɗin abin da ya faru,jiya tsakaninta da shi jiya saboda kwana ta yi muryar sa na maimaita godiyar da ya yi mata. A hankali ya shigo ba tare da ta sani ba don ta zage ta na haɗa mishi abincin da zai ƙayatar da shi. Ji ta yi an rungume ta ta baya ba tare da ta lura ya shigo ba.Wani irin ihu ta saki tare da matsawa gefe,sai kuma da ta lura shi ne ta ɗan saki murmushi. " Kai ki na da matsala Juwairaah!Yanzu da matar gidan na nan mai kike tunanin zai faru?Ke akan komai sai an ga gazawar ki?" Ta yi shiru kawai ta na murmushi ba tare da ta ce komai ba,don ita ba ta san Zainab ɗin ta fita ba. "Kawo min abinci yunwa nake ji." Ya faɗa tare da saka hannun shi a daidai gurin dimple ɗinta ya fita. Bin sa da kallo ta yi har ya ɓacewa ganinta ta yi ajiyar zuciya sannan ta shirya masa abinci. Bayan ta ije masa abinci ya na zaune da remote a hannunsa ya ce ba tare da ya yi duba gareta ba."Amaryar wucin gadi zo mu yi hira tunda matar so ba ta nan,na lura kamar kina da ciwon rashin magana." Sai ta tsaya ta na kallon shi da ya yi fuska kamar ba shi ya yi maganar ba. " Ki zauna mana kika yi min tsaye haba sai kace wata soja." Namma zama ta yi ba ta ce masa ƙala ba don ta lura so yake ta tanka. A.m da ya kasa controling ɗin kan sa ya matsa kuda da ita ya na mata wasu irin abubuwa. " Don Allah ina roƙon ka bu ɗaya.". Ta ce yayin da idanunta suka fara zubar hawaye tsayawa ya yi ya na kallonta zuwa can ya nisa ya ce da ita."Ina jin ki Juwairaah." A hankali ta yi ƙoƙarin saita muryar ta ta fara magana cikin sanyi. "Ka ce kar na saka soyayyar ka a zuciyata ni ma ina roƙon ka da ka dai na ƙoƙarin kusanta kan ka da ni mu tsaya daga iya sharaɗinmu,saboda ina tsoron kar zuciyata ta kamu da sonka duk da na san kai ɗin ba sa'ar soyayya da ni ba ne,kaddara ta haɗa mu ina jin tsoron ranar da zan tsinci kai na cikin soyayyar ka don na san ka yi min nisa na har abada,amma soyayya ba ƙarya ba ne kuma zuciya ba ta da ƙashi,A.m babu wata mace da za ta yi tozali da kai ba tare da ta faɗa cikin kogin son ka ba. Jikinsa ya yi sanyi matuƙa ganin maganar da take yi daga cikin zuciyarta ta fito. "Juwairaah kin taɓa ganin an yi zaman aure ba tare da haka ba?Duk auren da kika ga ya ginu to hakan ya gina shi.Bani da nufin na cutar dake ki yadda da ni ki yi ƙoƙarin yaƙar zuciyarki daga son jefa ki cikin wahala da take son ta yi,kafin na aureki sai da muka yi sharaɗi babu so a cikin tsarinmu don ba zan taɓa zama dake na har abada ba ,amatsayin matata.Kuma karki manta uban maƙudan kuɗi na sa na auro ki". Ya numfasa ya na kallonta ganin kukan da take yi hannunsa ya saka tare da tarar hawayen da yake zuba kamar an buɗe famfo. " Ki adana sauran hawayen ki a kwai ranar da zaki buƙace su kar fa su ƙare,na tabbata ranar da kika haifa min baby in na baki abin da na yi ninya Juwairiya zaki nemi hawayen ki ki rasa bayan kin ƙarar da su akan banza,don ni banga abin kuka a nan ba.Ki tuna mahaifiyarki na cikin kwanciyar hankali da jin daɗi shin hakan bai saka ki saka ni a cikin farin ciki ba?" Ya tambaye ta idanunsa a kanta hawaye suka ci gaba da zuba ganin taƙi magana sai sai ya miƙe ya fice daga gidan. "Humh ba na tunanin a kwai abin da za ka ba ni na yi farin ciki fiye da ka sani a cikin zuciyarka.Am ka ƙi ka gane abu ne na zuciya Allah ya jarabce ni da sonka tun kafin ka bijiro da manufar ka a kaina,na yi burin kar mu haɗu tun ranar da na yi tozali da kai a kundin rayuwata." Kuka take kamar wata zararriya ta na maganganu sosai daga baya miƙewa ta yi,bayan ta fahimci ya fice daga gidan ta ci gaba da aikinta. A haka rayuwa take wucewa A.m ya na more amaryar wucin gadi duk da ya ƙosa su rabu,amma ya na girmama lamarin Juwairiya a zuciyar sa. Tun ta na ɗari-ɗari da shi har ta saki sosai da shi domin ya bada duk wata ƙofa da zai saka ta saba da shi,har ta kai ga A.m ya na waya da Juwairiya a ɓoye su sha hira ya na tambayarta ko ya jefa ƙwallon a raga. Duk sadda ya yi mata wannan maganar hankalinta ya kan tashi matuƙa ita gani take irin abubuwan da yake mata son ta yake. Juwairiya ta saba da A.m ta na jin sa a ran sa kullum sai sun haɗu da juna ranar da Zainab take gida kuwa,dole sai ya kira ta a waya sun yi hira wannan ya ƙara saka ma Juwairiya son shi na mutuwa ta na jin duk ranar da ya rabu da ita mutuwa za ta yi. Amma idan Zainab ta na nan ko kallon Juwairiya ba ya yi,har yau in zai yi maganar ta ko Zainab ta yi mishi nuna yake bai riƙe sunan ta ba,sai dai ya ce wancan ko wa ta ke da suna. Tun Zainab na mata ƙorafin ta rinƙa cire hijabinta har ta gaji,ta dai na don ta fuskanci ko mai za ta yi mata ba za ta dai na ba,kuma ina ruwanta tun da ta fahimci Juwairiya a kwai tsafta da kula da kai. Juwairiya ta goge ta waye ta ƙara wani irin kyau jikinta ya ciko ko ina,ita kanta mamakin yadda ta goge take yi,sai dai ko hoda ba ta saka wa bayan kwalli duk da Zainab ba ta hana ta ba. To ina ma take da lokacin kanta daga aiki sai chert,don in dai ba ta gurin aiki ta na riƙe da wayarta,ko magana take hankalinta na kan wayarta. Duk lokacin da Juwairiya ta samu tsarki sai ta samu lemun tsami da ruwan gishiri ta sha,ita burinta ko a matsayin mai aiki za ta zauna in dai ya na nuna mata irin wannan soyayyar za ta rayu da shi na har abada. Kimanin tsawon wata bakwai A.m ya na jiran ya ji ta ce mishi ta na da ciki,amma shiru kake ji malam ya ci shirwa,har ya fara tunanin to ko shi ma baya haihuwa. Hankalin sa ya fara tashi sosai gashi A.m har ya kasa daurewa ya tambayi Juwairiya shi fa ya ƙosa,lallaɓasa take yi ta na faɗa mishi Allah ne bai kawo ba,amma a ranta ta san abin da take yi. Ya na zaune a falo zuciyar sa na tafarfasa da ya tabbatar Zainab ta ƙara tafiya ba tare da ta sanar mishi ba,ya ji a ran shi tunna ya na da Juwairiya zai ci gaba da haƙuri har zuwa sadda za su rabu,amma duk da hakan dole ta ɗauki mataki saboda ya kamata ta sanar mishi ko da bai amince ba,ba wai ta kashe wayarta tafi ba. Wayar A.k ya katse masa tunanin da yake yi sai dai bai ɗauka ba wayar ta katse ya bi,amma ba network sai a ka ce wayar a kashe. Wani irin bugu ya ji ana yi mishi wanda ya tada hankalin sa da sauri ya fita don shi a zaton shi ɓarayi ne suke so su shigo mishi,duk da ce wa ƙarfe huɗu da rabi ne na yamma. Ya na isa get ɗin maigadi ya sheƙo da gudu ya na faɗin." Ka yi haƙuri ina bayi na zaga.Wannan wa ne mahaukaci ne yake ƙwanƙwasa ƙofa Allah ya sa lafiya." A.m bai kalle shi ba ya buɗe kofar sai kuma ya ƙame cikin tsananin mamaki ganin Baba Sani a tsaye ya na ta mazurai. NI MA NA YI MAMAKIN GANIN SA SABODA NA SAN BA ALKHAIRI YA KAWO SHI BA NA IJE BIRONA DON NA HUTA. KUCI GABA DA BIBIYAR LINTAFIN KAR KU GAJI BARI NA TUNA MUKU DA SUNAN LINTAFIN. SAKACINA KO HALIN MAZA TAKU JAMLA LAWAL ZANGO TUNATARWA DON ALLAH ƳAN'UWANA MATA KADA KARATUN LINTAFI YA ƊAUKE HANKULANMU MU MANTA DA BAUTAR UBANGIJI,KU TUNA ALLAH YA HALICCE MU DON MU BAUTA MASA NE. YAU TAKE JUMA'A KAR A MANTA KARATUN SURATUL KAHAFI ALLAH YA BA MU ALKAIRUN DA KE CIKINTA AMIN Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Mu haɗu a shafi noma sha shidda.Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 21* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM A.m ya tsaya cikin tsananin mamaki ya na kallon Baba Sani da ya ci magani fuskar sa babu walwala ko kaɗan, alamun da rashin mutunci ya zo koma fiye da haka don a wulaƙance yake kallon A.m da yake jin kamar ya kai mishi bugu. " Uban me ya kawo wannan mara mutuncin gidana ya akai har ya san gidana." Irin tarin tambayoyin da A.m yake yi ma kan sa wanda ya kasa amsa ko da guda ɗaya ne. " Kai Malam na ga ka na kallona kamar ba ka gane ni ba." Baba Sani ya ce cikin ɗaurewar fuska ya na ƙarasowa gurin A.m da ya harɗe hannun sa a ƙirji ya na kallon sa a wulaƙance burin sa ya ji mai yake tafe da shi. "Ba zan kalle ka ba ka san halina ba ni da mutunci mai ya sa ka zo gidana,bayan ka san duk abin da muka yi sirri ne a tsakaninmu,shi ne za ka biyo ni har gida saboda kai tantiri ne." A.m ya faɗa fuskar sa babu sauran fara'a ji yake kamar ya shaƙe sa,domin baƙin cikin dake cikin zuciyar sa. "Ban sani ba na ce ban sani ba wallahi kamar yadda kake faɗin ba ka da mutunci na fika,don ni yawo nake a tasha da gidan karuwai kai ko ina tunanin iskancin na ka haye ka yi,in ban da iskanci ƴar ɗan uwana a gidan ka kake tambayata abin da ya kawo ni gidan ka.Ai tushiya mafarin dawa." A.m ya zare idanun sa ya na kallon shi ganin yadda yake ɗaga murya ya na son kowa ya ji,duk da unguwar ta su ta manya ce kowa ya na cikin gidan sa,amma A.m hankalin sa ya tashi ƙwarai sai ya shiga waige-waige ba yan ya galla ma maigadi harara dake tsaye ya na kallon su. Sum sum ya wuce sannnan A.m ya taso ma Baba Sani cikin hargowa zai make shi,don yadda yake jin zuciyar sa na tafasa kai dukan shi ne samun sauƙi. Ganin da gaske dukan shi zai yi sai ya masa da sauri,amma yaƙi wucewa a gurin faɗa yake ya na hargowa tare da nuna A.m,da yake jin zuciyar sa kamar za ta yi bindiga. A.m ya ƙara kai ma Baba Sani duka daidai lokacin da motar A.k ta sawo kai,da sauri ya yi parking tare da fitowa ya riƙe A.m da yake hargowar dukan Baba Sani. " Ba ka da hankali ne A.m ka san me kake shirin yi ƙanin mahaifin Juwairiya za ka daka karka manta shi ya ba ka aurenta?" A.k ya faɗa don ya kwantar ma A.m hankali ganin yadda ya zuciya. "Allah ya sa mahaifinta ne yazo ba shi ba,tunna yaƙi kama kan sa wallahi zan kulle shi igiya ta yi rara." A.m ya ce cikin zafi yayin da yake jin kamar ya shaƙe shi,shi baƙin cikin sa yadda akai har ya gane gidan sa. " Bar shi A.k ka bar shi ya yi min rashin mutunci dama na lura ba shi da mutunci,amma tsoratar war sa ba za ta yi tasiri a cikin zuciyata ba. "Ka gaya mishi in ya na son lafiyar sa, to ya bar nan kar kuma ya ƙara gangancin wucewa ta hanyar gidan,nan ballantana ya yi tunanin ƙwanƙwasa min gida,ka san ba shi da mutunci da ba ni ya samu ba haka zai fasa ƙwan kowa ya ji." A.m ya ce ya na kallon sa da yake ta karkaɗa jikin sa alamun irin da rashin mutunci na zo ko fiye da haka. " Ka kwantar da hankalin ka bai kyauta ba duba ga irin halaccin da muka yi masa,amma ka tsaya mu ji mai yake tafe da shi." Ya ce da A.m sannan ya juya ya kalli Baba Sani ya ce."Mai ya sa ka yi haka ba yan mun yi waya da kai na ce maka zan zo." Baba Sani ya kalle shi tare da kaɗa kan sa ya na ce wa."To dussa ne ni da za ka shanya ni kwana biyu na jira ka ba ka zo ba,shi ya sa na yanke shawarar na je gurin wannan ɗan mara mutuncin komai zai tafi daidai." Tsaki A.m ya yi ya ce da shi." Ai ko in ka ƙara gangancin zuwa ƙofar gidan nan ni ne ajalin ka,don na tsane ka tsana mai tsanani mugu kawai wanda ya kasa riƙe ƴaran wan sa." A.k ya kalli Baba Sani ya ce." To wai tsaya don Allah mene ne ba mu yi maka ba,za ka zo ka dami rayuwar mu?Kuma na gaya maka zan zo har gida aiki ne ya yi min yawa kai kuma mara haƙuri." "Oho koma me zaku ce kuce amma ni ba ruwana gara ku tsaya ku ji mai yake tafe da ni ba wai ku tsaya ɓaɓatu ba." Ya ce ya na girgiza jikin shi har da ƴar waƙar shi irin na cikakkun ƴan bariki. A.m ya watsa mishi mugun kallo ya na jin wani irin tsanar shi mai tsanani ta na zagaye duk ilahirin jikin sa ya ce. " Ko ma me ya kawo ka ka ɓace min a ƙofar gidana ko na kira ƴan sadda su tafi da kai." "Sojoji za ka kira ba ƴan sanda ba kuma abin kunya a gare ka take,ka kulle surukin ka don ko banza na gama da kai tun da ƴar wana kake aure shi ya sha nono ya saki na kama." Ya ba A.m amsa jin abin da ya faɗa babu ko ɗigon damuwa a zuciyar sa. A.m ya yi ƙuta ya ce." Allah ya tsare ni na haɗa zuriya da kai dangin matsiyata,ai ko ba mata a duniya gara na zauna ban yi aure ba da na auri zuriyar ka jinin matsiyata dangin talauci." Ya faɗa cikin ɓacin rai ya na jin kamar ya shaƙo shi ya gama masa aiki,don ya ƙara masa baƙin cikin da ke cikin zuciyar sa. " Ok to haka kace ko ɗan ƙaruna to sako min ƴar ɗan'uwana wacce kuka yi auren kwangila da ita,dama na zo na tuna maka da yau saura wata biyu da kwana shirin da takwas da yini ɗaya,amma fa ban da kwana auren kwangila ya ƙare ma'ana kuɗin ka sun ƙare shekara ɗaya ka iba,kuma waɗannan watanni biyu da kwanaki suka rage sai a shirya sako min ƴata,don Juwairiya ba ta da uban da ya fini." A tare suka buɗe baki tsananin mamaki ya kama su ko kaɗan ba su taɓa tunanin haka zai faru ba,lallai Baba Sani ya cika tantiri ɗan duniya ne wanda ya zama lamba ɗaya. A.m cikin fushi ya taso kan sa ya na faɗin." Baka da hankali matar ta wa kake maganar kwanakin rabuwarmu,kai za ka sake ta ni nake da ikon sakinta,kuma babu ɗan iskan da ya isa ya sakin min mata. Ya numfasa ya na jin wani irin tashin hankali da mamakin sa ya ci gaba da ce wa."Kuma da kake maganar haka auren ta na yi don ta haifa min yaro,ammma ko ɓatan wata ba ta taɓa yi ba shi ne har za ka zo ka ce wa'adi ya cika?To na ga uban da ya isa ya sakin min mata." " Allah ko ɗan zamani hauka kake yi ka yi abu da ƙuruciya ni kuma zan nuna maka da wanda ya riga ka shan iskar duniya,ya girme ka ko da da sakan ne.Bari kaji lokacin da ka zo nai man auren Juwairiya na bi dindigi na gane kai ko ɗan waye da duk wani labarin ka,har da asalin matarka da komai na ta na sani zan iya zuwa gurin aikin ta na kai mata recording ɗin da na yi,lokacin da ka zo neman auren Juwairiya har ma da na ɗaurin auren ku." Sai suka zare ido jikin A.m ya yi sanyi matuƙa har ya kasa magana don ya cika tantiri na gaske! Ganin yadda maganar sa ta razana su sai ya yi dariya ya ciro wayar sa ya kunna recording ɗin suna ji,babu wanda ya iya ko tari a cikin su sai tsantsar razana da A.m ya ji musamman a ce ya kai ma Daddy kamar yadda ya yi ninya. A.k ya gyara tsayuwar sa ya na jin wani wani irin tashin hankali ya na ziyartar sa,wani irin gumi yake jiƙa shi don ko kaɗan bai yi tunanin Baba Sani ya na da wannan wayon ba,lallai sun yi boko mai zurfi amma shi ya nuna musu aiki da shi. " To kun shirya saurara ta ko na tafi don ni ba na son ɓata lokaci." A.m shiru ya yi ya ɗauke kan sa ji yake kamar ya fisgo shi ya danƙara wayar da ƙasa. A.k ya kalli A.m da ya kasa ce wa komai ya ce da shi." Ka shirya zama da Juwairiya a matsayin yadda ko wace mace take a gidan aurenta ko har yanzu ka na kan bakan ka ku...?" " Allah ya kyauta na zauna na har abada da gaiyar tsiya ai in wannan mara mutuncin ya na raye ba zan taɓa haɗa zuriya da su ba,kuma mai zan yi da gayyar matsiyata ba na son Juwairiya yaro nake son ta haifa min na saketa,sannan ba zan yi asarar kuɗina ba dole sai ta haifa min baby,wallahi ko dashe ne sai am mata don ba zan yi asarar kuɗina ba." A.m ya katse A.k da yake magana cikin zafi da kakkausar murya mai hargowa. " Kuɗin ka ne zai tafi a banza ka maida matsiyata masu kuɗi,dama ta hanyar wani Allah yake azurtawa ɗan ƙaruna,yanzu sai ka ƙaro kuɗi na shekarar ne ko shekara biyu,amma fa ka sani ba zan yadda Juwairiya ta zauna a cikin wannan daular ba,don haka sai ka shirya kawai ka je a farke mahaifarta ayi mata da she ta haihu kowa ma ya huta." Ya ce ya na kallon A.m da jikin sa ya yi sanyi don yanzu yake nadama ashe tunanin halin sa ya wuce wannan. Sannan ya ɗora da ce wa "Mahaifiyar Juwairiya ta taso ni kan sauran lokacin da ya rage Juwairiya ta dawo aure za ta yi mata,sosai ta yi min bore har ta na barazanar kai ni kutu ƙila tare za a kai mu ko kuma ka ba ni kuɗin da zan san yadda zan yi na kawar da idanunta kafin wa'adin ya cika." Har zuwa lokacin shiru suka yi suna kallon juna da mamakon sa. "A.m ka na jin abin da ya faɗa na fara shakku an ya mutum ne shi ko aljani? Allah ba shi da imani karfa ya zo ya ruguza komai,zan ji kunya sosai domin ni Daddy zai fi ba ma laifi don ban kasance aboki na ƙwarai ba." A.k ya ce ran shi a ɓace ganin abin da suka yi cikin sirri ya na son ya fasu. " Kyale matsiyaci ka ba shi kuɗi kawai don ba zan iya sakin Juwairiya ba matuƙar ba ta haifa min yaro ba,don ina son jinina ya fito ta tsatson ta tabbas ubanta mutumim kirki ne don ya ba ƴar sa tarbiya na ƙwarai,amma na san kai yaranka sai dai su ɗauki halin dabbobi don ba su yi dacen uba na ƙwarai ba." Dariyar jin daɗi ya saki ganin ya ci galaba a kan sa ya ce." Allah ya sa karuwai za ka kira su ni na san halin su,kuma na san irin tarbiyar da na basu in dai kawai na ji bayani wato kuɗi abokan harka.In baka accourt numba ne ko cash za a bani." Takaici ya hana A.m magana sai A.k ne ya kalli A.m ya dafa kafaɗar sa ya na faɗin "Ka koma ciki kawai zan ji da shi." Kamar ƙaramin yaro ya juya ya shiga ciki da ƙyar yake ɗaga ƙafafun sa ya na shiga falo ya zauna shaɓar, ya na jin wani ƙunci a ran sa abu ya haɗu ya tarun masa goma da ashirin. Juwairiya ta fito daga kicin jin shigowar sa wanda ta ɗan ji hayaniya sama-sama,amma ba ta sheda abin da yake faruwa ba,asalima komawa kicin ta yi ta ci gaba da aikin ta don babu kyau laɓe. Hannu ya miƙa mata ta iso gare shi janyo ta ya yi ta faɗa ƙirjin shi tare da matse ta da ƙarfi har sai da ta yi ƙara ya ce." Juwairiya ina cikin damuwa sosai abu ya yi min yawa.Zainab ba ta son farin cikina wai dama haka ne abin da kake so shi yake wahalar da kai?Tana amfani da son da nake mata ta na azabtar da zuciyata,ga Baba Sani ya zo ya ƙara min zafi." " Baba Sani ya zo gidan nan na shiga uku." Ta ce tare da zare jikinta daga gare shi ta zare idanunta don ta san zuwan shi ba alkhairi ba ne. Kan sa ya ɗaga masa ya riƙe hannunta sosai." Yanzu ta tafi."Ya kwashe duk yadda suka yi ya gaya mata cikin rauni yake maganar. Juwairiya ta yi shiru ta na kallon sa sai ya ba ta tausayi sosai juya mishi baya ta yi da nufin ta ce mishi ya bayyana auren su kawai,don ta gama kamar ya fara son ta da irin kashe ta da shaukin kala-kala da yake yi,amma sai ta ji muryar sa ya na faɗin. "Juwairiya don kawai ina kwaɗayin na ga ƙwaina a duniya kuma ke ce mace ta biyu bayan Zainab da na ji zan iya rayuwar auren wucin gadi da ita,da ace zan iya zama da wata ba yan ke da zan rabu dake ne kawai saboda tantirin ƙanin mahaifin ki sam ba shi da mutunci,sai dai kamar yadda ba zan iya rabuwa da Zainab ba domin an halicci zuciyata don ita haka ba zan iya rayuwar auren wucin gadi da wata mace ba in ba ke ba." Tasowa ya yi ya rungume ta ta baya kamar yadada Juwairiya take hawayen jin ya na faɗin zai iya rabuwa da ita hak shi ma ya fara hawayen rashin ɗa. Juyo da ita ya yi suka fuskanci juna dukkannin su hawaye na zuba fuskar su ya ce."Kin san na yi miki ƙoƙari Juwairaah don Allah ko da nine ba na haihuwa ki yadda na zuba kuɗaɗena ayi miki dashen mahaifa kin ga Zainab ita an yanke mata mahaifar." Da yadda yake magana ya ba ta matuƙar tausayi sosai ta ƙara sautin kukan ta ta na ganin an ya ta yi masa halacci kuwa,duba ga irin abin da ya yi mata kuma sai da ta yi masa alƙawari karo na farko ta ji ba ta kyauta masa ba,don har ciki ta zubar wanda bayan ta sha lemun tsamin,amma har wata biyu bai zoba sai da zai zo ta ji ciwo sosai,sai dai shima bai yi ma zuciyarta adalci ba saboda ta na son shi ko idanunta ya isa ya isar mishi da tsaƙon hakan,amma ya yi biris da ita ko tunanin shi bai gane son shi take ba." A tare suka fara tafiya kowannen su ya shige ɗaki domin samawa junan su maslaha daga halin ƙuncin da suke ciki. A.k da Baba Sani ya sasha fama kafin Baba Sani ya amince ya karɓi kuɗin da ya ba shi,amma ya rantse in har lokaci ya ƙare zai zo ya ƙara karɓar wani kuɗi,kuma A.m ya sa a ran shi dole ya saki Juwairiya ko da ba ya so. A.k ya yi shiru kawai ya na kallon sa har ya gama zuba mishi rashin mutunci ya tafi,a ran sa takaicin A.m yake yi sosai don shi ya jawo musi wannnan tashin hankalin,haba!A ce kana auren mace wani yazo ya yi maka iko da ita sai ka ce ya na zaman dadiro. Ai dama duk abin da aka yi tare da son zuciya a kwai nadama a cikin sa dole mutum ya yi nadama, yanzu in da duniya ta san matar sa ne har wani banza ya zo ya maida su A.t.m ɗin sa,to koma mene ne ai tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwa ka doka. Sati biyu da Zainab ba ta nan Juwairiya ta yi amfani da damar ta koya mishi wani kalar kulawarta,wanda shi kan shi mamakin ta yake don yanzu ta cire kunya ta na son ta saka mishi soyayyarta a ciki zuciyar shi,don haka duk abin da ta san zai faranta mishi rai kuma matar sa ta kasa da shi Juwairiya ta cika gurbin sa,shi kan sa mamakin yadda ya saki da ita yake yi. Sai dai ya kan tuna Juwairiya ba macen da namiji zai iya wulaƙantawa ba ne ko da kuwa ba ya son ta,don Allah ya yi mata abubuwa da dama ga tsananin kula da ibada sosai,sam ba ta wasa da ibada wanda hakan ya na matuƙar ƙara masa ƙimarta a idanun sa. In ka gan su a gidan zaka ɗauka wasu masoya ne ko da yake ya sha gaya mata shi kan sa bai san ya aikai ya sake da ita da yawa ba,amma kawai su rayu tamkar ma'auratan da suka yi auren soyayaya domin ya na jin zai iya mata komai a zaman su in dai zai faranta mata. A.m ya kai da komai ba ya iya yi sai dai ta yi masa hatta abinci a baki take ba, gabaki ɗaya ya shagwabe ya koma kamar wani ƙaramin yaro ya na fatan ina ma ace Zainab ɗin shi take da wannan hali na kula da shi lailai da ya more. Juwairiya ta dage sosai ta saka wata irin shaƙuwa a zuciyar A.m ba tare da ya san haka ba,shi ya na danganta hakan da irin kular da take ba shi shi ya sa in ya ji kewarta sai ya ɗauka jikinta da yake matuƙar so yake sa shi jin kewarta. Amma take zai nemi waya ya kirata su shi hira sosai,ya kuma ɓata lokacin sa ya na waya da ita. Duk irin kular da take ba shi ta mai da kanta tamkar baiwa a gare shi ta na jiran ta ji ranar da zai rungumeta ya ce mata ina son ki! Amma bai taɓa faɗin haka ba sai kalaman da suke sakata kuka yake faɗi irin su,kina da wata irin baiwa da ba ko wace mace take da shi ba,in kika riƙe alƙur'ani ki na karatu wani irin ƙarin ƙima kike samu a idanuna,domin Allah ya jarabce ni da son mace mai kula da ibada. "Juwairiya duk ranar da muka rabu zan yi fama da kewar ki ina kishin mijin da zaki aura nan gaba domin ya yi dacen mace ta gari da baiwar kyau da sura. Alokacin da nake kallon ki cikin hijabi sai nake jin tsanar ki kamar ba ki waye ba,ashe Juwairaah mata masu saka hijabi wata baiwa suke da shi na kyawun sura kike ɓoyewa.Surar ki abin sha'awa ce ga kowa. Har lau ina faɗa miki zuciya ta da gangar jikina za su yi kewar ki,amma ba komai zan mai da kula ta akan ɗan ki sai ya zama wani abu a rayuwa,Allah ya sa ki haifa min baby mai kamar ki." Duk lokacin da ya faɗi haka Juwairiya ringume shi take ta saka kuka iya ƙarfin ta shi kuma ya ɓuge ya yi ta aikin rararrashi. A haka dai suke zaman su cikin kulawa da juna da girmama juna don in Juwairiya na mishi magana,gabaki ɗaya hankalin sa yake ba ta ko tari ba ya yi sai ta gama ya na matuƙar girmama lamarin ta,don ita ma ta na ba shi kulawa har ya na kawai ya ƙyale Zainab ta tafi duk in da yake so tun da ya na da wanda take kusam makwafin ta kawai Juwairiya ce baya jin ta a zuciyar ta amma komai na ta ya yi masa. Ranar wata alhamis Juwairiya ta dage ta shirya ma A.m abincin da yafi so wanda duk sai da ta zauna ta tambaye shi,ta kuma saka su a cikin ranta don kullum sai ta tambaye shi abin da yafi ƙauna a cikin rayuwar sa,kuma duk ya gaya mata. Ƙarar shigowar mota ta ji da sauri ta miƙe daga sallayar da take zaune bayan ta idar da salla,ta na karatun alkur'ani ta rage zaman jiran dhi don ta ƙagu ya dawo musamman da ya kirata ya ce mata a kwai labari mai daɗi. A ranta tunani take ko zai zo ya faɗa mata ya na sonta shi ya sa ta ɗauko kur'ani ta na karantawa,saboda ta zaƙu matuƙa da ya shigo. Ɗaga labulen ke da wuya ta leƙa kawai sai ta ga Zainab ta fito janye da akwati,wani irin tashin hankali ya ziyarce ta ta saki wata ƴar ƙara na rashin jin daɗin dawowar ta ta zauna jaɓar! Sai kuma ta yi zubbur ta miƙe da ta kalli kanta a madubi sai da gabanta ya buga ta yi kyau matuƙa ga ƙarin haske da ta yi,da jikinta bai da haske amma yanzu wani irin ja ta yi sosai jikinta kamar ka losa jini ya fito. Falo ta fito amma lokacin har Zainab ta shige ciki sai ta koma ɗaki ta yi kiran A.m tare da yi mishi albishir da Zainab ta dawo. Zubbur ya miƙe ya tattara komai ya taho gida don ya ganta saboda ya yi mising ɗinta sosai. Ya na shigowa ɗakin ya same ta a zaune ta na ɗaki waya take yi ganin sa sai ta kashe wayar ta miƙe ta na zare ido,tare da dafe ƙuncinta a tunanin ta mari zai kai mata kamar na farko. Amma sai ya ba ta mamaki sosai ya ganin ya harare ta ya saki tsaki ya nemi guri kusa da ita ya zauna. Abin sai ya ba ta mamaki ta kalle shi ta ce." Habibi i miss you zuc.." Wata uwar harar ya daka mata tare da taɓe bakin sa. "Rufe min baki shashasha kawai ni za ki yaudara duk abin da kika ga dama ki je ki yi ta yi na zuba miki ido duniya ce,tunna ƴan'uwan ki dabbobi ne ba su san a kwai Allah ba bare annabi ya faku." Ya miƙe ya sauko ƙasa don ya ci abinci ita ma sai ta biyo shi dama wanka ta yi ta na son ta sauko ƙasa ta ci abinci,sai aka kira ta ganin kiran na kuɗi ne don wata Hajiya ce take son ta yi mata oder kayan ɗaki za ta aurar da yara biyu. Biyo shi ta yi da sauri suka sauko ƙasa duk yadda take ta mishi hira bai tanka ba don ya so ace Juwairiya na gefen sa yake cin abincin ya yi ta mata sanni ,ita kuma ta yi ta murmushi dimple ɗinta ya na lotsawa shi kuma ya yi ta saka hannu a gurin don ya na burge shi,sai ya ciro wayar sa ya tura mata da tsaƙon godiyar abincin har da steaker na kis akai ma abinci. Rungume wayar ta ta yi tare da sakin ma hoton sa da ta ɗauke shi ba tare da ya sani aba suna zaune a falo,saboda bai taɓa ce wa zai ɗauke ta hoto ba duk da in ta yi kwalliya ya yi ta yabawa shi ya sa ita ma ta ɗauke shi ba tare da ya sani ba. Kuma ya yi kyau sosai kamar wani balarabe ta saka pasword a gurin hoton kafin ta buɗe sai ta rubuta sunan ta da full sunan shi. Da sauri ta saka ƙaton hijabin ta har ƙasa saboda tsoron fita kiran da Zainab ta yi mata,sai da gabanta ya buga don gani take hijabin ƙara mata kyau kawai ya yi,amma dai ya rufe surar jikinta da A.m kullum sai ya yi ta yabon shi ya na zuzuta wa. A hankali ta taku har zuwa in da suke duk da dukan da gabanta yake yi. Zainab haka kawai ta tsinci gabanta ya faɗi ganin yadda Juwairiya ta canza har sai da ta miƙe, gabaki ɗaya ta zama kamar wata matar gidan yadda fuskar ta ya canza ta ƙara haske sai abin ya ba ta mamaki ƙwarai ta kalle ta tare da sakin ƙara ta ce. TO MASU KARATU ABIN DA ZAINAB ZA TA CE YA TSORA TA NI NA MIƘE DA SAURI HAR BIRO NA YA FAƊI GASHI NA NEME SHI BAN GAN SHI BA KUCI GABA DA BIBIYAR LINTAFIN DON JIN YADDA ZA TA KAYA A CIKIN LINTAFIN NAN MAI FARIN JINI. BARI NA TUNA MUKU DA SUNAN SHI SAKACINA KO HALIN MAZA TAKU JAMILA LAWAL ZANGO JAMCY Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 22* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM "Ke uban me kike yi haka ki ka canza ko kayan shafana kike amfani da shi in ba na nan? Duk da na kulle ɗakina." Zainab ta ce ta na kallonta cikin tsananin mamakin yadda ta ga Juwairiya ta koma lokaci guda. Juwairiya hankalinta ya tashi ita kanta ta yi tunanin hakan dama dole ta yi maganar canzawarta,ko A.m da suke tare kullum sai ya yi maganar ta ƙara kyau bare Zainab da ta ɗan jima ba ta ganta ba,sai ta yi shiru ta na zare ido. "Dear ba ka ga yadda yarinyar nan ta zanca ba kalli jikinta ka gani da key na na tafi,amma ina tunanin shafe-shafe take yi da siyan supplement irin yadda ƴan matan yanzu suƙa ɓace da siya don su yi kyau. To in ma shi kike yi wallahi ina tausayin ki matuƙa don babu in da zai kai ki sai motar nadama,domin duk tashen kyau da kika yi daga ƙarshe cutar canser ita ce ajalin ki,kin ga kin kashe kan ki a banza saboda kwaɗayin duniya da son burge namiji,gara ki tsaya a haliitar da Allah ya yi miki,saboda namijin da kike yi don shi gudun zai yi,kin ga wa gari ya waya? " A.m da ko kallon Juwairiya bai yi ba haka zalika bai kalli Zainab ba da take zuba nasiha,a ran sa ya na tunanin dama ta na da hankalin yi ma wani nasiha ta kasa yi wa kanta.Ya na cin abincin sa hankalin sa kwance,irin ba ruwana can ku ƙarata ba ta shafe ni ba. A yatsine ya juya ya kalli Zainab sannan ya yi ma Juwairiya kallo ɗaya ya ɗauke kansa don ji ya yi ta burge shi sosai ya ije cokalin abincin sa ya na hararar da ta zame masa ƙa'ida tare da kallon Zainab." "Ta ina zan gane hakan tun da ba kallon ta nake yi ba ke ma tsokana na kike bayan kin san idanuwana ba sa iya kallon wata mace sai ke,kuma in ta na shafe-shafe ina ruwan ki ba aure za ta yi ba.Kuma ni ba na tunanin haka wataƙila canjin abincin da ta samu ne ta canza kin san ko wace mace da kalar jikinta.Kuma ga shi ta iya girki sosai wallahi ina yabawa abincin ta a kwai saka natsuwa a zuci." Zainab ta harare shi ta tsaki tsaƙi jin abin da ya ce." Oho Allah ya sa a duniya za ka ce ita ta ci gasar iya girki bai dame ni ba, ba wahala na zo yi a duniya ba bare na bautawa wani can,kuma da kake magana in dama ba ta iya abinci ba korar na zan yi tun da dalilin da ya saka aka ɗauko ta kenan." Kamar ba zai ce komai ba ganin yadda ta ƙule amma ya na son ya ƙuntata mata, saboda ya fahimci in ya ce dukan ta zai din ga yi haka za su ci gaba saboda ba za ta taɓa canza halinta ba,shi kuma sam ba ya son ya mai da gidan sa gidan dabbe musamman da yanzu Juwairiya ta ɗauke shi kamar wani waliyi." Spoon ya ɗauka ya taɓe bakin sa tare da ɓare ledar tuwon shinkafa da ta tuƙu sosai ya zuba miya,ya kalli Zainab da take huci kamar wata kububuwa don ya ya bi Juwairiya ya ce."Ai ita komai ta iya ta na da ƙoƙari matuƙa dubi gidan nan komai tsaf-tsaf sai tashin ƙamshi da yake saukar da nishaɗi a zuciya ga..." A.m ya yi shuru da maganar da yake yi jin an yi jifa da kayan abincin da yake ji a ƙasa. " Na ji ta iya koma mene ne ba ruwana kuma in ban da munafunci ce wa ka yi ba a gida kake kwana ba in na yi tafiya shi ne kake maganar iya abincin ta." Miƙewa ya yi a gadare ya ba ta amsa da ce wa."An gaya miki kuɗin banza nake samu da zan din ga yawo hotel ina kwana?Da ma sau ɗaya da kika yi tafiya na kwana a can tun da na ga ba canza wa za ki yi ba, na na haƙura ina kwana a gida ai da babu gara ba daɗi ko banza a kwai wace za ta ba ni abinci." "Ya ishe ka a gaban wata banza daƙiƙiya kake gaya min wannna maganar?Ya zama dole Juwairiya ta bar gidan nan duk da ba na tunanin ko kallon ta za ka iya kuma na yadda da kai A.m,amma ai ta isa aure kawai zan ɗauko yarinya ƙarama in ya so ta koya mata aiki ta bar min gidana." Am ya kalle ta ya ɗaga kafaɗunsa alamun bai dame shi ba ya ce." Ya rage na ki Zainab mijinki na ke matuƙar ba za ki zauna ki kula da ni ba,ni kuma ina da damar da zan hana duk wata mai aki shigowa gidan nan sai wanda na ya ba da abincin ta tun da ni ake girka ma wa,in kuma za ki canza ta fine amma kece za ki zama makwafinta ba ki ba fita gantali sai kin girka min abinci." " Kalle ni da kyau ai wallahi ƙarya ka ke don ba ka nemi aure in da matar ka za ta dafa maka abinci ba." Ta faɗa ta na juya jikinta tare da takun girma sannan ta ɗora da ce wa." Kuma kan ka ake ji ni ƙara fita zan yi saboda kaya ake so da yawa,amma kafin na tafi dole na kawo yariyar da Juwairiya za ta koya ma aiki." Ta wuce zuwa da sauri bayan ta harari Juwairiya ta ce "Kuma da ga yau na hana yin girki tare da na ku ki yi mana na mu daban kuma daban." " Allah ya sa bangon duniya za ki ba wata ƙasa ba mu zuba ni da ke shege ka fasa." A.m ya faɗa mata lokacin da ta haye sama ya juyo ya kalli Juwairiya da ta bushe a tsaye ta na kallon dirama,girar sa ya ɗaga mata tare da kashe mata ido ɗaya ya ganin ta firgice ya manna mata kiss a kumatu. "Abinci ya yi daɗi ƙwarai " "A kwai tukwici an jima." Zare idanunta ta yi ta zuba mishi ido lokacin da ya haye sama ya na sakin mata murmushi mai tsada wanda ya saukar mata da kasala har sai da ta zauna. A hankali Juwairiya ta ja jikinta ta shige cikin ɗaki ta na mamakin A.m da kullum saka ta yake a cikin shakku. Ranar wata safiyar talata Juwairiya ta shirya za ta gurin Mama.Ko da ta isa gidan Mama ba ta nan sai da ta jira ta sannan ta dawo daga moƙota da ta shiga. Cikin mamaki Mama ta tsaya ta na kallonta tare da riƙe bakinta don ta rabu da zuwa gidan kwana biyu. "Juwairiya kin gan ki kuwa haka kika dawo sai kace amaryar da take ganiyar cin amarci!Gaskiya kin yi kyau sosai." Gaban Juwairiya ya yanke ya faɗi gani take kamar Mama na zargin wani abu,irin yadda take kollonta cikin mamaki. " Kai Mama hutu ne fa kawai saboda kuɗi suke da shi sosai." Mama ta matsa kusa da ita ta zauna tare da riƙe hannunta ta na shafawa. "Gaskiya kin yi kyau matuƙa ki na sane da saura wata biyu da kwanaki ki gama aikin ki ko?" Ta tambaye ta da ƙosawa sannan ta ɗora da ce wa." Na matsu ƙwarai na ga kin yi aure ji nake kamar rai na ya na jiran wannan ranar ne kawai." Mama ta faɗa ta na ƙarewa Juwairiya kallo tare da tunani barkatai a zuciyarta. " Mama aure lokaci ne ai zan yi in lokacina ya yi kuma ni yanzu aure tsoro yake bani,ji fa Mariya har sun rabu da mijinta.Na matuƙar tsorata Mama ina tsoron kar na yi aure na dawo ina zawarci." Ta faɗa yayin da idanunta suka yi rau-rau tuna maganar da A.m yake gaya mata a kullum. " Ko wa da ƙaddarar sa Juwairiya kuma mutum ba zai iya tsallake ta ba,wataƙila zaman su ya ƙare da mijinta a kwai rabon wani a gaba shi ua sa suka rabu,amma kar ki saka wannan a ranki ki saka a ranki za ki yi aure da zuciya ɗaya." Ta faɗa ta na kallonta sannan ta miƙe tare da juya ma Juwairiya baya ta ɗauko kuɗi ta ce."Kin ga wannan kuɗin nan,ina adana su ne in kika gama aikin nan kamar yadda aka iba sheƙara ɗaya,in dai Sani bai amince ki yi aure ba to za a haifi ɗa mara ido tsakanina da shi." "Mama hakan ma ba zai faru ba in sha Allahu aure zan yi kar ki ta da hankali Mama." Juwairiya ta faɗa jin abin da Mama ta ce ma ta sai hankalinta ya tashi matuƙa, ta shiga zubar hawayen da ta kasa gane dalilin yin sa saboda tarin damuwar da yake ranta. A ranar Juwairiya ta je da nufin ta ba Mama irin tarin kuɗin da A.m yake ba ta saboda hannun sa a sake yake,amma jin irin maganganun da take yi mata mai kama da wanka da ruwan jurwaye, sai hankalinta ya tashi ta koma ba tare da ta iya ba ta kuɗin ba,saboda ta na tsoron kar Mama ta tuhume ta. Koda ta fito za ta tafi Mama ta ɗauki tsawon lokaci ta na mata nasihar da ta kula da mutuncin kanta,a haka suka rabu jikinta kamar an yi mata dukan tsiya. Zaune suke a falo Zainab ta na gefen A.m da hankalin sa,ya ɗauku akan labarai da ake yi tashar aljazira.Zainab ta na riƙe da filet da ta yanka apple ƙananata na ci. Zainab ta kalli A.m da ya ɗan juyo ya na kallon ta ta ce." Ka san me wannan shashashan yaron ya ce?" Ya ɗauke kan sa ga barin kallon ta tare da ɗaukar remote da ke gefen kujerar da ta ke,ya canza tasha ganin an gama labarai ya ce. " Wa kenan." "Amir ma na." Ta na nufin cousing ɗinta sai ta ci gaba da ce wa." Kirana ya yi wai don Allah ya na son Juwairiya." A.m da maganar ta dake shi ya kalle ta zabure ya na faɗin." Amir ɗin ne ya ce ya na son ta kai amma ya fara shaye-shaye." Zainab ta kalle shi ganin yadda ya razana a tunaninta,ta ɗauka ta ɗauka ya na mamakin kamar shi ya na ɗan manya zai ce ya na son ta,don haka ta gyara zama ta na ƙara shige masa ta ce."Kai ma ka razana ni kaina hankalina ya tashi sai da na yi mishi tatas! Saboda ba shi da hankali mai zai ci da Juwairiya ƴar matsiyata!" Miƙewa ya yi ya na faɗin." Amma zan koya mishi hankali matuƙa sai ya yi nadamar faɗin sonta da ya ke yi ke ba ma ita ba ko wani ne ba zai ƙara faɗin ya na son ta ba." " Ai gara ka yi mishi magana mahaukacin ƙila ya taɓu ne,amma na ƙalubance ka da ka ce ko wani ne ya ce ya na sonta zai sani,kamar maigadi da direba Bala in suka ce su na sonta ai faɗuwa ta zo da zama." "Ko ma dai waye ya faɗa ki tsawatar masa don ko da hauka kar su yi gigin faɗa mata." Ya ce ya na ƙoƙarin barin gurin amma sai ta ƙira sunan shi ya tsaya ya na kallonta. " Juwairiya fa dole ta bar gidan nan don aure za ta yi duk jin daɗin girkin ta da kake yi haka za ka haƙura ka bar shi,kuma na yi magana da Anty Fati za a kawo min yarinya ƙarama kafin Juwairiya ta tafi ta saba da gidan kuma ta koya mata girki." Dubara ce ta faɗo masa sai ya dawo ya zauna ya na fuskantar ta ya ce."Haka ne na san dole ta yi aure,amma kafin nan mai zai hana mu saka Juwairiya a makaranta ko da part time ta din ga zuwa,kin ga sai ta karanta abin da ya shafi girki da yadda za ta koya ma yarinyar da za ki ɗauko ko ba komai mun taimaki rayuwar ta,ke kan ki ba kya son zama da jahila marasa ilimi." Zainab ta ɗan yi nisa ta na tunani domin ita sam ba ta ga amfanin saka ta a makaranta ba,saboda iya girkin da ta iya ya isa ba sai ta koyo ba. " Meye alfanun haka a gare mu Juwairiya gwana ce gurin girki ba sai mun kai ta makaranta ba."Ta ce ta na kallon sa." Ok tun da haka kika ce fine ni tunani kawai na yi ya kamata mu taimake ta,amma na fahimci ranki ba so ba a bar maganar." Ya faɗa ya na ƙoƙarin hayewa sama shi ya yi tunanin hakan ne don kawai ya ragewa Juwairiya,zafin raɗaɗin rabuwa da shi fahimtar da ya yi ta na son karatu sannan ya shirya zuwa ƙasar waje yi mata dashen ƙwai na haihuwa don shi ya sadaƙar shi ne ba ya haihuwa duna ga rashin samun cikin da ba ta yi ba. A ran sa ya saka bai wuce su ƙara wata tara a tare ba saboda ya huta da ɗan iskan nan Baba Sani ya tabbata zai ƙara neman sa. Kwana biyu da maganar mai aiki sai ga shi an kawo wata yarinya wace ba ta wuce shekara sha uku ba,sannan ta na da hankali matuƙa ga natsuwa ba ta da hayaniya. A ranar da aka kawo Binta mai aiki yarinyar ta shiga cikin ran Juwairiya matuƙar gaske,don komai Juwairiya ta ɗauka za ta karɓa ta ce ita za ta yi,sai yarinyar ta shiga ranta matuƙa musamman da ta gaya mata labarin mahaifiyarta ta rasu,kishiyar Babar ta take gallaza mata har ta kawo ta aikatau. Da fari Zainab ta ƙi amincewa na su saka Juwairiya a makaranta,amma daga bisani ita da kanta ta nuna masa amincewarta don tun ranar da ya yi mata magana bai ƙara ta da maganar ba. Cikin ɗoki ya gaya ma Juwairiya da ta kawo takaddunta na shedar kammala sakandiri zai saka ta a makaranta,hakan ya yi mata daɗi ƙwarai sai dai da ta sanar ma Mama sai taƙi rashin amincewa,ita a ganin ta a wanan shekarun aure ya da ce ta yi, amma da ta ga Juwairiya ta nace kuma ta san alfanun karatun sai ta amince,da sharaɗin in har ta samu miji za ta yi aure kuma koda ya ce bai amince da karatun ba. Take ta amince da hakan don ta san yadda Allah ya sa ta shiga makarantar ko sun rabu da A.m,Allah ba zai kawo mata wanda zai hana ta karatun ba duba ga yanzu ilmi shine ginshiƙin zaman duniya. A.m zai yi tafiya zuwa chaina Zainab ta buƙaci su tafi tare don ita ma ta na da siyaryar da zai kai ta ta yi matuƙar mamaki da bai hana ta ba ya yi musu viza suka wuce tare. Tafiyar su da sati ɗaya A.m ya dawo saboda ba daɗewa zai yi ba. Ya shigo da murna ya na kwaɗawa Juwairiya kira ta fito da sauri jin muryar sa,dama ta na laɓe ta na kallon shigowar motar sa ta na son ta je garesa,don ta yi missing ɗin shi a lot sai dai ta san Binta na ganin ta fita za ta bita,saboda yanzu bayi ne kawai za ta shiga ba tare da ta bita ba. Jin kirar ya sa ta daure ta fito Binta na biye da ita kamar yadda ta za ta,sai ta tsaya daga bakin ƙofar ta na sakin mishi lallausar murmushi. Hannu ya ware da nufin ta iso gare shi yayin da idanun sa suke bayyana matuƙar kewarta da ya yi. Duk da gangar jikinta na buƙatar haka amma sai ta langaɓe kanta ta na nuna masa Binta da ta yi tsuru-tsuru ta na kallon ikon Allah. Tsaki A.m ya yi da ya kai idanun sa gurin da take nuna masa shi kam har ga Allah ya manta da ita,sai ya ji tsanar ta a ransa matuƙa ganin za ta hana shi hutawa ga shi da alama yarinyar za ta yi munafunci. Hararar ta ya yi ganin yadda ta kafe shi da ido ta na kallon ikon Allah. "Ki same ni a ɗaki." Abin da ya ce kenan tare da ije jakar shi da nufin ta ɗauko masa. Hankalin Juwairiya ya tashi sosai ta juya ta kalli Binta da ta daina kallon sa,lokacin da ya haye sama ta juyo da idanunta ga Juwairiya da ta yi tsamo-tsamo kamar wacce ta faɗa cikin randa. Sai ta juya ta shiga ɗaki ahankali Juwairiya ta sunkuya ta ɗauki jakar da ya ije ta nufi ɗakin sa kamar wace ƙwai ya fashe mata,yayin da take jin matuƙar kunyar Binta don ta san tunani barkatai za ta yi a ranta,tun da ita ba yarinya ba ce a shekarunta ya kamata ta fahimci wani abu. Ta na shiga ɗakin ta ije masa jakar shi da nufin ta bar ɗakin.Am da yake zaune ya sunkuya ya na cire takalmar shi da ya jira ta ta zo cire mishi,amma ganin shiru ba ta zo ba ya fara cirewa. Da sauri ya miƙe tare da janyo hannunta ya haɗa ta da gini ya yi mata rumfa ya na faɗin."Matar wucin gadi ina za ki ko ba ki yi murnar dawowata ba?" Fuskar sa bayyane da murmushi yake magana ya na jin wani irin kewarta da ya yi. " Please ka cikani ina jin kunya matuƙa ban san ya Binta za ta ɗauke ni ba,ƙila a mutunjyar banza.Zargi nake matarka ta na son gano wani abu shi ya sa ta kawo ta gidan nan." Juwairiya ta furta jikinta a sanyaye duk a tsorace take gani take kamar Zainab za ta iya shigowa ga kuma Binta a gidan. Sakin jikinta ya yi ya koma ya zauna ganin yadda take kyarma,ya kwanta a kan gado tare da riƙe yatsun hunnuwan sa ya tallabe kan sa ya na kallon sama. "Ki kwantar da hankali ba na zargin haka saboda Zainab ta ba ni duk wani yadda na ta kamar yadda nima na yadda yadda da halayen ta.Game da yarinyar nan kina tunanin saboda ita zan ƙi more kuɗina ne ki duba irin bita da ƙullin da wancan mara mutuncin yake min. Sannan maganar samun ciki na yanke shawarar zamu je ƙasar waje ayi miki dashen ƙwai kawai ina ga hakan zai fi." Juwairiya ta gwalalo idanu tsoro ya kamata matuƙa har ta fara dana sanin ƙin yadda ta samu ciki,gashi yanzu ya na shirin kai ta ƙasar masu jajayen kunni a ilata mata rayuwarta. Sai kawai ta juya ta fice ba tare da ta ce masa komai ba don in ta yi ƙoƙarin yin magana ta san kalmar haƙuri za ta iya ba shi,akan ta na zubar da ciki ba tare da sanin sa ba. " Ina jiran ki ki shirya min abincina kuma ke za ki bani don haka sai ki kauda idonta a gurin." Ya ɗan ɗaga murya yadda za ta ji ganin har ta fice daga ɗakin. Bayan ta shirya masa abinci kamar yadda ya ce haka ta bi umurnin sa bayan ta aika Bintu ta siyo mata kati. Duk da zargin da Bintu take musu sai ta fita siyo katin a ranta ta na Allah Allah, ta dawo ta ga abin da zai faru a gidan ita har yanzu ba ta dai na mamakin ware hannun sa da A.m ya yi ba akan ta shiga. Juwairiya da take ba A.m abinci a baki ta na jin ƙarar buɗe ƙofa ta ije cokalin tare da zurawa ta shige ɗaki,wanda hakan ya ba A.m dariya ya ɗauki cokali ya ci gaba da cin abin sa ya na tunanin yadda zai kori Bintu a gida. Suna zaune da Bintu Juwairiya na koya mata karatun kur'ani ta ji wayar ta ta yi ƙara da sauri ta ɗaukajin shigowar tsaƙo. "Dare ya yi zan yi bacci ina jiran ki a ɗakina ki yi sauri ko na zo na ɗauke ki." Tsananin mamaki ya kamata ta zare ido ta na kallon Bintu da ta ke kallonta ganin ta firgita. Ƙin zuwa ta yi ta kuma ƙi mai da masa da martani,don ta san duk rashin kunyar shi ba zai zo ya ce ta zo su kwanta ba tun da Bintu ba yarinya ba ce,kuma ko da ta zo irin yadda Zainab ta gabatar da ita ga Bintu a walaƙance na matsayinta na ƴar aiki wacce ake so ta koya ma Bintu aiki ta maye makwafin ta. Suna zaune har ƙarfe goma sannan suka kwanta amma ta kasa bacci tunanin sa ya hana ta bacci. Kamar yadda take juye-juye haka shima yake ta yawo akan gadon shi becouse he missed her a lot da ga ƙarshe tashi ya yi,ya saka takalmin shi ya sauko ya na ƙwanƙwasa ƙofa. "Juwairaah ina kike ki zo ki haɗa min shayina." Ya ce da ita cikin ɗaga murya ya na ƙwanƙwasa ƙofar,amma ta kasa koda motsine saboda figita don ko kaɗan ba ta yi tunanin zai iya biyo ta ba. Jin ta yi shiru sai ya ci gaba da buga ƙofar ya na faɗin."Na san ba bacci kike ba in kuma baki zo ba zan ɗauko spare key na buɗe duk kuma abin da na yi miki ba ruwana." A hankali ta miƙe don kar ta tashi Binta da take tunani ta yi bacci ta fita cikin sanɗa. Dariya ya saki ya ce." Matsoraciya da ki tsaya ki gani abin da zai faru." Juwairiy ta haɗe rai ta ce da shi."Baka tunanin Binta za ta iya gaya ma matarka abin da ke faruwa " "Kin cika tsoro Zainab ba irin matan da za a gaya ma wannan ba ne, ta yadda yadda da ni babu abin da zai faru,kuma ya zama dole ta bar gidan nan wallahi." Hannunta ya kama suka haye sama duk yadda ta so ta dawo ɗaki amma ya ƙi ya kafe dole a can za ta kwana,tun ta na ganin wasa yake mata sai da ta ga ya sakin mata nauyin sa ya na ta shara baccin gajiyar hanya mai tsawo da ya ɗauko,ya barta ta na ta karanta watsiƙar jaki da juye-juye don ko kaɗan ba ta samu ta rintsa ba. Washegari da asuba ta so ta koma ɗakinta amma da zai fita sallah sai ya saka makulli ya rufe ta,sai da ya dawo ya kasheta da zumar soyayyar shi ya kuma sa ta bacci wanda ta yi shi saboda rashin baccin da ba ta yi jiya. Sai misalin tara ya barta ta sauko cikin tsoro a hankali take taku don kunya kasa shiga cikin ɗakin ta yi,sai ta zarce kicin kawai ta ɗora musu abin karyawa saboda kiran ciroma da cikinta yake yi. Juwairiya ta so ta fita daga kicin ɗin hani Binta a kicin ta na ƴan aikace-aikace." Anty sai yanzu kika tashi ai na gama ayyukan ma."Ta ce mata ta na mata wani irin kallo na zargi. Juwairiya ta sosa kanta ta na yaƙen dole." Ok sannu kin yi ƙoƙari bari na ɗora mana girki." Ta ce da sauri ta na son ta kauce ma idanun Binta.Sai ta ɗauki tukunya ta ɗora a gas.Sun yi nisa da aikin su babu mai ce wa komai ita Binta mamakin ganin irin zaman da Juwairiya take yi da mijin Anty Zainab bayan ta san ita ƴar aiki ne,yayin da Juwairiya kunyar kwana da ta yi aɗakin sa take ji saboda ta san Binta ta fahimci ba a ɗakin ta kwana ba,duba ga irin maganganun da take mata na rashin tsoro ya hanata bacci saboda girman ɗakin. " Uhumh." Abin da Juwariya ta ce kenan ta ji gaba da aikin ta." Anty bari na je na wanke bayi kafin ki gama abinci." " Ok." Ta ce ba tare da ta kalleta ta ba.Ta na aikin ta sai ta ji an rungume ta ta baya da sauri ta waiga ta kalle shi a razane.".Na lura so kake ka saka a karya ni a gidan nan kafin na bar shi." Ta faɗa a raunane sai hawaye don tsoron Binta take yi sosai ita gani take Zainab ta ije ta ne don ta saka ido akan gidan. " Juwairiya sarkin tsoro don Allah tsoron ki zai cutar da rayuwar mu ne? Ita ba ta bani kulawa ba kuma na ɗan shekarar ma ba za ta bari na huta ba." Ya faɗa tare da shagwaɓe mata kamar zai yi kuka sai ya ba ta dariya suka yi duka."Ina dai jiye mana abin da zai je ya dawo ne ka san halin Anty Zainab kuma ko ma meye akai na zai ƙare,tsorona kar ta illanta ni kaga mijin da zai aure ni zai yi asara a..." Hannunta biyu ya haɗe da ƙarfi har sai da ta yi ƴar ƙara da hawayen wahala."Ki sa aya a bakin ki kisan irin maganar da za ki yi dani,a gabana kike maganar wani ƙato zai mallake ki koma meye ai ni mijin ki ne kya bari auren ya ƙare kafin nan,ko ba ki san ina kishin mijin da za ki aura ba saboda ki na da baiwar da dole mutum ko ba ya son ki ya yi kishin ki." Ya ce yayin da idanunsa suka nuna ƙarara abin da yake nufi,hakan sai ya bama Juwairiya mamaki sosai ta saki baki da hanci ta na kallon shi. "Yes gaskiya ne abin da na faɗa bacin na san wace ce ke sai nace da gaske ne ki na yin abin da Zainab ta faɗa,don haka ina son jikinki da halayen ki matuƙa." Ya ce da ita tare da lakuce mata hanci ya ƙara rungumeta.Juwairiya ta ji wani iri lokacin da ya furta hakan ta so ace ita ya ce ya na sonta ba jikinta ba,sai ta ji hawaye na sauka a ƙuncinta. " Ni fa ba ni da lokacin ganin hawayen ki ba kuka na ce ki yi min ba,duk da kwana biyu na yi kewar su ki kawo min abincina ina falo." Da sauri Juwairiya ta ture shi daga jikinta gani Binta tsaye ta shigo ta na kallon su ta furta." A'uzu billahi minash shaiɗanir rajiim." A.m da ko kaɗan bai razana ba ya daka mata tsawa ya ce." Don ubanki aljanu kika gani da za ki yi ta'awizi maza fice daga gurin nan." Ya kalli Juwairiya da ta kalli ƙofar da Binta ta ruga da gudu ta fice,sai hawayen ta ya ƙaru bai wani damu ba ya ce."Ki kawo min abincina." Ya fice ya barta cikin tashin hankali da kunyar Binta. A haka dai abubuwa sukai ta faruwa Juwairiya na jin kunya matuƙa A.m kuwa ya samo hanyar da zai kori Bainta daga gidan,don tun da ta shigo Juwairiya ta dai na sakewa da shi ko son ganin shi ba ta son yi gashi kuma ba haka ta sabar mishi ba. Ana gobe Zainab za ta dawo Juwairiya sun sha aikin soye-soye ta gaji matuƙar gaske ta na zaune ita da Binta,wanda yanzu suke zanan kurma a tsakanin su. Da sauri ta tashi ta ɗauko kur'ani saboda ta manta yau ba ta yi karatun da take yi ba wanda ta ibar ma kanta kullum. Binta ta yi zuru ta na kallon yadda take rera ƙira'ar hafsi cikin murya mai zaƙi,sai ta kauda duk wani tsoro ya ce. "Anty." Cikin sanyi Juwairiya ta ije kur'anin ta na kallon ta yayin da gabanta yake faɗi sosai,don ta san Binta magana za ta yi mata ganin yadda ta natsu. Ba tare da ta amsa ba ta zura mata ido ta na kallonta. "Na yi mamaki kasancewarki mace mai addini da hankali kika biyewa mijin Anty Zainab kuna alfasha bayan kin manta duka abin da namiji ya yi ado ne,ita kuwa mace ya na zama tabo da miki a rayuwarta kuma ya ci gaba da bibiyar zuriyarta." Jikin Juwairiya ya yi sanyi jin abin da ta ce amma ta kasa koda motsi bare ta yi tunanin za ta amsa mata.Ganin haka sai ta ɗora da ce wa. " Mahaifiyata kafin ta rasu ta ja layi sosai tsakanina da duka wani ɗa namiji wanda ba muharramina ba,saboda suna tsotse zaƙin da ke cikin rake su yada diddiga.kuma koma me ya faru Anty ke ce a ruwa saboda Anty Zainab ta na da kishi kuma ba ta da hali za ta iya komai ga kuɗi,yayin da kike talaka mara ƙarfi sannan kamar kin ci amanar tarbiyar da mahaifiyar ki ta baki ne." Hawaye suka wanke mata fuska ta kama hannun Binta ta rungume ta na kuka ta ce." Ya zan yi na fahimtar dake har yanzu da ƙuruciya a kan ki,kuma wasu maganar sun yi ma ƙwaƙwalwar ki nauyi ban san yadda zan yi ki fahimci ɗacin da ke zuciyata ba." Janye jikinta ta yi ta ce."Ina da hankali na san me nake yi,kuma na san ke mai aikin Anty Zainab ce kamar yadda ta gaya a gaban ki,sannan wanda kike kwana a ɗakin sa mijinta ne to mai kike so na fahimta in ba zina kuke yi ba?" Juwairiya ta gwalalo ido jin abin da ta faɗa daidai lokacin da suka ji muryar A.m ya daka tsawa da ƙarfi ya nufo kan Binta ya na faɗin. "Ke baki da hankali matar ta wa ta sunna kike faɗin muna zina! Allah ya tsare ni ban taɓa ba kuma ba na fatan na yi." Binta da ba ta fahimci komai ba ta ji dai ya kira Juwairiya,da sunan matar sa wanda ta saka a ranta ta yi kuskuren jin abin da ya faɗa ne. Ganin ya nufo ta ta miƙe tare da saka kuka ta ƙanƙame Juwairiya da ta razana saboda yadda ya canza lokaci guda. Ga mamakin Juwairiya sai ta ga ya ciro wuƙa a aljihun sa wanda ta tabbata da ita ya shigo,da ma da shirin sa ya zo kenan kuma ya samu hanya. Hannun Binta ya samu ya karta sai ga jini tar yarinyar ya saki wani irin kukan azaba tamkar numfashinta zai ɗauke ta na roƙon ya yafe mata,amma ina A.m ya yi nisa baya jin kira idanunsa sun kaɗa sun yi jajur baƙin cikin ce wa da ta yi suna zina da matar sa na sunna ya sa shi zai aikata aikin dana sani. TOFA A.M LAFIYAR KA ƊAYA KUWA MAI KE FARUWA KO KASHA WANI ABU NE BARI DAI NA GAMA TARABBABIN WANNAN LAMARI KAFIN NA ƊORA BIRONA. KU CI GABA DA BIBIYAR LINTAFIN DON JIN YADDA ZA TA KAYA A CIKIN LINTAFIN NAN MAI FARIN JINI. BARI NA TUNA MUKU DA SUNAN SHI SAKACINA KO HALIN MAZA TAKU JAMILA LAWAL ZANGO JAMCY Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 23* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM Cikin tashin hankali ta kama shi ta riƙe ta na kuka sosai kamar ranta zai fita ganin hankalin sa ba shi a jikin sa. "Na shiga uku A.m so kake ka yi kisa?". Ta faɗa cikin muryar kuka ta na girgiza shi gabaki ɗaya ta ruɗe gani take kamar zai ƙara yankar ta. Wani mugun kallo ya watsa mata ya sake ta ya na huci."Allah ya sa ki ƙara gigin aibata aurena sai na zama ajalinki." Binta da ta ji maƙura da gudu ta ruga ɗaki tare da kulle kanta ko kaɗan ba taɓa tunanin mahaukaci ba ne ganin zai illata ta. A ranta ya zama dole tabar gidan domin ba za ta zauna ba ya kashe ta. Ta shiga cikin tsananin mamaki da ya ce Juwairiya matar shi ce,to mai hakan yake nufi bayan Anty Zainab ta gaya mata yar aiki ne. Sam ba ta kawo cewar zai iya ije matar shi a gidan ta zama ƴar aiki ba,shi ya sa ta ɗauka kawai ya gaya mata hakan ne don ya kawar da tunaninta aka suna zina. Haɗa kayanta ta shiga yi domin dole in Anty Zainab ta dawo za ta bar gidan ba yan ta tsegun ta mata. Juwairiya kuwa kuka ta saki ta ƙara faɗawa jikin sa." A.m ka na cutar da zuciyata mai kake tunanin zai faru in har ta faɗa ma Anty Zainab abin da yake faruwa,kawai gidan nan zan bari ayau in ya so duk abin da zai faru ya faru,amm na gaji da wahalar da rayuwata da kake yi. Da ƙarfi ya janyo ta jikin shi ya na huci. "Juwairaah ki saurare ni ba ni da nufin na cutar dake kawai ki fahimci abin ɗaya.." Juwairiya ta katse shi ta na faɗin cikin kuka da murya mai ƙarfi. " A.m ya ishe ka ba ka sona ka tsane ni wannan dalilin ya sa kake wahalar da zuciyata da gangar jikina,kullum sai dai ka yi min maganar ka na son jikina halina da kyawuna shin ni bani da zuciyar da za.." "Juwairiya." Ya faɗa da ƙarfi tare da girgizata ya na zare idanunsa. "Karki kawo min maganar banza kin san dalilin aurenki so ban ga dadilin da za ki kawo min maganar banza ba." Fisge hannunta ta yi ta na kallon sa ta na ja da baya har ta kai bakin ƙofa da gudu ta fice. Ko da ta shiga ɗaki halin da ta ga Binta sai ta ba ta tausayi karɓar tsummar da ta ga yaga cikin kayanta ta na ƙoƙarin ɗaure gurin yankar. Hannu ta saka ta karɓi tsummar ta ɗaure mata hannun yayin da hawaye yake kwaranya a fuskokin su duka. " Ki yi haƙuri haka rayuwa take tafiya a ko da yaushe talaka shi ne a ƙasa ko da shi yake da haskiya." Ta faɗa ta na kallonta idanunta na ƙara zubar hawaye. Binta ba ta ce komai ba sai share hawaye da yake gangarowa a ƙuncinta da ta yi. A ranta ta saka ba za ta ƙara kallon kowa daga cikin su ba balle ta yi magana ta tono ma kanta tsuliyar dodo,ganin abin da ya yi mata ya sa ta fara tunanin ko bashi da imani ne amma har yanzu ba ta amince da faɗin cewar Juwairiya matar shi ce,sai dai in za su yi mata badda kama don kar ta gaya wa Zainab. Kallonta ta ƙara yi ta na jin tausayinta matuƙa ganin yankan da ya yi mata ya shiga ciki sosai. "Anya A.m ya na da hankali?" Tambayar da ta yi ma kanta kenan amma ta rasa amsa sai ta ɗago ta ƙara kallon Binta a karo na biyu. "Wannan dalilin ya sa na ce miki ba za ki fahimci komai ba." Ta faɗa tare da juya mata baya sai dai ta ji a jikinta kamar babu kowa a ɗakin ko da ta juyo wayam ba Binta ta fice daga ɗakin. Duk yadda ta so ta yi magana amma Binta taƙi tanka mata sai in ta ga za ta takura mata ta saka mata kuka,hankalinta ya tashi matuƙa ta yi zuru ta na kallonta. Binta ta saka a ranta ba za ta ƙara mata magana ba balle ta tanka a kan cin amanar da suke yi ita da shi,Allah Allah ta ke gobe ya yi Zainab ta dawo ta saka mata kukan ta kaita gida. A.m bai shigo gidan ba sai misalin bakwai bayan ya dawo daga masallaci kamar yadda bai neme ta ba,haka ita ma domin ko kiranta ba ta son ya yi saboda hankalinta ya tashi jin ya faɗi za a yi mata dashen ƙwan haihuwa. Sai ta fara nadama matuƙa ta na ji kamar ta gudu daga gidan don ta san mundin ta faɗa mishi to ita ma yanka ta zai yi ko ya kasheta,saboda ya gaya mata duk abin da ke tsakanin su ba da wata manufa yake yi ba burin sa ya samu baby shi ya sa yake mata haka don haka ta saka a ranta abin da ya fi na Binta zai yi mata. Kwanciya ta yi ba wani karsashi a tare da ita saboda duk yadda ta so ta zo su kwanta amma taƙi sai ta samu guri a ɗakin da Baba take zama ta kwanta. A.m da ya gama shirin baccin sa shiru ba ta zo ba dama bai saka ran za ta zo ba kuma shima ransa babu daɗi don sun yi ɗan tanka-tanka da A.k akan nemar shawarar sa da ya yi na dashen da yake so ayi mata,amama sai ya nuna rashin amincewar sa akan ya ƙara haƙuri har Allah ya kawo. A.m ya ji ba daɗi don ya gaji da jiran gawon shanu don haka ya nuna ma A.k rashin amincewar shi in da har ya ji zafi ya gaya masa magana,yayin da ya saka a ranshi kawai za su tafi ai shi ba uban shi ba ne da duk a bin da zai yi sai ya nemi shawarar sa. Ɗakin da take kwance ya nufa tare da saka cocilar wayarsa ya haska fuskarta,ba bacci take ba amma ta yi maza ta rufe idanunta jin shigowarsa. Ta yi mamakin da bai tashe ta ba ya juya ya fita. Hankalin shi ya ɗan tashi ya shiga tunannin ko ta gudu ne don bai ganta ba,sai kuma ya duba ɗakin da ya san Baba ta na zama ilai kuwa ta na ɗakin ta takure a guri taya ta na baccin wahala, don ko numfashi ba ta saukar wa ta daɗi ganin yadda ta takure kanta. Sai dai ya yi mamaki ƙwarai ko da ya matsa kusa da ita sai ya ga ta miƙe zubbur ta na salati,wanda ya saka a ranshi mafarkin shi take yi. "Inna lillahi na bani don Allah karka cutar da ni mahaifiyata ba ta da rai." Ta faɗa da muryar kuka ta na roƙonsa amma bai kula ta ba sai ya saka hannu a aljihun wandon sa ya zaro bindiga ya ɗora mata a goshinta. Ta buɗe baki za ta yi ihu amma sai ya saita daidai bakinta ya ce da murya mai sanyi."In kika yi ihu sai na kashe ki.". Ya faɗa da wata irin murya da ta ƙara tsorata ta wanda ya sa ta yi sauri ta rufe baki ta tare da mai da kukan. Ganin ta yi shuru ta na kallon sa har fitsari ta yi a wando. A.m ya kalleta tare da watsa mata harara ya fara magana da ce wa."Gobe Zainab za ta dawo Allah ya sa ki faɗi wani abu a tsakanina da Juwairiya kashe ki zan yi." Wani irin kartawa cikinta ya yi ta ƙara toshe bakinta ta na tunanin yau Allah ya kawo ta gurin jidali gashi mai gida na son ya kasheta. "Wallahi ba zan ce komai ba babu ruwana ka taimake ni karka kashe ni." Ganin ta tsorata ya sauke bindigar ya na shafawa ya ce."Good in kunni ya ji gangar jiki ya tsira ina fatan kin gane." Da da sauri ta ɗaga masa kai sannan ya fara taku zai fita wanda Binta ta fara addu'a Allah ya raba ta da shi lafiya. Ganin ya kuma jiyo sai hankalinta ya ƙunduma ya tashi ta ƙara firgicewa ta na tunanin mai ya saka ya dawo." "In Zainab ta dawo ina son ki yi ƙaryar aljanu a mai dake in da ka ɗauko ki in kuma ba haka ba wannan zan saka na kashe ki." Ya faɗa ya na nuna ta da bakin bindiga sannan ya juya ya fice daga ɗakin. A ranar kasa bacci ta yi ta na ta kuka daga ƙarshe dole ta koma ɗakin da suke kwana don gani take kamar zai dawo ya kasheta. Washegari gidan ya kacame sai gyara ake yi kasancewa da misalin sha ɗaya Zainab za ta iso shi kan shi gogan bai je ko ina ba ya na zaune a falo ta iso. Tun da suka shiga ɗaki ba'a ƙara jin ɗuriyar suba sai da aka kira sallar azahar sannan A.m ya yi wanka ya fito yayin da Zainab take biye a bayan sa don ta fito ta ba ma cikinta haƙƙin sa. Binta da take jiran fito ba ta jima da jin fitowarta ba lokacin ta na waya ta fito da gudu ta ruga zuwa waje sai ta dawo ta kalli Zainab ta ƙara rugawa waje,tun Zainab ba ta damu ba sai ta ɗan firgita tare da daka mata tsawa amma ba ta dai na ba ƙarshe fashewa da kuka ta yi ta kama suratai. Zainab da ta matsa ne sa da ita ta na faɗin."Na shiga uku ke Juwairiya fito ki ga abin da take yi dama Anty Fati ta san ba ta da hankali ta kawo min ita?" Ko da ta fito ta ga halin da take ciki sai hankalinta ya tashi matuƙa yayin da tsoro ya shigeta gani take kamar ta yi hakan ne don ta tona asirin su. "Gida za ni amai da ni gida a kwai dokin da nake hawa ni Sarkin ljanu a can in kuma yau ba hau ba duk saina yi maganin ku." Ta faɗa da tsamin murya ta na girgiza jikinta kamar ta na da aljanun da gaske. " Na shiga uku kin ji mai take ce wa?" Ta ce da Juwairiya da ta tsaya ta na mamakinta yayin da tausayinta ya cika ranta don ta san ta yi hakan ne don ta koma gida ita ba ta san A.m ya tsoratar da ita bayan wannan. Kama ta yi ganin ta na jijjiga sai hawaye ya wanke mata fuska. Zainab da ba ta taɓa ganin wai mai aljanu ba sai ta tsorata ainun take ta kira Anty Fati jikinta na ɓari ta sanar mata halin da Binta take ciki nan take ta ce bari ta turo direba da mai aikinta su taho da ita don sam iyayen ta ba su yi mata bayani ba. Zainab ta tsorata sosai a ranta Allah Allah take direban Anty fati ya iso,abincin da take ci kasa ci ta yi ta tsaya ta na kallon ikon Allah yayin da jikinta ke ɓari. Suna cikin wannan halin ya shigo da sauri ta ƙarasa gun shi ta yi masa bayani. Ya kalli Binta da take kaɗa kai kamar wata ƙadangaruwa ta na zare ido,sai hakan ya so ya bashi dariya amma ya cije. Wata uwar tsawa ya daka mata ganin ta gan shi sai ta razana kamar za ta gudu don Allah ya saka mata matuƙar tsoron shi. Ɗan natsuwa ta yi amma ba ta daina zare ido ba ita a dole ga mai aljanu. A.m ya kalleta sai ya kauda kansa tare da taɓe baki ya ce da Zainab da ta yi tsuru-tsuru ta na kallon Binta. " Maganin ki kenan da shegen kwashe-kwashen ki ta yi maza ya bar gidan nan ai ga yi nan kin je kin jawo ma kan ki mai almatsutsai." Ya yi maza ya haye sama ya na dariyar yadda Binta take yi sai ka ce wata ƙadangaruwa,saboda in ya tsaya dariya zai kubce masa. Direba na zuwa Zainab ta saka aka kwashe kayanta tare da yi mata ihisani aka wuce da ita. Ta na shiga ɗaki kuka ta fashe da shi na tausayin Binta haka kawai ya yi mata sanadin rabuwa da aikin ta bayan ya san ita marainiyace an ya ya kyauta kuwa. Ta na kallon shi akan mutum wanda ya fiye son kan sa bai damu ba in dai zai faranta ma kansa da masoyiyar sa bai damu don ya cutar da kowa ba. Don haka ko wayar da yake yi da ita in ya fita duk lokacin da Zainab take nan ta ƙi daga ƙarshe kashe wayar ta yi saboda haushin sa da take ji matuƙar gaske,don ya faye son kan sa akan komai. Zainab ba ta haƙura da neman mai aiki ba don har ta yi maganar a kawo mata wata. Makarantar da ta fara sai hakan ya yi maata daɗi sosai ikon Allah kenan duk da ta cire rai sai gashi Allah ya saka ta na da rabon yi.Abin da iyayen gidan ta suka zaɓa mata ya sa ta ƙara yadda da cewar nufin su rayuwarta ba ta da wani amfani sai dai don ta yi musu hidima saboda girki suka zaɓa mata,ita ta na ganin wani kalar girki ne ba ta iya ba,amma kuma da ta fara karatu sai ta raina kanta don gani ta yi kamar da can ba ta iya komai ba. Ganin hakan sai ya dage damtse burinta ta iya girki ta yadda za ta siye zuciyar A.m,da take jin kamar ana mata wahayin son shi. Duk da cewa makarantar sau uku take fita a sati amma ta na jin daɗin karatun,sosai fiye da komai ba kamar da da ita kaɗai take rayuwarta in dai matar gidan ta na nan. Juwairiya ta yi ƙawa ɗaya a makaranta wacce suka shaƙu sosai duk da ba su daɗe ba,sai dai ita matar aure ce har da yaranta biyu. Suna matuƙar shiri sosai komai ma su tare suke yi ga halin su ya zo ɗaya ba ruwan su da hayaniya,musamman ita da take kullum cikin bege da ƙaunar masoyin ta. Kimanini wata uku da fara karatun Juwairiya wanda Zainab ta ɗauko ƴan aiki har guda uku sai A.m ya yi tsalle ya kawo ƙauli da ba'adi. Ganin haka sai ta kori Baba in da aka kawo mata mai jini a jika ta na koya mata girkin amma ba ta kwana don ta na da miji sai dai tun safe in ta zo sai magariba take komawa gida. Ranar wata Juma'a Juwairiya ta tashi da ciwon kai mai zafi da zazzaɓi ko tashi ta yi sallah ta kasa ga wani irin sanyi da yake shiga cikin ƙashin jikinta ya na nuƙurƙusanta. Abin takaici gashi suna da test don ana gabda yi masu jarrabawa. Ganin ba zata iya zuwa ba gashi matar gidan ba ta nan kuma yau A.m zai dawo daga tafiyar da ya yi,wayarta ta ɗauka tare da duba numbar ta kiran numbar Hauwa Tukur amma wayar ba ta shiga ba sai ta yi tsaki ta jefar da wayar ta kwanta. Ta na kwance jikinta na ƙara zafi sosai kamar wuta misalin tara sai ga kiran Hauwa Tukur ya shigo,da ƙyar ta janyo wayar da ke kusa da ita ta kanga a kunninta ta na nishi a wahalce. "Hello Juwairiya ba za ki zo makaranta ba ne lafiya kin san muna da test ga shi Malam D.d ba shi da mutunci."Hauwa Tukur ta faɗa a ranta ta na tunanin mai ya hanata zuwa,kasancewar ba ta wasa da karatu. " Wallahi ba na jin daɗi ne kin san sai da lafiya ake komai.Don Allah ki yi min test ɗin in zai yi wu."Ta ba ta amsa ta na kyarmar jiki. Bayan ta yi mata sallama tare da mata alƙawarin in dai ya yadda za ta yi mata ta kashe wayar ta koma ta kwanta. Sai misalin shidda na yamma A.m ya shigo babu abin da ta yi masa na abinci. Ganin halin da take ciki ya ruɗe sosai kamar zai yi hauka a tunanin sa ciki ta samu,don haka jiki na rawa ya ɗaga waya ya kira likita ya zo ya duba ta. Juwairiya ta ji hankalinta ya yi ƙololuwar tashi jin ya kira likita ita yadda take jin ciwon gani take kamar ciki ne. Kawai sai ta ji hawaye ya fara sauka a ƙuncinta don ta san lokacin rabuwar su ya yi daga ranar za su fara irga kwanaki. Bayan likita ya zo ya yi mata gwaje-gwaje ya sa ta yi fitsari ta kawo masa. A.m da ya yi zugum duk ya ƙosa ya ji abin da likitar zai faɗa,ya na ta addu'ar Allah ya sa likita ya yi mishi kyakykywan albishir. "Ga wannan maganin za ka siyo maleria ce ke damunta in sha Allahu tasha magani za ta warke." Hankalin sa ne ya tashi matuƙa kawai sai ya ji hawaye na son ya zubo a ƙuncin sa yayin da zuciyar sa ta karye da tunanin zai samu ɗa. Jikin sa a sanyaye ya karɓi takaddar ya fice tare da likitan don ya siyo magani ko kallon ta da take zaune bai yi ba. Wani wawan ajiyar zuciya ta saki wani irin sanyi ya ziyarce ta jin ba ciki ta samu ba. A ƙalla sai da ta yi kwana uku sannan ta warke sarai ta shirya ta tafi makaranta. Suna zaune da Hauwa Tukur ba yan sun fito daga lakca Hauwa Tukur da hankalinta yake kan danna wayarta ta kalle ta da ta zuba uban tagumi ta yi nisa gurin karanta wasiƙar jaki. "Yawan tunani ba shi da amfani ga lafiya kuma ban ga dalilin da zai saka ki zo makaranta ki zuba uban tagumi,ba yan kin baro gwarzon ki a gida nifa da kika ce baki da lafiya na ɗauka ciki ne da ke." Wani irin tashin hankali ya ziyarce ta ta zare idanunta ta na kallonta. "Subuhanallahi ciki kuma ni fa ba matar aure ba ce." Ta faɗa tare da gwalalo idanu jin abin da ta faɗa yayin da take mamakin mai ya saka ta faɗi haka. Sakin dariya mai sauti ta yi ta ɗauki lemun robar da Juwairiya ke sha ta zuƙa tare da kwashewa da dariya. "To don Allah meye na tsorata haka sai ka ce na ce kin yi kisa." Ta faɗa ta na mamakin yadda ta razana haka saboda ta haƙiƙance ma kanta ita matar aure ce,sai dai in ba ta son ta ga ya mata amma ko wa ya kalle ta ya san ta na da aure. "Haba Juwairiya ko wane mutum ya kalle ki ya san kina da aure kin san a kwai matan da dole a gane matan aure,duba ga yanayin jikinta ki kalle kanki kema kin san bakya son ki gaya mini ne,to ki mai da wuƙar ni ban ce zan gan shi ba bare ki yi tunanin ko zan bashi ƙanwata ne." Ta ce da tsigar wasa saboda ta na son ta kwantar da hankalinta ganin yadda ta birkice lokaci guda. Jin abin da ta faɗa sai hankalinta ya tashi sosai duk da gargaɗin da zuciyarta take mata na kar ta faɗa mata halin da take ciki,amma ta na jin lokaci ya yi da za ta daina shanye damuwarta ita kaɗai ta sanar da ita ko don ta samu shawarar yadda za ta cire son maso wani a ranta. Kama hannunta ta yi ta haɗe da na ta ta kalli ta cikin muryar son kuka ta ce."Tabbas tunanin ki haka ne amma ina buƙatar mu samu in da babu mutane ina da damuwa ina son ki ba ni shawara." Ganin ta fara kuka sai ta riƙe hannunta suka koma in da babu mutane. "Tabbas tunanin ki gaskiya ne ina da aure amma auren sirri na yi da mijina na shekara ɗaya." Sai ta din ga kallonta irin kin zare kenan ko kuma baki san mai kike faɗa ba ta kasa magana sai kallonta take yi. Ganin ta kasa yadda da abin da ta faɗa mata sai ta ƙara fashewa da kuka ta na jin wani irin zafi a zuciyara ta. Hauwa Tukur da ta yi shiru ta na jinjina wannan lamarin mai kama da shirin fim ko hikaya a gare ta!A ranta ta na mamakin ta ya ya za'ai wannan aure ba tare da sanin mahaifiyarta ba!Ita ko wani irin so take mishi?An ya ta yi tunani kuwa mai ya kai ta namiji ba ɗan goyo ba ne ɗan masara ne ana goyon shi ya na kayan gemu." Maganar zuci take amma ba ta san maganar zuci ya fito fili ba. Ta riƙe hannunta ta na kuka sosai ta ce ba yan ta yi murmushi mai ciwo." Dole ki jero min waɗannan tarin tambayoin ni ma na san na yi kuskure,kullum cikin dana sani da kukan zuci nake yi." Ta saki hannunta ta miƙe tare da juya mata baya ta ƙara ce wa da ita."Allah ya jarabce ni da tsananin son shi sosai,amma A.m ya tsane ni baya sona ni ce mace ta farko da ya tsana saboda a koda yaushe cutarwa ce a tsakanin mu ya na ƙara saka min son shi a raina. Na san ce wa ban yi ma mahaifiyata adalci ba amma babu yadda zan yi ne Baba Sani yaƙi taimakonmu,gashi ba na son na rasa ta,kuma ko banza auren sa ya ceci rayuwata daga auren Alhaji Tanimu,amma kuma yanzu ina tsoron ranar da A.m zai rabu da ni na san ranar ita ce ranar da fitar numfashina zai yi bankwana da gangar jikina." Hauwa Tukur da take jin tashin hankali ita mamaki take ba ta da har ta yadda za ta iya saida ɗanta,amma sai ta danganta shi da don ba ta san son da yake tsananin uwa da ɗanta ba ne shi ya sa ta aikata wannan aiki,da kuma zafin talaucin da take ciki uwa uba Baba Sani da ya ke mugu azzalimi. Ta nisa sannan ta fara magana cikin mamakin mugun hali irin na Baba Sani. "Gaskiya na ga wauta da ƙuruciyar ki duk da kin yi hakan ne saboda ki taimaki rayuwarku,amma a kwai kuskure a ciki haba ta ya ya zan amince na auri mutum kuma na zauna a matsayin mai aikin matarsa har na iya wanke mata ƙazantarta wallahi hakan ba zai yi wu ba,na tabbata da kin ƙi amincewa in dai idon A.m a rufe yake ya na son yaro dole ya naimi wata hanyar k..." "Don Allah ki fahimce ni na san na yi kuskure amma kuma abin da ya faru ya riga ya faru!Ki ba ni shawarar yadda zan saka soyayyata a cikin zuciyar sa,yadda dake ya sa na bayyana miki damuwata saboda friend in need is a friend indeed." Ta katseta jin ta na ta maimaita maganar da wautar da ta yi bayan ta san hannun agogo ba zai taɓa dawowa baya ba. "Wane shawara zan baki ni fa ina son naga ranar da wannan lamari zai fasu har na zaƙu da na ga kin yi ciki don a kwai turka-turka kina ganin Zainab za ta yadda ta karɓi yaron ne?shi kan sa bai yi tunani ba domin ya ibo ruwan dafa kan sa ala'mura canzawa za su yi saboda man propose but Allah dispose. Sannan babban kuskuren da ya yi na kawo ki gidan sa Zainab ta sanki ina tausaya masa lokacin da maganar ciki za ta fito fili,don Zainab ba ƙaramin hauka za ta yi masa ba. Ni yanzu shawarar da zan ba ki shi ne ki ƙoƙarta a ki samu ciki za ki ga yadda komai zai canza." Saka kuka ta yi ta ce."Shawarar da za ki ba ni kenan?ba ki san waye A.m ba kuma ba ki san Zainab ba shi ya sa kike ganin kamar inna samu ciki zai soni wayar ta ta ciro ta nuna mata hoton A.m da Zainab wanda ta ɗauke shi na falon su da suka manna.. A duk lokacin da ciwon son shi ya kamata sai ta ciro hoton ta na gani saboda zuciyarta ta sare da soyayyar A.m ganin irin zuƙeƙiyar matar da yake aure,amma haka ba ya canza komai ta na ganin son shi kamar wahayi ake mata. "Duk da wahalar da shi da Zainab take mata har ƙasashe take fita kasuwancinta amma kullum ya na gaya min ita ce matar so ni matar wucin gadi ne,amma abin takaicina sai ya zo ya din ga more ni ya na gaya min irin baiwar da Allah ya yi min bai taɓa kuskuren faɗin ya na sona ba." Hauwa Tukur ta yi matuƙar tsorata da ganin su kamar wasu larabawa yanzu ta gane dole jikinta ya canza saboda irin daular da take ciki. Hannunta ta ƙara riƙewa ta ce."A.m ya haɗu irin mazan nan ne masu wayo da dubara sam ba za ki taɓa gane in da ya dosa ba,amma na yi mamakin in da kika samo wannan gayen saboda maƙura ne gurin kyau." Murmush mai kama da kuka ta saki."Don Allah ki ba ni shawara yadda zan jawo hankalin sa." Numfashi mai ƙarfi ta."Ikon Allah ita Zainab wata irin banzar mace ce ina tausaya mata ranar nadamarta saboda na ga sakacinta sosai mace sai kace mahaukaciya abubuwan da take yi sam babu tsari aciki kuma ni na fi ganin laifin A.m da ya barta take mishi wannan iskanci.Gaskiya ba na goyon bayanki da kike kare kanki daga ɗaukar ciki, wanda ko ba a faɗa ba na san irin kuskuren da matar sa ta yi kenan kuma na tabbata ta na nadama.Ga kuma in da son duniya ya kaita haba ai ya raina mata wayo ya kawo matar sa cikin gidan ta ya na more abar sa ya maida ita shashasha. Duk da ita ta na tunanin ba zai taɓa duba gareki ba saboda ba ku dace da juna ba tunaninta bazai kawo mata zai iya ɗaga ido ya kalle ki ba duba ga matsayin sa,ba ta san namiji ba haka yake ba abin da kake ganin yafi ƙarfin sa sai kiga ya mutu akan abin." Sai ta kwashe da dariya ta duk da ganin halin da take amma rainin wayon ya yi yawa gani take kamar ya na raina musu wayo ne daga ita har Zainab ɗin. " Matsalar ka bayyana damuwarka ga mutumin da ka yadda da shi kenan na yi tunanin za ki ba ni shawara,amma ba ki duba halin da nake ciki ba kin tsaya ki na min dariya." Ta faɗa a zuciye tare da ɗaukar wayarta za ta tafi. Da sauri ta ɗauki jakarta ita ma ta kama hannunta."Afuwa lamarin ne a kwai rikitarwa ni dai ina baki shawarar ki kasance a shirye, saboda duk ranar da Zainab ta san abin da ke tsakanin ku Allah kaɗai zai raba ku lafiya yanzu ki ɗaga waya ki kira A.m ki sanar mishi da kina son shi mijinki ne fa,wanda yake dawowa ba yan ki ya kwanta mai zai hana ki sanar da shi." Ta ce mata ta na kallonta a ranta jinjina lamarin take yi."Ba zan iya gaya masa ba kuma ba zai bani damar haka ba haba ya kamata ya ce ya gane irin son da nake masa ko ƙwayar idanuna ya kalla ya kamata ya gane." "Ai ko dole ki sanar masa meye amfanin dakon son mutumin da bai sani ba kuma ko banza,daga ranar da kika gaya masa irin son da kike masa wallahi ko baya sonki ya kalle ki a matsayin kina son sa zai din ga kallon ki kuma ko banza masoyinka yafi maƙiyinƙa sannan a tunanina a haka wani abu mai girma zai shiga tsakani ba tare da ya sani ba." Juwairiya jikinta ya yi sanyi matuƙar gaske zuciyarta ta halasto mata irin tarin son da take dakon sa ta ji ya na tasowa nan take ta faɗa kogin zuma har ta ji za ta iya kiran sa ya zo ta sanar mata da damuwar zuciyarta duk da kafin su yi aure sai da suka yi sharaɗin babu wannan wayarta ta zaro domin ta kira shi. WANI IRIN FIRGITA NA YI SABODA BUGUN ZUCIYAR JUWAIRIYA DA NAKE JI YA SA CIKINA YA MURƊA NA TASHI DA NUFIN NA JE BAYI,AMMA KODA NA DAWO TSABAR TASHIN HANKALI BAI SA NA GANE MAI KE FARUWA BA SABODA SAUKAR BUGUN ZUCIYARTA JI NAKE KAMAR ANA BUGAMIN GUDUMA. TOFA KO YA ZA TA KAYA A M ZAI AMINCE DA SOYAYYARTA? KU CI GABA DA BIBIYAR LINTAFIN DON JIN YADDA ZA TA KAYA A CIKIN LINTAFIN NAN MAI FARIN JINI. BARI NA TUNA MUKU DA SUNAN SHI SAKACINA KO HALIN MAZA TAKU JAMILA LAWAL ZANGO JAMCY Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 24* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM A tare zuciyarta take bugawa da ringing ɗin da wayar take yi.Ta kira sau biyu bai ɗauka ba sai jikinta ya yi sanyi ta ije wayar,ta kalli Hauwa da ta kafe ta da ido. " Na kira shi amma bai ɗauki ba ina tunanin wayar ba ta kusa da shi."Ta faɗa cikin karayar zuci. Zama sukai suna jiran kiran wayar ko wannen su zuciyarsa na buguwa tamkar za ta fito. Sun jima a gurin suna jiran kiran sa har suka gaji.Ita ta fara miƙewa ta kalle ta ta ce." Mai zai hana ki fara nuna masa so misali ki din ga nuna mishi kin yi kewar shi ,da kalamai masu zafi kuma ki din ga tura masa,ai shi ba yaro ba ne dole ya fahimta wataƙila ya san za ki kamu da son sa shi ya sa ya ce kar maganar so ya shiga tsakanin ku." "Ki na ganin haka shine mafita na riga na ɗaukar wa kaina in har bai ce ya na sona ba ba zan taɓa yadda na bar ciki ya fito a jikina ba."Ta gaya mata cikin sassanyar murya. " Allah kawai ya san me ya ɓoye a gaba amma ki dage da addu'a kuma ki din ga nuna masa irin yadda kike son sa a aikace ke fa matar sa ce,kuma tun da ya har ya iya haɗa jiki da ke ban ga abin da zai hana ya soki ba,amma ni fa nafi son ki bari ki sami ciki naga irin haukar da zan yi. Maganar ya gundireta fara tafiya ta yi ba tare da ta ce mata komai ba, a ranta sam ba za ta amince da shawarar ta ba, ta yi alƙawari ba za ta dai na zubar da ciki matuƙar ba zai zauna da ita na har abada ba. Kamar yadda suka shirya sai ta fara ɗan sakin layi ta na yi masa wasu irin abubuwa saɓanin hankalinsa saboda har mamakin ta yake wai dama haka take! Duk wani abin da take mishi ya biye mata har ma ya na mata fiye da haka. Ranar da suka shirya za ta gaya mishi amma a waya don ba za ta iya taran idanun shi ta furta mishi ba. Da fari text ta ce za ta rubuta mishi sai Hauwa ta ba ta shawarar ta kira shi. Cikin sa'a ringin ɗaya ya ɗauka ta na sanar mishi da ta na son ta yi magana da shi kuma maganar is verry important sannan kuma comfidential. "Ok ba ki da damuwa tun da kina cikin makaranta ki bani ɗan lokaci,ina gidan A.k na je gaida matarsa ni da Zainab bari na shigo cikin makarantar,ba sai kin gaya min a waya ba." Duk yadda ta so ta hana shi zuwa don tafi son su yi a waya amma ya kafe ga shi nan zuwa,daga bisani kashe wayar ya yi ganin za ta yi masa gaddama. "Ya ce ga shi nan zuwa yaƙi yadda na gaya masa a waya." Ta faɗa yayin da zuciyarta take bugawa."Gaskiya ya na girmama lamarinki bari na ɓoye yau ina son na ga A.m, a zahirin gaskiya da ya sace zuciyar rabin raina ya hana ma ƙawata sukuni." Dariya ta yi ta kauda kanta ba ta ce komai ba saboda ƙirjinta yake bugawa. A lokacin da motarsa ta shigo sai Hauwa ta miƙe da sauri ta laɓe,ta yadda za ta din ga kallon duk abin da ke faruwa ba tare da ya ganta ba. Har kusan in da take ya ƙaraso da motar sa sannan ya yi parking ya fito ya taho in da take. Kallonta ya yi lokacin da ya zauna akan ɗaya daga cikin kujerun, da suke a gurin tare da sakin wani wawan ajiyar zuciya. "Kin tsorata ni fa wallahi na ɗauka ko babu lafiya,amma tun da na gan ki lafiya lau faɗa min matsalar ki." Ya faɗa ya na kallonta tare da riƙe mata hannu suna kallon juna ido cikin ido. Sun ɗauki tsawon lokaci suna kallon junan su ba tare da sun ƙifta ba. Da sauri A.m ya miƙe tare da juya mata baya domin ko ba ta faɗi abin da take son faɗi ba,idanunta sun bayyana tsaƙon su dama ba tun yau ba yake ganin ta na sakin layi,wanda yake biye mata don ya faranta mata. In ko ta na son ta faɗa masa son shi take, kamar yadda ya gani a ƙwayar idanunta, ya kamata ya yi maza ya dakatar da ita, don ba zai taɓa son wata mace ba bayan Zainab ɗin sa. Juyo wa ya yi ya kalleta ta da take ta in da inda ta in da za ta fara."Juwairaah kar ki ce ki na sona don ni ba na sonki." A zabure ta tsaya gaban sa ta fara hawaye kamar an buɗe famfo. A hankali ta nuna kanta da yatsa ta ce."Ba ka sona A.m da gaske ba ka sona kake yi min abubuwa irin na wacce ake so?" Ƙara masowa ya yi kusa da ita."Yes ni fa ban taɓa jin ina son ki ba,kawai ina girmama lamarin ki kamar yadda na sha gaya miki.Saunawa kike son na gaya miki ba na sonki ko kafin na aure ki na faɗa miki,Zainab ita ce macen da nake so kuma na aure ki da sanin ki akan ki haifa min yaro na bata.Wai mai ya sa kike dawo da hannun agogo baya ne?" Ya faɗa cikin ɗaga murya duk da babu mutane sosai a gurin sai ɗaya biyu,amma har an fara taruwa ganin ya na magana da ƙarfi. "Ina sonka ba zan fasa sonka ba!Na fara sonka tun kafin ka bijiro mini da aurenka, kuma na san kai ma ka na sona sau nawa kasha faɗa mini ka na son surar jikina da halina,mai ya sa ba za ka so zuciyata ba?" Ta faɗa cikin muryar da tafi nasa amo don ji take kamar za ta yi hauka. "Ni fa ban taɓa ce wa ina sonki ba sai surar jikinki,kuma ta ya ya zan yi na saka son macen da na san ban ba mu dace ba.Ki tuna mahaifinki har ya mutu bai bar muku komai ba,sanin kan ki ne mahaifina ya yi fice a duniya." A.m ya faɗa ran sa na suya ganin ta na son ta tara mutane, wannan kamar cin mutunci ne mai ya sa ba ta gaya masa a gida ba. Cikin jin zafin ta ya fara tafiya zuwa motar shi, da gudu ta bishi ta durƙusa a gaban sa ta na hawaye."Tabbas haka ne ka faɗi gaskiya mahaifina bai bar mana komai ba sai talauci,amma ka sani ba kuɗi ba ne kawai Allah yake sawa a so mutum shi ya sa har yanzu na kasa gasganta son Zainab kake yi. Saboda ka na sonta ne don kawai ita ajin ka ce na san watarana za ka fahinci gaskiya, za ka gane a kwai baiwar da Allah ya kan yi ma bayin sa aso su ba wai sai dukiya ba. Ni na san watarana za ka soni kuma sai ka yi nadamar abin da ka gaya mini ko ina raye ko ba ni raye." Ta numfasa ta na jan numfashi ganin ya yi shiru ya na kallonta sai ta ɗora da ce wa."Ina sonka ba zan fasa sonka ba sai ranar da numfashina ya yi bankwana da gangar jikina." Tafiya ya fara yi bai ce mata komai ba.Kamar wata zararriiya ta miƙe ta juya ta na kallon shi ta kira sunan shi. "Ina sonka! Ina sonka!! Ina sonka!!!" Cak ya tsaya ba tare da ya juyo ba ya na jin kukan ta na yi mishi zafi sai ya ƙara sauri ya shige motar sa ya fice daga harabar makarantar a guje. Durƙushewa ta yi a gurin tare da saka razanannen kuka. Da sauri Hauwa ta fito ganin motar sa ta ɓace tare da kama ta ta na son ta miƙar da ita. Faɗawa jikinta cikin muryar kuka da sheshsheƙa. " Ki taimake ni A.m ba ya sona ya tsane ni na tabbata son shi zai kashe ni domin na fi buƙatar na mutu fiye da ina kallon ya na fifita wata a kaina.Wayyo Allah na!Ina ma a ce mutuwa na yi ban haɗu da shi a cikin rayuwata ba." Hauwa ta ruɗe ganin kukan da take ba na wasa ba duk da guy ɗin ya cancanki a so shi,amma ita a ganin ta bai kamata ta so shi haka ba ganin za ta cutar da rayuwarta a banza. Da ƙyar ta ja ta suka bar gurin domin su kaucewa mutanen da suka fara taruwa. Ruwa ta miƙa mata wanda ta karɓa tare da ɓalle murfin,ba ta ije gorar ba sai da ta shanye duka. "Ki yi haƙuri ban baki shawarar ki faɗa masa ba don ya wulaƙanta ki,da ace na san abin da zai faru kenan da ban ce ki gaya masa ba.Kici gaba da addu'a babu abin da ya gagari Allah.Amma da kin bari ki samu ciki wataƙila ta nan kawai za mu ci galaba a kan sa." "In har A.m bai amince da soyayyata ba ni kuma ba zan yadda na samu ciki da shi ba, na gwammace na yi ta rayuwa da shi a haka da na haihu da shi ya gujeni." Abin da ta faɗi kenan cikin murya kaukausa ta ɗauki jakarta ta tafi. Tun daga ranar A.m ya ɗauke mata fuska wanda sai da ta yi mishi kuka,sannan ta ba shi haƙuri ta janye maganar so a tsakanin su sannan suka shirya. ***** Zainab ta yi kuɗi na ban mamaki mace ce mai aji wadda take son ta zama babbar mace a kan komai. Ta na da kuɗi da aji da ilmi ta na jin ta a cikin manyan mata masu amsa sunan su. Ita kanta ba za ta iya irga iya dukiyar da take da shi ba.A yanzu sam ba ta yawan zuwa aiki domin ta zamo babba, a asibitin da take aiki ba ta wani zuwa sai dai in za ayi aiki tazo ta farɗe ta ɗinke. Zainab ta na da matuƙar ƙoƙari a gurin aikin ta shi ya sa kullum take ƙara samun ɗaukaka ta ko ina. Irin kuɗin da take samu ta zama babbar mace yar lukuta duk da ba ta son ta yi ƙiba, aikuwa saboda kuɗi ya zauna ta cika ta batse tamkar za ta fashe,ta yi wani irin kyau sosai abin ka da farar mace alkyarbar mata. Duk yadda A.m ya so ya kafa mata doka dole ya watsar da makaman sa ya ɗauki ƙaddarar sa,bayan ya fahimci matar sa mai aji ce kuma mafi ɗaukaka a cikin matan duniya saboda tarin ilmin da Allah ya yi mata. Saboda ƙarin girmar da ta samu haka ya rage zuwa aiki da take yi,sai dai in yawon ta ya tashi ta fice, sai hakan ya ƙi ba A.m damar kasancewa da amaryar wucin gadi kullum su na tare da Zainab, in dai ba fita ta yi ba wanda kwana biyu ta rage yawo. Rashin fitar ta sai ya takura su duka musaman A.m da kwana biyu ba su haɗuwa sai a waya. Saboda ƙwarewar Zainab mahaifinta ya yi mata alƙawarin gina mata asibiti na ta mallaki wanda har an fara aikin gini. Wata tafiyar ta kama A.m a kan kampani da suke ƙoƙarin buɗewa na sarrafa fata,Daddy ya ɗora A.m akan kayan da za ayi amfani da su. A.m ya shirya viza tare da Juwairiya domin ya yi matuƙar kewarta,ba tare da ta sa ni ba sannan ya na son a duba lafiyarta don ya matsu da ta samu ciki su rabu. Zuciyar sa ta kan buga daram! A duk lokacin da ya tuna zai rabu da ita,saboda ya shaƙu da ita sosai sai dai ya san dole watarana za su rabu. A.m da yake ta tunanin hanyar da zai bi ya samu ya tafi da ita,amma ya rasa ko da ya yi musu viza bai sanar da ita ba. Ranar talata ya kirata bayan ya gaya mata za su tafi sai hankalinta ya tashi matuƙa,don ita ba ƙaryar da ya ce ta yi ba ne yake tada mata da hankali. Tunanin ta yadda za ta bayyana masa abin da ke faruwa ne,saboda ta san muddin ta gaya masa sai ya kaita kushewarta,ganin yadda A.m yake nuna mata tsantsar damuwar sa akan rashin samun cikin ta. Kamar yadda A.m ya gaya mata akan ta yi ƙaryar Mama ba lafiya, ta yadda zasu samu su tafi,haka kuwa aka yi bayan ta shirya kayan ta akan za ta je ta yi sati biyu saboda ta yi jinyar Mama. A jirgi hankalinta ya yashi ƙwarai ta ƙanƙame shi cikin tsananin tsoro ta na jin kamar numfashinta zai ɗauke,kasancewar ta na tsoron hawa jirgi sosai ko lokacin da ta raka Mama haka ta din ga ƙauyanci. A.m kuwa sai dariya yake mata ya ciro wayarsa ya na musu bidiyo, ganin yadda ta tsorata ta na ƙauyanci,sam bai damu da kallon su da ake yi ba. Juwairiya ta shiga cikin sabuwar duniya ta din ga zuba ido ta na ƙauyanci,yayin da zuciyarta take yabawa da ƙasar. Bayan sun sha baccin gajiya ita kuwa sai da ta yi ɗan zazzaɓi, shi ya riga ta tashi ya na ƙoƙarin cire kayan jikin sa ya shiga bayi don ya watsa ruwa. Kallonta ya yi ganin ta tashi suka zuba ma junan su ido,na tsawon lokaci can kuma sai suka kwashe da dariya. Hannu ya miƙa mata ya na faɗin."Matar wucin gadi zo mu je ki taya ni wanka." Dariya ta yi tare da noƙe kafaɗarta ta miƙe za ta fita daga ɗakin, ganin ya taho zai kamata kan dole sai ta taya shi wankan. " Don Allah ka cika ni kunya nake ji." Ta faɗa ta na ɓoye fuskarta da murya na son jan hankalinsa,shi kan sa bai yi tunanin ta na da irin wannan muryar ba,saboda cikin salo da jan hankali ta furta har da ɗan yi mishi fari. " Kin san Allah dole yau sai kin taya ni wanka ko da kuwa muryar ƴar baby za ki yi don na gaji matuƙa." Hannunta ya kama ya na son ya ja ta zuwa bayi amma ta ƙi cikin salo take magana da muryar kuka akan ya ƙyaleta. Ganin za ta ɓata mishi lokaci cak ya ɗauke ta bai direta ko ina ba,sai cikin bayin ya tsunduma cikin ruwan da ta ji sanyin shi matuƙa. Saboda tsaɓar shagwaba kuka ta saka mishi da gaske,wanda hakan ya bashi dariya ya watsa mata ruwa a fuskarta. "Sarkin kuka dama mai hali baya fasa halin sa na manta fa matar wucin gadi ƴar ƙauye ce sam ba ta san soyayyar turawa.Allah sarki Zainab sai na tuna lokacin da muka zo cin amarcinmu mun yi soyayya sosai saboda ita mai aji ce." Wani irin hajijiya na kishin abin da ya faɗa ya kamata,amma ba ta son ran sa ya ɓace ko ta ɓata na ta,sai ta kalle shi ta yi dariya har da kashe mishi ido ta ce." Allah ko duk da ni matar shige ce ba matar so ba amma ka rubuta ka ije,zan nuna maka soyayya wanda ba zai taɓa gogewa zuciyar kaba ko da kuwa mutuwa na yi ba rabuwa mu kai ba." Ta bashi amsar abin da ya faɗa duk da ranta bai yi mata daɗi ba. " Allah ya sa ni dai na san tsabar shagwaɓarki ba zai baki damar haka ba, matar wucin gadi domin ke ma buƙata kike a lallashe mai hawayen banza. Jin abin da ya ce sai ta saka kuka sosai ta na ƙarawa har da diddire ƙafafunta a cikin ruwan. "Na rantse ka rubuta ka ije watarana wannan hawayen da kake kira na banza,sai sun zama abu mafi daraja a gurin ka wanda zubar su zai zama guba a cikin zuciyarka kuma da hawayen ka za ka rarrashe su." Lakuce mata hanci ya yi tare da shiga cikin abin wanka ya ƙara dannata cikin ruwa ya ce." A kwai kuwa tabbas ranar da kika haifa min yarona kina kukan rabuwa da shi,ni ma zan zubar da nawa saboda tausayin ki da na ɗana wanda ba zan taɓa gaya masa ya na da wata uwar bayan Zainab." Da sauri ta duƙar da kanta cikin abin wankan lokacin da ya saka hannun sa ya na ƙoƙarin yi mata wanka,hawayen dake zubo wa a fuskarta suka haɗe da ruwan suka gauraye ba tare da sanin ta yi kuka ba. Wata irin kula A.m yake ba ta sosai sun sha yawo kusan babu ai da bai kai ta ba,ya yi yawo da ita ko ina tare da yi mata siyayya har ya na tonon ta da kayan lefe ya yi mata tunna bai yi ma matar wucin gadi ba. Irin rayuwar da A.m ya nuna mata a ƙasar ta haƙiƙance ma kanta tabbas ya na sonta,kuma kafin su bar ƙasar za ta ƙara gaya masa ta na sonsa a karo na biyu,don har yanzu ba ta yadda ba ya son ta ba. Bayan sun dawo daga yawo Juwairiya ta na kicin girki take yi,wanda A.m ya takura mata sai ta yi mishi tuwon ta mai daɗi na shinkafa da miyar taushe. Tare suka je suka yo cefane ko da ta shiga kicin ɗin bin ta ya yi da wayar sa,ya saita ta na girki ya na mata video,hakan sai ya yi matuƙar burgeta ta na ƙara son A.m,saboda namiji ne wanda ya iya kula da mace ko da baya sonta,amma yanayin kular da yake mata ya isa ya nuna mata cewar ya na sonta. Ko da ta gama abincin a ranar cewa ya yi shi zai ba ta a baki saɓanin da da ita take ba shi. Haka ta zauna ya din ga ciyar da ita ya na ɗaukar ta hoto. Da suka zo gun kwanciya A.m ya rungumota ko mai ya tuna,sai ya miƙe ya tsaya a bakin windo tare da zuge labule ya na kallon waje. Hakan da ya yi sai ta gane a kwai magana a bakin sa, ba ta miƙe ba amma ta tattara dukkan hankalinta ta na kallonsa. "Juwairaah gobe za mu je akan maganar dashen ciki da za'a ayi mik, likita ya ce za ayi miki gwaje-gwaje kafin ayi." Gabanta ne ya faɗi jin abin da ya ce ba ta ce masa ƙala ba,amma ta ji sanyi matuƙa da ta ji ya ce sai an yi gwaje-gwaje kafin a farke ta,ta san likitan ba zai yi mata in ya gwada ya ga lafiyarta ƙalau. Dawowa ya yi kan gadon ya kama hannunta ya riƙe cikin murya mai sanyi ya fara magana.Na san ce wa ban kyauta miki ba don ba mu yi da yi miki aiki ba,amma ki taimake ni wannan ne kawai damata na yi miki alƙawarin ba ki duk wani jin daɗin duniya, in har za ki yadda a yi miki dashe ki haihu ." Wasu zafafan hawaye suka wanke mata fuska wato har yanzu ya na kan bakan sa,abin da yake yi mata ya na yi ne don ta yarda a farke ta ba soyayya ba ne. Jikinta ya yi matuƙar yin sanyi kamar ruwa ya cinye ta ayau ta yi ninyar ta gaya masa ta na son sa,amma ta cire ran A.m zai so ta a rayuwa ta na son a karo na biyu,kawai sai ta yanke shawarar gara su je Allah ya saka likitan ya ce ba ta haihuwa ya yi mata aikin,fatan ta a ce shi zai zama sanadin numfashinta ta huta da tarin baƙin cikin da take fuskanta. "Na amince in dai hakan zai saka ka farin ciki saboda burina kenan,na saka ka a cikin sa ko da ace ni zan fuskanci akasin haka." Hannunta ya riƙe kam sai ya rungumeta." Na san cewa duk ranar da muka rabu zan yi kewar mace,mai haƙuri da hali na gari ina miki fatan Allah ya baki rayuwa ingantacciya,kuma na miki alƙawari zan bawa ɗanki kulawa." Komawa ta yi ta kwanta ba tare da ta amsa ba ta na zubar hawaye. Washegari A.m da kan sa ya shirya ta suka tafi asibitin.Bayan gwaje-gwaje da likitan ya yi musu har da ita,ya tabbatar masa da lafiyar ta ƙalau ba sa buƙatar wani dashi.Magani ya ba su wanda duk lokacin da zai yi tarayya da ita ya yi amfani da shi. Duk da cewar bai ji daɗi ba ya so ayi komai a wuce gurin,amma haka ya baro asibitin cikin jimami,ran sa duk babu daɗi bayan ya karɓi maganin. A.m da gaske yake nufi da ya ce mata kafin su koma gida sai ya ba ta tsaraba,ita dai dariya ta ke masa suna gudanar da rayuwa a ƙasar mai wuyar mantawa. A ranar da zasu dawo ta na kwance ta na tunanin in da za ta kai abubuwan da ya siya mata,saboda ya yi mata siyayya ya kashe mata kuɗi na ban mamaki ta san ko hauka ta yi ba za ta kai ma Mama kayan nan ba,haka kuma ba za ta kai gidan sa ta na amfani da shi ba amatsayin ta na ƴar aiki,mamakin sa take da ko tunani bai yi ba ya yi mata irin waɗannan siyayya. Ta yanke shawarar kai ma Mariya ta ije mata kuɗin kuma sai ta din ga sakawa a banki. Kamar yadda suka tsara jirgin su na sauka ta wuce gida kan sai ta ƙara sati,in ya so sai ta ce jikin Mama ne ya tsananta. Juwairiya ta tsorata lokacin da ta yi sallama Mama ta amsa mata ta na ƙudundune da bargo,sai hankalinta ya tashi ganin ta yi wa Zainab ƙaryar Mama ba ta da lafiya gashi ta same ta ba lafiyar,shi ya sa ƙaryar ciwo babu kyau don ita gani take kamar ƙaryar da ta yi ne ya kama Mama. "Mama dama baki da lafiya shine baki kirani kin gaya min ba."Ta faɗa cikin tashin hankali ganin ta na jin jiki. "Na so na kira ki ita ta hana gani take kamar jikin ba zai yi zafi haka ba." Ibrahim ya ba ta amsa don ta kasa magana sai hawaye dake gangarowa,saboda tsananin zafin ciwo kuma duka kwana biyu ta fara ciwo. Asibiti ta samo mai adaidaita ya kai su bayan an yi mata allura aka ba ta magani,suka dawo gida ta shiga jinyar Mama. Rashin lafiyar Mama sai ya hanata komawa gidan ta na jinyar Mama da yanzu ta fara jin sauƙi. "Juwairiya ya kamata ki koma aiki kin san yau saura kwana goma sha biyar shekara ɗaya ya cika,kuma kin san na gaya miki ko duk duniya mutumin nan zai baki ba zan lamunta ki ƙara ko da kwana ɗaya ba." Mama ta ce mata cikin murya mai ɗan zafi duk da jikinta babu ƙarfin da za ta ɗaga murya. Gabanta ne ya faɗi ta ɗago ta kalli Mama sai jikinta ya yi sanyi ta ce."Na sani Mama kuma da zarar lokaci ya cika ni kaina gida zan dawo na yi aure kamar yadda kike buƙata,amma ki kwantar da hankalin ki kin ga yanzu ba kya jin daɗi." Ta miƙa mata kofin kunu tsamin da ta sa ta dama mata saboda tafi son abu mai ruwa-ruwa. "Ai ina tuna miki ne don ranar da shekara ɗaya ya cika in har baki dawo ba sai dai ki ji na kai Baba Sani kotu." Ta karɓi kofin kunun da ta miƙa mata ta fara sha.Jikinta ne ya yi sanyi ta miƙe ta fice daga ɗakin domin ba ta ƙaunar ta ji Mama ta irgo mata kwanakin rabuwar su duk sai ta ji hankalin ta ya tashi. A yau take son ta je ta gyara layinta da kampani m t n suka kulle mata tun washegarin da ta dawo saboda ciwon Mama ta kasa zuwa ta gyara,amma yau ta ga jikinta ya yi sauki ya sa ta shirya don ta san A.m zai neme ta har ma da Zainab saboda ta ƙara kwanaki akan sati biyu. Kasancewar da yamma ne sai ta yanke shawarar ta tafi a ƙasa tun da babu wani nisa. Tafiya take a hankali kamar ba za ta taka ƙasa ba ji ta yi wata mota ta sharo ta na shirin tureta. Da sauri ta matsa gefe cikin tashin hankali ta na tunanin waye wannan mahaukacin da zai kasheta. "Ke amaryar wucin gadi ina za ki je ba tare da izini mijinki ba?" Muryar A.m ya daki kunninta lokacin da yake saukar da gilas ɗin motar sa. Mamakin ganinsa da tsorata ta da ya yi ya sa ta ɓata fuska amma da murmushi ɗauke a fuskarta. "Allah ka ba ni tsoro na yi mamakin ganin ka"Ta ce mishi lokacin da ta tsaya a gefen shi. A.m ya kashe mota ya fito ya tsaya kusa da ita ya ce."Ina ta nemar wayarki ba ta shiga na kira wannan kwaɗayayen Baba Sani amma kin san me ya ce."Wai sai na biya shi zai haɗa ni dake hankalina ya tashi hakan nan na daure na zan zo gidan ku sai gashi mun haɗe kin yi satar fita." Dariya ta yi jin abin da ya ce."Ni ba satar fita na yi ba layina aka rufe zan je na buɗe ne."Ta bashi amsa ta na kallon shi. "Lafiya ba ki dawo ba gidan babu daɗi kwana biyu na yi missing ɗinki ga tubbina da ya yi rashin daddaɗar abincin.Gaskiya gangar jikina da tubbina sun yi rashin har na kasa haƙura ." Zuba mishi ido ta yi jin abin da ya faɗa kamar da gaske. "Ai ko ya kamata ka fara sabawa ko ka manta saura kwanaki mu rabu.Kuma meye abin damuwa bayan ka na da matar so a gida ban ga dalilin da zai saka ka damu da matar wucin gadi ba." Ta faɗa cike da tsantsar kishin Zainab da ya bayyana ƙarara a fuskarta. Kallonta ya yi tare da matsowa daf da ita ta yadda har suna jin numfashin juna ya kama hannunta ya ce. "Kishi ko?" Ya saki hannunta ya juya mata baya sannan ya ci gaba da magana. "Bai kamata ki saka kishin matata a zuciyarki ba kin san cewa ita ce matar so.Kin sa dalilin aurenmu am sorry to say da Zainab ta na haihuwa babu abin da zai saka na aure ki.Kawai ni na san in muka rabu zan yi kewarki da kishin mijinki don ki na da baiwar da ba kowa ce mace take dashi ba." Ta na son ta yi magana kuka ya ƙwace mata amma hakan na ta daure ta ce."Mai yasa ka shigo da ni cikin rayuwarka ka san ba gurbina a cikin zuciyarka?" "Saboda ki haifi yaro na bawa Zainab saboda ina son na ga ƙwaina ya sa na aure ki."Ya faɗa muryar sa a ɗage. "To mai ya sa kake gaya min maganganun da suke yaudarar zuciyata?Ka tsaya iya kan abin da kake buƙata a gareni." Cikin kuka take mishi maganar sai ta juya za ta ruga da gudu da sauri ya janyo ta zai rungume ko mai ya tuna ya sake ta ta ruga da gudu ta na kuka. Cikin motar shi ya faɗa ya na wani irin huci kamar mesa ya daɗe a gurin sannan ya figi motar a guje kamar zai tashi sama. Lantana mai aikin Zainab da take laɓe a bayan kango ta na kallon A.m da ya yi shirin rungume Juwairiya ta fito cikin tsananin mamaki ta na kallon in da motar shi tabi. Zaro idanunta ta yi cikin tashin hankali ta na mamakin da ma cin amanar ta suke shi da ita?Allah Sarki baiwar Allah ta na can ta damu da ita gashi wayarta ba ta shiga,ashe ita ta na can suna cin amanarta.Haba!Biri ya yi kama da mutum ai ko yau dole Zainab ta ji abin da suke yi ita ta na can sai tsabar son kuɗi ta ɗauko mace zuƙeƙiya ta ije ma mijinta. TO FA WAYYO ALLAH BA RI NA YI NAN DON GASKIYA BAN SHIRYA GANIN WANNAN TASHIN HANKALI BA. KU CI GABA DA BIBIYAR LINTAFIN DON JIN YADDA ZA TA KAYA A CIKIN LINTAFIN NAN MAI FARIN JINI. BARI NA TUNA MUKU DA SUNAN SHI SAKACINA KO HALIN MAZA TAKU JAMILA LAWAL ZANGO JAMCY Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 25* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM Hajiya Zainab tana zaune a ƙaton katafaren falonta ita da ƙawarta mai suna Nabila wacce suka taso tun yarinta,amma ita tana aure a Abuja ta zo ganin gidane da kuma ta ya Zainab murnar asibitin da ta buɗe. Lantana ce ta shigo saboda tsabar gulma jikinta har kyarma yake yi. Duk da ganin tana tare da baƙuwa amma sai ta kasa haƙuri har baƙuwar ta tafi, matsawa kusa da ita ta yi ta fara magana don tsabar gulma da yake cinta. "Hajiya don Allah in ba za ki damu ba ina son na yi magana da ke kuma mai mahimmanci." Zainab ta kalle ta sheƙeƙe tare da jan tsaki ta na tauna jingam a bakinta. "Ni fa Lantana na fara gajiya da halinki yadda kika san ke kika kawo babu duniya,na san yau ma bai wuce ki ce na baki kuɗin aiki kafin wata ya ƙare ba,kuma na rantse ko me za ki ce ba zan bayar ba." Ta faɗa hankalinta na kan waya ta na hira da matar da ta addabeta take ta tura mata da sallama kullum,ba ta daina ba har sai da ta yi nasara ta fara magana da ita suna gaisawa. Lantana ta kalleta a ranta ta ce."Banza mara mutunci kawai ai wallahi don kawai iskanci suke yi da ita da na so ma ya aureta na ga ƙaryar iya shege." Amma a fili sai ta ce." Ba wannan ya kawo ni ba idanuwana sun yi mummunan gani kuma in kika ji,wallahi hankalinki zai tashi matuƙa ba na son abin da zai cutar da ke ne kasancewar ki na taimaka min. " Ke dakata karki dame ni da shegen surutunki." Ta ce bayan ta ije wayarta sannan ta kalleta ta ci gaba da cewa." Za ki iya magana ba ni da matsala ƙawata ce tun na yarinta." Lantana ba haka ta so ba amma tun da ta faɗi haka gashi gulma na iban ta sai ta kwashe abin da ta gani,harma da ƙara magi da gishiri don ya yi zaƙi cakwai ta fara gaya mata. Ba ta kai ga ƙarshen labarin ba in da take tunanin zai fi ɗaga hankalinta. Zainab ta miƙe kamar wata mahaukaciya ta kai mata raruma. Wani irin shaƙa ta kai mata cikin ihu ta zare idanunta kamar mahaukaciya. " Ke baki da hankali mijina kike maganar kin gan shi da wata in ma da wata kika gan shi,bai kamata ki haɗa shi da wata ƙazamiya kucaka yar matsiyata ba." Sai kawai ta rufeta da duka da mari take kai mata. Lantana ta hau ihu da ƙarfi ganin dukan da take mata ta ƙara sakin ƙara ganin ta wawuro wani gilas za ta maka mata. " Don Allah ki taimake ni wallahi abin da na faɗa miki gaskiya ne,ba zan shirya irin wannan ƙaryar na gaya miki kawai don na ɓata miki." Ta faɗa yayin da ta ruga ta ɓoye a bayan Nabila da ta miƙe cikin tashin hankali ganin za ta yi kisa. " Zainab be patient kar fa kishi ya sa ki aikata dana sani,ya kamata ki yi ma maganarta kyakykyawar fahimta,ita ba ƙaramar yarinya ba ce da za ta yi miki gulma don son ranta." " Ke Nabila dakata wallahi yanzu za ki fita da fashashshen kai mundin kika yadda da abin da take faɗi,mijina mai aji da kyau za ta haɗa shi da mai aikina.Na yadda da A.m ba zai taɓa kula wata ƴa mace ba,don ban taɓa ganin ya kula mata masu aji ba bare ita ƙazama mara gata da aji." Ta ce da ita tare da ƙara rarumar abu ta yo kanta da shi. Nabila ba ta damu da abin da ta ce ba ta tunkare ta tana ƙoƙarin ƙwace makamin da ta ɗauka. Da ƙyar ta samu ta zauna tare da dafe kanta ta ce."Na yi baƙin cikin da ki na nan ta kawo min wannan baƙin labari,da bakya nan sai na nuna mata haukana." Sai kuma ta kai mata shaƙa da ƙarfi saboda gani take kamar ta raina ta ne ta kawo mata wannnan labari. Lantana idanunta suka kaɗa suka yi jajur ta na ƙaƙari saboda ta shaƙe ta sosai,sai zaro idanu take ta na dana sanin gaya mata gashi za ta baƙunci lahira ba ta shirya ba. Lantana ta sadaƙar mutuwa za ta yi ta tabbata da ita kaɗai ne da Zainab a gidan, sai ta kasheta dama haka take da kishi akan mijinta take barin shi ya na garari. Da ƙyar Nabila ta ƙwaci Lantana da take fitar da numfashi sama-sama. Ta samu ta tura ta cikin ɗaki tare da rufe ta a ɗakin ta dawo gurin Lantana da take murza wuyanta. " Kin tabbata abin da kika gani gaskiya ne?" " Wallahi da gaske ne Hajiya da idona na gansu."Ta faɗa cikin kalar tausayi. " Ok ga wannan ki riƙe na gode da kika gaya mana ki ci gaba da saka ido a kansu." Lantana da ta ga an miƙa mata farare gal da su sai ta washe baki,ta karɓe ta soke sannan ta kalle ta ta ce. " Hajiya na gode dama tuntuni nake lura da ita yadda take mishi kallo kamar mayya,zan ci gaba da bibiyar su amma fa sai dai ki bani numbar ki ba zan gaya ma Hajiya Zainab ba kashe ni za ta yi." Bayan ta gama da Lantana ta buɗe ɗakin ta shiga ta na zaune akan gado,ko kaɗan ba ta nuna damuwarta akan maganar ba,saboda ta saka a ranta A.m ba zai taɓa dubi ga wata ƴa mace ba. Nabila ta zauna a gefen ta suna fuskan tar juna. Zainab na yi matuƙar mamakin irin yadda kika yadda da mijnki duk da ba ina zargin sa ba ne, amma Lantana ba za ta taɓa gaya miki ƙarya ba musamman in kika dube ta za ki ga alamun gaskiya a fuskarta,na tabbata a kwai ƙamshin gaskiya a maganarta ko da kuwa ba haka maganar take ba. Duk da cewa A.m mutumin kirki ne wanda bai damu da irin wannan rayuwar ba,ni kai na ba na tunanin zan iya tarayya da mai aiki duba ga yadda ya tsani duk wani talaka,amma ki tsaya ki yi karatun ta natsu ki saka ido domin namiji ba shi da tabbas!" Zainab ta kalli Nabila a wukaƙance tare da miƙewa ranta a ɓace ta ce. " Ba na son wulaƙanci Nabila mijina za ki din ga haɗa shi da wata.A kwai yadda a tsakaninmu da shi,muddin kika ce za ki faɗi wani abu na rashin kirki a garesa wallahi yanzu za mu raba jaha da ke." Ta buɗe baki za ta ƙara magana ta ɗaga mata hannu tare da nuna mata ƙofa."Ki fitar min daga gida na yanke duk wata alaƙar da ke tsaƙaninmu." Miƙewa ta yi ta ɗauki jakarta ta na kallonta. " Bazan yi fushi da ke ba ƙawata zan yi miki uzuri har zuwa lokacin da za ki gane gaskiya,ni na san dole wata rana za ki neme ni bayan kin gane cin amanarki yake yi." Har ta fara taku bayan ta gama magana sai kuma ta dawo,ta tsaya gaban Zainab tare da riƙe hannunta ta na hawaye ta ci gaba da magana. " Ba wai ina son na tona miki rayuwar aurena ba ne a'a sai don na gaya miki don ki ɗauki darasi a ciki.Kamar yadda kika ba wa A.m amana haka na ɗauki yaddata na ɗora akan Al'amin,ba ni da haufi akan sa na yadda da shi fiye da yadda na yadda da kaina.Kwasam na kama shi da kwandom a aljihun sa wanda hakan ya ɗaga hankalina matuƙar gaske har sai da na kwanta jinya.Na yi kuka sosai rikici sosai muka yi sai daga baya na haƙura bayan duk mutuncin sa ya zube a idanuna." Fara tafiya ta yi bayan ta gama gaya mata ta na kuka. Jikinta ya yi sanyi da sauri ta kama hannunta ta riƙe tare da faɗawa jikinta ta fashe da kuka sosai. "Don Allah Nabila karki saka zuciyata ta gasganta abin da kike faɗa min domin zuciyata ba za ta iya jure ganin A.m da wata mace ba!Kin ji na rantse miki duk ranar da A.m ya yi gigin kallon wata ƴa mace to ni ce ajalinmu baki ɗaya,nufin sa zai iya ganin ɗansa a duniya bayan ni na lalata rayuwata saboda shi?" Ta ce ta na kuka tamkar wata wacce aka yi wa mutuwa sai kuma ta janye jikinta tare da share fuska. " Kai ina! Zuciyata kasa karɓar zargin da kike masa A.m ya yi min alƙawarin ba zai kula ko wace ƴa mace ba kuma na yadda da shi,in kuwa zargin da kike masa ya zamo gaskiya wallahi sai na canza kamannin ko wace ya mace da ta haɗa jiki da shi, ke bama Juwairiya wulaƙantacciya ba ko yar gidan uban waye acid zan wasa ma shegiya ta mutu kowa ya huta." Cikin matsancin kuka take magana gabaki ɗaya hankalinta ya tashi,sosai duk da ta yi ƙoƙarin ta saka zargin da take ma A.m,amma in ta tuna ko kallon fuskarta ba ya yi bare ya riƙe sunanta sai ta ji sanyi ta kauda zarginta. " Haba Zainab kamar ba ki waye ba ina bokon na ki yaje? Ai yanzu karki nuna komai ki nuna tamkar ba ki san da wannan maganar ba,sannan ki saka matakan tsaro ki sa ido sosai a tsakanin su duk wata hanya da zai saka ki fahimci ko da wani abu ki kula da ita sa..." " Kai." Zainab ta ce sannan ta kalle ta taci gaba da magana." Ta ya ya za'ai na kauda kishina na saka ido don in gano abin da suke yi,ba zan iya ba ni kawai zan tambaye shi ne in ya gaya mini ƙona su duka zan yi,in ya so duk abin da zai faru ya faru!" Ta furta cikin tashin hankali yayin da take ji sam ba za ta iya ba. "Na san ba zai iya auren ƴar aiki ba,amma yanzu sun cika ɗora kwaɗayin su ba sa iya ɗauke idanun su. Ki ɗan danne kishinki ki gano wani abu in har kika gane ya na tare da ita, ni zan siyo miki acid ki watsa mata,ko ki bani kwangilar watsa mata babu uban da zai ɗaure ni yar manya ce ni mijina kuma canal." Da ƙyar Nabila ta yi nasarar kwantar mata da hankali,duk da har yanzu ta kasa amincewa,don haka ta saka a ranta ya na dawowa za ta tambaye shi dole ya gaya mata komai. A tare suka fito daga ɗakin suka nufi kicin in da Lantana take aiki,ganinZainab da gudu ta ruga ta na faɗin. "Wallahi Hajiya na gan...." Da sauri Zainab ta ɗora ɗan yatsa a bakinta kan ta yi shiru,don ta na jin kamar ta ƙara mata wani dukan.Kuɗi ta ƙara ma Lantana da take ta murna sosai ga duka ga samun kuɗi ita kam yau gulma ta yi riba. Zainab na zaune a gaban madubi ta na tsantsara kwallliya zuciyarta cunkushe da tunani kala-kala. Ji ta yi an rungume ta ta baya sannan ya ɗora kan sa a bayanta,ba ta juya ba kasancewar tun kafin ya shigo ƙamshin turaren sa ya bayyanar masa da shigowar sa. Fuskarta a ɗaure ta juyo ta kalle shi sama da ƙasa haka kawai sai ta ji wani mugun haushin sa da tsanar haɗa jiki da shi. Sakar mata murmushi ya yi tare da kamo hannunta. " Gibbiyar mata sarauniyar mata a cikin birnin zuciyar Abdurrahman mai na yi ake fushi da ni? Ko don rashin dawowata da wuri ne am so so sorry babyna wallahi wani uzuri ya tsare ni na kira wayarki ba ta shiga." Ya faɗa da muryar sa mai sanyi da take kwantar mata da hankali ya kuma san ya na sace zuciyarta da ita. Ganin ta ƙi kula shi sai ya kamata suka faɗa gado ya na shaƙan kamshin turarenta ya na faɗin. " Wane irin turare kika sa yau kamar yafi wanda kike shafawa daɗi,don ban taɓa jin ƙamshi mai kwantar da zuciya da saka nishaɗi a rai ba.. Gaskiya kuma kwalliyar ta yi na kuma yaba bari kiga in siye ta koma nawa ne babu tayi." Ƙoƙarin warware tawul ɗin dake jikinta yake yi ya na gaya mata kalamai masu daɗi da kwantar da hankali. Da sauri ta ƙwace jikinta ta harare shi ta saki tsaki ta saka kayanta ta fice daga ɗakin ba tare da ta kalli in da yake ba. Tsayawa ya yi yana kallonta ran sa ya ɓace saboda ya tsani tsaki ita ma ta san haka,don haka bai ƙara kula ta ba ya tuɓe kayan sa ya watsa ruwa,bai nemi abincin ba saboda sai da ya tsaya gidan A.k ya ci abinci tun da ya san Juwairiya ba ta nan gashi ya kasa iya cin abincin Lantana. Kwanciyar sa ya yi ba tare da ya ƙara kula ta ba,wanda hakan ya sa ta fara yadda da abin da Lantana ta faɗa mata,tun da har zai iya ƙyaleta ganin ta yi fushi ba tare da ya rarrashe ta ba ko ya tambayi ba'asi. Tun tana saka ran zai zo ya rarrrasheta amma sai ta ji shiru,ta kalli agogon hannunta ƙarfe ɗaya na dare sai ta sauka a chert ta shige ɗakin sa tare da buga ƙofar da ƙarfin gaske. Tsayawa ta yi a kan sa ta na huci kamar wata mesa ganin bacci yake yi,filo ta ɗauka tare da maka masa ya buɗe ido cikin razana ganin ta tsaye a kan sa sai ran sa ya ɓace,ya kalle ta bai ce mata komai ba amma idanun sa suna masa kallon gargaɗi. " Kaga Malam ka tashi magana nake son mu yi da kai."Ta ce dashi tana girgiza ƙugu idanunta a bushe kamar ba dare ba. " Zainab." A cikin wata irin murya ya yi magana sannan ya ɗora da ce wa." Don Allah bacci nake ji ki bari sai da safe." Ya rungume filo tare da mirginawa ya ci gaba da bacci,komai ya tuna sai ya juyo ya na kallonta ya miƙo mata hannu yana nufin ta zo su kwanta. Wani irin kallo ta watsa mishi." Ka ga Malam wallahi sai ka tashi ba za ka barni da baƙin ciki na kasa bacci ba don ba zan iya bari gari ya waye ba." Sai ta fara tsiya ta na mishi wasu irin maganganu da ya kasa gane mai take ce wa,sannan kuma ta hana shi bacci da ga ƙarshe dole ya tashi saboda magana take da murya mai ƙarfi,kuma abin da take faɗi ya yi mugun ɗaga masa hankali duk da bai wani fahimce ta ba. Tashi ya yi zaune ya na mata wani mugun kallo. " Wallahi baki da mutunci ga shi na tashi gaya mini damuwarki,amma ki sani in na ji maganar ba ta da mahimmanci kin san sauran." Ya faɗa da muryar gargaɗi ganin ta hana shi bacci. Hararar shi ta yi tana faɗin" Oh koma me za ka ce kai ka sani tun da ka zama munafuki, ka bani mamaki fir'auna a zuci Annabi Musa a baki." Ta faɗi hakan ne don ta gane ko ƙarya Lantana take mata don har yanzu ta kasa yadda da abin da ta faɗa mata. Bai ce mata komai ba ya ƙara watsa mata mugun kallo na na gargaɗin ta iya bakinta. Cikin tsanani mamaki A.m ya ji ta watso mishi tambayar da ya girgiaza shi ta ce. " Mene ne alaƙar ka da Juwairiya?" Ya shiga cikin tsanani tashin hankali ya ruɗe matuƙa ya kuma razana domin jikin shi rawa yake ayi,jin tambayar da ta watso mishi ya shiga damuwa Baba Sani ya faɗo mishi a rai yana tunanin ko shi ya faɗa mata,ya san zai iya don ya na shakkar sa ba shi da mutunci na ƙarshe. Allah ya so babu wadatacciyar haske a ɗakin sai fitila mara haske na bacci dake kunne mai kama da babu,domin da a kwai ya tabbata babu abin da zai hana ba ta gano gaskiya ba,saboda jikin sa ya jiƙe sharab da gumi sai zufa yake karyo mishi,ya na ji a ran sa in Allah ya haɗa shi da Baba Sani sai dai Allah zai raba su. Shirun da ya yi sai zuciyarta ta karye ta fara tunanin to ko gaskiya ne. A.m da yaga zai tona a sirin kanshi da kanshi sai ya dake cikin wata irin murya ya ce." Mai ya sa kike min wannan banzar tambayar waye ita kuma meye haɗa ni da ita? Ƴar aikin ki fa kike danganta ni da ita kin cuce ni,mai zan yi da ƴar matsiyata jinin talauci kin taɓa ganin na kula wata mace duk da damuna da suke yi balle ita. Wani irin sanyi ta ji ya kamata jin abin da ya faɗa dama ta san ce wa babu yadda za ayi ya kulata,amma don kar ta yi saurin sauko wa ta ce." Ba wani nan munafiki ai ni ka bani mamaki ka rasa wacce za ka kula sai ita,to bari ka ji na rantse maka ba ita ba ko wace mace ka kalla nine ajalinta saina illata rayuwarta,yadda ko waɗanda suka kawo ta duniya ba za su so su ganta ba balle kai kana tunanin zaka haihu ne ni bana haihuwa." A.m da ya koma ya kwanta jikin sa a mace hankalin sa ya tashi sosai,ya ɗan ji daɗi da ya fahimci ba Baba Sani ya gaya mata ba,don in da shine duka zai ɓata lamarin ya tabbata sai ya kunna mata wannan recording da ya yi,amma a ran sa ya na mamakin wane munafukin ne ya gaya mata,ya san ce wa A.k ba zai taɓa gaya ma matar sa ba." Domin ya cire mata shakku sai ya miƙe cikin ɗaga murya ya ce. " Look Zainab na lura baki da hankali ko kuma kin sha wani abu ko kin fara ɗaukar zigin ƙawaye,in baki yadda da ita ba mai zai hana ki daina yawo ki zauna ki kula da ni,wanda ni kaina zan fi buƙatar haka,bawai ki tsaya kina zargina da wata kucaka ba,kamana kike tunanin zan iya kula ta mai take dashi kuma waye ubanta a duniya." Ya yi ƙuta ya ci gaba da magana da ƙarfi ganin maganganun sa suna tasiri a kanta saboda ta yi shiru ta na sauraren sa. Janyo ta ya yi zuwa jikin sa." Zainab please trust me." Ya ƙara marairaice murya ya na shafa bayanta da ta yi lamo a jikin sa kamar wata mage ta na ƙara jin madarar son sa na ƙwaranya a zuciyarta. A.m da ya ji ta yi lamo a jikin sa ya saki gwauron numfashi,ya na tunanin yadda zai yi ta amshi yaron da Juwairiya za ta haifa masa,amma ya saka a ran shi dole ta karɓa ko ana ha mata ana ha maza. " Bai kamata ki yadda da zugin maƙiya a kanmu ba ki tuna na yi miki halacci har yau babu wanda ya san ke ce bakya haihuwa,kuma na kasa haɗa wata mace da ke na riƙe alƙawarin da ba yi miki duk da ina son naga ƙwaina a duniya fiye da rayuwata,hakan ba zai sa ki yadda da ni ba?" Zainab jikinta ya mutu murus duk da ta yadda da shi,amma ta ɗauki aniyar cusgunawa rayuwarta da wulaƙanta ta agaban shi,domin ta cire ɗan shakkun da take yi a zuciyarta kuma in ta gane gaskiya Lantana ta kuka da rayuwarta. " Ka yi haƙuri zauji zuciyata ce ta kasa gasganta hakan bayan na san halinka fiye da kaina,amma in sha Allahu ba zan ƙara maka irin wannan tuhumar ba, kuma ni ma na fahimci maƙiya ne suke son su raba mu sai dai su mutu don ni da kai mutu ka raba." Rungumota ya yi ya ce." Wannan dalilin ya sa nake matuƙar son ki auren mu da ke sai mutuwa za ta raba ni da likitar likitoci. Yauwa bari na siya kwalliyar da aka hana ni siye bayan daga kallo ɗaya na siya babu ta yi gashi yanzu har ta yi arha."Dariya ta saki suka manta komi . A.m bai tambayi wanda ya gaya mata ba amma ya zama dole ya ƙara saka tsaro saboda someone is behind ko kaɗan bai yi tunanin Lantana ba ce. Cikin tsananin mamaki Baba Sani ya tsaya a ƙofar gidan sa ya na kallon Maama da ke tsaye da ƴan sanda guda biyu a bayanta. " Yauwa ranka ya daɗe ga shi nan ku kama shi."Ta faɗa fuskarta babu walwala. " Ranka ya daɗe don Allah kar ku kama ni na rantse gobe Juwairiya za ta dawo na gaya mata,amma ta ƙi ji duka yau sati biyu da shekara ta yi kuma wannan bawon Allah ya taimaki rayuwarta."Ya faɗa ya na zare ido. " Ok kin ji abin da ya ce ki yi haƙuri in har ba ta dawo ba sai mu ɗauki mataki."Ɗaya daga cikin ɗan sandan ya faɗi. " Ba komai Allah ya kaimu goben in kuma ba ta dawo ba zan kai gaba,ko da kuwa baku ƙwato min haƙƙina ba." Ta ce ta kalle Baba Sani cikin ɓacin rai ranta ya na faɗa mata a kwai abin da Juwairiya da Baba Sani suke ɓoye mata. A daren da suka yi maganar da misalin ƙarfe biyu na dare Mama na zaune a sallaya ta na karatun kur'ani bayan ta idar da sallar nafila. Sai ta ji kamar ana buɗe get ɗin gidan tsoro ya hana ta motsi zuwa can ta ji an shigo. Wasu ƙattin maza majiya ƙarfi guda uku suka shigo. Da sauri ta miƙe ta na salati kafin ta furta komai sun shaƙa mata wani abu a fuska ta zube luuu a ƙasa. TO FA MASU KARATU NA IJE BIRONA SABODA TSORON WAƊANNAN MUTANE INA TUNANIN SU WAYE. KU CI GABA DA BIBIYAR LINTAFIN DON JIN YADDA ZA TA KAYA A CIKIN LINTAFIN NAN MAI FARIN JINI. BARI NA TUNA MUKU DA SUNAN SHI SAKACINA KO HALIN MAZA TAKU JAMILA LAWAL ZANGO JAMCY Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 26* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM A cikin motar da suka zo da ita suka sakata,sun yi tafiya mai nisa gaske sannan suka tsaya. Duk nisar tafiyar da suka sha amma Mama da Ibrahim ba su farfaɗo ba. Wani ƙaton gida suka shiga da su tare da kwantar da su,sannan suka fice daga gidan. Kusan awa ɗaya Mama ta yi sannan ta farka cikin tsananin razana tana salati.Ta kalli in da take yayin da take tsananin mamaki,idanuwanta suka firfito tana mamakin in da ta tsinci kanta. Ibrahim dake kwance ta rungume tana jijjiga shi,cikin tashin hankali tana mamakin ganin ta a wannan gida. Ko da ya buɗe ido sai ya cika da tsananin mamaki ya kalle ta ya ce. "Mama ina ne nan kuma mai ya kawo mu wannan gida?" Mama dake cikin tashin hankali ba ta ba shi amsa ba,sai miƙewa da ta yi tana ƙarewa gidan kallo. Duk da rashin ƙarfin jikinta amma haka ta miƙe ta kama hannun Ibrahim suka fito waje. " Madam lafiya ina za ki je." Ta ji muryar wani mutum wanda yake tsaye a get ɗin gidan,ya na sanye da kakakin sojoji da bindiga ɗauke a hannunsa. Mama ta ja baya da sauri tana kallon sa da tsoro a fuskarta. " Waye kai kuma mai ya sa kake tambayata?Zan koma in da kuka ɗauko ni." Ta ba shi amsa da muryar tsoro a fuskarta,tana ja da baya saboda ta tsorata ƙwarai da ganin sa. " Madam ki yi haƙuri oga bai ba mu izinin ki fita ko da ƙofar gida ba ne." Ya ce cikin ɗaure fuska ba tare da ya kalle ta ba,balle ya ga tashin hankalin da ke ɗauke a fuskarta. " Waye kai mene ne haɗina da kai har za ka ce ba zan fita ba,sannan waye agan ka ina ruwana da shi." Ta jera masa tarin tambayoyin da take tunanin ba zai amsa mata ko ɗaya ba. " Wannan kuma sai ki jira har sai ya zo ki yi mi shi tambayoyi,amma ba ni da masaniya ina kan aikina ne kawai. Mama da fari ta ɗauka wasa yake mata amma da ta dage kan dole sai ya buɗe mata,sai ta ga ya ɗaure fuska ya ɗaga zungureriyar bindigar sa,ba tare da ya ƙara kallon ta ba. Da sauri ta kama hannun Ibrahim suka koma ciki,saboda ta tsorata da shi gani take kamar zai harbe ta. " Inna lillahi! Wai me ke faruwa ne na kasa gane komai ya Allah ka fahimtar da ni,na san cewa Baba Sani ba zai taɓa killace ni a gidan nan ba don kawai na buƙaci Juwairiya ta dawo." Ta faɗa cikin tashin hankali tare da rashin madafa tana ji kamar ta yi hauka. " Ina Juwairiya mai ya sa ita ba'a taho da ita ba?" Ta tambayi kanta da tsananin mamaki yayin da ta rasa ta in da za ta fara tunani,domin lamarin ya ɗaure mata kai sosai. " Ko masu garkuwa da mutane ne suka sace mu?" Ta faɗa tana kallon Ibrahim da ya cika da mamaki ya na kallon daular gidan da aka kawo su. A jiyar zuciya ya yi mai nisa sannan ya sauke tagumi ya kalli Mama,da fuskarta ya nuna tsantsar tashin hankalin da take ciki. " Ba na tunanin za'ayi garkuwa damu har gida sannan aka wo mu cikin wannan daular Mama! Ki duba irin wannan gidan na masu kuɗi ne sosai.Ni dai ina zargin a kwai wata a ƙasa.Tabbas a kwai lauje cikin naɗi." " Haka ne Ibrahim zuciyata ta fara hasasomin haka,sai dai ina zargin duk abin da ya faru a kwai saka hannun Baba Sani a ciki.Zuciyata ta fara zargin in da ya tura Juwairiya ba alkhairi ba ne,sai dai ina ɗan jin sanyi ne, in na tuna da Juwairiya yarinyar kirki ce,na yadda da tarbiyar da na ba ta sam ba na tunanin za ta aikata abin da nake zargi,duk da cewa ba'a shedar ɗan yau." Hannu ta ɗora a ka yayin da gabanta ya faɗi ras!Sa'ilin da wani tunani ya faɗo mata. " Kar dai a ce Baba Sani ya yi mini ƙarya ne akan aiki zai kaita,ya saka ta a hanyar banza?" Ta tambayi Ibrahim da take tunanin bai fahimci abin da take nufi ba. Mama ta saki ƙara tare da zubewa a ƙasa tana faɗin." Ya Allah na kasa samun natsuwa zuciyata,na shiga ruɗanin halin da Juwairiya take ciki,kar a ce Baba Sani ya ɓata mini tarbiyar da na gina ta akai,ya saka ta a harkar banza.Kar a ce da kuɗin da take aikata alfasha muke ciki." Sai ta girgiza kanta tana kuka da ƙarfi ta ci gaba da faɗin. " Iya tsawon yaushe zan zauna a wannan gidan ba tare da na san gaskiya ba,in har Juwairiya ta canza tarbiyar da na ba ta tabbas ba zan iya yafe mata ba,domin na ci burin na ga na aurar da ke Juwairiya kar ki yi mini haka." Da sauri Ibrahim ya taso ya rungumeta yana rarrashi ganin tana son ta fita hayyacinta. "Mama mu bi abin da sannu-sannu kar ki aibata ta,na san cewa sam Anty Juwairiya ba za ta aikata haka ba,tabbas a kwai abin da ke faruwa.Kuma duk wanda ya sa aka kawo mu cikin wannan daular,to a kwai saka hannun Baba Sani a ciki don zuciyata ba ta yadda da irin sanyin da ya yi ba,lokaci guda ya zubda duk wani makaman sa akanta." Mama ta shiga cikin tsananin ruɗani ƙwarai ta yi ihu ta yi kuka,tana roƙon mutumin da ya taimaketa ya gaya mata abin da ke faruwa,amma ko kallon ta bai yi ba don ba'a ba shi izinin haka ba,bayan haka shi bai san komai game da lamarin da ya faru ba. Ganin irin kukan da Mama take yi tana kiran sunan Juwairiya ta ƙi shiga cikin gidan,a farfajiya ta tsaye tana kuka sosai ya kalle ta ya ce. " Hajiya ba ni da nufin na cutar da ke gara ki koma ciki,don wallahi ko kukan mutuwa za ki yi ba zan buɗe miki ki fita ba. Jin haka Mama ta ƙara sakin wani kukan ta zauna a gurin ta ƙi motsiwa,sai kuka da take yi domin kanta ya kulle. ***** A ranar da aka ɗauke su Mama Juwairiya ta yi wani irin bacci mai nauyin gaske,ba ta tashi ba sai da ta ɗauki tsawon lokaci tana bacci mai kama da na mutuwa. Buɗe idanunta ta yi cikin tsananin mutuwar jiki don ji take ko ɗan yatsa ba za ta iya ɗagawa ba. Sai da aka ɗauki tsawon lokaci sannan ta samu ta iya tashi zaune. Ɗaga idanunta da ta yi ta kalli agogon da ke manne a bangon ɗakin,da gudu ta miƙe tana salati saboda tunawa da ta yi ko sallah ba ta yi ba. " Na shiga uku mai ya faru yanzu fa ƙarfe ɗaya har da kwata,wane irin bacci na yi ko dai mutuwa na yi na dawo?" Ta tambayi kanta domin wannan bacci da ta yi bai yi kama da na lafiya ba. Da sauri ta miƙe ta shige ba yi tana tunanin to wane sallah ya kamata ta fara. Bayan ta idar da sallah sai ta yi sauri ta ruga zuwa falo,saboda kiran curoma da cikinta yake yi.A haka dai ta ƙarasa tana mamakin jin gidan ya yi shiru,kamar ba mutane a gidan. Ta shiga cikin tsananin tashin hankali da ta duba lungu da tsaƙo ba ta gan su ba ,sai ta fara kuka da salati tana dubawa cikin tsoro.Ta ɗauki tsawon lokaci amma ba ta ji ɗuriyar kowa ba. Tana tsaye a farfajiyar gidan motar Baba Sani ya sawo kai.Da sauri ta ƙarasa gurin shi cikin muryar kuka don tunaninta ya fara ba ta yana da saka hannu na rashin ganin su,ko kuma shine ya ɗauke su. " Baba Sani ina Mama na duba ko ina ban ganta ba." Wata irin tsawa ya daka mata ya ce."Ku ji min munafuka ban sani ba,duk abin da ke faruwa ba da saka hannunki ba za ki raina min wayo." Zare idanunta ta yi ta ce."Wallahi ba ni da masaniya akan komai mai ya faru?" Kallonta ya yi sai ya matso kusa da ita ya fara magana cikin ɗaga murya." Jiya A.m ya sameni ya ce kun yi da shi zai kai Mama wani gari har zuwa lokacin da za ku rabu,saboda na gaya masa ta kawo min ƴan sanda." Ya faɗa ranta a ɓace da baƙin ciki ƙarara a fuskar sa." Wallahi sam ba haka na so ba na so a ce yabar mini komai a hannuna,saboda na yi baƙin cikin irin daular da ya kaita." Juwairiya ta kaɗu da jin abin da ya faɗa sai ta saka kuka sosai,ganin yanzu Mama ta san abin da ta aikata. A ƙasa ta zauna tare da ƙara sakin kuka." Na shiga uku ba zan iya ƙara gaɗa ido da Mama ba,wane irin kallo za ta yi min wallahi na yi dana sani ƙwarai,yanzu idanuwana ba za su ƙara ganin ta ba har saina haifa mi shi yaro."Sai ta ji hawaye na sintiri akan fuskarta. Sosai ta shiga tashin hankali ta na jin ba za ta ƙara iya haɗa ido da Mama ba,don ta san daga ranar da ta ji abin da ke faruwa za ta tsaneta na har abada. Ganin irin kukan da take yi sosai kamar ranta zai fita a ranta ta na jin baƙin ciki matuƙa. Baba Sani bai duba halin da take ciki ba ya ce." Ki kwantar da hankalin ki ni kaina na yi alƙwarin saina raba auren ku,in har na buƙaci kuɗi bai ba ni ba,wallahi saina tona asiri komai ya wargatse saboda na tsani ganin ki a cikin wannan daular,in kuma baya haihuwa ne sai ya sake ki don ba za ki zauna da shi ba." Ba ta ce masa uffan ba har ya gama magana ya fice. Juwairiya sai ta ji ba za ta iya zama a cikin gidan ba,domin duhun da ya yi mata yafi duhun ƙabari. Ta yi kuka har ta ba uku lada tana ji wani irin kunyar Mama matuƙa tun kafin ta haɗa ido da ita.Take nadama ta shige ta har ta fara tunanin ba za ta taɓa yadda ta ƙara haɗa ido da Mama ba,matuƙar A.m bai aminta da ita ba a matsayin matar sa,wacce zai yi rayuwa da ita na har a bada. Duk kiran da yake mata ƙin ɗagawa ta yi tana cikin haɗa kayanta,sai ta ji hucin mutum a bayanta,wanda ta gane A.m ne domin in dai ya zo guri turaren sa yake fara bayyana kan sa. Kuka ta saka masa sosai tana dukan sa aƙirjin sa,ba tare da ya hana ta ba ya ƙyaleta don ya san dole ta yi,ita da take da hawayen banza ba'a taɓa ta ba ta yi kuka ina ga an rabata da Mama. Ganin tana ta dukan sa amma ya ƙi ko motsi sai ta ƙara fashewa da kuka tare da faɗawa jikin sa. " Mai ya sa zaka rabani da Mama anya ka yi min adalci kuwa,da wane ido kake son na kalle ta?Bayan ta san cewa na yi aure ba tare da sanin ta ba! Ni na san Mama ba za ta taɓa yafe mini ba,domin ita ba irin Baba Sani ba ne." Ƙara rungumeta ya yi tsam a jikinsa ya na jin gangar jikinsa ya yi kewarta matuƙa. " Ki gane ba ni da nufin na cutar da ita sai dai na yi hakanne don kar ta hanani samun farin cikina.Ina cikin damuwa sosai aurenki da na yi na yi ne don na samu cikon burina,amma kullum damuwa yake ƙara min ga Baba Sani da ya maida ni bankin sa, ga Mama sannan Zainab ta fara zargina dake jiya na shiga tashin hankali domin a kwai wanda yake bibiyarmu.Anya Juwairiya ke alkhairi ce a gareni?" Ya faɗa yayin da idanuwansa suka canza launi saboda tsananin damuwar da yake ciki. Da sauri ta janye jikinta gare shi tana jin wani iri zafi sosai jin abin da ya faɗa. " Wayyo Allah na! Na roƙe ka ka cire min son sa a cikin zuciyata mutumin da nake so fiye da rayuwata,yake ganin ni ba alkhairi ba ce a rayuwarsa." Ta faɗa a fili sai hawaye suka ci gaba da turereniya a fuskarta. Tasowa ya yi zai riƙe ta ya buɗe baki ya ce." Sam b......" " Don Allah ka fita daga gidan nan ba na son ganin ka! Ka fita kafin kasa zuciyata ta buga."Ta katse shi tana nuna masa hanyar fita. Cikin zafi ya kalle ta." Ok na ji zan fita amma ki gaggauta dawowa gidana domin ki haifa min babyna mu rabu tun kafin Zainab ta fahimci komai,sannan Zainab ta sha alwashin cusgunawa rayuwarki domin ta gano gaskiyar lamarin dake tsakaninmu,don haka ki shirya duk wani cin kashi da za ki gani a gidan,sannan ba zan yi koma baya ga lamarin ba domin mu samu mu fita daga zarginta." Sai Juwairiya ta fara kallon sa kamar wani mahaukaci yayin da take ji tabbas A.m ba ya sonta kamar yadda ya sha faɗa mata. Wani irin baƙin ciki ya tokareta wanda y saka ta ji a ranta za ta iya bijire musu duka tare da tona asirin komai,don a yadda take jin zuciyarta ba za ta iya ɗaukar cin kashin da Zainab za ta yi mata ba. Tabbas za ta tona komai ta fito ta nuna ma duniya ita ma matar shi ce,in yaso sai sama da ƙasa ta haɗe,haka kawai ya din ga ƙwallo da rayuwarta don kawai ya ga tana son sa. Riƙe rigar A.m da ya juya zai fita ganin ta ƙi cewa komai da nufin ta gaya masa baƙaƙen maganganu,amma yayin da ya zuba mata idanun sa masu kama da an zuba zaiba a ciki,sai ta ji wata irin narkakkiyar dalma na son sa ya zagaye duk ilahirin jikinta,kuma ba ta taɓa ganin Mama ta yi sa in sa da mahaifinta ba. Juwa ta yi da sauri ta yi ta shige ɗaki tare da sakin kuka mai ƙarfi. A.m ya daɗe a ƙofar gidan ya duƙar da kansa a kan sitiyarin motar sa,sosai ya jima a gurin ya na jin damuwa a ran sa. Wayar sa ya zaro ya nemo numbar ta da ya yi saving da suna damuwata,domin haka yake kiran ta tun da ta shigo cikin rayuwar sa ta saka mi shi damuwa. Da ya yi nufin ya kirata akan su tafi sai kuma ya tuna bai san wanda yake musu shishshigi ba,da sauri ya figi motar sa a guje ya bar ƙofar gidan,a ran sa ya na addu'ar Allah ya sa ta dawo yau saboda ya yi missing ɗin girta. A ranar ta shirya ta koma gidan A.m saboda gidan ya yi mata babu daɗi. Suna zaune a falo Zainab ta kwanta gaba ki ɗaya a jikin shi tana zuba mishi shagwaba,yayin da shi kuma sai biye mata yake yana ƙara saka ta cikin lambun son sa. Hankalin sa na kan ƙofa ganin yamma ta yi ba ta shigo ba,wayar sa ya zaro ya ƙara tura mata da tsaƙon da ya tura yafi sau ba adadi kamar haka. "Aslm mai kike yi har yanzu ba ki dawo ba,na gaya miki kar ki ƙara mintuna a gidan na maza ki dawo.Da fatan za ki bi umurnina a matsayina na mijin ki n wucin gadi." Tun da ta ƙaranta sau ɗaya ba ta ƙara gigin ƙara karanta wa ba,duk da tsaƙon yana shigowa duk bayan mintuna. Da siririyar sallama ta shigo wanda idanun A.m yana kallon ƙofar shigowa.Karab suka haɗa ido ya yi sauri ya ɗauke kan sa,sai ya ɗan ture jikin Zainab ya miƙe da sauri zai haye sama. Zainab da sauri ta kalli bakin ƙofa ta kuma mai da idanunta kan A.m da ya miƙe yana danna waya zai haye sama. " Honey ina za ka je." Ba tare da ya kalle ta ba ya ce." Ba shopping kika ce zan kai ki ba?Ina son na watsa ruwa zafi nake ji."Ya faɗa ba tare da ya kalle ya ba. Hannun sa ta kama ta riƙe tana sakin mi shi lallausar murmushi. Tare nake son mu yi jirani just one minute." Ta juya kan Juwairiya dake tsaye kamar sanda tana kallon su."Sannu mara mutunci Mamar ta ki mutuwa ta yi da kika je kika zauna?" Juwairiya da take jin gabaki ɗaya ranta babu daɗi ,ba ta tanka mata ba sai ajiyar zuciya da ta sauke,na alamun wacce ta ci kuka ta ƙoshi. " Ke ni za ki kawo wa rashin mutunci banza yar matsiyata ki kula in kika ce hauka za ki yi mini,wallahi sai in kashe ki in kashe banza,na ga uban da zai tsaya miki.Ai ni duk wanda ya shiga gonata saina raba sa da rayuwarsa,kuma mu zuba mu gani shege ka fasa." Ka sa ce mata komai ta yi ta saci kallon A.m da ya jingina jikinsa da kujerar dinning har yanzu,danne-danne yake a wayarsa ba tare ya tanka ko kallon ɗaya daga cikin su ba. " Ni fa zafi nake ji so zan shiga ciki sai kin shigo."Ya faɗa babu ko ɗigon damuwa a ran sa. " Yarinyar nan ta ba ni haushi fa tana sane da kuɗi nake biyan ta,amma ta je gida ta zauna Allah saina cire kuɗina don ba zan yi asara ba."Ta ce tana kallon A.m ko zai ce wani abu. Watsa mata mugun kallo ya yi tare da jan tsuka." Duk abin da za ki yi mata ki ba ƴar aikin ki ba ce,ina ruwana wannan ya rage naki." Yana gama faɗin haka ya haye matakalan bene ba tare da ya kalle ta ba. " Ki yi haƙuri jikin ta ne ya yi tsanani har sai da muka kwanta asibiti k..." "Rufe min baki shashasha." Ta katse ta cikin tsawa. " Da ga yau duk wani aikin gida ya koma kan ki Lantana ba za ta ƙara komai a gidan nan ba,maza ki wuce underwears ɗina sun yi datti ki haɗa da na A.m ki wanke.Ta faɗa tare da kama kunninta sai kuma ta saki ta haye sama. Tun daga wannan ranar take wahalar da ita duk wani aikin gidan ita take yi,dalilin haka ko makaranta ba ta zuwa wani lokaci,domin ƙawayen ta take kwasowa ta saka ta girki,har in za su tafi ta ba su abincin ba sai sun yi girki ba. Wani lokacin sai ta kira ƙawarta ta ce ga za ta turo Juwairiya ta yi kwana biyu ta taya ta aiki.Ga zagi da cin mutunci komai aka yi ita ce. Juwairiya ta yi shiru ne sakamakon tsorata ta da A.m ya yi kan in ta yi gigin tona asiri,zai cutar da Mama sannan ba zai gaya mata in da take ba.Hakan ya sa take jure duk wani cin kashi da take mata. Kusan tsawon lokaci ta yi tana saka ido a tsakanin su haka Lantana ko tari ta yi idanunta na kanta. A.m ya kauda duk wani abu da na zargi da shiga tsakanin su,har faɗa yake ma Juwairiya kamar bai santa ba,kuma kullum cikin sata aiki yake in dai yana gida. Duk wani saka ido ta yi ta gaji daga bisani ta ci gaba da harkokinta dama ta san A.m ba zai taɓa iya kalon ta ba,balle yanzu da duk ta zube ta lalace saboda wahalar aiki da ƙuncin son maso wani da take yi,sai hanci da ta yi gashi kullum sai ta yi mafarkin Mama da Ibrahim. Tafiya ta kama Zainab ba tare da wani shakku ba ta bar ƙasar bayan ta saka Lantana,ta din ga kwana a gidan har ta dawo hakan bai wani ɗaɗa A.m da ƙasa ba ya amince. Cikin dare bayan sun yi bacci A.m yake shaƙa mata Lantana maganin bacci,wanda in ta kwanta sai safiya take farkawa. Sai safiya ta yi ta din ga ƙorafi tana mamakin baccin da take yi ita dai Juwairiya dariya take mata sosai. Juwairiya ta gasganta A.m ƙarshe ne gurin wayo da basira,ita kanta mamakin sa take ga wayo da iya kalami ga mace wanda hakn yake sa ta mutu ƙaunar sa. Zaune suke a cikin makaranta ita da Hauwa Juwairiya ce ta siyo su agwaluma da yalon Bello,tana ta ci tana lumshe idanun ta domin su take son ta ci. Hauwa ta kalle ta ganin yadda take ci kamar wata mayunwaciya. Ganin yadda ta kafe ta da ido sai ta ɓalli agwalumar ta cige baki,saboda tsami amma haka take son sha. " Humh ke ma ka yi mamaki kamar wata mayya haka na tashi ina son na sha agwaluma,bayan ni ba mutuniyata bace saboda tsaminta."Ta ƙara ɓalla tare da lumshe idanunta saboda daɗi. Dariya Hauwa ta saki ta ce."Anya lafiyarki ƙalau kuwa ko dai ciki kika samu?Ni fa ina ganin kamar ciki ne da ke?" Da sauri ta miƙe tare da yar da agwalumar cikin tashin hankali ta zare ido ta ce."Na shiga uku ciki fa da kika ce gaske ne?" " Ina zan sani tunanin haka nake gani a jikinki yau kuma kin zo da baƙon lamari abin da ban taɓa ganin kin sha ba kike sha.To ke ya kamata ki gane yaushe rabon ki da yin ɓatan wata?" Ta tambaye ta ganin yadda ta diririce har hawaye sun fara sintiri a fuskarta. " Umh umh wallahi na manta tashin hankali ba zai barni na tuna ba,amma ina ganin kamar tun ina gidan Mama wayyo Allah na bani!" "Mene ne na banuwa Juwairiya fata za ki yi Allah ya sa wannan cikin ya dasa so tsakanin ki da mahaifinsa." " Tab!Ai wallahi in Zainab za ta iya haihuwa to ni ma zan bar wannan cikin a jikina zubar da shi zan yi ko da zan rasa rayuwata ne,nufin ki na fara irga watannin rabuwa da A.m na koma gurin Mama? Ba zan iya ba domin ban san da wani idon zan iya kallon ta ba."Ta ce cikin kuka. " Haba wai ke mai yasa ba ƙya fahimtar magana da ɗaukar shawara ne! Ki bar cikin jikin ki na tabbata shine makamin da zai jawo kusanci tsakanin sa da mahaifin sa." Hauwa ta faɗa cikin zafi domin zuwa yanzu ta fara ba ta haushi ganin ta cika kafiya da taurin kai. " Na lura ba kya sona so kawai kike na rabu da farin cikina.To sai na zubar da cikin nan kuma babu wanda ya isa ya hana." A zafafe ta furta cikin ɓacin rai tana gani n kamar ba ta son zaman ta da A.m. " Ni ban ce ba ina baƙin cikin yadda kika ɗauki so kika ba ma namiji wai shin shine kaɗai namiji a duniya,na tabbata ko rabuwa kuka yi za ki samu namiji mai kyau ki aura,ke ma ki na da kyau." Miƙewa ta yi tare da ɗaukar takaddun ta."In har za ki taimakamin na zubar ki zo ki raka ni asibiti,in kuma ba za ki ba ai na san hanya." Ta nufi hanyar fita da sauri Hauwa ta biyo bayan ta duk da ba ta farin ciki da zubda cikin amma babu yadda za ta yi. Likita ya kalle ta cikin mamaki sam ba ta yi kama da mutuniyar banza ba,amma mai ya sa take son ta zubda ciki? Da kuma ya tuna mugu ba shi da kama. " Don Allah likita ka taimaka ka zubda cikin nan ko nawa ne za mu baka." Juwairiya ta faɗa jikinta na rawa ta kwaso duk kuɗin da ke jakanta ta ije a teburin sa. Duk tsoron da take ji na allura haka ta bari ya zumbuɗa mata tana cige baki,sannan ya ɗauko wani magani ya ba ta kan in ta ji ciwo ta sha guda biyu. Tun kafin ta dawo gida take jin wani irin jiri kamar za ta faɗi! Ko da ta dawo gida kwantawa ta yi saboda ciwon da mararta take yi,yayin da ciwon yake ci gaba kamar ana tsira mata allura. A haka ta kwana kamar za ta baƙunci lahira, duk yadda ta so ta ɗauki waya ta kira Hauwa ta gaya mata za ta mutu,saboda Zainab na nan A.m ko kallonta ba zai yi ba,amma ta kasa saboda ciwon mutuwa da take ji. Washegari ko ɗaga ɗan yatsarta ba ta iya wa sunan Allah kawai take faɗi a bakinta da yake motsawa,tana kukan rabuwa da Mama ba tare da sun yi bankwana ba. Jinin dake zuba kamar an buɗe famfo ya sa ta gane mutuwa za ta yi,sai ta fara maimaita kalmar shahada numfashinta na ɗaukewa. Zainab da duku-duku ta fice asibiti saboda a kwai wani bawon Allah da za ta yi mata aiki da misalin biyar da rabi na safe,tun jiya aka so ayi aikin sai dai an kawo shi ta riga tabar asibitin,kuma ƙa'ida ne in har ta koma gida ba ta dawowa. A.m dake zaune a falo ya na kallon news mamaki ya kama shi ganin har wannan lokacin ba ta fito ba ta ɗaura abin karya. Miƙewa ya yi tare da saka takalmi ya nufi ɗakinta. Halin da ya ganta ya yi masifar ɗaga mishi hankali,ba tare da wani tunani ba ya taitayeta ya saka a mota ya nufi asibiti da ita. Da ƙyar aka samu aka tsaida jinin bayan cikin ya fita.Hankalin A.m ya tashi gani yake kamar mutuwa za ta yi wani irin tausayin ta ya kama shi,ya na jin bai yi mata adalci zai barta ta mutu a ɗaki. Zura mata ido ya yi cikin tausayi ya na shafa kanta.Da sauri ya kamata ya riƙe tare da tallabota ganin ta buɗe ido. Juwairiya zuciyarta ta buga ganin likita ya shigo riƙe da fayal a hannun sa,tsananin tsoro ya cika mata zuciya don ta san yau a sirinta zai tonu. A hankali A.m ya maida hankalin shi kan likitan da ya miƙa masa fayal,ya ba masa bayani da harshen turanci duk da cewar Bahaushe ne shi. " Ina baka haƙuri na zubewar baby don madam ta yi ɓari ne,har sai da muka yi mata wankin ciki.Ga waɗannan maganin za ka siya an sallame ta." Wani irin tashin hankali ya ziyarce shi riƙe likitan ya yi tare da jijjiga shi." Mai ya sa ka bari cikina ya zuba ka san shekara nawa na yi ina son na haihu?Wallahi sai kun dawo min da cikina don ba zai yiwu ba!" A.m ya faɗa ya na naɗe hannun riga zai yi dabbe gani yake kamar gazawar su ya sa cikin ya fita. " Am sorry wallahi bamu da hannu a cikin zubewar cikin na nan! Amma na yi mamakin yadda kake son kaga ka haihu matar ka ta iya zubda cikin dake jikinta,don bincike ya nuna mana magani tasha mai ƙarfi har cikin ya fita." Sai A.m ya kalle shi kamar mahaukaci ko bai fahimci mai yake nufi ba,ya kuma juya ya kalli Juwairiya wacce ta bayyana gaskiyar zargin da yake mata,saboda yadda ta yi tsuru-tsuru na rashin gaskiya.Wani irin shaƙa ya kai mata cikin tashin hankali. Zainab da ke tafe a cikin motar ta tana tuƙi cikin tsananin nishaɗi,sakamakon ta yi aiki cikin nasara wanda hakan yake saka ta tsananin farin ciki a duk lokacin da ta yi aiki. Wayarta ta ɗauka ta kira layin A.m amma har ta yi masa kira biyar bai ɗauka ba. Ko da ta iso haka kawai sai ta ji gabanta ya faɗi. Maigadi ya wangame mata get ta shiga ta yi parking da sauri ta shige ciki,saboda yunwa take ji matuƙa.Da fari ta so ta fara cin abinci amma sai ta ga rashin dacewar hakan ta shige wanka. Bayan ta fito tana ɗan dube-dube a cikin dirowar gadonta sai ta ga wani magani an ɓoye shi a cikin dirowar. Da sauri ta buɗe gabanta ne ya buga dam! Sa'ilin da ta ga sunan dake manne a kwalin maganin. " Maganin ɗaukar ciki da wuri."Ta maimaita sunan maganin da Hausa. " Me A.m yake yi da shi bayan ni ba na haihuwa?" Tambayar da ta yi ma kanta kenan amma ba ta da amsarta. Wayarsa ta gani duka uku a gida bai ɗauki ko ɗaya ba sannan ba shi a gidan. Juwairiya sunan da ya faɗo mata a rai kenan ta saki wani irin ƙara,da sauri ta sauko har tana faɗi ta mulmulo amma ba ta kula ba. Wayam babu ita sai wayarta dake yashe a kan gado.Da sauri ta ɗauki wayar duk da ta san a halin da take ciki ba za ta iya karanta komai ba. TO FA ƘARA! ƘARA!! ƘARA !!! KU CI GABA DA BIBIYAR LINTAFIN DON JIN YADDA ZA TA KAYA A CIKIN LINTAFIN NAN MAI FARIN JINI. BARI NA TUNA MUKU DA SUNAN SHI SAKACINA KO HALIN MAZA TAKU JAMILA LAWAL ZANGO JAMCY Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 27* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM Ta na riƙe da wayar cikin tsananin tashin hankali yayin da jiri yake iban ta da ƙyar take iya buɗe ƙwayar idanunta. Sai dai duk iya iyakan ƙoƙarinta don ta gano pattern ɗin da ta saka wayar,amma ta kasa har ta haƙura za ta kwaɗa wayar da ƙasa sai kuma ta fasa,ta ƙara kwatantawa sau biyu cikin ikon Allah a na biyun wayar ta buɗe. Bincike ta fara yi a wayar wanda iya yinta ba ta ga wani abu da zai dasa mata zargi ba,saboda Juwairiya ta adana duk wani abin da ya shafi A.m a cikin wayar ta ɓoye shi. Ta yi nufin ta ije wayar sai kuma wata dubara ta faɗo mata ta danna numbobin A.m. Tana fara danna numbobin sai ga numbar A.m ta fito ɓaro-ɓaro an yi saving ɗinta da rubutun larabci,wanda iya ƙwaƙwanta ta yi ta gane mai sunan yake nufi,amma ta kasa saboda rubutun babu wasulla,ga shi karatun arabin na ta an yi ɗan cikin cokali. Durƙushewa ta yi a gurin tare da saka wani gigitaccen ƙara,kamar wata mahaukaciya ta fara rotsa,duk wani kayan ƙawa dake cikin gidan tana ƙunduma ashar. "Wallahi ku dawo gidan nan nice ajalin ku sai na kashe ku duka mundin na gane cin amanata kuke." Gurin mai gadi ta nufa kasancewa yau Lantana ta na hutun ƙarshen mako da take yi. "Kai ina A.m ya yi bayan gida a buɗe sannan Juwairiya ita ma ba ta nan?" Jikin sa ya kama rawa dama tun da yaga Am ya fito da Juwairiya a hannun sa,ya sha mamaki ganin tana matsayin mai aiki ya ɗauko ta. Sai ya ƙara kallonta ya ga yadda ta birkice kamar wacce aka kwanto daga turu, tana zare ido ai ba za a ji mutuwar Sarki a bakin sa ba. " Hajiya ban sani ba da yake na zaga bayi yau na tashi da motsawar ciki."Wani wawan mari ta sakin mishi. " Banza wawa kawai banga amfanin aikin ka ba." Ta juya saboda ba ta cikin yanayin da za ta iya wani dogon magana. ****** A.m da ya shaƙe ta tamkar zai kaita lahira yana jin zai iya kashe ta,saboda tsabar tashin hankalin da yake ciki.Ga baki ɗaya idanun shi sun yi jajur tamkar garwashi wuta,ya canza kalar da ba ta taɓa sanin yana komawa ba. Da ƙyar take kakari saboda wahalar da ta sha,ga kuma A.m yana shirin kaita lahira ba tare da kwananta sun ƙare ba. " Uban me na yi miki da za ki kashe min yaro?Da kuɗina na siye rayuwarki a she ke kike hana ciki ya shiga jikinki? Na rantse yadda kika salwantar min da yaro sai na kashe ki." Juwairiya da take jan numfashi da ƙyar idanunta sun yi gulu-gulu,domin A.m ya yi mata shaƙa ba na wasa ba. Likitan dake tsaye yana kallon A.m da ya zama mahaukacin ƙarfi da yaji,tsoro yake ya matsa kusa da shi kar ya illata shi,amma da ya ga yana shirin kisa,sai ya matsa tare da riƙe shi da ƙarfi ya ce."Ma za ki tashi ki fita don ki ceci rayuwarki." Duk da ba ta jin ƙarfi a jikinta amma haka nan ta ruga,daidai lokacin da A.m ya ture likitan ya faɗi ƙasa ya bugu da bango,ya ɗauki wani ƙarfe dake gefe ya ɗaga zai maka mata. Da sauri ta fice daga ɗakin cikin tashin hankali, tana jin kamar ta sume jikinta babu daɗi,amma ya zama dole ta ceci rayuwarta,don yau ta ƙara tsoron A.m sosai a ranta. A.m da haushi ya ishe shi ganin Juwairiya ta gudu,ya san ko ya duba ta ba zai gan ta ba,saboda asibitin bene ne ga lungunan dake cikin asibitin,ƙarfen da ya yi ninyar maka mata shi ya buga ma likitan,tare da ficewa da sauri yana neman ta. Sai dai ya nemeta sama da ƙasa bai ganta ba ƙara ya saki cikin ƙaraji, ya rantse yau da ya ganta sai ya raba ta da numfashinta,sannan kuma sai ta gaya masa dalilin ta na zubar masa da ciki. Ya kai ma iska naushi cikin takaici yana dunƙule hannun sa,ji yake kamar ita yake duka.Allah ne kawai ya taimake ta da ta gudu da yau sai dai wata ba ita ba. " Wayyo Allah dama ina haihuwa da gaske zan iya haihuwa?" Ya daɗe a gurin yana ganin kamar za ta fito daga ƙarshe ya shiga motar sa,wanda Allah ne kawai ya sa ya iso gida. Sai dai yana shiga cikin gidan ya tsaya cikin tsoro ganin an yi ma gidan kaca-kaca,komai na gidan an fasa hatta tv dake manne plasma duk ta yi raga-raga da su. Ko da ya shiga cikin ɗakin sa sai ya gwammace gara ɓarnar falo da ta yi akan na cikin ɗakin,saboda duk wani takaddu na shi na amfani sai da ta yaga su ta yi mi shi ɓarna sosai. Tsayawa ya yi da mamaki yana kallon ta tsoro ma ta ba shi,ganin yadda ta wargaza gashin kanta ta zama kamar wata mahaukaciya. Tashin hankalin da yake ciki yasa ya kasa tambayarta abin da yake faruwa,duk da zargi da yake yi akan ta gane komai. Zainab ta ƙaraso gurin sa cikin tashin hankali,ta shaƙe shi idanunta sun canza kala,tsabar kishi cike a idanunta ji take kamar ta kashe shi,kawai ta huta domin ya cuce ta. " Munafuki azzalimi mayaudari yau Allah ya tona asirin ka,dama amanata kuke ci kamar yadda Lantana ta faɗa min ka ƙarya ta? A.m ɗanka kake son ya fito ta zina ?Ba na haihuwa mai ya haɗa ka da maganin ɗaukar ciki da wuri." Duk da cewar ya ji maganar ta dake shi amma sai ya sauke ajiyar zuciya da ya tsaya iya nan ta sani. " Zainab ki fahimce ni wallahi ba na zina kuma ba zan taɓa yi..." "Rufe min baki mazinaci kawai? Yau Allah ya tona asirin ka na gama yadda da kai.Ni da ba haihuwa nake ba,in fact ba ni da mahaifar da zan ɗau ciki kake shan ƙwayoyin ɗaukar ciki da wuri." Ta ja numfashi da sauke nauyayyar a jiyar zuciya,tana gumurzun kuka gaba ki ɗaya ta fita hankalin ta. A.m da ya rasa abin yi ƙarasawa kusa da ita ya yi yakai hannu zai taɓa ta,da sauri ta janye jikinta tana mishi wani wulaƙantaccen kallo. " Ni Allah ya tsare ni na ƙara barin ka taɓa ni da hannun zina ai..." " Zainab!" Ya katseta cikin ƙaraji sannan ya nuna ta da ɗan yatsa." Kar ki ƙara kirana da mazinaci in ba haka ba jikinki ne zai gaya miki."Ya ce cikin ɓacin rai. " To meye kai in ba mazinaci ba ko fasiƙi kake son na ce maka,wallahi na tsane ka ba na son ko kallon mayaudariyar fuskar ka,dole ka sake ni ba zan zauna da mazinaci ba." Ta ce tare da ƙara cikwikwiye shi sannan ta ɗora da cewa." A.m yar aikina fa kake nema!Na shiga uku Juwairiya ƴar matsiyata mai take da shi wanda ba ni dashi?" Girgiza hannunta yake yi akan ta sake shi,ya fara magana da muryar sa da yake sace mata zuciya,amma sai ta ɗaga mishi hannu dare da daka mishi tsawa,kamar wani ƙaramin yaro tana masa wani mugun kallo. "Sake ni na ce ka bani takadda ta kuma na rantse maka,sai na maida Juwairiya kalar da duk wani ɗa namiji ya ganta ba zai yi sha'awar ta ba.Ai ni ka gama tsara ni da kalamanka na yaudara matsiyaci kawai." Ƙwace jikin shi ya yi yana hararar ta ji yake kamar ya kai mata bugu,ganin ta ƙara masa tashin hankali. " Ki san maganar da za ki gaya mini mijinki ne, ni in har kika ƙara zagina zan miki hukunci,yanzu jikinki zai gaya miki ba tare da na yi nadama ba." Ƙara cakumo shi ta yi ta kama gaban rigar sa ido cikin ido ta ce."Na faɗa kuma abin da ya fi haka zan faɗa banza mai zan yi dakai sake ni na ƙara faɗi mazinaci ƙazami!" Mari ya kai mata amma sai ta goce da sauri tare da fisgo rigar shi,ganin ya na son ya fita a ɗakin ta kama ta sai da dire ta har ƙasa. Duka ya kawo ma hannunta da ƙarfi ta saki jikin shi tare da sakin ƙara,amma kuma sai ta yi kukan kura ta kama shi da dambe. A.m da yake jin zuciyar shi a wuya ba tare da tunani ba,ya shiga jibgar ta kamar ya samu jaka don iya ƙarfin sa yake dukan ta. Da fari ta biye mishi tana kokuwa da shi,amma da ta ji kasheta zai yi,da gudu ta ruga ɗaki ta ɗauko gyale sai gida. A.m ya durƙushe a gurin cikin nadama tare da kai ma bango naushi." Tabbas na gasganta cewa ke ɗin ba alkhairi ba ne a rayuwata!Juwairiya na tsane ki kuma wallahi sai kin yi nadama sosai,don sai na illata rayuwar ki yadda kika sa na doki matata mafi soyuwa a gare ni." Juwairiya da take jin rashin ƙarfin a jikinta,amma haka take gudu don ta tseratar da rayuwar ta,saboda yau ta ƙara gasgantawa A.m ba shi da imani kashe ta zai yi. Hawaye yana zuba a fuskarta da ta tuna irin tashin hankalin da A.m ya shiga,saboda jin ta zubda ciki nan take tsananin nadama ya shige ta sosai. Tsayawa ta yi cikin tashin hankali ta rasa in da za je,gidan Hauwa ya faɗo mata a rai sai ta tari ɗan mashin. Tana shiga ta rungume Hauwa da ta fito daga cikin ɗaki jin muryarta tana kuka. " Juwairiya lafiya mai ya faru?"Ta tambaye ta cikin tashin hankali. " A.m ya yi fushi da ni na shiga uku! Wallahi ya tsane ni baya sona!"Ta ce tare da sakin wani irin kuka. " Don Allah ki daina kuka ki yi mini bayani mai ya faru." Ganin ta kasa magana sai kuka take na fitar hankali. Zaunar da ita ta yi sannan ta ba ta ruwa tasha sosai ta kama hannunta ta riƙe." Don Allah ki gaya min mai ya faru." Zubbur ta miƙe tare da ɗaukar hijabinta.Hauwa ta riƙe mata hannu ta ce." Wai mai ke faruwa ina A.m ki sanar da ni." " Gurin A.m za ni ya yi fushi da ni ya gane na zubda ciki,don Allah ki zo mu je mu bashi haƙuri,wallahi ba zan iya rabuwa babu shi ba,don ina son sa." Da takaici ya ishi Hauwa tsaki ta yi ta kamata tare da zaunar da ita akan kujera." Ba na son shashanci kin san ba kya son ki rabu da shi,kika zubda cikin da yake so?Babu yadda ban yi da ke ba,amma da yake kunnin ƙashi ne dake kika ji ƙi.Na rasa yadda zan yi ba kya jin magana haba ya kamata ki fahimci mai kike yi." Share hawayenta ta yi ta ce." Zan je na ba shi haƙuri ba zan ƙara zubda cikin ba,in dai haka zai saka shi farin ciki,amma ki je ki ba shi haƙuri don Allah." Hauwa ta yi shiru ta na jinjina lamarin domin sam bai yi mata daɗi ba,ta san da ma in dai A.m ya sani gakan zai faru,gara da ya sani ya ɗauki mataki. " Hankalina ya tashi sosai baki ga irin fushin da ya yi ba ,na san cewa ba zai taɓa nema na ba,gashi garin neman gira na rasa rasa ido.Na san ayanzu ya tsane ni ba ya son ganin fuskata. " Rashin ɗaukar shawara irin na ki shi ya ja miki,Juwairiya ya kamata ki gane gaskiya.Ni dai yanzu shawarata kar ki ce zaki koma gurin sa saboda ya yi fushi dake mai tsanani." Ta ce tana kallonta da takaicin abin da ta jawo ma kanta,sannan ta ci gaba da cewa."Yanzu kin ga ba ki da lafiya ki ci abinci kisha magani,ni na san da zarar A.m ya huce zai neme ki don lamarin ku sai ku." Ta faɗa tare da miƙewa ta nufi kicin bayan ta rufe ƙofarta da key,saboda a take-taken ta za ta iya fita ta je gurinsa. A.m ya daɗe a ɗakin yana zaune tamkar mutum-mutumi,gaba ki ɗaya ran sa ya ɓace da abin da ya faru,duk sai ya ɗauki laifin komai ya ɗora akan Juwairiya. Wayar sa ya fara dubawa don ba zai ce ga in da take ba.Sai dai ya gwammace dama faɗuwa ta yi kan yadda ya ga Zainab ta mai da wayar.Sai ya ɗauki key ɗin mota ya fice gidan A.k. A.k na kwance a falonsa yana ya ɗora yaron sa a kan ruwan cikinsa yana mishi wasa. A birkice ya shigo fuskar sa babu walwala ji yake kamar ya ɗora hannu aka ya yi ta ihu. Zama ya yi ba tare da ya tanka ma Matar A.k da ke tsokanar shi ba,ganin haka sai ta ja bakinta ta tsuke. A.k ya matso kusa da shi tare da dafa kafaɗun sa." Lafiya mai ya faru."Shiru ya yi zuciyarsa kamar za ta ƙone sai tafarfasa. "Mu je cikin falonka ina cikin matsala A.k wallahi na rantse da zan ga Juwairiya ni ne a jalinta."Ya faɗa da ƙarfi cikin ɓacin rai. Da sauri ya ja shi suka shige falonsa har da saka key. A.k da ya yi shiru kamar ruwa ya cinye shi cikin tsananin mamaki yake kallon sa,domin lamarin ya girgiza shi. " Yanzu kana nufin Juwairiya ba ta gidan,ina ta tafi na san dai ba za ta je gidan Baba Sani ba,sannan Zainab ta yi yaji yanzu lamari ya ɓace." A.m ya yi ƙuta ya ce." Ina zan san in da take wallahi yarinyar nan ta ɓata min lissafi komai ya rikice,ban san wace hanya zan bi na shawo kan Zey,don ta yi fushi sosai,in da Allah ya taimake ni ba ta gane ta yi ɓari ba,saboda ba ta tuhume ni akan haka ba.Ina ji ina gani ta yi min asarar babyna abin da na daɗe ina nema." Sai ga hawaye shar a fuskar sa ya na jin tsananin baƙin cikin asarar da tayi masa. Wayar A.k ya fara ringing da sauri A.k ya kalle shi ya ce." Daddy ne yake kira kuma ina ga kai yake nema tun da kace Zainab ta fasa wayar ka." Gaban A.m ya faɗi da ido ya nuna masa da ya ɗaga wayar. A.k ya danna wurin amsawa tare da saka sifikar wayar. " Ina abokin ka yake dama ya fara hauka ne?Ƴar mutane zai daka kamar ya samu jaka,maza ka taho da shi zaku gane baku da wayo tun da kai ba za ka iya ba shi shawara na gari ba." Ɗif Daddy ya kashe wayar ba tare da ya ji mai A.k zai ce ba,don ya san suna tare da A.m. Shiru suka yi kamar ruwa ya cinye su ko tari babu wanda ya iya yi. A.k ya kalle sa da takaici yana gani duk shi ya janyo komai,haba ka auri mace ka ije wa matar ka,amatsayin ƴar aiki abin ya yi muni kuma babu tausayi a ciki. " Lamarin mata haƙuri ake yi sai haƙur in ka ce dukan mace zaka din ga yi,to ya zaka yi duk ranar da ka haɗa mata uku ko huɗu?" " Allah ya kyauta ya kuma tsare ni da tara mata uku,ko ita Juwairiya rabuwa da ita zan yi,zuciyata ba ta son wata ƴa mace sai Zainab."Dariya A.m ya yi suka fice. Daddy ya yi faɗa kamar zai ari baki yana ta huci ji yake kamar ya rufe shi da duka. "Saboda baka da hankali sai ka kama mace da duka goto-goto da kai.To wallahi maza ka je ka dawo da Zainab in ba haka ba za ka fuskanci fushina mai tsanani.Kuma duk ranar da ka ƙara dukan musu ƴar mutane wallahi sai na ɓata maka rai." A.m ya yi shiru yanzu yake tsananin dana sani da ya duke ta. Ko da ya shiga shashin mahaifiyar sa ranta ya ɓace matuƙa ta yi mishi tatas!Akan ya je ya dawo da Zainab.A.k yake ta bada haƙuri. Daddy ya yi mishi faɗa sosai ya ƙara masa da hadisan monzon Allah da nasiha,sannan ya ba shi umurnin ya je ya dawo da ita. Miƙewa suka yi kai tsaye gidan su Zainab suka nufa.A.m gabansa na ta faɗuwa don ya san ba za su kwashe ta daidai ba. Jefi-jefi yana kallon hanya yana jin matsanancin ɓacin rai,in ya tuna da Juwairiya sai ya ja tsaki da ƙarfi ya kauda kan sa,daga ƙarshe ya ɗauki laifin komai ya ɗora akan Zainab don ita ta bada ƙofa har ta shigo rayuwar su. Maigadi ya wangale ƙofa da alamun wani zai fita daga cikin gidan don ko hon ba su yi ba,Daddy Zainab ya fito da shiri makullin mota riƙe a hannun sa zai fita,ganin su ya sa ya tsaya yana musu wani irin wulaƙantaccen kallo. Ya rantse da ace A.m ba ɗan amininsa ba ne yau kotu za ta raba su da shi,tun da har ya iya dukan masa ƴa guda tsoka ɗaya a miya. " Mara mutunci uban mai ya kawo ka gidana ko ka zo ka ƙara dukanta a gabana ne? Ashe dama ba ka da mutunci na ɗauki abu mafi soyuwa na ba ka?" Masifa yake musu bai bari sun shiga daga ciki ba ya shiga zagin su har da A.k da ya yi rakiyan,sai da ya samu na shi kason saboda mahaifin Zainab ya yi fushi,bakinsa har kumfa yake saboda an bugi shalele. A.k haƙuri yake badawa har da duƙawa ya kuma janyo hannun A.m,don ya duƙa da ya yi ƙikam ya na tsaye,zuciyar sa na tafarfasa jin rashin mutuncin da yake musu,a gaban ƴan aikin gidan. Da ƙyar ya basu izinin shiga cikin falon baƙi suka zauna kusan awa babu wanda ya bi ta kan su. Tsalam mahaifiyar Zainab ta shigo cikin falon tana kallon A.m a wulaƙance. " Sannu isashshe da za ka kama min ƴata da duka,an ce maka jaka na aura maka? Na rantse Zainab ba za ta dawo gidan ka ba,tun da ba ka da mutunci. Mai take amfana da shi da auren ka sai tsiya da haƙuri na rashin haihuwa da ba ka yi,shine saboda kai mara mutunci ne za ka kama min ita da duka akan wata banza ƴar aiki,to wallahi ba ka isa ba don ba za ta dawo gidan ka ba. Shekarar ku nawa da aure ko ɓatan wata ba ta taɓa yi ba,dole ka sakin mini ƴata ko kutu ta raba mu."Ta faɗi tana harare-harare. Duk irin rarrashin da A.k ya yi musu amma sun kafe kan ba za ta koma gidan sa ba,sai nanata maganar haƙurin da take yi saboda rashi haihuwar da baya yi. Cikin fushi A.m ya miƙe yayin da idanun sa suka kaɗa suka yi jajur. Ya buɗe baki zai yi magana da sauri A.m ya kama shi suka fice waje.Hannun sa ya ja zuwa mota ba tare da ya ce komai ba,ya shiga motar suka fara tafiya.Ganin yadda yake huci sai ya kunna ƙira'ar alkur'ani. Suna tafe babu wanda ya yi magana sai zuwa can A.k ya kalli A.m ya ci gaba da tuƙi.Jingina kan shi da kujera tare da lumshe idanun sa. A lokacin da A.k ya shigo cikin falon A.m riƙe baki ya yi cikin tashin hankali yana kallon yadda falon ya hargitse babu mamora a falon " Taɓ sai ka tanadar mata wasu ka ije saboda duk ranar da ta san da igiyar auren ka da Juwairiya,wallahi in babu kayan da za ta fasa sai dai wani Abdurrahman ba kai ba,lallai Zainab na da zafin kishi."Ya faɗa cikin tsigar mamaki da tsokana. A.m da ran sa a ɓace ya kalle sa da takaici ya ce." Fata ma kake min ko so kake na rasa wani shashin na jikina,ni kaina yau na ƙara tsorata da lamarin ta,dole na ɗauki mataki kafin ta san da wannan zancan in dai ba so kake na koma tafiya da ƙafa ɗaya ba." Dariya A.k ya yi sosai ya ce." Wannan ya rage naka ni dai babu ruwana tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwa kan duka,kuma wanda bai ji bari ba ai ya ji hoho." A.m ya matsa kusa da shi ya gallah masa harara."Ni ba wannan ba yanzu ya zamu yi da waɗannan marasa mutuncin gaskiya bazan iya zama ni kaɗai a cikin gidan nan ba,ni da nake da zuƙa zuƙan ƴan mata biyu yanzu na koma babu ko ɗaya.Gashi yaunwa make ji wunin yau ko ruwa ban saka a bakina,saboda matsalar da damuwata ta saka ni." " Ya rage naka sai ka san in da zaka je kaci abinci amma ba'a gidana ba,don matata ba kukun ka ba ne,ko da ka ga ada ina baka abinci saboda babu wanda zai baka ne,amma yanzu tun da a kwai Juwairiya sai ka je ka yi biko."Tsaki ya saki take fuskar sa ta canza. " Na rantse har yanzu ina kan bakana sai na hukunta ta za ta san da wane irin namiji take zama,da na je na kirata gara na kwana banci abinci ba."Ya ce da A.k da ya ɗauki makullin motar sa. " Ok fine ya rage naka da na yi tunanin za ka yi bikon matar wucin gadi,ka huta kafin matar so ta dawo,saboda iyayenta sun yi fushi sosai kuma dole sai ka danne zuciyar ka akan duk abin da iyayenta za su yi maka,ƴar su kake aure kuma kai ka dakar musu ƴa." " Na ji don Alkah ka tafi babu abin da kake yi sai ƙara tafarfasa min zuciya,da na so na gaya ma mahaifiyarta magana amma kuma na gode da ka hana ni da na yi katoɓara." " Ok bari na tafi tun da ba za ka dawo da matar wucin gadi ba,sai ka ci gaba da cin abincin Lantana,sannan kar ka yi gigin zuwan min gida mai mata biyu ya zama gwauro." Ya ce yayin da A.m ya fito don ya raka shi ba tare da ya bashi amsar shaƙiyancin da yake mishi ba. Ya shiga cikin mota ya zauna tare da riƙe sitiyarin ya kalli A.m da yake riƙe da murfin motar yana jiran ya shiga,ya rufe mishi ƙofar motan. " Ya kamata ka yi tunani A.m lokaci yana wucewa lamura canzawa,suke yi ka sanar da iyayen Zainab komai ka bayyana Juwairiya a matsayin matar k,tun kafin lamura su kwaɓe maka.Na tabbata da kai ne ba ka haihuwa Zainab ba za ta zauna da kai ba." Rufe mishi motar ya yi ganin ya shigar da ƙafafunsa ciki,saboda fahimta da ya yi maganar da yake masa ba ta tasiri a zuciyar sa. " Na riga na yi wa Zainab alƙawari ina sonta ba zan iya haɗata da wata ƴa mace ba.Na san cewa Juwairiya na sona sai dai ba ta san irin namijin da ya kamata ta so ba,duba ga ni ba ajin aurenta ba ne kuma babban goro ai sai magogin ƙarfe!Don haka ina kan baka na." A.k ya ja motar sa ya fice ba tare da ya ƙara ce masa komai ba. Zainab zaune a ɗaki ita da ƙawarta Nabila suna hira,wacce ta yi takakkiya ta taho Zariya tun daga Abuja,saboda kiranta da ta yi tana kuka ta gaya mata abin da ya faru. Nabila da ta gaji ta ɗauko gajiyar hanya tana zaune akan gadon Zainab abinci take ci. Wayar Zainab ta yi ƙara kusan sau goma na kiran ta,amma sai taƙi ɗaga wayar daga ƙarshe kashe wayar ta yi ta wurgata can gefe a fili ta furta. " Maye kawai mazinaci." Ko da ba ta gaya mata ba ta san wanda yake kiranta. " Yanzu kin tabbata abin da na ke gaya miki ko kin yadda namiji buhun ƙaya ne? Wai ki gaya min ta ya akai kika gane suna cin amanarki?" Zainab ta saki tsaki ta kalle ta da ɓacin rai ta ce." Ni ba wannan ba ina acid ɗin da nace ki taho min da shi?" " Karki damu tsaƙon ki yana ije a jakata amma don Allah ki gaya mini,ya akai kika gane bayan duk kin ɗana musu tarko sun tsallake?" "Wani magani na tsinta a cikin drower ta A.m ya na sha na ɗaukar ciki da wuri." Ta ce cikin damuwa yayin da idanunta suka kawo ruwa. " In yana shan maganin haihuwa to meye hujjarki ko kina tunanin,A.m zai so ya haifi ɗansa ta zina bayan ga matar sa ta sunna?Sannan ni ban ga abin da kika faɗa a matsayin shedar suna cin amanar ki ba." Ta faɗa da tana kallon Zainab da ta yi tsuru-tsuru ta manta cewar,ba ta taɓa gaya ma kowa ba cewar ita ce ba ta haihuwa,sai ta shiga in da in da daga ƙarshe hannunta ta kama tare da fashewa da kuka cikin kuka ta ce " Yau zan gaya miki wani sirri amma don Allah ko sauran ƙawayen, ba na son ki gaya musu cewar na gaya miki ni ce bana haihuwa ba A.m ba,domin ya yi min alƙawarin ba zai faɗa wa kowa ba kuma ba zai ƙara aure ba." Gwalalo idanu ta yi cikin mamaki jin abin da ta faɗi da gaske ita ce ba ta haihuwa ba A.m ba. Sai tsananin mamaki ya kamata ta shiga kaɗa kai kamar wata ƙadangaruwa zuwa can ta nisa ta ce." Har yanzu wannan ba hujja ba ce Zainab saboda wataƙila A.m ya na shan ƙwayoyin ne don yana tunanin ƙila ƙwayoyin Zai taimaka miki." "Haba akan me za ki ce haka bayan na gaya miki cewar mahaifata aka yi min aiki aka cire.Kuma idan haka ne mai yasa ka bai gaya min ba"Ta faɗa cikin ƙosawa jin bin da ta ce. " Wannan ma ba hujja ba ce har yanzu ba ki da hujja Zainab.Kina abu kamar ba likita ba bayan kin manta mahaifa takan tiƙo a jikin mace ko da an cire ta,mata nawa ne suka haihu bayan a n cire musu mahaifa?.Musamman ke da baki taɓa haihuwa ba." " Wayyo Allah kin sani a ruɗu in kin ce duk wannan ba hujja ba ce,to numbar A.m da na gani a wayarta shi kuma mene ne?"Ta ce da ita tana kuka sosai. " Ba zan ɓata bakina gurin faɗa miki irin son da nake masa ba.Na roƙe ki kamar yadda kika yi min alƙawarin za ki watsa mata acid ki taimake ni ki yi yadda muka shirya,ga bayanin in da take gidan kawunta wanda na samu labarin mahaifiyarta ta ɓata." "Ok tun da haka kike so zan yi amma na so a ce mun ɗan ƙara lokaci,mu samu ƙwararan sheda, yau ɗin nan zan cika aikin ki na koma Abuja bari na gama cin abincin.Niƙabi zan saka na watsa ma shegiya ki huta. BARI NA YI NAN DON YAU BANI DA TACE WA LAMARIN YAFI ƘARFINA. KU CI GABA DA BIBIYAR LINTAFIN DON JIN YADDA ZA TA KAYA A CIKIN LINTAFIN NAN MAI FARIN JINI. BARI NA TUNA MUKU DA SUNAN SHI SAKACINA KO HALIN MAZA TAKU JAMILA LAWAL ZANGO JAMCY Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 28* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM Zainab dake shatatan hawaye ta karɓi acid ɗin da ta miƙa mata,tana jin wani irin tsanar Juwairiya a ranta kamar ta je ta watsa mata da kanta. Ganin Momy suka yi ta shigo tana murmushi a fuskarata ta zauna a gefen su. " Humh ta yaro kyau take yi ba ta ƙarko." Ta ce tare da dafa kafaɗar Zainab da har yanzu take ɗigar hawaye,saboda gani take kamar a mafarki yake faruwa,ba ta taɓa tunanin fuskantar haka da ga gare shi ba. Ajiyar zuciya mai ƙarfi ta saka tare da rungume Momy sai ta ƙara fashewa da kuka. " Momy har yau na kasa yadda cewa A.m zai iya kula wata mace bayan ni,mace mara aji wanda ba ta da daraja a duniya duk cewar zargi nake yi amma in na tuna,sai na ji kamar na shaƙe kaina na mutu." Cikin kuka ta faɗa da shagwaba gaba ki ɗaya ta haye jikin Momy tana shagwaba,sannan ta ɗora da cewa. " Ke sheda ce irin wahalar da na sha kafin ya amince da soyayyata! Yanzu sai wata aba wacce ban ɗauke ta da ƙima ba ta shiga tsakanimu.Abin da ya yi min na ji na haƙura da shi amma fa babu macen da za ta raɓe shi,face na zama ajalin ta." "Na sani ba sai kin ɓata bakinki ba amm ni bana goyon baya akan acid ɗin da zaku watsa mata,saboda in har da gaske yake son ta zai iya yin komai don ta samu lafiya daga ƙarshe kin ga ke kika rasa,amma da za ki bar komai a hannuna da sannu za ta gane kuskuren shigowa rayuwarki da ta yi sa..." " Momy yanzu kina nufin na fasa watsa mata acid ɗin?" Ta katse ta da tambaya tana magana da muryar kuka. " Abin da nake so kenan in har zai yiwu kar ki manta ke ce ƴata ɗaya tilo da na mallaka, ta ya ya za ai na bar rayuwarki ta ƙuntata ki bar min komai a hannuna,mijinki kuwa sai ya gane bashi da hankali don wahalar da shi za muyi ki ƙyale shi,zai gane ba irin ki ake wulaƙanta wa ba." " Ai ni da nace ba zan kona gidan sa ba kawai ya sakeni na haƙura da shi."Ta ce cikin shagwaba tare da riƙe hannunta. " Ba ki da hankali mijinki za ki bar ma wata banza ƴar aiki? Ashe kishinki na banza ne tun da har za ki hau dokin zuciya ki kyale ma wata mijinki." " Wannan karon Nabila ce ta karɓe maganar da cewa." Momy ya kamata ta fahimci waye mijinta sannan kin san Zainab da baƙin kishi,ni har yanzu na kasa gane gaskiyar lamarin dake faruwa,amma ya kamata ta gwara A.m ta nisan ta kanta da shi har sai ya gane kuransa. Zainab cikin zumɓura baki ta ce." Ki bar shi da ni yake yi ba Anty Safna za ta tafi ingila ita da mijinta ba,bin ta zan yi na huta acan ba zan dawo ba sai na huta." Nabila da mamaki ta kalle ta ta ce." Ki bar shi da ƴar aikin na ki Zey?" " A''a na san cewa tun ranar da abin ya faru zai kore ta, so nake na gwara shi kin san yana masifar sona dole hankalin sa ya tashi." Dariya ta yi ta ce." Haka ne ai bai kyauta ba amma yanzu Momy zuwana bai da amfani an fasa watsa mata acid ɗin?" " Ƙwarai kuwa Nabila ku bar min komai a hannuna ita Zainab ta fita waje ta huta kafin muga abin da zai faru." Haka kuwa aka yi washegari Nabila ta koma Abuja. A ranar da su A.m suka yi nasara Zainab ta fito musu sun ga rashin mutunci,don tun A k na saka baki yana ba ta haƙuri ta dawo,har ya gaji ya koma gefe yana kallon A.m da ya yi kalar tausayi,kamar zai yi kuka yana roƙonta. Cikin muryar sanyi ya ce." Ki fahimce ni tun lokacin da muka je ƙasar waje aka yi miki aiki,na tambayi likita ya ba ni wannan maganin tunanina ko za ki iya haihuwa." Kallon mayaudari ta yi masa ba tare da ta tanka masa ba,domin gani take ya ci uwar rainin wayo. " Allah ki yadda da ni don Allah ki dawo ɗakina zuciya da gangar jiki sun yi kewarki." Ya faɗa a raunane kamar zai yi kuka tare da kama hannunta. Fisge hannunta ta yi ta harare shi tare da yatsina fuska." Ai ka gama tsarani wallahi gara ma ka fita harkata,domin zuwa gobe in sha Allahu na bar ƙasar nan ba zan dawo ba saina huta iya son raina."Ta ce da shi tana kallon sa a yatsine Wannan karon murya a ɗage ya fara magana." Kar ki sake ki fita wata ƙasa don ba da izinina ba,kuma in kika sake kika je Allah saina ɓata miki rai" " Ai kin banza kawai a suwa ai ni yanzu duk abin da ka zaɓa a aurenmu daidai ne in ba rabuwa za mu yi na fi son haka,da na zauna da fasiƙi wanda ba shi da aji ya rasa macen da zai kula sai ƴar aiki.." " Ya ishe ki Zainab sau nawa zan gaya miki babu wani abu da ya shiga tsaƙaninmu da ita kin ƙi bani dama na yi miki bayani,ban taɓa kallonta da nufin wani abu ba don ni ban ga abin da zan nema ajikinta ba,kar ki manta yawo take a cikin hijabi kamar wata ƙonanniya.Yarinyar da ba ta da waye wa mai zan yi da ita...." Zainab tsaki ta yi ta wuce kawai gani zai tsarata ya bita kamar zai shige cikin ɗakin ya na faɗin." Na gaya miki kar ki bar ƙasar nan ba tare da izinina ba." Garam ta kulle ƙofar saura kaɗan ta haɗa da hannun shi da ya kai da nufin ya kamo ta ganin za ta shige. Bango ya kaima duka tare da kama kan sa ya riƙe. A.k da ke zaune hankalin sa na kan waya amma a zahirin gaskiya yana jin badaƙalar da suke yi ne,mamakin aminin na sa yake yi saboda ya saki da yawa Zainab ta raina shi sama ba ta ganin darajar shi balle ta girmama auren su. Ganin ya nufi hanyar fita ya miƙe cikin ƙosawa shi kansa ya gaji da zuwa biko,yana ji a ran sa ba zai ƙara rako shi ba don ya gaji da ruwan rashin mutuncin da yake kwankwaɗa daga gurin Zainab da iyayenta. A mota suna tafiya shiru A.m ya yi ƙuta ya kalli A.k da hankalin sa ya na kan tuƙi ya ce." Ka na jin wannan yar rainin wayon ko,wai wata ƙasa za ta!Zainab ta raina ni matuƙa ban san yadda zan yi da ita ba,amma in dai ta yi gigin fita waje Allah sai na hukuntata." Shiru A.k ya yi ba tare da ya tanka mishi ba yana tuƙin sa a ran sa cewa ya yi." Kamar da gaske zai iya." Ƙaramin tsaki ya yi ganin haka sai A.m ya kama bakin sa ya yi shiru bai ƙara cewa komai ba,don maganar da yake masa kame-kame ne lamarin Zainab yana ba shi haushi sosai. " Har yanzu ban ji kayi maganar Juwairiya ba."A.k ya faɗa ba tare da ya kalle shi ba. " Shiru ya yi ba tare da ya tanka ba duk da ya ɗan daina jin zafin ta amma har yanzu yana jin haushin asarar da ta yi mishi. " Ka rabu da ni da wannan shiriritacciyar ina maganar matar so wake ta matar shige,sai ka bari na gama da wanda zuciyata take muradi ba wata can ba." Tuki A.k ya ci gaba da yi ba tare da ya tanka a bin da ya ce ba a ran sa shika ɗai ya san me yake tunani. Juwairiya riƙe da waya a hannunta suna kokuwa da Hauwa da ta rantse ba za ta kira shi ba. " Hauwa ki taimake ni don Allah kada ki sa zuciyata ta fashe! Na san har yanzu A.m yana fushi da ni ne haƙurin zan ba shi." Wani mugun kallo ta sakin mata ta ce." Wai ke ba ki da aji ne? Shi ya sa ya raina ki ya ke wulaƙantaki,Allah ya halicci mace da daraja mai girma a gurin ɗa namiji in kika ba shi lokaci da kan sa zai kira ki,don haka ba zan ba da wayata ba." " Wayata tana gidan sa babu ta in da zai kira shi kuma na san cewa ba zai taɓa kirana ba,ko sau ɗaya ki bani na kira shi don Allah." Ta faɗa tare da marairaice fuska hawaye a kan ƙuncinta. " Bari na tura masa da tsaƙon haƙuri daga gareki in har yana buƙatar ya kira ki zai neme ki,amma ba zan bari ki kira shi ba nuna son da kike masa ya yi yawa shi yasa yake gasa miki gyaɗa a hannu. Sai ta koma ta zauna ta zabga tagumi da kalar tausayi har hanzu hawaye na turereniya a fuskarata. Yanayin da ta yi sai ya ba Hauwa dariya da takaici. Wayar ta ɗauka ganin taƙi cin abincin da ta ije musu ta faɗa kogon tunani. Tsaƙon haƙuri ta tura masa da basu wuce kalmomi biyar ba ta ije wayar. A.m dake kwance a kan makeken gadon sa da yake jin faɗin sa ya kai faɗin duniya.Filo ya jawo ya rungume da tare da jan tsaki. Tsananin ɓacin rai yake ɗauke da shi saboda ya ya je gidan su Zainab ta bar ƙasar. Da ƙyar ya iya dawowa gida ya kwanta yana jin wani irin zafi a ran sa.Tun ranar da tsaƙon ban haƙuri ya shigo daga Juwairiya wanda yau kwana biyar da shigowa, bai ko karanta da kyau ba balle ya tura reply wani irin haushinta yake ji da yanzu ya fara irga ranakun da zai zama Daddy. Wayar sa ta yi ringing har sau uku sai a na huɗun ya ɗauka a kasalance ba tare da ya tanka ba. " Ban yi tunanin za ka amsa kirana ba balle ka ɗauka."Muryar Baba Sani ta daki kunnin sa. Da hargowa ya ja tsaki da takaicin ƙin duba wayar da bai yi ba ya ɗauka,wanda hakan ya kasance ne saboda baya son ya kalli wayar lokacin da kiran ya shigo. " Ban san kai ba ne da babu abin da zai saka na amsa wayar,mara mutunci mai ya sa ka kira wayata?" " Na kan yi mamaki in ka yi min wannan tambayar Juwairiya da take gidan ka irin mangwaro ce ka samo ka shuka ta fito,da kake tambaya ta dalilin kiran ka." Shiru A m ya yi masa a yanayin da yake baya buƙatar tashin hankalin Baba Sani don yana shakkun shi sosai. " Na so na zo da kaina amma dana tuna baka da mutunci,kuma ka yi min gargaɗi sai na dana tsufana,gudun kar na mutu da ƙafa ɗaya sanin baka da mutunci,kuma sam baka girmama na gaba da kai. "Fine gara da ka yi ma kanka ƙiyamullaini ƙaƙi zuwa in da nake da sai ka raina kan ka wallahi."A.m ya ce ran shi a ɓace. " Ƴar ɗan'uwana na biyo naji ba'asi A k ya zo nemanta jiya."Gabansa ne ya faɗi ya yi shiru bai tanka ba,amma tsoro fal a zuciyar sa ya manta Mama ba ta gari,kwata-kwata bai yi tunanin in da za ta je ba,saboda haushin da ta ba shi ko tunanin halin da take ciki bai yi ba. " Na ji ka yi shiru ne ko ka ɓatar mini da ita ka san fa ita ɗin dukiya ta ce,so ka kiyaye don wallahi zan iya shuka rashin mutuncin da baka taɓa tunanin in da shi ba." " Har a kwai wani rashin mutuncin da za ka yi min da zai firgita ni bayan san baka da mutunci gabaki ɗaya rayuwarka,a tsiya za ka ƙare don baka gaji arzikiba garyar matsiyata." Dariya Baba Sani ya saki jin abin da ya faɗa sai ya ba shi amsa da. " Ashe masu arziki zasu zama matsiyata don in ka yi gigin ɓatar da ita saina zaman maka ƙadangaren baƙin tulu,don haka ka kula ba ni da mutunci kai ma sheda ne." A.m da ran shi ya ƙara ɓaci matuka kaɗa kan sa ya yi sannan ya ba shi amsa" Kama ta ya yi na zo na kamaka in ji dalilin da ya sa take zubar min da ciki,don na san wataƙila kai kake saka ta kuma wallahi in har na gane da saka hannun ka sai na saka kaf zuriyarku an ɗaure ku."Ya ce da shi ciin ɗaga murya . " To shikenan ɗan Ƙaruna ina jiran ka amma ƙila ni zan fara ɗaure ka,matuƙar ka salwantar min da ƴar ɗan'uwa kuma jarina,wai yaushe kuɗin da ka ba ni zai gama aiki?"Ya canza maganar da sigar tambaya. Da takaici ya kama shi jifa fa wayar ya yi ba tare da ya kashe ba,yana jin dariyar Baba Sani can kuma ya kashe wayar. " Ina ga Juwairiya da tsinannen Babanta Sani su za su yi ajalina." Ko me ya tuna da sauri ya ɗauko wayar da ya yi jifa da ita. Numbar da ta turo masa da tsaƙon haƙuri ya fara bincika duk da bai wani karanta tsaƙon sosai ba. Wayar na ringing tana ƙara tayar masa da zafin dake cikin zuciyar sa. Sau uku ya kira amma ba'a ɗaga ba har ya yanke shawarar ba zai ƙara kira ba,sai kuma ya ji muryar wata mace ta yi sallama. " Ina Juwairiya take." Ya faɗa a gundure da takaicin kiran da ya yi." Ban sani ba kuma in ga wrong number ka yi saboda ban san mai wannan sunnan ba " Ta faɗa da ɗan daga murya dama abin da ta yi ninyar ta yi masa kenan,saboda yanzu matuƙar haushi yake ba ta yana can yana wahalar da kan shi,ga in da ake masa son mutuwa. " Ko da ban san ke wace ce ba kar ki raina min wayo kin san dai abin da ke tsakaninmu ,ba kiran ta na yi don ina so ba,a'a saboda ta ɓata mini kuma sai na nuna mata kuren ta."Ya ce da Hauwa ran sa a ɓace. " Ok kai da ka santa kake wannan maganar amma na yi maka bayanin ban san ta ba balle na sa abin da ya haɗa ku." Hauwa haushi yake ba ta ji take kamar ta kama shi ta yi masa shegen duka saboda irin mutanen nan masu gatsali. Ta buɗe baki za ta yi magana ji ta yi an fisge wayar Juwairiya ce daga bayan ta wacce ta shiga bayi a she ba ta san ta fito ba. Jikinta har rawa yake lokacin da ta kanga wayar a kunninta tare da fashewa da kuka. " Hello don Allah ka yi haƙuri ka yafe min wallahi ba zan ƙara ba zuciyata za ta fashe na rashin ka a kusa da ita k..."Wata uwar tsawa ya daka mata. " Ban kira ki don ki gaya min tsoki buruku ba kin ji na rantse kar ki bari mu haɗe dake don sai kin raina kanki.Gidan uban wa kike Baba Sani ya kira ni ya ce min ba ki a gidan sa?Da auren kike gantali ni dama na san ƴan iskan ƙawaye kika yi da su suke zuga ki,to makarantar ma na daƙile tun da baki san mutunci ba kuma na rantse miki za ki fuskanci fushina mai tsanani." " Don Allah ka yi haƙuri ka yafe min na yi kuskure ba zan ƙara ba." Hauwa ce ta fara kiciniyar fisge wayar da ta yi mata kyakykyawar riƙo. "Dole A.m ya din ga wulaƙanta ki haba kamar ba mace ba duk kin zubar da ajin ki ya raina ki an faɗa miki so hauka ne haka ake nuna ma masoyi ?" Duk yadda ta so ta karɓe wayar ta ƙi bata,har duƙawa ta yi tana ba shi haƙuri yayin da idanunta ke zubar da hawaye. " Gidan ƙawata Hauwa Tukur." Ta bashi amsa har tana in ina garin saurin ta faɗa masa." Minti goma na baki ki dawo gida in ba haka ba za ki fuskanci hushina." A wannan lokacin Hauwa ta ƙarɓe wayar."A.m duk abin da kake yi Allah yana kallon ka,don Allah ya jarabce ka da ƙaunarka sai ka din ga wahalar da ita?Ina jiye maka ranar da Allah zai kama ka a kanta...." " Ke karki kawo min maganar banza matata ce fa kin san irin maƙudan kuɗin da na saka na aure ta?In har na gane ke kike zugata saina ɗaure ki igiya tai rara.Maza ta dawo cikin mitinan da na bata." " Juwairiya ba za ta dawo ba saboda ba ta da lafiya sosai in har ka matsu da ta dawo to ka zo ka ɗauke ta." Ɗif ta kashe wayar cikin ɓacin rai saboda tunanin da take mishi ya wuce wannan. " Haba Hauwa kina gani har sallar dare nake yi don ya kira ni shine za ki ce ba zan koma ba,kin san wannan batsa kika yi don tafiya zan yi."Ta ce cikin murna. "Ki ce dabbe za'a yi a gidan nan na ga wanda zai kada wani ko da ganina kin san ba za ki ibi komai a jikina.Wallahi mugun haushin sa nake ji ya faye son kan da da yawa na, yi baƙin cikin ɗauke Mama da ya yi ita ce kawai za ta iya ƙwatar miki ƴancin ki,don ke baki maida kanki mace ba shi yasa yake gara ki ya na amfani da son da kike masa. A.m da yake jin haushin kiran da ya yi mata yana ta zagaye kamar mai ɗawafi. Ya fi kusan minti talatin yana jiran ta dawo ko ba komai ya rage damuwar abinci da kullum yake fama da yunwa,don ko gidan su ya je babu wanda yake masa tayin abinci,ya san ana yin hakan ne don a hora shi. Wayarsa ya ɗauka yana tsaki ya tura tsaƙo kamar haka. " Turo min da adireshin gidan." A lokacin da tsaƙon ya shigo Hauwa na tsaye ta riƙe Juwairiya ƙam da take son ta fice daga gidan. " Ina tausaya miki Juwairiya ko wani namijin kika aura ba A.m ba za ki sha wahala sosai,na lura baki iya ɓoye so ba in dai kina son mutum su maza ba'a musu haka yayin da suka fahimci mace ma son su wulaƙanci yake biyo wa baya." Hawaye ta share ta kalle ta ta ce." Wataƙila ba ki taɓa soyayya ba ne shi ya sa kike daɗin haka amma son da nake ma A.m irin na in ban same shi ba sai rijiya." " Ina na taɓa so ai kin san auren ƙiyayya na yi da mijina.Ta yi mata gatse sannan ta ɗora da cewa "Ai ko kina ruwa wallahi don ina tausaya miki." Kama hannun Hauwa ta yi ta riƙe sai hawaye shar!"Ki bar ni don Allah na tafi." Kallon ta ta yi tana dariya ta ƙara cewa." To mara aji matar mahaukaci, ya ce na tura masa da adireshin gidan, sai ki kwantar da hankali don na fiki murnar tafiyar ki ko banza yau zan yi bacci lafiya, ba tare da na yi rarrashin kukan da ake min duk dare ba.In kun so sai ku kashe kanku munafukai kawai."Wani irin daɗi ya lulluɓe jin zai zo duk da tana tsoron haɗuwar su amma idanuwanta suna ƙaiƙayin son ganin sa.Yana isowa hon ya shiga yi ba ƙaƙƙautawa. Da gudu ta ruga har tana bige ƙafa da ƙofa amma bata kula ba,ko sallama ba ta yi mata ba sai hannun da ta ɗaga mata. Duk da bugun da zuciyarta take mata amma gaka nan ta yi shahada ta shiga suka zuba ma junan su ido. A.m da yazo da fushi duk sai ya nemi fushin ya rasa musamman da ya ga ta rame kamar wacce ta yi ciwon shekara. Kau da kan sa ya yi ga barin kallon ta ya ɗauki biro ya saka a tsakanin yan yatsun ta ya matse da ƙarfi har sai da ta yi ƴar ƙara saboda zaba. " Kin san irin girman laifin da kima yi mini?Kin ɓata mini rai ƙwarai kuma saina miki horo mai tsanani,na rantse kika ƙara gigin ƙara zubar min da ciki saina illata ki sannan jikina ba zai yi wahala ba sai kin mayar da abinnda kika zubar. Ƙaryar iskanci kike ba ki san waye ni ba muje gidan za ki ga abin da zai faru dake." Tsananin tsoro ya cika mata zuciya ganin irin muguntar da ya yi masa,sai ta ji tsoron kar yazo ba kowa a gidan ya kashe ta a banza,saboda har yau tana tuna irin shaƙar da ya yi mata. Ganin fuskar sa babu fara'a hankalinta ya ƙara tashi. " Ka yi haƙuri na gane kuskure na insha Allahu ba zan ƙara ba kuma na yi hakan ne..." " Ban tambaye ki dogon surutu ba in har kina son na yi haƙuri to ki ƙoƙarta ki mayar da abin da kika yi mini asarar shi a yau." Ya faɗa ba tare da ya kalle ta ba hankalin sa na kan tuƙin da yake yi. Yanayin yadda ya ya nuna mata hankalinta ya ɗan kwanta,domin ta yi tunanin fuskantar haka daga gare sa,ta ɗauka dukan mutuwa zai yi mata kuma ya kore ta. Tun da ya faɗi wannan maganar bai ƙara cewa uffan fa har suka iso gida lokacin a na kiran sallar isha'i,don haka parking kawai ya yi ya fice masallaci. Ajiyar zuciya ta saki mai ƙarfi tana ƙare ma gidan kallo wanda rabon ta da wata biyu kenan Da ta tuna Zainab sai da gabanta ya faɗi ras! Duk da ta san ba ta gidan shi ya sa ya je ya ɗauko ta,a ranta take tunanin ko ta yi tafiya zuwa waje. Bayan ya shigo tana zaune a falon gidan sai ƙare wa falon kallo take saboda ganin ya canza,kallonta ya yi sai kuma ya ɗauke kan sa zai haye sama. Da sauri ta riƙe hannun shi." Don Allah ka yi haƙuri ka yafe min wallahi na tuba kuma na yi nadama." Hararar ta ya yi tare da galla mata tsaki ya janye hannun sa sai kawai ta faɗa jikinsa tana kuka sosai. " Ke fa matsala ce ta ko ina bayan asarar da kika yi min kukan banza za ki rarrashe ni da shi ko?Kawai zan haƙura ne in har kin yi alƙawarin yau za ki mayar min da asarar da kika yi min."Ya faɗa cikin wata irin murya. Ɗago kanta ta yi tana share hawaye ta kalle shi sai kuma kunyar abin da ya faɗi ya sa ta sunne kanta tana murmushi. " Yunwa nake ji ƙwarai kin korar min matar so,sai ki maye makwafin ta kafin ta gama hutun ta dawo,sai ki yi ƙoƙarin mai da asarar da kika yi mini don ba zan wahalar da kaina ba. Da sauri ta tashi ta ƙwalalo masa ido tana dariya sai kuma ta nufi kicin,wanda dama kafin ta yi alwala sai da ta ɗora masa abu mai sauƙi wanda zai ci,don ita yau murna ba zai barta ta ci komai ba. Mamaki ta yi da ta ga ya biyota kicin ɗin duk da ƙorafin abin da ta yi masa yake yi,da kuma yi mata gargaɗin kar ta ƙara sai ta ji sanyi sosai a ranta ,saboda yana da saurin fushi zai kuma iya yanke komai ba tare da tunani ba,amma kuma yana da saurin sauka. Ba ƙaramin mamaki ta yi ba da ya nuna mata shifa da gaske ita za ta mai da asarar da ta yi masa Hakan ya sa ta dage sosai don ta faranta masa saboda ya manta komai.Daga ƙarshe da kan sa ya karɓi jagoranci komai,saboda bai san ya yi missing ɗinta alot haka,a haka bacci ya yi ya kasheta da ƙaunar sa da take sakata hauka a kan sa,sai ya fake da duk a cikin horo yake mata wanda so yake ya maida asarar da ta yi masa. Sai da suka makara sallar asuba ita ce ta farka ta zare jikinta sannan ta tashe ki,kan dole a gida ya yi sallah,ya kuma sawa suka koma bacci. Ba su tashi ba sai misalin sha biyu na rana kiran wayar da A.k yake yi ya tashe shi. Tsaki ya saki zai kashe wayar sai dai da sauri ya miƙe ganin kira rututu a wayarsa,da ya kalli agogo salati ya fara yana ɗan buga bayanta ganin sha biyu har ta gota. Miƙe wa ta yi ita dama tuni ta farka ba ta so ta farkar da shi ne,ya sa ta ci gaba da kwanciya amma yunwa take ji matuƙa. " Hello hala yau mutuwa ka yi ne ana ta kiran waya ka san muna da baƙi sai ka zo ka buɗe mini falon ka ina waje baƙi na ta jira. Da sauri A.m ya sauka ƙasa shaf ya manta da client din sa da za su zo yau yana faɗin." Ki sauko ki bani abinci mai sauƙi fita zan yi." A.k ya dogare a bakin ƙofa yana kallon sa ganin sa da kayan bacci." Wai hala rashin matan na ka ya sa ka fara shaye-shaye ne? Haba bacci har sha biyu da ƴan mintina sai ka ce wanda ya yi sabon aure. Shafa kansa ya yi ya ce." Kai fa banza ne bari na watsa ruwa mu tafi." Yana ƙoƙarin hawa Juwairiya ta fito da nufin ta shiga kicin ta ɗora girki kanta a sunkuye ta gaishe da A.k da ya yi tsaye yana kallon Am da yake shafa kansa. " Kai amma ka ci uwar ɗan rainin wayo ka bar ni ina can ina ta neman ta,Baba Sani ya tasa ni a gaba ashe kana nan ka na cin amarci har da makara." Tsaki ya yi ya harare shi daidai lokacin da ta shige kicin ya sausauta murya ya ce."Nima ganinta na yi ta dawo." Ya na taɓe baki ya yi maganar ya ɗauki remote ya kunna tv bari na yi sauri na watsa ruwa ka rage zama. " Allah ya yi munafuki anan ka yi sauri ka fito kai ka sani da gulmarka." Dariya ya yi ya bugi bayansa." Da babu ai gara ba daɗi."Ya ce tare da haye wa sama. Kusan sati biyu tun da Zainab ta tafi Lantana ba ta zoba,sakamakon yarta da take aure ta haihu an yi mata aiki ta tafi jinya.Hakan ya ba su damar sakewa suna jutawar su. Kullum ranar duniya sai A.m ya kira Zainab amma ba za ta ɗaga ba, kuma yana ta biko gurin iyayenta,sai wulaƙanci suke masa daga ƙarshe mahaifinta da kan sa ya kira Daddy A.m a kan ya daina zuwa gidan shi Zainab sai ta huta za ta dawo.Da zarar ta dawo za ta dawo ɗakinta don haka ya daina damunsa. A.m ya yi fushi sosai sai ya yi zuciya ya ƙyaleta musamman da ga matar wucin gadi,ta dage tana faranta masa ko ba komai zai yi maleji kafin ta dawo. Juwairiya ta yi amfani da wannan damar ta saka rayuwarta a cikin ta A.m duk da irin gwasaleta da yake yi, yana yabon Zainab amma da ya fita zai kira ta yana gaya mata ya yi missing hawayenta na banza don Allah ta yi mishi kukan zai siya. In ya faɗi haka dariya take mishi ta ce ashe kukan banza ya ƙara matsayi tun da har siye ake son ayi.Haka dai suke zaman su cikin girmama juna da kulawa. Washegari Zainab ta kira lantana aka ta je ta gyara mata gidan ta,saboda tun da ta tafi kewar sa ya dame ta ko bacci kasa yi take yi,duk kiran da yake mata rungume wayar take yi tana kuka,amma shegen girman kai ya hana ta ɗaukar wayar in ta tuna kuma da abin da ya yi mata sai ta ji duniyar ya yi mata zafi.Ita tunanin ta A.m zai biyo ta ƙasar ne. Sai dai tana tunanin yadda za ta iya danne zuciyarta,ta zauna da Juwairiya bayan ta gane amanarta suke ci,duk da A.m ya yi mata rantsuwar yana shan magani ne saboda ita, amma kuma bai ƙaryata numbarsa a wayar Juwairiya ba,sai dai ya nuna sam bai san zancen ba wataƙila son sa take don kwanaki ana kiran sa da baƙuwar numba,bai dai taɓa ɗagawa ba ne shi yasa bai fahimci komai ba. Zainab ta gane sam ba za ta iya rayuwa babu shi ba,amma dole ta canza zaman su domin sai ya gane kuran sa,ita kuwa Juwairiya Momi ta ce ta bar lamarinta a hannunta don sai ta yaba wa aya zaƙinta. Lantana ta shigo gidan da mamakin ƙofar a buɗe duk da ta ga motar A.m a gidan,amma ta san ba' abarin ƙofar falon a buɗe. Tura ƙofar ta yi ta shigo tana ƙarema gidan kallo yadda yake tashi da ƙamshi da gyara komai tsaf,jikinta ya bata a kwai mace a gidan. Tsaye ta yi tana ɗan tunani sai kawai taga Juwairiya ta rugo da gudu daga sama tana dariya,jikinta daga ita sai yar bes fara da wando fari tirikwata wa da A.m ya siyo mata da suka fita,saboda shi yana koyi da hadisin ma'aiki wanda yake mana koyi da saka fararen kaya. Da gudu take saukowa tana dariya shi kuma ya biyo ta cakulkuli yake mata wai kan dole sai ta yi mishi kuka yaga hawayen banza. Kamar yadda Lantana ta yi tsuman tsaye tana kallon su haka suma suka zuba mata ido cikin firgici. TO FA NIMA IDANU NA ZUBA MUSU TARE DA BASU LOKACI DOMIN NA GA REACTION ƊIN SU KU CI GABA DA BIBIYAR LINTAFIN DON JIN YADDA ZA TA KAYA A CIKIN LINTAFIN NAN MAI FARIN JINI. BARI NA TUNA MUKU DA SUNAN SHI SAKACINA KO HALIN MAZA TAKU JAMILA LAWAL ZANGO JAMCY Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 29* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM Juwairiya kunya ta kama ta matuƙar gaske ji ta yi kamar ta nutse a ƙasa,juwaya ta yi za ta koma ciki,amma sai A.m ya janyo ta tare da haɗa ta da ƙirjin shi. " Ke! Wace irin mahaukaciya ce da za ki shigo gidan ma'aurata kai tsaye sai ka ce ɗakin gidan ku." "Lantana jikinta ya kama rawa kamar mazari saboda tsawar da ya daka mata,ta yi mugun firgita ba ta gane abin da ya ce ba. " Ka yi haƙuri yallaɓai wallahi ban san ka na ciki ba,kuma Hajiya Zainab ta ce na zo na gyara gidan za ta dawo." Ta faɗa jikinta na rawa kanta na asa ta na mamakin abin da ta gani don ta firgita. A.m ya yi farin ciki sosai jin abin da ta ce sai ya ɗan ture ta daga jikinsa,ya kalli Lantana da har yanzu idanunta a ƙasa suke,ba ta son ta ƙara ganin abin da ta gani,domin ƙila ƙarya suke mata. " Ok sai ki je ki yi aikin ki munafuka na sha mamaki da Zainab ta tunume ni akan ina tare da Juwairiya,a she ke ce munafukar da take son raba aure. Wallahi kin ji na rantse miki in har kika yi gigin faɗa mata abin da idanun ki suka gani,kaf ƴan gidan ku ni ne ajalin su don bom zan siya na tashi gidan." Ware idanunta ta yi tsananin tsoron sa ya kamata saboda idanun sa sun tabbatar mata da zai yi fiye da haka. " Ba ke kin iya munafunci ba to bari na ƙara miki da abin da zai kashe ki,don ba za ki iya faɗa mata ba duk munafuncin ki saboda in ban kashe ki ba,to ita za ta yi ajalin ki kin ga gulma ta yi riba kenan." Ya ce da ita ya na zare mata ido domin haushi take ba shi,tun da ya ji ita ta faɗa mata komai,ga shi yanzu ta korar masa da matar so. "Juwairiya matata ce wanda na aura a bisa wasu dalilai da ba zan gaya miki ba,saboda bai shafe ki ba." Ya ƙara matse ta sosai a jikin sa kiss ya sakin mata a kumatunta,ya na mata wani irin kallo da ya saka ta kauda idanunta saboda kunyar Lantana. " Kin ga in ta dawo sai ki gaya ba mata yau ƙin ƙara gani ba kuma iyakan runguma ba,ki sanar mata duk abin da kika gani kar ki rage." Lantana da sauri ta shige kicin tare da rufe ƙofar. " Innalillahi na shiga uku!" Ta sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi yayin da kanta ya kulle ta rasa in da za ta fara tunani. " Wallahi wannan mutumin ya rikita ni na rasa mai zan fara tunanin,a halin yanzu zuciyata ba za ta iya fahimtar komai ba,domin ya saka ni a cikin ruɗu."Ta ce yayin da ta ɗora hannu akanta. " Da gaske ya ke faɗin matar sa ce ita?A 'a lamarin nan a kwai rikitarwa! Ji fa yadda ta koma tamkar wata gilas,saboda tsabar kyau kai Zainab shashashar mace ce,wai ta je hutu ai kuwa ki dawo za ki ga sakamakon hutu." " Wa ni ai komai na ga kuna yi ba zan iya gigin gaya mata ba,haka kawai ku da holewa ni da shan bugu.Kai amma fa A.m ƙarshe ne gurin rashin mutunci don ko kaɗan Zainab ba ta yi tunanin ta na gidan ba." Irin maganar da take yi a zuciyarta kenan ta buɗe ƙofar a hankali ta na leƙen su,sai ta ga sun ƙara rugawa da gudu sun yi ciki. " Allah ya kai mu ki dawo gidan nan za mu sha kallo!Allah ya sa kar ki yi shigowar dare in ba ma idanuna abinci,sai ki gane sakaci kika yi ko halin maza A.m yake nuna miki."Ta faɗa sannan ta kama aikinta zuciyarta cinkushe da tunani kala-kala. Bini-bini za ta leƙa ta na kallon sama amma sai ta ji shuru kamar bacci suka yi. " Ha ina tausayin ki yarinya ba ri Zainab ta dawo."Ta ce ta na aiki cikin mamakin lamari da al'ajabi. " Humh namiji bunun ƙaya." Abin da take ta nanatawa kenan a cikin zuciyarta. A.m ya rungume hannun shi ya na kallonta da ta kwanta akan cinyar shi,ta ɗora filo a ƙirjinta idanunta lumshe kamar ta na bacci,sai dai a zahirin gaskiya ba bacci take yi ba. Zuciyarta cinkushe da kishi da tunani jin Zainab za ta dawo,domin a yadda take jin son sa da kishin ta ba za ta iya ɓoye kanta ba,kamar yadda ta yi a farko ta na jin ko sama da ƙasa za su haɗe za ta nuna kanta a wannan karon. Kamar yadda take tunani shi ma haka zuciyar sa take cinkushe da tunani,ga shi ya gagara samo mafita. Duk da cewa zuciya da gangar jiki sun yi kewar Zainab,amma in ya tuna za ta dawo gaban sa yake wani irin yankewa ya faɗi. Ya sani a yanzu babu wanda zai kalle ta yabce ita yar aiki ce,duba ga yadda ta koma tamkar wata tarwaɗa. Ya na ta tunanin ko ya ɗauke ta daga gidan sai dai ya na jin ba zai iya jure rashin abincinta ba,saboda har yanzu ya kasa iya cin abincin Lantana. Wayarsa ya zaro ya gwada wayar Zainab da ya daina kira,saboda ƙin ɗauka da take yi. Sai dai ringing ɗaya ya ji ta amsa tare da sakin kuka. " Ka daina sona A.m ban taɓa tunanin a kwai ranar da zan yi fushi da kai ka ƙyale ni ba." Ta amsa daga ɓangarenta ta na wani irin kuka da yake tafarfasa masa zuciya. Tsam Juwairiya tamiƙe daga jikin sa ta fice daga ɗakin ba tare da ta kalle shi ba,yayin da zuciyarta ke mata luguden bugu na kishin sa. Binta da kallo ya yi ganin ta canza kalar fuskarta kamar ba wacce ya sani ba. Sai da ta fice daga ɗakin ya saukar da nauyayyar ajiyar zuciya. " Ya kike son na yi kin mai da ni kamar wani ƙwallo don kawai kin ga Allah ya jarabce ni da son ki?Kawai na ba ki dama kije duk abin da kika yi ninya ki yi,ni dai har yanzu ba zan fasa gaya miki ina sonki ba." Ya ce da ita ya na jin tsananin haushinta da kuma fargabar abin da zai faru,domin ya na ji a jikin sa kamar lokaci ya yi da zai gaya mata zaman Juwairiya a gidan su,don su daina samun saɓani,duk da ya san zai sha wahala kafin ta amince. " In har ka na sona da gaske A.m ka daina kawo rigima a cikin aurenmu,sannan ka tuna da alƙawarin da ka yi min don Allah karka canza." Shiru ya yi bai ce komai ba ya rufe bakin sa da hannun sa ya na jin saukar kukan da take yi. " Ka yi shiru ba ka ce min komai."Ta faɗa cikin muryar kuka. " Mai kike son na ce miki Zainab wane irin halacci ne ban yi miki ba! Ki dawo a kwai wata magana mahimmanciya wace za mu tautauna,kuma in kika fahimce ni in sha Allahu ba za mu ƙara samun tarnaƙi a aurenmu b." " A.m a kwai matsala ne don Allah ka faɗa min?" Ta tambaye shi da zaƙuwa jin muryar sa ta canza." Babu kuma kar maganar da na ce miki za mu yi ya ɗaga hankalinki domin alkhairi ce." " Ok to shikenan baby ba matsala,amma fa ka canza gabaki ɗaya,domin da ace babu wata matsala cewa za ka yi in jira ka mu taho tare."Ta ce da shi da wata kalar murya. " Wataƙila da izinana kika tafi?" Ya ce da ita a ƙufule kawai sai ta ji ya datse wayar, a lokacin da take faɗin. " Tun da ba za ka zo ba sai ƙarshen za mu dawo,saboda zamu tsaya mu yi siyayya." Miƙewa akan gadon ya yi tare da shafa gemun sa da ya ƙawata masa fuska. Wani irin damuwa ya ji ya lulluɓe shi sosai. " Gaskiya na canza shawara ina ganin kawai zan ɓoye Juwairiya duk san da ta samu ciki,sai na saka Zainab ta yi cikin ƙarya a zuwan ita take da ciki in ta haihu ɗan ya zama Zainab a zuwan ita ce ta haihu." Take ya amince da shawarar sai ya miƙe da sauri ya saka takalmin sa ya fice zuwa ɗakinta. Ta na tsaye a gaban mirrow ta juya bayanta tare da ɗan jingina kanta da gefen mirrow,a ranta ita kaɗai ta san mai take tunani,domin iya tsananin damuwar dake kan fuskarta na hango.Ba tare da ta san ya shigo ba ya fara magana. Kallon sa take yi da wani irin canji a fuskarta har ya gama mata bayani,ba ta tanka ba illa kallon sa da take kamar baƙo a gare ta. Ganin ba ta da ninyar magana sai ya saki tsaki ya juya ya na faɗin." Ina fatan kin ji mai na ce." Ko kaɗan A.m bai canza mata ba wai don Zainab za ta dawo,haushin da take ba shi duk ya yi mata maganar abin da ya tsara sai ta yi shiru ta zamar masa kamar wata kurma. Zaune suke a falo sun dawo daga siyayya A.m ya ce ta raka shi a kwai turaren da yake son ya siya. Sun zaune a falon ƙasa sun baje kayan ciye-ciye suna ci Turaren da ya siyo ya na son ya yi haɗa da wanda yake shafawa,saboda turaren ya tafi da imanin sa gashi ba zai iya canza wanda yake fesawa ba. A hannunta ya kama ya fesa mata a hannun ya ce." Matar shige ki ji ƙamshin sa ya yi daɗi ko?" Juwairiya har ga Allah ƙamshin bai yi mata ba,kallon sa ta yi ta ɓata fuska tare da toshe hanci." Humh ni ban ji wani ƙamshin daɗi ba don ni warin almiski ya yi mini,kuma ni ba na son almiski." " Allah ko ka ji gulma wannan turaren ko shugwaban ƙasa ya shaƙi ƙamshin sa ba zai kushe ba,balle ke ni na san gulma ce irin ta ki don ko wanda na ke shafawa ba ki taɓa cewa ya na daɗi ba." Dariya ta yi lokacin da ta toshe baki ganin haka sai ya ji haushi sosai ya biyota ya na faɗin." Allah sai na fesa shi a jikin ki duka." Zagaye falon suke yi har ya kamata zai fara fesa mata turaren,yayin da take roƙonsa don har ga Allah bai yi mara ba. Wayar sa da take aljihun wandon sa ta fara ƙara da sauri ya ciro,jin kiɗan da ya saka ma Zainab ce. " Hello gani a airport ka zo ka ɗauke ni." Ya kalli Juwairiya da ta ji abin da Zainab ɗin ta ce saboda ta na jikin sa ya ɗaga wayar. Da ido ya yi mata magana sannan ya ɗauki key ɗin motar sa ya fice. Ta na ganin sa ta faɗa jikin sa tare da sakin kuka sosai." I miss you honey." Da so ya yi ya ture ta ganin irin shigar da ta yi duk da cewar a da in ta yi shiga wani lokacin ya na ƙorafi,amma yau ganin ta da gyale ta yi roling ɗin sa,sai ran sa ya ɓace sosai,domin shi da za ta fara shigar Juwairiya ya na so,saboda ya gane hijabi wani sirri ne da Allah ya bawa mata duba ga jikin Juwairiya da yake mamakin ƙirar sa. Ga mamakin ta sai ta ga ya yi shiru, bai cika magana ba sai kallon hanya da yake yi,hakan bai saka ta damu ba saboda ta yi tunanin ko har yanzu fushi yake yi da ita,duk da cewa ita ya kamata ta ƙi masa magana,amma sanin hali sai ta kama bakinta ta yi shiru. Wayarta ta ɗauko ta yi kiran Momy ta gaya mata jirgin su ya sauka lafiya. Ko da suka isa gida wanka ta shige saboda ta gaji matuƙar gaske,kanta har wani sarawa yake yi saboda ciwo,in da Allah ya taimake ta ta ci abinci a jirgi,so babu abin da za ta nema illa ta yi sallah ta bi lafiyar gado. Ya shigo da dubuwar farar rigar bacci wanda ya ɗaure igiyar ta bayansa,ganin ta kashe fitilar ɗakin ya kunna fitila mara haske. "Zainab ki tashi magana za mu yi kuma mai mahimmanci." Ya ce da ita don yau yake son ya gaya mata komai,gudun kar ta ganta a gidan lamari ya jagule,saboda ya tabbata gobe in ta yi ido biyu da ita,zarginta zai zama gaskiya don ta wuce a kalle ta ace mata ƴar aiki. " Wash Allah na!Haba A.m na gaji fa wallahi kaina ciwo yake yi,komai za ka gaya min ba zan fahimta ba, ka bari zuwa gobe sai ka gaya mini duka fa yanzu na dawo." Ta ce mishi cikin ƙorafi saboda ta san bai wuce ƙorafin abin da ya faru a tsaƙanin su zai yi mata magana ba. Miƙewa ya yi ya koma ɗakinsa ya san tun da ta ambaci sunan sa ba za ta saurare shi ba,dama in dai ta kira sunan shi yayin da suke sa'in sa ba,ba za ta yi abin da yake so ba. Washegari da safe A.m tun da ya yi sallah bai dawo ba,sakamakon ƙanin sa da aka kira shi bashi da lafiya ya na asibiti. Zainab ba ta tashi ba sai kusan ƙarfe da rabi saura minti biyu,wanka ta yi sannan ta yi salla,saboda duk tashin da A.m ya yi mata ba ta tashi ba,gajiya ce sosai a jikinta har zuwa sadda ta tashi ba ta daina jin bacci ba. Wani irin yunwa take ji a daddafe ta yi sallah,sannan ta zira doguwar riga ko hoda ba ta shafa ba ta fito don ta karya,ta san cewa zuwa wannan lokacin Lantana ta kammala abinci. Da ga wanka ta fito bayan ta ɗauki tsawon lokaci ta na dirje jikinta, da yake wani irin haske tamkar zara cikin wata,ita kanta mamakin hasken da ta yi take yi ta san cewa ta na da haske,amma ita ba fara ba ce sai dai yanzu wani irin haske ta ƙara har kusan kashe ido take yi. Duk da ta ɓata lokaci gurin yin kwalliya amma fa ba wata kwalliya ta yi ba,kasancewar ta ba mai irin sha'awar kwalliya irin waɗan da ƴan mata suke yi,su zama tamkar aljanu. Wata doguwar riga ta saka kalar milk amma jikinta an yi mata ado da farin duwatsu,masu kyau don yanayin rigar ya fi kama da na indiyawa. Turaren da ta ɗauka wanda A.m yake shafawa tun da shi ta feshe jikinta da shi,ta na son ƙamshin sa sosai saboda in ta shaƙi ƙamshin sa ji take kamar A.m na kusa da ita,amma wanda ya siyo sam ƙamshin sa bai yi mata ba,har cikin zuciyar ta ta tsani turaren, amma shi gani yake kamar watsa take masa. Juwairiya a yadda ta tsara ma kanta hak za ta fita Zainab ta ganta,don ta na ji a ranta kuma ta rantse ba za taci gaba da ɓoye kanta ga a gurin ba,za ta bayyana na komai kuma duk ta shirya da abin da zai faru. Sai dai kuma yadda ta ga surarta ya fito ba za ta iya fita a haka ba,kasancewar ta mai alkunya da yakana. Ƙaramin hijabi ta ɗauka ta rufe jikinta da shi sannan ta ɗauki sabuwar wayar da A.m ya canza mata mai kyau da tsada,bayan ya gargaɗe ta da kar ta bari kowa ya ga wayar saboda tsadar ta. A lokacin da ta kama murfin ƙofar fita ɗakin sai abin ya mata mamaki,domin ita kanta mamakin kanta take na yadda ta shirya hakan,duk da ta san dala za ta ɗauko ma kanta babu gammo. "Sannu da shigowa Hajiya Zainab barka da dawowa Allah ya ja zamanin ki a gidan A.m." Lantana ta ce mata kamar ta na mata gatsali kamar kirari,amma a zuciyarta dariyar ƙeta take yi don ta san za'a kwashi ƴan kallo. "Lantana ya kai ban ga abinci a dinnig ba ke wace irin shashasha ce,kin san na dawio ko dama haka kike barin mijina da yunwa?" " Allah ya huci zuciyarki Hajiya!Amma ba ni nake girki a gidan nan ba tun da kika tafi"Ta ce cikin sauri saboda ita ta ƙosa ayi ta ta ƙare. " Ban gane ba shi yake yi ko fita yake ya siyo bayan son na ki."Ta tambaye ta da mamaki duk da ta san A.m ya tsani abincinta kamar yadda yake mata ƙorafi. " Ba' a waje yake siyo ba Juwairiya ce take girkawa,amma yau ban san mai ya hana ta fitowa ta girka ba."Tsabar gulma da yake cinta har saurin baki da take yi ta faɗa in ina ta fara. " Juwairiya?" Ta faɗa cikin zare ido don ita ko kaɗan ba ta tunanin ta na gidan ba. " Wayyo Allah na! Uban me yar iskan yarinyar nan take min a gida?Da ma ta na gidan nan ba ta bar gidan ba." Lantana ta matsa daga gefe tare da kare wuyanta ganin ta nufe ta,a ranta addu'a take yi. Buɗe kofar kicin ɗin ta yi ba tare da ta nuna ko ɗar a ranta ba,duk da ta ji hargoguwar Zainab sai dai hakan bai razanata ba. Lokaci guda Zainab ta yi shiru lokacin da ta yi ido biyu da ita. Gabanta ne ya yanke ya faɗi dam!Ganin ta canza mata kamar ba ita ba. Wani irn tashin hankali ya ziyarce ta ba tare da wani tunani ba ,shaƙeta ta yi tare da sakin wani irin kuka. "Ke dan ubanki mai kike yi a gidana?" Juwairiya ta fisge gabar rigarta da ta riƙe ba tare da ta ce mata komai ba, ta nufi gurin gas za ta ɗora abinci,da ba tare da ta ji tsoron ta ba. Lantana kuwa tsalle ta yi gefe jikinta har rawa yake ganin yadda hankalin Zainab ya tashi,duk ta ƙosa a fara ta ga yadda za'a ƙare, a zuciyarta ta so ace munafukin ya na nan,sai ta ga ƙarya da nuna isa ya na faɗa mata matarsa ce. Shaƙeta ta yi sosai kamar za ta kaita lahira ta na faɗin." Wallahi yau sai kin raina wayon ki saina nuna miki kuskuren shiga gonata da kika yi,duk cin mutuncin da kika yi mini ashe ki na nan a gidan kuna cin amanata bari ya dawo haɗaku zan yi na ƙona." A.m dake tafe a mota da sauri har baya ganin gaban sa ya so ace ya na gida uwar haka,sai dai ciwon ya tashi sosai don aiki a ka shiga da shi afendis ke damun sa. Ya na tuƙi amma hannun shi rawa yake yi saboda ya san a wannan lokacin,Zainab ta farka kuma komai zai iya faruwa. Ko da ya iso gida bai yi parking ba ya ije motar tare da rugawa zuwa cikin gidan. Zargin sa ya tabbata daidai saboda tun kafin ya shigo cikin falon,yake jin ƙarar Zainab da hargowa. " Zainab ki bar abin da kike yi ki tsaya zan yi miki bayani."Ya ce da ita don yau ta faru ta ƙare. Wani irin banzan kallo ta yi mishi tare da sakin ƙara." Uban me take mini a gida kalle ta fa A.m sam ba ta yi kama da mai aiki ba,duk tunani na tabar gidan na..." "Wannan dalilin ya sa nake ta son ki ba ni dama na yi miki bayani "Ya katseta ya na faɗin haka. " Bayanin me za ka yi mini buƙata ta kawai ta bar gidan nan." Janye rigarta ta yi da ƙarfi ta ture Zainab daga jikinta cikin tsawa. " Ya ishe ku gabaki ɗayan ku na gaji kuma kar ki ƙara riƙe ni ki na tuhuma ta,saboda matsa..." Wani irin saukar mari ta ji ƙuncinta mai zafi wanda ya saka ta ji jiri ya kwashe ta,ta yi taga-taga za ta faɗi amma ta riƙe drower na kicin ɗin. " Ki iya bakinki kuma ki tsaya a matsayin ki."A.m ya faɗa bayan ya kwasa mata mari. " Ka ƙyale ta ta faɗi abin da za ta faɗa yau sai na wulaƙanta rayuwarki." Juwairiya da ta ji saukar marin har ƙwaƙwalwarta ta rintse idanunta cikin kuka sosai,don yau ta tabbatar A.m ba ya sonta! Munafiki ne mayaudari ne kawai ya na more jikinta ne da mugayan kalamansa da yake yaudarar ta. Ta buɗe baki za ta yi magana sai ƙamshin turaren A.m da ya canza ya daki hancinta,wani irin amai ya taso mata duk yadda ta so ta mai da shi ina ta makara! Da sauri ta ruga zuwa bayi amma tun kafin ta kai ta fara amai tamkar za ta amayar da ƴan hanjinta. Sai Zainab ta din ga kallon A.m da ya tsaya tamkar gunki ta buɗe baki za ta yi magana,ta kasa sai ta ji kamar babu harshen ta a cikin bakinta,yayin da kanta ya ɗaure iya ɗaurewa kuma ya yi mata nauyi,jin kanta take ya yi nauyi, tamkar an yi mata gammo an ɗaura mata duniya da abin da ke cikinta. Matsawa ta yi gurin A.m sai kuma kamar an tsikare ta,ta ruga da gudu cikin ɗakin Juwairiya da take ta sheƙa amai tamkar ba za ta yi rai ba. Allah sarki tsayawa ta yi ta kasa komai kamar jira take ta gama ta fito ta yi mata sannun a yadda ta nuna,amma iya tashin hankali da take ciki ya sa ta yi mutuwar tsaye,har ta kasa banbance wace rayuwa take ciki tsaƙanin ta duniya da lahira. A.m da ya ƙaraso da sauri don bai fahimci wainar da ake toya wa ba,ya yi tunanin ko Zainab ta biyo ta ne da dake ta. Abin tausayi amai take yi tamkar ba za ta daina ba,kuma A.m ya yi mamaki har ta gama amai ta fito bayan ta wanke bakinta,Zainab ba ta tanka ba,sakamakon suman tsaye da ta yi. Wani irin ajiyar zuciya ta saki tare da firgita kamar wacce ta dawo daga doguwar suma. Duk da cewa ita ba likitar mata ba ce,amma a iya zaman ta cikin asibiti ta san yadda ake gane mace mai ciki. Hannu Juwairiya ta kama tare da duba tsakiyar hannun,sannan ta ɗaga ƙwayar idanunta. Gabanta ya buga da sauri sabo da fahimci abin da Zainab take dubawa,lokacin da ta je asibiti ita da Hauwa abin da likitan ya duba kenan ya ce mata ta na da ciki. Sam ba ta yi tunanin ciki ne da ita ba saboda wancan ba ta yi amai ba sai kwaɗayi. " Na shiga uku ya Allah karka saka mafarkin da nake yi ya zama gaskiya!Ka sa na buɗe idanuna tun kafin na aikata abin da duniya za ta yi tur da ni a cikin mafarkin. Juwairiya take da ciki wa ya yi mata?" Ta faɗa cikin ƙaraji tamkar wata zararriya ta na ihu gabaki ɗaya kamanninta ya canza Juwairiya da A.m har ma da Lantana da ta yi laɓe a bakin ƙofa ta na jin mai ke faruwa!Suka haɗa baki gurin faɗin " Cikiiii." Sai kawai na ga Lantana ta hantsila ta yi waje cikin tashin hankali,ba tare da na yi wani tunani ba na bita a guje,saboda ba zan iya ganin wannan badaƙalar ba. KU CI GABA DA BIBIYAR LINTAFIN DON JIN YADDA ZA TA KAYA A CIKIN LINTAFIN NAN MAI FARIN JINI. BARI NA TUNA MUKU DA SUNAN SHI SAKACINA KO HALIN MAZA TAKU JAMILA LAWAL ZANGO JAMCY Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 30* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM Zainab ji ta yi ƙasa ba za ta iya ɗaukar ta ba,ta yi kukan kura sai ta faɗa kan Juwairiya ta ƙara shaƙe mata maƙogaro. " Uban wa ya yi miki ciki da ma ke ƴar iska ce." A.m da sauri ya yi kanta tare da ƙoƙarin ɗaga ta kanta ganin ta na son ta yi mishi illa."Ba ki da hankali ƴar mutane za ki kashe?"Ya ce lokacin da ya ɗaga ta daga jikinta. " Barni da ita wallahi in a kwai abin da yafi kisa zan yi mata! Ta ya ya za ayi tayo ciki ta shigo mini da shi gida." Sai kuma ta ce." A.m don Allah karka sa na haukace ahalin yanzu ji nake kamar numfashi na zai ɗauke!Ka da zargina ya zama gaskiya ka barni na koreta a gidan ta je can ta nemi uban cikinta." " Zainab ki tsaya ki fahimce ni na yi miki bayan..." "Wai mai za ka gaya mini?In dai ba ka na son ka faɗa mini yau ne ranar da fitan numfashina zai yi bankwana da gangar jikina"!To na roƙe ka don Allah ka ƙyale ni.Juwairiya ta fita daga gidan nan shine kawai zai saka na fitar da zargi a cikin zuciyata."Ta ce tana kuka sosai. " Sam ba za ta bar gidan nan ba samun sauƙin ki shine ki fahimci abin da zan gaya miki,domin ba ni da nufin na cutar da ke duk abin da yake faruwa na yi ne don ke." Ja da baya ta fara yi tana mishi wani irin kallo,sai ta kalli ta ta kuma ƙara kallon sa kawai sai ta shaƙe shi. " Na shiga ukuna ni Zainab zuciyata ,za ta buga A.m zai kashe ni,ka da son yara da kake yi don kawai ba na haihuwa ya sa ka naimi Juwairiya ka haihu ta zina! Tur mai za ka yi da ɗan zina kuma ya fito ta jinin matsiyata." Sai kuma ta sake shi ta nufi kanta tana faɗin."Wallahi saina kashe ku iyaye sun danƙaramin dukiya,shine za ku din ga zina akan gadona har ku samu ciki h." " Ya ishe ki Zainab! Kar ki ƙara ai banta min yaro,kin san halina ba zan taɓa aikata zina." Ya buɗe baki zai gaya mata matsayinta sai ya kasa ya sunkuyar da kan shi ƙasa,yayin da tsananin tausayi ya kamasa ganin yadda ta koma kalar tausayi tana kallonsa. " Ki fahimce ni Zey ke san ba zan taɓa haɗa ki da..." " Ba na son ji! Ba na son ji!! Mayaudari munafiki mai alƙawarin banza.Tur da na aureka na yi nadamar ranar da na ce ina sonka,kar ka matso kusa da ni in ba haka ba kashe ka zan yi!" Ta faɗa tana girgiza kanta tare da toshe kunninta ganin ya nufi ta zai riƙe ta. " Wannan dalilin ya sa na yi duk iyakan ƙoƙarina na fahimtar dake." Ya ce da ƙarfi ya na kallonta sannan ya ci gaba da cewa." To tun da ba ki bani dama ba,bari na gaya miki gaskiya..." Katse shi ta yi da ƙarfi tare da ƙara cakume shi ta ce." Mai za ku gaya mini mai kake son kace?Abu ɗaya na sani cewar mijina A.m ya na kwana tare da ƴar aikina,wallahi kaf duniya sai sun ji don a jarida zan buga,A.m ya yi ma ƴar aikina ciki za su haifi ɗan shege ɗan zin." Wani irin shaƙa ya kaima wa da ya sa ta ji numfashinta zai ɗauke. " Kar ki ƙara aibata min ciki ɗan dake cikinta halastacce ne kuma ta aure muka same shi,don ban san ta ba a matsayin ƴa mace ba,sai da aka karɓar min aurenta." Ya zaro idanun sa ganin ba ta fahimci abin da ya faɗa ba." A taƙaice Juwairiya matata ce ta sunna wanda Daddy ya karɓar min aurenta! Don haka karki ƙara aibanta min yaro don wallahi sai kin gane baki da wayo." Kawai gani ya yi ta sulale a ƙasa ta faɗi sumammiya.Da sauri ya yi kanta ya na kiran sunan ta. Gabaki ɗaya ya ruɗe ya rasa ta in da zai fara rungumeta ya yi cikin tashin hankali sunanta kawai yake kira. Da gudu Juwairiya ta shiga kicin ta ibo ruwa ta watsa mata,amma sam ba ta farfaɗo ba jikinta ya yi ɗip kamar babu rai a jikin. " Zainab don Allah kar ki mutu ki barni ba zan iya rayuwa ba,in har babu ke a cikin duniyar nan,ki tashi na yi miki bayanin na aure ta ne don ke,don Allah ki buɗe ido. A.m yake faɗi ya na jijjigata cikin tashin hankali." Ya kamata a kaita asibiti fa kar ta mutu." In ji Lantana da take kallon tashin hankali wanda ba' a saka mishi rana. A.m ya miƙe daidai lokacin da Lantana ta ruga kiran direba,don ya kasa komai sai zare idanu da yake yi. Zubbur ya ga ta miƙe tare da sakin wani irin ƙara wanda sai da gidan ta girgiza,kawai sai ta saki dariya kamar sabon kamu. Wani ihun ta saki da ƙarfi ta yi kansa ta na faɗin." Ƙarya kake yi wallahi ni kaɗai na tashi a gidanmu na rayu ni kaɗai ban taɓa sharing ɗin wani abu ba,sai kai abin da nafi so fiye da komai a rayuwa.Ina hakan ba zai taɓa faruwa ba!" Ta ƙara riƙe shi ƙam ta ci gaba da cewa.Ƙila mafarkinmu duniyar mahaukata ya kawo mu,don na lura kai kanka ba ka san mai kake faɗa ba,don wataƙila baka cikin hayyacin ka." Mari ta kawo mishi cikin zafin nama ya kauce tare da riƙe hannunta,ya zare idanun sa ya ce."Tabbas bari na ƙara gaya miki ita ɗin matata ce,gaskiya kunninki yake gaya miki,kamar yadda igiyar aurena uku yake a kanki,haka ita ma amma ki tsaya ki sauraare ni,kin san ina sonki ba zan yi abin da zai cutar dake ba. na aureta ne don na..." "Kai." Ta daka mishi tsawa da idanunta da suka rine sukai jajur!Saboda tashin hankali. " Karka gaya min maganar banza ka rabu da ni macuci haƙiƙa ka cuce ni,ka kuma yaudareni.Ka manta ka yi min alƙawarin ba za ka taɓa min kishiya ba,balle ka sanar da ni ce ba na haihuwa shi ne yau ka auri wata mace ban sani ba,kuma saboda cin mutunci ka kawo ta gidana ka na kwana da ita a gadon da iyayena suka siyar mini,wallahi mafi girmar kuskuren da ka yi ka kawo ta gidana,ka maida ni banza shashasha sauna! Ashe in bana nan sakewarka kake da ita?Har kana mini munafucin baka riƙe sunann ta ba. Wayyo Allah na! A.m ya maida ni banza ya kawo matarsa gidana a matsayin mai aiki!Wace irin banza ne ni har na kasa gane tsakanin su? Wallahi sai kun yi nadamar abin da kuka yi mini,zan nuna maka cewar da gaske ba a yi ma family ɗinmu kishiya,take yanzu zan kasheka in kashe kaina haka kuma in kasheta!Mutuwar kasko za mu yi daku,ban taɓa sharing ko da wani abu ba balle na haɗa jiki dakai ƙazami kawai." Da gudu ta ruga kicin kafin ya farga har ta ɗauko wuƙa ta yi kansu ta na faɗin." A yanzu za ayi ta taƙare yanzu zamu yi mutuwar kasko,hisabi akan abin da kuka yi mini zan yi muku tun kafin aje lahira ku haɗu da ubangiji,munafuki mai karya alƙawari." " Zainab ki ki natsu karki aikata dana sani! Look Zainab kar ki aikata abin da kike son yi,sheɗan ne yake so ya kaiki ya baro,don Allah ki natsu zan yi miki bayani,ina da dalilin da ya sa na ɓoye miki auran." Kallon mahaukaci take mishi ta tsaita wuƙar daidai gurin Juwairiya tana matsawa kusa da ita. " Saina nuna miki kuskuren da kika yi mijina za ki aura,kin yi babban kuskure ni kaɗai nake rayuwa a gidan mahaifina,haka dangimmu kaf babu wata mace da aka yi wa kishiya sai ni?Wallahi ba ku isa ba,sai na nuna muku kuskurenku." Gadan-gadan ta yi kanta data tsorata ganin ta nufo ta da wuƙar,ɓoyewa ta yi a bayan A.m da hankalin sa ya tashi matuƙa,saboda yadda Zainab ta koma za ta iya yin komai. " Zainab kar ki kashe musu ƴa za ki yi dana sani fa shari'a ba za ta ƙyale ki ba kema kashe ki za'a y." "Don na kashe ƴar matsiyata uban wa zai taɓa ni na san ko an kulle ni Daddy zai fito dani."Ta bashi amsa idanunta a bushe. " To ni in kika kashe min ɗa wallahi saina kulle duk yan gidanku ba ke ba,saboda ko ba komai zan ga ɗana a duniya na rungume shi iyayena su yi alfahari da hakan."Ya ce mata cikin zafi da ɗaga murya. Kukan kura ta yi taho kan kanta da gudu jin abin da ya faɗa,yayin da idanunta suka rufe ba ta ji ba ta gani. " Yadda ba na haihuwa kai ma ba za ka taɓa ganin ɗanka ba,saboda kai na lalata mahaifata,don na faranta maka shine za ka auri wata,wallahi baka isa ba." Da sauri ya cakume ta ya riƙe ƙam iya ƙarfinsa ganin abin da take shirin yi. Juwairiya ta sadaƙar mutuwa za ta yi lokacin da ta yi kanta da wuƙar.Ta rintse idanunta tana salati. Fuɗuwa suka yi a ƙasa ita da shi ya fara kiciniyar karɓe wuƙar. Sai kawai ta kai mishi wukar jikin shi Allah ya ba shi sa'a ya kauce,wuƙar ta yanki hannun sa sosai. Ba Juwairiya kawai ba hatta wanda ta yi yankan sai da ta ɗan firgita ganin irin jini da ya fara tsartuwa a hannun sa. A.m ya kira sunan Allah da ƙarfi ya ji wani irin raɗaɗin azaba yana ziyartar sa,jikin shi ne ya kama rawa ganin duk da yankar da ta yi masa,jini na zuba amma ba ta razana ba,sai ta nufi Juwairiya da ta yi kan sa ta kama hannun sa tana kuka,mai haɗe da salati matuƙar tsoro ya shige ta ganin abin da ta yi. " Ai na gaya muku wallahi sai kun gane kuskuren ku na cuta ta da kuka yi!"Ta faɗa lokacin da ta yi kanta. Da sauri A.m ya miƙe ya saka ƙafafun sa ya taɗiyeta ta faɗi yarab!Amma da ƙarfin hali duk da buguwar da ta yi,sai da ta ƙara nufo ta da wuƙar. Ƙara hankaɗe ta ya yi za ta faɗi ya tare ta bayan wuƙar ya faɗi gefe. Ta saki ihu tana zage-zage kamar wata mahaukaci. Da ƙarfin tuwo ya riƙe ta tare da yin dubara ya sakata a cikin ɗaki,sannan ya jawo ƙofar ya kulle. Wayar sa ya ɗauka ya kira Mominta don ita kaɗai yake tunanin za ta shawo kanta. Zuciyar sa a fusace ya ja hannunta suka fita,a cikin mota ya saka ta sannan ya shiga ya ja. A.m dake tuƙi gabaki ɗaya hankalin sa ya tashi ƙwarai,ko a mafarki bai taɓa tunanin abin da Zainab za ta yi mishi ba,duk da daman ya san zai sha fama da ita. Ya juyo yana tuƙi da bai san in da za shi ba ya kalle ta,sai ya ga ta dunƙule jikinta hawaye yake turereniya a fuskarta,kamar rawar sanyi take yi ganin yadda ta takure lokaci guda. Ya sani cewa ya tono ma kan musamman in iyayen sa suka ji abin da ke faruwa,don ya san Zainab sai ta fallasa komai. Guri ya samu ya samu ya yi parking ba tare da sanin abin da zai yi ba,ya kwantar da kan sa a jikin sitiyarin ɗin. Karo na farko yau ta ga karaya a fuskar shi tun iya rayuwar da suka yi ba ta taɓa ganin abu ya saka jikin shi ya yi sanyi ba,ko da kuwa Baba ne Sani da ta lura ya na matuƙar tsoron shi,amma yana ɓoyewa,sai ya ba ta tausayi sosai. Ta kalli hannunsa da yake tuƙi jini duk ya ɓata in da ya riƙe kuma ya na ta zuba,kawai sai ta saka kuka tare da cire ɗaukwalin da ta ɗaura,ta kama hannun za ta ɗaure. " Asirina ya tonu ko kaɗan ban taɓa tsammanin lamarin zai tafi ta haka ba,ina tsoron mahaifina in ya ji abin da na aikata,Daddy zai yi fushi sosai.Dama haka Zainab take da kishi kai mata basu da tunani wallahi!Duk abin da na yi don na faranta mata ne. " Ina tsoron Daddy in ya jin wanan lamarin ban san abin da zai yi min ba,wataƙila ya tsame ni daga cikin yaran shi." Kamota ya yi ya riƙe da hawaye a fuskar shi ya ce." Ki ba ni shawara na rasa yadda zan yi zuciyata za ta fashe." Kawai sai ta fashe da kuka sosai tana tausayin kanta da shi,don ita kanta tana tsoron ranar da za ta koma gurin Mama. Rungumeta ya yi ƙam yana jin kamar rungumar za ta yi masa maganin damuwar sa. Wani irin hucin zafi ya ji a jikinta da sauri ya matsa gefe yana kallon ta,daidai lokacin da ƙamshin turaren sa ya ƙara taso mata da amai,ta buɗe motar a guje ta fara sheƙa shi. A.m hankalin sa ya tashi sosai ya tsaya yana kallonta ya rasa wani tunani zai yi,gashi ko ruwa babu wanda za ta kuskure bakinta da shi. Sannu yake ta jera mata ya riƙe ta sosai kamar zai mayar da ita jikin shi,sam bai damu da aman da take yi ba. Da ta gama aman ta miƙe sai ta ji jiri ya kamata za ta zube a ƙasa,da sauri ya tare ta ta faɗa jikin shi,bai damu da jinin da ke zuba ba ya riƙe ta sosai da hannun. Mota ya mai da ita sannan ya ja suka wuce asibiti. " Doctor ka fara duba ta da gaske wani cikin ta ƙara samu?" Ya ce da likitan bayan ya zaunar da ita akan kujera. Likitan ya kalle shi ya ga irin jinin dake zuba a hannun sa,sannan ya juya ya kalle ta da ta yi sanyi sosai,ciki mai ilinbo gabaki ɗaya jin wani iri take a jikinta. " Ya kamata na fara duba ka kalli bleading hannun ka yake yi.". "Kar ka damu da ni doctor kawai ka duba ta ina son na sani da gaske na kusa zama uba"A ɗokan ce yake magana.Ya faɗa jin abin da likitan ya ce. " Ok to shikenan bari na kira doctor Garkuwa ya duba ka kar ka fara ganin jiri." " Congratulation ina farin cikin sanar dakai matarka na da ciki sati uku." Sujjada kawai ya ga ya yi sai ya rungume shi yana murna." Ashe nima zan zama Baba! Allah na gode maka." Gurin da take kwance ya nufa ba tare da ya ji kunyar doctor dake tsaye yana kallon sa yana dariya ba,ya bata hot kis bayan ya rungume ta. " Da gaske za ki haifa min Baby?" Dariya doctor ya sannan ya kalle shi ya ce."Aman da ta yi ya ɗan galabaitar da ita so yanzu za mu ba ta rest bed zuwa an jima sai ku tafi,na rubuta muku maganin da zai dakatar da aman." " No doctor a ƙara mata ruwa kawai saboda jikinta ya yi weak ina son yarona ya samu kuzari,kasa ka mata drip kawai ba na son abin da zai cutar da shi,kaga in ba ta da ƙarfi ba zai samu damar ya juya yadda yake so ba." Dariya ya yi sosai ya bugi bayan sa." To fa yau Allah ya haɗani da patient sabon shiga to Allah ya sa madam ta haifi ƴan biyu,amma jikinta ba sai an saka mata ruwa ba,ka ba ta maganin nan da zarar kun je gida. Duk yadda doctor ya yi da shi amma ya kafe sai an yi mata ƙarin ruwa,don kar yaron sa ya wahala,dariya sosai yake masa ganin yaushe akai daren da har gari ya waye yaron da ko gudan jini bai zama. A.m ya ruɗe duk da tashin hankalin da yake ciki amma in ya tuna zai sami baby,sai ya ji ya ɗan rage damuwar shi. Wayar sa ya zaro ya kira A.m akan ya zo asibiti ya same shi. ********* Zainab ta sa saki wani gigintaccen kuka lokacin da Momi ta shigo gidan tana sallama. Ƙofa ta shiga bugawa tana faɗin." Momi ki buɗe ni ina ɗaki ya kulle ni." Jikin Momi ya kama rawa sosai ganin jinin da ya zuba a hannun A.m face-face a falon. " Mai ya saka ya kulle ki lafiya wai mai ke faruwa ne jinin waye a ƙasa?" Ta jero mata tarin tambayoyi cikin tashin hankali. " Faɗawa jikinta ta yi ta saka gigitaccen kuka. " Momi tun da na taso na taɓa neman wani a bu na rasa?Kuma kin taɓa ganin na yi sharing ɗin wani a bu a gidammu,ko da mota ce?" Da sauri ta girgiza mata kai alaman " a'a." To wai Momi A.m yake tare da Juwairiya mai aikina da Lantana ta ba ni labarin suna tare, kuma wai auren ta ya yi har tana da ciki,ya ije ta a gidana suna rayuwar aure." Sai ta saki razanannen kuka tana girgiza kanta. " Ni wallahi gani nake kamar mafarki nake yi! Komai ya canza cikin ƙanƙanin lokaci.Wayyo Allah na!Na shiga uku." Da sauri ta miƙe a zabure." What impossible! Amma wasa kike mini ko?Haba ina ta ya ya za'ai A m ya aikata wannan ɗanyan aikin, bayan ya san ba'a yi wa family ɗinmu kishiya,sannan kika ce ta samu ciki wa ya yi mata,bayan shi baya haihuwa ku..." " Momi ki tsaya ki fahimce ni na san na yi miki laifi ban taɓa gaya ma kowa ba,amma ki yi mini uziri don Allah!" Ƙara miƙewa ta yi a zabure bayan ta gama gaya mata abin da ta ɓoye mata tsawon shekaru. Zaro idanunta ta yi da ƙarfi ta furta." Innalillahi wa inna ilaihir raju'un! Zainab. "Da gaske ne ke ce ba kya haihuwa ba A.m ba?" TSANANIN FIRGITAR DA TA NUNA YA TADA HANKALINA NA IJE RUBUTUN DON NA SAMU NATSUWA. KU CI GABA DA BIBIYAR LINTAFIN DON JIN YADDA ZA TA KAYA A CIKIN LINTAFIN NAN MAI FARIN JINI. BARI NA TUNA MUKU DA SUNAN SHI SAKACINA KO HALIN MAZA TAKU JAMILA LAWAL ZANGO JAMCY Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 31* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM " Momi da gaske ne duk abin da na gaya miki na aikata,tabbas na sha maganin hana haihuwa don kar na haihu in tsufa A.m ya guje ni.Amma duk abin da na yi saboda shi ne ina..." Wani irin gigitaccen mari Momi ta kwasa mata sai da ta wuntsila. " Zainab are you stupid! Kin san abin da kika aikata kuwa kin san irin tashin hankalin da kika saka kan ki? Inna lillahi na shiga uku! Mai ya sa kika ɓoye min ina matsayin mahaifiyarki? Da duk haka ba ta faru ba." Zainab da ta ji saukar marin Momi sai da ta yi suman wucin gadi,ta dafe ƙuncinta cikin tashin hankali,saboda tun da take Momi ba ta taɓa kai koda ɗan yatsarta jikinta ba. " Momi marina fa kika yi?Bayan ba ki taɓa ko yin ihu mai ƙarfi gare ni ba,balle ki ɗora hannunki a jikina." Momi da take cikin tashin hankali saboda abin da ta aikata,kallonta ta yi ji take kamar ta rufe ta da duka. " Wallahi Zainab ji nake kamar na rufe ki da duka! Kin yi kuskure sosai in har kika yi wasa sai zaman duniya ya gundure ki,saboda girmar laifin da kika aikata. Maihaifinki na matuƙar son ya ga kin haihu haka nima, dangin A.m suna nan suna tsananin damuwar su akan rashin haihuwa da ba ku yi,ina kallon sa a matsayin azzalumi baya haihuwa ya kuma ƙi rabuwa da ke,ashe tawa ƴar ne ba ta haihuwa." Ta faɗa cikin kuka sosai wanda ya ɗaga hankalinta sosai. Hannunta ta riƙe tare da fashewa da kuka ta ce." Idan har za ki yi irin kukan nan, ya kamata ni na yi hawayen jini Momi,amma har yanzu ban ji tashin hankali ba sosai don ba na haihuwa,asalima ni yara sam ba su dame ni ba saboda wahala kawai suke baka, kuma kin san Momi na tsani ƙazanta sam ba na son na wahalar da rayuwa." Momi ta fisge hannunta ta juya mata baya,ta na kallon windo cikin wata irin murya,mai nuna tsantsar damuwa ga mamallakin muryar ya shiga. " Har yanzu ke yarinya ce ba ki gane komai ba,amma na tabbata za ki yi nadama in har ba ki ɗauki mataki ba,na rantse miki duk ranar da ki ka yi sake A.m ya haihu,daga ranar za ki fara son yaran duniya ba ki ɗaya." Ta juyo da ita suna fuskantar juna cikin murya mai sanyi ta ce."Duk da cewa Allah ya mallaka mini ke,amma mahaifinki har yau yana kukan rashin ɗa,ba za ki gane mai nake nufi ba sai ranar da kika yi hankali gurin tunanin wa zai gaji dukiyarki.Ki duba irin dukiyar da kike da shi in kika mutu wa za ki bar mawa?Ko so kike duniya suci. A.m yana da kuɗi da ahalin sa mene nufin ki akan dukiyar babu rabon ki a ciki?" " Haba Momi mai zan yi da wata dukiya iya abin da Allah ya mallaka mini ya ishe ni, ba sai na nemi agajin kowa ba,ga kuma dukiyar mahaifina, da ni ce kaɗai mallakin sa." Ta ce da Momi cikin jin ƙosawar maganar ta, don ita ba ta yi tunanin za ta ɗauko mata wannan shirmen ba,saboda damuwarta ta fi gaban wannan.Abu ne na zuciya da Allah ya ke halittar so a ciki,sam ba za ta yadda wata ta ƙwace mata shi ba. " Ba za ki gane ba ne Zainab dole ki ɗauki mataki na san mai kike nufi,kuma magana ta tana kan hanyar damuwarki,kin ga in kika yi gigin barin abin da kike faɗi ya faru,wallahi sai kin raina kan ki." " Wannan dalilin ya sa na ce tuntuni mu watsa mata acid amma Momi kika ƙi,da yanzu matsalata ta kau yanzu gashi kin sakani a cikin matsala,don ko kaɗan ban yi tunanin tana cikin gidana ba."Ta ce da ita tana ganin kamar Momi ta ja mata duk abin da ya faru. " Na hana ki ne saboda watsa mata ba shine mafita ba,in har yana sonta to zai yi komai don ya ceci rayuwarta.Na bari ki dawo hankalinki ya kwanta sai mu ɓullo ma abin ta ruwan sanyi,ba tare da ya yi tunanin da saka hannunmu a ciki." " To yanzu Momi ya zan yi?Ba zan iya barin ma wata kucaka ƙazama yar talaka mijina ba,ina son sa shi kan sa ya san irin son da nake masa.Ki taimake ni mijina ya dawo gareni Juwairiya ta fita daga rayuwar sa,in har ba so kike ki rasa ni ba,don na yi rantsuwar ba zan taɓa barin wata ta raɓe shi ba,ko da ace ba ni tare da shi! In ko hakan ta kasance mutuwa zan yi,sai dai ku nemi wata ƴar." Jijjiga ta da ƙarfi take yi ganin yadda ta fita hayyacinta tana watsi da kayan ɗakinta. " Ya isa ki natsu ki gane wace ce mahaifiyarki sam ba zan bari hakan ta faru ba,ko da ace zan yi yawo tsirara ne! Kin san wace ce mahaifiyarki ya kamata ki zama jaruma.Irin zuciyata ya kamata ki ɗauka,ba in aka yi miki abu ki ce za ki rama ta kisa.Sab ba haka jarumi yake cin nasarar sa ba,dagewa za ki yi ki saka makamanki ki yaƙi duk wanda ya zama garnaƙaƙi a cikin rayuwarki." Ta faɗa yayin da ta yi shiru tana kallonta don ba ta fahimci mai take cewa ba." Bari na baki labarina wanda baki taɓa sani ba Zainab.Mahaifin ki yaso wata mace kamar ransa yana jin zai iya mutuwa in bai same ta ba,ita kuma ƙawatace da muka haɗu a makaranta. Mun shaƙu sosai muna shiri da ita,duk ƴan'uwanta na san su,don har zuwa nake na kwana a gidan su.Mahaifinta hamshaƙin mai kuɗi ne sosai suna da kuɗi,yayin da ni ina karatu a gidan kawuna shi ya ɗauko ni ya sani a makaranta iyayena talaka. Tun da na fara mahaifinki na ɗauki son duniya na ɗora mishi sosai,sannan ina son na canza rayuwata daga ƙangin talauci. Matar kawuna ta yi mini hanyar wani malami ya ta kaini gurin sa,don ya janye hankalin sa daga gareta,amma sai dai in na yadda da sauran ƙwayayen haihuwana za'a yi asirin,in da za'a bar ɗaya kawai wato ɗa ɗaya zan haifa a duniya.Ba tare da damuwa ba na amince.A lokacin har an saka ranar auren su biki ya rage kwanaki aka fasa auren,in da ya zo gidammu da fari iyayena sun ƙi,amma ganin zai haukace dole aka ɗaura aurenmu wanda dalilin haka ta aikata suicide. ta mutu. Sai dai na fara nadama bayan aurenmu duk lokacin da hankalin sa ya dawo jikin sa,sai ya kasance ina yawan zuwa a juyar masa da hankali,a haka muka rayu har na haife ki bayan na haife ki sai Allah ya saka mi shi tsananin sonki,domin yana son yara sosai ya sha gaya min zan haifa masa yara da yawa." Momi ta yi nisa tana kallon Zainab da ta yi zuru ta zuba mata ido tana kallonta cikin al'ajabin labarin da take gaya mata. " Na yi matuƙar dana sani sosai da na yadda aka yi amfani da sauran ƙwaina,saboda dangin sa sun takura mi shi akan ya ƙara aure,sai dai na yi ruwa na yi tsaki har yau ya kasa ƙara auren.Don haka ki share hawayen ki A.m bai isa ya zauna da wata mace ba bayan ke,ke kaɗai ce za ki zauna da shi har abada,na yi miki wannan alƙawarin in...." " No Momi don Allah kar ki saka wani abu daban a cikin aurena! Ina son A.m ina burin na rayu da shi har abada,kuma kin san ni ba na son waɗannan halayen da kike yi,don haka in ba za ki taimaka min ba,kawai ni zan watsa mata acid ko na ɗauketa a garin."Ta ce da Momi cikin shagwaɓa tana kallonta yayin da hawaye suke ƙara turereniya a fuskarata. " Banza shashasha! Ita kin san abin da ta yi har A.m ya kula ta? Ki zauna garin kallon ruwa kwaɗo ya yi miki ƙafa,kuma Allah kin ji na rantse miki ko ke baki yadda da hakan ba,dole mu zamu ɗauki mataki." "Haka ne Momi ki yi haƙuri amma gaskiya ba zan amince da abin da kike so ba,zan kira Anty Lubna na san za ta ba ni shawara." Gabaki ɗaya kayan sawarta suka kwashe ita da Momi,bayan ta kira mahaifinta ta sanar masa take ya buga ma Daddy A.m waya saka yi kaca-kaca. Jikin Daddy ya yi sanyi to fa asiri ya tonu ya san cewa a kwai daru saboda shi ya saka hannu aka ɗaura auren. Jikin shi ya kama rawa saboda irin zagin da mahaifin Zainab ya din ga yi mi shi,ya san dole ya kira ainihin mahaifin shi ya gaya mi shi. Wani irin zufa take tsefo masa don ya san Allah kawai zai fidda shi,sai yanzu yake ganin mugun wauta da ya yi har suka yi galaba ya amince da aure. Wayar sa ya zaro ya don ya kira A.m cikin fushi.A ran sa yana baƙin cikin halin dukan mata da A.m ya ɗaukar wa kan sa. ********** " Wai mene ne haka ne A m ka san mai kake yi kuwa a asibiti muke,kuma ka duba idanun mutane a kan ka suke sam ba ka da kunya." A.k da ya yi wa Juwairiya rumfa da take kwance kan gado,ya kuma tura hannun sa a cikinta wai zai ji in da yaron yake. Juwairiya da wani irin kasala ya rufe ta zuciyarta tashi take yi,kamar wani aman yake son ya zubo mata. Da sauri ta ture hannun sa ji ta yi kamar an ɗora mata wuta a in da ya ɗora mata hannu a cikin. Ita ji ta yi da ya matso ta kamar wani irin wari za ta ce ko ƙamshi mara daɗi yake mata. Hannunta ta saka ta toshe hancinta da jin wani amai zai taso." Don Allah ka matsa kusa da ni sam ba na son jin ƙamshin ka kusa da ni."Ta faɗa da muryar kuka tana jin wani ƙunci a tare da ita. A.m ya yi turus kamar zai saka kuka ya juya ya kalli A.k da ya zuba masa ido sosai cikin son dariya. " To fa baban baby ka ce kai ma ka shiga daga ciki kenan." Ya faɗa a ransa yana tunanin kamar Juwairiya tana daga cikin jinsin matan da Allah ya halitta,a lokacin da suka samu ciki sai Allah ya jarabce su da tsanar miji tsana mai tsanani,yayin da suke ƙaurace ma mazajen su wasu har suna cutar da kan su. Don matar sa tana daga cikin irin masu wannan halittar,duk sanda ta samu ciki shikenan zaman lafiya ya yi ƙaura a gidan su har ta haihu. " Humh ka na ji fa wannan yar rainin wayon take faɗin na matsa,ai ita ta san in da ba babyna da yake jikinta ba babu abin da zai saka na matso kusa da ita,bayan ta san babu macen da nake so irin matar so."Ya faɗa yana hararar ta sosai ganin ta hana shi jin motsin baby. Ga mamakin sa sai ya ga ta mayar masa da hararan da ya yi mata,don ita har ga Allah ta ji wani irin tsanar shi a cikin ranta,ba wai don abin da ya faru ba,sai dai wani canji da ta ji a jikinta,saboda in ya matso wani irin wari take ji har da ƙarni-ƙarni a jikin sa,wanda yake tado mata da hararwa. A.k da ya yi tsuru yana kallon abin al'ajabi ganin yadda suka ɗauki fushi,bai taɓa tsammanin Juwairiya tana da tsiwa ba. " Ikon Allah yau kuma irin murnar da za ku nuna kenan,bayan yau Allah ya kusan cika muku burin ku.Kai zaka samu magaji,ita kuma za ta koma gurin Mama kamata ya yi ku nuna ma Allah godiyar ku." A tare suka harari junan su sai ta ji wani irin kewar Mama da son ganin ta ya kamata. Hawaye ta soma zubarwa wanda ya ɗaga hankalin A.m,cikin ɗaga murya ya daka mata tsawa. " Ki yi ma mutane shiru so kike ɗana ya gado shegen kukan ki na rashin dalili." A.k da yake kallon dirama dafa kafaɗan sa ya yi ganin yadda ya daka mata tsawa. " Haba A.m be a man. Baka ka san ba'a ɗaga ma mata masu ciki murya,irin shi ne suke haihuwar ɗa motsi kaɗan sai ya birkice." Da sauri ya kalli A.k cikin razana ya kama hannun sa ya riƙe sosai." Da gaske kake?Ina ga zan duba duba google akan yadda zan kula da cikin saboda kar a samu matsala, ina son yarona ya fi ɗan kowa a duniya,kuma ba na son ya yi kama da waccan abar mai emotionally fence."Ya ce yana nuna ta da bakin sa tare da galla mata harara. Tura bakinta ta yi ba ta ce masa komai ba,don ita yanzu haushin sa take ji na rashin dalili A.m ya ƙara hassala don ya tsani raini, karfa don ta ga ta samu ciki tace za ta yi mi shi rashin kunya,da kuma ya tuna abin da A.m ya gaya masa sai ya duƙa kusa da ita. " Kin san fa yanzu bake kaɗai ba ce,don haka duk kulawar da zan ba ki babyna nake ma wa,ki kwantar da hankalin ki yarona ya sakata ya wahala ya yi ƙatoto." Ya ƙara sausauta muryar da ba ta taɓa sanin yana da shi ba." Baby mai kake son ci?Ka faɗi duk abin da kake so zan kawo maka shi." Ture hannun sa ta yi ganin ya ƙara kawo wa "Don Allah ka ƙyale ni ba na son cin komai." " Ba ke na tambata ba babyna nake magana da shi don na san dole yana buƙatar abinci." Ya faɗa a kausashe don shi jin yake anya zai iya ɗaukar raini daga gare ta. " Ka dai kula da abin da na ce maka, in ka din ga daka mata tsawa ta haifi yaron matsoraci, kai ka sani ka san dai wannan shikenan babu ƙari."A.k ya ce da shi. Sosa kan shi ya yi." Na ji kuma zan kiyaye in sha Allah.Dole na samu babban likita wanda zai dinga ɗorani a kan yadda ake rainon ciki." Juwairiya ta miƙe ta tana wani yatsina irin na masu ciki gabaki ɗaya ta ji wani canji a jikinta.Dambu da kalallaɓa ta ji kawai tana son ta ci,amma ta san ko ta faɗa masa ƙila ba zai nemo mata ba. Amma kuma da ta ji son cin abincin zai saka mata amai,in dai ba ta ci ba kallon sa ta yi ta ce." Ni fa dambu zan ci da kalallaɓa kuma yanzu nake so." A.m ya zare ido ya ce." To yar rainin wayo gara dambu na san shi matar A.k tana yi,amma kuma mene ne kalallaɓa?Ni fa kar ki raina mini wayo ƙila ba baby ba ne zai ci." " Ko ma waye zai ci dole ka nemo ai wallahi tausayinka nake ji,don yanzu ka shiga hannu dole ka zama ɗan siyayya."A.k ya ce mishi yana kallon doctor da ya turo ƙofa ya shigo. " Yauwa doctor yau she zan dawo ka ba ni shawarar yadda zan kula da babyna." Dariya ya yi suka tafa da A.k." Abinka da sabon shiga."Hararar A.k ya yi jin abin da ya faɗa. Wayar sa da take da can gefen Juwairiya ta ɗauki ruri sosai.Gaban sa ne ya faɗi don ya san kiran bai wuce daga gidan su. " Please A.k ɗaga wayar ba zan iya ba na san bai wuce Daddy."Ya faɗa yayin da fara'ar shi ta kau. Shi kan sa A.m a tsorace yake ya san ayau Allah kawai zai raba su da shi. Da ya ɗaga wayar sai ya saka ta a hands pree. " Kaicona Abdurrahman! Yau na yi dana sani da na ɗora yaƙinina akan ka.Abin da ka aikata kenan?A she baka da hankali wallahi ban taɓa sanin mahaukaci ba ne kai sai yau.Maza ka taho gida ina neman ka duk in da kake, da kuma yarinyar da Zainab ta ce ka dake ta saboda ita,don ni bazan ce matar ka ba ce sai dai kuma in ka canza iyaye bayan ni da Daddy ɗinka.Minti biyar na baka." Mahaifin A.m ya faɗa yana huci ya kashe wayar,yana kallon Daddy da ya yi tsuru-tsuru. A.m jikin sa ya yi sanyi ya kalle ta duk tana jin abin da ke faruwa,amma ba ta nuna komai a ranta ba. "Mahaifina ya na son ganina dotor ka sallame mu." Ya faɗa jikin sa a sanyaye saboda ya san a yau duk wanda yake da ƙima a idanun su, ƙimar shi za ta zube,ya san mahaifiyar sa ba ta da wasa mace ce da ba ta ɗaukar raini,hankalin sa ya ƙara tashi da ya tuna ƙannin sa ko ya za su kalle shi. " Ka san Allah babu in da za ni, sai da na gargaɗe ka amma ka yi mini rashin mutunci,yau sai ka ƙwaci kan ka da Daddy,amma babu in da za ni na san Daddy ya yi fushi sosa."A.k ya ce da ya ga yana kallon sa. " Juwairiya tashi mu tafi sai ki jure duk abin da za ki gani,sauƙinta ma siyen ki na yi da kuɗina balle ki ce na kai ki in da za'a wulaƙan ta ki." Hankalinta ya tashi gabaki ta fita hayyacinta ji take kamar ta ga ta ɓace. " Na shiga yau zan ga ahalin A.m wani irin tarba za su yi mini?Yau na san zan sha wulaƙanci wataƙila dukana za su yi." Ta faɗa cikin tashin hankali ganin yadda shi kan shi ya ruɗe,sai ta raya a ranta babu in da za ta don ba za ta je su kashe ta ba. Kamar ya san mai ta raya a zuciyarta ya ja hannunta,da ƙarfi ya nufi mota yayin da gabansa yake dukan tara-tara. A.k kuwa daga asibitin gida ya koma ko aiki ya ƙi zuwa,tunanin shi Daddy zai iya bin shi gurin aiki,bayan ya shiga gida ya sanar da maigadin gidan sa duk wanda ya zo ace ba ya nan,ya rantse ba zai ƙara zuwa aiki ba sai ranar da aka gama wannan rikici. A lokacin da ya gaya ma matar sa ta yi shiru,ta zuba mishi ido tana jin tatsuniyar da yake mata,zuciyarta na matuƙar mamakin sa,tsawon shekara biyu suka shirya hakan,amma ko wanka mai kama da jirwaye bai taɓa yi mata ba,sai abin ya ƙara ba ta matuƙar mamaki ta din ga kallon sa tana son ta yi magana amma ta kasa. Kofin gilas ɗin da ke hannunta ta saki tare da zare ido da ta ji ya ce." A yanzu Juwairiya na da ciki kuma Zainab ta gane,Daddy ya yi kiran sa tsoro ya sani na ƙi zuwa don babu irin abin da ban faɗa masa ba,amma ya yi kunnin uwar shegu da ni sann..." " Na shiga uku wayyo Allah na! Oh Zainab mai ya kai ki aikata wannan kuskuren lallai kin yi sake."Ta ce da tsananin mamaki sai abin ya ba ta tsoro hararar A.k ta yi ta ƙara cewa. " Amma wallahi kun munafunce mu gaskiya ba ku yi mana adalci ba,haba Baban Najwa yanzu watarana in za ka ƙara aure haka za ku munafunce ni." Dariya ya yi ganin ta birkice kishi ƙarara a fuskarta." Baki fahimce ni ba A.m ya kashe maƙudan kuɗi ya auri Juwairiya akan za ta ba shi baby in ta haihu su rabu ya bawa Zainab,wannan dalilin ya ije ta a gidan sa don tana haihuwa za su rabu,sakacin Zainab ya kusanta Juwairiya da shi,don tana da hankali ga kula da tsafta da iya girki ni kaina in na ci abincinta ina yabawa." Ya numfasa sannan ya ɗora da cewa."kuma kin san A.m da son kula shi ya sa nake kallon Zainab a matsayin wawiyar mace,saboda mijinta irin mazan nan ne masu son mace ta mai da su yaro,a yadda na kula da A.m zai iya barin mace ta yi masa komai na kulawa,wanda ita ta gaza hakan da haka Juwairiya ta samu ta saka shaƙuwa a tsakanin su,duk da har yanzu yana kan bakan shi na rabuwa da ita,ni dai lamarin yana ɗaure min kai sosai ina tunanin yadda za ta haihu ta ba wa wata mace ɗanta.Sannan ba lallai ba ne Zainab ta riƙe." " Humh wannan lamari a kwai rikitarwa har yanzu zuciyata ta kasa yadda da kai,don kun yi matuƙar ba ni mamaki,ashe duk ƙus-ƙus da kuke yi maganar auren ne,in na yi maka magana ka ce kuna maganar kampani,ai ga shi nan kun ibo ruwan dafa kan ku,sannan ba ka kyauta ba da ba ka je ba." " Wa ni wallahi babu in da zani tsuntsun da ya ja ruwa." Bugun ƙofa ya ji da sauri ya shige cikin ɗaki bayan ya ce " Don Allah ko wane ne ki ce ba na nan,kar na zo na fito Daddy ya zo." Dariya ya ta saki a ranta tana mamakin wannan girman lamari da ya faru da ita. " Ikon Allah duk cika da isar Zainab taƙama da kuɗi! Yau ita ce da kishiya kishiyar ma talaka da take wulaƙantawa." Sai kuma ta nisa ta kuma cewa." Allah sarki Juwairiya kin yi wauta ina tausaya ma rayuwar ki ko ya ya iyayen A.m za su karɓe ki waɗannan ƴan nuna isa da raina talaka."Wayarta ta ɗauka ta shige ɗakinta. A.m da yake jin bai taɓa jin matsananciyar kunya irin ta yau ba,da ya yi hon maigadin gidan su ya buɗe masa get. Sai ya ji kamar ya koma lokacin da ya yi parking ya fito. " Ki biyo ni." Kawai ya ce hankalinsa a tashe ya nufi cikin gidan yayin da take taku cikin tsoro,ganin irin daular duniyar da ya kawo ta sai ta raina kanta. Juawairiya ta tsaya cikin tashin hankali tana kallon mahaifin A.m da ko ba'a gaya maka ba,za ka nuna sa ka ce shine saboda sun yi matuƙar kama kamar har ta ɓace. Ta kuma kallon sauran mutanen da ke falon sun taru da yawa sun zuba mata ido. Kyawawa da su masu zubin larabawa kamar A.m da su ta yi yawa.Sai tsananin kunya ta kamata ba ta taɓa jin ta muzanta irin na yau ba. " Inna lillahi wa inna ilaihir raju'un! A she da gaske ne ba ƙarya ba A.m ya zama uban kan sa ya yi aure?Ko kuma karuwa ce ya ije a gidan sa?" Mahaifin A.m ya faɗa ganin Juwairiya ta ɓoye a bayan sa,sannan sam Zainab ba ta gaya musu ba ta haihuwa da kuma maganar ciki ba. Gani suka yi Daddy ya yanke jiki ya faɗi sharab! Gabaki ɗaya suka saka kuka suka yi kan shi. TO FA MASU KARATU GA DAI JUWAIRIYA TA BAYYANA CIKIN FAMILY ƊIN A.M SHIN ZA TA ƘARƁU KO YA YA? KU CI GABA DA BIBIYAR LINTAFIN DON JIN YADDA ZA TA KAYA A CIKIN LINTAFIN NAN MAI FARIN JINI. BARI NA TUNA MUKU DA SUNAN SHI SAKACINA KO HALIN MAZA TAKU JAMILA LAWAL ZANGO JAMCY TALLAH!TALLAH!!TALLAH!!! INA ƳAN MATA DA MATAN AUREN DA SUKA SHAYAR SUKE SON MARTAR ƘIRJIN SU YA DAWO? INA MATAN DA SUKE FAMA DA RASHIN ƘIBA KO INA A ƘAME? MAZA GARZAYO KI SIYA INGANTACCEN MAGANIN GYARAN NONO DA ƘIBA,MAGANIN AN RIGA AN GWADA KUMA YA NA DA AKYAU ƘWARAI.BARI IN GAYA MIKI YAR'UWA DUK WADDA TA CE MIKI MARTABAR ƘIRJINKI,ZAI DAWO MATUƘAR JIKINKI BAI MURJE BA,TO GASKIYA KUƊIN KI KAWAI ZA TA CI. IN HAR KINA SON MAGANIN YA YI AIKI A JIKIN KI SAI KIN DAURE,KIN SHA SAFE DA YAMMA.SANNAN MUNA AIKAWA KO INA SIYAN NAGARI MAIDA KUƊI GIDA. MAGANIN AKAN FARASHI MAI TSAUƘI IN KINA SO MAZA GARZAYO KI KIRA WANAN NUMBAR ( 07088268243) KO (08144072423) Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 32* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM " Don Allah Abba ka tashi kar ka mutu?" A.m ya faɗa sannan ya yi kan sa da sauri,take wani irin nadama ya shige shi. "Mahaifiyar sa umma ta zabga mishi mari, cikin ɓacin rai ta nuna masa hanyar waje,idanuwanta suna zubar hawaye. " Fita daga gidan nan ba na son ganin ka! Sannan ba na burin na ƙara tozali da kai Abdul,ka cuce mu ka zubar da tarbiyar da muka ba ka,Abdul karuwa fa ka ije a gidan ka?" Kawai sai ta saki razanannen kuka ta kifa kanta jikin Mahaifin sa, tana wani irin kuka mai cin zuciya. A.m da ya ji matsanancin tashin hankali ya kauda kan sa,ga barin kallon Juwairiya da ta rintse idanunta,tana jin wani irin ƙuna mara misaltuwa a zuciyarta jin ana kiranta da sunan karuwa. A.m ya buɗe bakin sa zai yi magana,daidai lokacin da Daddy ya ibo ruwa, ya yayyyafa ma mahaifin sa a jiki. " Ba na son na ji muryar ka na tsane ka A.m ka fita nace! Wane ido kake son mu kalli iyayen Zainab,da ka tozarta mu a gurin su,bayan ka ije karuwa sannan ka yi ma ƴar su duka,tun da nake da kai,ka taɓa ganin mahaifin ka ya ɗauki ko da tsintsiya ya buge ni da shi?"Ta ce mi shi cikin tsigar tambaya. "Momi na tuba ki yafe min amma kin san ba zan taɓa aikata zina ba,Momi ba halina ba ne k..." " Ka tashi ka fita na ce banza mara tunani!Haka kake son ƙannin ka su yi?" Duƙa wa ya yi da nufin ya kama ƙafafunta,amma sai ta janye,da sauri tana mi shi wani mugun kallo. " Maza ka fita da wannan abar mara hankali kawai, ka rasa macen da za ka kula sai ƴar talaka ƙazamiya tir! Wallahi ka zubda ajin ka." A.m ya miƙe cikin dana sani ya kama hannun Juwairiya da ta ji yau ta tsani kanta fiye da kullum,ta muzanta iya muzanta tana jin kamar ta nutse a ƙasa,ganin yadda mutanen gidan suke kallonta tamkar sun ga kashi.Fara tafiya ya yi da ita yana jan hannunta. " Wayyo Allah na shiga uku ya zan yi da raina wai yau ɗan da na ba ma tarbiya ne! Yake riƙe da mace maccen da ba muharramin sa ba." Sai ta fashe da kuka mahaifin sa kuwa tun da ya faɗi,bai ƙara cewa komai ba sai kallon A.m da yake yi tamkar bai san shi ba. " A.m dawo mu yi musu bayanin ita ɗin matarka ce ba yadda suke tunani ba,mu daina ɓoye ɓoye mu gaya musu gaskiyar komai." Abba da ke kwance ya miƙe cikin mamaki ya ce." Na lura baku da hankali dukan ku,ta ya ya za'ai ya yi aure ba tare da sani na ba?" Ya tambaye shi cikin tsananin mamakin sa ya kuma kalli Daddy da ya yi fuska sosai,ganin ana muzanta mi shi shalelen sa. " Mai ya sa za ka tambaye ni dalilin auren sa bayan ka mallaka min shi halak malak?" Abba ne ya harzuƙo gani yake kamar Daddy ya raina mi shi wayo,don haka cikin fusata ya cakume shi. " Ba ka da hankali ne?Kai da shi duk kun zare! Duk da na ba ka shi kyauta,ai kwarmin ido ba ramin ba ne,in ba ka sanar da ni auren sa ba,ka gaya ma mahaifiyar sa da ta yi rainon cikin sa har na tsawon wata tara,ta kuma yi ɗawainiyar shi." Sai Daddy ya din ga kallon sa cikin wani irin kallo yana matsawa,yayin da idanun shi suka fara zubar hawaye,ya kalli A.m da hankalin shi in ya yi dubu to ya tashi,ganin tun da yake bai taɓa ganin iyayen na sa sun yi ko da sai in sa ba. " Allah na gode maka da ka san da ni a duniyar har ka jarabce ni da rashin haihuwa,yau ga ɗan'uwana wanda muka fito ciki ɗaya da shi ya yi mini gorin ɗa,ya nuna ban isa da ɗan shi da ya haifa ba,wanda na yi tunanin yaransa duka mallakina ne." Da baya baya yake tafiya yana zubar hawaye, duk da ya san abin da A.bba ya ce gaskiya ne,bai kyauta ba da ya biye masa aka yi auren ba tare da sanin su ba,amma ya ji zafin gorin da ya yi mishi sosai ya ji ƙuna a zuciyar sa fiye da tunani. " Amma ka san ba ku kyauta mana ba,haba ta ya ya zai yi aure ba mu sani ba,sannan ya ije matar sa a gidan sa,kuma ba tare da matar sa ta sani ba?Anya kana ganin ganin kun yi mata adalci kuwa?Sannan ya rasa macen da zai so sai yar talaka mai zai yi da ita" Ya numfasa ya ja numfashi yana kallon sa sannan ya ɗora da cewa." Yarinyar nan ƴar aminin ka ne,kana ganin bai tozarta ka ba ka duba iri tashin hankalin da mahaifinta ya yi maka."Ya ce yana kallon sa. " Tabbas ƴar aminina ne kuma na san haka,amma ka sani duk abin da ya faru ita ta jawa kanta,da fari da suka zo da maganar korar su na yi na ƙi yadda da maganar su,amma da ga baya A.m ya gaya mini,ita Zainab ɗin ce ba ta haihuwa sannnan kuma ta saka shi dole ya yi mata,alƙawarin kar ya yi mata kishiya,bayan duk abin da ya faru ita ta ja ma kanta,saboda mugun son duniya. Saboda haka na amince bayan na duba irin ƙuncin da nake shiga sakamakon rashin haihuwa,wanda yau gashi kai ma da kake ɗan'uwana ka goranta mini."Ya tsaya da maganar domin ya huta kaɗan. Abba da sauran mutanen da ke tsaye cikin mamaki suke kallon Daddy,suna al'ajabin wannan maganar da ya tayar da hankalin su. " Ganin na ƙi yadda da maganar amma sai A.m ya nuna ya haƙura,wanda ni na ƙi yadda ne kan ya canza haukar maganar da ya yi mata,na ba zai ƙara aure ba,amma sai ya nuna sam shi ba zai ƙara aure ba,saboda haukar so da ya rufe mi shi ido. "Na amince A.m ya aureta ne saboda in har ba ta hakan ba, a yadda ya nuna ba zai taɓa ƙara aure ba,ni kuma ba na son ya rayu ba tare da ya ga ɗan sa a duniya ba,sanan in na fito fili na nuna kan dole ya ƙara aure ban san ya mahaifin Zainab da ita za su ɗauke ni ba."Ya ƙarashe maganar cikin mutuwar jiki yana ƙara goge sauran hawaye da yake maƙale a fuskar sa. Ya kama hannun Abba ya riƙe sosai tare da sakin kuka ya ci gaba da cewa." Ka yafe mini amma yau ka nuna min iyaka ta,na san in da zan tsaya akan yaran ka,amma ka sani ba laifi na yi ma Allah ba da ya hana ni haihuwa,kullum ina godiya ga Allah da ya yi mini tarin ni'imomi a rayuwa." Abba da jikin sa ya yi sanyi sosai ganin ɗan'uwan sa ya yi fushi sosai,shi kan sa ya yi dana sanin maganar da ya gaya masa,wanda hakan ya faru sakamakon ɓacin rai da dokin zuciya,sannan ya yi baƙin cikin abin da su yi haba sai ka ce shi bai fi su hankali ba,amma kuma duk abin da ɗan'uwan sa ya yi masa bai kamata ya yi masa gorin haihuwa ba,duk da cewar bai san lokacin da maganar ta fito ba,don magana zarar bunu ce. Dukkannin su sun cika da mamaki iya mamaki da gaske A.m yana haihuwa ya yi musu ƙaryar haka,don kawai ya faranta ma mace bayan ya san in da ace shi ne baya haihuwa da ba za ta zauna da shi ba. Mahaifiyar sa ta zo gaban sa ta din ga kifa masa mari, har sai da ƙanin sa ya janye shi daga gurin. " Ka cuce mu sam ba ka yi mana adalci ba!Kasan iya tsawon lokacin da na ɗauka ina tashi cikin dare,akan Allah ya sa ka samu ɗa.Kusan kullum sai na yi maka addu'ar ya kauda matsalar da kake da shi,ina tunani da tsoro a kwai ranar da Zainab za ta yi maka tawaye ta rabu da k...."Kawai sai ta ƙara sakin kuka da ƙarfin ta. Abba ya kalli Juwairiya da ta gaji da tsayuwa ƙafafunta har rawa suke yi,ya kuma juya idanun sa ga Daddy da har yanzu yana jin babu daɗi akan maganar da Abba ya yi masa. "Ka yi haƙuri ka yafe mini na san na yi kuskure da na gaya maka haka,musamman da na riga na mallaka ma shi duniya da lahira,amma abin da kuka yi kamar ba na masu hankali ba,ga in da abin ya kai ku." Ya yi shiru ko Daddy zai ce wani abu amma sai ya ga ya ɗaure fuska don haka ya ci gaba da cewa. "Kuma sai ya rasa wacce zai aura sai ƴar talaka har da kai ka biye mi shi?Haba ta ya ya za'ai kamar shi ya auri ƴar talaka.Ai wannan kamar ya zubar mana da mutunci ne b...." "Wannan kuma sai ka tuhume sa domin cewa ya yi zai aure ta, su rabu bayan ta haihu ya ba wa Zainab yaron.Wataƙila son ta yake shi ya sa ya yi mini ƙaryar haka." Da sauri A.m ya kalli Daddy ya ce." Ba sonta na ke yi ba Daddy da gaske nake yi,yaron Zainab zan ba ta riƙe ita kuma za mu rabu bayan ta haihu,saboda mahaifiyar ta ma ba ta san tana auren ba." " What mene kake cewa Abdul! Anya kana da hankali kuwa."Mahaifiyar sa ta ce cikin tsananin razana. A.m ya cire tsoro ya gaya musu duk abin da ya faru har ɗauke Mama sai da ya faɗa musu,da yadda Baba Sani ya takura wa rayuwar su,da dalilin da juwairiya ta amshi auren sa,sannan kuma ya yi alƙawarin tana haihuwa zai rabu da ita. Umma ta din ga mata wani irin kallo na mai kama da tausayi ko akasin haka. " Sam ba ki yi ma mahaifiyar ki adalci ba,duk da cewar kin yi hakan don ki ce ci rayuwarta,amma ta ya ya za ki yi aure ba tare da sanin mahaifiyarki ba?Gaskiya wannan babban kuskure ne da kika aikata,saboda mahaifiyarki Allah kaɗai ya san halin ƙuncin da take ciki." Umma ta faɗa cikin tsananin mamaki lallai ɗan yau sai abar su,gabaki ɗaya san mai da mutane shashashu,sun ƙullah hakan ba tare da sanin kowa ba,ita kuwa Zainab wata irin banza ce da har mijin ki zai auri mace ya ije a cikin gidanki ba tare da ta fahimta ba. " Yarinyar tana da kyau da natsuwa amma mai zai saka,A.m ya je gidan wulaƙantattu takala ya auro ta?"Ta faɗa a zuciyarta tana jin babu daɗi a ranta na haɗa jini da talaka da yake son ya yi. " Kuma sai ka rasa ƴar wa za ka aura sai yar gidan Malam Shehu Abdul kenan son yarinyar kake yi?Bayan ka ce za ku rabu duk da wannan hauka kake yi,ka taɓa ganin in da ɗan wani ya riƙe ɗan wani?" Da sauri ya kalli ta jin mahaifin sa ya faɗi haka,ya ci gaba da kallonta na ɗan wani lokaci,yana son ya gano da gaske ne abin da mahaifin sa ya faɗa,kasancewar sa mai saurin gane abin da yake zuciyar mutum. Taɓe bakin sa ya yi don shi bai ji wani abu na so a zuciyar shi dangane da ita ba,ya san dai yana matuƙar son babyn da za ta haifa. " Daddy ba na sonta sam ba ta a tsarin matar da nake so,saboda ni ban san mace mai saurin kuka da shiru-shiru,wallahi ban aure ta don ina son ta ba,kawai ni na aure ta don ta haifa mini yaro na ba wa Zainab,kuma in sha Allahu sai na nuna mata na san mahimmancin alƙawari,sannan na fara...." " Rufe mini baki shashasha! In ba son ta kake ba,mai ya sa ka rasa macen da za ka aura ka je ka aure ta?" " Saboda ita kawai na ji zan iya zaman aure da ita,amma fa na wucin gadi bayan Zainab."Ya ba Abba amsa da sauri. " Ai ko baka isa ba tun da ka shigo da ita rayuwarmu dole ka zauna da ita na har abada,Juwairiya za ta ci gaba da zama da mu a matsayin matarka sannan za mu je in da ka ɓoye mahaifiyarta,saboda son zuciyar ka mu dawo da ita,shi kuwa Baba Sani ka barni da shi na san mai zan yi mi shi,saboda ya yi watsi da zumunci Allah sai ya hukunta shi.Sai ku san yadda za ku yi kai da mahaifin kaku dawo da matarka,tun da ku kuka shirya abin ku can ku ƙarata in har ta ga dama ta zauna da kai in ba za ta iya ba,babu dole sai ta zaɓi mai yiwu wa saboda ina son na ga yaran ka,fatana ta haifa maka yara da yawa." A.m ya ji wani irin saukar abu mai kama da guduma ya sauka a kan sa." Ina sam ba zan iya karya ma Zainab alƙawarin da na yi mata ba,in sha Allahu saina nuna mata ni na san mahimmancin alƙawari ba zan zauna da ita kamar yadda suke tunani ba." Hamdiyya wacce take cousing ɗin A.m ce ,tana zama a gidan sakamakon haɗarin mota da iyayenta suka yi.Sai Abba ya ɗauko tana karatu a gidan,ta kama hannun Juwairiya da ta ke jin kamar za ta faɗi ta zaunar da ita,sai kuma ta kama hannunta ta ce. " Anty Juwai ta shi muje ciki na ga duk kin gaji da tsayuwa." A.m ya sauke ajiyar zuciya da ƙarfi yana jin daɗin yadda abin yazo,duk da cewar ya sha mari amma da ɗan sauƙi. Tun ɗazu yake kallonta da ta yi tsaye tsamo kamar wacce ta faɗa ruwa,sai hawaye dake turereniya a fuskarata,tana jin irin tarin cin fuskar da suke mata,amam kuma ko mai ya faru ita ta ja ma kanta. " Alhamdulillah." Ya faɗa a ran sa jin abin da Hamdiya ta ce dama tun ɗazu yake kallonta,yana son ya ce ta zauna saboda babyn shi,amma yan jin kunyar idanun iyayen na sa. Duk yadda Abba ya so Daddy ya saki fuskar shi, amma ya ƙi saboda y ji haushin abin da ya faɗa masa. Ko da ya rako shi zai tafi sai Abba ya kama hannun sa ya riƙe kamar zai yi kuka ya ce."Ka yi haƙuri da abin da na yi maka raina ne ya ɓace.Abdurrahman haihuwar sa kawai na yi amma kai ka yi duk wata ɗawainiya ta sa,don Allah ka manta komai ba ma shi ba,ka na da iko akan sauran yarana,kawai zafin zuciya na abin da kuka aikata ya sa na faɗi hak.Juwairiya za ta zauna da mu zuwa wani lokaci sannan ta koma ɗakinta ina ka taɓa jin anyi haka! Da yake ɗan na ka mahaukaci ne igiyar kuɗi tana ibar sa,yana tunanin kuɗi zai iya mi shi komai." " Babu komai Allah ya kauda fitina a tsakaninmu."Ya ce a daƙile kuma ba tare da walwala ba. Zama ta yi a katafaren falon Umma ta yi tsumu tana kallon dukiyar da aka jera a falon,a ranta tana son ta ga wane gida yafi kyau a tsakanin na A.m da na iyayen sa. Umma ce ta shigo ta zauna a falon sai gabanta ya faɗi ta ji wani irin banbaraƙwai,ta kasa ko motsi ga miyau da ya cika mata baki kuma yunwa take ji. " Hamdiya." Umma ta yi kiranta da ta shiga kicin don ta sama mata abin da za ta ci. Da sauri ta fito hannunta ɗauke da tire na dafaffiyar shinkafa da kayan lambu a sama. Ta ije kusa da ita tana kallonta haka kawai ta ji ta burgeta." Anty ki ci abinci daga ganin yanayin ki na san yunwa kike ji."Ta faɗa da murmushi a fuskarta,burinta ta saki jikinta ganin yadda ta yi. Juwairiya ta kalli shinkafar sai ta ji sam bai yi mata ba,asalima naman kajin da aka yi girkin da su,take jin ƙarnin su kamar suna ɗanye. Amai ne ya taso mata da gudu za ta miƙe gashi tana jin kunyar Umma da take zaune tana sanar ma ƴan'uwanta abin al'ajabin da suka ta shi da shi. Da sauri ta miƙe gabaki ɗaya hankalinta ya tashi ba ta san sadda ta kai hannu ta riƙe ta da take ta shara amai kamar ba za ta daina ba. A lokacin A.m ya yi sallama ya shigo." Subuhanallahi doctor ya ba mu magani bari na ɗauko mata ai lokacin sha ya yi don ba na son babyna ya wahala." Wata irin uwar harara Momi ta yi mi shi jin abin da ya ce." Kar ka zama mara tausayin mata masu ciki,saboda in ka fara da haka to a haka za ka ci gaba mahaifin ka in har ina da ciki har ije aikin sa yake yi." " Sorry Momi." Ya yi mata sannu sannan ya fakaice idanun Momi ya banka mata harara." Ai ke Abba yana son ki ni kuwa ba so tsakaninmu."Ya faɗa a zuciyar shi ya fita. Hamdiya ta ga hararar da ya yi mata sai jikinta ya yi sanyi ta kalli yadda take kwarara aman,sai tausayinta ya cika mata zuciya. Ɓaro mata maganin ya yi ya miƙa mata tasha amma sai ya dawo.Kwantawa ta yi a kan duguwar kujera gabaki ɗaya jikinta ya mutu. " Momi na ji an ce in mace na da ciki tana yawan amai yunƙurin aman na iya saka yaron cikin ya fita?" A.m dake kan kujera ya zuba ma cikinta ido shi duk ya ƙosa cikin ya ɗan fito,ta yadda zai din ga shafawa yana jin ɗan sa. Wintsilowa ya yi tare da zare ido ya ce." Wai haka momi?" Sai abin ya ba ta dariya ita kanta ba ta burin ɗan ya fita domin ƙila ta fi shi murnar cikin,kawai tana ɗan damuwa ne ɗan zai fito ta gurin ƴar Malam Shehu,amma ya suka iya da ƙaddara. " Kamar haka na ji malaminmu ya ce lokacin da yake mana bayanin ciki da matankan kula da shi."Ta ce ba tare da ta bari wacce ya tambaya ta ba da amsa ba,a ranta tana jin daɗin yadda maganar ta ƙarɓu. " Na fa manta ke ma likita kike karanta don Allah Hamdiya ki rubuto min, duk yadda ake kula da mace mai ciki,sai na san yadda zan kula da babyna."Ya ce sannan ya juya yana kallonta da ta yi lamo kamar mai bacci don wahala,a ranta tana jin ta yi Mama ƙaton laifi in dai haka ta sha wuya kafin ta haife ta. " Ok ba ka da matsala ya A.m.Anty Juwairiya ta so mu je ki gaya min me kike so na dafa miki."Ta maida maganar gurinta tare da kama mata hannu. Juwairiya tana matuƙar shan wahalar cikin nan,duk abin da ta ci sai ta yi aman shi,in dai ba kalallaɓa ba ko fate,shi ma sai an dafa irin abincin gidan yarin.In kuma ta gama ci ta yi ta amai ko tashin zuciya duk kyawu da ƙibar da ta yi gabaki ɗaya ta rame ta zube ta fita hayyacinta. Ita abin da ya fi ba ta damuwa shine sam ba ta son duk wani turare da suke shafawa, sai wata humra da Hamdiya ta ba ta tana shafawa. Tana jin duk lokacin da ya matso gurinta sai ta ji amai,saboda ta gane ba turaren da ya canza ba ne ba ta so,kamshin jikin sa ne ba ta so,tun bai gane ba har ya gane,wanda hakan ya ɓata mishi rai sosai.Ya din ga kumfar baki yana tsiya ya kuma rantse ko mutuwa za ta yi sai ya zo gareta don ya din ga jin lafiyar ɗan shi,rikici sosai suka yi da ƙyar Umma ta sasanta,akan dole ya yi haƙuri ya nisanta kan shi da ita,ya dai ji ta ne amma ya saka a ranshi ko mutuwa za ta yi,sai ya matso ya ji lafiyar baby ɗin sa. Hamdiya ta yi zuri tana kallonta da ta rintse idanunta kamar bacci take yi,amma tsabar laulayin yake damunta har wani siririn hawaye yake biyo gefen kumatunta. " Anty Juwairiya ni fa ɗazu kin ba ni mamaki sosai ina jin Ya A.m yana gaya miki wai ba son ya matso kusa da ke yake ba,tun da ya samu abin da yake so lafiyar baby ɗin shi yake so ya ji,ya kusa dawo da matar so?" Ɗan tsaki ta yi tana ganin babu amfanin maganar,da can da take son shi ba ta wani damu ba,balle yanzu da take jin yana mata wari-wari.Ganin ba ta amsa ba sai kallonta take da alama ba ta son maganar. " Ai wallahi kin ban mamaki sosai haba ina mace kamarki, wani namiji zai din ga nuna wata tafi ni,ina bai isa ba wallahi ya yi kaɗan.Ya A.m bai fiki kyau ba sai haske kawai da zai nuna miki saboda shi jan ga fur ne." Ta ja numfashi tana kallonta ko za ta ce wani abu amma sai ta ga ba ta tanka mata ba,illa lumshe ido ta yi." Kuma da yake cewa ya na da matar so in har ba son ki yake ba mai zai saka ya shigo rayuwarki." Murmushin dole ta yi ta kalleta ta ce don ta lura ita tana da sauƙin kai ba ruwan ta da ɗagawa,kamar sauran ƴan'uwan A.m da kan su a ɗage yake suna fisgan kai,duk da cewar sun yi murna da jin ɗan'uwan su zai samu baby daga gare ta,amma da suka zo haka suka din ga nuna feeling. " Kar ki damu da ni Hamdiya a halin yanzu na ƙosa na rabu da cikin nan na koma gurin Mama,saboda kullum sai na yi kuka ashe dama haka ta sha wahala da ni,amma na ha'inceta na yi aure ba tare da sanin ta ba?" Sai ta fara kuka sosai dama mai shirin kuka ne, aka jefe shi da kashin awaki,tsananin laulayin da take fama da shi ya dame ta. TO MASU KARATU KU DAI BIYO NI KU JI YADDA ZA TA KAYA A TSAKANIN SU YAU BAN YI TYPIND DA YAWA BA,SABODA BA NA JIN DAƊI KU YI HAƘURI DA WANNAN ANA TARE. KU CI GABA DA BIBIYAR LINTAFIN DON JIN YADDA ZA TA KAYA A CIKIN LINTAFIN NAN MAI FARIN JINI. BARI NA TUNA MUKU DA SUNAN SHI SAKACINA KO HALIN MAZA TAKU JAMILA LAWAL ZANGO JAMCY TALLAH!TALLAH!!TALLAH!!! INA ƳAN MATA DA MATAN AUREN DA SUKA SHAYAR SUKE SON MARTAR ƘIRJIN SU YA DAWO? INA MATAN DA SUKE FAMA DA RASHIN ƘIBA KO INA A ƘAME? MAZA GARZAYO KI SIYA INGANTACCEN MAGANIN GYARAN NONO DA ƘIBA,MAGANIN AN RIGA AN GWADA KUMA YA NA DA AKYAU ƘWARAI.BARI IN GAYA MIKI YAR'UWA DUK WADDA TA CE MIKI MARTABAR ƘIRJINKI,ZAI DAWO MATUƘAR JIKINKI BAI MURJE BA,TO GASKIYA KUƊIN KI KAWAI ZA TA CI. IN HAR KINA SON MAGANIN YA YI AIKI A JIKIN KI SAI KIN DAURE,KIN SHA SAFE DA YAMMA.SANNAN MUNA AIKAWA KO INA SIYAN NAGARI MAIDA KUƊI GIDA. MAGANIN AKAN FARASHI MAI TSAUƘI IN KINA SO MAZA GARZAYO KI KIRA WANAN NUMBAR ( 07088268243) KO (08144072423) Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 33* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM "Hamdiya na roƙe ki kibar maganar nan don Allah,domin babu abin da zai saka ni sai tarin baƙin ciki.A halin yanzu wannan ba shi ne a gabana ba,ina son na koma gurin Mama ina jin ban kyauta ma ta ba,duba ga irin wahalar da na ke sha,wallahi ji na ke komai na duniyar ya yi mini zafi. Sai ta saki kuka sosai tare da miƙewa tsaye, da nufin ta fice da da falon,amma wani irin jiri ne ya ibe ta,wanda ya saka ta koma da sauri ta zauna,tare da rintse idanunta. " Haka ne ba ki yi mata adalci ba,amma ki gode ma Allah da iyayen A.m su ka karɓe ki,in da ace kin haihu ne ya karɓi ɗan sa,da wane irin ido za ki kalli Mama?" "Duk da haka ban yi mata adalci ba alhalin yanzu,iya tsananin wahalar da na ke ciki,ya kamata na gane kuskuren da na aikata." Sai ta ƙara sakin kuka." Ki yafe mini Mama ina nan dawowa gareki na nemi yafiyar ki." "Ya kamata ko da za ki koma gurin Mama,ki nemi mutuncin kan ki a gurin Ya A.m,saboda abin da ya yi a gaban iyayenmu ya ƙona mini rai sasai,yana tare da ke amma ya dubi tsabar idanun ki ya ce baya sonki a gaban kowa." Juwairiya ta kalle ta da kamar ba za ta ce ko komai ba,amma kuma ganin yadda ta mai da hankalinta da damuwarta gareta, amatsayin ta na yar'uwar sa,sai ta ce. " Haka ne amma ni ban ga abin damuwa ba,tun kafin mu yi aure yake gaya mini ba ya sona,yana da matar so ni kuwa auren wucin gadi muka yi da shi,duk da ada ina masifar son sa, amma haka ya din ga wulaƙanta ni yana kirana da matar shige,a yanzu na yadda ni matar shige ce,kuma na ƙosa mu rabu na huta da warin da nake ji a jikin sa." Hamdiya ta kwashe da dariya tana kallon ta." Yanzu babban Yaya ɗan gayu mai ji da ƙwalisa kike cewa yana wari?" " Wallahi wari yake yi mini mai haɗe da ƙarni sam ba na so na ji muryar shi,sai na ji warin ya fara tunkaro ni." Ta faɗa tana zuciyarta na tashi saboda maganarsa da ta yi. " To Anty Juwai ba kya tunanin wannan wata dama ce da za ki yi,amfani da shi ki ƙwato ƴancinki a gurin sa?Kamar yadda yake nuna miki baya son ki ki nuna kin tsane shi fiye da wanda yake miki,ko da kuwa ba gaskiya ba ne a zuciyarki,sabada wani lokacin in ka nuna tsanar mutum ƙarara ko da shi ba ya ƙaunar ka,hakan ya kan sa ka ya ji abin ya dame shi matuƙa,sai ki ga da ga baya ƙauna ta zarge a tsakani" Ta ce tana kallon ta amma ganin ba ta ce komai ba,sai ta ci gaba da magana tana cewa. " Allah ki nuna mi shi sam ba kya son ganin sa,saboda cikin da ke jikinki a yanzu zai so ya din ga zama kusa dake yana ririta cikin,ke kuma sai ki yi amfani da damarki ki wahalar da shi,domin duk faɗin da yake ba ya son ki ni ina ganin yana yaudarar kan sa ne,saboda in da ba ya sonki,ba zai aure ki ba koda kuwa na kwana ɗaya ne,duba ga matsayin sa da na iyayen sa." " To a yanzu mai kike so na yi?Bayan kin san ni ko kallon sa ba na son yi."Ta ce da ƙosawa saboda ita ambatar sunan sa da take yi,ya ishe ta sai tana jin kamar za ta yi amai. " Ki wahalar da rayuwar shi sam kar ki nuna tausayi,kuma kar ki bari ya matso kusa dake."Ta faɗa ba tare da shakku ba. " In dai wannan ne kar ki damu fiye da haka zan yi mi shi."Ta ba ta amsa tare da mai da kanta ta kwanta,saboda wani irin bacci da take ji. Tun Momi na ɗari-ɗari da ita da mutanen,gidan har suka saki suna nuna mata wani irin ƙauna,da abin da ke cikinta.A.m gabaki ɗaya sai ya ji hankalin sa ya tashi,don ya so ace masoyiyarsa ake nuna wa ƙauna ba ita. A.m ya ba ma Zainab lokaci zuciyarta ta huce sannan ya je gareta,saboda ya san cewa a halin yanzu babu abin da zai ce mata ta kula shi,Daddy ya gaya masa kutu mahaifinta yake so ya kai a ba ta takaddarta,in har A.m ya ƙi sakar mi shi ƴa,yayin da shi kuma ya dage don bai ga abin da zai saka ya rabu da ita ba. Juwairiya na zaune akan ɗaya daga cikin kujerun falon Hajiya Binta,abokiyar zaman Umma,ita da Hamdiya da ba ta daɗe da dawowa daga makaranta ba. Hajiya Binta ta fi kowa tarerayarta a cikin gidan,saboda ta ya ba da hankalinta sosai kuma mace ce mara damuwa da ɗora ma kai jiji da kai,ku san duk ta fi kowa sauƙin kai a gidan. Fate ne ta yi mata da ga ɗan manja sai magi da gishiri,in ban da kwatira ta ciki babu abin da zai saka ta sha. Hira suke yi sosai da Hamdiya sai Hajiya Binta da take saka musu baki jefi-jefi,yayin da hankalinta yake kan tibi tana kallon shirin daɗin kowa. A.m ya yi sallama ya shigo cikin shadda kalar bula mai kyau. Daga ɗakin mahaifiyarsa yake aka ce mi shi tana nan,ya taho da zumuɗinsa ya ganta saboda tafiya da ya yi,zuwa cairo har tsawon sati ɗaya. Idanunsa akan cikin shi burinsa ya ga ya fara girma don har yanzu shakkun tana da ciki yake yi ya ƙosa ya ga cikin ya fito. " A a lale barka da mutanen turai."Hajiya Binta ta faɗa tana kallonsa da ya yinsallama ya shigo.Gefenta ya zauna yana shafa kansa. Bayan ya gaishe ta ya kalli Juwairiya da ta haɗe girar sama da ƙasa,ba tare da ta kalle shi ba ta kauda kanta gefe,tana shan faten duk da ta ji ya fitar mata a rai,saboda ƙamshinsa da ta shaƙa. Hamdiya ta gaishe shi ta fita Hajiya Binta ta miƙe tana faɗin." Bari na kawo maka abinci Momi ba ta dawo daga gurin aiki ba." Bai amsa ba ta shige kicin don haka ya ɗago kan sa ya watsa mata wani kallo da ƙyamar a faten da take ci. " Matar shige ya babyna da fatan ki na kula min da shi?Ba ki bar shi ya yi kukan rashina ba." Wata uwar harara ta sakin mata kullum a zaman su tana ƙara sanin A..m, baya ƙaunarata kamar yadda yake nuna mata,sam bai gaya mata ya yi tafiya ba. Ganin taƙi tanka mishi sai ya tashi ya koma gefenta tare da rungumota gabaki ɗaya yan faɗin." Allah Sarki baby na yi missing ɗin ka bari na ji lafiyarka." Juwairiya da ƙarfinta ture shi gefe tana toshe hancinta,yayin da ta fara kakarin amai. " Don Allah ka rabu da ni kar ka ƙara matsowa kuda da ni! Ba na sonka kuma ba na son na ji ƙamshin turaren ka.Wallahi wani irin wari kake yi,wanda i don't want to say ga irin sa." A.m ya zaburo cikin ɓacin rai ya kalle ta da ƙarfi ya ce." Ke kar ki raina mini wayo kin ce ba ƙya son ƙamshin turaren na canza kan dole, yanzu wannan daga Cairo na siyo shi,za ki raina mini wayo ki ce ina wari,bayan duk zuriyar ku babu ba wanda zai iya siyan turaren."Cikin ɗaga murya yake maganar,amma sai ta kalle shi ta saki ɗan ƙaramin tsaki,wanda ya ji ran sa ya ƙara ɓaci sosai. " Ya akai yi Abdurrahman tana fama da kanta kake ɗaga mata murya?"Hajiya Binta ta faɗa lokacin da ta kawo masa abinci ta ije a gaban sa. Hararar Juwairiya ya yi ganin tana mi shi wani kallo sama-sama yana mamakin rashin kunyar da take so ta fara yi masa. " Ya zan yi da ita gabaki ɗaya tun da ta samu ciki take yi mini gani-gani,duk turaren da na sa sai ta ce bai yi mata ba,tana son ta nisanta ni da babyna."Da shagwaɓa ya yi maganar da kuma murya mai alamun ɓacin rai. " Sai ka yi haƙuri ka san sha'anin mata in suna da ciki,wataƙila ba ya yi mata daɗi ne saboda ana fuskantar haka." Kasa cewa komai ya yi saboda takaici sai hararata yake yi,yayin da ita hankalinta ba shi garesa goruba take ta gwawiya. " Cinyau kawai daga samun ciki komai kika samu kici,kuma ni takaicina cimar talakawa da kike yi."Ya yi tsaki ya ƙara cewa."Dama duk abin da ka haɗa da talaka sai ya ba ka haushi,yanzu fisabilillahi mai za ki ci da waɗannan cimar wahalar da kike yi,to wallahi ba za ta saɓu ba dole ki canza ni zan tsara miki kalar abincin da za ki ci,kar yarona ya fito yana cin cimar talakawa." Juwairiya da takaici ya ishe ta tun da yake gaya mata magana bai taɓa damunta kamar na yau ba,ta buɗe baki za ta mayar masa magana,amma idanun Hajiya Binta ya saka ta kasa,sai kawai ta shige ɗakin ta yi kwanciyarta. " Dole fa sai ka jure dama haka mata suke yi in suna da ciki,in ka yi haƙuri laulayi ne yana fara girma za ta daina." Ta ce masa tana kallon sa da murmushin abin da ya ce." Haba ji fa don Allah wannan abin mai kama da icce take ciki,salon ya karce yarona."Ya faɗa bayan ya ɗauki goribar yana juyata a hannunsa. Miƙewa ya yi lokacin da take dariyar abin da ya ce." Bari na gaisa da baby na dawo ko hutawa ban yi ba."Ya wuce ɗakin da ta shiga. Juwairiya na kwance sai ji ta yi mutum ya kwanta gefenta tare da ɗora hannunsa a cikinta. Kafin ya yi magana wani irin amai ya turnuƙo ta shiga kyara shi a jikin sa.Am hankalinsa ya tashi sosai ran sa kuma ya ɓace,ganin yadda ta ɓata mi shi jiki da amai. " Wannan wane irin rainin wayo ne?Amai za ki yi mini a jiki."Ya faɗa yana wani yatsina fuska tamkar shi ma zai yi amai Ɗaga idanunta ta kalle shi a wahalce ta tabbata A.m ba shi da tausayi a zuciyar sa. Miƙewa ta yi za ta shige bayi ta ce." Na ce ba na son ganin ka balle na ji warin jikinka,ba ciki kake da buƙata ba?Meye na ka da sai ka addabi rayuwata,in na haihu sai ka yi yadda kake so da babyn, amma kar ka ƙara kusa toni,saboda babu wanda na tsana fiye dakai a duniya sa..." " To tun da ba kya sona sai ki zo ki kashe ni!An gaya miki ni ɗin son ki nake yi,kawai saboda na ji ɗumin yarona nake matsowa garaki.Aikin banza kawai."Ya ce da ƙarfi saboda ya ji zafin tsanar shi da take faɗin tana yi,a tunanin sa ba wannan lokacin ya kamata ta nuna masa ba ta son ya matso gareta ba,saboda yanzu yana buƙatar ya din ga jin girman babynsa. Ƙoƙarin cire rigar da ta ɓata ya yi ya ije mata a gefenta." Kin san Allah sai kin wanke rigar nan,kuma in mutuwa za ki din ga yi ba amai ba sai na din ga jin motsin babyna saboda babu uban da ya isa ya hanani kuɗi na biya."Ya fice cikin ɓacin rai.Tsaki ta yi ta gyara jikinta ta koma ta kwanta Bacci ya soma ɗaukarta ta ji ƙarar waya da sauri ta miƙe ganin numbarsa ne ya sa ta datse kiran ta koma ta kwanta,sai dai yawan kiran da yake yi ya sa ta ɗauka ba tare da ta ce komai ba. " Hello ki na ji na?"Ya tambayeta cikin ƙosawa. " Umh." Kawai ta ce mi shi ba tare da ta ƙara cewa komai ba." Na kasa tafiya gida ina falon momi don Allah ki zo ki gaya mini kalar turaren da kike so na din ga sawa,amma ki bar ni na din ga jin lafiyar babyna don Allah." Ta yi shiru tana tunanin mai za ta ce mi shi sai ta ji ya ƙara cewa." In dai a kwai kalar ƙamshin da ya yi miki,ki faɗa mini zan siye shi ko nawa ne." " Ni babu ƙamshin da nake so sai humrar da Hamdiya take shafawa."Ta ce da shi. Kamar tana ganin sa ya ware idanun sa da ƙarfi ya ce." Amma ba ki da hankali ni ne zan shafa turaren humra mata fa suke sawa."A ƙufule kuma cikin muryar tsawa ya gaya mata duk da ya san A.k ya gaya mi shi,ba a yi ma mai ciki tsawa,amma abin da ta ɗauko na rainin da ta ɗauko ba zai ɗauka ba. " In ba za ka shafa ba dole ne dama ban ce dole sai ka shafa ba,na san ta mata ce, ita take birgeni kuma nake son ƙamshinta,don haka ka sha zaman ka,ba dole sai ka zo in da nake ba ko ka taɓa jikina,don yanzu kamar yadda ka tsane ni baka son wallahi na fi ka tsanar ka." Ɗif ta kashe wayar har wani huci take ita kanta ta san ta koyi tsiwa,wanda ta rasa gane dalilin haka kowa ma haushin sa take ji. A.m da ya yi sagalo da waya a hannunsa tsananin mamakinsa ya kamata,tunaninsa yaushe ta canza. Hamdiya ya ƙwala ma kira sai ga ta ta fito da sauri." Don Allah sis turaren da na shafa ba shi da daɗi?"Dariya tambayar ta ba ta don ta san kanun,amma sai ta ƙunshe dariyar ta kalle sa yadda ya ci magani ran sa a ɓace ta ce."A a yana da daɗi Ya A.m duk turaren a kwai daɗi da fatan ka yi mana tsarabar sa?" Tsaki ya saki." A a wancan ƴar rainin wayon ta ce wari nake turaren bai da ƙamshi,tun da ba ta son turaren zan kawo miki sai na canza wani,yauwa ta ce turaren da kike shafawa take so humra ina son ki ba ni."Ya faɗa ba don yana so ba ran sa na suya saboda ta ce yana wari,kamar shi duk wanka da gayu da yake yi. Duk yadda ta so ta ɓoye dariyar sai da ta dara ganin yadda ya yi." Mai za ka yi da humra ta mata ne f.." " Ya kike so na yi kwata-kwata ta hanani in ji ɗumin babyna ni kuma ba zan iya zama ba tare da jin ɗumin shi ba."Ya faɗa ba tare da ya ji kunyar ta ba. Ganin yadda ya yi maganar ba wasa sai ta shige ɗaki tana dariya ta kawo masa. " Bari na shafa sai na je." Ya faɗa yana sinsinar kwalbar turaren amma bai ji wani daɗin da take da shi ba. " Da ka yi haƙuri sai ka canza kaya ka shafa ka dawo kar ta ƙara wani amai,tun da a kwai ƙamshin wancan turaren da ba ta so a jikinka."Ta ce da shi. Ficewa ya yi ya nufi motarsa ba tare da ya tanka mata ba,shi a ganin sa Juwairiya raina mi shi wayo ta yi,shi ya sa take faɗin yana wari. Bai zo gidan ba sai washegari gabaki ɗaya kunya ta kama shinda ya fara shafa humrar sai ya ji sam ƙamshinta ba ta yi masa ba,amma kan dole ya shafa ya ɗauki wayarsa da ya gama tura ma Zainab tsaƙon text na ban haƙuri da gaya mata dalilin da ya saka ya aure ta,ya sauko ƙasa. A.k ya gani zaune a falon wanda tun ranar da bin ya faru bai ƙara ganin shi ba,har ya yi tafiya ya dawo sai yau. Kamar yaro ya duƙa lamun yana ba shi haƙuri tare da ƙama kunninsa duka. A.m da ke saukowa yana ganin sa ya ɗaure ya kauda kan sa don ya ba shi matuƙar haushi,wato da kashe shi za a yi sai dai a kashe shi kenan,shi ya gudu don haka ko kallon in da yake bai yi ba ya kama hanyar fita Da gudu A.k ya ruga ya kama hannunsa yana roƙonsa tare da yi masa dariyar ƙeta. Da takaici ya ishe shi bin shi ya yi da gudu suka kama tsere-tsere kamar wasu yara,har A.m ya riƙe hannunsa tare da ɗaukar filon kujera,ya din ga maka masa a jiki shi kuma yana dariya. Da ya gaji sai ya faɗa jikinsa suna haki can kuma suka saki dariya suka tafa. " Wato ka gudu ka barni duk abin da zai faru ya faru ko?Wallahi ban san ba ka da mutunci ba sai a lokacin sam ba ka cika aboki ba." Dariya ya yi." Ah to ya kake son na yi kaga laifina haka kawai yadda Abba ya harzuƙa so kake na ja ma kaina?Ai tsunttsun da ya ja ruwa...." " Aiko na sha mari sosai kumatuna har sai da suka yi."Ya faɗa masa jin abin da ya ce. Dariya suka ƙara yi sannan A.m ya miƙe." Well zan je na ga babyna ka san mun shiga da ga ciki,yanzu ina da wanda zan kula da shi so yanzu lokacin sa ne." " To sabon shiga ofis nake son na je saboda tsoron kar mu haɗe na fara zuwa gidan ka sabon shiga." " Ni fa ƙamjin turaren humra nake ji na mata ko Zainab ta dawo ne?"A.k ya ce yana wani shinshine-shinshine. Bugu ya kai masa a baya." Gulma babu kyau ban sani ba."Dariya ya yi ." Allah da gaske nake yi kamar irin na Maman Najwa da take shafawa,na sani ko lallaɓo abin ka ta dawo."Ya ce da shi lokacin da ya buɗe mota zai shiga. " Ba ita ba ne wancan ƴar rainin wayon ce,wai ba ta son ko wane irin turare sai wannan turaren,har yanzu cewa take ina wari ka san Allah bacin cikina da ke jikinta da sai ta gane ba ta da wayo da take faɗin ina wari." Dariya sosai ya yi." Ikon Allah sai haƙuri haka yawancin masu ciki suke yi,amma mafi yawancin mazaje ba sa ganewa sai suna ganin kamar ƙarya suke yi,bayan da gaske iya gaskiyar su suke faɗa.". Rufe motar ya yi." Ok bari na je mu gaisa sai na shigo."Ya ta da motar sannan A.k ya wuce gurin motarsa. A.m ya yi sallama a cikin falon mahaifiyarsa wacce ya tabbata tana gurin aiki a wannan lokacin,kamar yadda ya yi tunani haka ne kuwa don babu kowa sai yan aiki da suke ta hidimar su. Kai tsaye ɗakin da ya san take ya nufa a ƙofa suka kusan karo, da Hamdiya ta ta fito da gudu da kofin tea a hannunta tana kurɓa. Matsawa ya yi gefe ganin yadda take sauri kamar za ta tashi sama." Barka da zuwa Ya A.m na yi latti sosai so by." Ta fice ba tare da ta bari ya amsa gaisuwan ba."Shirmanmun yara kawai mutum ya san yana da lecture amma ya tsaya yana ɓata lokacin sa."Ya ce tare da tura ƙofar ɗakin. A.m da ya yi turus a tsaye gani tana bacci ya yi kamar ya juya,saboda abin da Hamdiya ta rubuto masa har da ba a tashin mai ciki da ga bacci. Sai kuma ya fasa ya yanke shawarar ya gaisa da shi kawai a hakan. Hannunsa ya saka ya ɗaga rigarta ya ɗora hannunsa a lafaffen cikinta da bai nuna alamun tana da ciki ba.Tsaki ya yi don shi ya matsu ya ga cikin ya fito. Juwairiya da take bacci ta ji kamar an taɓa ta kafin ta buɗe ido sai ta ji ƙamshin A.m da ta tsana. Da sauri ta buɗe ido ta yi ido biyu da shi da yake tsaye yana taɓa cikinta. Ture shi ta yi tare da miƙewa da gudu ta ruga bayi.Tsabar takaici ya sa A.m tsayuwa kamar an dasa shi har ta gana amai, ta fito ta tsaya can nesa da shi yayin da miyau ya taru a bakinta. " Na lura iskanci da rashin mutunci yake saka ki kike mini wulaƙanci,kin mai da ƙamshin jikina sai kace warin kashi da na matso kusa dake ki fara amai,to ki sani wallahi ko kayan cikinki za ki mayar sai na din ga gaisawa da babyna,don na lura so kike kawai ya shaƙu dake ke kaɗai saboda in na raba ku,ya ne me ki,don ki sani ba zan zauna dake ba kamar yadda iyayena suka faɗa mini." Tsaki ta yi ta tofar da miyau sannan ta yi mishi kallon banza ta ce." Na lura ba turaren da ka shafa ba ne na tsana,kaine na tsana kake mini warin da ya fi na kashi ɗoyi,don haka kai ya dama in ka rabu da ni,saboda in zan din ga jin irin wannan warin da nake ji a jikinka,to zan yi fatan Allah ya nisanta ni da kai har ƙarshen rayuwata." Cikin mamaki ya tsaya yana kallonta a ran sa tunani yake to ko dama yaudarar sa take da take cewa tana son sa,jin irin kalaman da take mi shi,wai yaushe ta zama haka duba ga da ko kallon sa cikin ido ba ta yi,sai hawayen banza da take mi shi,lallai ya yi sake ta raina shi. " Tun da mun tsani junanmu na ji daɗi sosai kin ga rabuwarmu za ta zo cikin sauƙi,amma wallahi ba ki isa ki hana ni jin ɗumin babyna ba." Da sauri ya matso tare da ƙanƙame ta kamar zai mai da ta cikinsa. Juwairiya ta saka kuka da ƙarfi ji take da ya rungume ta kamar ana soka mata allurai,yayin da wani amai ya ƙara ta so mata. Momi da ta dawo sakamakom mantuwar da ta yi ta ji kukan Juwairiya da ƙarfi,duk da ta ga motar A.m a gidan,amma kukan da ta saka da ƙarfi ba na lafiya ba ne. Turus! Ta yi tana kallon sa yayin da kunya ya kama dukannin su. Shafa kan sa ya yi." Momi rashin mutunci take mini wai wari nake yi duk iya gayuna,shi ya sa na murɗe mata baki don ni ba na ɗaukar raini." A kunya ce ya faɗa ganin ta gan shi rungume da ita." Ba na son iskanci maza ka tattara ku tafi gidan ku,don ta ce kana wari shi ne za ka mata irin wannan matsar ina falo fa na ke jin ƙarar ta,kaman ta abin da yake cikinta." " Na sani raina ni ta yi da yawa don kawai ta samu ciki,to ta sani ba zan ɗauki raini da ga gareta ba.Kuma Momi ta zauna a nan kawai har ta haihu "Ya ce da ita saboda sam baya son ta ƙara komawa gidansa,shi burinsa ya san yadda zai yi ya dawo da Zainab. " Ka san Allah gobe zan tura masu aiki su gayara muku gidanku ku je can ku ƙarata in kun so ku kashe kan ku."Ta juya ta shige ɗakinta don ta ɗauko abin da ta manta. A.m ya juya ya kalle ta tare da banka mata uwar harara." Kin san Allah ki gaya musu anan za ki zauna in kika bari aka tilasta mini yaga-yaga zan yi da naman jikinki,don kullum ina jikinki ina jin ɗumin babyna ina ya so duk abin da zai faru dake ya faru.Bayan nan matar so za ta dawo in ba so kike ta yi miki dukan mutuwa ba." Kwatankwacin hararar da ya ke masa ta mayar masa ko in ce fiye da haka ta ce." Allah ya ba ka sa a in ka so ka shige cikin jikina ka zauna ba ka raɓe ni ba,amma ina gaya maka wallahi in ka takurani zubar da cikin nan zan yi sai na ga ƙaryar raɓar jikina tun da na gaya maka ba na son ka na tsane ka tsana mai tsanani,sannan matarka ta dake ni ta daɗe kai za ta yi ma illah,kuma wallahi in har ka yadda na koma gidanka sai na hana ka ko shan ruwa a gidan kai da matarka?..." Da sauri ya kawo mata shaƙa yayin da idanunsa suka yi jajir jin tace za ta zubar da ciki. Juwiriya ta takura ta tsandara ƙarar saboda hankalinta ya tashi ƙwarai ganin yadda ya canza kammanni,ƙarar ya saka Umma ta yarda abin da ta ɗauka ta rugo ɗakin da gudu,har da ma aikatana gida. ƘARAR YA SA NI MA NA RUGA A GUJE GANIN A.M ZAI SHAƘE TA BAI JI ABIN DA A.K YA FAƊA MI SHI BA. TO MASU KARATU KU DAI BIYO NI KU JI YADDA ZA TA KAYA A TSAKANIN SU YAU BAN YI TYPIND DA YAWA BA,SABODA BA NA JIN DAƊI KU YI HAƘURI DA WANNAN ANA TARE. KU CI GABA DA BIBIYAR LINTAFIN DON JIN YADDA ZA TA KAYA A CIKIN LINTAFIN NAN MAI FARIN JINI. BARI NA TUNA MUKU DA SUNAN SHI SAKACINA KO HALIN MAZA TAKU JAMILA LAWAL ZANGO JAMCY TALLAH!TALLAH!!TALLAH!!! INA ƳAN MATA DA MATAN AUREN DA SUKA SHAYAR SUKE SON MARTAR ƘIRJIN SU YA DAWO? INA MATAN DA SUKE FAMA DA RASHIN ƘIBA KO INA A ƘAME? MAZA GARZAYO KI SIYA INGANTACCEN MAGANIN GYARAN NONO DA ƘIBA,MAGANIN AN RIGA AN GWADA KUMA YA NA DA AKYAU ƘWARAI.BARI IN GAYA MIKI YAR'UWA DUK WADDA TA CE MIKI MARTABAR ƘIRJINKI,ZAI DAWO MATUƘAR JIKINKI BAI MURJE BA,TO GASKIYA KUƊIN KI KAWAI ZA TA CI. IN HAR KINA SON MAGANIN YA YI AIKI A JIKIN KI SAI KIN DAURE,KIN SHA SAFE DA YAMMA.SANNAN MUNA AIKAWA KO INA SIYAN NAGARI MAIDA KUƊI GIDA. MAGANIN AKAN FARASHI MAI TSAUƘI IN KINA SO MAZA GARZAYO KI KIRA WANAN NUMBAR ( 07088268243) KO (08144072423) Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 34* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM " Abdurrahman!" Ta kira sunansa cikin tsawa ganin ta'asar da yake son yi. " A she har hanzu ba ka da hankali wai sai yaushe za ka daina kai hannunka jikin matanka da sunan duka?Ba ka ganin abin da ke cikinta wanda ka daɗe ba ka samu ba,so kake ka yi mana asara." Da muryar tsawa take mi shi magana cikin zafi domin ranta ya ɓace sosai da ta shigo ta ga ya kai mata shaƙa. " To wai tsaya kisa za ki da za ka shaƙe ta?" Ta tambaye sa cikin ƙubula saboda ta fahimci ba shi da hankali. " Momi cikina fa ta ce za ta ƙara zubar wa,ba ki san ta ba ne ba ta da mutunci za ta iya aikata abin da ta ce,shi ya sa zan fara gwada mata sakamakon abin da za ta gani." Ya kalli Juwairiya da ta yi tsamo-tsamo cikin tashin hankali da tsoro,domin ba ta manta shaƙar da ya yi mata na asibiti. " Yarinya kin san Allah kika yi wannan gigin tare za ku tafi lahira da shi." Fakaitar idanun Momi ta yi ta kalle shi ta yatsina baki ta balla mi shi harara,tare da murguɗa baki ta kuma ƙara yatsina fuska.Cikin zafi ya ƙara nufar kanta. Momi dafe kanta ta yi ta kalle su duka sai suka ƙara ba ta haushi,ta kalli agogon hannunta ta har lokacin da aka ba ta ya wuce. " Maza kwashe kayanta yau za ta koma ɗakinta wallahi ba za ku saka mini ciwon kai ba."Ta faɗa tare da fara janyo kayanta. " Momi don Allah ki bar ni a nan ba na son na koma gidansa."Ta faɗa sai kuma ta kama kuka saboda tana tunanin yadda zaman su zai yi a gidan,sannan wa zai rinƙa tarairayarta kamar yadda su ke mata. "Momi ba zan ƙara ba don Allah ki bar ta anan yanzu ta zama ƙazamiya ba ta komai zuwa za ta yi ta ɓata mini gida."Ya ce da ita saboda yana tsoron kar Zainab ta ji tana gidan,shi da yake son ta dawo in ta ji komai zai ɓace. " Oho ko mai za ku ce yau za ku tattara ku bar mini gidana." Taƙwala ma mai aikinta kira ta ce." Kwaso mata kayan abinta su tafi,sai kun bar gidan nan zan fita." Da ya fahimci da gaske take yi sai ya ɗauki jakar da Momi ta tilasta mi shi ya ɗauka,yana hararar ta da take ta matsar ƙwalla. A mota sun yi shiru babu wanda yake tari a cikin su,A.m ya so ya yi mata magana amma da ya ga ta shigo,sai ta zauna a gidan baya ta ɗauki ɗankwalinta ɗaure hancinta da shi,wato alamun har yanzu warin yake mata. Kamar kurame babu wanda ya yi magana sai shi da yake ta jan tsaƙi. Ko da suka shiga falon zaune ta yi a falo ba tare da ta kalle shi ba,ta janyo wayarta ta kunna data ta haye whatsapp da Hamdiya ta buɗe mata,don ita da chert kwata-kwata bai dame ta ba. " A ɗakin masu aiki za ki ci gaba da zama kamar da,don har yanzu matsayin ki na nan bai canza ba."Ya ce mata yana mata wani mugun kallo. Ba tare da ta kalle shi ba ta ƙara sautin ƙarar wayarta da tsaƙwanni ke ta shigowa rututu,sai da ta nisa ta ce." Ni ma ba na buƙatar ya canza kuma ba zan zauna da mutum yana mini warin jaɓa ba,gara na ƙarashe sauran watannin da zan yi ba tare da na kusanta kaina da kai ba,don haka kar ka damu na zaɓi in da na saba zama." " Hakan ya yi ai sai ki ci gaba da zama kayan ɗakin kawai zan canza don ɗana ba zai kwanta in da talawa suke rayuwa ba."Ya ce tare da ɗaukar wayarsa ya fara hawa sama. " Aiko sai ya kwana don ba shi da mara ba da talakawan a jikin ƴar talaka ya fito ka ga shima dangin matsiyata ne." Da sauri ya sauko ƙasa kamar zai isa gareta amma sai ya fasa ya yi mata wani mugun kallo. " Ƙarya kike yi ko da ya a fito a jikinki sai da na saka kuɗina na siye ki da maƙudan kuɗi,kuma kar ki manta wacce zan ba ma wa gaba da bayanta arziki suka gada ba tsaya ba." " To dangin ƙaruna ai dai ba a canza ma tuwo suna."Ta ce tare da ɗaukar goruba ta fara ci don ta san ya tsani ya ganta tana ci. Tsaki ya yi ya haye sama ba tare da ya ƙara ko kallonta ba. Juwairiya na zaune a cikin falon ta ga ana shigowa da kayan ɗaki masu kyau,har aka gama jerawa suka tafi sannan na shiga ya yi kyau sosai. Kwanciya ta yi ba ta tashi ba sai gabda magariba,wani irin ƙulululu ta ji cikinta ya yi na yunwa,sai ta far hawaye da ta tuna irin gatan da suke mata. Kicin ta shiga ta don ta yi faten da ya zama kamar al'ada ku san shi ne abinta a kullum. Sai dai ko da ta shiga kicin ɗin warin gas ya hana ta yin komai,duk da toshe hancinta da ta yi ta kasa zama a kicin ɗin. Kayan ciye-ciyenta ta kwaso ta dawo falo tare da kunna kallo ta zauna tana ci.Gidan ta ji ya yi mata faɗi saboda babu kowa a gidan sai maigadi,A.m kuma tun da ya fita bai dawo ba. Bayan ta yi sallar magariba da ƙyar ta jira isha'i tana gyangyaɗi,akan daddumar ta kwanta sai bacci. Sai misalin tara ya shigo ganin bai ganta a falon ba sai ya yi mamaki saboda da sai ta kai ƙarfe sha ɗaya tana kallo. Ɗakinsa ya shiga ya yi wanka kafin ya zo ya yi sallama da ita,don haka ko turare bai shafa duk da yana jin wani iri,amma gudun rigimarta ya haƙura. Dariya ya yi ganin yadda ta dunƙule kanta tana bacci a dadduma sai ya shafa mata addu'a ya ɗaga ta cak ya kwantar akan gado tare da rufo mata ƙofa ya fita. A.m dake ta juye-juye a ɗakinsa shi kaɗai yana jin kewa na damunsa musamman na Zeey ɗin sa shida yake hutawa da matansa biyu,amma ɗaya ta gagare shi,don haka ba tare da wani tunani ba ya fice daga ɗakin,bayan ya fesa turaren da take so a ɗakin. Cak ya ɗaga ta don ya san ba za ta amince ta biyo sa ba,sai dai kafin ya isa da ita ta farka tana mi shi bore amma bai kula ta ba,har sai da ya dangana ta da ɗakin ya kwantar dare da rufe ƙofar. " Ki kwanta har na fara bacci Momi ta kira ni ta ce kar na sake ki kwana ke kaɗai a ɗaki,saboda gudun matsala." Bakin sa ya taɓe yake magana ba tare da ya dube ta ba,ganin yadda ta ci magani tana mi shi bore. " Amma ka san ba na son ƙamshin jikinka ba zan iya kwana da kai ɗaki ɗaya ba,sannan na yi alƙawarin babu abin da zai ƙara kawo ni ɗakin nan,saboda na gama aikin da aka biya ni." " Na sani ni ma ba wannan ya sa na kawo ki ba ko da haƙuri nake yi nake kula ki don na samu baby,amma kin san ai na wuce ajin da zan kula ki.Fatana matar so ta dawo mu ci gaba da zamanmu lafiya." Ya ce tare da kwanciya can gefen ta. " Oho ko ma me za ka ce ba ni da matsala Allah ya sa matar ladan gona nake a gareka bai shafe ni ba."Ta ce sannan ta fara mi shi bore tana yatsina fuska kan za ta bar ɗakin. " Kin san Allah ko aman me za ki yi ba zan raba kwana da ke ba,sai matar so ta dawo gara ki kwantar da hankalin ki ki kwanta ya fi mi ki." Juwairiya da ta gaji da ta kwanta bayan ta ɗaure bakinta don ta lura komai zai ta yi mi shi ba zai mai da ta ɗakinta ba,sai ta kwanta don babu yadda za ta yi. A.m da ya kasa bacci yana ta mutsu-mutsu yana jin tana ƙorafi har ta gaji ta yi bacci,amma shi ya kasa bacci. Wani irin juyi ya yi sai ga shi ya rungumota ya matseta a jikin sa. Da sauri ta ture jikinsa cikin ɓacin rai." Don Allah matsa za ka takura mini ina bacci,ka san ba na son na ji na raɓe ka." Ba tare da ya buɗe idanunsa ba ya ƙara matseta a jikinsa yana jin zafin jikinta ya yi masa daidai da sanyin jikinsa. " Ki kiyayeni har yanzu a matsayin matata kike don haka ina da ikon da zan taɓa ko ina a jikinki."Ya raɗa mata a kunninta. " Ai ba ka isa ba in ba haka ba amai kake son ka yi wanka da shi do.." " Allah ya sa abin da ya fi mai za ki yi amma saina matso kusa da ke,ko ranar da kika yi mini ba kashe ni ya yi ba,in ma da gayya kika yi,sannan ki korar mini matar so sannan ki barni maraya,ai ba ki isa ba,yanzu ɗin maneji zan yi kin san ba kamar ta kike ba." Ba tare da ta ji baƙin cikin abin da ya ce ba sai ta saka mi shi kuka sosai,jin abin da yake mata sannan tana jin duk in da ya taɓa na jikinta kamar yana ɗora mata garwashin wuta. " Ai in har ka taɓa ni ba zan yi wanka ba don ba na son na saka ruwa a kaina." " Wannan kuma ke ya shafa matsalar ki ne ke da Allah."Ya ce mata ba tare da ya fasa abin da ya yi ninya ba. Ganin da gaske yake ta ture jikinsa da ƙarfi za ta miƙe,amma sai ya saka ƙarfin tuwonsa ya riƙe ta ƙam. " Ka rabu da ni sadda ka je neman aurena cewa ka yi in samu ciki in haihu ai baka nuna bayan cikin a kwai abin da zai shiga tsaƙaninmu ba." Dariya ya yi jin abin da ta ce sannan ta ƙanƙame jikinta sosai,sai ya tsaya cak ya kalle ta ransa ya fara ɓaci. " Har yanzu matata kike so ki kiyaye ni karki kai ni bango in yi miki dole gara ki saki jikinki." "Mugu azzalimi wallahi gobe gidan Momi zan koma ko na ɗauko Hamdiya mu rin ƙa zama tare."Ta ce da shi jin ya kai mata wani wawan kis. " Allah ya ba ki sa a dama ki na da hali mai kyau da za ta karɓe ki,na san mugun halinki na ƙazanta ya saka Momi ta kore ki,ita Hamdiyar ba mahaukaciya ba ce kamar ki." Ganin abin da take mi shi ya tashi zaune da ɓacin rai ya ce." Juwairiya ki fita idona ina tausayinki ne don babyna na rantse da yanzu jikin ki ya gaya miki."Ya ce mata ran shi a ɓace. " To meye sabo a gareni ka duki matar so balle ni ai halinka ne."Da ɓacin rai ya kalleta ganin ta ƙi yadda sai ya sausauta murya. " Kar kiji ina roƙon ki gaisawa da babyna zan yi kuma maneji zan yi da zarar Zainab ta dawo ko kallonki ba zan ƙara yi ba." Ganin ba za ta kula sa bai saurara mata ba sai da ya samu natsuwa ya matsa gefe.Juwairiya da sauri ta miƙe tana kwara amai da fari biriss ya yi da ita amma gani yadda ta ke ƙaƙari sai ta ba shi tausayi ya isa gareta tare da kama jikinta. " Karka taɓa ni dama na san ka tsane ba ka sona duk abin da zai cutar da ni shi kake so." Tsaki ya yi ya koma ya kwanta kuma ya ƙi buɗe mata kofa da ta gaji ta kwanta ita ma. A.m da ya jima bai yi bacci ba yana ta tunanin canjin da ya ji a jikinta domin ta canza kamar ba ita ba,komai na jikinta ya zama wani iri wanda shi kan sa ya kasa tantance komai. Hunnunsa ya tura cikin gashin kanta yana murmushi mai ɗauke da ma'anoni wanda shi kaɗai ya san me yake nufi. Haska fuskarta ya yi da wayarsa sai yaga ta yi bacci tana saukar da numfashi a hankali,yayin da fuskarsa take wani irin haske mai walwali. Murmushi ya yi kamar ya rungumota su kwanta amma ya san mai zai faru sai ya kwanta cikin annashuwa,tare da tofa mata addu'a ya kwanta da tunani barkatai a zuciyarsa. " A.m ka tashi don Allah." Juwairiya ta ke bubbuga shi a hankalinda wata irin murya,amma sai bai ji ta ba kasancewar bai ya daɗe bai yi bacci ba. Ganin haka kawai sai ta saka mi shi kuka da ƙarfin ta.Da sauri ya buɗe ido tare da kunna fitila,ya kalli agogo ƙarfe biyu da kwata. "Lafiya mai ya same ki?" Ta riƙe cikinta tana hawaye ganin haka ya ruɗe ya kamo ta jikinsa. Ture shi ta yi ta ce." Cikina ke ciwo kuma na kasa bacci." " Mai ya faru take ciwo ko baƙin ciye-ciyen ki za ki ja mini asara."Ya ce da ita cikin ɓacin rai da ta tashe shi da tsakar dare,saboda bacci ne a idanunsa. " Yunwa nake ji kuma ɗanwake zan ci."Ta ce tana fargabar abin da zai ce mata. "Abinci da tsakar daren nan an ya ki na da hankali kuwa?" " Yunwa nake ji sosai kuma ba zan iya bacci ba sai na ci abinci,ko da na dawo banci abinci ba,sannan kai ba ka damu dani ba,balle ka tambayeni." Sai ta saka kuka tana." Allah Sarki ni dai kawai ka mai da ni gidan Momi na fi son na zauna acan,saboda kai ba ka iya komai ba sai zalinci da mugunta." A.m tun yana tunanin ko wasa take masa har ya gane da gaske yunwar take ji,tashi ya yi da sauri ya na dana sanin ɗauko ma kansa jangwam da ya yi,ya buɗe mata ƙofa ya ce cikin tsawa." Malama dallah zo ki fita gabaki ɗaya daga dawowarki kin tada hankalina ki bari gobe in na kira ki sai ki yi mini abin da kika ga dama.Ai kin san in da kicin ɗin yake sai ki je ki girka tun da kin zama cin yau,in ban da iskanci da tsakar dare za ki ta she ni,Allah ya sa ki yi girki da aljanu su tsorata ki."Ya ce a fusace yana kallonta kamar ya shaƙure ta. Turo bakinta ta yi ta ce." Babu in da zan ni anan zan kwana kuma ni ba zan iya girki da kaina ba,saboda warin gas ba ya barina na yi kuma in dai na yi girki ba ya mini daɗi,don haka kai za ka girka mini kuma ɗan wake zan ci." Tsananin mamaki ya sa shi kasa magana a ransa yake mamakin yau she ta raina shi haka da har za ta kalli tsabar idanun shi ta ce shi zai dafa mata abincin da za ta ci. " A she za ki mutu don ko da rana ba ki taɓa ganin na shiga kicin na yi ma matar so girki ba balle ke yar karan kaɗa miya,kuma in ban da kin raina,ni zan yi miki girki kici da tsakar dare ko ba ki kalli agogo ba." Ya yi tsaki ya koma ya kwanta yana jin haushin tashin shi da ta yi. Juwairiya ta takura ta saka ƙara domin har jiri take gani saboda yunwa,sai ta fara kuka ganin ya kwanta. " Ai kuwa mutuwan kasko za ayi ni da abin da ke cikina don har na ji ya daina motsi,kuma tabbas in banci abinci ba mutuwa zan yi ka ga kai ka rasa ko banza Mama tana da Ibrahim,kai kuwa matarka juya ce ba ta haihuwa" A.m da yake ji kamar ya shaƙure ta saboda takaici a she Momi wahala suke ji shi ya sa ta haɗosa da ita,amma jin abin da ta ce sai ya miƙe yana murza idanunsa,ya kalli cikinta da sauri ya ce. " Amma kin san ban iya kunna gas ba kuma ban iya ɗanwake ba." Ta so ta yi dariya ganin yadda ya yi maganar da tausayin kan sa a fuskarsa,sai ta ƙara gasganta maganar da Hamdiya ta yi mata cewar duk abin da ta saka shi zai yi,saboda cikin in ko hakane duk sai ta wahalar da rayuwar su duka. Mu je na nuna maka sannan Momi ta haɗa mini garin ɗan waken sai na zuba maka iya yawan ruwan da ake so ka kwaɓa." Tsaki ya yi ya zura duguwar jallabiya suka fice yana tafe yana tangaɗi don bacci yake ji.Haka kuwa aka yi ta nuna masa sai da ta fita ya kunna,bayan ya zuba ruwa ya ɗauko kayan garin kamar yadda ta ba shi umurni ya kawo mata tana zaune a falo da wayarta tana daddannwa ya ije mata fuskar shi babu fara'a ko kaɗan. Da ya kwaɓa ya koma kicin yana mamakin kan sa." A she haka nake son ɗana?"Sai ya yi dariya ya ƙara cewa." Na rantse duk ranar da ka fito zan rinƙa kissing ɗinka wunin ranar shi ne horan da zan yi maka son." Bayan ya saka su ƙwama-ƙwama duk da ta gargaɗe sa amma yana son ya baƙanta mata. Gyangaɗi ne ya kama shi sai ya ji muryarta da ƙarfi a bakin ƙofa ta ce." A.m." Da sauri ya duba girkin har ruwan ya ƙone saura kaɗan ya yi sauri ya kwashe sannan ya kai mata. " Ji don Allah wani irin ɗanwake ne kamar an jefi ƙato."Ba tare da ya kalle ta ba ya fara tafiya zai haye sama. " To ina za ka je nufin ka ni kaɗai za ka bari a falo tsoro nake ji." Dawowa ya yi yana harara ta." To ki zo mu je ɗakina ki ci acan bacci nake ji." " Allah ya kyauta ba zan koma ɗakin ka ba ai ka sa cin abincin zan yi."Ta ba shi amsa a taƙaice. Kan two seater ya zauna yana kallon yadda take cin ɗanwaken tana ta kushewa. Gabaki ɗaya sai ya ga ta canza kamar ba wacce ya sani ba,mai sanyin hali da haƙuri da kuka akan ya sota. " Kai wai haka masu ciki su ke yi ko tashi ce ƴar rainin wayo?"Ya tambayi kansa zuciyar sa na tafarfasa. Tun yana jiran ta gama har bacci ya kwashe shi a taƙaice a ranar anan suka kwana,sai da asuba kiran sallah ya tashe shi. " Sai ki tashi ki yi sallah saboda iskanci kalli in da kika bar mu muka kwana kamar wasu marayu,kin takure guri ɗaya ji kuma kwanciyar da kika yi salon ki cutar mini da baby."Ya ce tare da fara tafiya zuwa ɗakinsa don ya yi alwala jin amfara salla. Haka suke zaman na su gabaki ɗaya ta mai da shi ɗan aiki da ya fara ƙorafi sai ta saka kuka ta ce baby,shi kuma sai ya ruɗe ya yi duk abin da ta saka shi kullum gidan nan cike yake da kayan ciye-ciye,tun bai iya soya kalallaɓa ba har ya ƙware saboda ƙa'ida ne sai ta tashe ya yi mata ɗaya daga cikin su,tun yana ƙorafi har ya saba,gabaki ɗaya ba ya samun bacci wadatacce,kullum cikin ƙorafi take yi sannan duk wani turare ya saka Juwairiya za ta yi tsalle ta dire ta ce ba ta so,ƙamshin wanda take so shi ya kama gidan ko ina,shi kan sa yana tsoron ranar da Zainab za ta shigo cikin gidan nan. Kafin ta daina amai sun sha jarfa tun daga ranar da ta dawo duk dare sai ya ɗaukota da kan sa ,ta yi masa bore amma ya jure saboda sho kaɗai ya san yanayin da yake tsintar kan sa,amai ne dai ƙa'ida wanda kullum dare sai ta yi shi,amma hakan ba zai hana sa bin da ya yi ninya ba. A.m ya rame sai hanci kamar shi yake laulayin saboda ba ta barin sa ya huta duk da ta yi mi shi ƙorafin ya ɗauko Hamdiya,amma ya ƙi saboda ba zai iya ɗauke idanunsa a kanta ba,kuma takura musu za ta yi duba ga yadda take nuna ƙyamar sa ko kusa da ita ya zauna sai ta toshe hanci,A.k ya ke lallaɓar sa cewar sa za ta daina da cikin ya fara girma. A lokacin da cikin ya yi wata uku ya fara fitowa ya yi girma kamar ba ɗan wata uku ba,ganin fitowar cikin A.m kamar zai yi hauka don murna,wani irin kula ya nuna mata a ranar kamar zai mai da ta cikinsa,ya sa ta saka duguwar riga baƙa,wacce ta bayyana cikin a fili sosai saɓanin atamfa riga da siket ta yi ninyar sakawa,don ita kunya take ji matuƙar gaske. Fita da ita ya yi ya siyo mata kayan ciye-ciye sannan ya lodo mata kaya kamar hauka,saboda kayanta ba ta jin daɗin su tafi son doguwar riga,gidan A.m suka je matar A.k kamar za ta yi hauka tana taya sakaryar ƙawarta kishi,yadda ta ga yana mata kamar zai cinye ta,sannan ganin irin kyawu na Juwairiya da hankali sai ta tsorata tana ganin ta yi sakaci sosai. Sun daɗe a gidan A.m na ta yanga har yana faɗa musu cikin ya fito wanda take ta saka hannunta tana karewa.Suna ta zolayar shi yayin da daɗi yake ji kamar ya kashe shi wai zai ga ɗan shi ya riƙe kuma har a kira shi da Baba. Daga gidan su A.k gidan Daddy ya kai ta bayan sun jima ya kai ta gidan su,saboda na cin roƙon sa da take ta yi. Hamdiya ta ji daɗin ganin yadda yake ta yi mata sai da ya gaya ma kowa cikin ya fara fitowa,wanda hakan ya ba ta kunya sosai kamar za ta nitse,shi kuwa ko a jikin sa bai damu ba. Hamdiya ta ƙara zugeta sosai tare da ba ta shawarwarin yadda za ta wahalar da su har da Zainab da ta ji mahaifin sa ya ce yaje biko,saboda kamar sun fara saukowa. TO MASU KARATU KU DAI BIYO NI KU JI YADDA ZA TA KAYA A TSAKANIN SU YAU BAN YI TYPIND DA YAWA BA,SABODA BA NA JIN DAƊI KU YI HAƘURI DA WANNAN ANA TARE. KU CI GABA DA BIBIYAR LINTAFIN DON JIN YADDA ZA TA KAYA A CIKIN LINTAFIN NAN MAI FARIN JINI. BARI NA TUNA MUKU DA SUNAN SHI SAKACINA KO HALIN MAZA TAKU JAMILA LAWAL ZANGO JAMCY TALLAH!TALLAH!!TALLAH!!! INA ƳAN MATA DA MATAN AUREN DA SUKA SHAYAR SUKE SON MARTAR ƘIRJIN SU YA DAWO? INA MATAN DA SUKE FAMA DA RASHIN ƘIBA KO INA A ƘAME? MAZA GARZAYO KI SIYA INGANTACCEN MAGANIN GYARAN NONO DA ƘIBA,MAGANIN AN RIGA AN GWADA KUMA YA NA DA AKYAU ƘWARAI.BARI IN GAYA MIKI YAR'UWA DUK WADDA TA CE MIKI MARTABAR ƘIRJINKI,ZAI DAWO MATUƘAR JIKINKI BAI MURJE BA,TO GASKIYA KUƊIN KI KAWAI ZA TA CI. IN HAR KINA SON MAGANIN YA YI AIKI A JIKIN KI SAI KIN DAURE,KIN SHA SAFE DA YAMMA.SANNAN MUNA AIKAWA KO INA SIYAN NAGARI MAIDA KUƊI GIDA. MAGANIN AKAN FARASHI MAI TSAUƘI IN KINA SO MAZA GARZAYO KI KIRA WANAN NUMBAR ( 07088268243) KO (08144072423) Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 35* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM Zainab zaune a cikin ɗakinta riƙe da wayarta,hawaye ne ke sintiri a fuskarta da ta jiƙe sharkab da hawaye.A ranta tana jin wani irin tsananin baƙin ciki da tashin hankali mai tsanani,duk sadda ta tuna abin da ya faru tsakaninta da A m,wanda har yau ta kasa yarda wai a zahirin gaskiya lamarin ke faruwa. " Wayyo Allahna! Da gaske A.m ka guje ni saboda wata ƴa mace marar gata a duniya,da gaske jikinka da na ke kishinsa ka mallaka wa wata mace wulaƙantacciya.Me ya sa ka yi mini haka bayan ka yi mini alƙawarin ba za ka taɓa haɗa jikinka da wata ƴa mace ba?" Sai ruwan hawaye suka ci gaba da turereniya a fuskarta tana jin tsantsar baƙin ciki da kishin Juwairiya a zuciyarta. Ƙaran tsaƙo da ya shigo a cikin wayarta ya saka ta yi tsaki tare da jefar da wayar,wanda ta san A.m ne ya yi,don kusan a rana sai ya yi mata sun fi goma,amma ba ta taɓa gigin buɗe wa ba.Da wayar a kashe take barin ta sai yanzu da ta ji zuciyarta ta ɗan rage zafi ta kunna ta. " Ba zan ɗaga wayarka ba macuci azzalumi mayaudari! Ka mai da ni shashasha ka sa ina ta iyayi a cikin ƙawayena mijina ba ruwan shi da mata,ni ce mace kaɗai birnin zuciyarsa a she banza ka mai da ni rainin wayonka ya fi na kowa,yanzu da wace fuskar kake son na kalli ƙawayena suna faɗa musu?Haba ai gara a ce mutuwata na sanar musu." Sai kuma ta miƙe kamar wata zararriya ta ƙara cewa bayan ta fisge ɗan kwalin kanta ta ya mutsa gashinta da ke ɗaure tare da cilli da ribon ɗin. "Mai ya sa na rayu don na ga ranar da A.m ya yi wa wata ciki bayan ni ba na haihuwa?" Kamar wata zararriya sai kuma ta ɗauki wayarta da sauri tare da ƙoƙarin ɓuɗe saƙon da ya yi mata. " Na rantse sai na koyar da ku hankali sai na shayar da ku ruwan baƙin ciki saboda girman zunubin da kuka aikata mini." Ta ce sannan ta fara karanta tsaƙon cike da jimami da tashin hankali bayyane a fuskarta. (Zainab don Allah ki tsaya ki fahimce ni tabbas na san ban yi miki adalci ba,amma in kika fahimce ni za ki gane na yin wannan auren ne saboda ke."Kalar saƙonnin da ya turo mata ranar farko kenan.) Wata uwar ashar ta danna masa sannan ta buɗe na gaba. (I dan son Juwairiya nake yi ta ya ya za yi na ije ta a gidanki a matsayin mai aikin gidanki,haba ya kamata ki gane na yi hakanne duk saboda ke.Kin san irin yadda nake son yara .Kin ji na rantse miki da zarar ta haihu zan saketa kuma na ba ki yaron da ta haifa, ta fita daga rayuwarmu domin an halicci rayuwata da ke kaɗai.) Ire iren saƙonnin da yake yi mata kenan waɗanda ba ta dubi zuwa gare su,sai yau ta fara dubawa domin ta gaji da zama ita kaɗai zuciya da gangar jiki sun yi rashin sa,da zarar ta yi shiru muryarsa take mata amsa kuwwa ma kunnenta. " Ka cuce ni!Da na yanke rabuwa zan yi dakai sai dai na lura ba zan iya yin haka ba,domin kai ne namiji na farko wanda na ji zan iya mutuwa akan sa,amma mai ya sa ka zaɓi ka cutar da ni bayana ka san ina son ka matuƙ...." " Mijin na ki za ki yi fushi ki bar ma wata! Lallai ba ki da hankali." Momi da take tsaye ta harɗe hannunta a ƙirji tana jin abin da take cewa,ta tambayeta da mamaki a fuskarta. "Momi ya kike son na yi A.m ya cuce ni bazan iya yafe masa ba." Rungumeta ta yi tana rarrashi ta ce." Na yi magana da Hajiya rabi gobe za ku je in da na gaya miki s..." " No Momi na gaya miki ba zan ɓata aurena da wannan ba in har ba za ki taimaka mini,ta wata hanyar ba to ni zan koma ɗakina na rantse sai na ga bayanta,da kaina zan ɗauki mummunar mataki a kanta.Ita da abin da ke cikin zan bankawa wuta duk su ƙon..." " Rufe mini baki banza kawai shashasha! Ana nuna miki hanya ki na kaucewa ki je ki yi duk abin da kika ga dama,ai dama da za ki aikata ba ki nemi shawarata ba,wai ke daɗi miji ai gayi nan in da ya kaiki,duk abin da kika ga dama ki je ki yi,amma ina tuna miki mundin kika salwantar mi shi da ciki ba zai barki ba.Ita yarinyar kin san ta yadda suka yi har ya aureta kasancewar ta ƴar matsiyata." Fuuuu! Ta fice daga ɗakin ranta na zafi sosai saboda gani take ba ta da wayo,da ba zata bi hanyar da ta saka ta ba don ita ce kawai mafita a garesu. Sai ta kife kan gado tana kuka domin duniyar ta yi mata zafi sosai. Kusan sau uku yana kiran wayar ba ta ɗauka ba,sai a na huɗu kamar an saka ta dole ta janyo wayar tare da kanga ta a kunninta. " Munafiki mayaudari mai za ka ce mini na baro gidanka ba za ka bar zuciyata ta samu sausauci ba."Ta faɗa a zafafe da ɓacin rai. Ya saki naunauyar ajiyan zuciya mai ƙarfi wace ta taɓa zuciyarta,ya rintse idanunsa yana jin zafin abin da ta ce mi shi,amma sai ya daure ya ce da murya sansanya. "Zainab please don Allah kar ki kashe waya ki bari ki saurari abin da zan gaya miki don Allah!" Tsaki ta yi ta yi shiru ba tare da ta tanka masa ba. Ya cire wayar a kunninsa ya kalli wayar don a tuninsa ta katse wayar,amma sai ya ga ba ta yanke ba,sai ya fara magana da muryar da ya san yana kashe mata zuciya,yake kuma narkar da bargon soyayyarsa ya zagaye duk wata kafa da take jikinta har ta kasa gane girmar laifin da ya yi mata. " Kin san Allah ya jarabce ni da son yara ko?Sannan ki duba irin tarin dukiyar da nake da shi,amma ba ni da magaji Zey ba kya tausayin rayuwata,ke kan ki ina za ki kai ɗumbin dukiyar da kike da shi?Sannan in muka mutu ba mu da wanda zai rinƙa yi mana addu'a,duniya za ta manta da mu." Ya numfasa ko za ta ce wani abu amma sai ya ji ta yi shiru don ji take kamar ta shaƙe shi ta wayar. Wannan dalilin ya sa na ga da in ce miki mu yi adopting yaro a gidam marayu, na ga dacewar kawai na auri mace na siyi ɗan da za ta haifa." Shiru ta yi bayan ta ji duk abin da ya ce zuciyarta ta kasa yadda da lamarin da ya faɗa,ba rashin son ɗa da ba ta yi bane ya dameta don ba za ta iya wahala da shi ba,amma kuma wannan ba matsala ba ce saboda za ta iya ɗaukar mai aiki ta kula da rayuwarsa,to amma ita Juwairiyar za ta iya ɗauke idanunta daga gareshi." Abin da take ta tunani kenan a cikin zuciyarta, sannan kuma mai ya sa bai gaya mata ba tun lokacin,sai kawai ta sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi. Kamar ya san abin da ke zuciyarta ya ce." Na ƙi gaya miki ne don ba lallal ba ne ki amince,sannan kuma idanuna sun rufe sosai ina son na ga yarona a haɗa sunana da na sa,idan kika san Juwairiya matsayin matata ba za mu taɓa samun zaman lafiya,ga shi rashin faɗa miki bai yi amfani ba saboda na so ace cikin ƙarya kika yi lokacin da ta samu ciki,sai mu yi ƙaryar ciki har ta haihu." Jikinta ya ƙara yin sanyi matuƙa kamar wacce ta fito da ga firjin. " Haba dama na san A.m ba zai taɓa cin amanata ba sai yana da dalili ga shi yanzu baƙin kishina ya saka na je na tona asiri,da yaron ni zan ce na haife shi."Ta ce take wani irin mugun nadama ya shigeta ganin yadda ta kwafsa gefe guda kuma sai ta ba shi laifin ƙin gaya mata da ya yi. " Ki yi haƙuri ki dawo gareni ji nake kamar zan mutu na yi rashin waɗannan hot kis na ki masu zafi da sanyaya zuciya,yanzu aikina ya ƙare da ita ko kallonta ba zan ƙara ko kallonta ba ke kaɗai ce matata."Ya ce mata da salon muryar shi da yake rikita ta. " Na ji zan dawo duk da ka zubar da ƙimata a idanun duniya amma ta zauna a gidanku har ta haihu in ya so sai a bani yaron ita ta tafi." Gaban sa ne ya faɗi ras!Amma kuma ba zai iya gaya mata gaskiya ba,gara in ta dawo sa fuskanci wannnan matsalar. " Ba ki da matsala na zo na ɗauke ki?"Ya ce zuciyar sa da fargaba. " Ba yau ba." Ɗif ta kashe wayar tana jin haushin sa matuƙar gaske domin ya zubar mata da ƙima a gurin mutane. A.m ya riƙe waya yana kallonta sororo har yanzu zuciyarsa bugawa take yi,ya san in ta dawo ta ga Juwairiya a kwai dirama,balle ta ga yadda ta koma ta yi wani irin kyau komai na jikinta ya buɗe shi kan sa baya iya ɗauke idanunsa a kanta. Mai da wayar ya yi cikin aljihunsa ya fesa turaren da ya zamar masa dole,tun ba ya son ƙamshin har ya fara so don babu yadda zai yi,sai ya fara saukowa ƙasa zuciyarsa na ta ɗar ɗar " A.m!" Ta kira sunan shi da ƙarfi kuma cikin isa da gadara ba tare da ko ɗan girmamawa ba,ganin yana son ya fita bai kalle ta ba,duk da ya ganta a falon. Wani irin kallo ya yi mata ganin yadda ta zauna a falon riga daban zani daban sai hular sanyinsa wacce ya ba ta saboda jin sanyi da take yi,tana riƙe da remote a hannunta fuskarta cike da tsiwa,ga kayan ciye-ciye nan a gabanta da ta gama da wannan ta janyo wannan. Kusa da ita ya zo ya tsaya yana ƙare mata kallo." Ba na hana ki kiran sunana gatsai babu girmama wa ba,ko banza yanzu kya karrama sunana da Baban baby." Kallon shi ta yi a yatsine ta ce." Ba wani Baban da zan kira ka, sai ka bari wadda za ka ba wa yaron in ta dawo ta rinƙa ce maka.Kuma ni ba wannan ba ciyo ya ƙare shi nake son ka siyo mini." Gefen ta ya zauna tare da lakuce mata hanci ya shafa cikin wa da da sauri ta ture hannunsa tana hararar sa.Hannunsa ya ware ya ce. " Allah ina roƙon ka ka fito da baby lafiya na huta da wannan yarinyar da ta addabi rayuwata." Taɓe bakinta ta yi ta ce." Oho koma me za ka ce ka ce amma ni buƙata ta ka siyo mini ciwo." " Amma na gaya miki ba lokacin sa ba ne Juwairiya,Allah ko waɗanan da kika ga na samo miki wani ƙauye can aka yi mana kwatance ki tausaya wa rayuwata ki kalli yadda na koma." Ya faɗa da muryar sanyi da yake bayyana tausayi don kawai ta tausaya mi shi. " Ashe ma a kwai in da ake siyar wa ai na ɗauka babu shi ne Allah ko bangon duniya sai ka samo mini."Ta yi maganar cike da shagwaba tana game a wayarta. "To ba in da za ni don na lura abin naki rainin wayo ne."Ya ce tare da miƙewa zai fita. Juwairiya sai ta kama rigarsa ta riƙe za ta fara kuka." Allah sai ka siyo ko da yake ba zan damu ba,ai na ji an ce in mai ciki ta ga abu tana so ba a siya mata ba, yaron da tabon rowa yake fitowa kuma jikinsa baƙi-baƙi yake yi,sannan ka ji abin da Hamdiya ta ce cikin kuma na iya zubewa,gara ni zan iya ƙara wasu da yawa kai kuwa fa ƙila ni in na yi aure ƴan biyu zan fara haihuwa masu kyau ba irin ka ba babu kyau sai koɗaɗɗiyar fuska..." Buge bakinta da sauri ya yi kuma ta ji zafi ta sa kuka. " Mara mutunci kawai da aurena kike faɗin za ki auri wani ki haihu." Ya ɗaga kafaɗarsa yana mata murmushin ƙeta ganin yadda take hawaye saboda ta ji zafin buge mata bakin da ya yi. " Ji be ta mai hawayen banza har sallar dare zan rinƙa yi kar yarona ya gado ki,saboda in zai rinƙa irin kukanki ƙila na rinƙa tunaki in mun rabu." Taɓe bakinta ta yi tare da sakin rigar shi ta koma ta zauna ta ɗauki yalon Bello ta ci sannan ta ce." Kai har a kwai abin da zai saka ka tuna da ni in mun rabu,ni kam na ƙosa mu rabu na huta da addabar rayuwata da kake yi." A.m da ya tuna Zainab za ta dawo sai ya matsa ya zauna kusa da ita tare da ɗaure fuskar shi. " A kwai maganar da zan yi dake kuma mai mahimmanci ba na wasa ba,don na lura yanzu na sakin miki fuska gabaki ɗaya kin raina ni.Matar gidan za ta dawo duk wannan iskancin ki ije shi a gefe,saboda kin san ba za ta ɗauka ba yadda kike gara ni kamar wani ƙwallo,sannan maaganar turare ya tsaya iya ɗakinki dole zan canza wanda na ke shafawa domin na faranta ranta." " To ni dama na yi maka dole ne in dai ka shafa wani ba wannan ba kar ka sake kazo kusa da ni."Ta ba shi amsa kai tsaye jin abin da ya ce. Bai ba ta amsa ba ya ɗora da cewa." Maganar tashina da daddare da kike yi na yi miki girki zan daina ke ko da safe ne,saboda kin san Zainab ba za ta ɗauka ba,don tun da na ke da ita ban taɓa shiga kicin ba na yi girki,da tashina da kike yi na zauna zaman jiran ki a falo ƙarshe sai dai na kwana anan.Kin san Allah kika yi wannan gigin sai na ɓata miki rai."Ya ƙarashe maganar da nufin gargaɗi. " Wannan kuma bai shafe ni ba abin da na sa ni in har baby ya ce zai ci abinci Allah sai na zo na tashe k.." " Juwairiya ranki zai ɓace fa ki kiyaye ni." Da kaukausar murya ya katse ta jin abin da ta ce sai kuma ya duƙa a gabanta duk da bai so yin haka ba." Don Allah ki tausaya mini kamar yadda na ke son yaron jikin ki haka na ke son Zainab." Wani iri ta ji babu daɗi a ranta abu mai kama da kishi wanda ba ta gane hakan ba ya tsaya mata a maƙogaro sai ta miƙe da sauri ta shige cikin ɗakinta. " Momi ki barni Allah yau a gidan Mijina zan kwana,saboda na lura ba zan iya rayuwa in babu shi ba,kuma ya sanar da ni duk abin da ya yi saboda ni ne yana tsoron kar watarana a tilasta mi shi, ya yi aure ya sa ya auri yar talakako in ce ya siye ta don ta haifa mana baby." Zainab ce take gaya wa mahaifiyarta maganar saboda ƙwace wayarta da ta yi jin suna hira da shi. " A she ke banza ce ke anya nonona kika sha lallai na yadda ba ki da hankali." Ta numfasa saboda takaici da ya rufe mata ido ta ci gaba da cewa." Don ya gaya miki wannan ƙanzon guregen kika yadda da shi,karki manta namiji ne fa shi,yau na yadda ba ki da hankali karki bari a ƙwato miki ƴanci ki koma gidan na sa da kanki za ki dawo kina kuka,don wallahi zaman gidan sai ya so ya fi ƙarfinki." Momi ta ce cike da takaicinta saboda ta yi-ta yi da ita su je gurin Malami,amma ta bijire mata. " Ko ma me za ki ce ki ce amma ni ba zan je na ɓata aurena ba,na san A.m na sona kuma da zarar ta haihu za ta bani ɗan ta koma in da ta fito,kuma yanzu a gidansu ya ije ta." Momi da ta harzuƙa kamar ta kwasa mata mari take ji." Au haka kika ce ni da na so a zubar da cikin ne,saboda barin a haife shi kamar wani babban kuskure ne za ki yi."Ta ce mata tana son ta shawo kanta. " No Momi barin sa ya ga ƙwansa shi zai saka ya samu natsuwa, kin san in son sa ba zan so na ga yana cikin damuwa ba,kawai ya haihun hakan zai fi mana samun kwanciyar hankli." " To ai ke kika sani duk abin da ya ƙara faruwa karki ƙara nema na ki je ciwon so ya kaiki ya baro." Ranar da A.m ya je ɗaukota ya sha faɗa sosai a gurin Daddy. Daddy ya yi masa faɗa sosai kamar zai kai mi shi duka har ya ɗora da cewa." Ka ji na rantse maka don kawai Zainab ta aikata kuskure a rayuwarta,wanda mun yi mata faɗa sosai da kuama kunyar mahaifinka da na ke ji,da albarkacin son ka da take yi maka,amma wallahi kulle ka zan yi sai igiya ta yi rarara. Sakaran banza kawai ka rinƙa dukan mace goto-goto da kai ba ka jin kunya,tun da nake da ita ban taɓa saka hannu na buge ta ba sai kai,an ce maka jaka na haifar maka." Ya numfasa tare da ɗorawa cikin zafi sa ƙunar zuciya na saboda ƙara dukan shalele da ya yi. " Na so ka sakin mini yarinya na tura ta in ingila ta yi rayuwarta a can,ai ka san kai kai ke da asara,saboda duk wanda ya yi rashin Zainab ya tafka babbar asara wallahi,ga kyau ga kuɗi da ilmi." A.m shiru ya yi don haka A.k ya ƙi rako shi don ya san dama zai ga rashin mutunci. Haka suka shanya shi kusan rabin awa yana jiran ta har ya yi fushi ya raya a zuciyarsa in har ba ta fito ba,minti biyu ya yi zai tafi,sai ga ta ta fito tana cika tana batsewa da tiren kayan lambu a hannunsa. Ware hannunsa ya yi har ta taho za ta faɗa sai kuam ta duƙa tare da sakin kuka sosai. A hankali ya ƙaraso ya ɗaga ta ya rungume." Is ok babyna na riga na gaya miki duk abin da ya fa.."Katse sa ta yi cikin kuka. " Dole na yi kuka sosai kamar yadda kake rungume ni a faffaɗar ƙirjinka haka kake mata gaski.." " Wa ya gaya miki? ai irin wannan yana faruwa ne don kana son mace,ni kuwa kin ga sam ba na sonta,kawai na tsaya na zaɓo mai kyau don kar a haifa mana baby mummuna."Ya ce da tsigar rarrashi." Tsarata ya ci gaba da yi yana gaya mata kalamai masu kwantar da zuciya,har ta manta komai ta miƙe akan za ta ɗauko kayanta su tafi. Momi kuwa ko kallonta ba ta yi saboda ta yi fushi da ita sosai,sai haɗa kayanta take yi cikin sauri kamar wacce za ta tashi sama,ko da ta yi mata sallama tsaki ta yi ta juya mata baya. A.m dake tuƙi idan ya juyo ya kalle ta sai ta balla masa harara ta saki tsaki tare da kauda kanta. Wani irin fargaba yake damun sa in ya tuna Juwairiya na gidan,kuma ya san Zainab ba za ta yadda ba,sannan a halin yanzu ba zai yadda ta yi nisa da shi ba,saboda in ya ga ɗan cikin da ya fara fitowa sai yaga kamar ɗansa yake gani,uwa uba ga ɗumin jikinta da yake masifar so ya ji sa a kusa da ita,duk da yaki ce sa da take yi. " Zainab ina son za mu yi magana don Allah ki natsu ki fahimce n ." " To mai kake so ka gaya mini yanzu kuma?Don Allah ka ƙyale ni na gaji da yaudara ta da kake yi kana gaya mini kalaman bakinka na yaudara." Ta katse shi da murya mai ƙarfi saboda haushi ya ke ba ta sosai ji take kamar ta shaƙe shi,domin ya ha'ince ta ya ije mace a gidanta ba tare da ta sani ba. Kawai sai hawaye suka fara turereniya a fuskarta daga ƙarshe fashe mi shi da kuka ta yi sosai. " Allah ka na gani A.m ya cuce ni na yi dana sani son ka da nake yi,ga shi na kasa iya cire shi a raina.In kana son ka samu baby mai zai saka sai ka kawota cikin gidana,har yanzu in na tuna akan gadona kake kwana da yarinyar nan,ina ji kamar na sha guba na mutu." Shiru ya yi ya riƙe sitiyarin motarsa yana kallonta yayin da yake ta tsaƙe-tsaƙe a zuciyarsa. " Duk ya riga ya wuce wannan meye amfanin dawo da hannu agogo baya,sannan na gaya miki dalilin aure k.." " Don Allah kar ka taɓa ni baka san ƙyamar ka nake yi ba,mu tafi kawai ka tada motar duk abin da za ka ce mini in mun je gida ka gaya mini."Ta ce mi shi yayin da ta ga ya yi nufin kamata. Kifa kan sa ya yi akan sitiyarin yana jin kukan da take na damun sa,amma ya san za ta yi fiye da wannan in ta ganta a gidan,da yadda ta sake abin ta don shi kan sa tsoron rigimarta yake yi,shi ya sa ya so ya yi mata bayani amma ta ƙi sauraran sa,kawai sai ya tada motar komai ta fanjama fanjamjam. TO MASU KARATU KU DAI BIYO NI KU JI YADDA ZA TA KAYA A TSAKANIN SU YAU BAN YI TYPIND DA YAWA BA,SABODA BA NA JIN DAƊI KU YI HAƘURI DA WANNAN ANA TARE. KU CI GABA DA BIBIYAR LINTAFIN DON JIN YADDA ZA TA KAYA A CIKIN LINTAFIN NAN MAI FARIN JINI. BARI NA TUNA MUKU DA SUNAN SHI SAKACINA KO HALIN MAZA TAKU JAMILA LAWAL ZANGO JAMCY TALLAH!TALLAH!!TALLAH!!! INA ƳAN MATA DA MATAN AUREN DA SUKA SHAYAR SUKE SON MARTAR ƘIRJIN SU YA DAWO? INA MATAN DA SUKE FAMA DA RASHIN ƘIBA KO INA A ƘAME? MAZA GARZAYO KI SIYA INGANTACCEN MAGANIN GYARAN NONO DA ƘIBA,MAGANIN AN RIGA AN GWADA KUMA YA NA DA AKYAU ƘWARAI.BARI IN GAYA MIKI YAR'UWA DUK WADDA TA CE MIKI MARTABAR ƘIRJINKI,ZAI DAWO MATUƘAR JIKINKI BAI MURJE BA,TO GASKIYA KUƊIN KI KAWAI ZA TA CI. IN HAR KINA SON MAGANIN YA YI AIKI A JIKIN KI SAI KIN DAURE,KIN SHA SAFE DA YAMMA.SANNAN MUNA AIKAWA KO INA SIYAN NAGARI MAIDA KUƊI GIDA. MAGANIN AKAN FARASHI MAI TSAUƘI IN KINA SO MAZA GARZAYO KI KIRA WANAN NUMBAR ( 07088268243) KO (08144072423) Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE. *SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 36* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM Shiru ya biyo tsakanin su babu mai magana kowa yana tsaƙe-tsaƙe a zuciyarsa,sai kukan Zainab da sheshsheƙa da yake tashi a hankali. Ko da suka isa gidan da gudu ta fice daga cikin motar ba tare da ta kalle shi ba,ta haye sama kai tsaye bayi ta wuce,tare da sakar ma kanta shower tana wankan dole,don kawai kar ya kula ta. A.m da ya gaji da zama tashi ya yi ya leƙa bayin don ya tabbata ta kammala wankan,ƙin fitowa ta yi,yana leƙawa ya gan ta a tsuguna tana kuka sosai. Jikinsa ya yi sanyi sosai shi kan sa bai yi tunanin tana kishin sa haka,don gani ya yi abin ya wuce misali,saboda duk ta bi ta rame kamar ba Zainab ƴar ƙwalisa ba. " Zainab don Allah ki fito daga bayin nan ki zo mu fahimci juna,karki saka wata cuta ta kama ki."Ya ce da ita cikin tsananin tausayin ta. " Ka fita don Allah na dawo gidanka ne don ba zan iya rayuwa babu kai ba,amma hakan baya nufin na sake amincewa da kai."Iya abin da ta ce mi shi kenan ta ƙara sakin kuka,mai tsuma zuciyar mai sauraro. Da ya gaji da tsayuwar jira sai ya fita falo don ya duba lafiyarta,amma sai bai gan ta a falon ba,cikin sanɗa ya leƙa ɗakinta sai ya gan ta kwance tana bacci da sauri ya ja ƙofar ya fita,tare da sakin ajiyar zuciya mai nauyin gaske. A.m dake tuƙi ya fita don ya siyo musu abin da za su ci,duk da cewar mai aikin da Momi ta kawo musu ta yi abinci,amma ya rasa ta in da zai fara lallashinta,shi kan sa bai yi tunanin haka take ba,saboda ya gaya mata dalilinsa amma sam ta ƙi ta manta komai. Ko da ya dawo siyo musu abinci ɗakin Juwairiya ya fara zuwa,amma har wannan lokacin tana bacci. Jikinta ya taɓa sai ya ji ɗumi hankalinsa ya tashi jin zazzaɓi a tare da ita.Wayarsa ya ciro tare da kiran likita don ya duba ta,ya ije mata kayan ciye-ciyen ta ya fice daga ɗakin ba tare da ya tashe ta ba,saboda gudun rigimarta da yake tsoro. Ɗakin Zainab ya nufa amma sai ya ji ta kulle har da makulli. Bai yi ko tari ba ya juya zuwa ɗakin sa ya ɗauko spare makulli ya buɗe. Har yanzu tana zaune bayan ta yi sallar magariba hawaye yana bin ƙuncinta. " Ya kamata don Allah ki manta komai Zainab kukan ki yana cutar da zuciyata,na yi miki bayani amma kin ƙi saurarata."Ya faɗa bayan ya tallabo ta jikinsa. " Na fahimce ka kawai na kasa yadda da abin da ke faruwa a tsaƙaninmu n..."Ya katse ta da cewar. " Wallahi ba ni da nufin na cutar da ke. Ita ma katsesa ta yi ta ce." Ya wuce sam bana son ka ko ambaci sunanta don Allah ka kyaleni kawai." Ganin haka sai ya ja ta jikinsa yana shafa bayanta,kamar wata ƴar baby yayin da ita kuma ta lafe jikinsa,tana jin ƙaunarsa fiye da ta da. Ya mantar da ita komai da kalar soyayyar da yake nuna mata, wanda take ji ba za ta iya rabuwa da shi ba,sannan za ta iya zama ajalin duk wata mace da ta yi gigin raɓarsa. Da a kira salar isha i sai suka yi wanka sannan suka kwanta,a ran A.m na ta addu'a Allah ya sa kar wancan rigimammiyar ta tashe su,saboda sam Zainab ta ƙi yadda ya yi mata bayani. Juwairiya bayan ta yi salla ta zauna tana cin kwaɗon zogala, wanda ta saka mai aiki ta yi mata tun yamma,saboda jikinta da babu daɗi ta kasa ci.Wanka ta shiga duk da ba ta son ta yi amma jin jikinta yake yi mata wani iri. Likita da ya shigo ya kira wayarta da A.m ya tura mi shi da cewar in ya zo ya kira ta. Duk yadda likitan ya so ya yi mata allura ta ƙi, don ita ba ta ga wani ciwon da zai saka A.m ya kira likita ba,ta lura mugu ne so yake kafin ta haihu duk ya tsire mata jiki da allura. Cikin dare misalin biyu da kwanta kasa bacci duk da ba ta yi ninyar zuwa ɗakin su ba,kamar yadda Hamdiya ta yi ta zuga ta don har text ta yi mata,amma ita tsakani da Allah yunwa take ji matuƙar gaske,wanda take jin za ta iya shiga cikin wani hali kafin gobe. " Inna lillahi A.m ɓarayi ne suka shigo cikin gidan nan!"Zainab ta faɗa da tashin hankali a fuskarta jin ana ƙwanƙwasa musu ƙofa. A.m da bai samu ya rintsa ba har sai da lokacin da take tashin sa ya gota,sannan wani nauyaryar bacci ya ɗauke shi. Ƙara juyawa ya yi tare da rungumo ta amma sai ta ture shi cikin tashin hankali tare da girgiza shi da ƙarfi. " Na shiga uku! Allah ya sa ba ƴan garkuwa da mutane ba ne suka zo."Ta faɗa a tsorace wanda ya saka A.m miƙewa da sauri cikin tashin hankali. Ji ya yi kamar ya ɓoye saboda bai san ta in da zai fara ba. Ƙofar ya nufa da tsoro a fuskarsa har zai murɗa ta riƙe shi ta ce. " Don Allah karka buɗe su cutar da kai." " Mene ne". Ya ce cikin wata irin murya da ya saka ta kalle shi da shakku a fuskarata. " Tambaya kake mene ne A.m?Ka san waye a tsaye a ƙofar ɗakin ne?"Da tashin hankali ta faɗi tana masa wani irin kallo. A.m da ya yi tsuru-tsuru kamar ɓarawo a hannun mata sai kawai ya buɗe ƙofar ta bayyana, da take tsaye da kayan bacci duguwar riga a jikinta da hijabi da ta ɗora ga ɗan titsin cikin da ya fara fitowa a jikin hijabi. Zainab ta girgiza idanunta ta ƙara ta kuma kallonta da ta yi tsaye fuskarta cike da tsiwa,tana musu kallon kamar ta ga kashi har da wani ɗan girgiza take. Ta ƙara girgiza idanunta ta kuma goge fuskarta a ranta tana tunanin anya Juwairiya ce ta canza kala ta dawo haka. " Ka san lokacin cin abincina ya yi shi ne baka girka mini batun ɗazu cikina ke ciwo." Ta ce da shi ba tare da ko fargaba tana kallon su duka da tsuka tsaya ƙiƙam kamar wasu gumaka. A.m ya yi wani iri da shi ya kalli Juwairiya sannan ya kalli Zainab da ta yi suman tsaye,har yanzu ta kasa yarda ita ce a gabanta. Sai haushin kan sa ya kama shi gani yake kamar bai cancanci ya zamo mijin mata biyu ba,duba ga dukannin su tsoron su yake yi. " Innalillahi!Momi na shiga uku da gaske wannan yar iskar yarinyar da ka ce tana gidanku ashe tana gidan nan?" Ta faɗa tare da cakume shi tana kuka kawai sai ta ɗaga hannunta za ta mare shi da sauri ya riƙe ya ce." Zainab ki kula har yanzu da saurana don ban zama irin mazannan da mace za ta rinƙa duka ba.Na so na yi miki bayani amma ke kullum ba kya yi mini uzuri ki saurare ni.Abba ya tilasta mini na kawo ta gidana amma da zarar ta haihu zan sallame ta." Zainab ta kalle shi ta fashe da kuka ta ce." In har kana son zamana a gidan,nan ya zama dole ta bar gidan nan don na tsaneta ba na son ƙara kallonta,kuma har wani abinci kake mata A.m tun da nake da kai ka taɓa dafa mini ko ruwan zafi." Hunnunta ya kama ya galla ma Juwairiya harara ya ce." Saboda babynmu nake yin hakan kin san mai ciki duk abin da ta ce dole ayi mata,kin san Allah da ke kike da cikin nan in da ana yi ma mutum numfashi to zan sauwaƙe miki yin sa,don haka duk abin da nake yi mata saboda baby ne,kuma da zarar ya fita shikenan." Ya ce mata da murya sanyayya yana kallon Juwairiya a wulaƙance. " Gaskiya dole ka yi magana da Abba ta koma gidanku na yarda,ko miliyan nawa zan ba da in har za a kula da ita amma ta bar mini gidana." Ta faɗa masa cikin karayar zuci saboda ganin yadda ta koma ya firgita ta. Tsaki ta saki ta kalle su duka ta ce." Kan ku ake ji ni kaina na ƙosa na bar wannan gidan da baku san haƙƙin kowa ba sai kanku."Ta juya ta koma falo. "Yanzu da gaske girkin za ka ka yi mata da wannan daren?"Kawai sai ta saka kuka ganin yana saka doguwar riga. "Yarona zan yi wa girki karki damu cikinta ya shiga na wata huɗu, kin ga mun kusa yarda ƙwallon mangwaro mu huta da ƙuda."Ya ce da muryar rarrashi. A lokacin da ya fita kifa kanta ta yi ta din ga kuka sosai baƙin ciki cushe a zuciyarta,tana jin wani ɗaci na ganin ta a gidan,wasu irin abu da suka faru dama waɗanda ba su faru ba ta rinƙa hasasowa,sai ta ƙara sakin wani kukan tana buga kanta da gini. Da ga ƙarshe kasa zama ta yi ganin uku har ta gota ta sauko ƙasan,sai ta ga a wannan lokacin A.m ya kammala ɗanwaken ya kawo mata,amma saboda muguntar da ta saba ta ce sai ya jira ta ta gama. Da takaici ya ishe ta komawa ɗaki ta yi tana ta kuka sosai a yadda ta ga Juwairiya, daga yau ta ije aiki har sai ta haihu ta bar musu gidan,don ba za ta iya barin ta da shi ba a cikin gidan. Kamar yadda suka saba kwana a falo haka ta kasance yau ita Juwairiya ba ta yi bacci ba,sai shi da yake ta gyangyaɗi daga ƙarshe bacci ya kwashe shi. Ta gyara zamanta ta ci gaba da kallo tana karanta lintafin Hausa novel mai suna(Burin duniya na Jamila Lawal Zango Jamcy)Wanda Hamdiya ta tura mata saboda ya rage mata kaɗaici.Sai dai tsoro da tashin hankalin da yake cikin lintafin da tausayin Khairi da kuma takaicin doctor Garkuwa ya sa ta ije lintafin, da tsananin tsoro ta kashe wayar gabaki ɗaya. A.m da ya ji kiran salla zubbur ya miƙe ya kalle ta wadda tsoro ya sa ta baccin dole. Ji ya yi kamar ya shaƙeta da sauri ya haye sama ko tashin ta bai yi ba,saboda takaicin gani girkin da ya yi mata ko guda uku ba ta ci ba. Ya tura ɗakin ya shiga har yanzu bacci take yi saboda bayan kukan da ta sha bacci ya ɗauke ta ba don ta so ba. " Zainab ki tashi kiyi sallah." Sai ta yi tsuru tana kallon sa yayin da hawaye yake bin gefen fuskarta. " Na rasa ta yadda zan fito na yi miki bayani ki yarda da ni Zainab."Ya faɗa muryar kaukausa domin shi yana ganin bai kamata ta ɗaga hankali a kan yarinyar da baya jin sonta a cikin ransa ba. " Na gaya miki ba so a cikin auren nan na yi shi ne don kawai mu samu ɗa,kuma na yi miki alƙawarin da zarar ta haihu zan cika miki alƙawarin da na ɗaukar ma ki ba ta saki uku." " Zuciya ce take ɗar-ɗar amma tun da haka ka ce shikenan ka yi ma Abba magana ta koma gidanku."Ta ce mishi lokacin da ta yi hanyar bayi. " Wannan ba zai yiwu ba domin Abba ya ce dole sai na zauna da ita,amma ni ba zan iya zama da wata mace ba bayan ke,ki yi haƙuri har ta haihu sai mu bar garin bayan na saketa mu koma London sai mun ɗauki tsawon shekaru kowa ya manta mu dawo." Rungume shi ta yi tare da manna mi shi kis ta ce."Na yadda da kai mijina na san duk wannan matsalar ni na kawo shi,domin da ban biye wa son zuciya ta ba,da son gayu da ƙyalƙyali na haihu ko da ɗaya ne, da baka janyo Juwairiya cikin rayuwarmu ba,na yi takaici sosai ban san cewa kana son yara haka ba,sannan ba za ka iya rayuwa dole sai ka so ka ga ɗanka." Sai kuma ta sake shi ta sa kuka ta ci gaba da cewa." Kaicona da na bi ruɗin duniya na ƙi bari na haihu ko sau ɗaya ne,ina ma matan da suke shan maganin hana haihuwa don wani buri na su,ko mazan suka umurce su za su daina duba ga irin yadda na tsinci kaina cikin nadama.Don Allah A.m karka karya alƙawarin da ka yi mini,saboda kishin ka zan ije aikina har Juwairiya ta haihu na ƙosa ta fita daga cikin rayuwarmu ba zan iya barin ka kai da ita ba,wallahi jiya da na gan ta hauka ne kawai ban yi ba,saboda duk kyan da na ke da shi na tsorata da ganinta.Ashe haka mata suke canzawa in suna da ciki." Riƙe ta gam ya yi har cikin ran sa yana jin tausayinta don in ya kalli cikin Juwairiya ji yake yi kamar zai sume,to ina ga ranar da ya fito duniya ya ga ɗan mutum ace na shi. " Na yi miki wannan alƙawarin ba ki da matsala." Duk wani abun da A.m zai yi ya kwantar da hankalin Zainab yana yi,abu ɗaya ne ya ji sam ba zai iya ba yadda ta hana shi ko da kallon Juwairiya,domin ko motsi ya yi idanunta na kan sa. Gabaki ɗaya ta ije duk wani yawonta da take nadamar yin sa da ta yi,tana zaman gida sai ta yi kwanaki ba ta fito ba. Duk sadda ta ga cikin Juwairiya da yaƙe ƙara girma, sai ta shiga ɗaki ta yi kuka ta yi kuka har ta ji babu daɗi,watarana sai ta yi ta buga kanta a bango tana nadamar riƙon sakainar kashin da ta yi masa. Ba ta ƙara shiga tashin hankali ba sai da Juwairiya ta fara kubburi duk da alokacin cikinta wata shidda da sati biyu,hankalinsa ya yi dubu ya tashi kamar zai yi hauka,wanda Zainab ta ka sa gane akan baby yake yi ko uwar baby. Da suka je asibiti likita ya ƙara tura su scanning sannan jini za a ƙara mata,saboda jininta ya yi ƙasa,take A.m ya ce a iba na shi a saka mata. Zainab ta tada hankalinta matuƙa tsiya sosai suka yi akan ya siya jini a saka. Sai dai ba ta yi nasara a kan sa ba, don kwana biyu ya yi ana iban jinin sa wanda aka sakawa Juwairiya,da yanzu ta fara raina kanta ganin yadda take komawa har kammanninta sun fara canzawa,ga ƙafafuwanta da suke kubbura. Bayan an saka mata jini suka dawo gida Allah ya ɗauki wani irin tausayin Juwairiya ya saka a zuciyar A.m,wanda ko juya idanunta ta yi sai ya ji wani madarar tausayinta a cikin ransa. In yana gida sam ba ya iya zama a ko ina sai falon ƙasa,daga baya ƙarya ya yi wa Zainab cewa Momi ta ba shi umurnin ta koma sama,in ya so a ba ta ɗaki ɗaya ta zauna madadin zaman ta a ƙasa. Zainab hankalinta ya ƙara tashi saboda tun da ta dawo ta ga duk sun canza mata suna wani nan-nan da ita. Kullum suna sintiri gurin kawo mata abinci na ƙwaɗayi,haka Momi da Abba kullum sai sun kirata sun ji lafiyarta. Ta raina kanta matuƙar gaske kullum cikin nadamar abin da ta aikata take.Ga tarin dukiyar da take buri ta samu ta samu don yanzu Ƙasar ingila take son ta haɗa hannu da asibinta,kuɗi kam ba ta da matsalar su amma babu kwanciyar hankali,saboda ta lura yanzu sam hankalin A.m ba shi a jikinsa,da ta yi masa magana ya ce zuwan baby ne. A.m da Zainab suka shirya zuwa waje suka yo siyaryar kayan baby,wanda ita kanta Zainab ba ta san iya yawan kuɗin da ta kashe ba. A.m sai haɗa tarin dukiya yake yi ma Juwairiya har da wasu share ɗin sa na waje yake son ya bar mata,saboda kar in suka rabuya rage mata jin zafin rabuwa da baby. Ita kanta Zainab ta yi masa alƙawarin za ta ba ta dukiya masu yawa, ita dai burin ta ta bar mata A.m da babyn da yanzu take jin ta fara son sa a cikin ranta,don son da za ta nuna masa shi kawai zai ƙwato mata martabarta a gurinsa. Bayan Juwairiya ta dawo sama wata ƙaryar ya shirga ma Zainab akan dole yanzu ya rinƙa kwana da ita saboda cikinta da ya shiga wata na bakwai. Da fari ƙin amincewa ta yi amma daga baya sai ta yarda akan za su dun ga kwana dukansu tare. Sai dai A.m yaƙi mata ya ɗan nuna mata hakan ba zai yiwu ba ta amince,don ta san yanzu in dai ba rashin tausayi ba bazai kalle ta ya buƙaci wani abu daga gareta ba,duba ga yadda ta koma. Juwairiya na ɗanɗana kuɗarta duk wani wahala da take ba ma mutanen gidan,da tsiwa kan dole ta watsar domin yanzu ta kanta take yi,kusan kullum cikin wahala take domin cikin na matuƙar ba ta wahala sosai,kamar za ta mutu ko nishi ta yi sai ta ji wani azaba,ita kam ta sheda mutuwa za ta yi,shi ya sa kullum take kuka sosai akan ya kai ta gurin Mama,saboda ta san mutuwa za ta yi. Ranar wata daren Alhamis A.m hankalin sa ya tashi matuƙa ganin yadda take sauke numfashi sama-sama. A lokacin cikin wata takwas ya shiga amma duk wanda ya ganta sai ya tausaya mata,saboda ta yi wata irin ƙatuwa a yadda kamanninta suka canza ina tunanin ko Mama ta ganta sai ta yi da gaske za ta gane ta. A.m hankalin sa ya tashi ƙwarai tun da ya fara kwana da ita ya shiga tashin hankali,ganin irin wahalar da take ji sam ba ta samun bacci. Hannunsa ya sa da nufin ya kamata cikin tausaya,amma sai ta ture shi ta riƙe kwankwasonta tare da rintse idanunta,tana jin wani irin azabar raɗaɗin mutuwa yana shigar ta. " Wayyo Allah na!Mama ki yafe mini dama haka kika ji kika haife ni! Wayyo Mama ba laifina ba ne halin da kike ciki ya sa na amince da abin da mugu azzalimi ya zo mini da ita.Baba Sani Allah sai ya saka wa mahaifina sam baka riƙe maraicin da mahaifinmu ya baka amana ba." Sai ta cige baki ta miƙe da nufin ta tashi,amma ta kasa da sauri ta koma ta zauna, tare da jingina kanta a kan gadon don ji take kamar ɗan dake cikinta zai fito ta bakinta. A.m da yake jin wani tashin hankali kusan haka suke kwana duk da sun je asibiti,amma sai a ce musu lokaci bai yi ba,sannan (E.D.D)ɗinta bai yi ba balle ayi mata aiki,don haka su jira lokaci. Duk iya juriyar sa in ya ganta cikin wannan tashin hankalin sai ya ji hawaye da nadama na shigar sa. Bai san cewa ya shaƙu da ita ba musamamman lokacin da ta fara masa tsiwa, tana nuna ba ta son sa da tsoron sa. Hunnunsa ta kama ta riƙe ta kalle shi da fararan idanunta wanda yanzu suka koma suka rine saboda ruwan azabar da take kwankwaɗa. " Bazan yafe maka ba kai da Baba Sani, kai harma da A.k duk da na san ka tilasta shi ne,amma wataƙila da ya jajirce bai amsa ba da ba ku zo gurina tun da kana jin maganar sa b...." " Juwairiya ki yi shiru za ki haihu lafiya ki koma gurin Mama in sha Allahu Mama za ta ƙara tozal..." Katse shi da ƙarfi ta yi." Ka yi shiru don Allah mutuwa zan yi! Jikina ya ba ni bazan ƙara ganin Mama ba a rayuwata,ka raba ni da Mama don kawai burinka na ka samu ɗa.Ka tuna ni ma ƴa ce wacce uwa ta haifa take sonta, kamar yadda kake son ɗan da za ka haifa,saboda burinka na haihu ka ba wa matarka ka nisanta ni da Mama A.m ba ka yi mini adalci ba,na tsane ka bana sonka.Dubi irin wahalar da nake sha amma fatan ka na haihu ka rabani da ɗana,saboda ka faranta ma matarka.Wai shin ita ce mace kaɗai a duni..." Wani irin hajijiya da take yi ya hana ta ƙarashe maganar sai da ta ɗauki tsawon lokaci ta ce a wahale. " Wayyo Mama na ƙara girmama lamarin uwa a raina,na san haƙƙin ki yake bibiyata tur da irin ƴa kamata wacce za ta aikata wani abu ba tare da sanin mahaifiyarta ba!Tur da ni kaicona da na yi miki butulci na yi aure ba tare da sanin ki ba. A m ka ɗauki kukana ka tura ma Mama ta yafe mini ko na samu salama a makwancina."Ta ce yayin da idanunta ke rufewa muryarta na ƙasa-ƙasa. " Inna lillahi wa inna ilaihir raji'un!"A.m ya faɗa cikin tsananin tashin hankali yana jijjigata. " Da gaske mutuwa za ki yi Juwairiya! Don Allah kar ki mutu wallahi ban aure ki don na kashe ki ba,ki buɗe idanunki Juwairiya ki tashi don Allah mai kike so na ce ma Mama da take zaman jiran ki?" A.m ya ruɗe sosai jijjigata yake amma tamkar babu rai a jikinta. Hawaye yake yi cikin tashin hankali a ransa yana tunanin dama haka mata ke haihuwa. Yana tsaye a kanta yana jijjigata ya rasa na yi zuwa can sai ta buɗe idanunta, tana wani irin jijjiga kamar wacce ta kamu da tsinƙa-tsinƙa,sai jini ya fara zuba sosai kamar an buɗe famfo. A.m ya miƙe daga jikinta tare da sakin wani iri ƙara ya ce. " Juwairaaaaah!" Kawai ya zube ƙasa babu numfashi. TO MASU KARATU KU DAI BIYO NI KU JI YADDA ZA TA KAYA A TSAKANIN SU YAU BAN YI TYPIND DA YAWA BA,SABODA BA NA JIN DAƊI KU YI HAƘURI DA WANNAN ANA TARE. KU CI GABA DA BIBIYAR LINTAFIN DON JIN YADDA ZA TA KAYA A CIKIN LINTAFIN NAN MAI FARIN JINI. BARI NA TUNA MUKU DA SUNAN SHI SAKACINA KO HALIN MAZA TAKU JAMILA LAWAL ZANGO JAMCY TALLAH!TALLAH!!TALLAH!!! INA ƳAN MATA DA MATAN AUREN DA SUKA SHAYAR SUKE SON MARTAR ƘIRJIN SU YA DAWO? INA MATAN DA SUKE FAMA DA RASHIN ƘIBA KO INA A ƘAME? MAZA GARZAYO KI SIYA INGANTACCEN MAGANIN GYARAN NONO DA ƘIBA,MAGANIN AN RIGA AN GWADA KUMA YA NA DA AKYAU ƘWARAI.BARI IN GAYA MIKI YAR'UWA DUK WADDA TA CE MIKI MARTABAR ƘIRJINKI,ZAI DAWO MATUƘAR JIKINKI BAI MURJE BA,TO GASKIYA KUƊIN KI KAWAI ZA TA CI. IN HAR KINA SON MAGANIN YA YI AIKI A JIKIN KI SAI KIN DAURE,KIN SHA SAFE DA YAMMA.SANNAN MUNA AIKAWA KO INA SIYAN NAGARI MAIDA KUƊI GIDA. MAGANIN AKAN FARASHI MAI TSAUƘI IN KINA SO MAZA GARZAYO KI KIRA WANAN NUMBAR ( 07088268243) KO (08144072423) Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW AND COMMENT. SAKACINA KO HALIN MAZA?* *RUBUTAWA:-* *JAMILA LAWAL ZANGO* *SADAUKARWA GA:-* *SUMMY M NA'IGE* _(Aminiya)_ *FIRST CLASS WRITER'S ASSO....* *Page 37* BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM Zainab da ke kwance ta miƙe cikin tashin hankali jin ƙarar A.m ta ruga ɗakin da gudu.Abin ta gani ya yi matuƙar razana ta,ɗora hannunta ta yi aka tare da sakin ihu,saboda ta rasa me za ta yi. Girgiza sa ta fara yi tana faɗin." A.m ka tashi don Allah kar ka mutu ka bar ni!Ka san ba zan iya rayuwa babu kai ba." Ta kalli Juwairiya da take cikin wani hali gani ta yi kamar babu rai a jikinta,sai jikinta ya kama rawa ta rasa baƙin ciki za ta yi?Ko akasin hakan. Dabara ta faɗo mata ta ruga da sauri ta ibo ruwa ta watsa masa. Buɗe idanunsa ya yi da sauri tare da miƙewa ya kamata kamar zai ɓallata ya ce." Ina Juwairaaah ta mutu ko?" Zainab da ta kasa magana idanunta ta kai gurin da take kwance rai kwakwai mutu kwakai. Da sauri ya bi in da ta kalla da idanunsa sai ya miƙe zubbur ya nufe ta ya ɗauke ta zai fita da ita. " A.m dare ya yi fa yanzu ina zaka kai ta?" Ta yi masa tambayar da ko kallonta bai yi ba ya fice,ba ta ankara ba sai jin tashin motarsa ta ji ya fice da ga gidan. A.m da yake tuƙi cikin tashin hankali Allah ne kawai ya kai shi asibitin. Ba tare da ɓata lokaci ba likitoci suka rufu a kanta,wacce ba ta san halin da take ciki ba. Jikinsa har rawa yake yi wani irin tashin hankali ya ziyarce shi,ji yake kamar zai yi hauka,domin ya rasa asarar babyn ɗinsa ne bai so ya yi,ko halin da take ciki ya saka shi cikin wannan halin. Wayarsa ya zaro a cikin daren ya kira A.k ya fi sau goma sai dai bai ɗaga ba,sannan ya kira iyayensa ya sanar musu. Ya yi shiru yana tsaye a gurin ɗakin da aka kwantar da ita sai leƙe ta windo yake yi,amma duk iya ƙoƙarin da likitocin suke yi ba ta farfaɗo ba,sai ya duƙar da kan sa yana jin tsananin tausayinta,yayin da hawaye yake bin ƙuncinsa. " Na shiga uku! Yanzu in yarinyar nan ta mutu ya zan yi?" Ya tambayi kan sa cikin tsananin tashin hankali mara misaltuwa. Salati ya ji tana yi cikin murya ƙasa-ƙasa sai kawai ya danna cikin ɗakin ya durƙusa a kusa da gadonta ya kama hannunta ya riƙe. " Juwairiya ina son ki!Ina son ki!! Ina son ki!Kamar yarda kika faɗa mini na maimaita miki,na roƙe ki don Allah kar ki mutu ki bar ni wallahi ina son ki,ban san cewa son ki nake ba sai yau da na ga za ki mutu ki bar ni.Na haƙura da baby kar ki mutu don Allah ki tashi zan rayu da ke ko da ba za ki ba ni baby ba." Cikin wata irin murya yake maganar yana ji kamar ciwon ya dawo jikinsa,ganin yadda take shan wahala matuƙa. Juwairiya ta buɗe baki za ta yi magana amma sai wani irin nishi ya hana ta,ta rufe bakin da sauri tana salati a ranta,don ta sadaƙar mutuwa za ta yi,wannan nishin na cire rai ne. Kawai sai suka ji kukan jariri yana ta tsala kuka sosai duk ya cika asibitin da ihu. A.m ya saki hannunta da ta rufe idanunta jin wani irin ciwo ya ta so kamar ba ta haihu ba. Ya kai hannun da sauri zai ɗauki babyn yana faɗin." Alhamdulillahi adada ma khalaƙa." Da sauri wata nurse ta riga shi ɗaukar babyn,sai ya duƙa ƙasa yana jin kamar an yi masa bishara da gidan aljanna. " Doctor Marwan ina ga kamar ƴan biyu ne za ta haifa da wani jariri a cikinta." Doctor Bilal ya faɗa cikin razana ganin ciwo ya koma sabo. " Anya kuwa ba na tunanin haka saboda scanning ɗinta ya nuna mana yaro ɗaya."Ya ba shi amsa da shakku a fuskarsa. Tun suna tunanin cewar mahaifa ce za ta biyo har suka yadda ƴan biyu a cikin. Ganin irin wahalar da take sha A.m kuma kamar zai zare kamata ya yi ya riƙe,sai murna ta koma ciki. Likita ya bada umurnin a fitar da shi saboda yana ɓata musu aiki,duk lokacin da ya ga sun danna cikinta ta saki ƙara mai razanarwa,sai ya ware zai bugi likitan. Duk yadda likitan ya so ya raba hannun su, amma ina ya ƙasa saboda sun riƙe junansu ƙaƙam,sun ƙi saki daga ƙarshe kan dole ya ƙyale shi. Duk iya ƙoƙarin su jaririn ya ƙi fitowa,amma kuma in suka saka hannun suna taɓa kan sa. Hankalin su ya tashi matuƙa gashi a lokacin ƙarfinta ya ƙare,ko motsi ba ta iya wa balle ta yi nishi,sai idanunta da take wulƙita su cikin raɗaɗin azaba. " Ina gani ya kamata a kira doctor Garkuwa don shi kawai zai iya maganin wannan matsalar,ƙila ya ce a shirya mata aiki fa,domin ba ta da ƙarfin da za ta iya nishi yaron ya fito."Doctor Bilal ya ce da doctor Marwan. " Ba ya ƙasar ka san ya yi tafiya zuwa ƙasar America akan ƙwallon gasar ƙafa da zai buga." " Kai wai me ya saka doctor Garkuwa yake yin haka! Sai ka buɗe asibiti amma ba za ka rinƙa kulawa da patient ba,kullum ba shi da aiki sai zuwa ƙasashen waje akan ƙwallon banza,wanda iyayensa ba sa son yana yi Yanzu ya yake son mu yi da wannan baiwar Allah da take cikin wani hali?"Ya faɗa cikin tashin hankali. " Waye wannan Garkuwa mahaukaci ne shi zai fifita ƙwallon ƙafa akan mutane?Na rantse in ya kashe mini mata sai na kashe shi ko kuma kotu za ta raba mu."A.m ya ce cikin hargowa bayan ya shaƙe likitan. Da ƙyar ya ƙwace kan sa ya ce." To sakar mini riga shi ma ɗan zafin rai ne kamar kai sai ka bi shi can ku ƙarata."Ya ce tare da ƙwace rigarsa. " A nemo amininsa doctor Isa abin takaici jiya ya gama duting dar." " Ashe asibitin mahaukata na kawo matata ba ku da hankali,asibintin ya zama ƙyalƙyali banza,ba ku damu da halin da take ciki ba,to bari na gaya muku in har Juwairiya ta mutu kuma duk sai na kashe ku." Likitan ya buɗe baki zai yi magana da fushi ganin ya raina ƙoƙarin su,sai suka ji kukan jariri da ya kusan faɗowa ƙasa,wanda taimakon Allah kawai ya fito da shi daga cikin. " Wayyo Allah na! Ƴaƴa biyu! Wallahi ƴaƴa biyu kika haifa mini gaskiya aurenmu mai albarka ne." A.m ya faɗa yana kallon jaririn da ya daina kuka saboda wahalar da ya sha. " Na yi mata allurar tsaida jini amma ya ƙi tsaya fa."Nurse ɗin ta ce cikin tausayin wahalar da take sha. Shiru kawai ya yi ya tsaya yana tunanin wace alllura zai ƙara yi mata,kafin wannan mahaukacin mijin na ta ya farga. Hankalin su ya tashi ƙwarai duk yadda suke ɓoye-ɓoye sai da ya fahimta,ya riƙe hannunta ƙam yana hawaye." Juwairaaah na ga tashin hankalin dama haka mata suke wahala in za su haihu? Allah Sarki Momi zan kasance mai yi miki biyayya har ƙarshen rayuwa,zan miki duk abin da kike so duk da na san ko mai na yi miki ba zan taɓa biyan ki ba.Bazan raba ki da yaran ki ba Juwairaah domin in na yi haka Allah sai ya hukunta ni,wallahi kin biya ni komai da kika haifa mini yara har biyu duka maza." Ba ƙaramin wahala su ka yi ba kafin su tsaida jinin,don har idanunta sun fara ƙaƙƙafewa. Ya tsura mata idanu yana kallon fuskarta da idanunta ke rufe tana saukar da numfashi a hankali. Kiran sallar asuba na farko ya sa shi ya miƙe sai kuma ya kalli jikinsa,ba tare da ya shirya ba dariya ta kama shi ganin duk wannan diramar da ake kayan bacci ne a jikin sa. Wayarsa ya ɗauka yana kiran mutane yana gaya musu,don a ranar har wanda bai kamata ya gaya wa Juwairiya ta haihu ba,sai da ya gaya musu,saboda in dai zai ga numba a wayarsa sai ya kira ya faɗa musu. A.k ya fara isowa cikin asibitin kafin ya shigo sai ga motar su Daddy kowa yana rige rigen shiga,don ko gaisawa ba su yi da junan su ba. " Wallahi ta haihu ka gan su ni ma na zama Baba Allah Daddy za su rinƙa kirana suna gudu suna bina,kuma fa kama da ni suke yi har da tabon fuskata."Ya ce da A.k da ya sawo kai cikin ɗakin yana nuna masa yaran da suke cikin shawul,duk da ba su taho da kaya ba,amma tsarin asibitin ne komai na buƙata a kwai. " Ikon Allah ka ga sabon shiga yara biyu a lokaci ɗaya! Gaskiya Juwairiya ta iya haihuwa.Amma na kasa gane tsakanin kai da ita wanda ya yi naƙudar duba ga yadda jikinka ya ɓace da jini."Ya faɗa yana dariya bayan ya karɓi yaran a ran sa yana ta ya amininsa murna. A.m ya ji kunya sosai saboda iyayensa da suka shigo shafa kan sa ya yi ya ce." Bari kawai ƴar albarka ta ci baƙar wahala,amma duk da haka bayan shekara za ta rinƙa kawo mini kyawawan yara irin waɗannan." Momi kuwa rungume yaran ta yi ta saka kuka sosai." Ikon Allah ashe a kwai ranar da zan ga yaranka Abdul,sam ba ka kyauta mini ba da ka ɓoye mini wannan lamari,don kawai ka birge wata mace can wacce ta cuci kanta da kanta,wai kai ɗan soyayya haka kawai ka hana ni ganin sanyin idanuwana jikokina."Momi ta ce tana goge hawaye. " Sha kuruminki Momi duk da cewa ana shan wahala amma duk shekara za ta rinƙa kawo miki irin waɗannan."Sai ya haɗa hannunsa ya kama mahaifiyarsa ya rungume yana hawaye. " Momi tabbas na ƙara girmama lamarin uwa a raina ashe haka mata suke shan wuya kafin su haihu!Mutuwa ce kawai ba ta yi ba.Momi zan miki biyayya har ƙarshen rayuwa,ko da wuta kika tura ni zan shiga." Kama hannunsa ta yi ta haɗa." Kana yi mini biyayya Allah ya yi maka albarka ya shirya maka zuriya." Sai kawai ya saki ƴar ƙara yana dukan A.k ya ce." Yes ni ma na kai lokacin da za a yi ma yarana addu'a." " Ya A.m ina Anty Juwai ɗin?"Hamdiya ta tambaye sa don burinta ta gan ta. " Kull karki ƙara ce mata Anty ai daga yau ta girma Maman ƴan biyu za ki ce,saboda kin rage mata matsayi."Dariya suka kwashe da shi. Bayyana irin farin cikin da suka shiga abu ne mai wuya musamman A.m, da yake ji a ran sa dole sai ya yi sadaka don bai taɓa tunanin haihuwa ta farko,za ta haifa mi shi zuƙa-zuƙan yara har guda biyu kuma duka maza. Gida ya dawo don ya yi wanka sannan ya yi wa Zainab albishiri,saboda ya bar ta cikin jimamin halin da ake ciki. A lokacin gari ya waye ko da ya dawo tana ɗakinta ga mamakinsa sai yaga tana bacci,don haka bai tashe ta ba ya wuce bayi ya yi wanka,sannan ya saka turaren da yake so don ya san daga yau ba za ta ƙara yi masa ƙorafi ba. Wani irin gayu ya yi cikin murna da annashuwa bai taɓa tunani yana sonta haka ba,da ya duba halinta da haƙuri ga kula da ibada sai ya ga tabbas ta ya kamata a so ta,uwa uba kuma girkin da take mi shi. Ya auna tsaƙanin son Zainab da ita wa ya fi so sai dai shi kan sa ya rasa ganewa,domin har yanzu yana son Zainab saboda soyayyarta daga Allah ne,bayan nan ga tausayinta da ya cika mi shi rai,ya san cewa za su kai ruwa rana in ya gaya mata abin da ke zuciyarsa,amma ya zai yi ita zuciya ba ta da ƙashi,shi kan sa ba yin kan sa ba ne Allah ne ya saka mi shi sonta a cikin zuciyarsa,domin zuciya an halicce da son mai kyaukyata mata. Ya sauko zuwa falo har ya ɗauki makullin mota zai fita, sai kuma ya tuna bai yi magana da Zainab ba,da sauri ya juya zai haye saman,a ran sa yana ma kan sa faɗa dole ya yi adalci a tsakanin su. Matuƙar kunya ta kama shi ganin ta a saman bene tsaye da kayan bacci tana kallon sa,sosai ya ji kunya don fa har ya murɗa kofa zai fita ba tare da ya yi mata magana ba. " Inna lillahi! Tabbas zuciyata ta gaya mini yau A.m ya yi sabon abu, wanda ya saka har ya manta da ni Zainab wacce yake iƙirarin ba zai taɓa rayuwa babu ita ba."Ta faɗa yayin da idanunta suka kawo ruwa don ko bai gaya mata ba,farin cikin da ke ɗauke a fuskarsa ya bayyana hakan. Dawowa ya yi da sauri ya hayo in da take." Tabbas ta haihu Zainab na ci ƙwallon Juwairiya ta haifa mini yara kyawawa har guda biyu." " Wayyo Allah na!." Ta faɗa tare da zubewa ƙasa ta dafe kanta tana jin wani irin tashin hankali." Kamata ya yi ya rungume ta kalle shi da hawaye a fuskarata." Na shiga uku da gaske yau ka samu abin da za ka raba mana soyayya da su?Kuma ba yarana ba?"Ta ce cikin kuka. " Haba Zainab ke da za ki yi murna Allah ya albarkance mu da yara har biyu,bai kamata ki nuna tashin hankali a rana irin ta yau ba.Na gaya miki babu abin da zai saka na raba son da na ke miki har yanzu son ki na nan a cikin zuciyata sa..." Tura shi ta yi ta miƙe ta ce " Ka barni na yi kuka domin ya zama dole a rayuwata,haihuwa fa ka yi da wata mace yau ko mutuwa ka yi Allah ya cika maka burinka ka samu magaji,ni fa A.m ba zan taɓa haihuwa ba duk da tarin dukiyar da na mallaka.Kaga ya zama dole in yi kuka ko abin da ya fi kuka."Kawai sai ta rushe da kuka ta kama ƙarfen benen ta riƙe bayan ta miƙe tsaye. " Haba Zainab yarana ai naki ne na har abada bai kamata ki ce haka ba,kuma na yi miki alƙawarin ba zan taɓa nuna miki wani abu akan yaran ba,sannnan zan kasance dake har ƙarshen rayuwata in har ina numfashi a duniya." Tun Zainab na kuka yana rarrashinta har ya gaji ya miƙe ya ce." Bari na kai kaya ana ta jirana." Ya fice daga gidan. Ƙaramin hauka ta yi duk da ta san A.m zai cika mata alƙawarin da ya ɗaukar mata,amma ta ji kishin ta matuƙar gaske kamar ta je ta kashe ta,amma babu yadda za ta yi saboda ta san cewa ta yi sakaci sosai. A ƙalla sai da ta yi sati ɗaya a asibitin sannan ta warware ta samu lafiya sosai. Yara sun ci sunan kakannin su wato Dadddy da Abbu,wayyo Allah zo ka ga murna gurin takwaran Hassan wani irin gata ya nuna musu na ban mamaki. Momi ta ce a kai Juwairiya gidanta har ta gama wanka,daga nan sai ayi taron suna da shagalin bikinta da ba su san da auren ba,amma A.m ya nuna ina sam hakan ba zai yu ba domin ba zai iya kwana ba tare da yaransa ba,sai dai in za ta ba shi gurin kwana to ya yarda,daga ƙarshe Momi aka ce ta je ta kula da ita,ƙila ya manta yana da wata matar da zai tare a gidan,saboda ta lura yarda take zumuɗin yaran babu abin da ba zai iya ba. A.m da ya ɗaukar wa kan sa alƙawarin in har mai asibitin ya dawo sai ya yi masa nasiha,akan ya kula da asibitinsa don ranar gobe kiyama sai Allah ya tamabaye shi akan yadda yake sakaci da rayuwar al.umma. Sai dai ya kama bakinsa ya tsuƙe saboda ganin sa da ya yi,zai iya cewa tun da ya ke bai taɓa ganin mutum mai ɗagawa da girman kai irin sa,duk da cewa shi ma ya san yana da na sa,amma doctor Garkuwa ya dame shi ya shanye,yana kallon mutum kamar kashi wanda sam A.m bai fahimci haka halintar idanunsa take ba,shi a bin da ya ƙara ba shi haushi da shi zuwa da gajeren wando da yake yi a asibitin,wanda ya fahimci dabi'ar sa ne,saboda ya ji ƴan asibitin suna gulmar sa ko waje zai fita da gajeren wando yake fita,kamar zai tsallake wuta.Sai dai kuma matashi ne mai kyau da kuɗi da aji ɗan kwallo wanda sunan sa ya zagaye nahiyar duniya. Sau ɗaya Zainab ta danne zuciyarta ta je asibitin sai dai ta sha kuka,ta yi alƙawarin ba zata ƙara zuwa ba,saboda abubuwan da ta gani yadda suke ji da ita,don Hajiya Binta take mata wanka,Momi kuwa kullum tana asibitin . Ta sha kuka ta bari a sallamota su yi ta taƙare da A.m ya karɓi yaran ita za ta shayar da su ya sallami Juwairiya don zuciyarta za ta buga,wataƙila kuma ta amshi ta yi da Momi take mata,saboda ba za ta iya barin sa da ita ba na har abada,duk da ta san ko yau ta bar gidan ta fita na har abada ganin yadda danginsa suke nan-nan da ita kamar za su lashe ta don so. Wani irin so yake nuna musu na fitar hankali don a yarda yake ji da su ko kan sa ba ya ƙauna haka. Hajiya Binta ta hana shi sakewa da Juwairiya, saboda tun da ta haihu ta canza mi shi babu tsiwa,sai shiru-shiru sai kuma hawaye da take yawan zubarwa in har ya yi mata magana,wanda hankalinsa yana tashi matuƙar gaske,ya yi mata tambayar duniya ba za ta amsa mi shi ba,gabaki ɗaya ta canza mi shi kamar wata kurma,wanda hakan yake ɗaga hankalinsa matuƙa. Zainab ta raina kanta ta muzanta tun tana mamakin halin da yake mata, har ta daina tana kallonsa kawai don ta fahimci shi bai ɗauke shi wani abu ba. Ko kwance suke haka zai ɗauki hoton su ya yi ta kallo yana dariya kamar mahaukaci,in har tana son ya yi mata magana to ta ce ai Hasan ya buɗe ido ka ya yi kaza,sai ya saki baki ya yi ta zuba yana hira,gabaki ɗaya bai da lokacin ta sai na yaransa. Duk da cewar Hajiya Binta tana mi shi faɗa amma bai san lokacin da yake aikata hakan ba,shi dai ya san yana musu son mutuwa. Kwance suke Zainab tana gefen sa da kofi a hannunta tana shan tea,domin ya ɗumama mata jiki,kasancewar lokacin sanyi ne. A.m da waya a hannunsa yana ta kallon video na yaransa da ya yi musu,yau kwanan su sha takwas. Dariya yake sosai yana kallon Husain da yake buɗe ido sai ya rufe da sauri ya ƙuma ƙara buɗe wa. Zainab ta miƙe cikin fushi ta fisge wayar da take hannunsa ta kwaɗa ta da ƙasa ta tarwatse. Hannu ya ɗaga da sauri zai mare ta ko mai ya tuna ya fasa ya dunƙule hannun sa ya saki. " A she ba ki da mutunci kishi kike da yarana Zainab?" Kawai sai ta fashe da kuka ta ce." Na gaji A.m zuciyata gab take da ta buga! Ka san yarda nake son ka kuwa?Ka dai na kula ni ba ka da lokacina kullum sai na yaranka ba dole na yi kishin su.Ka sani ko da yaran nan sun dawo gurina ka ce haka za ka rinƙa yi musu,wallahi ba zan lamu ta b..." " Ya she ki kar ki kawo mini maganar banza! Idan yaran ki ne za ki furta hakan,in har kika ce za ki yi kishi da yaran da na haifa to kin saka ma kan ki wahala,don ina son yarana fiye da komai Shekaru nawa na ɗauka ba tare da na samu magaji ba."Ya katseta da faɗin haka. " Zan yi kishi da su har ƙarshen rayuwata in har haka za ka rinƙa yi musu,sannan Juwairiya ta haihu don haka ka cika mini alƙawarin da ka ɗauka." Kallonta ya yi sheƙeƙe ya ce."Sai ta gama wanka zan tara ku na yanke duk abin da na zartar."Ya faɗa a ɗaure ya ɗauki wayarsa ya koma ya kwanta. " Ai ko wallahi ka ɗauko ma kan ka tashin hankali matuƙar ka ce ba zaka rabu da ita ba,domin ba zan zauna ku kashe ni a gidan nan ba,son da nake maka ba zai bar ni na iya barin mata kai ba.Bari na gaya maka ka ji ina sonka in har kace za ka haɗa ni da wata zan ɗauki mataki sosai kuma na bi duk yadda zan yi na rabaku ban damu da girman zunubin da zan ɗauka ba,domin zuciyata ba za ta iya bar ma wata mace kai ba,don haka kashedi nake maka da kakkausar murya!"Ta fice daga ɗakin da gudu tana kuka. TO MASU KARATU KU DAI BIYO NI KU JI YADDA ZA TA KAYA A TSAKANIN SU YAU BAN YI TYPIND DA YAWA BA,SABODA BA NA JIN DAƊI KU YI HAƘURI DA WANNAN ANA TARE. KU CI GABA DA BIBIYAR LINTAFIN DON JIN YADDA ZA TA KAYA A CIKIN LINTAFIN NAN MAI FARIN JINI. BARI NA TUNA MUKU DA SUNAN SHI SAKACINA KO HALIN MAZA TAKU JAMILA LAWAL ZANGO JAMCY TALLAH!TALLAH!!TALLAH!!! INA ƳAN MATA DA MATAN AUREN DA SUKA SHAYAR SUKE SON MARTAR ƘIRJIN SU YA DAWO? INA MATAN DA SUKE FAMA DA RASHIN ƘIBA KO INA A ƘAME? MAZA GARZAYO KI SIYA INGANTACCEN MAGANIN GYARAN NONO DA ƘIBA,MAGANIN AN RIGA AN GWADA KUMA YA NA DA AKYAU ƘWARAI.BARI IN GAYA MIKI YAR'UWA DUK WADDA TA CE MIKI MARTABAR ƘIRJINKI,ZAI DAWO MATUƘAR JIKINKI BAI MURJE BA,TO GASKIYA KUƊIN KI KAWAI ZA TA CI. IN HAR KINA SON MAGANIN YA YI AIKI A JIKIN KI SAI KIN DAURE,KIN SHA SAFE DA YAMMA.SANNAN MUNA AIKAWA KO INA SIYAN NAGARI MAIDA KUƊI GIDA. MAGANIN AKAN FARASHI MAI TSAUƘI IN KINA SO MAZA GARZAYO KI KIRA WANAN NUMBAR ( 07088268243) KO (08144072423) Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_. Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce. Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani. COMMENT,READ FOLLOW READ AND SHARE.