*SHU'UMAR MASARAUTA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ƙirƙirarran labari ne bai faru a gaske ba. Ban yi shi don cin zarafin kowacce ƙabila da Masarautunsu ba. SHAFI NA ƊAYA Masarautar Zazzau (1953) Wani irin zafi take ji yana ratsa ta tun daga tafin ƙafarta har zuwa tsakiyar kwanyarta, dalilin haka ya sabbaba mata karkarwar jiki tamkar wacce ta ji kiɗan gangi. Wanda hakan ne ya haifar mata gumin da ke tsatssafowa daga kowacce kafar da ke cikin ilahirin jikinta. Ba yau ne karo na farko da haka ya taɓa faruwa da ita ba, sai dai a wannan ranar ji take tamkar an saka ta a tukunya ana dafa naman jikinta da ruwan zafi. A hankali ta cije baki tana yarfe hannu haɗe da lumshe idanu. Baiwa Maimuna da ke bayanta tana mata fifita cikin ƙwarewa a makirci ta fakaice ta, ta yanki ƙasan jelar gashin kanta ɗan ƙanƙani ta yadda ba za ta fahimci hakan ba. Da sauri ta soke shi a jikinta haɗe da sauke ajiyar zuciya don ko babu komai ta san ta tsira daga siraɗin Fulani Umaima. Ta ɗan numfasa a hankali. "Ki gafarce ni uwar ɗakina zan ƙarasa sashen Takawa na ce Jakadiya ta karɓo miki magani kamar yadda na ji kin ambata a baya, ranki shi daɗe lamarin ciwon nan na ki ƙara ƙamari yake yi amma tuba nake idan da kuskure a kalamaina uwar ɗakina." Ta so musa mata kamar yadda ta yi kafin zafin jikin ya fara galabaitar da ita, dalilinta na yin haka bai wuce yadda take gudun kada Bayin cikin masarautar su fuskanci zaman doya da manjar da ke tsakaninta da Mai martaba ba. Gyaɗa mata kai ta yi haɗe da ruƙo hannunta ta furta, "Idan kin fita Maimuna ki turo mini Baiwa Zainaba." Cike da girmamawa ta russana, "Allah ya ƙara wa Fulani lafiya, Ubangiji ya buɗi ido lafiya ya kawo mana Yarima mai jiran gado cikin yalwar ariziƙi da ƙoshin lafiya." Da hanzari ta fice a gaggauce don ko kaɗan ba ta son wargaza shirin ɓoyayyar uwar ɗakinta. Sai da ta turo wa Fulani babba Zainaba sannan ta wuce sashen Fulani Umaima cike da firgici, tana tafe tana waige kamar sabuwar munafukar da ta yi gulma a fada. Da yake Fulani Umaima ta kwana da sanin shirinsu, tun da doshin magriba ta sallami bayinta suka wuce sashensu na bayi. Tamkar wacce aka jefo daga sama haka ta faɗa ɗakin Fulani Umaima da ke tsaye tana kai kawo don gudun samun matsala a shirinsu, duk da tana da yaƙinin Baiwa Maimuna ba za ta iya shallake wa umarninta ba. A ƙasa ta zube tana sauke numfashi ta furta, "Hutawarki lafiya Fulani mai magajin masarauta, zinariyar Mai martana haskenki bai tsaya iya shi kaɗai ba kin haske lungu da saƙon cikin Masarauta. Ina gwanar wani ga tawa? Kin yi taki kin yi ta kowa, garnaƙaƙin dutse kike kowa ya ja da ke shi zai faɗi..." Fulani Umaima ta katse ta da cewar, "Ina fatan komai ya tafi yadda ya kamata?" Baiwa Maimauna ta saki murmushi, dalilin haka ya sa Fulani Umaima ta sauke ajiyar zuciya duk da ba ta kai ga jin amsar Maimuna ba amma ta fahimci sun yi nasara domin kuwa labarin zuciya a tambayi fuska. "Ranki shi daɗe an gama aiwatar da komai, ga wannan." Maimuna ta ƙarasa maganar tana kunto gashin kan Fulani Babba ta miƙa wa Fulani Umaima. Wani yalwataccen murmushi Fulani ta saki, Baiwa Maimuna ta ci gaba. "Yanzu haka tana can magashiyan har ta umarce ni da na aika Jakadiya ta karɓo mata ragowar maganinta a wurin Mai martaba." Wata irin dariya ce ta suɓuce wa Fulani Umaima wacce ba ta tsammace ta ba, tuna wacce take gabanta ya sa ta tsuke fuska haɗe da furta. "Ki jira ni." Uwar ɗakinta ta shiga can ƙarƙashin gado ta zura hannunta, ta ɗauko wani ƙoƙon kan ƙwarangwal. Wani garin magani ta ɗebo a ciki ta kulle a cikin wata 'yar busasshiyar ƙaramar fata. Ta fito zuciyarta fes cike da takun isa da ƙasaita. Sai da ta koma kan ƙasaitacciyar kujerarta ta zauna sannan ta miƙa wa Maimuna. "Ki fara zuwa ki karɓo maganin wurin Mai martaba, amma ki tabbata wannan kika ba ta ta yi amfani da shi, za ki zuba mata a ruwa ko abinci kuma ki tabbatar da ta shafe jikinta da shi. Duk dare ina buƙatar ganinki domin akwai fitar sirrin da nake so mu yi." Cike da girmamawa Maimuna ta russuna. "An gama ranki shi daɗe, fansar kaina gare ki ya shugabata domin kai da kaya duka mallakar wuyane. Ki sa a ranki na aiwatar da duk abin kika buƙata na gama, Allah ya taimaki giwar Takawa ɗawusu mai yawan ado." Fulani Umaima ta gyaɗa kai sannan Baiwa Maimuna ta miƙe, har ta je bakin ƙofa Fulani ta furta. "Ki tabbata ba a samu matsala ba, idan aka samu matsala ki kuka da kanki." Baiwa Maimuna ta russuna. "Godiya nake uwar gijiyata." Sai da Maimuna ta ɗaure maganin wurin Fulani Umaima sannan ta nufi sashen Mai martaba, Jakadiya ta samu ta sanar da ita saƙon Fulani Babba. Kai tsaye Jakadiya ta tunkari turakar Takawa. Sai da rangaɗa sallama haɗe da kirarin girmamawa sannan ta isar da saƙon Fulani Babba. Kamar ba zai amsa mata sai kuma ya miƙe ya nufi wata jakar fata da ke saƙale a jikin bango ya zura hannunsa, wasu ƙullin magunguna biyu ya ciro ya miƙa wa Jakadiya, ta karɓa tana godiya. Har ta fara tafiya ya furta. "Daga yau a sanar da ita ta riƙa karɓar magani kafin almuru, ba a koyaushe muke da buƙatar hakan ba." Jakadiya ta amsa sannan ta fice ta damƙa wa Baiwa Maimuna tana jaddada mata saƙon Mai martaba. Maimuna na shiga sashen Fulani Babba ta same ta kamar yadda ta bar ta, Baiwa Zainaba na gefe tana matsa mata ƙafafuwanta da suka ɗan kumbura. Cike da girmamawa ta miƙa mata maganin da Fulani Umaima ta bata sannan ta furta, "Allah ya ƙara wa Fulani lafiya, Ubangiji ya shiga lamuranki uwar ɗakina. Mai martaba ya ce a jiƙa rabi, rabi kuma a shafe miki jiki da shi." Idanun Fulani jawur kamar sabon barkono ta buɗe su a hankali ta furta. "A yi yadda ya da ce Maimuna." Zuciyar Maimuna ƙal ta tashi jiki na rawa ta jiƙa maganin kamar yadda Fulani Umaima ta gaya mata, ta taimaka wa Fulani Babba ta tashi zaune haɗe da kai mata ƙoƙon bakinta. Tas ta shanye shi sannan Maimuna ta shiga shafe mata a jiki gabaɗaya, sannu a hankali ta ji wata sassanyar iska na ratsata. Ta koma ta kwanta sakamakon jin daɗin jikinta da ta fara yi. Ta dubi su Baiwa Maimuna. "Maimuna za ku iya tafiya, Zainaba a tabbata an gyara makwanci su Khadija." Cikin girmamawa suka zube ƙasa, "An gama ranki shi daɗe, Allah ya ƙara lafiya ya kawo mana Yarima lafiya." Ba ta iya amsa musu ba sai ma runtse ido da ta yi sakamakon jin wata irin hayaniya da ta yi a tsakar kanta, ga wani irin jiri da ke ɗaukanta. A ɓangare ɗaya kuma wani abu mai tsini ya fara fusgar can cikin ƙasanta. A gurguje Maimuna ta fice haɗe da sake ba wa Zainaba umarnin gyaran ɗakin su Khadija da yake ita ce gaba da ita, ta juya ta fice daga ɓangaren 'yayan Fulani Babba. A sanyaye Baiwa Zainaba ta bi Maimuna da kallo don haka kawai take jin zuciyarta na wasuwasi a kan Baiwa Maimuna tun da ta taɓa ganinta ta shiga sashen Fulani Umaima sau biyu. Kai tsaye sashen Fulani Umaima ta faɗa, kuma a wurin da ta tafi a nan ta koma ta same ta. Fulani Umaima na ganin Baiwa Maimuna ta faɗa uwar ɗaki, wani sirrintaccen akwatinta ta ɗauko ta buɗe cikinsa. Kamar kullin idan za ta ziyarce shi haka take saka wannan sihirtacciyar rigar da Boka Bamagujen dutse ya bata, a lokacin ma sai da ta tube kayanta gabaɗaya sannan ta zura rigar mai ɗauke da launin ja, baƙi, ruwan ɗorawa da launin ruwan ƙasa. Rigar ɗinke take da waɗansu ƙananan layu sai kuma wasu ƙananun rubutu da aka yi da larabci, wani ɗan ƙaho ta riƙe a hannunta sannan ta fito wurin da ta bar Baiwa Maimuna. Hannu ta miƙa wa Maimuna babu musu da yake ta san kwanan zancen ta ɗora tafin hannunta a saman na Fulani Umaima, wanda ta tabbata ba don wannan sirrintacciyar tafiyar da suke yi ba babu dalilin da zai kai hannunta jikin Fulani Umaima, musamman yadda take nuna ƙyamar bayi da talakawa ƙarara a fili. Saka hannun Maimuna cikin na Fulani babu jimawa, ta runtse idanunta ta ɗaga hannunta da ta ke riƙe da ƙahon ta busa sau uku sannan ta kira sunan Bamagujen dutse sau uku. Wata irin guguwa ce ta karaɗe cikin ɗakin kamar ƙiftawar ido sai ga su a bakin wani ƙaton farin dutse mai ɗaukar ido, wurin kamar rana tarwai babu abin da ba ka iya gani. Kamar yadda yake bisa al'ada a duk lokacin da suka ziyarce shi, sai da suka saka ƙafarsu ta hagu a tare a kan wani jini da ke malale a gabansu. Sun ɗan ɗauki kamar minti biyu a haka sannan suka ji an bushe da wata irin dariya wacce take alamta musu aikin da ya da ce su yi a gaba. Ƙafarsu suka sake ɗagawa suka ɗora a kan wani kabari da ke gaban wannan jinin sannan suka fara takawa suka haye can sama dutse. Zaune suka hango shi babu ko ɗigon sutura a jikinsa, Maimuna ta kawar da kanta gefe don har cikin zuciyarta ba ta son ziyartar wannan shu'umin bokon don dai ba ta da yadda za ta yi ne. Suna ƙarasawa wurin wata ƙaramar bishiyar kuka Maimuna ta russuna tana faɗin, "Fatan nasara a kodayaushe ya shugabata." Fulani Umaima ta ci gaba da tafiya don Maimuna ta san ko karen hauka ne ya cije ta ba ta isa ta ƙara koda taku ɗaya ba. Fulani na zuwa sai da ta fara ɗiban wani jan ruwa a cikin wani ƙoƙon kan ƙwarangwal ta wanke fuskarta, sannan ta nemi wuri ta zauna tana fuskantar Boka Bamagujen dutse. "Barka da aiki uban gidana." Jinjina kai ya yi ya furta. "Barkanki Fulanin Sarki Abdul'aziz." Shiru ne ya ratsa Fulani Umaima ta kawo ido ta sa wa Bamaguje, ya saki murmushi don ya san wace ce Umaima. Ga tsananin buƙata fal ƙirjinta ga kuma taƙama da izzar mulki, kallo ɗaya ya yi mata ya fahimci halin da take ciki. "Umaima kin yi ƙoƙari." "Sanin haka ya sa na kawo ziyara a ranar da ka buƙata." Ta amsa masa a taƙaice. "Kin aiwatar da komai yadda ya kamata, don haka kishiyarki ita da Sarki Abdul'aziz sai kallo sai hange daga nesa. Matuƙar ba asirin nan ne ya karye ba, ba na jin kishiyarki za ta sake ɗaukan ciki a doron ƙasar nan. Ke ba ma ciki ba ina mai tabbatar miki ita da sake yin wata mu'amala da Sarki Abdul'aziz sai dai a lahira idan ana yi. Ina ragowar kayan aikin?" Ya wurga mata tambaya. Jin haka ya sa Umaima ta saki malalacin murmushi ta ɗebo gashin Fulani babba da gashin Sarki Abdul-aziz, haɗe da ƙasar maƙabarta da ta gidan tururuwa ta miƙa masa ba tare da ta tanka masa ba. "Mun sakar mata lalurar fitsarin kwance, kuma mun saka mata lalurar mantuwa da warin jiki." Bamaguje ya faɗa yana jefa tarkacen da Fulani Umaima ta bashi a cikin wata tunkunya da ke cike da jini tana tafasa. Kusan duk abin da suke tattaunawa Maimuna tana jin su, haka kawai ta ji tausayin uwar ɗakinta ya ɗarsar mata. Musamman da ta tuna zallar cin amanar da take yi mata mai haɗe da zagon ƙasa. "Ina maganar cikin jikinta ya kwana?" Fulani ta tambaya cike da izza. Bamaguje ta ɗebi wani jini mai yauƙi ya watsa a jikin wani allon farin ƙarfe. Take waɗansu inuwoyi suka bayyana, yana fara nazartarsu sai gani ya yi ɗuff komai ya ɗauke. Cikin da damuna ya sake ɗiban jinin ya watsa har sai da ya yi haka sau uku sannan ya dubi Umaima cikin damuwa. "Kishiyarki a daren yau za ta haihu!" Dum! Fulani ta ji tsakiyar kanta ya sara kamar wacce aka buga wa guduma. Rai a ɓace ta dube shi. "Wanne irin mugun labari nake ji haka, zancen banza kenan ƙafa ta mutu ta bar takalmi. Cikin jikinta ya fi komai ɗaga mini hankali..." Da sauri ya katse ta. "Tun fil azal kundunsa rubuce yake da zanen ƙaddararsa, cikin kishiyarki shu'umin ciki ne lulluɓe yake da almara tamkar yadda masarautarku ta kasance SHU'UMAR MASARAUTA. Kamar yadda na gaya miki a yau za ta haihu..." Duk dakiya da ƙarfin zuciya irin ta Fulani Umaima sai da hawaye ya suɓuto mata, Bamaguje ya tsaya yana kallonta haɗe da jinjina kai. "Yau shekarata biyar kenan a cikin masarautar nan ko ɓatan wata ban taɓa yi ba, tun Fulani babba na da goyon fari Takawa ya auro ni. Bamaguje kana son na ƙare rayuwata cikin ƙasƙanci da rashin mamora?" Girgiza kai ya yi, ya sauke ajiyar zuciya. "Wa ya ce miki ba za ki haihu ba?" Fulani ta zuba masa idanu zuciyarta na bugawa. "Yanzu haka kina ɗauke da juna biyu na tsawon makwanni uku." Kamar a mafarki haka ta ji kalaman Bamaguje na ratsa majiyar sautinta. "Ki yi imani da ni Umaima matuƙar ina numfashi ba za ki tozarta ba." Sanyi ta ji har cikin ranta. "Da kai na dogara Bamaguje na yi imani da kai tun da ba ka kunyata mahaifiyata ba na tabbata ba za ka tozarta ni ba." Ta yi maganar a raunane. Wata ƙatuwar kunama ya ɗauko da hannunsa ya ce, "Ba ni hannunki." A firgice ta wurga masa kallon baka da hankali, ya saki murmushi don ya fahimce ta. "Umaima kenan kura kike ga tsoro ga ban tsoro." Umaima ta haɗe fuska kamar ba ita ba. "An ya kuwa? Kar fa ka manta ko kura ta rame ta fi ƙarfin gawurtattun karnuka, dalilin haka ya sa masallacin kura ba a ba wa kare limanci." Murmushi Bamaguje ya yi. "Kwantar da hankalinki kamar kin faɗa rijiya. Matso kusa ki ji." Bamaguje ya furta. Tun bai rufe baki ba Umaima ta matsa kusa da shi, raɗa ya yi mata a cikin kunne lokaci ɗaya ta bushe da wata iriyar dariya cike da farinciki. Ta koma mazauninta na farko tana sauraronsa. "Ki tabbatar da kin aiwatar da abin da na umarce ki, don kuwa kowa rai ya yi wa daɗi ba ya mai shi ba." "Bamaguje kenan! Ai ranar biyan buƙata rai ba a bakin komai yake ba." Umaima ta furta cike da nishaɗi. Kashe mata ido ɗaya ya yi yana ƙare mata kallo, ganin haka ya sa ta fahimci inda ya dosa. "Tukwina fa?" "Ka sallame ni kenan?" Ita ma ta wurga masa tambaya. Gyaɗa mata kai ya yi Umaima ta miƙe babu ko kunya ta sauke rigar tsubbun jikinta, Maimuna ta sunne kai ƙasa zuciyarta na bugawa. A fakaice take ƙare wa tsohon kallo cike da ƙyanƙyami don ko ita da take baiwa gani take ba za ta iya haɗa jiki da shi ba. Bamaguje na shirin ɗora hannu a jikinta ta ɗan ja da baya haɗe da sakin murmushin mugunta. "Na sadaukar maka da kishiyata a wannan daren, shi ne tukwicin da zan iya yi maka." Ba ta jira cewarsa ba ta ɗora rigar a jikinta. Bamaguje ya gyaɗa mata sannan ya furta. "Za ku iya tafiya." Umaima ta yi masa jinjina da hannu sannan ta sake ɗiban ruwan da ta wanke fuska da shi ta nufi wurin da Maimuna ke zaune hannunta ɗauke da kunamar da Bamaguje ya damƙa mata. Abin da suka aiwata a farkon zuwansu yanzun ma haka ne ya faru, sai da suka koma daidai wurin da suka buɗe ido suka gan su tun farkon zuwansu sannan, Fulani Umaima ta ɗaga ƙahon ta runtse ido ta busa haɗe da kiran sunan Bamaguje. Ƙamshin ɗakin Fulani ne ya ankarar da Maimuna dawowarsu gida, cike da girmamawa ta zube ƙasa ta furta. "Allah huta gajiya uwar gijiyata." "A kullin ina sake jaddada miki bakinki ƙanin ƙafarki Maimuna, duk ranar da kika bari kwaɓarki ta yi ruwa na ji sirrina ya fita za ki bambamce mini tsakanin tsaba da tsakuwa." Fulani ta yi maganar cikin sigar gargaɗi. "Maimuna ta duƙa kai ƙasa. "Wace ni uwar gijiyata? Kada Allah ya nuna mini ranar da zan aikata miki wannan zunubin ranki shi daɗe." Fulani ta taɓe baki, "Za ki iya tafiya." Da sauri Maimuna ta fice ko waige ba ta yi. Har za ta nufi sashen su na bayi sai uwar ɗakinta Fulani babba ta faɗo mata. Haka kawai ta ji sam ba ta kyauta ba. Zuciyarta ta ci gaba da azalzalarta da ta je ta ga halin da take ciki. Cikin sanɗa ta nufi sashen Fulani babba gabanta na faɗuwa. A haka ta ci gaba da tafiya har cikin ɗakin, ras! Ƙirjinta ya buga jikinta ya ɗauki karkarwa sakamkon ganin Fulanin a yashe babu sutura a jikinta. Wani tafkeken maciji ta gani a tsakanin ƙafafuwanta ya kafa kansa a saitin ƙasanta, ga wani irin gurnani da macijin ke yi. Idanun Fulani a rufe amma sai mutsu-mutsu take yi, da alama ma bacci take yi. Daga bayanta ta ji an dafa kafaɗarta, wani abu ne ya tsarga mata ta yi mutuwar tsaye cikin sanyin jiki ta waiwayo. Karaf idanunta suka sauka a kan Fulani Umaima da ta haɗe girar sama da ta ƙasa. _Ummou Aslam Bint Adam_🌚 07062062624. *SHU'UMAR MASARAUTA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ƙirƙirarran labari ne bai faru a gaske ba. Ban yi shi don cin zarafin kowacce ƙabila da Masarautunsu ba. SHAFI NA BIYU Ras! Ta ji gabanta ya yi mummunan faɗuwa, lokaci ɗaya ta nemi yawun bakinta ta rasa. Cikin firgici ta buɗe baki za ta yi magana Fulani Umaima ta katse ta. "Me kike yi a nan kuma uban me kike leƙe?" Maimuna ta zube a ƙasa jiki na rawa ta furta. "Ki yi mini aikin gafara uwar gijiyata, na zo na ji ko Fulani nada buƙatar wani abu kafin na tafi." Da hannu Fulani Umaima ta nuna mata hanya, sum sum sum Maimuna ta fice jiki na karkarwa. Fulani Umaima ta leƙa Fulani babba da ke kwance, ta saki murmushi mai ɗauke da ma'anoni a hankali ta furta. "Mu zuba mu gani idan tusa na hura wuta, in dai ni ce yanzu kika fara gani." Daga haka ta fice daga ɗakin. Fulani babba ta jima a haka sannan ta farka, a hankali take sauke ajiyar zuciyata. Duk da a mafarki ta ga Mai martaba yana kusantarta abin ya yi mata daɗi, ta ji farinciki matuƙa saboda idan ba mantawa ta yi ba rabon da wani abu ya shiga tsakaninta da Takawa tun cikin jikinta bai fi wata biyu ba. Danshin da ta ji a jikinta ne ya sa ta kai hannunta, da mamaki take kallon makwancin nata. Da ƙyar ta yunƙura ta tashi nan take fitsarin da ke naɗe da zaninta ya fara ɗiga, da farko ta yi tsammanin ko faya ce ta fashe mata tun da a halin da take ciki tana iya haihuwa a kowane lokaci, musamman da take jin ciwon mara sama-sama. Sai dai zarni-zarnin da ta ji ne ya sa ta shinshina hancinta. A hankali ta furta. "Fitsari? Ni kuma? Kai ina jin dai faya ce ta fashe." Gudun wasu-wasi ya sa da kanta ta ɗebo ruwa ta sa a katifar ta sauya kayan jikinta amma har lokacin gani take faya ce ta fashe mata. Banɗaki ta shiga ta yi wanka ta fito sannan ta ɗan ci abinci, a hankali ta ji mararta na ci gaba tsikararta daga baya bacci ya sake yin awon gaba da ita. Fulani Umaima kai tsaye sashenta ta wuce don a ranar ba ta jin sha'awar zuwa wurin Mai martaba. Da shigarta babu jimawa sai ga Jakadiya ta shiga ɓangarenta da saƙon Mai martaba na gayyatarta zuwa turakarsa, ba don ta so ba haka ta amsa mata. Jakadiya har za ta tafi Fulani ta dakatar da ita. "Jakadiya ba na son ki yi nisa da sashen Fulani babba." Jakadiya ta amsa mata sannan ta fice. Cike da kissa Fulani Umaima ta shirya kanta da sihirtattun turarrukan da Bamaguje yake haɗa mata, ta ƙarasa turakar Mai martaba. Zamanta babu jimawa suka ji wata ƙarar busar sarewa. Da sauri Fulani da leƙa kusurwar turakarsa idonta ya sauka a kan ƙaton shurin da gudajen turuwa suka zagaye da ke cikin ɗakin, gabanta ya yanke ya faɗi don ta san tun da ta ji wannan sarewar a yau mai afkuwa za ta afku. Mai martaba ya saci kallonta, haka kawai yake jin shakkarta a zuciyarsa. Amma ko shakka babu wannan busar sarewar da shuri ya saki na da alaƙa da cikin jikin Fulani babba wanda yana da yaƙini za ta iya haihuwa a cikin daren nan. Ya so ya tanka wa Fulani Umaima amma sai ya fasa, hakan ya sa ta saki murmushi cikin kissa. "Jikina yana ba ni Fulani babba na gab da kawo mana Yarima, wannan abin farinciki ne. Tun da shuri ya saki sarewa na tabbata a yau za mu iya samun ƙaruwa a gidan nan." Faɗaɗa murmushinsa ya yi, ya janyo Fulani Umaima jikinsa ya furta. "Wannan haka ne yanzu me kike ganin ya kamata a yi?" "Ina ganin zai fi kyau a yi dakan ɗaka shiƙar ɗaka... sai a kira Jakadiya ta zauna a wurinta koda ciwon zai tashi tana kusa da ita, a madadin a kira Ungozoma. Amma sai yadda kace ranka shi daɗe farin jakada." Fulani Umaima ta ƙarasa magana tana sunkuyar da kai ƙasa. Ajiyar zuciya Mai martaba ya yi, "Na baki wuƙa da nama mai farar zuciya Allah ya yi miki albarka." Fulani Umaima ta amsa sannan hirar tasu ta fara sauya salon faranta ran ma'aurata. Zuciyar Fulani Umaima ƙal ta je ta samu Jakadiya da zancan Takawa, Jakadiya na gama sauraronta ta yi ƙasa da murya tana ɗan waige sannan ta ce. "Wani ma ya yi rawa ma ballantana ɗan makaɗi? Ai wallahi sai mun ga abin da ya ture wa buzu naɗi. Ina mai yi miki albishi tauraruwar Mai martaba gobe war haka Fulani Babba na nan cunkushe da baƙin ciki fal ƙirjinta, idan an isa a yi Yarima ba a ɗakinki ba shegiya nake." Fulani Umaima ta saki dariyar ƙeta. "Jakadiya tamkar zuma haka kike ga zaƙi ga harbi. Na aminta da ke fiye da haka ma za ki iya aikatawa." "Ai shi abin kasuwa na mai ciniki ne, ni ta ki ce Fulani har abada ina bayanki. Fulani kin manta ɗayan kirarin nawa kaska rabi mai jini ki bar shi da gashi." Fulani Umaima ta jinjina kai alamun gamsuwa. Jakadiya ta sake ƙasa da murya. "Allah ya taimake ki ni zan ƙarasa zan biya na taso Baiwa Maimuna da zarar haihuwa ta taho gadan-gadan zan turo miki ita." Murmushi Fulani Umaima ta yi har Jakadiya ta yi gaba ta sha gabanta da sauri ta furta. "Jakadiya a kawo mini kayan Bayi sashena, sannan a tabbatar an bawa Maimuna ta kawo mini cikin hanzari." Shiru Jakadiya ta yi tana nazaratar Fulani. Cikin zuciyarta tana ayyana ƙwarewarta a mugun makirci da ƙuduri. Da sauri Jakadiya ta wuce ɓangaren Fulani Babba a lokacin da ta ƙarasa dare ya tsala sosai, sai da ta yi sallama sannan ta shiga har cikin ɗakinta. Shigar Jakadiya ya yi daidai da farkawar Fulani babba, ƙarasawa ta yi gabanta ta ce. "Allah ya taimaki uwar ɗakina ya ƙarawa Fulani lafiya. Yanzu haka Mai martaba ne ya turo ni a kan na kwana da ke saboda yanayin da kike ciki, domin tuni shuri ya saki sarewa." Murmushi Fulani ta yi don ko ba komai ta ji daɗin yadda Takawa ya ba ta kulawa, hannu ta miƙa wa Jakadiya alamar ta taimaka mata. Wani abu ta ji ya tsira wa mararta haɗe da bayanta. Cije baki ta yi jin ciwon na ƙara tsanani gadan-gadan. A haka ta miƙe ta ƙarasa banɗaki da ƙyar don ta gyara jikinta, a lokacin da ta tashi ta sake lura da fitsarin da ya jiƙe makwancinta sharkaf, na wannan lokacin har ya fi na baya yawa da wari. Fulani na dawowa kafin ta shiga ɗakin ta ci karo da wata mata baƙiƙƙirin a tsaye a dokin ƙofa. Hannu ta miƙa mata cikin wata irin murya ta furta. "Ba ni cikin jikinki!" Da Mamaki Fulani ke kallonta har lokacin ciwo na cin ta, "Wace ce ke? Me ya sa zan baki cikin jikina?" Tana rufe baki ta ga matar ta miƙa hannuwanta masu ɗauke da waɗansu irin baƙaƙen farata da zaƙwa-zaƙwan yatsu, ta miƙa hannun da niyyar shafa saman cikinta, Fulani da sauri ta ja baya haɗe da furta. "A'uzubillahi, Innalillahi..." Da gudu ta ga matar ta shige cikin sashenta, wata uwar ƙara ta ƙwalla nan take sai ga Jakadiya ta nufo wurin da gudu. Jiki na karkarwa Fulani ta ce, "Jakadiya baki ganta ba?" Jakadiya ta waiga hagu da dama ta ce, "Wa kenan ranki shi daɗe?" Dum! Fulani ta ji kanta ya yi nauyi tana son tuna a kan abin da Jakadiya take tambayarta amma ta manta, gumin da ke tsattsafo mata ta share ta ce, "Ba komai mu je Jakadiya marata ciwo take. Wash! Bayana zai ɓalle." Jakadiya ta taimaka mata suka ƙarasa ciki, kafin fitowar Fulani daga banɗaki tuni Jakadiya ta gyara wurin ta haɗa gabaɗaya kayan karɓar haihuwa. Ganin zaƙi haɗe da jini ya fara bin ƙafar Fulani ya sa Jakadiya ta shimfiɗa mata ƙatuwar leɗa, Fulani da ƙyar ta yunƙura ta hau kai tana jin ƙasanta tamkar ɗa zai faɗo. Fulani Umaima ce ta yi sallama daga bayanta Baiwa Maimuna na biye da ita, yadda Fulani Umaima ta marairaice tana yi wa Fulani babba sannu sai ka rantse zuciyarta cike take fal da tsoron Allah. Wani jan ƙoƙo ta miƙa mata ta furta, "Mai martaba na cikin tsananin damuwa da jin halin da kike ciki, musamman da ya tuna da mutuwar Marigayya Fulani Samira. (Matar Sarki Abdul'aziz ta uku ce da ta rasu wurin haihuwa.) Ya umarci da a kawo miki wannan yanzu na karɓa a hannun Shamaki." Ɗago kan Fulani babba ta ga Fulani Umaima ta sauya mata a kammani, har take ganin kamar ta taɓa sanin kamannin, sai dai kuma ba ta jin za ta tuna kalar fuskar. Baiwa Maimuna da ke tsaye jikinta ya yi sanyi don ta san garin maganin ba ya wuce na wurin Bamaguje. Fulani Babba ta karɓe za ta kai baki ta ji wani irin nishi ya taso mata, cikin tsananin azaba ta wurgar da ƙwaryar gefe ta riƙe Jakadiya da ke gefenta, take jaririn ya faɗo ya fara mutsu-mutsu yana tsanyarewa da kuka. Wani irin baƙin ciki ya turniƙe ta Jakadiya ta waiga tana kallon Fulani don sanin irin hukuncin da za su yanke, da sauri Fulani Umaima ta fita sakamakon manta kunamar da Bamaguje ya bata. Jakadiya ta tsugunna ta sa reza ta yanke masa cibiya, a tunaninta ko Fulani Umaima ta zubda makamanta ne tun da jaririn ya riga da ya zo duniya. Ta gama yanke masa cibiya kenan Fulani Umaima ta faɗo ɗakin hannunta ɗauke da wata ƙatuwar kunama, a daidai lokacin Fulanin ta sake wani yunƙurin babu jimawa wani jaririn ya faɗo. Kusan mutuwar tsaye gabaɗaya suka yi, fuska babu walwala Fulani Umaima ta ƙarasa ta ɗora kunamar a kan jinin da ke zuba daga ƙasan Fulani Babba, kunamar na fara zuƙar jinin Fulani babba ta yanke jiki ta faɗi jikinta na wani irin karkarwa. Fulani Umaima ta saki shu'umin murmushi, sai dai kuma ganin jariran biyu ya sa ta samu shakkun wanda za ta aiwatar da mugun ƙudurin a kansa, na farkon da jakadiya ta yankewa cibi ta naɗe a zani ta ɗauka, take zuciyarta ta ƙwaɗaita mata wata shawara. Kiran Baiwa Maimuna ta yi ta damƙa mata shi, sannan ta ƙarasa gaban ɗayan jaririn da ko cibiya ba a yanke masa ba. Wutsul-wutsul yake yana kuka ta ɗauki kunamar da ke cikin jinin ta buɗe bakinsa da ƙarfin tsiya ta matse kunamar a cikin bakinsa. Take wani irin ruwa mai yauƙi haɗe da jini ya fara ɗiga a bakinsa. Kamar yadda yaro yake kama mama haka jaririn ya riƙa tsotsar jini da ruwa mai yauƙin. Ya jima yana sha sannan jaririn ya fara wani irin kakari wani farin ruwa mai haɗe da jini na fita daga hanci da bakinsa. Fulani ta waiga wurin Baiwa Maimuna ta furta, "Ina buƙatar ki fita ta ƙofar baya a sirrince, ki samu ƙaton kogi ki jefa shi ko kuma ki samu wani ƙaton ramin ki binne mini shi. Duk rintsi kada ki bar shi da sauran numfashi, idan ba haka ba ranki zai yi mummunan ɓaci." Baiwa Maimuna da jikinta ya gama sanyi ta ce, "An gama ranki shi daɗe." Har Maimuna ta yi gaba Fulani Umaima ta katse ta, "Iya ruwa fida kai. Kowa ya biya allonsa ya wanke. Ki tabbatar ba a samu matsala ba, wallahi matuƙar asiri ya tonu sai kin gayyaci mutuwarki da bakinki. Ni da kika ganni ba na ƙwaina sai da zakara don haka ki bi sannu, shawara ce na baki don kar ki bari kwaɓarki ta yi ruwa." Baiwa Maimuna ta russuna rungume da jaririn ta furta, "Tuba nake ragamar damisa a ja ki da nisa. Na yi tsammanin kin fahimci somu-somun hauka zubda yawu. Mai ƙafa ɗaya ma ya yi rawa ballantana mai biyu? Indai ni ce har gaban abadan ba zan taɓa baki matsala ba." Fulani Umaima ta saki malalacin murmushi ta furta, "Na aminta da ke Maimunatu, idan kin kammala komai ki samu Jakadiya akwai kyakkyawar kyauta. Amma ina buƙatar ganinki da zarar kin kammala." Cike da girmamawa Baiwa Maimuna ta ce. "Godiya nake giwar Takawa fara mai farar aniya, sikari baki yi farin banza..." "Ba mu da isasshen lokaci ki hanzarta ki fita." Fulani Umaima ta katse ta a taƙaice. Daga haka Baiwa Maimuna ta fita daga sashen Fulani ta ƙofar baya, cikin duhu haka ta ci gaba da tafiya tana ratsa bishiyoyi da ƙayoyi har ta samu ta fita ta can bayan Masarauta. Ganin har lokacin jaririn bai daina kakarin da yake yi ba ya sa Jakadiya ta dubi Fulani Umaima. "Ranki shi daɗe me zai hana mu ƙarasa shi tun da har yanzu bai ƙarasa mutuwa ba?" Da ido Fulani ta kafe jaririn. "Bamaguje bai ba ni damar haka ba, ki tsaya kawai mu zura wa sarautar Allah ido. Kuma ni kaina ba na son ya mutu yanzu, na fi son na dasa wa Fulani Babba ɓacin ran da har ta mutu ba za ta manta da shi ba." Jakadiya ta jinjina kai a daidai lokacin da jaririn ya tsagaita da wannan kakarin, a lokacin Fulani Babba ta farfaɗo. Ta yunƙura a hankali da niyyar tashi da yake jikinta babu ƙwari sai Jakadiya da Fulani ne suka taimaka mata. "Sannu Yaya, barkanmu da arziƙi Allah dai ya kawo mana Yarima lafiya." Fulani Umaima ta furta tana sakar mata murmushi, wani irin yammm take ji a jikinta kamar tafiyar kiyashi, jiki babu ƙwari ta sakar wa Fulani Umaima murmushi. Idonta ne ya kai kan jaririn da ke kwance ta kafe shi da idanu, wani abu take son tunawa amma kanta ya yi nauyi ta gagara tunawa. Jakadiya ta saki guɗa da ƙarfi tana ɗaukan jaririn da ilahirin jikinsa ya haɗe da gumi, ga wani irin zafi zam a kan fatar jikinsa. Guɗar da Jakadiya ta yi ce ta alamta wa Dogaran da ke kewaye da sashen saukar Fulani babba, kafin wani lokaci tuni labari ya isa wurin Mai martaba. Fulani da Jakadiya tuni suka gyara jariri da mai jego, an turare ɗakin da turaren wuta ko ina sai buga ƙamshi yake yi. Sai dai Fulani babba tana ƙare wa yaron kallo ta fahimci kamar idanunsa ba daidai suke ba, ga yawu da yake ɗan ziraro masa ta gefen bakinsa hancinsa na yoyon majina. Ƙura masa ido ta yi tana son tuna wani abu da ya shafi lokacin da take naƙuda har zuwa haihuwarta, sai dai nauyin da kanta ya yi ne ya haddasa mata ciwon kai ɓari ɗaya take jin kamar zai tarwatse mata. A hankali ta kalli Fulani Umaima cike da murmushi, "Na gode sosai da kulawarki ƙanwata." Fulani Umaima ta saki murmushin yaƙe don saboda rufewar ido har gani take babu abin da maganin Bamaguje ya yi wa jaririn, amma saboda kissa sai ta furta. "Haba Fulani babba me ye abin godiya ina ce da kai da kaya duka mallakar wuya ne?" Fulani babba ta jinjina kai cike da jin daɗi ta ce. "Amma kuma yaba kyauta tukwici in ji masu iya magana." "Ai lamarin tuwona maina aka yi, ni dai bari na wuce Fulani na ji asuba ta fara ƙaratowa." Fulani Umaima na zuwa sashenta ta faɗa gado cike da tashin hankali. "Ya zame mini dole na ziyarci Bamaguje kuma a yau ba sai gobe ba sai ya hallaka mini Fulani da abin da ta haifa, idan ba haka ba zuciyata bugawa za ta yi." Ta ƙarasa maganar tana shiga cikin uwar ɗakinta. Tafiya mai nisa Baiwa Maimuna ta yi har sai da ta yi nisa da masarauta, ta shiga cikin wani daji mai duhun bishiyoyi. Kuka jaririn ya fara yana wutsul-wutsul, bankaɗa zanin ta yi ta ji tausayinsa ya mamaye zuciyarta. Da yake asuba ta yi haske ya fara mamaye cikin dajin, wani ɗan rami ta hango da ke gefen wata murgujejiyar bishiyar kuka, kallon bishiyar kukar kaɗai ya isa ya tsoratar da gangar jikin mammallakiyar ƙwayar idon. Da sauri ta ƙarasa wurin ta tsugunna sai a lokacin ta lura da zagayyan gidan tururuwar da ke wurin, taku ta fara jiyowa a ɗan nesa da ita da sauri ta saka shi a ciki ta bar wurin ta ɓoye a bayan wata bishiya, amma ga mamakinta sai ta ji shiru babu kowa. Gudun kada asirinta ya tonu ya sa ta fara zabga gudu ta nufi hanyar gida, a yadda take ji ba ta jin za ta iya kashe jaririn da bai ji ba bai gani ba, don rashin imaninta bai kai nan ba. Tana cikin gudun ta ji ta yi karo da wani abu garam! Har sai da ta faɗi ƙasa. Tsoro, firgici da matsanancin tashin hankali ya mamaye ta, take jikinta ya hau karkarwa sakamakon ganin bishiyar kukar da ta kwantar da jaririn a gabanta ta tsaya dass kamar yadda ta baro ta a baya. _Ummou Aslam Bint Adam_ 🌚 07062062624. *SHU'UMAR MASARAUTA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ƙirƙirarran labari ne bai faru a gaske ba. Ban yi shi don cin zarafin kowacce ƙabila da Masarautunsu ba. SHAFI NA UKU Fulani Umaima har ta zura hannu za ta ɗauko ƙahon ta busa sai kuma ta ayyana ta bari idan Maimuna ta dawo ta ji yadda ta ƙarke idan ya so sai ta ziyarci Bamaguje, saman gadonta ta faɗa ta kwanta babu jimawa bacci ya yi awon gaba da ita. Sannu a hankali ta fara jin dariya sama-sama, sai dai kuma yanayin dariyar ya tababtar mata da dariyar ƙaramin yaro ce. Ba ta tsinke zaren tunaninta ba ta hango wani jariri tube tamkar a lokacin ya zo duniya, tunkaro ta yake yana ci gaba da ƙyaƙyata dariya hannunsa da wata murtukekiyar igiya yana jan waɗansu murtuka-murtukan shanu, hannunsa ɗaya ɗauke da kwari da baka. A tsorace ta miƙe tana ja da baya ganin jaririn na saita ta da niyyar harba mata, jin bango ya tokare ta ta baya ya sa hankalinta ya sake kai wa matuƙar ƙololuwar tashi. Sai da yaron ya zo gabanta ya furta, "Ba yanzu ba! Zan ƙara miki lokaci." Yana gama maganar ta ga ya juya yana ci gaba da ƙyaƙyata dariya. Firgigit Fulani Umaima ta tashi daga nannauyan baccin da ya ɗauke ta har ya gayyato mata mafarkin da ke neman wargaza kwanyarta. Ajiyar zuciya take saukewa akai-akai sannan ta jingina da bango, da ta ga zaman ba zai kai ta ba ta faɗa banɗaki ta yi wanka ta ɗauro alwala ta gabatar da sallar asuba, a lokacin da tuni rana ta jima da fitowa. Kamar a mafarki haka ta ga bishiyar na sake tunkaro ta, a yadda take a zaune a ƙasa ta fara ja baya ilahirin jikinta na karkarwa. Wata irin iska mai haɗe da guguwa ce ta taso, Baiwa Maimuna ta sa hannuwa biyu ta rufe idanunta jin ƙura na shigar mata ido. Kamar an yi ruwa an ɗauke haka Maimuna ta ji wurin shiru tana buɗe idanunta ta nemi bishiyar ta rasa, a zabure ta tashi ta ci gaba da gudu kamar wacce ake bi a baya za a zare ranta. Ta jima tana abu ɗaya sannan ta ƙarasa ta bayan masarautar, a lokacin tuni gari ya waye. Sai da ta fakaici idon Dogarawan da ke gefen hanya sannan ta yi sauri ta shiga cikin gidan, tafiya take kamar za ta tashi sama don kallo ɗaya za ka yi mata ka fahimci kwanciyar hankali ya yi ƙaura daga gangar jiki da ruhinta. A haka da samu ta ƙarasa sashen matan sarki tana gab da shiga sashen Fulani Umaima ta ci karo da Uwar bayi, ƙare mata kallo ta yi sama da ƙasa sannan ta ce. "Maimuna daga ina kike haka?" Marar gaskiya ko a ruwa gumi yake, take Maimuna ta yi fiƙi-fiƙi baki na rawa ta furta. "Amm da ma... Yanzu..." Daga can baya Jakadiya ta katse ta, "Uwar Bayi tare muka kwana da ita a sashen Fulani babba yanzu haka gyare-gyare ta gama yi mana." Jinjina kai Uwar bayi ta yi sannan ta wuce, Jakadiya ta ƙarasa wurin Maimuna ta ce. "Ya kamata ki riƙa sara kina duban gatarinki, ki riƙa gayyato nutsu kina yafa wa a gangar jikinki. Kin san sarai wace ce Fulani Umaima." Ajiyar zuciya Maimuna ta sauke ta amsa wa Jakadiya sannan ta wuce sashen Fulani Umaima jiki a saɓule. Tun da ta doshi sashen take jin gabanta na faɗuwa ta rasa dalili, gani take kallo ɗaya idan Fulani ta yi mata asirinta zai iya tonuwa. A haka ta lulluɓa mayafin jarumta ta shiga cikin gidan tana karkaɗe jikinta da ya yi butu-butu da ƙasa. "Barka da hutawa ranki shi daɗe." Ƙuri Fulani Umaima ta yi wa Maimuna tana karantar yanayinta. "Binne jariri tamkar wacce ta yi dambe da jarumai biyar, Maimuna me yake faruwa na ga jikinki kamar wacce aka tono daga rami?" Ras! Gaban Maimuna ya faɗi, murya na rawa ta ce. "Ranki... Shi daɗe... Dama... zuwa na yi na sanar da ke an aiwatar da komai... Cikin nasara." Shekararta kusan hudu da Maimuna, ta karanci halaye da ɗabi'unta sarai. Take ranta ya yi mummunan ɓaci don ta fahimci zallar ƙarya a saman harshenta. "Me ya sa na amince za ki iya yi mini komai ban aiwatar da kaina ba?" Fulani Umaima ta yi maganar cike da murmushin yaƙe. Ɗakinta ta faɗa ta ɗauko ƙaho cikin shigar ziyarar Boka Bamaguje, ba ta tanka wa Maimuna komai ba ta miƙa mata hannu, zaro idanu Maimuna ta yi ta ji wani abu yana tsarga mata. Babu yadda za ta yi ta ɗora hannunta a kan nata, ba su jima ba sai ga su a fadar Boka Bamaguje. A wurin da ta saba zama koyaushe yanzun ma a nan ta zaune, gumi ya jiƙe jikinta sharkaf zuciyarta na dakan lugude kamar za ta hudo ƙirjinta. Fulani Umaima ta ce, "Bamaguje ina zargin Maimuna da cin amanata." Bamaguje ya saki murmushi. "Ba zargi ba ne domin yanzu haka duka jariran Sarki Abdul'aziz suna raye a doron ƙasar nan. Ba ta kashe shi ba kamar yadda kika buƙata." Wani yawu mai ɗaci Fulani Umaima ta haɗiya, ta wurgawa Maimuna kallon tsana. A firgice Maimuna ta zube bisa gwiwoyinta hawaye bibbiyu na zuba, "Ki gafarce ni uwar ɗakina wallahi..." Daga wurin da Fulani take ta ɗaga mata hannu. "Kin wargaza mini shirina Maimuna. Na yi rantsuwa da abin da ya busa numfashina sai na shayar da ke ruwan uƙuba mai tsanani." "Faɗuwa ce ta yi daidai da zama." "Ban fahimci kalamanka ba Bamaguje." "Ina nufi sarane za a yi a kan gaɓa. Kin san akwai muhimmin aikin da na alƙawarta miki kwanaki, zan sadaukar da shi a kan baiwarki. Idan kuma za ki samo wata sai a aiwatar a kanta." Jin kalaman Bamaguje ya sa Fulani Umaima dariya ta sauya fuska cikin damuwa. "Amma kafin aikin Bamaguje ya aka yi aka haihu a ragaya? Na yi tsammanin kunamar da ka ba ni za ta hallaka jaririn Fulani? Ina fa tsoron kada wankin hula ya kai ni dare." Wata baƙar mujiya Bamaguje ya ɗauka ya sa hannu ya fige fukafukanta da ranta, ta saki wani kuka cike da azaba sannan ya jefa ta cikin wani daskararran jini. Ya shiga gudanar da al'amuran tsubbunsa, yana cikin yi ya ga tukwanen gabansa sun rushe. A razane ya ɗago yana ɗan ja da baya, ya sake kai hannun da niyyar sake aiwatarwa kamar saukar aradu ya ga wata baƙar kwari da baka ta faɗo tsakiyar tukwanen. Tashin hankalinsa ne ya tsananta, ya ɗago yana sharce gumin fuskarsa da ke cike da gashi. Garin wata farar ƙasa mai walwali da ɗaukan ido ya ɗebo ya watsa, nan take wata narkekekiyar baƙar saniya ta bayyana jingine da kwari da bakar nan. Da bayyanarta babu jimawa duka wutar wurin ta ɗauke, ƙirjin Bamaguje ya buga ya ɗago ya dube ta. "Tabbas wanzuwarsa a doron ƙasa akwai sanadi, ban san wacce kalar baiwa da matsayi ruhinsa ke ɗauke da shi ba. Sai dai a duk bincikena na garara gano taƙamaimai wane ne shi? Abu ɗaya shafin ƙaddararsa ya buɗe mini shi mai nasara ne, sai kuma samun goyon baya da taimakon ruhi da ke lulluɓe da fatarsa..." Cikin rashin fahimta Fulani Umaima ta katse shi, "Ban fahimci gurbin da kalmanka suke neman samun zama ba, wane ne shi wanda kake magana a kansa?" "Jinin Sarki Abdul'aziz wato jaririn da kika sa aka fitar da shi, tabbas akwai ɓoyayyan al'amari a tattare da wannan yaron. Babban kuskuren da kika tafka kenan, da kika sa aka fitar da shi daga masarautar ba tare da shawara da ni ba. Zancan da nake yi miki yanzu ruhinsa ya yi nisan kiwon da babu hallitar da ta isa ta kawar da shi daga doron ƙasa. Ba zan ɓoye miki ba, daga ni har sauran matsafan da ke doron ƙasa ba na jin akwai wanda zai iya bankaɗa miki labuben sirrinsa, ba ina miki magana a kan masakin ɗan'uwansa ba domin wannan da shi da gawa marabarsu sauka da hawan numfashi. A yadda kika gan shi a haka zai ƙare rayuwarsa a nannaɗe, hatta ruwa da abinci idan ba a ba shi ba sai dai ya dauwama da yunwa. Shi kuwa wance ingarma ne mai ɗauke da rikitattun al'amura, amma ba zan yi miki iyaka ba Umaima idan har kina ganin za ki jarraba wani masanin fiye da ni ga fili ga mai doki." Wata gwauruwar ajiyar zuciya ta sauke fuska ɗauke da damuwa ta ba shi amsa, "Ba zan ja da kai ba Bamaguje domin na tabbata zaɓenka da mahaifiyata ta yi a matsayin madogara ba za ta yi zaɓen tumun dare ba, a halin da nake ciki babban burina bai wuce masarautar Zazzau ɗin nan ta dawo ƙarƙashin ikon abin da zan haifa ba wala Takawa yana raye ko baya raye." Bamaguje na ƙarasa jin kalamanta ta ɗauko wani baƙin ƙaho ya kai shi saitin idonsa na hagu ya haske wani allon farin ƙarfe mai ɗauke da rubutun jini, ƙahon da ke hannunsa na fesar da wani tartsatsin jini a jikin kaskon. Ƙuri ya yi yana kallo yana sake fahimtar al'amuran da ke wanzuwa a kwarmin ƙwayar idonsa, kamar kazar da aka jefa da gishiri haka Bamaguje ya ajiye ƙahon ya dube ta. "Za ki haifi gawurtacce kuma ingarman matashin saurayi, mai cike da isa ƙasaita da izzar mulki. Kuma zai kasance sarki wato magajin karagar sarki Abdul'aziz..." Murmushi da murnar Fulani ya katse kalaman Bamaguje ta ce. "Tabbas da kuwa mun shimfiɗa mulkin da wani mai numfashi bai taɓa aiwatar da makamancinsa ba. Sai na shayar da Fulani babba ruwa mamaki domin sai na gasa mata tsakuwa a tsakiyar tafin hannunta." Bamaguje ya kafe ta da idanu yana faɗin, "Haba Umaima me kike ci na baka ma zuba, ai duk gaggawar ungozoma ta bari a haihu. Kuma duk gaggawar asara ta jira yi samu. Kamar yadda na gaya miki jininki zai kasance sarkin ƙasar Zazzau ne kaɗai bisa taimakon jini da ruhin wata hallita, ban san ya zan fasalta miki ita ba amma ta kasance mai ɗauke da rikitattun al'amura. Wanzuwarta a doron ƙasa sanadi ne, kuma ta kasance abar farautar al'umma da dama ciki kuwa har da mahaifina wanda ya shafe shekara da shekaru cikin halwar tsafinsa yana dakon zuwanta. Ban gama tabbatar da abin da nake zargi ba amma tabbas na ga walƙiyarta a cikin masarautar Sarki Abdul'aziz, wannan zai sauƙaƙa miki cim ma muradinki..." Da sauri Fulani ta katse shi cikin ƙagauta. "Wacce irin hallita ce? Me ne ne alaƙarta da masarautar Zazzauna? Shin dole sai da taimakonta ne abin da zan haifa zai kasance Sarkin masarautar Zazzau?" "Akwai ɓoyayyun al'amura game da ita, a sura ta zahiri ta kasance bil'adam kamar kowa. A baɗini tana da ɗauke da al'amura masu hautsina kwanya. Halwar tsafina bai fayya ce mini komai ba, sai dai ina mai shawartar ki da ki tabbatar kin yi nasara a kanta. Ina daga nan zan ci gaba da dafa miki domin ni ba iya boka kaɗai nake a wurinki ba, akwai wata ɓoyayyar alaƙa mai ƙarfi a tsakaninmu. Ba don na yi wa mahaifiyarki alƙawarin binne wannan sirrin ba da tuni na fayyace miki shi, amma ko ga iya haka na dakata na yi miki jurwaye mai kamar wanka don haka dabara ta rage wa mai shiga rijiya." Da yake hankalin Fulani ba ya jikinta ya sa ba ta fahimci inda kalaman Bamaguje suka dosa ba, tana shirin yi masa magana ta ji ya ci gaba da ce wa. "Tana da matuƙar hatsarin gaske don haka dole ki yi takatsantsan, wannan shawarar ina baki ita ne ba a matsayina na bokanki ba ina ba ki ita ne a matsayina na makusancinki. Wani abin da ɓatattu da dama irina ba su sani ba wannan hallitar na da wata tawaya ɗaya wacce da a ce an santa da tuni an yi galaba a kanta..." "Wacce irin tawaya gare ta?" Bamaguje ya wara hannuwansa haɗe da faɗin, "Ni kaina ban santa ba, sai dai allon tsafina ne ya alamta mini haka. Ammma zan baki wannan sirrintaccen littafin mai ɗauke da labarin abin da ya taɓa faruwa a masarautar Daura, wannan al'amarin ya faru a shekara ɗari da hamsin baya da suka shuɗe. Ƙa'idar littafin ba a karatunsa kowacce rana sai ranar Lahadi ko Laraba daga bayan la'asar zuwa sallar isha'i. Ki bi shi a sannu ki karanta zai taimaka miki matuƙa. Umaima!" Boka Bamaguje ya ambaci sunanta cikin wani irin yanayi. Fulani Umaima ta dube shi cike da ƙwarin gwiwa babu alamar karaya ko tsoro a tattare da ita. "Jarumta da dakakkiyar zuciyarki na matuƙar birge ni, tabbas kin cancanci shiga sahun mace mai kamar maza. Na yi imani da abin bautar da nake bauta tare da siddabarun da na gada a wurin iyayena da kakanni sai na ci gaba da dafa miki kin kasance mai nasara har ƙarshen rayuwarki." Fulani Umaima ta saki murmushi. "Ai dama duka ɗaya baya kada sadaukan jarumai, don haka na dulmiya kogin azaba na yayyafa wa ruhi da gangar jikina don kada wani hatsari ko firgici ya razana ƙwarin gwiwata." Umaima ta ɗora tafin hannunta a saman tukunyar tsafinsa ta runtse idanunta ta ci gaba da cewa, "Na yi imani da kai Bamaguje kuma na yi maka alƙawari wallahi sai jinina ya mulki ƙasa da masarautar Zazzau bakiɗaya." Bamaguje ya jinjina kai sannan ya ɗauko wani irin littafi mai ɗauke da bangon ƙarfe wanda yake ɗauke da launin ruwan zaiba. A tafin hannunta ya ɗora mata, wani irin zuuuu ta ji a tafin hannunta kafin ta ankara ta ji wani sauti na furta. "Hidayaaaa!" A razane ta buɗe idonta suna haɗa ido Bamaguje ya jinjina mata kai, "Kamar yadda majiyar sautinki ta jiye miki haka ne wato Hidaya ba zan ce miko komai ba, domin amsar tambayar ki na cikin kundin littafin." Fulani ta rungume littafin ƙam kamar wani zai ƙwace shi, sannan ta waiga wurin da Maimuna ke zaune kamar gunki ta gagara motsa koda yatsanta ne. "Bamaguje ka aiwatar mini da duk abin da ka yi niyya a kan waccan la'ananniyar." Bamaguje na jin haka ya bushe da dariya, Maimuna ta fara mutsu-mutsu tana son tashi ta gudu amma ta gagar tashi. Yana daga wurin da yake zaune ya turmutsa hannunsa a cikin wani kabari, ya ɗauko ƙoƙon kan mamacin da ke ciki ya fara takawa har ya isa wurin da take zaune. Ɗora mata kan ya yi a kanta na ɗan lokaci take jikinta ya fara karkarwa, ya jima a haka sannan ya saka wata ƙaramar tsafatacciyar wuƙa ya yanki tsokar jikinta. Wajen kabarin ya koma ya tura fatarta a cikin kabarin sannan ya furta. "Wannan da kike ganinta a zahiri ne take tamkar rayayya amma ba ta da amfanin komai kuma za ta zame miki tamkar raƙumi da akala. Yanzu ki tafi da ita zuwa turakar Sarki Abdul'aziz, kuma a wannan ranar nake son ki sa Sarki Abdul'aziz ya kusanceta ta gaba da baya." A firgice Fulani Umaima ta ɗago ta kalle shi cikin tashin hankali. _Ummou Aslam Bint Adam_ 🌚 07062062624. *SHU'UMAR MASARAUTA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga ɗaukan tsattsauran mataki don haka a kiyaye. *Masarautar Zazzau ta sauya zuwa Masarautar Huddam.* SHAFI NA HUƊU Wani irin kallo Fulani Umaima ta watsa wa Bamaguje, shi ma ya yi ƙuri yana kallon ta da daƙwa-daƙwan idanunsa jawur kamar sabon barkono, ta katse shirun da ce wa. "Ka na nufin Baiwata Maimuna ce Takawa zai kusance ta? A saboda wanne dalili kuma ba ka ganin tamkar na miƙa kai a kan hanyar da asirina zai tonu?" Bamaguje ya girgiza mata kai. "Matuƙar ina numfashi kullin za ki kasance lulluɓe cikin bargon rufin asirin da babu wani mai numfashi ya isa ya yaye miki shi, dalilin da ya sa na ce ki aiwatar da wannan aikin matuƙar Sarki Abdul'aziz ya kusanci Maimuna ta gaba da baya za ki sha gaban kowa. Wane na mai faɗa a ji a cikin ƙasar Huddam?" "Sarki Abdul-aziz." Umaima ta amsa masa. "Ki saurare ni da kyau. Ba akwai wata baƙar rijiya mai baƙin murfi a turakar Mai martaba ba wacce suke kallon juna ita da tsohon shuri mai tsohon tarihi?" Umaima ta gyaɗa masa kai. "Mai martaba na gama mu'amala da ita ki tabbatar kin ɗebi najasar jikinsu sai ki shafa ta akan saman murfin take murfin zai buɗe, ki zura Maimuna cikin rijiya ki koma gefe su zuba ido zai koma ya rufe kamar yadda yake da farko. Maruƙar kika aiwatar da komai yadda ya kamata za ki sha gaban duk wata hallita da ke cikin ƙasar Huddam, kwarjini da tsoronki zai mamaye zuƙatansu ta yadda kina faɗar maganar za a aiwatar miki. Sai dai akwai sharaɗi duk ranar da aka fito da Maimuna daga cikin wannan rijiyar wannan asirin ya karye, amma kuma abu ne da kamar wuya gurguwa da auren nesa domin yanzu haka rabon da a buɗe rijiyar yau kimanin shekara ɗari da hamsin kenan." Umaima ta sauke ajiyar zuciya. " Duk wannan ban ɗauke shi abu mai wahala ba, shin ya za a yi na wuce da Maimuna har turakar Takawa ba tare da wani ya gan ni ba, kuma na sa shi ya yi mu'amala da ita?" "Umaima a kullin kin fi son a yi miki ciki a yi miki goyo, za ki saka hannu ki ƙwaƙwalo ƙwayar idonta ki jefa a cikin wancen sihirtaccan ruwan, yadda za ta makance ta daina gani haka za ki ci karenki babu babbaka ba tare da wani ya kawo miki cikas ba. Kuma daga wannan lokacin hatta uwar da ta kawo ta duniya ba za ta sake tambayarta ba, yadda matacce ke mantawa da rayuwar baya haka duk wanda ya santa zai manta da shafinta." Umaima ta yi masa jinjina da hannu. "Na gode sosai Bamaguje faɗi kowanne irin tukwici kake buƙata." Bamaguje ya saki murmushi, "Ki je Umaima zan fanshi aikina a cikin masarautarku." Umaima na gama sauraronsa ta miƙe ta ƙarasa gaban Maimuna da ke zaune kamar butum-butumi, ƙaramar wuƙa ta saka ta ƙwaƙwalo idanunta ta watsa cikin wani koren ruwa kamar yadda Bamaguje ya faɗa mata. Ta koma gabansa ta yi masa sallama da faɗin duk abin da ake ciki za ta sake ziyartarsa. Ta rungume littafin a jikinta hannunta ɗaya riƙe da Maimuna na biye da ita kamar raƙumi da akala. Duk wani abu da take gudanarwa na siddabaru sai da ta gudanar babu jimawa sai ga su a cikin ɗakinta a tsaye. Kai tsaye uwar ɗakinta ta wuce da Maimanuna ta buɗe wani akwatinta na ƙarfe da take ajiyar abubuwanta na sirri ta ajiye littafin, sannan ta koma falo ta zauna tana ta zuba murmushi don gani take ƙiris ya rage haƙonta ya kai ga cim ma ruwa. Bayan fitar Fulani Umaima daga sashen Fulani babba, Jakadiya da kanta ta ɗan tattara wurin. Ta leƙa madafa tana tambayar su Baraka ko ruwan zafin ya tafasa, a daidai lokacin ta same su sun fara kwashe ruwan. Bayan an zuba aka kai banɗakin Fulani babba, shi kuma jaririn Jakadiya ta zauna ta sulle shi tas. Sai da gari ya waye tangararan sanna Jakadiya ta ɗauki Yarima ta wuce da shi turakar Mai martaba. Farinciki fal fuskarsa ya karɓi jaririn yana jin son shi a zuciyarsa don ya jima yana mafarkin samu ɗa namiji. Huɗuba ya yi masa da suna Abubakar sannan ya ba wa Jakadiya ta mayar da shi, Jakadiya na mayar da shi Fulani ta rungume jaririnta suka kwanta bacci. Jakadiya da kanta ta sanar da Baiwa Zainaba a kan duk wanda ya zo mata barka a ce masa tana hutawa. Sai a lokacin ita ma Jakadiya ta wuce can sashensu na Bayi ta samu ta yada haƙarƙarinta don ta yi ramuwar baccin daren da ba ta yi ba. Fulani Umaima tun da ta dawo ta kasa zaune ta kasa tsaye don burinta bai wuce ta ga ta aiwatar da abin da Bamaguje ya umarce ta ba. A yadda ta jingine Baiwa Maimuna a haka ta same ta a bayan ƙofa, bayan ta idar da sallar asuba ta riƙo hannun Maimuna tana faɗin, "Wuce mu je sashen Mai martaba." Babu musu Maimuna ta fara tafiya tana biye da Fulani. Duk da ta aminta ɗari bisa ɗari da hatsabibancin Bamaguje, a lokacin da ta fita harabar da Bayi suke kai wa da kawowa sai da gabanta ya faɗi, jikinta ya ɗauki rawa tana tsoron kada su ankara da Maimuna wacce take tafe da ƙwaƙwulallun idanuwa asirinta ya tonu. Amma ga mamakinta duk wurin da ta gifta sai dai Bayi su riƙa zubewa ƙasa suna kwasar gaisuwa. Cike da izza, ɗagawa, faɗin rai da alfari Fulani Umaima ta ci gaba da taku ɗaiɗai tana kallonsu a banzace ba tare da ta amsa ba ta wuce. Ba su yi mamaki ba domin ba wannan ne karo na farko da ta saba yi musu haka, wulaƙanci da tozarta na ƙasa da ita kamar a jininta yake don haka kowannensu ya sake shiga taitayinsa. Lokacin da ta isa sashen Sarki Abdul-aziz shiru ta ji wanda hakan ya alamta mata baya nan, can gefen gadon sa ta zaunar da Maimuna sannan ta fara jiyo motsi daga jikin windonsa. Tana leƙawa ta hango Takawa a cikin lambun shaƙatawarsa zaune a kujera a gefensa ɗawisu ne da ƙananan tsuntsaye suke ta kaiwa da kawowa. Har ta nufi ƙofar da za ta sada ta da lambun ta tuna ba ta ɗauko sihirtaccen turarenta, da sauri ta fice don kar Sarki Abdul'aziz ya dawo ba tare da ta kammala shirinta ba. Da fitarta ba a ɗauki minti biyar ba Sarki Abdul'aziz ya taso kai tsaye ya nufo cikin turakarsa, gabansa ya ji ya yanke ya faɗi ƙwarin gwiwar da ke tattare da shi ta tarwatse. A razane yake bin kan gadonsa da kallo, sakamakon ƙwaɗayin idanunsa da suka hango masa abin da ba yi tsammani ba. Fulani Umaima na zuwa ta wuce ta zaro akwatinta da ke ƙarƙashin gado, ta buɗe ta da niyyar ɗaukon turaren amma zuciyarta ta fara kwaɗaita mata son sanin abin da yake ƙunshe a cikin littafin da Bamaguje ya damƙa mata. Ta sake tuna matuƙar ta rasa karatunsa a wannan ranar sai dai ta bari zuwa wani makon mai zuwa. Ɗaukan littafin ta yi ta koma gefen gado ta zauna, za ta sa hannu ta buɗe ta tashi da sauri ta je ta saka kuba a ƙofarta ta rufe sannan ta sake komawa ta buɗe shafin farko daga cikin littafin, ƙwayar idonta ta sauka a kan jimlar farko da aka yi rubutunta da ajami. BAN SAN KAINA BA Da mamaki ta sake furtawa da bakinta, "Ban san kaina ba! Me hakan yake nufi?" Duk harsashen kwanyarta ta gagara lalubo mata amsar tambayarta don haka ta sake mayar da kanta ta ci gaba da karatun. Ban san mizanin tubalin ginin da ya dace na jingine rayuwata ba, balle na san kaina da abin da rayuwata ta ƙunsa, abu ɗaya na sani ban san kaina ba. Ban san wace ce ni ba domin kuwa wata hallita ce ke sarrafa zuciya da ruhin gangar jikina. Ban san asalina ba ballantana na binciki dangina, hasali ma kusan duk wani Bawa ko Baiwa da za ka gani a cikin masararutar Kabbab kusan kowa akwai tushe da asalin yankin da ya fito, nawa asalin ya yi rauni dalilin da ya sa ko a cikin Bayi na kasance ƙasƙantacciyar baiwa. Wacce take fuskantar tsangwama, kyara da duk wani nau'in cin zarafi saboda babu mutum ɗaya da zan kalla da sunan dangina. Har ya zame mana jiki a kowacce rana idan rana ta take muna karkasuwa ɓangare-ɓangare domin gudanar da ayyuka daban-daban. Ni da su Dije muna ɓangaren bangon yamma muna sirfen geron da za a yi wa su Fulani fura da shi, a lokacin rana ta take sosai daga bayana na ji an saka hannu an dafa kafaɗata wacce na ke kai taɓarya ina yin surfe da ita. A hankali na waiga ƙwayar idona ta sauka a kansa, cike da fargaba da sake waro idanuna haɗe da tattaɓa gefen fuskarsa don tabbatar da ƙwayar idona ba yaudarata take ba. Tun ban fi shekara biyar a duniya ba nake mafarkinsa ba dare babu rana, domin a duk lokacin da zan yada haƙarƙarina gangar jikina ta samu hutu bacci ya yi awon gaba da ni sai na yi mafarki da wannan hallitar. "Ki taya ni murna da farinciki domin na samu 'yancina, na zama kamar kowa mai ɗauke da rayuwar gashin kai. Na yi miki alƙawarin sai na karɓo miki karagarki, a kullin Kaka na sake jadadda mini mu tabbatar da mun ba wa alƙawari muhimmanci kuma mun cika shi, wannan zai dawo da ƙima da martabar ahalinmu, wacce zuri'armu ta tarwatse silar cin amanar da aka yi mana." Kalamansa suka mamaye masarrafar jina, mamakina ya ninku dalilin ganin ƙwalla na zuba daga ƙwayar idonsa. "Ke Hidaya kar ki raina wa kanki hankali, kina nufin mu za mu ci gaba da surfen kina can kina kalle-kalle banza da wofi? Wallahi kika bari muka surfe na cikin turmin nan sai dai ki surfe wannan kwano ukun ke kaɗai." Kalaman Safare suka katse ni, da sauri na waiga wurinsu kowaccensu ta sakar mini harara kamar idanunsu zai faɗo. A zuciyata na furta. "Ko dai su Safare ba sa ganin wannan saurayin?" Daga bayana na ji ya sake taɓo ni. "Ba za su taɓa ganina ba, saboda wasu muhimman abubuwa. Ke ma akwai dalilin da ya sa kike rayuwa a cikin Masarautar nan har kike mu'amala da su. Ki ci gaba da haƙuri kin san idan aski ya zo gaban goshi ya fi zafi." Yana gama furta mini waɗannan kalaman na neme shi na rasa. Wata irin azaba ta riyarci ƙafata sakamakon wurgo mini taɓarya da su Safare suka yi, na sunkuya cike da azaba ina matsa ƙafata. "Ga shi nan ki yi ki surfa ragowar, kuma kin fi kowa sanin halin Uwar tuwo matuƙar aka gama surfen aka bar ki a baya za ki yaba wa aya zaƙinta." Idanuwana na kai kan ƙwaryar da ke cike da gero har kusan kwano uku, tausayin irin wuyar sirfen da zan sha ya mamaye ni. Dole ƙanwar na ƙi, na sunkuya na ɗauko taɓarya kafin na ɗago na ji saukar bulala a tsakiyar bayana, azaba ta sa na wurgar da taɓaryar ina ihu haɗe da soshe-soshe. Ragowar mutanen da ke wurin babu wanda ya motsa ballentana na saka ran wani daga cikinsu zai kawo mini ɗauki, sai da Uwar tuwo ta gaji da dukana don kanta sannan ta nuna ni da murtukekiyar dorina. "Ki yi gaggawar ƙarasa surfen gabanki idan ba haka ba wallahi sai na sa Balele ya kai ki ɗakin duhu, shegiyar yarinya da idanu kamar na ƙwanƙwamai." Tun ba ta ƙarasa zagina ba na suri taɓaryar da a tsaye ta kusan tsayina, jiki na karkarwa na fara daka cike da tashin hankali. Ganin haka ya sa Uwar tuwo ta yi gaba tana buga wa sauran Bayin da ke tsaitsaye tsawa, da tafiyarta babu jimawa waɗansu zaratan samari biyu suka kewaye ni. "Shugaba wannan ba aikinki ba ne." Mamaki ya lulluɓe ni domin ko a mafarki ban taɓa cin karo da su ba, haka kuma suturun jikinsu bai yi kama da kayanmu na bayi ba. Na sake mamakin kalamansu da suke kirana da shugaba. Tsaye na yi ina bin bayan Uwar tuwo da kallo samakon har lokacin ina hango ta sai da ta ɗan yi nisa da ni, takaicin dukan da ta yi mini ya mamaye ni na fara ayyana da ina da hali sai na karɓi doriyar hannunta na zane ta ita ma ta ji irin abin da muke ji. Ihun da na ji Uwar tuwo na yi ne ya dawo da ni hayyacina, na kai ƙwayar idona wurin cikin mamaki nake bin ta da kallo. Kamar yadda na ayyana haka Uwar tuwo ke tsalle tana ihu, hatta ni da nake nesa da ita haka na riƙa jiyo sautin saukar dukan da ake yi mata.Ta jima cikin wannan halin sannan ta faɗa gefe ɗaya tana sauke ajiyar zuciya, kamar wacce aka ce na waiga ina juyawa wurin turmin na yi tozali da abin da ya daskarar da ni. Gabaɗaya geron da ke wurin an surfe shi an dake mini tas, tsoro ya mamaye ni da ganin wannan lamarin. Duk da ba sabon abu bane a wurina na ji kalamai daga cikin zuciya, amma a wannan karon na razana, "Kada ki tsoro ta Shugaba domin firgici ba hali ko ɗabi'ar ahalinku ba ne." Jin haka ya ƙara mini ƙwarin gwiwa na ɗauki ƙatuwar ƙwaryar na ɗora ta a kaina da ƙyar, kafin na ƙarasa wurin da Uwar tuwo ke kwance tuni Bayi suka taimaka mata aka kai ta can ɓangarenmu na Bayi. Kallo ɗaya za ka yi wa Bayin da ke wurin ka fahimci kowa ya sha jinin jikinsa, don babu hayani tsit wurin ya yi kamar an yi mutuwa. Kamar kullin idan kowannenmu ya dawo daga sashen da yake yi wa hidima, mukan taru a sashenmu na Bayi. Zaune muke gabaɗaya a tsakar gida, wasu daga cikinmu na zaune kusa da yayyansu suna wasa. Waɗanda suke da ƙanƙarta shekaru kamar nawa da ba su wuce sha uku ba suna kwance a jikin iyayensu, idanuwana suka ciko da ƙwalla sakamakon ganin ni kaɗai ce wari ɗaya ba ni da makusanci. Ko da ba ni da iyaye ya kamata wasu su tausaya mini su ƙaunace ni kamar yadda na ga wasu Bayin da aka samo marasa iyaye ake kula da su, me ya sa na kasance mai baƙin jini kowa ba ya ƙaunata?" Ba zato daga gefen kunnuwana na ji an furta mini. "Ke kike da kowa Hidaya! Kada ki karaya domin lokacin na nan da za ki tabbatar da haka." Abin ka da mai shirin kuka an jefe shi da kashi awaki nan take hawaye ya fara kai-kawo a ƙwayar idona. Jiki a sanyaye na miƙa zuwa gaban Jakadiya na tsugunna, da mamaki gabaɗaya suka juyo suna kallona. Ban damu da irin ƙalubalen da zan fuskanta ba, babban burina bai wuce ni ma na san wace ce ba. "Lafiya kika zo kika saka ni a gaba kamar tsohuwar mayya?" Gabana na dakan lugude na tattaro kalaman bakina da na guntso na fesa mata. "Don Allah Jakadiya su waye iyayena?" Kamar haɗin baki haka na ji sun tuntsire da dariya, sai da suka yi mai isar su sannan Jakadiya ta nuna wurin da Uwar Bayi ke zaune. "Akwai tarin bayanai dangane da samuwarki, ki tafi wurin Uwar Bayi za ta warware miki zare da abawa." Cike da ƙwarin gwiwa na miƙe cikin sassarfa na isa gaban Uwar Bayi, na baje tagwayen kunnuwana ina sauraron makoma da tushena. Ajiyar zuciya Fulani Umaima ta sauke ta kai hannu ta rufe shafin littafin ba don ta gaji da karatun wannan hargitsattsan labarin mai cike da rikitar da kwanyar mai karatu ba. Mayar da littafin ta yi cikin akwatinta sannan ta ɗauko turaren da take amfani da shi a duk lokacin da za su yi wata mu'amala da Mai martaba. A cikinta ta soke shi sannan ta rufe ɗakinta ta fice kai tsaye ta wuce sashen sarki Abdul'aziz, haka kawai ta ji gabanta na faɗuwa ba tare da ta san dalili. Babban tashin hankalinta bai wuce kada laƙanin jikin Takawa ya wargaza mata shiryayyan shirin ta a kan Maimuna ba. _Ummou Aslam Bint Adam_ 🌚 07062062624. *SHU'UMAR MASARAUTA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga ɗaukan tsattsauran mataki don haka a kiyaye. SHAFI NA BIYAR Cikin mugun yanayin ta kafe shi da ƙwalaƙwalan idanuwanta masu razana duk wanda ya yi tozali da ita, a hankali Sarki Abdul'aziz ya fara ja da baya jikinsa na karkarwa. Bai yi tsammani ba ya ji bayansa ya bugu da bangon ɗakin, cikin tsinkewar zuciya yake sauke ajiyar zuwa. Da wata irin sanɗa ta taso daga kan gadon tana durfafo wurin da yake tsaye, ganin tana gabda cin masa ya sa ya fice da sauri daga cikin ɗakin ya ƙarasa wurin dogaran da ke tsaron sashensa. Yanayinsa kaɗai ne ya tabbatar musu da tabbas Takawa yana cikin damuwa, tun bai ƙarasa wurinsu ba suka zube cikin girmamawa. "Allah ya taimake ka ya ƙara lafiya da nisan kwana, ɗawisu sarkin ado mai taƙama da ikon Allah..." "Ya aka yi kuka bar waccan hallitar ta shiga har cikin turakata?" Mai martaba ya katse su fuska a tamke babu ɗigon fara'a. "Tuba muke ranka shi daɗe, Allah ya huci zuciyar amale a gafarce mu wannan ne na farko na ƙarshe." A daidai lokacin Jakadiya ta ƙarasa ita da Baiwa Saro hannunsu ɗauke da kayan lambun da ake kai wa Sarki Abdul'aziz kamar wannan lokacin. Dogaran ta gani sun nufi turakar Takawa kafin su ƙarasa su ka ga wata baƙar mage ta fito daga cikin turakar idanuwanta jawur kamar gauta tana bin mutanen wurin da wani irin kallo. A zabure Jakadiya ta furta. "Ka gafarce ni uban gidana ka yi mini afuwa, amma ba ni da masaniya game da sakacin Dogaran ƙofa da har suka bar kyanwar nan ta shiga cikin turakarka." Jakadiya ta yi maganar jikinta na karkarwa don ta san a duniya babu abin da Takawa ya fi tsoro sama da mage, wannan ɓoyayyan sirri ne da ba kowa ne ya sani ba saboda gudun kada magauta su fahimci lagonsa. Ita ma Jakadiya abin da ya sa ta sani tun wani lokacin da ta taɓa shiga sashen Mai babban ɗaki (Mahaifiyar Takawa.) wata mage ta shiga har suma ya yi a wurin, kuma ko da ta ga haka sai da Mai babban ɗaki ta tsawatar mata a kan wannan sirrin. "A kiyaye gaba, ba na buƙatar sake ganin kowacce hallita a sashena." Gabaɗaya suka amsa masa cikin girmamawa. Jakadiya da kanta ta shiga ta jera kayan lambun kamar kullin sannan suka fice bayan ta tambayi Takawa ko akwai wani abin da yake da buƙata, ya ba ta amsa fuska babu walwala. Har bayan wani lokaci Sarki Abdul'aziz bai saki jikinsa ba, ganin bai sake jin motsin komai ba ya sa ya ɗan saki jikinsa. Cike da ƙwarin gwiwa Fulani Umaima ta ƙarasa cikin turakar Mai martaba, ganinsa zaune a gefen gado kusa da baiwa Maimuna ya sa ta zaro idanu cikin fargaba har sai da ya fahimci ruɗewar da take ciki. "Lafiyarki Umaima?" Cikin kissa ta daidaita nutsuwarta ta ce, "Dama na yi mamaki ne ganinka shiru, kar dai ka jima kana jirana." Murmushi ya sakar mata haɗe da girgiza kai. Ta ƙarasa wurinsa asirtaccan ƙamshinta ya ratse hancinsa, ya lumshe ido cike da jin daɗin ƙamshinta. "Ki tabbata kin sa shi ya shiga bayan gida kafin ki saka wa Maimuna turare a gabanta." Kalaman Boka Bamaguje ya dawo mata raɗau a cikin kunnuwanta. Miƙe wa ta yi ta furta. "Sarkina bari na haɗa mana ruwa mu ɗan watsa ko?" Ba ta jira cewarsa ba ta nufi banɗaki ta haɗa komai da kanta sannan ta zuba turaren da Bamaguje ya bata, bayan dawowarta ta taimaka masa ya rage kayan jikinsa sannan suka wuce banɗaki. Da kanta ta ɗebi ruwan ta watsa masa cikin sigar tsokana, sai kuma ta yi farat ta furta. "Na yi mantuwa." Kallon da ya yi mata ne ya alamta mata yana buƙatar ƙarin bayani daga gare ta. "Ina zuwa." Kawai ta furta ta fice a gaggauce. Sai da ta tabbatar da ta rufe ƙofar ta baya sannan ta koma turakarsa cikin sauri ta ɗaga doguwar rigar Maimuna ta kwara mata turaren a ƙasanta sannan ta shafa mata a fuskarta, ita ma ta murtsuke jikinta da shi ta rage kayan jikinta ta sake komawa cikin banɗakin. Tana shiga ƙamshinta ya daki hancinsa, take ya ji wani irin yanayi ya tsarga masa. Buƙatar ya kusance ta ta yunƙuro masa, ganin saƙwannin da yake aika mata ya tabbatar mata da haƙonta zai cim ma ruwa, don haka ta fara neman shawarar da za ta yanke wa kanta. A hankali ta yakice shi tana faɗin, "Sarkina a banɗaki muke mu ƙarasa turaka." Bai musa mata ba, ta ƙarasa sheƙa musu ragowar ruwan sannan suka fito hannunta na riƙe da shi, idanuwansa a rufe suka ƙarasa don haka ko da ta zaunar da shi a gefen gado ta ga ya rarumo Baiwa Maimuna da ke zaune kamar gawa. Fulani Umaima ta koma gefe ta zuba masa ido zuciyarta ƙal, tana nan tsaye Takawa ya gama mu'amalarsa da Maimuna ya koma gefe ɗaya sai gani ta yi numfashinsa ya ɗauke. Da sauri ta ƙarasa ta ɗebi najasar jikinsu ta isa bakin rijiyar da tun da take shiga cikin turakar ba ta taɓa taka wurin ba, wata irin kuɗa ta fara ji a cikin kunnuwanta ga wata 'yar juwa-juwa da take ji sama-sama. A haka ta samu ta zuba najasar a kan rijiyar take murfinta ya buɗe, wata baƙar ƙura ta turnuƙe ta. Sai daga baya komai ya washe, ganin haka ya sa Fulani Umaima ta koma ta janyo hannun Baiwa Maimuna sai da suka je bakin rijiyar Fulani Umaima ta furta. "Maza ki shiga rijiyar nan da ƙafar hagu." Ba musu Maimuna ta ɗaga ƙafarta ta zura cikin rijiyar ta zauna a kan wani mulmulallan baƙin dutse. Kamar yadda Bamaguje ya gaya mata Maimuna na gama shiga murfin ya taso da kansa ya rufe ruf. Ta koma can gefen Sarki Abdul'aziz ta kwanta tamkar da ita Takawa ya gama mu'amala. Bayan ɗan wani lokaci Mai martaba ya fara motsawa, jin haka ya sa Fulani Umaima ta fara sauke ajiyar zuciyata tana rarumo shi cikin kissa da kisisina. Wani irin nauyi dum! Kansa yake yi masa don haka ya gagara tunano abin da ya faru a baya, ganin yanayin da suke ciki ya sa ya sakar mata ajiyar zuciya ya yunƙura suka wuce banɗaki don tsaface jikinsu. Irin rawar jikin da yake yi a kanta ne ya sake tabbata mata da tabbas alƙaluman tsafin Bamaguje ba su zube a ƙasa banza ba, ta ci gaba da narke masa tana cin karenta babu babbaka. Daren ranar a sashen Sarki Abdul'aziz ta ƙarashe shi har zuwa wayewar gari. Cikin abin da bai fi wuni biyu ba, maganar haihuwar Fulani ta yaɗu cikin da wajen Masarautar Huddam, musamman da ya kasance an san Takawa ba shi da ɗa namiji sai a wannan lokacin. Manyan mutane da masu kuɗi haka suka dinga zuwa suna bada gaisuwa haɗe da yi masa barka da samun ƙaruwa, mafi yawa daga cikinsu har da sha tara ta arziƙi suke kawowa. Duk da Fulani Umaima ta san jaririn a nakashe yake hakan bai hana ta jin ƙyashi, baƙin ciki da ƙunci a kan kyaututtukan da Fulani Babba take samu ba. A lokacin sai ta tsiri kwanciya da tsirfar ciye-ciye wani lokacin har amai take ƙaƙalowa a turakar Mai martaba, duk da cikin jikinta babu abin da yake saka ta. Ganin haka ya ɗaga hankalin Takawa har ya aikata sashen magunguna aka kira masa Ungozoma da jikar Baushe don su duba ta su ba ta magani. Tashin farko aka sanar wa da Sarki cikin da ke jikin Fulani Umaima, farin ciki kamar zai zuba ruwa a ƙasa ya sha. Ita kuwa Fulani Umaima ko kaɗan ba ta nuna wa Takawa ta san da cikin jikinta ba, nan ta shiga gwalangwaso da feleƙe wani lokaci hatta ƙamshin Turakarsa ce wa take ba ta so. Cikin wannan yanayin aka ɗebi kwanaki mai jego tana ɓangarenta tana jego ita kuma Fulani Umaima tana rainon cikinta, gabaɗaya gidan sarautar ya zagaye da ƙananan maganganu. Jin labarin cikin Fulani Umaima da Fulani Babba ta yi ba ƙaramin faranta ranta ya yi ba, kuma rashin ganinta kwana biyu a ɓangarenta ko kaɗan bai dame ta ba don ta san yadda laulayin ciki yake ba shi da daɗi. A ɓangare ɗaya Fulani Babba na cikin matsanancin tashin hankali sakamakon yadda fitsarin da yake zuba daga jikinta yake sake ta'azzara, tun tana ɓoyewa har ya zamana sai da Baiwa Zainaba ta fahimci halin da take ciki, ga shi abin kullin gaba yake yi da ta kwanta ko bacci minti biyar ba ta yi tana farkawa sai dai ta ji ta sharkaf da fitsari, ga kuma jinin biƙi duk shimfiɗarta ta haɗu ta dagule. Ana gobe suna da asuba bayan ta tashi ta sake ganin wurin ya yi sharkaf da wani irin zarnin da ke tashi har ya wuce misali. A wannan lokacin take zuciyarta ta karye ganin lalurar tata a kullin gaba take yi ba baya ba, a daidai lokacin yayarta da suka zo daga Masarautar Bassar ta shiga ɗakin, ganin ta a zaune ya sa ta ɗan yamutsa fuska. "Fatima wai mene ne yake wari ne?" Da yake mai shirin kuka ne aka jefe shi da kashi awaki take Fulani Babba ta fashe da matsanancin kuka, da mamaki Halima ta furta, "Fatima me yake faruwa ne?" Sai da ta yi mai isarta sannan ta miƙe tana nuna wa yayarta ta ce. "Ki duba ki gani Yaya Halima wai ni ce yau nake malala fitsarin kwance. Ni dai na fi zargin tun ranar na haihu na haɗu da wannan iftila'in, duk yadda zan yi takatsantsan ina runtse idona duk gajarta bacci sai dai na tsinci kaina a cikin fitsari." Jakadiya da ta zuro kanta da niyyar sanar da Fulani Babba ruwan wankanta ya yi zafi ta yi fakare tana sauraronsu. Yaya Halima cike da damuwa ta jinjina kai. "Kin sanar da Mai martaba?" Girgiza mata kai kawai ta yi don ba ta son ta buɗe baki har ta iya sanar da danginta zaman doya da manjar da ke tsakaninta da Takawa. Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta furta, "Ya zama wajibi na sanar da Yakumbo a nemar miki magani, domin wannan fitsarin ba na lafiya ba ne. Ni fa dama zuciyata da hankalina ba su taɓa aminta da wannan kishiyar taki ba..." Da sauri Fulani Babba ta katse ta. "Yaya kada ki zargi Umaima domin ban taɓa zarginta a kan wani mugun abu ba, zamana da ita babu wata matsala ni dai a yi mini magani amma Allah ya sani babu sa hannun Umaima a lalurata." Inuwar da Yaya Halima ta hango a wurin labule ya sa ta furta. "Waye a wurin nan?" Jikina na rawa Jakadiya ta faɗa ɗakin tana faɗin, "Allah ya taimaki Fulanin Takawa, uwar yariman gobe da yardar Allah. Dama ruwan wanka na kwashe na zo sanar da uwar gijiyata." Daga cikin ɗakin Fulani Babba ta furta. "Saƙonki ya isa Jakadiya." "Godiya nake zinariya fara mai farar aniya bangon talakawa da marasa gata, Allah ya raya mana yarima ya gaji karagar da babu kamarta a faɗin nahiyar nan." Yaya Halima ta amsa tana bin Jakadiya ta kallon tuhuma. Sai da ta ga Jakadiya ta fita sannan ta furta. "Da alama wannan farar zuciya taki na iya kai wankin hula ya kai ki dare, jikina yana ba ni idon masarautar nan yana kanki." "Yaya Halima shi zato zunubi ne! Don haka..." Da sauri ta katse ta. "Dama ki ajiye zurfin cikinki kin amayar mini da abin da yake cikinki domin abokin kuka ba a ɓoye masa mutuwa." Idanun Fulani Babba ya ciko da ƙwalla don ita kaɗai ta san zafin da zuciyarta take yi mata, amma sanin Yaya Halima na daga cikin irin marasa haƙuri ya sa ta danne damuwarta ta furta. "Babu wani abu da yake damuna Yaya Halima, idan ma akwai na fauwala wa Allah saboda saniyar da ba ta da jela Ubangiji ne ke kore mata ƙuda." Yaya Halima ta taɓe baki ta fice ba tare da tanka mata ba, Fulani Babba da ta yi shirin wanka tana kai idanunta kan jaririnta. A kullin ta kalle shi zuciyarta na wasu-wasi a kan ingancin lafiyarsa, sai dai babu yadda za ta yi tun da ba fada gare ta a wurin Takawa ba balle ta yi masa bayanin halin da jaririn yake ciki. Kamar za ta tashi sama haka Jakadiya ta yi sashen Fulani Umaima a lokacin Fulani na shaƙar bacci ko sallar asuba ba ta yi ba duk da gari ya waye garau, da farko Bayin da ke kula da ita sun sanar da Jakadiya Fulani na bacci. Amma da yake bakinta cike yake fal da tsegumi a dole haka ta shiga tana ta rangaɗa sallama. Kamar a mafarki Fulani Umaima ta ji sallamar Jakadiya wanda hakan ne ya alamta mata akwai wani muhimmin abin da yake tafe da ita, tana daga kwance ta sa a yi wa Jakadiya iso har cikin turakarta. Jakadiya na shiga ta zube a ƙasa, "Hutawarki lafiya tauraruwar Mai martaba uwar yariman gobe da yardar Ubangiji. A yi mini aikin gafara na tashi uwar gijiyata a farar safiya..." Da hannu Fulani Umaima ta katse ta, kamar ba za ta yi magana ba sannan ta ce. "Akwai magana a bakinki Jakadiya don na tabbata banza ba ta kai zomo kasuwa." Jakadiya ta yi mata jinjina da hannu. "Allah ya ƙara yawan rai wannan yarinyar da nake ganinta mai hankali ashe lumbu-lumbu ce wutar ƙaiƙayi?" "Jakadiya tafi kanki tsaye. Fulani Umaima ta faɗa a gajarce. "Halima yayar waccan ragowar fitsarin, ita na ji tana shirin ɓallo mana ruwa. Ni kuma na ce har gaban abada kwaɓarmu ba za ta yi ruwa tsululu ba, sai dai a mutu har liman kowa ya rasa sallah..." Jakadiya ta kwashe duk maganganun da ta ji Fulani Babba suna yi ita da Yaya Halima. Murmushi Fulani Umaima ta saki. "Daga kallon da na ga tana bi na da shi ya sa na fahimci ruwa ba zai taɓa tsami banza ba. Ta shi ki je Jakadiya idan hantsi ya fito ki dawo akwai kyautar samirar alkaki da nakiya, zan haɗa miki da fallan zani da gorar maɗi. Na rantse da Allah sai na tabbatar wa Halima ba a taka shuri kowanne iri a zauna lafiya." Jakadiya ta sake zubewa. "Godiya nake uwar ɗakina, godiya nake zinariyar Mai martaba uwar duka mazauna ƙasar Huddam da kewayenta. Allah ya buɗi ido lafiya ya kawo mana Yarima cikin ƙoshin lafiya." Fulani Umaima ba ta amsa ba, inkiya ta yi mata da ido. Ganin haka ya sa Jakadiya ta fice daga ɗakin don ta san ba za ta amsa mata ba. Washegari ya kama suna jaririn Fulani Babba ya ci suna Abubukar Sadiq, haka kawai Sarki Abdul'aziz ya tsinci kansa cikin farin ciki duk ba ya iya nuna soyayyarsa game da yaron, ya so a gayyaci masu wasannin al'adar bahaushe amma wata irin fargaba yake ji da tsoron Fulani Umaima a zuciyarsa. Da ya yi wani yunƙuri sai ya ji kamar idan ya aikata bai kyauta wa Fulani Umaima ba. A haka aka ci taron suna sai dai hatta Bayin da ke cikin masarautar ranar sai ta zame musu daban sakamakon walwala da suka samu ta hanyar sauya abinci da sakewa. Fulani Umaima ta saki jiki sosai a ranar da kanta ta gayyaci 'yan wasan tauri aka gudanar da wasanni, tamkar babu wani mugun ƙuduri a zuciyarta. Bayan suna da kwana biyu 'yan uwan Fulani Babba suka tattara kayansu suka koma masarautarsu, ko a ranar da za su tafi sai da Yaya Halima ta jaddada wa Fulani Babba suna komawa za a aiko mata da magungunan da suka da ce. Ita ma kuma Fulani Umaima a ranar da suka tafi a ranar ta dira wurin Bamaguje ta shimfiɗe masa bukatunta, kuma take ya zartar mata da su, haɗe da jinjina mata bisa aikin Baiwa Maimuna da ta aiwatar ba tare da an samu matsala ba. Sai dai abu ɗaya da ya sanar mata ne ya nemi hargitsa kwanyarta har ta koma gida ta gagara runtsawa tana tunanin makomar abin da zai biyo baya. *Masu ganin laifin Fulani Babba na rashin yin addu'a kada ku manta labarin an sanya ya faru a shekaru saba'in baya da suka wuce (1953) Kun ga a lokacin ilimin addini bai yawaita ba, ba kamar yanzu da ilimi ya zaman ruwan dare ba. A mafi yawan wancan lokacin, camfi da tsubbace-tsubbace sun fi ƙarfi a kan yawaitar addu'a, babu wayewar kan da idan abu ya same ka kace bari ka duƙufa ba dare ba rana ka kai wa Allah kukanka.* _Ummou Aslam Bint Adam_ 🌚 07062062624 *SHU'UMAR MASARAUTA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga ɗaukan tsattsauran mataki don haka a kiyaye. SHAFI NA SHIDA Ajiyar zuciya Fulani Umaima ta sauke ta zauna a gefen gado, wani irin gumi ya fara tsattsafo mata. "Binciken da nake kan yi dangane da abin da kike ɗauke da shi a cikin cikinki, na shafe tsawon kwanaki ina bincike har yau na gagara sanin mene ne a ciki. Kullin duhu nake mai ɗauke da rashin alkairi, duhu ne mai ɗauke da tururi da ke ƙone duk wani makusancinsa. Ba ke kaɗai ba ni kaina ina da burin sanin me za ki haifa domin amfanar gobena. Ina buƙatar Magaji a halwar tsafina Umaima." A razane ta ɗago tana kallonsa, "Ban gane kalamanka ba Bamaguje, me ye alaƙar abin da yake cikina da gadon halwar tsafinka?" Bamaguje ya saki murmushi. "Wannan sirrintaccan sirri ne tsakanina da mahaifiyarki, ba alaƙar abin cikinki ya kamata ki tamabaya ba. Amma mu jirayi lokacin kin san ko ba daɗe ko ba jima akwai lokacin da ya za ta ɗakin ƙanwa." Sallamar Baiwa Salame ta katse Fulani Umaima daga duniyar taunanin abin da suka tattauna da Boka Bamaguje. Ba ta amsa mata ba don haka Baiwar ta koma, Fulani Umaima ta miƙe ta ci gaba da kaiwa da kawowa damuwa cunkushe a zuciyarta. Kamar wacce aka tsokara haka ta miƙe ta ƙarasa ta ɗauko akwatin sirrinta, ta ɗauko littafin da Bamaguje ya bata. Sai da ta sauke ajiyar zuciya sannan ta buɗe shafin da ta tsaya da karatu. Na jima a tsugunne gaban Uwar Bayi ina tsammanin kalamanta har sai da na fara yanke ƙauna da samun abin da nake buƙata, ba zato na ji muryarta a tsakiyar kaina. "Hidaya labarinki cike yake da almara, al'ajabi da ban mamaki. A tsammanina ni ce mace ta farko da na fara tozali da ke a cikin masarautar nan, ban sani ba ke 'yar cikinta ce ko akasin haka. Abu ɗaya na sani watarana na tafi isar da saƙon Fulani Hauwa na gan ki tsaye a jikin bishiyar kukar da ke bayan ɗakunan Bayi kina rusa kuka, gudun kada na yi latti a aiken da aka yi mini ya sa sai da na kai na dawo har lokacin ba ki daina kuka ba. Da yake a ranar an shigo da sababbin Bayi sai na yi tsammanin 'yar ɗaya daga cikinsu ce yawo ya kawo ta nan take kuka ta gaza gane hanya wurin mahaifiyarta. Sai na riƙe miki hannu muka wuce sashen Bayi na ƙaraci cigiya babu wanda yace 'yarsa ce, to da yake a cikin Bayin da aka kawo akwai wasu mata biyu da suka rasu sai na yi tsammanin mahaifiyarki na ɗaya daga cikinsu. Amma daga baya sai na ga 'yan uwansu suna cewa sam ba tare da su aka kawo ki ba, wannan dalilin ya sa kika ci gaba da zama a sashen Bayi ba tare da iyaye ba." Kalama Uwar Bayi suka zo ƙarshe a daidai lokacin da ni kuma bakin ƙomar idaniyata ta ɓalle, sai da na yi kukana mai isata na dube ta. "Haka zan ƙare rayuwata ba tare da sanin makomata ba." Uwar Bayi ta wara hannuwa. "Abin da na sani kaɗai na sanar da ke, idan Allah ya sa akwai rabo sai ki gansu ko a nan gaba ne." Yau ita ce rana ta farko da na ji daddaɗan kalamai daga bakin wani daga cikin Bayin da nake mu'amala da su, don haka na ƙirƙiri murmushin da bai kai zuci ba na furta. "Shi kenan ina godiya Uwar Bayi da wannan bayanin naki." Babu wanda ya sake tanka mini haka na tashi jiki a sanyaye kamar kazar da aka jefa da wuƙa na koma mazaunina na farko na zauna ina jin zuciyata babu daɗi. Ina jin su suka ci gaba da hirarsu sai dai ko kaɗan ba na fuskantar koda kalma ɗaya, zuciyata ta yi nisan kiwo a fannin tunani da na gagara janyo ta balle ta gane in da hirarsu ta dosa. Wani farin tsoho mai ɗauke da farin gemu na gani yana tunkaro ni, tsananin kammanin da muke yi da shi ya sa na tsaya cak ina kallonsa. Tun da na zo duniya ban taɓa ganin mai kamceceniya da ni ba, ban yi tsammanin ya kusance ni ba don haka na ji hannuwansa a cikin nawa. "Kada ki damu da sai kin san wace ce ke, kina da kowa kuma wannan masarautarki ce gadonki ce halak malak, sai dai ina mai ta'ajibin sanar da ke har duniya ta tashi ba za ki ga mahaifiyarki ba. Ni ne mahaifinki! Ni ne mahafinki!! Ni ne mahaifinki!!!" Firgigit na farka daga mafarkin da nake yi, na juya ina kallon yadda mutane ke baccinsu hankali kwance. Mamaki ya kama ni, cikin damuwa na furta. "Ya aka yi ka zama mahaifina? Kuma me ya sa kuka guje ni." Kamar alamara na ji an furta mini. "Ba mu guje ki ba, mun kawo ki karagarki ne don ki karɓi abarki." Waige-waige na fara yi don ganin mai tanka mini a cikin tsohon daren nan, har na yunƙura zan tashi sai na ji tsoro ya mamaye ni, ba shiri na koma na zauna bacci ya ƙaurace mini. A lokacin da bacci ya fara fisga ta na ji Uwar bayi tana tashinmu cikin hargowa da masifa kamar yadda ta saba duk asubar fari. A haka na ci gaba da gudanar da rayuwa cikin rashin daɗi, rashin 'yanci da ƙangin bauta. Mu Bayi ba mu da wani gata ba musan ci mai kyau da sha mai kyau ba, ana cikin haka watarana saƙo ya iso gare mu ana san Uwar bayi ta sake zaɓen Bayi ta kai sashen Fulani Hauwa kulu, haka kawai na ji gabana yana tsananin faɗuwa. Aka saka mu muka yi layi cikin tsautsayi ƙaddara ta yarfo mini hannunta, Uwar Bayi ta zaɓa har da ni a cikin mutane ukun da Fulani Hauwa take buƙatar ƙari.Tun da nake rayuwa a cikin Masarautar ban taɓa shiga sashen Fulani ba, hasali ma ban taɓa tozali da ita ba, sakamakon rashin imanin da nake jin ana faɗa game da ita. Wannan ta sa nake takatsantsan a kan abin da zai sa na kai kaina sashenta. Tun da muka dumfari hanyar sashen Fulani nake jin jikina yana yi mini wani irin zafi, hayaniya na fara ji sama-sama a kaina ga wani kiɗan tambura da nake ji yana tashi a tsakiyar kunnuwana. Sai dai yadda na lura ni kaɗai nake jin waɗannan baƙin al'amuran da ke yi wa duniyana dirar mikiya. Take gumi ya fara keto mini sakamakon yadda nake jin zafin na ratsani kamar wacca aka tsire a tukubar tsire. A babban ƙofar rumfar (Falo) Fulani Hauwa na coge, sakamakon yadda nake jin ana fisgata. Hayaniyar da nake ji ta fara rikiɗa zuwa muryar da nake jin tamkar na taɓa sanin mamallakiyar muryar. "Barka da zuwa Sarauniya." Na ji an furta. Waige na fara yi amma ban ga kowa ba, na riƙa jin busar sarewa a tsakar kaina ba tare da na ga masu yi mini ba. Ina nan tsaye na ji Uwar Bayi na faɗin. "Ku yi hanzari kada ku fusata Fulani kuke tafe laƙai-laƙai kamar marasa laka a jiki." Da sauri na ci gaba da tafiya har muka ƙarasa babban rufar Fulani da ta ƙayatu da kayan alatu kala-kala. Kaina na ji ya yi girma wata irin ƙasaita, isa da tsantsar izzar mulki na ratsa ni, da ƙyar nake taku cikin ƙasaita. Uwar Bayi da sauran Bayin da muka taho tare suka tsaya cak a bakin wata mashinfiɗa wacce bayi suke tsayawa idan sun shiga wurin Fulani Hauwa kulu. Ban kalle su ba na zarce kan ƙasaitacciyar karagar da ke cikin falon, na zauna ina kallon su Uwar Bayi ɗaiɗai. Da zamana na ji wani abu ɗau! Yana zagaye ƙoƙon kaina. Uwar Bayi kusan mutuwar tsaye ta yi ganin ɗanyan aikin da na aikata, bakinta na rawa ta furta mini. "Hidaya...hankalinki ɗaya kuwa? Kin san a fadar wacce kike?" "Ya kamata ki gyara linzamin harshenki, idan ba haka ba sai na sa an datse shi nan take. Wannan fadata ce..." Ashar ɗin da Fulani Hauwa kulu ta saki ya katse kalamaina, na dube ta cikin tsadaddiyar shigarta ina ƙare mata kallo. "Uban waye ya halatta wa wannan ƙasƙantaciyyar zama a karagata?" Cikin isa da ƙasaita na ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya, kamar ba zan amsa ba na ɗago ina kallonta a wulaƙance. "Wannan karagar iyaye da kakannina ce don haka ki gyara kalamanki." Na lura da razani a saman fuskarta, ɗan yatsanta na rawa ta nuna ni. "Ta tabbata ke ce Hidaya ko?" Na jingina da jikin kujerar na furta. "Ba tsammani ba ne ni ce Gimbiya Hidaya." Wata gwauruwar ajiyar zuciya na ji ta sauke. "Tabbas da alama tarihi zai kuma maimaita kansa. "Tarihi tuni ya sake maimaita kansa tun da gani na wanzu a gabanki." Fulani Umaima ta rufe littafin tana jin kanta na sarawa don a kullin labarin Hidaya ƙara hargitsa kwanyarta yake. Ta wurga shi cikin akwatinta tana sakin tsaki a fili don ba ta jin za ta sake ci gaba da karanta wannan rikitaccan labarin. Komawar su Yaya Halima Masarautarsu da kwana ɗaya labari ya dawo wa Fulani Babba na sabuwar lalurar da ta afka wa Yaya Halima na kurumcewa da makanta, hankalin Fulani Babba ba ƙaramim tashi ya yi ba. Da yake jego take yi babu damar ta tafi dubiya haka ta zauna ta ci kukanta a cikin ɗaki, ta sake ayyanawa zuciyarta ko da wasa ba za ta sanarwa da mahaifiyarta halin da take ciki ba don kar damuwa ta yi mata yawa. BAYAN SHEKARA GOMA Tafe suke a cikin wani baƙin ƙasurgumin daji mai matuƙar hatsarin gaske, su kansu sukan yi takatsantsan wurin shiga irin waɗannan dajijjikan sakamakon miyagun hallitu da iskokin da ke cikinsa. "Mai gado wai ni kam kin taho mini da baƙar bakata?" Umaru ya faɗa yana sake leƙen wani koren maciji da ke saƙale da wata koriyar bishiya. "A'a Malam tsakani da Allah ni kam na manta ka san sai da na ce idan za mu fito ka tuna mini." Da sauri ya ciro wata ƙanƙanuwar kwari da baka daga cikin ƙugunsa, bai cika harbi da ita ba don haka ya so Mai gado ta taho mata da farar bakar wurinta. Ya kalli macijin haɗe da matsa wata laya da ke saƙale a wuyansa, ya sakar wa macijin harbi nan take ya tsire shi wani koren ruwa mai kauri ya fara fita daga jikinsa. Yana shirin miƙa hannu ya ciro kibiyar daga can gefensu suka fara jiyo numfarfashi, Mai gado da sauri ta fara matsawa don tabbatar da zarginta. "Wash wayyo! Ku taimaka mini, ku kawo mini ɗauki tsafi zai taimake ku. Tsafi zai shiga lamarinku, ku taimaka mini kada na mutu idan na mutu tsafi zai yi fushi da ku." Gaban Mai gado ya faɗi ganin wata matashiyar mace mai tsohon ciki tsugunne babu kaya a jikinta, ƙugunta ne kaɗai ɗaure da ganye sai saman ƙirjinta. Kanta da wani irin cukurkuɗaɗɗan gashi ya zubo har ƙirjinta. "Malam zo ka ga." "Kada ki taɓa komai Mai gado, har yanzu ba ki gama sanin sharrin daji ba. Wannan ba kamar sauran dajijjika ba ne, ki yi takatsantsan." Yana ƙarasawa idanunsa suka yi tozali da matar, ta galabaita da alama naƙuda take duba da yadda jikinta ya ɓaci kace-kace. Mai gado ji ta yi ba za ta iya daurewa ba don haka ta ƙarasa ta ruƙo ta tana faɗin. "Baiwar Allah me ya kawo ki naƙuda cikin dokar dajin nan?" Wani irin nishi suka ji ta yi cikin galabaita da fita hayyaci tana faɗin. "Tsafi, tsafi ka dafa mini. Abin bauta ka tserar da jinina ko ɗon ta gagara magautana, tsafi ka taimaka mini." Rufe bakinta babu jimawa suka ji ta ƙwalla ƙara nan take ta haifo jaririyar 'yarta mai tsananin kama da ita. Mai gado na shirin taɓa jaririyar da sauri matar ta dakatar da ita, ta hanyar ture hannunta tana girgiza mata kai. "Zuri'ar RUMZU daban take da sauran al'umma, idan muka haihu tashin farko jinin wata al'umma ba ta isa ta taɓa mana 'ya'ya ba har sai mun gama da 'ya'yanmu ake taɓa mana su. Idan ba haka ba yanzu za ki mutu, abin bauta zai hallaka ki." Mai gado ta ɗan zaro idanu cikin tsananin mamaki. Umaru da ya juya bayansa ya jinjina kai yana taɓe baki. Hannu ta sa a ƙugunta ta ciro wata ƙaramar baƙar aska ta yanke wa jaririyar cibiya, ta sa wata siririyar fata ta ɗaure cibiyar tamau. Hannunta ta saka ta lakuto jinin da ke fita daga ƙasanta ta shafa a saman goshin jaririyar lokaci ɗaya jaririyar ta tsanyare da wani irin matsanancin kuka, jinin da ta lakata mata a goshi ya shiga wata irin tafarfasa a kan goshin jaririyar. Wani irin baƙin jini ya fara zuba daga cikin hancin jaririyar, kunnuwanta da ƙasanta. Mai gado tana tsaye tana kallon abin da matar take yi cikin al'ajabi da tsananin mamaki har sai da tsoro ya fara kamata. Ganin jinin ya zarce ƙa'ida ya sa matar ta saka bakinta ta zuƙo shi sannan ta fesar a gefe, take ciyawar wurin ta ƙone ƙurmus. Ta jima tana zuƙe jinin jikin jaririyar tana ɗiban jinin gabanta tana zubawa a goshinta, idan ya tafasa sai ya shige jikin jaririyar. Sai da matar ta gama ta ɗago ta dubi Mai gado cikin karyewar zuciyata tana faɗin, "Ban san ku su waye ba, amma na tabbata daga yanayinku ku masu karamci ne kuma tsafi zai shiga lamuranku ya dafa muku..." Da sauri Umaru ya waigo ya katse ta. "Baiwar Allah mu ba mu dogara da tsafi da sihiri ba, mun dai dogara da Ubangijin sammai da ƙassai." Jinjina kai ta yi tana murmushi ta furta. "Koma da wa kuka dogara ban damu da na sani ba, zan bar muku amanar 'yata domin na san dangina ba za su bar ni ba mutuwa zan yi, don na hangi tsinin mashin tsafin da Mahaifina ya wurgo min, idan ban damƙa muku ita ba tabbas har ita za su hallaka mu. Ba a nan doron ƙasa ba, ko ƙarƙashin ƙasa na nutse matuƙar ina numfashin na tabbata zuri'ata ta Rumzu ba za su bar ni ba." A firgice suke kallonta. "Wace ce ke? Mutum ce ko aljan?" Mai gado ta wurga mata tambaya a tsorace. "Sanin matsayin hallitata ba shi ne mafita ba, domin a yanzu ba lallai ya amfane ku da komai ba. Ga amana zan bar muku ku dubi darajar abin bautarku ku riƙe ta amana, na so a sanya mata suna HAIZAT amma dalilin mahaifinta ya nunke nawa don haka ya ce mini ya fi son a saka mata sunan JAWAHIR, ban san ma'anar sunan ba don ba ya daga cikin sunan zuri'ata. Sai dai na tabbata wannan sunan zai amfane ta zuwa nan gaba, idan ta isa zama budurwa ku ɗauke zuwa bakin kowacce irin bishiyar kuka akwai ajiyar da mahaifinta ya taɓa yi wanda ita za ta tono gadon da zai bayyanar da ita jininsa ce da hannunta. Wannan jaririyar ita za ta sanar da ku asalin wace ce ni har zuwa zuri'ata ta Rumzu, tun daga zubin hallita har zuwa tushenta. Na san dangina da bibiya, kafiya da matsanancin ruƙo duk rintsi kada ku bayyana ba kune asalin iyayenta ba matuƙar za ku shiga baƙon wuri ko al'umma, wataƙila ta iya tsira da rayuwarta daga kaidinsu." Tana gama maganar ta ɗora jaririyar a kan saman wani ƙaton gidan tururuwa, ta damƙi ƙasar gidan tururuwar tana runtse idanunta haɗe da furta waɗansu irin kalaman tsafi da su Mai gado ba su taɓa ji ba, tana gamawa ta shafa a jikin jaririyar gabaɗaya, take jinin da ke saman goshin jaririyar ya ɓace ɓat. Ta sunkuya saitin kunnen jaririyar tana yi mata raɗa, lokaci ɗaya jaririyar ta yi shiru tamkar wacce take sauraron kalaman mahaifiyarta. Wani irin jini ne ya ɓalle wa mahaifiyarta amma duk da haka cike da ƙwarin gwiwa da dakiyar zuciya ta ɗauki jaririyar ta fara takawa har zuwa bakin ramin kwarmin bishiyar kukar da ke gefenta ta ɗora jaririya a ciki, ta saka hannu ta dafa saman goshinta nan take suka ga ta fara wata irin jijjiga, idanunta suka firfito numfashinta ya ɗauke rai ya yi halinsa. Daga Umaru har Mai gado kusan mutuwar tsaye suka yi saboda al'ajabi don tun da suke a duniya ba su taɓa ganin makamancin irin wannan lamarin ya faru a gabansu ba. Mai gado ce ta iya motsawa ta ƙarasa ta ɗauki jaririyar da mamaki ta kalli Umaru jin jikin jaririyar ya yi wani irin sanyi kamar ƙanƙara. "Malam yanzu ya zamu yi da wannan gawar?" Ajiyar zuciya ya sauke yana shirin yin magana suka ga gawar matar na matsawa haɗe da nutsewa cikin bishiyar kukar da take jigine a jikinta. Cikin tsoro suka ja da baya suna kallo, kafin wani lokaci babu gawar babu alamarta ta nutsa cikin bishiyar kukar sai shatin jinin da ke manne a jikin bishiyar. Jiki na karkarwa Mai gado ta ajiye jaririyar a ƙasa tana ja da baya ta furta. "Mai gida Allah ya sani ba zan iya riƙon wannan abin ba, domin ba na ko tantama mahaifiyar yarinyar aljana ce ita kanta yarinyar dubi irin siddabarun da mahaifiyarta ta yi mata kafin ta mutu." Cike da gamsuwa Umaru ya ɗago zai yi mata magana, gabansa ne ya yanke ya faɗi sakamakon mugun gamon da ƙwayar idonsa ta yi. Da sauri ya ja hannun Mai gado suka faɗi can gefe haɗe da kurma ihun neman taimako. _Ummou Aslam Bint Adam_ 🌚 07062062624 *SHU'UMAR MASARAUTA* ©️AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga ɗaukan tsattsauran mataki don haka a kiyaye. SHAFI NA BAKWAI Koren macijin da Umaru ya kashe tun kafin haihuwar matar nan suka hango ya sulalo ya kafe su da ido yana kallo tamkar zai far musu da sara, suna nan cikin tsinkewar zuciya suka ga ya ƙarasa wurin jaririyar ya kanannaɗe ta, suna daga wurin da suke a gefen Umaru ya ce. "Mai gado an ya yau mun shigo dawa a sa'a kuwa?" Da sauri ta girgiza masa kai. "Tun wuri mu kama hanyar gida." Cikin sanɗa suka miƙe da niyyar tafiya sai dai bisa ga mamakinsu babu macijin babu alamarsa, don haka suka nufi hanya da niyyar tafiya. Cak Mai gado ta tsaya tana waige. "Tsayawar me kika yi Mai gado?" "Mai gida zuciyata ta karaya, ba zan iya tafiya na bar yarinyar can ba. Ka dubi yadda mahaifiyarta ta aminta har ta damƙa mana amanarta. Ba mu sani ba wataƙila samunta babbar rahama ne a tattare da mu, ta wani fannin ma gani nake Allah ne ya azurta mu da samunta ka duba ka gani haihuwata huɗu duk yanzu babu rayayye, idan muka bar ta a wannan ƙungurmin dajin ba mu san wacce irin rayuwa za ta gudanar ba." Jikin Umaru ya yi sanyi ya waiga yana hango jaririyar da ke tsala matsanancin kuka. "Mu je na ɗauko ta In Shaa Allah, Allah zai kare mu tun da ya ga kyakkyawar niyyarmu." Da haka suka rankaya suka wuce har gaban jaririyar suka ɗaukota, Mai gado ta kunto ɗankwalinta ta nannaɗe ta a ciki sannan suka nufi hanyar da za ta sada su da gida. Sai da fargabar da Umaru yake ciki ba wuce irin tarbar da mutanen ƙauyensu za su yi musu ba, musamman idan aka samu akasi wani al'amarin almara ya faru kamar yadda suka gani daga wurin mahaifiyarta. Sai dai sun ɗaukar wa kansu alƙwari babu wanda za su furtawa silar samuwar yarinyar don kada ta taso cikin tsangwama da ƙyara. Masarautar Huddam Ɗan matashin ne mai kimanin shekara goma zaune a cikin fadar Sarki Abdul'aziz a kan shimfiɗaɗɗiyar shimfiɗar alfarma yana sanye da rantsattsiyar alkyabba. Kallon mutane yake yi ɗaiɗai fuska a murtuke babu walwala, kallo ɗaya za ka yi masa ka tabbatar da mulkin gadarsa ya yi ba taka-haye ba. Gajiyar da ya yi da zaman cikin fadar ya sa ya miƙe cike da izza yana taku kamar ba zai taka ƙasar ba. "Takawarka lafiya Yariman masarauta, a huta lafiya sarkin gobe da yardar Allah." Fadawa suka ɗauka a lokacin da suka lura Muhsin ya miƙe da niyyar fita daga fadar, wasu daga ciki suka ƙarasa suna take masa ba. Hannu ya ɗaga haɗe da tsayawa wuri ɗaya cak, ya kusa minti ɗaya a haka sannan ya furta. "Ba na buƙatar rakiya." Lokaci ɗaya suka ja da baya sannan ya ci gaba da taku, duk hanyar da ya bi haka bayi da fadawa suke zubewa suna kwasar gaisuwa amma ko kallansu ba ya yi ballanta su saka ran zai tanka musu. Yana gab da shiga sashen mahaifiyarsa bisa tsautsayi wata baiwa ta fito da sauri don isar da saƙon Fulani Umaima, a rashin sani ta bangaje shi har sandar hannunsa ta faɗi ƙasa. Jiki na karkarwa ta zube ƙasa. "Tuba nake shugabana, a gafarce ni uban gidana ni mai laifi ce ba tare da..." Marin da ya ɗauke kuncinta da shi ya sa haƙoranta suka datse harshenta har sai da bakinta ya fashe, idanunta suka fara zubar da ƙwalla ta sake zube wa a ƙasa tana faɗin. "Godiya nake Sarkin gobe." Ɗaga kansa ya yi ya hango wani Bafade hannunsa ɗauke da murtukekiyar bulala ya furta, "A hora ta na tsawon wuni guda da alama ba ta gama sanin a gidan masarauta take rayuwa ba tun da ba ta san aikinta ba." Yana gama maganar ya wuce ba tare da ya jira cewarsu ba. A kishingiɗe ya tarar da mahaifiyarsa tana huatawa, wasu 'yan matan Bayi na tsugunne wurin ƙafarta suna yi mata tausa. Ganin yanayinsa ya sa ta tashi zaune haɗe da sallamarsu. "Wa ya ɓata ranka Muhsin?" Fulani Umaima ta tambaye shi. Bai tanka mata ba sai da ya zauna. "Wata baiwarki ce ta ɓata mini rai amma komai ya wuce." "Wace ce ita na sa a hukuntata?" Muhsin ya fara rage kayan jikinsa. "Na sa a hukuntata, ina Ruƙayya ban ganta ba?" Fulani Umaima ta yamutsa fuska, "Za ta wuce sashen Fulani babba ne, yarinya sai baƙin nacin tsiya kamar tsohuwar mayya." Take idanunsa suka yi jawur rai a matuƙar ɓace ya saki guntun tsaki, ba tare da furta komai ba. Ihun da Ruƙayya ke ƙwallawa ne ya ja hankalin Fulani babba da sauran bayin da ke harabar gidan, turus bayin suka yi suna kallon juna duk da ba yau ce rana ta farko da suka ga Abubakar na kama gashin duk wani mutum da ya kusance shi ba ciki kuwa har da mahaifiyarsa. Ruƙayya ƙanwar Muhsin ce ita take binsa shekararta bakwai a duniya, Allah ya haɗa jininta da Abubakar ba ta iya wuni guda cir ba tare da je sashen Fulani babba ta shiga ɗakin Abubakar ta tsaya yana yi mata gwaranci tana mayar masa ba. Babbar matsalar da ke damun Fulani Babba bai wuce yadda Abubakar yake cizgar gashin kansa yana ci ba, idan na kansa ya ƙare kuma duk wanda yake da tsautsayi idan ya damƙe ka haka zai dinga cizga har sai an kwace ka. Abubakar ya shiga shekara ta goma sha ɗaya, sai dai har lokacin a zaune yake ko motsi ba ya iya yi komai sai an yi masa. Fari ne sol kamar mahafiyarsa sai dai kammaninsa sak da Sarki Abdul'aziz, tun da ya taso ba ya iya magana sai dai gwaranci kuma har kawo lokacin yawu na dalala daga bakinsa. Idanunwansa duka biyun a juye suke, hannuwa da ƙafafuwansa suma a shanye suke babu abin da yake iya aikatawa hatta wanka da tsarki yi masa ake yi. Fulani Babba da sauri ta ƙarasa gaban Abubakar ta sa hannu cike da ƙunan rai ta ɗauke fuskarsa da mari, wannan ne karo na farko da ta taɓa sanya hannu a jikinsa da sunan duka. Zafin marin ya ratsa shi hakan ya sa ya ƙarasa cizge kitson kan Ruƙayya da ke bakinsa, sai kuma ya fashe da kuka yana gwara kansa da ƙasa. Cikin azaba ta sake ƙwalla ƙara take numfashinta ya ɗauke ta sume a wurin. Tamkar mayuwancin zakin da ya samu nama haka Abubakar ya tura sillin jelar kitson kan Ruƙayya da ya cizge cikin bakinsa ya fara tauna kafin wani lokaci ya haɗiye shi gabaɗaya. A firgice Fulani Babba ta shiga yayyafa wa Ruƙayya ruwa ta jima a kanta sannan ta sauke ajiyar zuciya a galabaice, ganin ta buɗe ido ya sa Fulani Babba ta ji farinciki har cikin ranta sai dai kuma wurin da ya ɗaye mata kitson tuni gefen kan ya kumbura suntum. Wani irin sara ta ji kan yana yi mata a daddafe ta iya miƙewa ganin haka ya sa Fulani ta ba wa Bayin da ke gefe umarnin su ɗauke ta zuwa cikin turakarta. Duk dauriya irin ta Ruƙayya sai da ta dinga zubda ƙwalla sakamakon yadda take jin kanta na sara mata kamar zai tsage gida biyu. Duk yadda Fulani babba ta so zaman Ruƙayya a ɗakin zuwa lokacin da zugin zai sarara mata fir ta ƙi yarda, don haka ta sake saka Bayi suka ɗauke ta tana gaba suna biye da ita a baya har cikin sashen Fulani Umaima. Ganin a halin da aka shiga da Ruƙayya ya sa Fulani Umaima miƙewa zumbur! Bakinta har rawa yake ta furta. "Me ya faru da ita?" "Laifi ne yayanta Sadik ya yi mata, wallahi tsatsayi ne Fulani don haka na zo da kaina ba saƙo ba..." "Dakata Fulani! Hawainiyarki ta kiyayi ramata. Ba tun yau ba na lura da take-takenki dangane da kiranyen da kika yi wa Ruƙayya. Lokaci ɗaya kin sa an lashe kurwar yarinya ba ta ƙaunar zaman wurin mahaifiyarta, wannan fa ba shi ne karo na farko na ji labarin wancen shagirigirbau ɗin ya maƙure ta yana yi mata ƙamshin mutuwa ba. Amma an yi ta yanke ta gille, wannan shi ne karo na farko kuma na ƙarshe da zai sake taɓa kowanne bil'adama a sashenki." Fulani Umaima ta ƙarasa maganar tana kai kallonta wurin bayin da ke riƙe da Ruƙƙaya. "A samu Jakadiya ta gaggauta sanar da Mai martaba ina buƙatar ƙwararrun masu magani, don ban san dafin da haƙoransa suke ɗauke da shi ba." Da sauri suka shimfiɗar da ita suka fice, Fulani Babba ta ƙarasa gabanta ido cike da ƙwalla ta furta. "Wallahi ko a mafarki ban taɓa jin Ruƙayya ba 'yata ba ce, tamkar yadda na ɗauki su Khadija haka nake jin ta, ta ya ina sane zan bari Abubakar ya illatata." Sai da Fulani Umaima ta saki murmushin takaici ta furta, "Me ya sa bai kama Khadija ko Sakina ya illata ba, saboda kina baƙincikin kin haifi sauna, wawa, shashasha shi ne ni ma kike burin ƙarfi da yaji na rasa waɗannan biyun da Allah ya ba ni." Tsoron hukuncin da Fulani Umaima za ta yanke ya sake mamaye Fulani babba, ta tsugunna bisa gwiwoyinta don ta san kome Fulani ta gaya wa Takawa hawa yake ya zauna ɗaram. Ba tun yanzu ba ta jima da dawowa daga rakiyarta, don ta lura sai abin da Fulani Umaima take so Takawa yake zartarwa. "Tabbas Abubakar bai kyauta ba amma ki dubi girman Allah ki yi haƙuri..." "Idan ba ki yi gaggawar fita daga sashena ba wallahi sai na shayar da ke ruwan mamaki." Fulani Umaima na gama magana ta yi ciki cike da zafin rai. Fulani babba ta sunkuyar da kanta ƙasa tana zubar da ƙwalla, dama ya ya lafiyar kura ballantana ta yi zawo. Gari banza ma Takawa ba ƙaunar Abubakar yake ba ina ga an ce ya taɓa 'ya'yan gaban goshi. Cike da zullimi ta fara yunƙurin tashi, daga bayanta ta hangi Muhsin na zaune yana aika mata da saƙon harara cikin kallon tsana. A haka ta ƙarasa sashenta gwiwoyinta a sanyaye, ta windo ta leƙa Abubukar da ke zaune yawu na dalala. Sai a lokacin ta samu damar fashe wa da matsanancin kuka duk da tana da tabbacin bayin da ke zagaye da ita suna sauraronta. "Ya Allah ba don ba ka so ko ƙaunata ka jarabce ni da wannan bawa Naka ba, Ya Ubangiji ina godiya bisa baiwa da wannan ni'imar da ka yi mini domin dubbunaina na buƙatar ko da makamancinsa ne. Ya Allah idan rayuwar wannan bawa naka mai tsayi ce Ubangiji ka yalwace shi da lafiyar ya zama kamar kowa, saɓanin halin da yake ciki. Idan kuma mai gajeren kwana ne Ubangiji ka gaggauta ɗaukar kwanakinsa ko na samu salama a rayuwata..." Kukan da ya ci ƙarfinta ne ya datse ragowar kalamanta. "Allah ya sanyaya zuciyar uwar ɗakina Ubangiji ya ƙara wa Yarima lafiya." Baiwa Zainaba ta furta jiki a sanyaye kamar kazar da tono wuƙa. "Zainaba na ɗauka ko kowa zai furta son ransa ke mai faɗa mini gaskiyar abin da ke cikin zuciyarki ne? A haka kike kiran Abubakar da Yarima kina ga ko a mafarki za a damƙa wa Abubakar karagar mulki ne." Tabbas kalaman Fulani Babba a turba suke domin kowa ya san halin da Abubakar yake ciki kuma ko a garin gaɓa-gaɓa babu wanda zai damƙa masa kujerar sarauta, ina ya san kansa ma balle ya san matsalolin talakawa? Sai da ta ƙara rissinawa ta furta. "Tuba nake ranki shi daɗe, In shaa Allahu Allah zai ba shi lafiya." Fulani babba ta amsa mata sannan ta wuce cikin sashenta. Ganin har zuwa dare babu wani saƙo ya sa Fulani babba ta ɗan fara sakin zuciyarta, har ta zauna su Khadija na soko mata hira wani ta amsa musu wani kuma ta yi musu shiru. Suna cikin wannan yanayin Jakadiya ta iso da kiran da Maimartaba yake yi mata. Take ƙirjinta ya buga dum! Zuciyarta kamar za ta yi tsalle ta fito daga ƙirjinta, da ƙyar ta tattaro jarumtar haɗa kalmomin da ta iya furta wa Jakadiya. A gurguje ta watsa ruwa ta ɗan gyara jikinta, don saboda yadda lalurar fitsarin da yi mata kamun kazar kuku har ji take haka kawai kamar zarni na tashi a jikinta. Da kwalliyarta fes ta ƙarasa turakar Mai martaba ƙamshi na tashi, haka kawai wani lokacin yake jin kamar yana tauye haƙƙinta ko yana yi mata ba daidai ba, musamman yadda ya ga ta fige ta lalace kamar ba ita ba. "Barka da hutawa Sarkina." Kalamanta ya ji na sauka a kunnuwansa, wani ɗaci ya ziyarci zuciyarsa kamar wanda ya haɗiyi maɗaci. "Barka!" Daga haka shiru ya biyo baya, ganin yanayin tarbar da Mai martaba ya yi mata ya sa jikinta ya yi sanyi. Cikin sanyin murya ta furta. "Allah ya taimake ka na ji saƙon kana son ganina." "Wani hukunci muka yanke da muke ganin shi ne mafi alfanu babu cuta babu cutarwa." Mai martaba ya faɗa fuska a haɗe kamar dafaffan kwanannan kunun tsamiya. Ƙirjinta ya hau dakan lugude, gumi ya fara keto mata ta ko ina. "Don haka ba ma buƙatar jayayya. Abubakar Sadiq zai koma ɗaya daga cikin ɗakunan gidan ajiya da gyaran hali, na sa a ware masa ɗaki guda wanda zai zauna a ciki, idan ya so duk wani abu da yake buƙata a aiwatar masa a can. Mun yanke wannan hukuncin ne domin sama wa lafiyayyun gidan nan mafita, idan yau ya nemi nasaka wannan jibi wancan watarana ina tunanin kaina zai dawo." Kafin dirar kalaman Takawa tuni hawaye ya gama wanke fuskarta. Cikin kuka ta zube a ƙasa hannuwanta biyu a saman cinyarsa ta furta. "Don Allah kada ka yi mini haka ranka shi daɗe, Allah ya sani Abubakar ba shi kaɗai na haifa ba akwai yayyansa Khadija da Zainab amma wallahi babu wanda na ke jin ƙaunarsa har a cikin jinina kamarsa. Wannan ƙasƙanci ne a ce jininka zai ƙare rayuwa a gidan ajiya da gyaran hali saboda ya kasance mai nakasa, in dai a kan Ruƙayya ne na yi maka alƙawari ko inuwarsa ba za ta ƙara gani ba ballanta shi. Don Allah ka..." Cikin tsawa ya katse ta. "Ba mu san lokacin da raini ya gifta a tsakaninmu ba Fulani, da har ake neman yin jayayya da mu. Mu ba ƙananan mutane ba ne sanin kanki ne ba tun yau ba; ba ma taɓa magana biyu. Tashi ki ba mu wuri, wannan hukuncin ba zai tɓa canzawa ba." Fulani babba duk yadda ta so dakatar da hawayenta abin ya gagara, don haka ta fice daga turakar zuciyarta na tuƙuƙin ɓacin rai. Tana shiga ɗaki ta fashe da wani irin matsanancin kuka, ganin kukan na ta ba na ƙare ba ne ya sa su Khadija rungume ta suka fashe da matsanancin kuka! Yau ita ce rana ta farko da ta ji zama a cikin gidan ya gama fita daga ranta, ta kuma ji wani abu ya tokare mata maƙoshi game da Fulani Umaima sai dai kuma a ɓangare ɗaya shakka da tsoronta ya hana zuciyarta sanar da ita gaskiyar abin da ke ranta. Sun jima ita da yaran a haka sannan ta miƙe ta nufi ɗakin Abubakar, ta same shi a kwance kamar yadda ta barci. Sai da ta share ƙwallah sannan fito daga ɗakin. Washegari tun safe Dogarawa suka cika umarnin Mai martaba, tun lokacin da aka fara jidar kayan Abubakar Fulani Babba take share hawaye don dai ba ta da yadda za ta yi. "Idan kika matsa mana da magana wallahi ranki zai yi mummunan ɓacin da ba ki taɓa gani ba Fatima." A razane ta dubi Mai martaba, yanayinsa kaɗai ya tabbatar mata babu alamar wasa a tattare da shi. Dole ƙanwar na ƙi ta zubar da makamanta, ta rungumi ƙaddarar da ta afka musu babu sallama. Ajiyar zuciya ta sauke bayan ta tuna yadda suka kwashe da Takawa, a daren ranar da ta sake zuwa sashensa tana yi masa magiya a kan ya bar Abubakar ya ci gaba da zama a sashenta. Hawaye ya gangaro mata sakamakon ganin wata irin birgima da Abubakar ya fara yi a cikin jar ƙasar da ke ɗakin saboda ɗakunan kowannensu babu daɓe a ciki. Wata ƙasar ya ci wata kuma ya burtune jikinsa da ita, tana ji tana gani bayan ta gama kallonsa ta fice daga ɗakin. Abin ka da gidan masarauta take labarin kai Abubakar gidan yari ya gama zagaye gidan kowa da abin da yake tofawa, sai dai mafi yawa daga cikin shakkun Fulani Umaima ya hana su faɗar gaskiyar abin da yake cikin zuciyoyinsu. "Allah ya taimake ki ni fa don kada a ce na saki linzamin harshena amma Allah ya sani na fara ɗora zargi a kan Fulani Umaima. Lamarin zamantakewar da ke tsakaninki da Takawa akwai fa ayar tambaya." Jakadiya ta yi wa Fulani babba maganar tana yin ƙasa da murya. "Jakadiya tafi kanki tsaye ba mu fahimce ki ba." Jakadiya ta sake yin ƙasa da murya. "Bari na fito miki a mutum Fulani, an ya kuwa Fulani Umaima ba ta bi ta ƙarƙashin ƙasa a kan Takawa ba, duba da yadda take cin karen ta babu babbaka a gidan nan kamar wacce ta wanke masa hannu aka. Yanzu musakin yaron nan Bukari me ya yi da zai fuskanci zama a sashen gidan ajiya da gyaran hali." Jin haka ya sa hawaye ya zubo wa Fulani Babba. A fakaice Jakadiya ta saki murmushin cin nasara, don babban burinta ita ma bai wuce ta samu sanadin dandalar arziƙin da su Fulani suke ci ba a matsayinsu na matan Sarki. "Jakadiya al'amurana a yanzu haka na miƙa su a wurin Ubangiji, duk ma wanda ya nemi ya ƙuntata wa rayuwata Allah ba ya bacci yana sane da abin da yake faruwa." Jakadiya ta taɓe baki a fakaice. "Amma ya kamata ke ma ki tashi tsaye domin kin san da sanyin safiya ake kama fara." Fulani babba ta ɗan sauya fuska don haka kawai ta ji ba ta aminta da waɗannan shawarwarin na Jakadiya ba. "Ni fa hatta ciwon yaron nan wallahi na jima da ɗora zargina a kan Umaima, saboda Allah yaro shi ba aljanu ba amma an mayar da shi wani iri. Kwanaki fa har barbaɗe na ga tana yi a turakar Mai martaba wai don ya daina jin ɗanɗanonki." A ɗan razane Fulani babba ta dubi Jakadiya sai kuma ta haɗe fuska. "Jakadiya muna buƙatar hutawa a ba mu wuri." Ganin babu fuska ya sa Jakadiya ta fice tana wurgawa Fulani babba mugun kallo. "Sakarai da ba ta gaji arziƙi ba kya ƙare a wahale cikin warin jiki da fitsari." Jadiya ta faɗa cikin jin haushin rashin samun nasara a kan Fulani Babba bayan ta fita waje. Wacce ta shirya biyan kuɗin karatun ci gaban littafin *SHU'UMAR MASARAUTA* Ƙofa buɗe take, za ta iya turowa ta wannan Acc ɗin da ke ƙasa domin free pages na gab da ƙarewa. Waɗanda suka fara biya su min afuwa zuwa lokacin da zan buɗe group bayan na kammala free pages. *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* *SHU'UMAR MASARAUTA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga ɗaukan tsattsauran mataki don haka a kiyaye. *Masu ƙorafe-ƙorafe ta pc da groups zan rage 100 daga yau zuwa ranar da zan gama free pages. Free pages za su ƙare a page a 10 daga yanzu zuwa ranar duk mai son karanta littafin za ta turo 400* SHAFI NA TAKWAS RIGAR ARƊO A gajiye tuɓus suka dawo gida sakamakon yawon kiwon da suka je cikin dokar daji, zamansu babu wuya wata farar dattijuwa ta ɗauko ƙorai guda biyu sai da ta fara zuba nono a cikinsu ta miƙa wa mai gidanta Baffajo. Ta jima a tsugunne tana jiran ya karɓa tana ɗagowa ta lura da yadda ya dulmiya cikin kogin tunani, a sanyaye ta kai hannu ta taɓa shi. "Yanzu Baffajo ba za ka daina wannan tunanin ba? Idan kai kana yi ni kuma sai ƙaƙa?" Ajiyar zuciya ya sauke. "Inna wuro aradun Allah lamarin yaron nan ƙara ci mini tuwo a ƙwarya yake, yanzu a ce ɗan mutum ba shi da abokan rayuwa sai gidan tururuwa da dokar daji? An ya Inna wuro ba za mu kai Kamalu wurin Malamijon farar riga ba?" Inna wuro ta yi jim cike da damuwa sanna ta furta, "Eh to hakan ma wani abu ne amma ni sai na ga kamar har da sabon shiga dawa..." "Kayya mu ba a dawa muka yi rayuwa tun daga ƙuruciya ba? Kin manta a lokacin baya tsakiyar dare nake tsintoshi a bayan rumfar can wurin shurin da ke gabas da shi." Kamalu ya ɗago fuska a haɗe don jin abin da Iyayensa suke furtawa, motsa baki yake kamar wanda zai yi magana, amma sai ya gimtse ya kawar da kai gefe. "Kamalu kai fa ba yaro ba ne a ƙalla shekarunka sun haure goma, mahaifinku girma ya kama shi ba ka ganin sauran 'yan uwanka ba haka suke ba." Kamalu ya sunkuyar da kai ƙasa ba tare da ya kalle su ba, A'iru da ke gefe ta furta. "Kwarankwasa dubu rannan har gani na yi yana ɗibar wani abu a kan gidan tururuwa yana sha, dubi wancan zobe." A'iru ta yi maganar tana nuna hannun Kamalu mai ɗauke da wani zoben azurfa mai ɗauke da wani irin zane. "Da bakinsa ya ce mini tsintarsa ya yi a kan shuri wai gadon Masarautarsu ne." A razane su Inna wuro suka dube shi, Baffajo ya ce. "Kamalu wa ya ba ka wannan zoben?" "Tsintarsa na yi." Kamalu ya furta kai tsaye ba tare da ɗago ya kalle su ba. Haushi ya fara kama Baffajo don haka ya ce, "Kai Kamalu hai ka shiga taitayinka, ba ka san dawa ba ko?" Kafin Kamalu ta ya ba shi amsa daga sama suka fara jin gudun dawakai da iface-ifacen mutane, kafin su yi wani yunƙuri tuni waɗansu Dogarai da sojojin masarauta suka farmusu cikin shammata suka riƙa taɗe su suna ɗaure su da wasu murtuka-murtukan igiyoyi a jikin manyan itatuwa. Lokaci ɗaya garin ya hautsine ban da ƙura babu abin da yake tashi, waɗanda suke da rabon tsira tuni suka shuɗa daji. Waɗanda aka riga da aka rubuta zanen ƙaddararsu kuma tuni aka damƙe su, a cikin waɗanda suka tsira har da Salele ɗan gida Baffajo. Shi kuwa Kamalu ko da ya ga abin da yake faruwa ko gezau bai yi ba, yana nan zaune wani Dogari ya isa gare shi ya fisgo shi da niyyar taɗe shi, ɗayan hannun nasa ya sa ya bigi gefen hannun Dogari, wata irin azaba ya ji tamkar an zuba masa ruwan dalma. Da kansa ya ƙarasa wurin wasu Dogarawa da ke tsaitsaye suna ɗaure ragowar mutanen da aka kama wanda ko tantama babu sun riga da sun zama bayi. Sai da aka ɗaure Baffajo da waɗansu mutane biyu sannan aka ɗaure Kamalu, a ɓangaren mata kuma tuni aka ɗaure Inna wuro da sauran mutanen da ke cikin rigar. Kafin wani lokaci rigar ta yi fayau sai kukan dabbobi da ƙananan tsuntsaye da ke tashi. ƘAUYEN GANGARE Jiki a matuƙar sanyaye suka ƙarasa cikin ƙauyen gangare hannun Mai gado ɗauke da jaririya, tun daga ƙofar gari aka fara jefa musu tambayoyin inda suka samu jaririya sabuwar haihuwa. Sai dai amsa ɗaya suke bayarwa tsintarta suka yi a cikin gona, da haka suka samu suka ƙarasa gida. Da zuwansu babu jimawa gidansu ya cika maƙil da mutane, wasu na taya su murna ya yin da wasu suka fara tsegungumi da ƙananan maganganu. Wani tunani Umaru ya yi take ya sa Mai gado ta ɗauki jaririya har ta ɗora ruwan da za ta yi mata wanka ya dakatar da ita kai tsaye suka wuce gabaɗaya wurin Mai gari. Umaru yana zuwa fadar Mai gari ya zube ya kwashi gaisuwa sannan ya gabatar da jaririyar hannunsu da mahaifiyarta ta yi mata laƙabi da Jawahir, bayan ya tsahirta ya karɓe ta daga hannun Mai gado ya miƙa wa Mai gari, sanƙira yana raɓe a gefensa. Tun da aka ɗago jaririyar Malam Malmo ya zura mata idanu ko ƙiftawa ba ya ni, wannan ya haddasa fargaba da tashin hankali a zuciyoyin Mai gado da Umaru, sakamakon sanin Malam Malmo sarai da mugun aikinsa. A sakaye Umaru ya ɗan yi gyaran murya ya furta. "Allah shi ba ka yawan rai yanzu haka Mai gado ta ɗora mata ruwan wankan da za a yi mata wanka da shi." Mai gari ya jinjina kai tare da yi musu nasiha a kan su riƙe ta da riƙon amana. Su Umaru har sun miƙe bayan mutane sun watse yana waigawa ya ga Malam Malmo yana yi wa Mai gari raɗa a kunne, haka kawai ya ji zuciyarsa ba ta aminta da wannan raɗar da yake yi wa Mai gari ba. Tsawar da sanƙira ya yi masa ce ta sa shi zura takalman fatarsa ya yi gaba jiki a sanyaye kamar kazar da aka watsawa gishiri. "Mai gado ina tsoron Malam Malmo a kan yarinyar nan kada fa a ce ya gano wani al'amari game da ita." Umaru ya faɗa bayan Mai gado ta yi wa Jawahir wanka tana shafe mata jiki da mai. "Ni kaina ina tsoro amma In shaa Allah babu abin da zai faru sai alkhairi." Wannan ƙawarin gwiwar da ya samu daga wurin Mai gado ya sa ya tashi ya fita don tatso wa Jawahir nonon akuyar da za a shayar da ita. Sannu a hankali suka ci gaba da rainon ta, tun suna ɗari-ɗari da ita har suka saki jikinsu sakamakon babu wani abu da suke gani na ban tsoro a tattare da ita. A ɓangare ɗaya kuma wata irin soyayya suke nuna mata, ga shi sai ta wuni ba a ji kukanta ba idan ba yunwa take ji ba. Abu ɗaya ne ya fara damun Mai gado da yake faruwa da Jawahir cikin dare, duk lokacin da ta farka don ta ba ta nonon akuya da dare sai ta ga wani baƙin jini ya tsattsafo a goshinta, idan kamar bacci ya ɗauke ta har asuba ta yi, sai da ga goshin na ta ya yi ɗan duhu amma babu jinin a jiki, zuwa wayewar gari kuma sai ta nemi komai ta rasa jinin ya washe. Tun tana barin maganar a ranta har ta taɓa tashin Umaru ta sanar da shi, shi kansa ya yi mamaki amma gudun kada ƙilu ta ja bau! Ya ce su zuba wa sarautar Allan ido tun da ba ta kuka wataƙila abin ya mata ciwo. Kwanan Jawahir goma Mai gari ya aika a kira masa Umaru, tun da Umaru ya ji kiran Mai gari gabansa ya faɗi har sai da Mai gado ta ƙarfafa masa gwiwa sannan ya nufi gidan Mai gari cikin wasuwasi. Yana zuwa aka yi masa iso har cikin shagonsa da yake hutawa a soro, ganin Malam Malmo ya sake tsinka zuciyarsa. Dole ƙanwar na ƙi ya zuba wa fuskarsa murmushin yaƙe cike da girmamawa ya gaishe su. "Umaru ka sani a gaban Mai gari kake don haka muke son duk maganar da muka tambaye ka ta zama gaskiyarka za ka faɗa. Wace ce yarinyar da ka zo da ita kuma a ina ka same ta?" Malam Malmo ya jefa masa tambaya. "Allah ya baka yawan rai wallahi tsintarta muka yi..." "Idan tsintarta kuka yi ina mahaifiyarta? Ko kuna nufin jaririya ɗanyar haihuwa za ta kawo kanta ne?" Mai gari ya katse Umaru. Shiru Umaru ya yi yana tsoron kada ya ba da kai bori ya hau, yana cikin nazari ya tsinci kalaman Malam Malmo. "Sanin kanka ne Umaru duk yankin nan babu wanda ya kai ni sanin sirrin tsafi da sihiri, na bincika kuma na gano waɗansu bayanai tun ranar da na ɗora ƙwayar idona a kan yarinyar nan. A zahiri ne kuke ganinta ƙanƙanuwa amma a baɗini basarakiya ce, shu'uma ce kuma tana ɗauke da rikitattun al'amura. Ita ba kamar kowa ba ce dalilin da ya sa mahafiyarta ta yo gudun fanfalaki da ita kenan daga cikin danginta, mukuma a ɓangarenmu na masu aikin tsubbace-tsubbace wannan yarinyar ta kasance tamkar taki ce da ke farfaɗo da shukar da ke cikin gona. Ya zama wajibi ka mallaka mana ita domin cikar muradinmu, a zahiri Mai gari zai karɓi riƙonta ta koma gidansa da zama. A baɗini kuma zan aiwatar da aikin da za ta kasance a ƙarƙashin ikona. Sharaɗi na biyu ya zama dole ka nuna mini daidai wurin da gawar mahaifiyar yarinyar nan take, idan ba haka ba wallahi sai na shayar da kai ruwan mamaki." Gumin da ya shiga keto wa Umaru ne ya bankaɗa sirrin da ke cikin zuciyarsa, cikin matsanancin tsoro ya ɗago jiki na rawa ya furta. "Duk abin da kuka buƙata haka za a yi ranka shi daɗe, da kai da kaya duka mallakar wuya ne." Malam Malmo ya saki murmushi cikin jin daɗi don ya ga tsoro malale a saman fuskar Umaru don haka ya furta. "Ba zan barka haka ba Umaru dole za mu aiwatar maka da naka tukwici mai tsoka." Umaru ya saki murmushin yaƙe yana godiya, sannan Mai gari ya sallame shi. Kamar zai tashi sama haka ya ƙarasa gidan yana alla-alla ya ɗauko Jawahir ya kai musu ko ya yarda ƙwallon magwaro ya huta da ƙuda. Masarautar Huddam A ranar da aka kai Abubakar ɗakin da ke ɓangaren gidan ajiya da gyaran hali ko runtse Fulani babba ba ta runtse ba, baƙinciki da ɓacin rai ya mamaye zuciyarta. Sai gabannin asuba sannan ta samu hawaye ya zubo mata, zuciyarta cunkushe da ɓacin rai. Wani abu da ya so ɗaure mata kai ganin ta wayi gari lafiya ƙamas babu fitsari a shimfiɗarta, ba ta ankara da haka ba sai da aka kira sallar asuba da za ta yi wanka kamar yadda ta saba duk asuba sai ta wanke fitsarin jikinta. Amma wannan ranar da ta kwana idonta biyu sai ta ga babu komai a jiki, mamaki cike da zuciyarta ta yi alwala bayan ta gabatar da sallah a gurguje ta nufi sashen da Abubakar yake kwance ɗauke da kayan sawar da za ta sake masa kamar yadda ta saba tsaftace shi. "Waye nan?" Aka furta mata cike da tsawa a lokacin da ta ƙarasa jikin babban ƙauren ƙofar. Baƙin ciki ya kama ta jin ƙasƙantaccan bawa na buga mata tsawa, da ace a sashen ta yake babu wanda ya... "Ina magana waye nan?" Kamalan Dogarin suka katse mata tunani. Sai da ta sauke ajiyar zuciya ta furta. "Fulani ce na zo wurin Abubakar." Cikin girmamawa Dogarawan suka zube. "A gafarce mu uwar gijiyarmu, muna neman afuwar saƙon da zai fito daga bakunanmu." Zuciyar Fulani ta fara azalzala kamar za ta hudo ƙirjinta, fargabarta ɗaya kada su ce mata wani abu game da Abubakar. "Allah ya taimake ki, ki yafe mu amma Takawa ya ja kunne da kada a sake buɗe ƙofar nan har sai hantsi ya ɗaga wurin ƙarfe tara." Da sauri ta dube su. "Yaushe ya bada wannan umarnin?" "Ranki shi daɗe jiya da dare." Sai da ta haɗiyi yawu mai ɗaci sannan ta miƙa musu kayan hannunta da akushin abincin da ta taho da shi. "A gyara Abubakar da shi a tabbatar da an yi masa wanka, wannan abincinsa ne." Jim suka yi sannan ɗaya daga cikinsu ya furta. "Allah ya taimake ki koda mun karɓi kayan nan sai lokacin da Takawa ya zartar za mu buɗe ƙofar, amma a gafarce ni ranki shi daɗe." Wani irin kukan takaici ne ya taso mata, gudun kada ta bar abin faɗa ya sa ta juya da sauri ba tare da ta amsa musu ba. Fulani babba na zuwa sashenta ta fashe da matsanancin kuka, tana tsaka da kuka ta ji Khadija mai kimanin shekara goma sha shida ta dafa kafaɗarta. "Ummi me ya sa kullin cikin kuka kike? Ummi kin san idanun masarautar yana ko ina a lungu da saƙo don Allah kada ki bari a samu a bin faɗe, komai ya yi tsanani maganinsa Allah kamar yadda na ji kina faɗa. Wuya ba ta kisa na san a kan Sadiq kike wannan kukan don Allah ki kwantar da hankalinki na tabbata babu abin da zai faru da shi." Khadija yarinya ce mai nutsuwa da sanin ya kamata, idan tana magana kamar babbar mace, a hankali ta goge wa mahaifiyarta hawaye ta ci gaba da tausarta har damuwar da take ciki ta yaye. Haka ta haƙurƙurtar da zuciyarta har lokacin da ya dace, sannan ta ɗauki kayan da kanta ita da Khadija suka nufi wurin Abubakar. Tun tasowar Abubakar ko da wasa Fulani ba ta taɓa yunƙurin ba wa wata baiwa hidimarsa ba, haka ta sawa ranta har zuwar ƙarshen rayuwarta za ta ci gaba da kulawa da shi ba tare da ta sare ba. A lokacin da suka ƙarasa ɗakin duk da kasancar safiya ce ƙudaje ne suka fara yi musu maraba, a kwance suka same shi kamar yadda Fulani ta bar shi da dare sai dai ya fitsari da kasaye duka kayan jikinsa. Ƙudajen da ke kai-kawo a kansa yake ɗaga kai yana cafko duk wanda ya zo hannunsa ya kai bakinsa ya cinye. A fakaice Khadija ta share hawayenta, sannan suka gyara masa jikinsa. Khadija ta kira Baiwa Salamatu ta damƙa mata kayan Abubakar don a wanke su, sannu a hankali Fulani babba take ba shi abinci wani ya karɓa wani ya zubar bayan sun gama suka tashi suka rufo shi suka fito daga sashen zuciyoyinsu babu daɗi. Tsaye take hannunta ɗauke da wata irin sharɓeɓen tsafaffiyar takobin da Boka Bamaguje ya bata don kare kanta da shi, ta hango ƙurar ɗan matashin yaron ya tunkaro ta da bai fi sa'an Muhsin ɗin ta a shekaru ba, duk yadda ta so hana shi shiga cikin ƙofar Masarautar Huddan sai abu ya gagara. Ganin haka ya sa ta zaburo da sauri kafin ta aiwatar da abin da yake ranta ya sa hannuwansa biyu ya mauje ta, ta faɗi ƙasa warwasa. Ɗagowar da za ta yi ta hangi Baiwa Maimuna a bayansa tana sakar mata murmushin mugunta, sai wata inuwa da ta gagara tantance wace ce ita. "Ban yafe miki abin da kika yi mini ba kuma sai na ɗauki fansa a kanki." Rufe bakin Baiwa Maimuna ta sa hannu ta fara jan Fulani Umaina a ƙasa kanta sai kurjewa yake jini na zuba, ko da ta hango Bamaguje yana tsaye a gefe yana kallonsu cikin magiya da tashin hankali ta fara roƙonsa. "Da kai kaɗai na dogara Bamaguje ka taimaka mini za su kashe ni." Wata irin mahaukaciyar dariya ta ga ya bushe da ita, ya juya mata baya ya fara tafiya yana faɗin. "Na riga na gaya miki kin yi sake wannan yaron ba kamar ɗan uwansa yake ba." Firgigit Fulani Umaima ta farka daga mummunan mafarkin da ta yi, a 'yan kwanakin nan ta rasa dalilin waɗannan miyagun mafarkai nata. Kusan kullin sai ta yi mafarkin wannan yaron yana barazana da rayuwarta. "Waye wannan da yake ƙoƙarin kutsowa cikin rayuwata har yake neman dagula lissafina?" Ta tambayi kanta ba tare da ta san amsar tambayarta ba. Ƙirjinta ya buga a lokacin da ta tuna jaririn da baiwa Maimuna ta fitar da shi yana nan a doron ƙasa, "Ƙarya ne ba shi ba ne! Ba zai taɓa razanar da ni ba." Fulani Umaima ta furta tana kai wa da kawowa. *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* *SHU'UMAR MASARAUTA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga ɗaukan tsattsauran mataki don haka a kiyaye. *Masu ƙorafe-ƙorafe ta pc da groups zan rage 100 daga yau zuwa ranar da zan gama free pages. Free pages za su ƙare a page a 10 daga yanzu zuwa ranar duk mai son karanta littafin za ta turo 400* SHAFI NA TARA Ayarin dakarun masarautar da ke tafe da su Baffajo tafe suke cikin gajiya sakamakon doguwar tafiyar da suka yi, a farfajiyar wata bishiya suka yada zango suna hutawa sai bayan sun huta sannan suka ci gaba da tafiya, cikin zuciyarsu kowa da abin da yake ayyanawa. Ganin magriba ta fara dosowa ya sa suka yanke shawarar kwana a cikin dajin washegari da asuba sai su ɗora daga inda suke tsaya. Ƙauyen Gangare Ganin yanayin da Umaru ya koma gida da shi ya sa Mai gado shan jinin jikinta. "Mai gida ya kuka yi da Mai gari na ganka duk a sanyaye." Ƙasa ya yi da murya ya furta. "Ina yarinyar nan take? Zan kai ta gidan Mai gari" Kallon rashin yarda ta bi shi da shi ta sake gyara goyon Jawahir da ke bayanta. "Me za ta yi a gidan." Kamar zai yi kuka Umaru ya ce, "Malam Malmo Mai gado ban san ya za mu yi ba, sun buƙaci na mallaka wa Mai gari ita." Rass! Ta ji gabanta ya faɗi, sai da ta sauke ajiyar zuciya sannan ta yi ƙasa da murya. "Ba zan iya rabuwa da Jawahir ba Mai gida, na san Malam Malmo sarai ba zai wuce tsubace-tsubbace zai yi da ita ba." Umaru ya waiga kamar wanda ake kallo duk a tsorace ya ce. "Ya zamu yi yanzu? Mene ne mafita?" Masarautar Huddam Wuni guda haka Fulani Umaima ta yi shi cikin rashin ƙwarin jiki, ba ta san dalili ba amma haka kawai za ta ji gabanta na faɗuwa. Har ta so dannewa ta ji zuciyarta na azalzala ba za ta iya jure rashin zuwa wurin Bamaguje ba. Tsufansa ya sake fitowa sosai don jiki da hannuwansa har karkarwa suke yi. "Ta zo duniya da ƙarfin iko, shi kuma yana gab da dawowa gidansu na gado." Bamaguje ya furta bayan ya gama sauraron ƙorafin Fulani Umaima. Ta ɗago a hargitse bakinta na rawa, ƙirjinta na dakan lugude. "Su waye? Kuma daga ina suke." "Garaje ga dami, daɗina da ke gaggawa Umaima. Na ɗauka za ki tambayi alaƙar shi da masarauta da ita kanta yarinyar." Ajiyar zuciya ta sauke. "Tamkar tagwaye haka suka kasance tsakaninta da Hidaya, sai dai waccan ruwan sanyi ce salam a kan wannan. Ban san a wanne muhalli zan tirke ta ba, abu ɗaya na sani ita ta kasance daga cikin wata irin zuri'a masu matuƙar hatsarin gaske. Na ga takobi a cikin jininta sannan wuta na gewaye sashenta, takaicina ɗaya Mahaifiyarta ta riga da ta binne duk wani al'amari da sirrin da ke ƙunshe a cikin rayuwarta. Daga ni har sauran matsafan duniya duk wani bincike da za mu yi ba za mu tantance takamaiman ainihin tushenta ba. Sai dai kuskure guda mahaifiyarta ta tafka wanda da shi kaɗai za mu iya cin galaba a kan wannan yarinyar." Cike da zumuɗi Fulani Umaima ta furta. "Mene ne shi? Duk wuya duk tsaninsa zan nemo shi..." "Bincike ya bayyana mini tana da matuƙar tasiri a rayuwarsa. Ina nufin jaririn da kika sa Maimuna ta fitar da shi shekara goma sha ɗaya baya, shi yake gab da shigowa gidan sarautarku. Sai dai kuma ita da shi za su kasance tamkar wuta da ruwa a fannin gaba, kowannensu ba zai ƙaunaci ɗan'uwansa ba. Shigarsa tamkar dasa nakiyar da ke tashin zamani da alƙaryarki ne, ba tun yau ba; na gaya miki shi ba kamar ɗan uwansa ba ne. Ruhinsa ɗauke yake da zaratan dakarun da ke sarrafa zuciya da tunaninsa, tun ranar haihuwarsa na fahimci zanen ƙaddararsa ya wanzu dalilin da ya sa na baki shawarar matse kunamar nan a cikin bakinsa, ashe tagwaye ne halwar tsafina ya gagara nuna mini. Tun yana jariri ya sauka a fadar Sarkin fararen aljanun doron ƙasa, da ke tsakiyar dajin Wuruju a daidai wurin da Baiwa Maimuna ta dire shi. Sun naɗa masa kambun da babu mai iya sauke shi sai mutum ɗaya wato wannan yarinyar." Bamaguje ya ƙarasa maganar yana haska wa Fulani Umaima inuwar wata yarinyar. Ta tsinci muryarsa ya ci gaba da faɗin. "Mu koma maganarmu ta baya na kuskuren da mahaifiyar Fargi ta tafka. Ta bar tauraron 'yarta a sake wanda duk wani matsafi kallo ɗaya ko bincike ɗaya idan ya yi a kanta zai fahimci muhimmancinta gare sa. Duk wanda ya mallaki ruhinta shi zai kasance mafi shahara a faɗin yankin nan a ɓangaren gawurtar tsafi da sihiri, runduna ce guda a tare da ita domin mahaifiyarta kafin ta mutu ta riga da ta juye mata nata jinin a jikinta." "Mene ne mafita, don ta ni gabaɗaya a mutu har liman a rasa mai jan sallah." Cewar Fulani Umaima da zuciyarta ta gama ƙeƙashewa. "A baya na fid da rai da samun wannan ɗaukakar, amma idan kin yadda me zai hana mu jefi tsuntau biyu da dutse ɗaya?" Mai Gado "Guduwa ita ce mafita, sai dai mu bar garin nan amma ka san muddin muna cikin ƙauyen nan Malmo ba zai bar mu da sauran numfashi ba." Shiru ya yi yana tunanin shawarar da ta kawo, ganin ya tsaya yana nazari ya sa Mai gado ta faɗa ɗaki ta ɗaura kayansu a cikin ɗankwali ta fito. "Allah ya sani na ɗauki aniyar kula da yarinyar nan, Malmo azzalumin mutum ne, na san halinsa sarai tun da ya ƙallafa rai a kan yarinyar nan ko mun damƙa musu ita sai sun hallaka mu don gudun tonuwar asirinsu." Mai gado ta faɗa tana miƙa wa Umaru ƙullin kayansu, sai da ya karɓa sannan ya furta. "Na gode wa Allah ya sa kika fahimtar da ni da tuni na sa mun yi tsalle mun afka cikin rijiya gaba dubu. Yanzu dai babu sauran lokaci mu bi ta ƙofar baya." Cikin sauri Mai gado da Umaru suka hankaɗe katangar karan da ke gewaye da gidan, kamar masu shirin tashi sama haka suka dinga sauri suna kutsawa ta ciki bishiyu duk da a lokacin magriba ta kawo kai. Sai da suka yi tafiya mai nisan gaske sannan suka ƙarasa wani ƙaramin gari a lokacin dare ya tsala sosai babu haske sai na farin wata, a gajiye suka zube a gefen ganuwar garin suna sauke ajiyar zuciya. Cike da galabaita Jawahir ta fara mutsu-mutsu sai a lokacin suka shiga damuwar abin da za su sama mata ta sha. Gorar ruwa Mai gado ta kunto ta ba ta sannan suka yi jigum-jigum, har sun zauna da sunan hutawa Umaru ya furta. "Mai gado an ya wurin nan yana da kyau kuwa? Me zai hana mu ƙarasa cikin garin nan mu nemi alfarma?" Mai gado ta yi murmushin takaici, "Duk in da za mu je matuƙar za su fahimci ba na shayar da yarinyar nan dole za su harbo jirginmu, kuma su ɗora mana zargi da tambayoyi a kanmu. Abin da muke gudu kuma ya faru ka ga an ƙi cin biri an ci dila." Umaru ya yi jum sannan ya furta. "Ina ganin mu ƙarasa bakin kasuwa mu kwana asubar fari sai mu bar garin, mu ɗora daga inda muka tsaya." Ta gamsu da shawararsa don haka suka yi gaba suna tambayar kasuwar garin har Allah ya datar da su, suna gab da shiga kasuwa suka ga wata mai fura da nono suka siya nono sannan suka ƙarasa. A bayan rumfunan kasuwar suka yada zango bayan sun take wa Jawahir cikinta da nono, babu jimawa baccin gajiya mai nauyi ya yi awon gaba da su. Sanyin asuba ne ya bige su suka farka don haka kamar marasa gaskiya suka sake nufar doguwar hanyar suka ci gaba da tafiya. Ba su yi tafiya mai nisa ba suka tsaya suka gabatar da sallah sannan suka ɗora daga inda suka tsaya. Sai da suka yi tafiya mai nisan gaske sannan suka tarad da wani ayarin mutane, yara, manya, maza da mata. Sai kuma Dogarawan da ke kai kawo a kansu, kallo ɗaya Umaru ya yi musu ya fahimci bayi ne aka kama. Da yake suna ɗan nesa da su da sauri Umaru ya ja hannun Mai gado ya furta, "Maza zo mu gudu idan Dogaran nan suka gan mu na tabbata kashinmu ya bushe don mun zama Bayi na har abada." Yana rufe baki suka juya da sauri. Cak! Suka tsaya cikin faɗuwar gaba, Mai gado ta riƙo hannun Umaru jiki na karkarwa. "Gidan uban wa za ku gudu?" Kalaman Sojan masarautar mai ƙirar samudawa ya ratsa su, gabaɗayansu aka rasa mai bakin magana. Ganin haka ya sa Dogarin tsula wa Umaru bulala a baya, cikin azaba ya hau susar baya yana faɗin. "Tuba nake ranka shi daɗe ba guduwa za mu yi don Allah ku yi mana rai." Da hannu Dogarin ya nuna musu hanyar da sauran mutanen da ke zaune a ƙasa suke, babu musu Mai gado da Umaru suka bi hanyar ba tare da sun furta komai ba. Tun da suka tunkari wurin mutanen wurin suka zuba musu na mujiya suna kallonsu. Bai san dalili ba haka kawai yake jin ƙirjinsa na bugawa, zuciyarsa kamar za ta yi tsalle ta hudo ƙirjinsa. Duk taku ɗaya da Mai gado take yi tana kusanto shi ji yake kamar ana ɗana wa zuciyarsa ruwan dalma, da wata irin ƙuda da wani surutai da ya gagare tantance harafi ɗaya ballantana ya yi wa kalaman nasu hisabi. Da yake hannunwansa biyu a ɗaure suke a jikin itace, kansa ya tura cikin ƙafafuwansa yana runtse ido. Bai yi aune ba ya fara jin sautin kukanta a tsakar kansa, yana yunƙurin buɗe idonsa kamar a mafarki ya ji an furta. "Ita daban ce don haka ta fito daga cikin wani irin ahali, tarayyarku alheri ce mai samar da taimakon juna a koyaushe. Sai dai zuciyoyinku za su gagara ba ku haɗin kan da za ku cimma manufarku ta alheri. " Firgigit ya ɗago kansa cikin mamaki, ba yau ce rana ta farko da ya fara jin waɗansu irin surutai a kansa ba. Amma na yau sun matuƙar dagula lissafinsa. "Wace ce ita?" Ya furta a fili. A daidai lokacin aka kama Umaru aka ɗaure ita kuma Mai gado aka kama ƙafarta ɗaya aka ɗaure, ta ci albarkacin jaririyar da ke bayanta. "Idan muka kama hanya a yanzu babu wani sauran hutu da za mu ƙara yi a hanya, domin mun kusa shiga cikin ƙasar Zazzau." Wani turɓunannan mutum ya furta fuskarsa a murtuke babu fara'a. A galabaice cikin yunwa, ƙishirwa da wahalar tafiya suka ɗauki hanyar da za ta sada su da ƙasar Huddam. Sai da suka yi tafiya ta kusan sa'o'i shida sannan suka ƙarasa cikin masarautar ta Huddam. A lokacin da suka je daidai ƙofar shiga Jawahir da ke a bayan Mai gado ta fara wata irin jijjiga idanuwanta suka fara yunƙurin kakkafewa, cike da tashin hankali Mai gado ta sauko ta, ganin halin da take ciki ya sa ta ƙwallah kururuwa cikin neman agaji. Da sauri Dogaran da ke wurin suka buga mata tsawa. "Hattara dai muna gab da shiga masarauta..." Ganin Jawahir na ci gaba da shiɗewa ga wani irin jini da ke tsiyaya daga hanci da kunnenta ya sa Mai gado ta furta. "Ku taimaka mini ɗiyata za ta mutu." A fusace wani Dogari ya ƙarasa da niyyar zubga mata bulalar da ke hannunsa, gannin halin da Jawahir ke ciki ya sanyaya jikinsa, yana shirin yayyafa mata ruwa suka ji gijif alamun faɗuwar abu. Suna waigawa suka hangi Kamalu ya faɗi ƙafarsa ɗaya na jijjiga, daga ƙugunsa zuwa tafin ƙafarsa take ya sauya launi zuwa jawur, jini ya fara zuba daga cikin kunnuwansa. Ganin haka ya sa Dogarawan suka sa aka ɗauke shi aka shiga da shi ciki, jiki a sanyaye Mai gado ta rufa musu baya hannunta rungume da Jawahir da har lokacin ba ta daina kakkafewa ba. Fulani Umaima Da yanayin damuwa ta dube shi, "Ban fahimci kalamanka ba Bamaguje." Bamaguje ya tattara nutsuwarsa wuri ɗaya ya furta. "A lokacin da nake ƙarami burin mahaifina kenan ya mallaki ruhin wannan yarinyar, sai dai kash binciken farko da ya yi ya bayyana masa lokacin da yarinyar za ta zo duniya ba ya raye. Ni kaina na yi tsammanin a farkon rayuwata za ta wanzu, amma sai ga shi sai da tsufa ya make gangar jikina. Ina son ko ba yanzu ba idan kun haɗu da yarinyar nan ki ribace ta har zuwa wannan tsibirin nawa. Domin ba za mu iya kamata da alƙaluman tsafi da sihiri ba, idan kika yi haka tamkar kin kawo ƙarshen rayuwar yaron da kika sa aka fitar da shi daga cikin masarautar ne. Wannan kaɗai za ki aiwatar mini sauran bayanan zan yi miki su daga baya." Fuska ɗauke da damuwa ta furta. "Ban santa ba ban taɓa ganinta ba ta yaya kake tunanin zan gane ta har na ribace ta na kawo maka ita?" Murmushi Bamaguje ya yi ya furta. "Daga shi har ita ba su kasance kamar kowa ba, kuma shigarsu cikin masarautarku zai ƙara tayar da rikitattun al'amuran da ke cikinta. Masarautarku shu'umar masarauta ce da ke raye a ƙarƙashin ikon waɗansu ɓoyayyun hallitu. Ko ban faɗa miki ba shurin da ke cikin turakar Takawa akwai dalilin wanzuwarsa, tun da kin san banza ba ta kai zomo kasuwa. Zan sake bincike game da wasu al'amuran ko za mu da ce a wannan karon." Bamaguje yana rufe baki ya watsa wani baƙin jini a cikin wata tukunyar ƙasa take wuta ta fara ci gangan-ganga, shiru ya yi yana nazartar abin da yake faruwa zuwa can ya saki wata irin dariya. Shiru Fulani Umaima ta yi tana kallonsa cike da ƙosawa. "Wani abin farinciki da ban za ta ba, kusan gabaɗayansu ruhinsu na da kusanci da juna..." Kalamasa suka katse sakamakon ganin wutar gabansa ta ɗauke yo kansa kamar za ta ƙone shi sai kuna ta ɗauke ɗif, bai so haka ba amma ko babu komai ya tsinci waɗansu abubuwa da za su ba shi narasa a game da yarinyar. "Ki sa ido sosai a wurin da kika binne jariran da kika taɓa binnewa a bayan ɗakin Sarki Abdul'aziz. Matuƙar kika ga an tone ta ba kowa ba ne face jininsa, ina nufin jininsa da kika fitar da shi. Idan har kika ga kan tinkiyar da kika rataye a ɗakinki wanda a kullin jini yake ɗiga a kan zanin kishiyarki ya fara tsutsa ta tabbata gabaɗaya su biyun suna da kusanci da ke, wato suna rayuwa a cikin masarutarku. Idan ba ki manta binciken da na yi miki a baya na gaya miki akwai wanzuwar rayuwar waɗansu ruhi masu ɗauke da rikitattun al'amura a cikin masarautarku waɗanda suke yunƙurin shiga al'amuran masarautarku. Lokacin ganawata da sarkin baƙaƙen aljanin ƙarƙashin ƙasa ya yi, zan ba shi aikin matar wani attajiri akan kishiyarta, ki ba ni wuri sai wani lokacin idan kin sake dawowa." Fulani Umaima guntun tsaki ta saki cike da takaici, ta yi masa bankwana ta koma ɗakinta. Lokacin da aka shigar da su Baffajo sashen Bayi aka wuce da su, kusan gabaɗaya jikinsu a sanyaye yake sakamakon ganin halin da Kamalu da Jawahir suke ciki don a tsammanin mutane da yawa mutuwa za su yi. A hankali Kamalu ya fara buɗe idanuwansa yana ganin mutane dishi-dishi, ajiyar zuciya ya sauke ya yunƙura da ƙyar; da sauri Baffajo ya ɗago shi yana zubda ƙwallah. Mutanen da ke wurin suke bi su da kallo cike da mamaki, Inna wuro ta share ƙwallah tana faɗin, "Na faɗa maka Kamalu ba zai mutu ba." Baffajo ya jinjina kai yana tallafo haɓarsa, "Amma har yanzu jikina yana ba ni za su iya halaka mini shi, wataƙila ba za su bar mana shi ba." Kamalu da ke zaune bai tanka musu komai ba sakamakon wata irin juwa da ke ɗibansa, waani dattijo tsoho ya gani a gabansa ya sakar masa murmushi tare da faɗin. "Muna ta ya ka murnar dawowa cikin ahalinka, ka tashi ka ƙarasa bakin rafin can ka ɗebi ruwan cikinsa ka ɗura a kunnenka, ka damƙi ƙasar cikinsa za mu yi maka iso har bayan turakar Mai martaba yanzu, aikin da za ka zartar sai kai domin abin salsala yake bi." Kamar wanda aka ƙara wa ƙarfi haka Kamalu ya miƙe daƙau, Dattijon ya kama hannunsa ya fara tafiya Baffajo da Inna wuro suna ƙwala masa kira, ko waiwayensu bai yi ballantana su saka ran zai tanka musu. *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* *SHU'UMAR MASARAUTA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* *Masu ƙorafe-ƙorafe ta pc da groups zan rage 100 daga yau zuwa ranar da zan gama free pages. Free pages za su ƙare a page a 10 daga yanzu zuwa ranar duk mai son karanta littafin za ta turo 400* LAST FREE PAGES SHAFI NA GOMA *🤔WAI NA CE KINA DA WAƊANNAN MATSALOLIN AMMA KIKE ZAUNE DA TARUN TUNANI FAL KWANYA?* *MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE* *SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?* *TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI'IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHEƘI KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI* *SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA'A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA'IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA'IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA* *Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.* 👉 *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.* *1. Supplements na gyaran jiki ciki da waje* *2. Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba* *3. Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya* *4. Supplements na karawa fata kyau da sheki glowing skin* *5. Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci* *6. Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki* *7. Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu* *8. Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.* *9. Supplements na karin ni'ima da dandano da tightening ciki da waje* *10. Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc* *11. Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement* *12. Supplements na gyaran HQ ciki da waje* *13. Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton* *14. Supplement na whitening/glowing skin* *15. Supplement for Acne, dark spots remover* *Da duk wasu nau'in supplement da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158* Ba iya su Baffajo ba hatta sauran Bayin da ke wurin sai da suka rufa musu baya, sakamakon ganin wurin da Kamalu yake ƙoƙarin kai kansa. A tarihin masarautar babban kuskure zuwa rafin tsamiya da doshin magriba, hasali ma a ranar juma'a akwai abubuwa biyu da suka haramta ga mazauna cikin masarautar. Na farko, duk ranar juma'a haramun ne shan nonon shanu, awaki ko na raƙumi. Duk wanda ya yi gangancin karya wannan ƙa'idar kuma zai iya tsintar talatarsa a laraba, domin a labarin da yake yawo a cikin masarautar an ce shekara sama da ɗari an taɓa samun turka-turka tsakanin Sarkin da ke mulki da Bafulatanar Aljana kafin daga baya aka sasanta, amma wannan labarin kusan na kunne ya girmi kaka ne don babu wanda kai tsaye zai ce maka ga daga wurin wanda ainihin labarin ya fito. Shi kuma wannan rafin ana kiransa da rafin tsamiya sakamakon wata narkekiyar bishiyar tsamiya da ke girke a tsakiyar rafin, shi wannan rafin yana daga can gefen sashen bayi kuma rafi ne mai hatsarin gaske. Ba a taɓa ganin ya ci mutum ba, sai dai duk wanda ya yi gangancin shiga cikinsa ranar juma'a, zai fito lafiya ƙalau daga cikinsa amma a ranar za a neme shi sama ko ƙasa a rasa. Wasu daga cikin mutanen gidan masarautar sun ce faɗan Bafulatana ne ya shafi rafin yayin da wasu suka ce alƙwarin babban sarkin Aljanin ruwa ne yake cika dalilin wata yarjejeniya da ke tsakaninsa da Sarki Muhammad Safwan wato Kakan Sarki Abdul'aziz na uku. Sarki Muhammad Safwan ya yi mulki kafin hawan Sarki Abdul'aziz da shekara ɗari da biyar, har zuwa wannan lokacin babu tsayayyiyar wannan magana. Sai dai duk mazaunin cikin masarauta ya kwana da sanin masarautarsu ta sha bambam da sauran masarautun da ke wannan nahiyar musamman a kan al'amura masu rikitarwa da ban mamaki. Da sauri Baffajo ya sha gaban Kamalu cike da damuwa ya furta, "Kamalu hai ina za ka je ne, can ba ka ganin kududdufi ne?" Tsohon da ke riƙe da hannun Kamalu ya sakar masa murmushi haɗe da faɗin. "Tabbas sun kasance iyaye masu baka kulawa amma ka sani dakatarwarsu tamkar komawar cigabanka baya ne." Jin Kamalu ya yi shiru ya sa Inna wuro ta furta, "Kamalu ko wani abu yana damunka ne?" Girgiza kansa ya yi ya furta, "Inna wani ne ya ce na je cikin ƙoramar can." Ras! Gaban Inna wuro ya faɗi, tana shirin yin magana daga bayansu suka ji an furta. "Tun wuri ku kama ɗanku idan ba haka ba wallahi matuƙar ya shiga cikin wancan rafin a yau sai dai nan gaba ki haifi wani." Uwar Bayi ta yi maganar cikin halin ko-in-kula. Take jikinsu ya ɗauki karkarwa, Kamalu na kai dubansa wurin tsohon ya ga ya tsuke fuska rai a ɓace ya furta. "Kai ba kamar kowa ba ne, jininka yana da bambamci da nasu don haka ba koma ne za ka riƙa bankaɗa musu sirrinka ba." Yana gama faɗar haka ya ɓace masa. A lokacin tuni Baffajo sun riƙe hannuwansa bibbiyu sun koma da shi cike da tsoro. Komawarsa babu jimawa Jawahir ta farfaɗo tana yin wata irin shaƙuwa mai ƙarfi, duk wanda yake wurin sai da jikinsa ya yi sanyi ganin halin da ƙanƙanuwar yarinya take ciki. A hankali take sauke numfashi, Mai gado ta sa ruwa da ɗankwalin kanta ta goge mata jinin fuskarta. Buɗe baki ta fara yi alamar tana buƙatar abinci, a nan ne kuma hankalin mai yankan kaba ya koma ga rina domin Mai gado ta manta sam da batun nonon da za ta bai wa Jawahir. Cikin damuwa ta kalli wata Dattijuwa. "Baba don Allah ku taimaka mini ko da nonon akuya ne yarinyar nan shi nake bata." Kusan lokaci ɗaya suka kalli juna a firgice, Uwar soro ta ce. "Baiwar Allah sai dai kam ki bata wani abin ba nono ba domin yau juma'a kuma duk ranar juma'a ba a shan nono a gidan duk wanda ya sha ya dinga aman nono har a zare ransa." Mai gado na jin haka ta rushe da kuka, don ɗan kwanakin da ta yi da Jawahir ta shiga ranta sosai. "To ke me ya sa bakya ba ta nono?" Mai soron baƙi ta sake wurga mata tambaya." Mai gado har za ta fallasa alaƙar da ke tsakaninsu da Jawahir sai kuma ta tuna da kalaman mahaifiyarta a lokacin da ta haife ta. "Tun lokacin da na haife ta babu ruwan nono a jikina, kafin zuwanmu nan har magani mun nema amma a banza kare ya sha tsamiya." Waɗannan kalaman na Mai gado suka ƙara dasa tausayin Jawahir a zuciyoyin mutanen da ke wurin, "Bakin da Allah ya tsaga na tabbata ba zai hana shi abinci ba, akwai baiwa Zinaru da ke shayarwa mai zai hana a roƙi alfarmar yau ɗaya ta shayar da ita?" Uwar tuwo ta furta. Zuciyar Mai gado ta yi ƙal ta ƙarasa wurin Baiwa Zinaru da ke goyon ɗanta mai kimanin shekara guda. Take Zinaru ta amsa ba ta musa ba, sai dai tana ɗaukar Jawahir ɗanta da ke gefenta ya ƙanƙame mahaifiyarsa yana tsanyare wa da matsanancin kuka haɗe da cusa kansa cikin jikin mahaifiyarsa. A lokacin babu wanda ya kawo komai a ransa don a tunaninsu ma kishine irin na yara yake yi don ya ga an ɗauki wata yarinyar, kai tsaye Zinaru ta rungume Jawahir ta fara shayar da ita, wani irin zuuu! Zinaru ta ji tamkar wacce aka kafa wa shocking har tsakiyar kanta. Ga wata irin zuƙa da take ji Jawahir na yi kamar za ta fige maman jikinta, suna nan tsaitsaye ruwan nono ya fara dawo wa Jawahir ta hanci da kunnuwanta. Wannan yanayin da ta shiga ya sake faɗar da gaban mutanen wurin, cikin masifa Jakadiya ta fara magana. "Wannan wacce irin masifa aka kawo mana saboda Allah, yarinyar tun da aka kawo ku sai faɗar mana da gaba kike yi." Mai gado jiki a sabule ta karɓi Jawahir ta fita zuwa bakin wata bishiya ta zauna cikin sarewa ta fara zubar da ƙwallah. Jawahir ta jima a haka sannan nonon da ke fita daga jikinta ya dakata da zuba, ba ta yi ƙasa a gwiwa ba ta sake goge mata haɗe da saka ta a baya ta goya ta. A ranar kusan kwanan zaune mai gado ta yi cike da rashin sabo da zaman baƙunta, uwa-uba rashin kyakkayawan makwancin saɓanin wanda suka saɓa kwana a ciki. Cikin Dare. Wata doguwar hanyar ya bi samɓal yana tafiya wacce babu komai sai dogayan bishiyu, tsawo da girmansu ya haddasa wa wurin duhu mai ban tsoro. Daga bayansa ya ji kamar ana bibiyarsa don haka ya yi saurin waigawa cikin tsoro da tashin hankali, wata baƙar mage mai ratsin fari ya gani tana tafe tana shinshina sawunsa. Tun bai yi wayo ba yake ƙaunar kyanwa don haka ya tsugunna da niyyar kai hannu kanta, da sauri ya ji an fisge shi gefe waɗansu surutai na tashi sama-sama a cikin kunnuwansa. Waigawa ya yi bai sake ganinta ba, ya ci gaba da tafiya. A jikin wata murgujejiyar bishiyar kuka ya hangi wata rantsatstsiyar karaga, "Je ka ƙarasa kan karagarka." Ya ji an furta masa. Wani irin sanyi ya ji yana ratsa shi, jiki a sanyaye ya fara takawa da niyyar hawa kan shimfiɗar da ke ɗauke da karagar, ga mamakinsa sai ji ya yi wannan baƙar magen ta hankaɗa shi gefe ɗaya. Ta ɗora wani mulmulallan abu mai kama da ƙawai a kan karagar, sannan ta fara zagaye karagar cikin ƙasaita. A can ƙasa ya faɗi kansa ya bugu da wani farin dutse take jini ya fara ɗiga, dafa wurin ya yi cikin azaba sai gani ya yi magen ta ƙaraso tana lasar jinin da ke zuba daga goshinsa. Ta fara ɗaga kanta tana da alamar tana son kai wa kansa farmaki wurin da ragowar jinin yake ɗiga. Ganin ta dumfaro shi ya sa ya ci gaba da ja baya zuciyarsa na dakan luguje, ganin haka ya sa magen ta fara wata irin dariya fiƙoƙinta na zubowa ƙasa ɗaya bayan ɗaya. Duk wurin da fiƙar ta faɗa sai ƙasar wurin ta rufta har ta yi tsalle za ta damƙi saman goshinsa. Firgigit Kamalu ya tashi cikin matsanancin tsoro, firgici da tashin hankali. A lokacin dare ya tsala sosai, ban da munsharin mutanen ɗakin da kukan tsuntsaye babu abin da yake tashi. Jin abu na gangaro masa a goshi ya sa ya kai hannunsa ga mamakinsa ya ji ya taɓa abu, da sauri ya yunƙura zuwa wurin aci-balbal ɗin da ke kunne a gefen ɗakin ya haske. Rass! Gabansa ya faɗi, jikinsa ya ɗauki karkarwa kamar mazari. "Jini!" Ya furta a kiɗime. Yana shirin komawa ya tashi Baffajo ya sanar da shi abin da faru ya ji an dafa kafaɗarsa. "Wannan gidan ba irin kowanne gida ba ne, sai ka ɗaura ɗamarar juriya da jajircewa. Gadon gidanku ba a sansu da sarewa ba, ka zama jarumi mara tsoro a haka ne za ka ƙwaci kanka. Ka gode wa Allah da ba ta yi nasarar yagar naman jikinka ba, kuma kada ka ɗauka za ta haƙuri. Wannan daɗɗaɗiyar mummunar manufa ca tunkafin haihuwarka, zan yi takaici ƙwarai matuƙar ta yi nasara a kanka kamar yadda ta ci galaba a kan mahaifiyar..." Sam Kamalu baya fahimtar kalaman da farin dattijon ke gaya masa, cike da damuwa ya katse shi. "Don Allah wane ne kai? Ya aka yi ka san mafarkin da na yi?" Murmushi Dattijon ya yi, "Yaro man kaza! Da sannu za ka fahimci turbar da nake son ɗora ka, izza da ƙasaitar jinin Sarki Muhammad Safwan ba za ta tashi a banza ba. Ba ni zan bayyana wa duniya waye kai ba, izza da tasirin jinin sarautar da ke jikinka ne zai bayyana wane ne kai. Ni Aminin Kakankakanka ne, ina bibiyar al'amarinka saboda waɗansu muhimman abubuwa da tasirinsu. Ta so mu je ka wanke ciwonka a wancan rafin, idan gari ya waye kada ka sanar da kowa mummunan mafarkinka hatta Baffajo da Inna wuro, domin wannan gidan sarautar cike yake da idanu mabanbanta." Tamkar raƙumi da akaɗa haka Kamalu ya bi bayan tsohon yana gaba shi kuma yana biye da shi, lokacin da suka ƙarasa bakin rafin wani irin sanyi ne ya fara ratsa shi har sai da jikinsa ya ɗauki rawar ɗari. Kaf kaf kaf haƙoransa suka fara rawa, ga wata irin juwa da take ƙoƙarin fisgar shi ko ta halin ƙaƙa, ɗagowa ya yi a wahalce ya furta. "Ba zan iya ba, ba zan iya zuwa ba sanyi nake ji." Rufe bakin Kamalu sai dajjijon ya sa hannunsa a tsakiyar goshinsa, a hankali ya ji sanyin da yake ji yana raguwa, "Ba na jin daɗi a duk lokacin da ga karaya a ƙwayar idonka, daga yau kada na sake jin ka furta kalmar gazawa. Tabbas za ka iya domin duk tsawon lokacin da muka ɗauka lokacinka muke jira, mu je ka aiwatar da abin da yake gabanka." Dattijon ya faɗa yana kama hannun Kamalu ya sanya ƙafarsa ta dama a cikin rafin, wani irin zuuu! Ya ji har cikin kwanyarsa. Gabansa na faɗuwa ya tsugunna a ɗebi ruwan ya wanke ciwonsa kamar yadda tsohon yake ba shi umarni, yana gamawa ya sake ba shi umarnin wanke fuskarsa ya ɗura masa ruwan a cikin kunnuwansa. Ruwan ya gani ya fara kaɗawa a hankali, daga baya kuma ya ga igiyar ruwan tana katantanwa da su. Yana shirin guduwa tsohon ya riƙe shi tsam a jikinsa, ganin a kowanne lokaci yana iya halaka ya sa Kamalu runtse idonsa. Sannu a hankali ya ji komai yana lafawa, hakan ya sa shi buɗe idonsa suka fara takowa suka fito daga ciki. Wani irin sauti yake ji cikin sigar kururuwa da neman ɗauki, lokaci ɗaya ya ji zuciyarsa na fisgar gangar jikinsa. Tafiya yake yi ba tare da ya san wurin da yake jefa ƙafafuwansa ba har ya zagaya wurin da yake jin ƙarajin sautin na kusantarsa a bayan ɗakin Mai martaba. A saitin kusurwar yamma ya hangi wani mulmulallan abu baƙi saboda duhu bai tantance takamaiman mene ne ba. Cikin dakiya da ƙarfin zucuya ya sa ka hannu da niyyar tonowa take zoben hannunsa ya mamaye wurin da haske, a nan ya yi tozali da wani abu mai tsananin wari da siffar jarirai har sai da ya ji tamkar ya amayar da kayan cikinsa. Tsaki ya yi cike da jin haushin abin da ya aikata, shi kansa bai san dalilin da ya sa shi aikata haka ba, ya dai ji ba za iya haƙura ba har sai ya taimaki abin da yake cikin ƙarƙashin ƙasar. Koda ya koma sama da ƙasa ya nemi Dattijon ya rasa, a bakin ƙofar ɗakinsu ya hangi Baffajo yana kai wa da kawowa yana ganin Kamalu ya ƙarasa yana tambayarsa inda ya je. "Baffajo fitsari ne ya tashe ni, na ga kana bacci shi ya sa ban tashe ka ba." Ya tsinci kansa da ƙin faɗa wa Baffajo gaskiyar abin da ya faru. Riƙo hannunsa Baffajo ya yi tsam kamar wani zai ƙwace shi suka ƙarasa cikin ɗakin, ƙwallah ce ta ciko idanun Baffajo ya furta. "A wannan farautar da aka yi mana mun rasa Salele Kamalu yanzu haka ban san duniyar da ya nufa ba, don Allah kada ka yi yunƙurin abin da zai raba ni da kai, ka ga wancan rafin dai an ce hallaka mutane yake don Allah koda wasa kada na ga gilmawarka a wurin." Kamalu ya jinjina kai sannan ya koma ya kwanta cike da tausayin mahaifinsa. Tun da asubar fari aka tashi duka Bayin da ke sashen kamar yadda aka sunnanta musu, bayan sun idar da sallar asuba Uwar Bayi ta shiga raba wa sababbin Bayi aikin da za su gudanar, waɗanda suka san aikinsu kuwa suka ci gaba ɗorawa daga inda suka tsaya. Sai da rana ta fara fitowa sannan suka samu zarafin kai abinci cikin bakunansu, Mai gado ita da Inna wuro kusan ɗura suka yi wa kansu da sauran baƙin Bayin da aka kawo su rana ɗaya. Baiwa Fatsim na ganin yadda suke cin abinci ta saki shewa tana yi musu kallon sheƙeƙe ta furta. "Ahayye! Allah na dawo inji kishiyar mai yaji, duk wannan feleƙen da kuke yi gumi ce ba ta yi gumi ba. Amma da sannu za ku gane karatuna." Gabaɗaya babu wanda ya tanka musu, wata Dattijuwa da suka ji ana jira da Uwar tuwo ta ƙarasa wurin ta ce, "Tun wuri ku cire kawaici da kara ku fara ƙwatar wa kanku 'yanci idan ba haka ba kowa takaku zai yi kamar takalmin sawarsa. Wannan gidan yana da matuƙar bambamci da wuraren da kuka fito..." Sallamar Jakadiya ta katse ta, fuska a haɗe ta dube su ɗaya bayan ɗaya. "Zan ɗebi sababbin Bayi gabaɗayanku zan kai ku sashen Fulani Umaima tana son zaɓar waɗanda suka yi mata domin tana buƙatar ƙarin masu yi mata hidima." Jin babu wanda ya tanka mata ya sa ta buga musu tsawa, jiki na rawa duka suka miƙe sai Inna wuro da ke faman jera loma da sauri don ita idan tana cin abinci tana tashi duk daɗin abinci ba ta iya cinsa, ballantana a nan da abincin dare da suka ci ko kaɗan bai ishe su. Jakadiya ta leƙa ganin Inna wuro na zaune. "Ke ce shafaffiya da mai ba ki ji abin da na ce ba?" Baki na rawa Inna wuro ta sanar da ita uzurinta, ai kuwa lokaci ɗaya ta ji an kwashe mata da dariya. "Ke a tsammaninki tun da kika shigo masarautar nan kina da sauran ikon da kanki? Ko kin manta matsayinki na Baiwa ne? Idan ba ki sani ba ki sani a yadda kika a cikin gidan nan sai yadda aka yi da ke, idan aka so ki kwana a tsaye dole ki kwana, gara tun wuri ki yakicewa kanki ɗan guntun 'yancin da kike taƙama da shi." A sanyaye Inna wuro ta tashi, idanunta suka ciko da ƙwalla. A duniya babu abin da ta tsana sama da yarfi da tozartawa. Babu yadda suka iya haka suka bi bayan Jakadiya haka kawai Mai gado ta tsinci gabanta na matsanancin faɗuwa, tun da suka nufi sashen Fulani Umaima Jawahir ke wani irin mutsu-mutsu har zuwa lokacin da Jakadiya ta sa suka jeru ɗaya bayan ɗaya. A hankali ta fara bin Bayin tana duba su a wulaƙance cikin yarfi da ƙasƙantarwa. Tana zuwa daidai kan Mai gado gabanta ya yanke ya faɗi, ta dube ta a yamutse. "A sauko da wannan jaririyar." Ba musu Mai gado ta kunto Jawahir da jikinta ya yi wani irin sanyi kamar wacce aka ciro daga ƙanƙara. Sauke idanun Fulani Umaima a kan ƙwayar idon Jawahir ya haddasa mata matsananciyar faɗuwar gaba, kalaman Bamaguje suka faɗo mata. Ba ta sake tsinkewa da lamarin ba sai da ta yi tozali da goshinta. 😁😁 Yanzu ne za a fara buga wasan, Shin me yake shirin faruwa tsakanin Fulani Umaima da Jawahir. Wai ma wace ce Jawahir ɗin nan kuma mutum ce ko Aljan? Ina Dattijon nan kuma me ye alaƙarsa da Shu'umar Masarauta, wai ma me ye silar wannan abubuwan da ke faruwa? Akwai ɓoyayyan sirri mai ƙarfi da Dattijon nan ya sani mai ya sa bai aiwatar da komai ba sai da Kamalu ya zo. Wai shin Bayin Masarautar da shi Kansa Sarki Abdul'aziz za su gane shi ɗin jinin masarauta ne? Idan Fulani Umaima ta fahimta me kuke tunanin za ta aiwatar? Ina labarin Abubakar zai warke a nan gaba ko a'a?😢 Fulani babba tana warkewa daga cutar fitsari ko bata warkewa? Maza hanzarta kada ki bari a yi babu ke, salon labarin daban yake. Namu ba irin nasu ba ne💃🏼💃🏼💃🏼 na san ba ku manta da BAƘAR DAULA ko AN YA BAIWA CE da ZAUJATU JINNUL-ASHIQ ba. Kar ki bari a yi babu ke wannan kafcan.🥳🥳🥳💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼 *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* 11 *🤔WAI NA CE KINA DA WAƊANNAN MATSALOLIN AMMA KIKE ZAUNE DA TARUN TUNANI FAL KWANYA?* *MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE* *SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?* *TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI'IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHEƘI KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI* *SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA'A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA'IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA'IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA* *Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.* 👉 *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.* *1. Supplements na gyaran jiki ciki da waje* *2. Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba* *3. Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya* *4. Supplements na karawa fata kyau da sheki glowing skin* *5. Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci* *6. Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki* *7. Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu* *8. Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.* *9. Supplements na karin ni'ima da dandano da tightening ciki da waje* *10. Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc* *11. Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement* *12. Supplements na gyaran HQ ciki da waje* *13. Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton* *14. Supplement na whitening/glowing skin* *15. Supplement for Acne, dark spots remover* *Da duk wasu nau'in supplement da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158* A yamutse Fulani Umaima take kallon Jawahir da goshinta ya tsattsafo da jini, ƙwayar idonta ta kaɗa jawur. Daga ɗan gaban Mai gado wata matashiyar baiwa da ba ta wuce shekara goma ba ta fara yin haɓo sakamakon daɗewar da suka yi a rana da kuma ɗaukan kayan da suka yi a safiyar ranar. Fulani Umaima ta kai dubanta wurin da yarinyar take zuciyarta na wasu-wasin ko dai yarinyar da Bamaguje ke magana ta iso cikin masarautar. "Me ye wannan a goshinta?" Fulani Umaima ta tambaya fuska a haɗe. Da yake Mai gado tana tsoron bayyanar wani abu daga wurin Jawahir sai ta furta. "A gafarce ni ranki shi daɗe kafin fitowarmu ne ina gaggawa na bige ta da garu har goshinta ya fashe." Taɓe baki ta yi a wulaƙance ta wuce har ta isa wurin yarinyar da ke haɓo, saboda yadda kowa yake tsoron ɓata ran Fulani Umaima suna ganin jini na zuba babu wanda ya iya taimaka mata har ta gama zagayen su, tana daga gefe ta nuna Inna wuro da wata baiwa ta furta. "Jakadiya akai waɗannan sashena za su ci gaba da yi mini hidima, a tabbatar da an ba su horo don ba na buƙatar rashin sanin yakamata." Ko kaɗan Inna wuro ba ta so haka ba domin a yanayin yadda ta fahimci Fulani Umaima sam ba za ta yi sauƙin hali da daɗin mu'amala ba. Kamar ta san abin da yake ran Inna wuro ta sake duban Jakadiya. "A sanar da su ƙa'idoji da tsarina tun kafin su fara aiki gobe, ba na buƙatar gidadanci a sashena." Tana gama maganar ta fice fuuu daga wurin, kamar 'yan matan amarya haka suka sake rankayawa suka koma can sashensu na Bayi. Wani irin bacci mai nauyi Kamalu ya yi har sai da Baffajo ya tashe shi sallar asuba sau biyu, da gari ya waye ne ya lura da sabon raunin da ke gefen goshinsa. "Kamalu a ina kaji rauni da farar safiya?" Kamalu ya ɗan yi jim kamar ba zai amsa ba sannan ya ce, "A makewayi ne Baffa." Baffajo ya yi shiru yana ƙare masa kallo don haka kawai ya ji bai yarda da abin da ya faɗa masa ba, guntun tsaki Baffajo ya yi cike da damuwa. Kwanansu biyu a cikin masarautar suka fara sabawa da al'amuran cikin gidan Sarautar tun daga kan ayyuka har zuwa yadda ake mu'amala da shugabannin gida zuwa sauran masu sarautun cikin masarautar. Kuma a wannan lokacin ne Fulani babba ta kira Jakadiya a kan ta sanar da Uwar bayi tana buƙatar ƙarin masu yi mata hidima musamman a ɓangaren Abubukar da kullin lamarinsa ƙara taɓarɓarewa yake. A cikin waɗanda aka zaɓa akwai Mai gado sai bayi guda biyu Indo da Basira. Aka wuce sashen Fulani Babba da su, sun yi matuƙar mamakin ganin sauƙin halinta saɓanin na Fulani Umaima. Basira da Indo aka wuce da su sashen Abubakar, za su riƙa gyara shi suna ba shi abinci da wanke kayan da ya ɓata. Yayin da Mai gado za ta zauna a sashen Fulani babba tana taya Baiwa Zainaba yi mata waɗansu hidindimun saboda goyon Jawahir da take da shi, Shi ya sa Fulani babba ta bar ta a ɓangarenta. Sannu a hankali suke gudanar da rayuwa cikin masarautar, har ta kai shaƙuwa mai ƙarfi ta shiga tsakanin Jawahir da su Khadija. Suna matuƙar son ta don wani lokacin idan suka ɗauke ta sai dai idan ta yi kuka su kira Mai gado su damƙa mata ita. A ranar juma'asu ta biyu da zuwansu Masarautar duk yadda Mai gado ta so nema wa Jawahir abin da za ta sha abin ya gagara tun da ta yi ƙanƙantar da za a bata kunu a wannan lokacin. Babu yadda ta iya haka ta zuba wa sarautar Allah ido har dare ya fara tsalawa, cikin fargaba Mai gado ta kwanta da tunanin irin kukan da Jawahir za ta yi cikin dare. Sai dai ga mamakinta tun tana gadin Jawahir har bacci ya yi awon gaba da ita, cikin baccinta ta fara jin tsotso da dariyar Jawahir kamar yadda ta saba ba ta nonon awaki ko na shanu idan dare ya yi. Da mamaki take bin Jawahir da ke faman yin amai alamar ta sha nono ta ƙoshi, ta tashi ta tallafo ta, ta sake rungume ta bayan ta tsagaita da aman ta kwantar da ita suka koma bacci. Asubar fari suka wayi gari da ganin mushen saniya a harabarsu, cike da kaɗuwa kowa yake bin saniyar don saninsu ne filin dabbobin Mai martaba ba ƙaramin nisa yake da shi ba tsakaninsu da wurin. Take Dogarawa suka janye ta gefe bayan gari ya waye aka sanarwa da Mai martaba, sai dai wani abin mamaki ko da aka je garken shanun Takawa babu ko ɗaya da ta yi ɓatan dabo, hasali ma kwance suke cikin kwanciyar hankali, haka aka ɗauki gawar saniyar aka kai ta wani ƙaton ramin da ake zuba bola a ka banka mata wuta. Mai gado ita kaɗai take mamakin wannan al'amarin, har ta saki jikinta ta ci gaba da gudanar da rayuwa kamar kowa. Da farko ta fara fuskantar ƙalubalen ɗan abin da take siya wa Jawahir Nono, ganin haka ya sa ta fara sana'ar ɗinkin muhuci tana ba wa Umaru yana fita bakin kasuwa yana siyar mata. Ɗan abin da suka samu da shi suke siya mata nono da sauran abin da ba a rasa ba. Daga baya da zama ya yi zama har su Khadija suka ji labarin nonon da jawahir take sha sai Fulani Babba take sa wa ake tatso nonon awakin Takawa ana ba wa Mai gado take shayar da Jawahir, sai dai babban tashin hankalin da suka ci gaba da fuskanta bai wuce duk sati da kalar mushen saniyar da za su yi tozali da ita da Asuba ba, zancan da ya karaɗe ciki da wajen masarautar har ya kai ga kunnen Fulani Umaima. A lokacin da Fulani Umaima ta sallami su Jakadiya kai tsaye ɗakinta ta koma, cikin damuwa take kai-kawo. Ganin ba za ta iya jure halin da take ciki ba ya sa ta ziyarci Bamaguje ko ta san abin da zai iya faruwa a gaba.Don haka kawai take jin zuciyarta na wasu-wasin akwai abin da zai iya faruwa a cikin masarautar. Tun isarta wurin ta fahimci yana cikin matsanancin ɓacin rai, ba ta damu da sanin halin da yake ciki ba don haka ta amayar masa da damuwar da ke cikinta dangane da rashin gane hallitu biyun da ya ba ta umarni. Ƙarasa kalamanta ya yi daidai da sauke yatsunsa biyar da Bamaguje ya yi a saman kumatunta, a firgice ta ja da baya cikin kaɗuwa da zallar tashin hankali. "Ni ka mara?" Ta wurga masa tambaya cike da ƙasaita da tsananin ɓacin rai. "Kin ɓata mini shiri kin kuma wargaza mini tanadina, me ya sa kin san ba za ki kawo mini yarinyar nan ba kika ɗaukar mini alƙawari har kika sa na je fadar Baƙaƙen aljanu na gana da Shugaba, ba fa iya ganawa muka yi ba da ƙyar da suɗin goshi na samu zai aiwatar mini da aikin da nake son cim ma muradina a kanta." Bamaguje ya faɗa jiki da muryarsa na karkarwa sakamakon tsufan da ya yi tukuf. Murmushin takaici Umaima ta yi don sai a yanzu ta fahimci manufarsa sarai, wato so yake ya yi amfani da iya wurin cim ma ƙudirinsa ita kuma ko oho. "Sai yanzu na fahimci in da ka dosa, tun ziyarar baya na fara ɗora zargi a kanka, idan ba ka manta ba a wani zuwa da na yi da bakinka ka ce mini ita yarinyar nan Yarima ba zai taɓa hawa karaga ba har sai ya aure ta. Daga baya ka ce mini na yi duk yadda zan yi na kawo maka ita domin aiwatar da aikinka a kanta, ashe ban sani ba tsuntsu biyu kake son jifa da dutse ɗaya. Duk duniya babu wanda ya taɓa yi mini abin da ka yi mini, kuma na yi alwashin wannan shi ne karo na ƙarshe zuwa fadarka. Ka san ni sarai Bamaguje ba na yafiya kuma ba na mantuwa don haka ina nan tafe zan waiwaye ka ko ba daɗe ko ba jima, ka riƙe duk wani taimako da kake ganin za ka iya yi mini." A zuciye Umaima ta juya za ta tafi, ta ji Bamaguje ya bushe da dariya. "Na san wannan ranar za ta zo da za ki bijire mini. Amma ki sani ta yaro kyau take ba ta ƙarko, ni ne dolenki idan aure bai kawo ki ba shika zai kawo. Da sannu ya za ta ɗakin ƙanwa idan da yawancin kwana..." "Ka san kowa rai ya yi wa daɗi ba ya mai shi ba. Kuma na kwance shi ya san daɗin katifa ba na tsaye ba, duk yadda za ka so samun farincikina ba kamar ni ba, ka rubuta ka ajiya duk ranar da dawo wurin nan da sunan neman taimako ka yi mini duk abin da ka ga dama. Ni Umaima 'yar sarki Habibullah Bn Muhammad Imam ba a taɓa yin kuskure biyu da ni, kada ka manta kowa da haɓarsa yake tagumi ba da ta wani ba." Umaima ta ƙarasa magana tana yin gaba abin ta cikin ƙunan rai. Ko kaɗan Bamaguje bai yi yunƙurin dakatar da ita ba domin sanin hali ya fi sanin kama, ya san wace ce Umaima ba tun yau ba. Ya kuma san duk daren daɗe wa za ta dawo wurinsa, takaicinsa ɗaya da ta wargaza masa shirinsa. Abin duniya goma da ashirin ya haɗe mata a lokacin da Jakadiya ta same ta da saƙon Takawa, ba ta tanka mata ba har sai da Jakadiya ta ɗago ta kalle ta. "Jakadiya ina cikin matsananciyar damuwa, duk faɗin gidan nan kin san da ke kaɗai na aminta har zan iya buɗa wa sirrina. Na yanke alaƙata da Bamaguje ta har abada. Ina tsoron ya haɗa mini tuggun da zai kwaye mini zani a cikin masarautar nan har Takawa ya juya mini baya." A firgije Jakadiya ta kalli Fulani Umaima, sai kuma ta yi shiru tana nazari. "Ƙarya ake uwar ɗakina ta ji kunya, wannan sharrin zuciya ne kuma ba za mu taɓa ganin haka ba har gaban abada. Allah ya huci zuciyarki ba za ki taɓa fuskantar wannan tunanin naki ba har abada. Idan kin yarje mini zan haɗa ki da wani Boka da na sani shekara ashirin baya, aikinsa tamkar yankan wuƙa yake sha yanzu magani yanzu. Sai dai kuma ban sani ba ko har yanzu yana nan cikin halwar tsafinsa, so samu dai shugabata na aikawa ƙanwar mahaifiyata takarda na ji daga gare ta. Domin tun da jimawa ita ta yi uwa da makarɓiya wurin haɗa ni da shi." "Jakadiya kin san da zamansa amma ba ki taɓa sanar da ni ba?" Umaima ta wurga mata tambaya. "Allah ya taimake ki na so yi miki iso wurinsa sai kuma na tuna yadda kika ba wa Bamaguje muhimmaci, don haka na ji tsoron yin kuskure a wurinki, amma a gafarce ni ko yanzu ake son na tura saƙo a shirye nake ranki shi daɗe. Wani ma ya yi rawa ballantana ɗan makaɗi, mutane nawa na yi hanya ballantana uwar ɗakina."Jakadiya ta yi maganar cike da rawar kai. "Na kasance mai son sirri a duka al'amuran da suka shafe ni, Jakadiya bakinki ƙanin ƙafarki. Ko kaɗan kada na ji kin ɓunta wa wani sirrina." "Na karɓa ina godiya ranki shi daɗe, idan ni ce har gaban abada ba zan taɓa baki kunya ba. Sai dai yana da sharaɗi, a ranar da kika ziyarce shi zai tara da ke kuma sai kin yi kwana arba'in baki yi wankan tsarki ba kuma za ki daina har sauran ibadu bakiɗaya." Fulani Umaima ta saki murmushi. "Wannan mai sauƙi ne Jakadiya ai aika masa da saƙon ziyarata." Da wata yammaci Muhsin sanye da kayansa masu matuƙar birgewa, har ya fara tafiya Fadawa suka taso da niyyar yi masa rakiya. Hannu ya ɗaga musu alamar ba ya buƙatarsu, can cikin lambun Mai martaba ya zagaya da yake lambun yana da hanyoyin kusan guda uku, hanya ta farko za ka iya shiga ta sashen Mai martana. Hanya ta biyu kana iya shiga ta sashen matan sarki da iyalansa, hanya kuma ta uku ta can ɓangaren bayi ake iya shiga sai dai akwai tafiya mai matuƙar nisa. Ga wanda ma bai ɗauki shekaru a gidan ba ba zai taɓa sanin da wannan ɓoyayyar hanyar ba. Kuma ko waɗanda suka san da ita ba sa gangancin kai ƙafarsu wurin, domin gujewa salwantar rayuwarsu don zunubi ne mai girma a kama Bawa da laifin shiga wurin. Kamalu tun yana yaro shi ma'abocin son shiga daji ne don a zargin da Baffajo yake yi ƙila a shige-shigensa ne ma har ya haɗu da makaran da suke taɓa shi lokaci-lokaci, don ma yana yi masa jiƙe-jiƙe da surkullensu irin na fulani amma a banza kare ya sha tsamiya. Ta bayan ɗakunan Bayi ya bi a lokacin rana ta buɗe kowa yana harkokinsa, tafiya yake ba tare da ya san wurin da ya dosa ba. Sai dai tsari da ƙwaytuwar wurin ya matuƙar birge shi, wata hanya ya bi haka kawai ya ji gabansa na faɗuwa. Sai da ya yi nisa sannan ya fara ganin kamar ya san wurin, mafarkinsa da ya taɓa yi na mage ya faɗo masa. A ɗan tsorace ya ci gaba da tafiya har ya fita daga wurin mai ɗan tsananin duhun bishiyoyi, can wani murgujejen shuri ya hanga da wasu fararen tsuntsaye a kai suna zagaye shi, da sauri ya ƙarasa wurin yana tsalle da niyyar kama ɗaya daga cikinsu. Kamar waɗanda suka san abin da ya kawo Kamalu kenan suka shiga zullo suna ƙoƙarin tsere masa, yanayin ba ƙaramin birge shi ya yi ba ya saki jiki yana tsalle-tsalle cikin nishaɗi. Da matsanancin mamaki Muhsin yaken bin bayan yaron da bai wuce sa'ansa ba da kallo, sai dai kuma ganin kayan bayin da ke jikinsa ya baƙanta ransa don tun kafin ya fito ya ce ba ya buƙatar rakiya. "Kai me kake yi a wurin nan?" Muhsin ya faɗa cike da isa da ƙasaita. Jin kalaman Muhsin ya sa Kamalu juyowa, kallo ɗaya ya yi masa ya ɗauke kansa gefe. Ya fahimci dai ba matsayinsu ɗaya ba a masarautar duba da yanayin tsadaddiyar suturar jikin Muhsin. Ran Muhsin ya ɓaci da ganin wulaƙancin da Kamalu ya yi masa, tasss ya sauke masa mari a fuska. "A yau ba sai gobe ba zan sa a hukunta ka zan ga..." Wawan marin da Kamalu ya zuba masa a fuska ya katse kalaman bakinsa, har sai da haƙoransa suka datse harshensa. A hargitse ya ɗago yana dubansa, Kamalu ya fara takawa ba tare da ya tanka masa ba ya nufi hanyar su ta bayi don ya ji zagayen duk ya gundure shi silar abin da Muhsin ya yi masa. Cikin tsananin ɓacin rai Muhsin ya bi hanyar sashen Takawa yana fara sauri duk da tafiya da sauri ba ta daga cikin ɗabi'arsa. Kafin ya ƙarasa tuni yatsin Kamalu sun fito raɗau-raɗau a saman kuncinsa, ƙarshen tsinin harshensa ya datse har ya fara tsattsafo da jini. Jama'a Kamalu ya taɓo ɗan masu gida🤭🤣🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️ *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* 12 *🤔WAI NA CE KINA DA WAƊANNAN MATSALOLIN AMMA KIKE ZAUNE DA TARUN TUNANI FAL KWANYA?* *MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE* *SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?* *TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI'IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHEƘI KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI* *SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA'A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA'IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA'IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA* *Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.* 👉 *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.* *1. Supplements na gyaran jiki ciki da waje* *2. Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba* *3. Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya* *4. Supplements na karawa fata kyau da sheki glowing skin* *5. Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci* *6. Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki* *7. Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu* *8. Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.* *9. Supplements na karin ni'ima da dandano da tightening ciki da waje* *10. Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc* *11. Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement* *12. Supplements na gyaran HQ ciki da waje* *13. Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton* *14. Supplement na whitening/glowing skin* *15. Supplement for Acne, dark spots remover* *Da duk wasu nau'in supplement da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158* Taku ɗaya biyu idan Kamalu ya yi sai ya saki guntun tsaki sakamakon ɓacin ran da ke cinsa a zuciya, a madadin ya bi hanyar da ta kawo shi zuwa ga wannan shurin, sai kawai ya yanke shawarar bin wata doguwar hanya mai ɗauke da waɗansu gajerun bishiyu masu kauri sai dai kuma kowacce murgujejiya bishiya a ɓarin ta na hagu a akwai waɗansu gidajen tururuwa guda uku, da mamaki yake bin wurin da kallo a zuciyarsa yana ta'ajibin ganin yadda bishiyoyin suke jere kamar an dasa su. Haka daga jikin gidajan tururuwar tamkar waɗanda aka kasa su wuri-wuri, kowanne guda ukun suna kewaye da bishiyoyin. "Kada ka yi mamaki Saraki." Ya ji an furta masa daga bayansa, yana waigawa idanunsa suka yi tozali da mamallakiyar muryar. Tun daga ƙofar sashen Mai martaba Dogarawan da ke tsaitsaye wasu suka fita ta ƙofar da Muhsin ya shigo, wasu kuma suka sha gaban Muhsin. "Karya ake wane mutum ya taɓo Yarima duk hatsibancinsa kai ko aljani ne ya kwana da yunwa." Cike da fushi Muhsin ya tura ƙofar ɗakin Mai martaba ganin yadda ya shiga ya sa Mai martaba ya kafe shi da ido a lokacin Fulani Umaima na zaune a gefensa suna hira. "Me yake faruwa da kai Muhsin? Na yi rantsuwa da girman Allah duk wanda ya taɓa ka sai na sa an zartar masa da mummunan hukunci." Fulani Umaima ta furta rai a matuƙar ɓace sakamakon ganin yadda Muhsin ya shiga yana zubar da ƙwalla idanuwa bibbiyu, ɓarin fuskarsa ta kumbura lokaci guda. "Yarima me ya faru muka ga sauyin yanayi a tattare da kai?" Takawa ya furta murya ɗauke da damuwa . Rushewa ya yi da matsanancin kuka haɗe da zubewa ƙasa a gaban mahaifinsa. Jikin Fulani Umaima har karkarwa yake tana shirin sake tambayarsa ta ji ya ce. "Wani yaro ne ya mare ni, kuma kayan jikinsa ne suka tabbatar mini daga sashen bayi yake..." "Ba a haifi mahaifinsa ba kowane ne, ƙarya yake ya mari Yarima ya kwana lafiya domin wutsiya raƙumi ta yi nesa da ƙasa har gaban abada." Fulani Umaima ta faɗa tana miƙewa tsaye. "Fulani a kwantar da hankali za mu ɗauki matakin gaggawa nan ba da jimawa ba." Ba don ta so ba ta koma ta zauna zuciyar na tafasa. A daidai lokacin Jakadiya ta rafka sallama daga bakin ƙofa, babu ɓata lokaci Takawa ya bada iso ta shiga hannuwanta ɗauke da kayan lambu. Da sauri ta dire kayan haɗe da dafa ƙirji tana kallon Muhsin. "A gafarce ni Ubangidan bisa al'amarin da ya faru da Yarima, yanzu na haɗu da su Bawa Ali yake sanar da ni mummunan al'amarin da ya faru da shi." "Jakadiya daga yanzu zuwa dare ina buƙatar Bawan da ya aikata wa Yarima wannan ɗanyan aikin cikin gaggawa."Cewar Fulani Umaima da ta ja Muhsin jikinta tana shafa tsagin fuskar sa wacce ta yi jawur hannuwan Kamalu sun yi masa ruɗu-ruɗu. "Jakadiya a sanar da sarkin gida ya tattara mana Bayi akwai muhimmiyar sanarwa da za mu fitar. A cika umarnin Fulani kamar yadda ta buƙata cikin gaggawa." Sarki Abdul'aziz ya furta. "An gama ranka shi daɗe, farij jakada mai tarin dubun alkairai." Jakadiya ta yi maganar tana miƙe wa bayan da Takawa ya sallame ta. Kafin wani lokaci tuni Dogarawan sashen Sarki Abdul'aziz sun bazama lungu da sakon cikin dajin duk da a lokacin ba su san takamaimai abin da ya faru da shi ba. Ajiyar zuciya Kamalu ya sauke don ya gane shi sarai sannan ya furta. "Ya aka yi ka biyo ni har nan?" Murmushi Dattijon ya yi sannan ya ja hannunsa suka koma jikin bishiyar ɗorawar da ke gefe, a kan ɗaya daga cikin shurin da ke wurin Dattijon ya zauna shi ma Kamalu kai tsaye ya hau shurin da ke kallon Dattijon. Wani irin shuuuuu ya ji a saman kansa, take ya ga dajin ya fara juya masa. Hannu Dattijon ya kai saman goshinsa ya dafa nan take ya ji komai ya fara dawo masa, buɗe idanunsa ya yi yana fesar da iska mai zafi. "Kada ka riƙa saurin taɓa lafiyar mutane domin kai ba kamar kowa ba ne." Dattijon ya yi maganar yana sakin murmushi. Kamalu ya bi shi da kallon mamaki, "Ya aka yi ka san wani abu ya faru?" Shi ma ya wurga masa tambaya. "Ko kuma ba zan yi mamaki ba, domin jinin Sarki Muhammad Safwan idan bai yi zafin rai ba wa zai yi? Ai dama harbi ga ɗan jaki gado ne." "Wane ne kai? Waye Muhammad Safwan, kuma me ya sa kake alaƙanta ni da shi?" Kamalu ya furta fuska a haɗe, don ya ƙagauta ya san waye wannan Dattijon da ya ke son kutsowa cikin rayuwarsa. A wannan karon ma murmushi Dattijon ya sakar masa, wannan ya sake ɓata ran Kamalu ya saki tsaki cike da damuwa. "Ko a kundin tarihi ban taɓa jin amintaka irin tamu ba. Ina matuƙar godiya ƙwarai aminina da wannan jajircewar da ka nuna mini. A dalilin haka zan sadaukar da jikan-jikana mai zuwa, ko da zai zama Sarki ko ba zai zama ba. A wannan lokacin na san ƙasa ta jima da binne idanuwana, amma duk rintsi kada ka wofantar da alƙawarin da muka ƙulla. Ka fi kowa sanin wane ne ni, don haka na tabbata zubi da surar halittarsa ita ce za ta bayyana daga tsatson da ya fito, matuƙar ya kasance jinina babu gauraye a ciki." Da sauri Dattijon ya dawo daga duniyar tunanin maganar da Marigayi Sarki Muhammad Safwan ya faɗa masa a lokacin da suke wata tattaunawa mai muhimmanci. Ganin Kamalu na bin shi da kallo ya sa ya furta. "Na tuna kalaman Aminina Mai martaba da muka taɓa yi da shi a baya game da zuwanka, tabbas na yi rashin amini na gari." Kamalu ya taɓe baki cikin halin ko-in kula ya yunƙura zai tashi don ya gaji da waɗannan kalaman Dattijon, sai kuma ya ji ya ce. "Sunana Maharaz. Ni aminin kakan-kakanka ne kamar yadda na sanar da kai a baya, ni da shi duka mun gudanar da rayuwarmu ne a cikin wannan masarautar. Waɗannan bushiyoyin da kake gani ni da shi ne muka dasa su da hannuwanmu..." Tafiya take kamar za ta tashi sama har ta ƙarasa sashen Bayi da tuni labarin abin da ya faru ya isa gare su, a tsaitsaye ta same su sun yi carko-carko cike da jimami. Jakadiya na ƙarasawa ta wurga musu mugun kallo cike da ƙasƙanci. "Da alama labari ya iso gare ku, don haka ku san da sanin kun ɗan ɗaya daga cikinku ya tsokano muku tsuliyar dodo." Jakadiya ta yi maganar tana zagaye su ɗaya bayan ɗaya. "Ai wanda bai gaji arziƙi ba dole sai ya nuna tsiya, ban da iskanci a ce kana ƙasƙantacciyar hallita amma za ka nemi cin zarafin ɗan masu masarauta. Tun wuri wallahi tun ba a je ko ina ba duk wacce ta san tana da ɗanta ne ya aikata wannan zunubin ta yi gaggawar fito da shi ida ba haka ba, za ku bambamce wa Fulani Umaima tsakanin tsaba da tsakuwa." Uwar Bayi ta yi maganar rai a ɓace. Take gaban Inna wuro ya faɗi, fargabar ta ɗaya kada a ce Kamalu ne ya aikata wannan mummunan aikin. "Allah Inna babu yaron da ya isa ya nuna mini yatsa ban karya shi ba ko ɗan gidan uban waye." Lokaci ɗaya kalaman Kamalu na baya suka dawo mata a lokacin da faɗa ya haɗa shi da ɗan Gunduman rigarsu. Wani abu ta ji ya tsarga mata take gumi ya shiga yanko mata cike da tashin hankali. "Ruwanku ne ku sauƙaƙa wa kanku azabtarwar da ke tunkaro ku don yanzu haka Takawa da Fulani Umaima ne suka umarce ni da na yi gaggawar tara ku a harabar sashenta." Rufe bakin Jakadiya hayaniya ta fara tashi kowa da abin da yake tofawa, sai dai a mafi yawan daga cikinsu kowa zame ɗansa yake ƙoƙarin yi. Inna wuro tana tsaye jigum ko motsin kirki ta gagar yi, ana cikin haka ta fakaici ido ta ƙarasa wurin Baffajo da shi kansa yana tsaye suna jajanta abin da ya faru. Sai da suka keɓe bayan ya kalli hagu da dama ya furta. "Inna wuro ina tsoron kada Kamalu ne ya aikata wannan abin." Idanun Inna wuro ya ciko da ƙwallah. "Wallahi abin da na zo sanar da kai kenan, ai kuwa yau da kwananmu ya ƙare." Ta ƙarasa maganar hawaye na zuba, da sauri ya katse ta. "Kul Inna wuro kada ki sake wani ya fahimci halin da muke ciki yanzu ina Kamalun?" "Tun la'asar rabon da na ga gilmawarsa, har A'iru na aika ba ta gan shi ba." Jinjina kai ya yi ya ce. "Koma can maza kada wani ya fahimci ba kya nan." Da sauri Inna wuro ta wuce jiki a sanyaye kamar akuyar da ta bi ta mahauta, a lokacin tuni Bayi sun fara bin hanyar da za ta sada su da can babbar haraba. Suna tafe ƙwai da fure Jakadiya Uwar Bayi sai zazzaga musu masifa suke cikin kyara, tsangwama da wulaƙanci, sai da suka isa babbar harabar sannan Jakadiya ta isa sashen Takawa ta sanar da Fulani Umaima da Mai martaba ta sanar da su ta cika umarninsu. Fulani Umaima da kanta ta riƙo hannun Muhsin suka ƙarasa wurin da Bayin ke tsaitsaye, fuskarta a matuƙar ɓace ta dube su cike da ƙasƙanci. "Ina mai ba ku shawara da tun ƙofar haƙurin da ta danne zuciyata ba ta buɗe ba ku yi gaggauta fito da yaron da ya nuna wa Yarima rashin ɗa'a, idan ba haka ba wallahi sai na shayar da ku ruwan mamaki." Hayaniya ce ta fara tashi sama-sama take Jakadiya ta buga musu tsawa sannan suka yi shiru. Ganin babu wanda ya nuna mai laifin a ciki ya sa Fulani Umaima ta sa Jakadiya ta rarraba layi-layi, sannan Muhsin ya fara bi ɗaya bayan ɗaya yana dubawa ko zai ga Kamalu. "Ka na nufin Baffajo na da sarauta ban taɓa sani ba? Idan haka ne me ya sa bai taɓa sanar da ni ba.?" Kamalu ya tambayi Maharaz bayan ya gama sauraron guntun jawabinsa. Shiru Dattijon ya yi yana nazari, kamar ya sanar da shi gaskiyar lamarin amma sai ya ga ƙuruciya mararan a ƙwayar idanunsa, don haka ya karkatar da akalar labarin. "Ni yanzu ba tsoho ba ne? Ka ga ai zan kai shekarun kakan-kakanka? Shi ya sa na ce maka ni aminin kakanka ne." Sai a lokacin Kamalu ya jinjina kai, "Kai a ina kake kwana? Kuma me ya sa ba ka saka kayan bayi irin namu?" "Lokaci na nan da zan warware maka dukkan zare da abawa." Sai da Muhsin ya zagaye Bayin da ke wurin gabaɗaya amma ko mai kama da Kamalu bai gani ba, ran Fulani Umaima ya yi ƙololuwar ɓaci. A fusace ta ja hannun Muhsin ta wuce sashenta tana umartar Jakadiya da tana son ganinta cikin gaggawa. Lungu da saƙon da ke cikin Masarautar babu wurin da ba su shiga ba amma babu hallitar da suka gani illa tsuntsaye da ƙananan dabbobi. Shi kansa Takawa ya yi matuƙar mamakin rashin ganin mai laifin daga ɓangaren Dogarawan har zuwa ɓangaren Muhsin. "Allah ya huci zuciyar uwar ɗakina ya sanyaya ran uwar gijiyata, an aikata babban kuskure kuma duk wanda ya aikata wannan ɗanyan aikin sai ya shiga uku, domin matsi shi ke sa kalangu tsami." Jakadiya ta yi maganar tana duƙar da kai ƙasa. "Idan kiɗa ya canza dole ma rawa ta canza Jakadiya. Na fara zargin Fulani babba da yi wa Yarima turen iska, jikina yana ba ni a masarautar nan ban ga bawa ɗaya da zai yi gangancin tsinka wa Yarima mari ba. Amma ba ta sanni ba, da yake yaro bai san wuta ba sai ya taka." "Kowa ya aikata abin da yake so zai ga baƙi ciki, Fulani babba ta tafka babban kuskuren da zai kai ta ga danasani. Yarima dai dashen Allah ne, kuma sai mun tabbatar mata da ko cikin tumaki rago ke zuwa fada." Fulani Umaima ta ɗan yi jim sannan ta ce, "Yanzu me ye abin yi?" "Abin yi a juyar mata da aniyarta kanta, ni na fahimci hassada ƙarara a wurinta tun da tana ganin ita ce uwar gida kuma Yarima ba ya gare ta." "Ki saka mana ranar ziyarar bokan da kika yi aike da jimawa." Jakadiya ta russuna. "Tamkar kin je gare shi buƙata ta biya uwar gijiyata."Fulani ta saki shu'umin murmushi sannan ta furta. "Tabbas sai na tabbatar wa Fulanu birnin kura ba a taɓa sa kare dillanci." Cike da banbaɗanci Jakadiya ta yi mata jinjina da hannu. "Allah ya taimaki uwar ɗakina, shi ya sa duk faɗin masarautar ba ni uwar ɗaki kamar ki." Fulani Umaima ta yi wa Jakadiyar kyautar ɗan kwalaye da alkaki sannan suka yi sallama ta bar sashenta. Miƙe wa Kamalu ya yi yana kaɗe jikinsa sakamakon ƙasar shurin da ya kwaso sannan ya furta. "Zan ƙarasa don Inna wuro kar ta ji ni shiru." Tsoho Maharaz ya miƙe suka fara tafiya ya ce. "Ni ma zan wuce sai an kwana biyu kenan?" Cikin halin ko-in-kula Kamalu ya ce, "Sai an jima." Daga haka Tsoho Maharaz ya bi ɓangaren da Muhsin ya bi hanyar da za ta sada shi da sashe Mai martaba, shi kuma Kamalu ya wuce can sashensu na Bayi. Yanayin yadda ya gansu ne ya tabbatar masa da abin da yake faruwa, da yake suna da yawa bai sa sun fahimci ba a yi binciken babu Kamalu ba. Alwala ya ɗaura yana shirin wucewa ya ji Baiwa Mai gado da wata baiwa suna jajanta abin da faru, taɓe baki ya yi don ba don Maharazu ya ce kar ya faɗa ba babu abin da zai sa shi bai sanar wa Inna wuro ba. "Magana ta gaskiya Galadima na jima da ƙudurta wa zuciyata haɗa Saifullahi da yarinyar nan Khadija, ko babu komai na san matsayina a masarautar nan zai ƙaru amma yanzu wani ƙishin-ƙishin nake ji kamar Mai martaba na son ba wa ɗan Sarkin ƙasar Farrom aurenta." Ciroma ya yi maganar cikin jimami. Galadima ya jinjina kai don shi kansa a kwai wani ƙuduri a zuciyarsa amma shi kam ba shi da matsala tun da Yarima da sauran lokaci kafin ya yi aure. "Ashe tunanin da ke ƙunshe a ƙwaƙwalenmu tamkar ɗan'juma ne da ɗan'jummai, tun da Allah ya ba wa Maryamu ciki nake addu'ar Allah ya sa ta haifi ɗiya mace. Ko ba komai idan ta girma na san ƙulle-ƙullen da zan yi har Yarima Muhsin ya aure ta, to ka ga kenan faɗuwa ta zo daidai da zama. Sai dai kuma dole mu yi takatsantsan domin ka san Fulani Umaima ba kanwar lasa ba ce, dole sai mun lura idan ba haka ba sai mu sha ruwa da ciyawa ko kuma mu yi shuka a idon makwarwa." Lokaci ɗaya Ciroma ya bushe da wata iriyar dariyar, sannan ya tsagaita haɗe da yin ƙasa da murya ya furta. "Wane mutum in ji mutuwa ai na tabbata matuƙar ba kai za ka bada ƙofa ba kwaɓar mu ba za ta taɓa yin ruwa ba, tun da idan ka ga ruwa ya gurɓace yana zaune wuri ɗaya ne." Ciroma ya kalli hagu da dama haɗe da sake yin ƙasa da murya ya ce, "Mai zai hana mu kawar da Mai martaba Abdul'aziz ida ya so baya biyan buƙatarmu. Ka ga Ɗana yana auren ƙanwar sarki kai kuma 'yarka na auren sarkin shi kansa, yoo me ya rage idan babu Abdul'aziz? Ka ga a fakaice ba mu za mu riƙa sarrafa masarautar da sarautar gabaɗaya ba?" A firgice Kamalu ya sake maƙalewa a kusurwar soron jin kalaman da su Galadima suke yi,jikinsa ya ɗauki karkarwa gumi na keto masa. Bai san dalili ba amma haka kawai ya ji zuciyarsa na bugu a kan kisan da za a yi wa Sarki Abdul'aziz. Bai yi tsammani ba ya ji wani irin tari ya taso masa, da sauri ya sa hannu biyu ya toshe bakinsa don ya sa matuƙar azzaluman nan suka gan shi kashinsa ya bushe. Ciroma da Galadima suka yi sororo haɗe da kallon juna sakamakon jin tarin Kamalu da suka yi, cikin sanɗa suka tunkari wurin da Kamalu yake tsaye. Kamalu kana ta jefa kanka a bala'i.🤔 SHU'UMAR MASARAUTA 13 *MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE* *SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?* *TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI'IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHEƘI KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI* *SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA'A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA'IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA'IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA* *Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.* 👉 *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.* *1. Supplements na gyaran jiki ciki da waje* *2. Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba* *3. Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya* *4. Supplements na karawa fata kyau da sheki glowing skin* *5. Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci* *6. Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki* *7. Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu* *8. Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.* *9. Supplements na karin ni'ima da dandano da tightening ciki da waje* *10. Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc* *11. Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement* *12. Supplements na gyaran HQ ciki da waje* *13. Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton* *14. Supplement na whitening/glowing skin* *15. Supplement for Acne, dark spots remover* *Da duk wasu nau'in supplement da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158* *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Jin takun tafiyar su ya sa gaban Kamalu ya ci gaba da faɗuwa jikinsa ya ɗauki karkarwa, can jikin bango ya sake maƙalewa yana fatan kada Allah ya sa su cim masa don shi kansa ya san idan suka gan shi tsaf za su iya kashe shi, ba su yi tsammani ba suka ga Jakadiya ta faɗo cikin soron hannunta ɗauke da aci bal-bal. Tana hango su Galadima ta kalle su da mamaki, "Yautai mugun tsuntsu ma sha miyarka sai ya yi dare.Daga ina kuke da tsohon daren nan?" Ta yi maganar tana kallon Ciroma. "Tararuwa mai wutsiya ganinki ba alheri, ina zuwa haka?" A yatsine ta kalle shi. "Jikina yana ba ni akwai ƙullin da kuke ɗaurawa don banza ba ta kai zomo kasuwa!" Ciroma ya wayance."Daga cikin gida muke ke fa ina za ki?" "Daga wurin Fulani babba nake zan kai saƙo wurin Abubakar." Lokaci ɗaya suka kwashe da dariya jin an ambaci sunan Abubakar, Jakadiya ta gimtse tata dariyar ta furta. "Ganin gida kare kan zagi kura amma ba a daji ba, na tabbaya ɗayanku bai isa yin dariya nan a gaban amale ba." Daga haka ta yi gaba a fili ta nuna tamkar ta ji haushin dariyar da suka yi, ita ma kuma a ƙasan zuciyarta dariyar take yi. Galadima da Ciroma suka duba wurin da suke zargin wani na laɓe amma babu kowa, sakamakon tun shigar Jakadiya Kamalu ya sulale ba tare da sun fahimta ba. Wannan ta sa suka ajiye ragowar maganar da suke yi ba tare da sun ƙarasa ba. Yanayin da Inna wuro ta ga Kamalu a ciki ya sa ta zaunar da shi a gefenta, ƙura masa idanu ta yi lokaci ɗaya ta fahimci tashin hankalin da ke tattare da shi. "Me yake damunka Kamalu?" Da yake a wannan lokacin Inna wuro sun samu 'yancin kansu ta hanyar mazajensu da suka yi ruwa suka yi tsaki suka haɗa bulo suka gina musu ɗakuna kamar yadda suka ga sauran bayin sun killace iyalansu. Jiki a sanyaye Kamalu ya furta, "Inna don Allah kada ki min faɗa idan na gaya miki." Inno wuro ta gyaɗa masa kai. "Kada ka damu Kamalu ba zan maka komai ba." "Inna bayan na kai wa Shamaki saƙonsa ina dawowa na ji wasu suna ce wa za su kashe mai martaba..." Tun bai ƙarasa maganar ba ta sa hannu ta toshe masa baki, take jikinta ya ɗauki karkarwa. Ta yi ƙasa da murya ta furta, "Babu ruwanka da kowa ka ji Kamalu, daga yau idan ka sake jin wasu na irin wannan maganar ka yi tafiyarka ka ji." Kamalu ya gyaɗa mata kai sannan ya hau shimfiɗarsa ya kwanta. Jawahir ta yi wayo sosai yarinyar ɓul-ɓul da ita gwanin birgewa, musaman da take samun kulawa a ɓangaren Fulani Babba, sai dai abin da har kwanan gobe ke faruwa bai fasa ba dangane da ganin gawar saniyar da ake wayar gari da ita duk ranar asabar da asuba. Fadar Sarki Abdul'aziz ta ƙayatu matuƙa da kayan alatu iri-iri irin na wancan lokacin. Waziri, Galadima, Ciroma da Malam Liman zaune suke a gabansa sai Dogarawan da ke tsaron ƙofa da sauaran Fadawan da ke zaune daga can gefe. "Dalilin da ya sa muka tara ku saboda wata muhimmiyar magana da ke ci mana tuwo a ƙwarya sakamakon firgici da talakawanmu suke ciki." Sarki Abdul'aziz ya yi maganar cike da izzar mulki. Shiru suka yi gabaɗaya suka sauraronsa ya ci gaba da cewa. "Akwai zancan mushen saniya da ake gani duk wayewar garin asabar a sashen Bayi, wanda da farko da aka sanar mana ba mu ɗauki abin da muhimmanci ba sakamkon al'amuran almara da muka saba gani yau da kullin a cikin masarautar nan, har sai da muka ga abin yana neman zarce ƙa'ida. Duk cikin dobobbin da Allah ya albarkace mu da su mun sa a ƙidaya su amma babu guda ɗaya da muka ji labarin ta yi ƙwarzane ballantana ta yi mushe, shin mene ne mafita kuma me kuke ganin yana haifar da haka?" Wani Dogari daga bayan Sarki ya russuna cikin girmamawa sannan ya furta. "Allah ya taimaki amale, ɗawisu mai yawan ado sikari ba ka yi farin banza ba." Daga gefe Waziri ya gyara zama sannan ya fara magana. "Allah ya taimake ka, ni ina ganin wannan ba abin mamaki ba ne duba da sanin wannan masarautar ba irin kowacce masarauta ba ce, a tawa fahimtar a ji daga bakin makusantan gidan na ainihi idan ya so daga baya sai a san abin yi ko a nemi shawararsu. Amma fa a harsashena kenan ranka shi daɗe." Lokaci ɗaya gabaɗaya suka aminta da shawarar Waziri, Sarki Abdul'aziz shi ma ya aminta da haka dalilin da ya sa ya yanke shawarar jin ta bakin zuri'ar da ke rayuwa a daular shuri. Daga haka suka shiga tattaunawa a kan abin da ya da ce, dangane da harkokin masarautar. Zaune yake a can cikin turakarsa a gaban ƙaton shurin ya tanƙwashe ƙafafuwansa sannan ya ɗora hannunsa na hagu a kan shurin ya furta. "Assalamu alaikum. Gafaranku dai ya ku ahalin cikin masarautar nan?" Daga cikin shurin ya ji an yi gyaran murya sannan aka amsa masa. "Wa'alaikas salam. Barkanka dai Sarki Abdul'aziz me kuma iyalaina suka yi maka? Don rabon da ka kawo mini ziyara har na manta." Da yake a wasu shekaru da suka wuce Sarki Abdul'aziz ya taɓa kai ƙarar jikan Dattijon sakamakon wata ɓarna da ya yi masa. "Ba ƙara na kawo ba Dattojo Maharaz, na zo ne dangane da wani muhimmin abu da yake faruwa a cikin masarautar nan." Murmushi aka yi daga cikin shurin sannan Maharaz ya ce, "Ba tun yau ba miyagun al'amura da ƙazaman abubuwa na faruwa a cikin masarautar nan kuma suna ta ci gaba da faruwa, sai dai kuma ban san wanne irin bacci kake yi ba Abdul'aziz." Takawa ya yi jim ba ya son ya bada ƙofar da za su haɗa shi da mutane don haka ya shashantar da zancen da cewar. "Wannan wata muhimmiyar magana ce..." "Dangane da Saniya ko?" Dattijo Maharaz ya katse Sarki Abdul'aziz don ya lura ba ya san sanin matsalolin da ya ɗauko masa waɗanda ke faruwa a cikin masarauta. Sai da Dajjito Maharaz ya numfasa sannan ya ci gaba da cewa. "Waɗannan saniyoyin da suke mushe ba daga gare mu suke ba, sun fito daga cikin zuri'ar RUMZU su suke shayar da 'yarsu cikin fushi, kuma idan har hakan bai zama illa ko wani tashin hankali ba kada ka yi gaggawa a kansu. Suna da matuƙar hatsari fiye da tunaninka, yanzu haka 'yarsu na cikin masarautar nan sakamakon zanen ƙaddararta da ya gindayo ta kanta har ta faɗo cikin masarautar da duk faɗin duniya babu shu'umar masarauta kamarta. Hasali ma akwai daɗaɗɗiyar gaba a tsakanin zuri'ata da su zuri'ar RUMZU, sai dai hakan ba zai sa mu ɗauki matakin a kan jikarsu ba, domin har a yanzu ita ba ta san asalin abin da ya faru ba ka ga kamar mun zalince ta ne. Kuma idan har muka taɓo su na tabbata zuri'arka da mazauna cikin masarautar nan sai ta fi shiga tashin hankali sama da mu, za a zubar da jini kamar gobe. Wataƙila ma tarihi ya sake maimaita kansa, tun da na ganta na ji a jikina zuwanta na tafe da muhimman al'amura masu warware matsalolin da ke tsakaninmu." Cikin ɗaurewar kai Mai martaba ya furta. "Yanzu haka za mu zura ido kenan? Kuma ina fatan zamanta ba za ta cutar da ahalina da talakawana ba ko?" "Babu abin da za ta yi muku domin haifiyarta kafin ta mutu ta yi mata musayar jini da nata, yanzu haka zuri'arta nemanta suke ruwa a jallo don tana ɗauke da kambun da mutane da dama ke burin mallakarta. Matsafa da bokaya na yunwar samunta domin matuƙar suka same ta tamkar jari za ta zame musu, kuskuren mahaifiyarta kenan da ba ta ɓoye tauraruwarta ba. Kai dai abu ɗaya zan sanar da kai, kamar yadda kuke ganin al'amura mabambamta a masarautar nan kuma kuke tafiyar da ita a yadda ta zo muku wannan ma ku ɗauke ta a haka. Ko da wasa har iyalanka kada ka sanar da su wannan mushen San ba daga gare mu ba ne, domin faɗar taka na iya jefa duk mutanen cikin masarautar nan a cikin halaka. Ba ka sani ba ko akwai wanda yake burin mallakarta a cikin masarautar nan, to kuwa muddin ya ɓallo maka ruwa babu makawa sai kun gwammace kiɗa da karatu." Gwaron numfashi Sarki Abdul'aziz ya sauke sannan ya furta, "Na yi maka alƙawari ya kai wannan Dattijo mai cikakken karamci." Murmushi Dattijo Maharaz ya yii ya furta. "Na san ba za ka taɓa bijire mini ba don haka nake sake godiya da irin girmamawar da kake yi mini. Ina mai yi maka albishir da wani alheri na nan tafe cikin iyalinka, duhu zai yaye sannan haske zai mamaye ka da ahalinka wala'alla ma ya tsamo ka daga wata irin sarƙaƙiya. Sai dai kuma akwai ɓacin rai, ɓacin ran da ka iya kai ka ga yin nadama a lokacin da nadamar ba za ta yi maka amfani ba." Gaban Sarki Abdul'aziz ya yanke ya faɗi, cikin rashin kuzari ya ce. "Wanne irin haske ne wannan da ke iya tsunduma ni cikin nadama...?" "Ba haske ne zai kai ka ga nadama ba, sai dai ƙulli da murɗa-murɗar da ke kanka ce za ta yi tasirin ko kuma silar tafiyarka kan turbar nadama. A ƙarshe ina mai yi maka fatan alheri mai ɗorewa kai da iyalanka, na barka lafiya Sarkin sarakuna." Ko kaɗan ba haka Takawa ya so ba, ya so a ce ya samu damar sake tattaunawa da Dattijo Maharazu amma babu yadda ya iya haka ya taso daga gaban shurin ya koma kam gadonsa, ya ji ma shi kaɗai yana maimaita kalaman da Dattijo Maharaz ya furta masa. Ganin babu wata mafita ya sa ya shiga banɗaki ya gabatar da al'awala don gabatar da sallar Isha'i. Bai san dalili ba amma haka kawai wani lokacin yake jin ba ya sha'awar yin salloli a kan lokacinsu, sai ya kai zuciyarsa nesa yake gabatar da su. "Kamar yadda muka alƙarwarta muku mun tattauna da Dattijo Maharazu har ya kara yi mana fashin baƙi." Sarki Abdul'aziz ya yi maganar bayan ya tara fadawa da sauran masu sarautun cikin masarauta. Cike da girmamawa suke jinjin kai sannan ya ci gaba. "Gabaɗayanku ba baƙi ba ne dangane da waɗansu al'amura da ke faruwa a gidan nan kamar shan nono ranar juma'a, rafin tsamiya, busar sarewar shuri da sauran abubuwan da aka saba gani yau da kullin." Sai da ya ɗan tsahirta ya ci gaba da jawabi. "A don haka su ma waɗannan mushen Saniyar na daga mazauna cikin masarautar nan, kuma a tabbatar an gargaɗi talakawa a kan koda wasa kada wani ya yi gangancin aiwatar da wani ƙudiri game da shanun, abu ɗaya aka lamunce a duk ranar da aka yi tozali da su a tabbatar an kawar da su zuwa babban juji kamar yadda ake yi a baya." Surutu ne ya fara tashi sama-sama kowa ya fara tofa albarkacin bakinsa bayan doguwar tattauna Mai martaba ya shiga gida sannan kowa ya kama gabansa. A kullin lamarim larurar Fulani Babba ƙara ta'azzara take, abin da yake sake ɗaga mata hankali bai wuce yadda fitsarin da take yi ya ci gaba da bibiyarta har ta kai tana yinsa ido biyu, daga baya sai abin ya zame mata tamkar mai yoyon fitsari ba ta ɗaukan wani lokaci mai tsawo sai zanin jikinta ya jiƙe sharkaf. Da ta ayyana za ta nemi magani game da ciwon ko ta sanar da Sarki Abdul'aziz sai ta ji kanta ya yi nauyi lokaci ɗaya ta manta halin da take ciki, hatta ibada sau tari idan ta yunƙura da niyyar gabatar da sallah sai ta fara wasu-wasin sallar Azahar ce za ta yi ko La'asar. Wani lokacin har sai tambayi Bayinta ko su Khadija idan suna kusa da ita, a ɓangare ɗaya kuma duk ranar da muradin mijinta ya bijiro mata na son ƙeɓewa da shi to ranar haka za ta kwana tana mafarkin Takawa ya zo zai kusance ta ta ƙarfin tsiya kuma duk yunƙurinta na ƙin amince masa haka zai yi amfani da ita ta ƙarfin tsiya sannan ya ɗago yana sheƙa mata wata iriyar dariya. Duk ranar da ta yi wanna mafarkin idan ta wayi gari wuni za ta yi wani irin ruwa mai ɗoyi yana ta fita daga jikinta. Abin ɓoye kusan ya fito fili domin kusan duk Bayin masarautar sun fahimci Fulani Babba ba ta da kwana a wurin Mai martaba, sai dai jifa-jifa ya kan neme ta da rana ta je turakarsa su ɗan taɓa hira shi ma ba wata hirar kirki suke yi ba. Kusan abin sai ya haɗe mata goma da ashirin ga ciwon Abubakar da kullin gaba yake yi ga ita ma nata, domin a wannan lokacin Abubakar bai ciki bambamce tsabar abinci ba da ƙasar da yake rayuwa a cikinta, kowanne ya samu danƙarawa cikinsa yake yi. Ya zama tamkar mujiya hatta bayin da ke yi masa hidima a tsorace suna yi masa su kammala, don sau babu adadi yana kama Bayi idan sun shiga bashi abinci ko gyra shi ya riƙa cizgar gashin kansu yana cinyewa. Dalilin haka ya sa Dogarawa ke ɗaure shi kafin a shiga ɗakin, hatta su kansu sai sun yi da mugun gaske. A 'yan kwanakin waɗansu irin mafarkai take yi na Abubakar wai yana zaune sai kuma ta ga wani mai tsananin kama da shi ya zo yana jan hannunsa a kan ya miƙe su tafi. A mafarkin da ta yi na ƙarshe kafin ya kama hannun Abubakar sai ya isa gare ta ya furta mata. "Me ya sa bakya sona kika bari na yi nisa da ke, ni ma ɗanki ne don Allah ki dawo da ni gare ki." Hawayen idanunta ta share ta furta. "Ta yaya uwa za ta ƙi abin cikinta ina matuƙar ƙaunarka..." Kalamanta suka katse a lokacin da ta ga ya riƙo hannu Abubakar ya miƙe tsaye tun yana tangal-tangal har ya take ƙafafuwansa, cike da murna ta fara bin su tana ƙwala musu kira amma kafin ta isa sun ɓace wa ganinta." Firgigit ta farka tana sauke ajiyar zuciya, ta yi mamakin nannauyan baccin da ya yi awon gaba da ita da tsakar rana. Sau tari ta kan yi mafarkin ta haifi tagwayen jariri duka maza, amma da ta tashi ɗaukansu sai ta nemi ɗaya ta rasa. "Barka da tashi uwar gijiyata." Mai gado ta furta da ke gefe zaune a gabanta. "Mai gado na jima ina bacci ko?" "Ranki shi daɗe ai hutu ne kika samu uwar gijiyata." Fulani babba ta matuƙar aminta da Mai gado saboda yanayin riƙon amana da rashin kwaramniyarta. Sai da Fulani Babba ta tashi zaune sannan ta tattara hankalinta wuri ɗaya ta furta. "Mai gado wata tambaya gare ni." "Ina sauraronki ranki shi daɗe?" "Don Allah mace na iya haihuwa ba tare da tana cikin hayyacinta ba har ta manta da abin da ta haifa?" Tafiya suke cikin baƙin dajin da ke cike da ban tsoro, firgici da tashin hankali. Kukan tsuntsayen da ke dajin ya isa ya hautsina kwanyar mai tafiya a cikinsa. Bakin wani kogo suka shiga suna tafe suna faɗin. "Mu masu bin umarninka ne sau da ƙafa." Jakadiya ce a gaba sai Fulani Umaima da ke biye da ita har suka ƙarasa bakin wata ƙatuwar rijiya da wani Boka ke zaune a saman ruwanta, a madadin ruwa a cikin rijiyar wuta ce ke ci ganga-ganga. Tsirara yake babu sutura a jikinsa, duk da dare ne amma kogon dutsen a haske yake tarwai kamar rana da wani sihirtaccen haskensa. "Barka da aiki Boka Shaddas, ka yi naka ka yi na kowa duk wanda ya ja da kai ya halaka." Faffaɗar fuska gare shi kamar faranti mai ɗauke da ƙaton hancin, jajayen idanu da jan leɓe. Wata irin dariya ya saki mai kama da kukan jaki." Ku dakata a nan me neman biyan buƙatar ita za ta ƙaraso." Ƙatuwar muryarsa ta ƙaraɗe cikin kogon dutsen, jiki na rawa Fulani Umaima ta fara takawa da sauri har ta isa gare shi. "Daga yau za ki daina sallah da wanka tsarki har tsawon shekara guda, ki tabbata duk abin da muka umarce ki za ki aiwatar mana kuma ki sa a ranki bauƙatarki tamkar ta biya ne." Fulani Umaima ta furta. "Duka na amince, matuƙar buƙatata za ta biya ko me kake so zan aiwatar da shi." A karo na biyu ya sake sakin dariya mara daɗin saurare. "Ba ma buƙatar tukwicin komai sai na jinin mahaifiyarki, mahaifinki da ɗan cikinki. Sannan kuma dole ne mu lashi zumar jikinki ta hanyar kusanctarki. Matuƙar kika aiwatar da wannan ina mai yi miki rantsuwa da sirrin tsafi da sihirina a duniyar nan babu abin da za ki nema a wurin mu ya gagare ki." SHU'UMAR MASARAUTA 14 *MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE* *SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?* *TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI'IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHEƘI KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI* *SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA'A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA'IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA'IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA* *Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.* 👉 *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.* *1. Supplements na gyaran jiki ciki da waje* *2. Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba* *3. Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya* *4. Supplements na karawa fata kyau da sheki glowing skin* *5. Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci* *6. Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki* *7. Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu* *8. Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.* *9. Supplements na karin ni'ima da dandano da tightening ciki da waje* *10. Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc* *11. Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement* *12. Supplements na gyaran HQ ciki da waje* *13. Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton* *14. Supplement na whitening/glowing skin* *15. Supplement for Acne, dark spots remover* *Da duk wasu nau'in supplement da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158* *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Jin takun tafiyar su ya sa gaban Kamalu ya ci gaba da faɗuwa jikinsa ya ɗauki karkarwa, can jikin bango ya sake maƙalewa yana fatan kada Allah ya sa su cim masa don shi kansa ya san idan suka gan shi tsaf za su iya kashe shi, ba su yi tsammani ba suka ga Jakadiya ta faɗo cikin soron hannunta ɗauke da aci bal-bal. Tana hango su Galadima ta kalle su da mamaki, "Yautai mugun tsuntsu ma sha miyarka sai ya yi dare.Daga ina kuke da tsohon daren nan?" Ta yi maganar tana kallon Ciroma. "Tararuwa mai wutsiya ganinki ba alheri, ina zuwa haka?" A yatsine ta kalle shi. "Jikina yana ba ni akwai ƙullin da kuke ɗaurawa don banza ba ta kai zomo kasuwa!" Ciroma ya wayance."Daga cikin gida muke ke fa ina za ki?" "Daga wurin Fulani babba nake zan kai saƙo wurin Abubakar." Lokaci ɗaya suka kwashe da dariya jin an ambaci sunan Abubakar, Jakadiya ta gimtse tata dariyar ta furta. "Ganin gida kare kan zagi kura amma ba a daji ba, na tabbaya ɗayanku bai isa yin dariya nan a gaban amale ba." Daga haka ta yi gaba a fili ta nuna tamkar ta ji haushin dariyar da suka yi, ita ma kuma a ƙasan zuciyarta dariyar take yi. Galadima da Ciroma suka duba wurin da suke zargin wani na laɓe amma babu kowa, sakamakon tun shigar Jakadiya Kamalu ya sulale ba tare da sun fahimta ba. Wannan ta sa suka ajiye ragowar maganar da suke yi ba tare da sun ƙarasa ba. Yanayin da Inna wuro ta ga Kamalu a ciki ya sa ta zaunar da shi a gefenta, ƙura masa idanu ta yi lokaci ɗaya ta fahimci tashin hankalin da ke tattare da shi. "Me yake damunka Kamalu?" Da yake a wannan lokacin Inna wuro sun samu 'yancin kansu ta hanyar mazajensu da suka yi ruwa suka yi tsaki suka haɗa bulo suka gina musu ɗakuna kamar yadda suka ga sauran bayin sun killace iyalansu. Jiki a sanyaye Kamalu ya furta, "Inna don Allah kada ki min faɗa idan na gaya miki." Inno wuro ta gyaɗa masa kai. "Kada ka damu Kamalu ba zan maka komai ba." "Inna bayan na kai wa Shamaki saƙonsa ina dawowa na ji wasu suna ce wa za su kashe mai martaba..." Tun bai ƙarasa maganar ba ta sa hannu ta toshe masa baki, take jikinta ya ɗauki karkarwa. Ta yi ƙasa da murya ta furta, "Babu ruwanka da kowa ka ji Kamalu, daga yau idan ka sake jin wasu na irin wannan maganar ka yi tafiyarka ka ji." Kamalu ya gyaɗa mata kai sannan ya hau shimfiɗarsa ya kwanta. Jawahir ta yi wayo sosai yarinyar ɓul-ɓul da ita gwanin birgewa, musaman da take samun kulawa a ɓangaren Fulani Babba, sai dai abin da har kwanan gobe ke faruwa bai fasa ba dangane da ganin gawar saniyar da ake wayar gari da ita duk ranar asabar da asuba. Fadar Sarki Abdul'aziz ta ƙayatu matuƙa da kayan alatu iri-iri irin na wancan lokacin. Waziri, Galadima, Ciroma da Malam Liman zaune suke a gabansa sai Dogarawan da ke tsaron ƙofa da sauaran Fadawan da ke zaune daga can gefe. "Dalilin da ya sa muka tara ku saboda wata muhimmiyar magana da ke ci mana tuwo a ƙwarya sakamakon firgici da talakawanmu suke ciki." Sarki Abdul'aziz ya yi maganar cike da izzar mulki. Shiru suka yi gabaɗaya suka sauraronsa ya ci gaba da cewa. "Akwai zancan mushen saniya da ake gani duk wayewar garin asabar a sashen Bayi, wanda da farko da aka sanar mana ba mu ɗauki abin da muhimmanci ba sakamkon al'amuran almara da muka saba gani yau da kullin a cikin masarautar nan, har sai da muka ga abin yana neman zarce ƙa'ida. Duk cikin dobobbin da Allah ya albarkace mu da su mun sa a ƙidaya su amma babu guda ɗaya da muka ji labarin ta yi ƙwarzane ballantana ta yi mushe, shin mene ne mafita kuma me kuke ganin yana haifar da haka?" Wani Dogari daga bayan Sarki ya russuna cikin girmamawa sannan ya furta. "Allah ya taimaki amale, ɗawisu mai yawan ado sikari ba ka yi farin banza ba." Daga gefe Waziri ya gyara zama sannan ya fara magana. "Allah ya taimake ka, ni ina ganin wannan ba abin mamaki ba ne duba da sanin wannan masarautar ba irin kowacce masarauta ba ce, a tawa fahimtar a ji daga bakin makusantan gidan na ainihi idan ya so daga baya sai a san abin yi ko a nemi shawararsu. Amma fa a harsashena kenan ranka shi daɗe." Lokaci ɗaya gabaɗaya suka aminta da shawarar Waziri, Sarki Abdul'aziz shi ma ya aminta da haka dalilin da ya sa ya yanke shawarar jin ta bakin zuri'ar da ke rayuwa a daular shuri. Daga haka suka shiga tattaunawa a kan abin da ya da ce, dangane da harkokin masarautar. Zaune yake a can cikin turakarsa a gaban ƙaton shurin ya tanƙwashe ƙafafuwansa sannan ya ɗora hannunsa na hagu a kan shurin ya furta. "Assalamu alaikum. Gafaranku dai ya ku ahalin cikin masarautar nan?" Daga cikin shurin ya ji an yi gyaran murya sannan aka amsa masa. "Wa'alaikas salam. Barkanka dai Sarki Abdul'aziz me kuma iyalaina suka yi maka? Don rabon da ka kawo mini ziyara har na manta." Da yake a wasu shekaru da suka wuce Sarki Abdul'aziz ya taɓa kai ƙarar jikan Dattijon sakamakon wata ɓarna da ya yi masa. "Ba ƙara na kawo ba Dattojo Maharaz, na zo ne dangane da wani muhimmin abu da yake faruwa a cikin masarautar nan." Murmushi aka yi daga cikin shurin sannan Maharaz ya ce, "Ba tun yau ba miyagun al'amura da ƙazaman abubuwa na faruwa a cikin masarautar nan kuma suna ta ci gaba da faruwa, sai dai kuma ban san wanne irin bacci kake yi ba Abdul'aziz." Takawa ya yi jim ba ya son ya bada ƙofar da za su haɗa shi da mutane don haka ya shashantar da zancen da cewar. "Wannan wata muhimmiyar magana ce..." "Dangane da Saniya ko?" Dattijo Maharaz ya katse Sarki Abdul'aziz don ya lura ba ya san sanin matsalolin da ya ɗauko masa waɗanda ke faruwa a cikin masarauta. Sai da Dajjito Maharaz ya numfasa sannan ya ci gaba da cewa. "Waɗannan saniyoyin da suke mushe ba daga gare mu suke ba, sun fito daga cikin zuri'ar RUMZU su suke shayar da 'yarsu cikin fushi, kuma idan har hakan bai zama illa ko wani tashin hankali ba kada ka yi gaggawa a kansu. Suna da matuƙar hatsari fiye da tunaninka, yanzu haka 'yarsu na cikin masarautar nan sakamakon zanen ƙaddararta da ya gindayo ta kanta har ta faɗo cikin masarautar da duk faɗin duniya babu shu'umar masarauta kamarta. Hasali ma akwai daɗaɗɗiyar gaba a tsakanin zuri'ata da su zuri'ar RUMZU, sai dai hakan ba zai sa mu ɗauki matakin a kan jikarsu ba, domin har a yanzu ita ba ta san asalin abin da ya faru ba ka ga kamar mun zalince ta ne. Kuma idan har muka taɓo su na tabbata zuri'arka da mazauna cikin masarautar nan sai ta fi shiga tashin hankali sama da mu, za a zubar da jini kamar gobe. Wataƙila ma tarihi ya sake maimaita kansa, tun da na ganta na ji a jikina zuwanta na tafe da muhimman al'amura masu warware matsalolin da ke tsakaninmu." Cikin ɗaurewar kai Mai martaba ya furta. "Yanzu haka za mu zura ido kenan? Kuma ina fatan zamanta ba za ta cutar da ahalina da talakawana ba ko?" "Babu abin da za ta yi muku domin haifiyarta kafin ta mutu ta yi mata musayar jini da nata, yanzu haka zuri'arta nemanta suke ruwa a jallo don tana ɗauke da kambun da mutane da dama ke burin mallakarta. Matsafa da bokaya na yunwar samunta domin matuƙar suka same ta tamkar jari za ta zame musu, kuskuren mahaifiyarta kenan da ba ta ɓoye tauraruwarta ba. Kai dai abu ɗaya zan sanar da kai, kamar yadda kuke ganin al'amura mabambamta a masarautar nan kuma kuke tafiyar da ita a yadda ta zo muku wannan ma ku ɗauke ta a haka. Ko da wasa har iyalanka kada ka sanar da su wannan mushen San ba daga gare mu ba ne, domin faɗar taka na iya jefa duk mutanen cikin masarautar nan a cikin halaka. Ba ka sani ba ko akwai wanda yake burin mallakarta a cikin masarautar nan, to kuwa muddin ya ɓallo maka ruwa babu makawa sai kun gwammace kiɗa da karatu." Gwaron numfashi Sarki Abdul'aziz ya sauke sannan ya furta, "Na yi maka alƙawari ya kai wannan Dattijo mai cikakken karamci." Murmushi Dattijo Maharaz ya yii ya furta. "Na san ba za ka taɓa bijire mini ba don haka nake sake godiya da irin girmamawar da kake yi mini. Ina mai yi maka albishir da wani alheri na nan tafe cikin iyalinka, duhu zai yaye sannan haske zai mamaye ka da ahalinka wala'alla ma ya tsamo ka daga wata irin sarƙaƙiya. Sai dai kuma akwai ɓacin rai, ɓacin ran da ka iya kai ka ga yin nadama a lokacin da nadamar ba za ta yi maka amfani ba." Gaban Sarki Abdul'aziz ya yanke ya faɗi, cikin rashin kuzari ya ce. "Wanne irin haske ne wannan da ke iya tsunduma ni cikin nadama...?" "Ba haske ne zai kai ka ga nadama ba, sai dai ƙulli da murɗa-murɗar da ke kanka ce za ta yi tasirin ko kuma silar tafiyarka kan turbar nadama. A ƙarshe ina mai yi maka fatan alheri mai ɗorewa kai da iyalanka, na barka lafiya Sarkin sarakuna." Ko kaɗan ba haka Takawa ya so ba, ya so a ce ya samu damar sake tattaunawa da Dattijo Maharazu amma babu yadda ya iya haka ya taso daga gaban shurin ya koma kam gadonsa, ya ji ma shi kaɗai yana maimaita kalaman da Dattijo Maharaz ya furta masa. Ganin babu wata mafita ya sa ya shiga banɗaki ya gabatar da al'awala don gabatar da sallar Isha'i. Bai san dalili ba amma haka kawai wani lokacin yake jin ba ya sha'awar yin salloli a kan lokacinsu, sai ya kai zuciyarsa nesa yake gabatar da su. "Kamar yadda muka alƙarwarta muku mun tattauna da Dattijo Maharazu har ya kara yi mana fashin baƙi." Sarki Abdul'aziz ya yi maganar bayan ya tara fadawa da sauran masu sarautun cikin masarauta. Cike da girmamawa suke jinjin kai sannan ya ci gaba. "Gabaɗayanku ba baƙi ba ne dangane da waɗansu al'amura da ke faruwa a gidan nan kamar shan nono ranar juma'a, rafin tsamiya, busar sarewar shuri da sauran abubuwan da aka saba gani yau da kullin." Sai da ya ɗan tsahirta ya ci gaba da jawabi. "A don haka su ma waɗannan mushen Saniyar na daga mazauna cikin masarautar nan, kuma a tabbatar an gargaɗi talakawa a kan koda wasa kada wani ya yi gangancin aiwatar da wani ƙudiri game da shanun, abu ɗaya aka lamunce a duk ranar da aka yi tozali da su a tabbatar an kawar da su zuwa babban juji kamar yadda ake yi a baya." Surutu ne ya fara tashi sama-sama kowa ya fara tofa albarkacin bakinsa bayan doguwar tattauna Mai martaba ya shiga gida sannan kowa ya kama gabansa. A kullin lamarim larurar Fulani Babba ƙara ta'azzara take, abin da yake sake ɗaga mata hankali bai wuce yadda fitsarin da take yi ya ci gaba da bibiyarta har ta kai tana yinsa ido biyu, daga baya sai abin ya zame mata tamkar mai yoyon fitsari ba ta ɗaukan wani lokaci mai tsawo sai zanin jikinta ya jiƙe sharkaf. Da ta ayyana za ta nemi magani game da ciwon ko ta sanar da Sarki Abdul'aziz sai ta ji kanta ya yi nauyi lokaci ɗaya ta manta halin da take ciki, hatta ibada sau tari idan ta yunƙura da niyyar gabatar da sallah sai ta fara wasu-wasin sallar Azahar ce za ta yi ko La'asar. Wani lokacin har sai tambayi Bayinta ko su Khadija idan suna kusa da ita, a ɓangare ɗaya kuma duk ranar da muradin mijinta ya bijiro mata na son ƙeɓewa da shi to ranar haka za ta kwana tana mafarkin Takawa ya zo zai kusance ta ta ƙarfin tsiya kuma duk yunƙurinta na ƙin amince masa haka zai yi amfani da ita ta ƙarfin tsiya sannan ya ɗago yana sheƙa mata wata iriyar dariya. Duk ranar da ta yi wanna mafarkin idan ta wayi gari wuni za ta yi wani irin ruwa mai ɗoyi yana ta fita daga jikinta. Abin ɓoye kusan ya fito fili domin kusan duk Bayin masarautar sun fahimci Fulani Babba ba ta da kwana a wurin Mai martaba, sai dai jifa-jifa ya kan neme ta da rana ta je turakarsa su ɗan taɓa hira shi ma ba wata hirar kirki suke yi ba. Kusan abin sai ya haɗe mata goma da ashirin ga ciwon Abubakar da kullin gaba yake yi ga ita ma nata, domin a wannan lokacin Abubakar bai ciki bambamce tsabar abinci ba da ƙasar da yake rayuwa a cikinta, kowanne ya samu danƙarawa cikinsa yake yi. Ya zama tamkar mujiya hatta bayin da ke yi masa hidima a tsorace suna yi masa su kammala, don sau babu adadi yana kama Bayi idan sun shiga bashi abinci ko gyra shi ya riƙa cizgar gashin kansu yana cinyewa. Dalilin haka ya sa Dogarawa ke ɗaure shi kafin a shiga ɗakin, hatta su kansu sai sun yi da mugun gaske. A 'yan kwanakin waɗansu irin mafarkai take yi na Abubakar wai yana zaune sai kuma ta ga wani mai tsananin kama da shi ya zo yana jan hannunsa a kan ya miƙe su tafi. A mafarkin da ta yi na ƙarshe kafin ya kama hannun Abubakar sai ya isa gare ta ya furta mata. "Me ya sa bakya sona kika bari na yi nisa da ke, ni ma ɗanki ne don Allah ki dawo da ni gare ki." Hawayen idanunta ta share ta furta. "Ta yaya uwa za ta ƙi abin cikinta ina matuƙar ƙaunarka..." Kalamanta suka katse a lokacin da ta ga ya riƙo hannu Abubakar ya miƙe tsaye tun yana tangal-tangal har ya take ƙafafuwansa, cike da murna ta fara bin su tana ƙwala musu kira amma kafin ta isa sun ɓace wa ganinta." Firgigit ta farka tana sauke ajiyar zuciya, ta yi mamakin nannauyan baccin da ya yi awon gaba da ita da tsakar rana. Sau tari ta kan yi mafarkin ta haifi tagwayen jariri duka maza, amma da ta tashi ɗaukansu sai ta nemi ɗaya ta rasa. "Barka da tashi uwar gijiyata." Mai gado ta furta da ke gefe zaune a gabanta. "Mai gado na jima ina bacci ko?" "Ranki shi daɗe ai hutu ne kika samu uwar gijiyata." Fulani babba ta matuƙar aminta da Mai gado saboda yanayin riƙon amana da rashin kwaramniyarta. Sai da Fulani Babba ta tashi zaune sannan ta tattara hankalinta wuri ɗaya ta furta. "Mai gado wata tambaya gare ni." "Ina sauraronki ranki shi daɗe?" "Don Allah mace na iya haihuwa ba tare da tana cikin hayyacinta ba har ta manta da abin da ta haifa?" Tafiya suke cikin baƙin dajin da ke cike da ban tsoro, firgici da tashin hankali. Kukan tsuntsayen da ke dajin ya isa ya hautsina kwanyar mai tafiya a cikinsa. Bakin wani kogo suka shiga suna tafe suna faɗin. "Mu masu bin umarninka ne sau da ƙafa." Jakadiya ce a gaba sai Fulani Umaima da ke biye da ita har suka ƙarasa bakin wata ƙatuwar rijiya da wani Boka ke zaune a saman ruwanta, a madadin ruwa a cikin rijiyar wuta ce ke ci ganga-ganga. Tsirara yake babu sutura a jikinsa, duk da dare ne amma kogon dutsen a haske yake tarwai kamar rana da wani sihirtaccen haskensa. "Barka da aiki Boka Shaddas, ka yi naka ka yi na kowa duk wanda ya ja da kai ya halaka." Faffaɗar fuska gare shi kamar faranti mai ɗauke da ƙaton hancin, jajayen idanu da jan leɓe. Wata irin dariya ya saki mai kama da kukan jaki." Ku dakata a nan me neman biyan buƙatar ita za ta ƙaraso." Ƙatuwar muryarsa ta ƙaraɗe cikin kogon dutsen, jiki na rawa Fulani Umaima ta fara takawa da sauri har ta isa gare shi. "Daga yau za ki daina sallah da wanka tsarki har tsawon shekara guda, ki tabbata duk abin da muka umarce ki za ki aiwatar mana kuma ki sa a ranki bauƙatarki tamkar ta biya ne." Fulani Umaima ta furta. "Duka na amince, matuƙar buƙatata za ta biya ko me kake so zan aiwatar da shi." A karo na biyu ya sake sakin dariya mara daɗin saurare. "Ba ma buƙatar tukwicin komai sai na jinin mahaifiyarki, mahaifinki da ɗan cikinki. Sannan kuma dole ne mu lashi zumar jikinki ta hanyar kusanctarki. Matuƙar kika aiwatar da wannan ina mai yi miki rantsuwa da sirrin tsafi da sihirina a duniyar nan babu abin da za ki nema a wurin mu ya gagare ki." SHU'UMAR MASARAUTA 15 *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Yanayin da Fulani take ciki na rashin Ruƙayya ya sake tunzura ta game da Bayinta don haka kowannensu yake kaffa-kaffa da shayin yin abin da zai saɓa mata. Ko motsi kaɗan idan ka yi matuƙar bai yi mata ba nan take za ra zartar maka da mummunan hukunci. Dama yaya lafiyar kura ballantana ta ci nama. Lokacin da mutanen Masarautar mahaifanta suka ƙarasa Masarautar Huddam domin yin gaisuwa sai Bayinta suka samu sauƙi game da tsangwama da ƙyarar da suke fuskanta. Ranar larabar da Boka Shaddas ya umarce ta a ranar ne ta je turakar Sarki Abdul'aziz don ta aiwatar da ƙudurinta, ta ji daɗi matuƙa da ta samu turakar tashi ba ya nan. Da sauri ta ɓarɓada maganin a saman gadon sa ta yadda ƙwayar ido ba za ta yi saurin fahimtar komai ba. Ta kewaya banɗaki ta haɗa masa ruwan wanka tana fitowa ta ji shigowarsa, cikin kissa ta sakar masa murmushi. Martanin murmushi ya mayar mata don bai manta ba rabon da ya ga fara'arta tun kafim rasuwar Ruƙayya, ya rungoma ta jikinsa suka zauna a gefen gado yana kallon fuskarta da ta yi fayau saboda ramar da ta yi. "Sarkina barka da hutawa, da fatan kana cikin walwala da farinciki?" Tallafota ya yi suna fuskantar juna. "Sarauniyata kin fi kyau a haka don Allah ki cire komai daga ranki. A lokacin da Allah ya ba mu Ruƙayya bai shawarce mu ba, don haka da zai karɓe ta ba zai yi shawara da mu na. In shaa Allah, zai ƙara azurta mu da wasu masu albarka a nan gaba." Take idanunta suka ciko da ƙwalla, ganin haka ya sa ya goge mata yana kwantar da ita a ƙirjinsa. "A baya ne nake kewar Ruƙayya Sarkina domin shaƙuwar ɗa da mahaifi daban take, ta fi gaban duk mai tunani. Babu wacce za ta fahimci hali da damuwar da nake ciki mahaifiya kamar. Damuwata ta yaye ƙunci ya kau, a yanzu tun da ina da kai ba za ka sake ganin ƙwalla a saman fuskata ba, ka zame mini taurarom da ke hasken birnin zuciyata don kawar da duhun da ya ratsa ta na 'yan kwanakin d suka shuɗe. Allah ya ƙara lafiya da nisan kwana Sadaukina, kulawarka a gare ni na ƙara mini ƙwarin gwiwa ɗari bisa ɗari." Ya ji daɗin kalamanta ƙwarai don haka ya ci gaba da bubbuga bayanta, babu jimawa hirar ta su ta fara sauya salo har Fulani Umaima ta ribace shi suka gudanar da mu'amala a saman shimfiɗar kamar yadda boka Shaddas ya gaya mata. A wannan karon Takawa ne ya fara zuwa banɗaki ya tsaftace jikinsa da ruwan da Fulani ta haɗa masa wanda ya ji magani da sihirtattun turaruka masu ƙamshi, bayan ya fito ita ma ta faɗa ta yi wanka ta dawo kusa da shi ta kwanta. "Ki taso mu je bakin bishiyar kukar can kada ki sa na yi asarar kuɗina Sailuba, ke fa idan kika sa kanki kin fiye gardama da taurin kai." Jakadiya ta yi maganar ƙasa-ƙasa ganin Sailuba na ɓata fuska. "Inna ya za a yi a ce na tuɓe a bakin bishiya da tsohon daren nan don Allah, ni wallahi kunya nake ji ba zan iya ba." "Sakaryar banza da wofi, wannan ita kaɗai ce damar da ke gaban kuma idan ta wuce ta tafi kenan har gaban abada. Matuƙar kika bi umarnina nan da ɗan wani lokaci kema za ki zama Fulani a gidan wallahi ko tantama ba na yi, sai kin kasance matar Takawa kamar yadda Umaima ke ji da kanta." Jin haka ya sa Sailuba ta miƙe da sauri, cikin sanɗa suka nufi bayan ɗakunan Bayi, a bakin wata bishiyar kuka suka tsaya sai da Jakadiya ta kalli hagu da dama sannan ta kunto garin maganin ta juye shi a butar gabanta da ke cike da ruwa. Daga can jikin katanga Uwar tuwo ce a raɓe tana leƙen Jakadiya cike da mamaki, dawowarta babu wuya daga banɗaki ta ji kalaman da Jakadiya take yi wa Sailuba. Tana nan tsaye har Sailuba ta tuɓe kayanta Jakadiya ta fara watsa mata ruwan maganin har ya gama gauraye jikinta gabaɗaya, tana ganin sun tunkaro wurin ta yi saurin komawa ta faɗa ɗakinta. Jakadiya ce ta fara wucewa sai Sailube da ke lulluɓe kamar sabuwar amarya. Uwar tuwo na raɓe a jikin labulenta ta ga giftawarsu. Jinjina kai ta shiga yi cike da mamakin Jakadiya, wani tunani ya gangaro cikin kwanyarta lokaci ɗaya ta saki wani shu'umin murmushi mai ɗauke da wasu ma'anoni. "Boka Bamaguje ya sanar da ni kin janye jikinki daga wurinsa, sai dai duk yadda na so jin dalilin haka abin ya faskara daga bakinsa. Me ya sa kike son jefa kanki a ƙangin rayuwar da ba za ta fisshe ki da komai ba, kin san muhimmanci Bamaguje kuwa da kike son watsa masa ƙasa a ido?" Mahaifiyar Fulani Umaima ta rattabo kalamanta cikin ɓacin rai. Fulani Umaima ta haɗe fuska, da farko kamar ta sanar mata abin da ya haɗa su, sai kuma ta ce. "Na samu wani sabon boka ne kuma aikinsa tamkar yankan wuƙa haka yake." "Ai shi kenan tun da haka kika zaɓa kowa rai ya yi wa daɗi ba ya mai shi ba, ni kaina ba don taimakon Bamaguje ba kin san ni da ke da ba mu samu wannan fadar haka ba." Fulani Kilishi wato mahaifiyar Fulani Umaima ta faɗa, don ba ta son ja da nisa saboda ko kaɗan ba ta san abin da za ɓata mata rai. Bayan kwana biyu tuni kowa ya watse ya rage sai ainihin mutanen cikin masarautar. Wataranar Juma'a da yamma Jakadiya ɗauke da tiren kayan marmari ita da Sailuba suka nufi sashen Takawa, fuskar Sailuba ta sha kwalliya kamar wacce za ta gasar kyau. A lokacin da suka shiga yana zaune yana rubuta wasiƙar da Sarkin Gumel ya turo masa a game da wani kasuwanci da yake son su fara ƙullawa, Jakadiya ce ta ƙarasa gabansa ta dire tiren hannunta. "Barka da hutawa Uban gidana, farincikin talakawa da marayu. Hatta masu iyayen ma ka riga da ka gama musu komai. Allah ya ja zamaninka ya tsare gabanka da bayanka, gaba salamun baya salamun ɗan toron giwa." Sai da ya ƙarasa rubutun da yake ba tare da ya kalle ta ba ya furta, "Jakadiya an yi sara a kan gaɓa, don yanzu muke shirin aikawa a kira mana ke." Jakadiya ganin ba ya kallonsu ya sa ta ɗan zunguro Sailuba da ta yi galala tana ƙare wa falon hutawar Sarki Abdul'aziz, da ya sha kayan ado da ƙyalƙyali iri-iri. "Allah ya baka yawan rai muna godiya da wannan nuna yabawar." Sai a lokacin Sailuba ta ɗan sake maƙe murya ta ce. "Barkanka da hutawa Sarkin sarakai, fari mai farar aniya bangon sikari a bika a lasa idan babu kai a zubar da ƙwalla." Jin sauyin murya a kan wacce ya saba ji ya sa ya ɗago a hankali ya dubi wurin da Sailuba take, ganin haka ya sa a yangance Sailuna ta isa gabansa da ragowar kwandon kayan marmarin ta ajiya tana faɗin. "Idan Mai martaba ya lamunce shin zan iya yanka masa kayan marmarin a yanzu ko sai zuwa an jima." Wata irin ajiyar zuciya ya sauke har lokacin idanunsa ƙirr a kan Sailuba, mamakinsa ɗaya bai wuce yadda ƙaramar yarinya ta iya wassafa kalaman ban girma a mai girman matsayi kamarsa ba. "Idan kuma Mai martaba ba ya buƙata zan jira a ƙofa har zuwa lokacin da zai buƙaci a yanka masa. A gafarce ni idan akwai kuskure a kalamaina ranka shi daɗe." Sailuba ta ƙarasa maganar tana sunkuyar da kai ƙasa kamar sabuwar amaryar da ke gaban surukarta. "Muna da buƙatar kayan marmarin." Sarki Abdul'aziz ya furta a takaice, sannan ya janye idanuwansa da ƙyar ba don zuciyarsa ta daina azalzalarsa a kanta ba. Jakadiya ta lura da yanayin da Mai martaba ya shiga don haka ta saki murmushin yin nasara a fakaice. Ta russuna tana faɗin, "Ranka shi daɗe a yi mini izini na tato maka ruwan 'ya'yan ibini." Gyaɗa mata kai ya yi sannan ta fice daga falon zuciyarta fes. Hakan da Jakadiya ta yi ne ya sa Sailuba ta samu damar yanka kayan marmarin tana yi tana karairaya cike da jan hankali. A fakaice Takawa yake satar kallonta da ta ɗago sai ya ɗauke kansa ya ci gaba da abin da yake yi, suna nan zaune Fulani Umaima ta shiga cike da isa da ƙasaita. Ganin Fulani Umaima ya sa zuciyar Sailuba ta yi baƙi ranta ya yi mummunan ɓaci, a ciki-ciki ta dubi Fulani Umaima ba tare da ta rissina ba ta ce. "Barka da shigowa." Galala ta yi tana kallon Baiwa Sailuba don ba ta jin akwai wanda ya taɓa yi mata irin wannan gaisuwar ta rashin ladabi. "Dakata!" Cak! Sailuba ta tsaya tana kallonta kanta a ƙasa. "Lokaci na nan zuwa da za mu fara haɗa kafaɗa, ba dai taƙamarki Takawa ba. Da sannu sa na mayar da ke bora fiye da yadda kika mayar da kishiyarki." Sailuba ta yi maganar a cikin zuciyarsa. "Ko mahaifiyarki ta cancanci ki gaishe ta a haka ballantana ni?" Fulani Umaima ta faɗa a wulaƙance. Shiru ya ratsa ba tare da Sailuba ta amsa ba, kuma ba ta jin za ta iya amsa mata don gani take a yanzu marabarsu kaɗan ya rage. "A ba mu wuri muna buƙatar keɓewa." Sarki Abdul:aziz ya furta ba don ya gaji da zaman Sailuba ba sai dai don ba zai juri ganin yadda Fulai Umaima take daka mata tsawa a gabansa ba. "Yadda kake so haka za a yi ingarman mazajen sarakuna, sarkin sarakai mai riƙe da kambun da babu masarautar da ke ɗauke da shi a kaf faɗin nahiyar nan. Ka huta cikin aminci ranka shi daɗe hasken talakawa, na barka lafiya bujimi namijin fama." Cikin wata irin murya mai fusgar hankali Sailuba ta yi maganar sannan ta miƙe kamar ba za ta taka ƙasa ba cikin kariraiya ta fice daga ɗakin. Daga Takawa har Fulani Umaima da ido suka raka ta sai dai kowa da manufar kallon da yake yi mata. Fulani Umaima kallon mamakin kalaman yarinyar ta yi waɗanda duk mai hankali idan ya saurara zai fahimci sannu a hankali take isar da saƙonta. Shi kuma Takawa kallon shauƙi da birgewa yake bin Sailuba da shi, take zuciyarsa ta fara raya masa wani abu. Ganin har lokacin hankalinsa na kan ƙofa ya sa Fulani Umaima ta zungure shi tana faɗin. "Ya dai ranka shi daɗe, me yake faruwa?" "Kin san fa su irin waɗannan bayin sai ana bin su a sannu don gaskiya da sauran ƙuruciya a tattare da su." Mai martaba ya yi maganar cikin wayancewa. Ba don Sailuba baiwa ba ce kuma ta san ko a mafarki ba sa'ar tsaran Takawa ba ce da tuni Fulani Umaima ta dasa wani zargi a kanta, amma a cikin zuciyarta take ayyana dole za ta gyara wa yarinyar zama don ta ga raini ƙarara a ƙwayar idonta. Sannu a hankali rayuwa ta ci gaba da tafiya, tun Jakadiya na jan Sailuba a ɗaiɗaikun ranaku zuwa sashen Takawa har ya zamana idan ita kaɗai ta je sai ya sa an kira masa ita, haka kawai yarinyar taka birge shi musamma da daɗaɗan kalamanta da kuma ƙuruciyarta. Fulani Umaima ko kaɗan ba ta san wainar da ake toyawa ba, don haka tun tuni ta manta da shafinta ta ci gaba da harkokin gabanta. Sai dai ta lura da ɗan ja baya da ta yi Mai martaba ya yi bai cika aikowa kiranta ta taya shi hira ba kamar yadda yake yi a baya. Jawahir ta yi wayo sosai don har ta fara tafiya da ƙafafuwanta a lokacin shekararta ɗaya har da rabi, tana da matuƙar shiga rai da saurin sabo da mutane ta saba sosai da su Khadija don a yanzu wani lokacin har kwana take a wurinsu. Ta kama abinci sosai babu abincin da ba ta ci sai dai kuma wani abu da yake ciwa Mai gado tuwo a ƙwarya ba bai wuce duk yadda za a kaɗa a raya da ita ba, ba za ta taɓa ci ko shan komai ba ranar juma'a. Kuma har kawo wannan lokacin ba a daima ganin gawar mushen saniya ba ranar Asubahin asabar. Da ta fara kuka kuma sai kunnuwanta su fara fesar da jini, lamarin da a kullin yake sake karya zuciyar Mai gado kenan. Akwai lokacin da wasu Bayi suka taɓa ɗaukan mushen saniyar suka shiga cikin daji suka feɗe ta suka haɗa wuta suka gasa kowannensu yanka ɗaiɗai ya ci take cikkunansu suka fashe kayan cikinsu duk ya fito waje, dalilin da ya sa aka gano gawarwakinsu wani matashin Bawa ne ya ce ya ga lokacin da suka wuce cikin daji da mushen saniyar. Wannan al'amarin ba ƙaramin ɗaga hankulan Bayin da ke cikin masarautar ya yi ba, hakan ne ya sake saka su kowannensu ya shiga taitayinsu, tun daga ranar babu wanfa ya sake yin gigin ɗaukan saniyar da niyyar ya gasa don ya kai namanta bakinsa. Watarana Sarki Abdul'aziz ya aika a kira Khadija a lokacin Jawahir na hannunta, duk yadda ta yi ta ajiye ta Jawahir ta ƙi yadda, don haka ta riƙe mata hannu suka fara takawa cikin birgewa duk wurin da suka bi sai an bi su da kallo. Suna shiga cikin turakar Mai martaba sai Jawahir ta cake a taƙi shiga idanunta sauke a kan shurin da ke cikin uwar ɗakin, da saka hannu tana nunawa haɗe da yin gwarancin da ba kowa zai gane ba. Ganin haka ya sa Khadija ta riƙo ta sai da ƙyar Jawahir ta shiga duk a tsorace take kamar wani ne yake yi mata gargaɗi. Sai da Khadija ta tsugunna cikin girmamawa ta gaishe da mahaifinta a zuciyarta tana mamakin kiran da ya yi mata. A hankali Jawahir ta tashi ta fara ɗan tsalle-tsallenta a ɗakin dalilin da ya sa ba su bi ta kanta ba. "Khadija mun aika a kira ki ne sakamakon Sarki Gumel Sarki Almustafa ya nema wa ɗansa Yarima Safwan aurenki kuma na ba shi ke duniya da lafiya." Ko kaɗan ta so a ce an ba ta zaɓi wurin zaɓar mijin aure amma babu yadda ta iya musamman da ta tuna matsayin mahaifiyarsu a cikin masarautar. "Godiya nake da zaɓinka ranka shi daɗe, Allah ja da kwana ya jiƙan mai Mai babban ɗaki." Murmushi ya sakar mata yana cikin magana suka ji motsin Jawahir ta wuce can uwar ɗakin Sarki Abdul'aziz, a bakin tsohuwar rijiyar ta tsaya ta fara bubbuga murfin rijiyar cikin gwarancin da take yi take faɗin. "Afuɗe... afuɗe ni ce... danzo ciki, afuɗe ..." Da sauri Khadija ta ɗauko ta tun kafin su fito Jawahir ta tsanyare da matsanancin kuka tana waiwayen rijiyar da Baiwa Maimuna take ciki. Sarki Abdul'aziz ya sallami Khadija sannan suka fice har bayan wani lokaci ba ta daina kuka ba. "Kin tabbata a kan idanuwanki ya ci wannan tufar da na damƙa miki?" "Me za a fasa Inna? Wallahi ita ya fara ci ma." Sailuba ta faɗa cike da farinciki. "Haba na gaji da gafara sa ban ga ƙaho ba, har yau so muke ya furta maganar aure amma shiru kake ji kamar an shuka dusa, don haka na koma jiya na sake karɓo miki na sha yanzu magani yanzu. Boka Shaddas ya ce mu bada zuwa nan da kwana biyu." Jakadiya ta ƙarasa maganar tana washe baki. Sailuba ta rungume ta, "Inna ina mai shaida miki matuƙar na auri Takawa, zan murzan kambun da har abada Umaima ba za ta murza shi ba, sai na shayar da ita ruwan mamaki daga ƙarshe na nuna mata bakin rijiya ba wurin wasan makaho ba ne." Bayan Kwana Biyar A ƙallah kusan watanni uku kenan da ta lura kullin alaƙarta da Sarki Abdul'aziz ƙara baya take, ta sha mamaki matuƙa duk da ya san cikin da take ɗauke da shi wanda a ƙalla ya tafi watanni biyar, nesa ba kusa ba ya fi ba ta kulawa a lokacin da take ɗauke da cikin Ruƙayya amma sai ta yi masa uzuri sakamakon 'yan tafiye-tafiye da yake yawan yi a lokacin. Babban tashin hankalinta bai wuce ganin yadda Boka Shaddas a mafarkinta da har kullin yake ƙyaƙyata mata dariyar ƙeta ba. A yau ma da ta ji Sarki Abdul'aziz ya neme ta a turakarsa cike da zumuɗi ta shirya sai dai tana shiga ta yi turus sakamakon ganin Fulani Babba a gefe ta yi kyau abin ta babu laifi, sai dai zuciyarta cike da fargabar kada fitsarin da ke yoyo daga jikinta ya zubo Mai martaba ya kore ta ko ya yi mata wulaƙanci a gaban Fulani Umaima ba . A wulaƙance ta dube ta sannan ta zauna can kusa da Takawa tana ɗaga hanci tana basarwa. "To da farko dai, Assalamu alaikum. Mun tara ku ne domin mu sanar da ku wasu muhimman abubuwan akhairi guda biyu. Na farko mun gama yanke magana mu da Sarkin Gumel mun tsayar da ranar ɗaurin auren Khadija da Yarima Safwan ranar juma'a mai zuwa, mun taƙaita abin ne sakamakon ana yin auren zai tafi ƙasar Mai duguri harkokin kasuwancinsa, don haka ba ma buƙatar ɓata lokaci. Fulani Babba ta yi shiru a tunaninta Fulani Umaima za ta amsa ta yi mata kara tun da zancan auren Khadija ake yi, shi ya sa ta yi shiru ta yi wa Fulani Umaima kara ba ta amsa ba. "Abu na gaba kuma da zan sanar da ku har ila yau a dai wannan juma'ar ne ni ma zan ɗaura aure da Baiwa Sailuba wacce tuni na 'yantata ta zama 'yar cikin gida, ina fatan za ku ba ni haɗin kai domin zama cikin kwanciyar hankali da lumana." Na ce ko akwai mai zuwa mu je dannar ƙirjin Umaima😕 SHU'UMAR MASARAUTA 16 *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* A razane Fulani Umaima ta miƙe tsaye jikinta na karkarwa har ta manta da cikin da ke jikinta, baki na rawa ta nuna Takawa don tuni idanunta suka rufe har manta matsayinsa a gare ta. "Me kake faɗa? Ka na nufin Sailuba baiwar gidan nan? Sailuba ƙasƙantacciyar baiwar da ba ta isa a 'yantata ba? Wallahi ba ka isa ba, ba zai taɓa faruwa ba, kai da ƙarin aure har abada." Cikin zuciyarta Fulani babba ta saki murmushin mugunta don ko kaɗan auren Takawa bai ɗaɗa ta da ƙasa ba, tun da ta san da ita da babu a gidan duk ɗaya ne ba ta saura fada a wurin Takawa. "Fulani ya kamata a san a gaban wanda ake magana, idan ba haka ba ranki zai yi mummunan ɓaci, zan zartar miki da mummunan hukuncin da ba ki taɓa tsammani ba. Na 'yanta Sailuba domin ita ce zaɓina wacce zuciyata take da muraɗin shimfiɗa rayuwar aure a tare da ita." Sarki Abdul'aziz ya furta cike da tsare gida. Kamar butum-butumi haka Fulani Umaima ta zuba masa idanu don gani ta yi ya koma mata kalarsa ta ainihi, a ɗan tsorace ta dube shi tana maimaita kalamansa a fili cike da mamaki. "Ina taya Mai martaba murna da fatan alheri a kan tagwayen labaran da ya sanar da mu masu ɗauke da farinciki, ba tun yau ba na san kai jajirtaccan gwarzon mazaje ne. Allah ya baka ikon kwatanta adalci domin kai ɗin mai adalci ne, kuma na tabbata za ta ci gaba da adalci kamar yadda kake yi a kodayaushe. Shigowar Sailuba cikin zuri'arka babban alkairi ne da ke tattare da faranta rai Zakina, na san ko mata ɗari a tara maka ba za ka taɓa za ni kunya ba." Fulani Babba ta yi maganar cikin sanyin murya da karyewar zuciya tana tunanin yaushe za ta koma kamar da a wurin Mai martaba, sai dai ta yi ƙoƙarin danne ɗacin da ke ranta ne domin ta fahimci zuciyar Takawa ta yi nisan kiwo a kan Sailuba, kuma duk wanda ya nemi ya nuna adawarsa game da auren ta lura zai iya shata masa layin da ke iya kai shi ga ƙunci haɗe da ɓacin rai. Ta san tana da zafin kishi a kan mijinta kuma uban 'ya'yanta, sai dai kuma dole ta adana kishinta har zuwa lokacin da zai yi mata amfani. Ya ji daɗin kalamanta sosai don haka ya sakar mata murmushi yana shirin ba ta amsa Fulani Umaima ta furta. "Munafukar banza munafukar wofi algunguma marar kishin kai, idan ke mai hankali ce ya kamata mu haɗa kai da ke don yaƙar annobar da ke shirin dumfaro rayuwarmu. Amma ku yi ku gama wallahi da ni kuke zancan, domin ni warki ce daidai da ƙungun kowacce shegiya." Daga haka ta fice daga ɗakin fuuu kamar za ta tashi sama. Ƙwallah ya gani a saman fuskar Fulani babba tana jin wani irin yanayi don rabonta da keɓewa da Takawa har ta manta, ba ta ji motsinsa ba sai ji ta yi ya tsugunna a gabanta. "Me yake damunki tauraruwata?" "Me ye ma bai dame ni ba a faɗin duniyar nan?" Ta furta a zuci, ta saki baki jin kalmar da ya furta mata, amma a fili sai ta girgiza kai, hannu ya sa ya goge mata fuska ya furta. "Ya kamata Fulani ta je don ta samu hutu." Galala ta yi tana mamakin wai yau Takawa ne yake furta mata kalamai masu taushi. Har bakin ƙofa ya mata rakiya ta wuce sashenta zuciyarta fes hatta Bayin da ke hidima a sashenta sai da suka fahimci sauyi daga gare ta. Yanayin yadda ya ga mahaifiyarsa ba ƙaramin mamaki ya ba shi ba, ya so ya basar amma ganin irin tashin hankalin da take ciki ya sa ya furta. "Ummina shin wani abu ya faru ne?" Idanunta jawur kamar sabon barkono ta dube shi. "Mene ne ma bai faru ba Yarima? Wai Takawa ne zai yi aure, auren ma ya rasa wa zai aura sai ƙasƙantacciyar Baiwa Sailuba 'yar wurin Jakadiya." Taɓe baki taga ya yi cikin halin ko'in kula. "To me ye abin damuwa Ummi..." Wata irin razananniyar tsawa ta yi masa har sai da ya razana don tun da ya zo duniya mahaifiyarsa ba ta taɓa yi masa haka ba. "Fice ka ba ni wuri sakaran banza mara tunani da kishin mahaifiyarsa." Da sauri ya fita don ya gama tsorata da yanayinta, ta shiga kaiwa da kawowa tana tunanin mafita. Kai tsaye ta sa aka kira mata Jakadiya, har ƙosawa ta yi kafin Jakadiya ta ƙaraso ɗakinta. Jakadiya babu damuwa ko ɗar a ranta don wani irin faɗi da girman kai ne yake ratsa ta. "Dakata nan baƙar munafuka, na janyo ki jiki a tsammanina da ke za mu yi tafiya cikin mutumci ashe ke 'yar kunama ce. Ban taɓa sanin ke kura ce lulluɓe da fatar akuya ba sai yau, amma bari ki ji Jakadiya kowa ya ci tuwo da ni miya ya sha. Wallahi-wallahi ba na ko kaffara tun da ke da makirar 'yarki kuka shiga gonata sai na sa kun girbe azababbiyar shukar da zan shuka ta da irin uƙubar da sai kun dinga gayyatar mutuwa da bakunanku, sai na shayar da ku tafasasshen ruwan mamaki; mamakin da har a zare numfashinku ba za ku taɓa mantawa da shi. Sai na jefa ku cikin jafa'in da boka ko wani mishiriki bai isa ya kuɓutar da ku ba, sai na dulmiya ku a kogin annoba, kogin da duk tsallan da za ku yi ba za ta ku taɓa yin iyo a cikinsa ba ballantana ki saka ran watarana za ki fito." A madadin kalaman Fulani Umaima su ɓata ran Jakadiya ko su razanata sai ta saki wata irin dariyar rainin hankali sannan ta tamke fuska ta furta. "Ai kin riga da kin yi sake ɗan zaki ya girma Umaima, kuma idan junanki sammako wani a tafe ya kwana duk abin da za a wanzar zai faru a ƙwayar idonsa. Ni da kike gani sai na numa miki ni lumbu-lumbu ce wutar ƙaiƙayi, kuma Sailuba tamkar ta dasa furenta a Masarautar Huddam ne domin mai wuri ya zo dole mai tabarma ya naɗe." Jakadiya ta ƙara matsawa gaban Fulani Umaima ido cikin ido ta ce, "Dube ni da kyau Fulani ko ga zubin ƙwayar idona kika kalla kin san ruwa ba sa'an kwando ba ne, tun wuri gara ki fara yi wa Sailuba biyayya ko kya shimfiɗa fada yadda kike so a wurin Mai martaba." Kan haɗaɗɗiyar kujerarta Fulani Umaima ta koma ta zauna sai da ta saki murmushin takaici sannan ta dubi Jakadiya. "Da alama son mulki da son zuciya irin na ki ya san kin manta wace ce Fulani Umaima, amma ki sani ko an ci birnin kura ba a taɓa ba wa kare dillanci. Don haka mu zuba mu gani ni da ku shege ka fasa." Ba tare da Jakadiya ta tanka mata ba ta fice daga cikin ɗakin kai tsaye ta wuce ɗakinta ƙirjinta na dakan lugude don ita kanta ta san faɗa da aljani babu riba. Ta san wace ce Fulani Umaima farin sani, koma mene ne za ta iya aikatawa don cikar muradinta. "Tun da na gan ki da tsakar ranar nan na tabbata da walakin goro a miya Jakadiyar Sarki Abdul'aziz." Boka Shaddas ya furta yana kallom Jakadiya da ta yi furƙai-furƙai cikin tashin hankali. "Ka taimaka mini ubangidana..." "Duk na ga abin da ya shiga tsakaninki da Fulani Umaima, kuma hakan ba ƙara min ɓata mini rai ya yi ba." Jakadita ta sake yin tsuru-tsuru hantar cikinta na kaɗawa. "Na so kin shawarce ni tun farko da ba ki ɓullo mata ta haka ba, sai mu ɓullo mata ta bayan gida mu ci birnin kura mu shinfiɗa fadarmu, so samu ki nuna mata ke za ki iya yi wa Sailuba baki ki tsine mata akan wannan auren da ake shirin yin, a taƙaice ki nuna mata ba kya son auren kuma ba da yawunki za a ɗaura shi ba, sai dai kash! Kin tarwatsa wannan matsayar, domin akwai wani sirrintaccan littafin da gawurtaccan matsafi Boka Bamaguje ya damƙa mata da na ci burin ki kawo mini shi ko ta halin ƙaƙa. Amma gabaɗaya kin ɓata goma ɗaya ba ta gyaru ba kuma dole mu sauya salo don na san a yanzu ba za ta sake aminta da kowacce irin Baiwa ba, ballantana a kawo mini littafin da zai sake ɗaga daraja ta." Kamar kazar da aka jefa da wuƙa Jakadiya ta dube shi da shanyayyun idanunta ta ce. "A gafarce ni uban gidana me ye abin yi yanzu, domin kuskure na riga da na tafka shi?" Boka Shaddas ya bushe da wata irin mahaukaciyar dariya sannan ya ce. "Taurarunta sun fara dakushewa daga gaban Mai martaba sakamakon aikin da na yi wa Sailuba, sai dai kuma har yanzu da sauran rina a kaba domin wannan dusashewar ta ɗan lokaci ce saboda aikin da Bamaguje ya yi mata har gaban abada matuƙar ba a tono shi ba, ba zai taɓa karyewa ba." Gaban Jakadiya ya yanke ya faɗi. "Sannan kuma ina mai farincikin sanar da ke yanzu haka cikin da ke jikin Umaima cikina ne, da abin da za ta haifa zan yi ƙoƙarin cimma ƙudurina a kanta. A nan za ta tabbatar da ta haifi jinin Boka Shaddas, amma kuma ki sani wannan rufaffan siri ne da ban lamunce ki sanar da kowa ba domin a ranar da kika yi kuskuren faɗarsa a ranar za ki bar duniya don haka bakinki ƙanin ƙafarki." Da sauri Jakadiya ta sa hannuwa biyu ta toshe bakinta, wannan shi ne ga ƙoshi ga kwanan yunwa. Amma dole ta zarge linzamin harshenta ko don ta kwana cikin salama tun da kowa ya kwana lafiya shi ya so. "Duk abin da kace ni mai bin umarninka ce madogarata." "To ai ba a nan gizo yake saƙar ba, yanzu hatta kishiyarta uwargidan Takawa martabarta ta dawo a idonsa. Sai dai kuma a banza man kare tun da Umaima ta riga ta kashe al'aurarta, har abada ba za ta sake moruwa ba. Tabbas barewa ba za ta yi gudu ɗan ta ya yi rarrafe ba domin Umaima ba yar a ƙasa ba, kin ga kuwa kamar kumbo kamar kayanta. Ungo wannan ki tabbatar da kin binne shi a bakin bishiyar ɗorawa, wannan ne zai sa duk buga-bugar da Umaima za ta yi ba zai hana komai game da auren Sailuba ba, tun da a yanzu taurarunta sun riga da sun yi ƙasa, a kowanne lokaci za ta iya yin faɗuwar baƙar tasa." Boka Shaddas ya ƙarasa maganar yana ɗauko wani baƙin bera wanda aka tsire jikinsa da allura da waɗansu ƙananun layu. Har ƙasa Jakadiya ta zube tana yi masa godiya sannan ta fice daga wurin. Sai da Ciroma da Galadima suka janyo ƙofar ɗakin ruf ta yadda wani ba zai ji abin da suke tattaunawa ba sannan suka kalli jun fuskokinsu ɗauke da damuwa. "Maganar gaskiya Takawa ya shammace ni ba zato ka na gani ya bayar da yarinyar nan Khadija yanzu mene ne mafita?" Ciroma ya yi maganar rai a ɓace. Guntun tsaki Galadima ya yi sannan ya furta, "Yanzu saboda wannan har ka sa sai mun zo nan?" Ciroma ya furta a taƙaice. "Ina gudun kada mu yi shuka a idon makwarwa kwaɓarmu ta yi ruwa tsululu, don haka na ce mu nemi ɗakin da za mu kashe mu binne ba tare da idon masarautar nan ya gifta a kanmu ba. "To me zai ɗaga hankalinka alhalin yarinyar nan ba ita kaɗai ba ce, ba ga 'yar uwarta nan Sakina ba, tun wuri ka samu Mai martaba da zancen aurensu wallahi a wata majiyar na ji an ce Waziri ma so yake ƙarfi da yaji ya aura wa ɗan wurinsa Bala ita, ka ga kada mu zo mu yi bori da sanyin jiki mu ga samu mu ga rashi." Riƙo hanunsa ya yi cikin jin daɗi. "Na matuƙar jin daɗin wannan maganar taka, dama an ce aikin mai shawara ba ya ɓaci sai da kuma ba shi da sirri." Galadima ya bushe da dariya, "To ai dama abokin kuka ba a ɓoye masa mutuwa ka ga sai mu ci mu lashe ba tare da wani ya sani ba." Ciroma ya ba shi amsa sannan ya yi masa sallama. Yana fita Zulai matar Galadima ta shiga ɗakin da sauri ta yi ƙasa da murya, "Mai gida an ya kana ganin ka yi farar dabara kuwa? Kar fa Ciroma ya..." "Haba Zulai kamar ba ki san mijinki ba?" Galadima ya katse ta. "Ai duk inda mai aro za shi da sanin mai kaya ne. Kina tsammanin a banza zan ce Ciroma ya yi wa Mai martaba magana game da auren haɗin da yake son yi tsakanin ɗansa da Sakina? Tsuntsu biyu na ke son jifa da dutse ɗaya don na san waye Abdul'aziz ba na jin zai bayar da 'yarsa ga mashayi, kin ga a lokacin kowa ya san da buƙatar Ciroma idan Takawa ya hana auren a daidai gaɓar ni kuma ƙit zan kashe shi, kin ga zargi zai hau kan Ciroma bayan an tura shi gidan yari kafin a naɗa Yarima sai na san yadda zan ɓullo a haɗa aurensa da yarinyar nan. Bayan wannan me ya rage Zulaihatuna?" Galadima ya ƙarasa maganar yana kallon Zulai. "Ayyiriyiriyiriiii! Shi ya sa ko kaɗan ba na kaicon zaɓar ka da na yi a matsayin mijin aure, ka biya ni ko ba sisi billahillazi da an ga sabuwar sarauta a ƙasar nan." "To tun da mu Marigayi ya ƙi mu da sarautar ba sai mu dasa 'ya'yanmu a kai ba, matar sarki idan ta iya jan birki ai ita ce Sarkin mai jan ragamar masarautar." Gabaɗaya suka kwashe da dariya. Tun bayan rabuwar Kamalu da dattijo Maharaz bai sake ganinsa ba kuma ko kaɗan ba damu ba saboda a kullin suka haɗu da tsohon bai wuce ya riƙa gaya masa maganganun da bai cika gane makamarsu ba, sannu a hankali ya saba da aikin wahalar da Bayi mazan suke yi sune saran itace, yin gine-ginen har fasa dutse ba a bar shi a baya ba. Lokaci ɗaya hasken fatarsa ya disashen ya yi duhu sosai don kusan kullin idan Inna wuro ta gan shi sai tausayinsa ya kamata. Watarana suna zaune bayan Kamalu ya dawo daga fasa dutsen da aka saka su hannuwansa duka sun farfashe, ya zauna yana cin abinci ya dubi Inna wuro idanu cike da ƙwalla. "Inna wuro yanzu shi kenan rayuwar Bayi a haka za ta ƙare? Ba mu da 'yanci ba mu da gata ba mu da lokacin kanmu ballanta mu amfani kanmu da kanmu? Inna wuro na gaji ki zo mu bi dare kawai mu gudu ina ganin sai mun fi samun kyakkayawar rayuwa." Ƙwalla ta zubo idanunta jin hannunsa yadda ya bushe ya yi tauri kamar katako a saman hannunta, duk wahalar da suke sha nasu nafila ne a kan mazan cikin masarautar. "Kamalu haka Allah ya ƙaddara mana, shi ne gatanmu yana kallon duk halin da muke ciki. Idan muka ce za mu gudu ina za mu je?" Kamalu ya cusa sandararran tuwon dawar bakinsa yana turawa da ƙyar yana share hawaye, a hankali Inna wuro ta riƙa lallashinsa har ya watsar da maganar guduwa daga cikin gidan. Inna wuro ita da Mai gado ta su ta fi zuwa ɗaya duk cikin sashen Bayin, sai dai kuma 'ya'yansu ko kaɗan ba sa jituwa duk da sun kasance ba sa'annin juna ba. Ko kaɗan Kamalu ba ya taɓa zama wurin da Jawahir take zaune, haka kawai ya ji ya tsani yarinyar musamman idan ya kalli ƙwayar idonta da yake ganin wata murgujejiyar bishiyar kuka a ciki. Ita kuma Jawahir duk lokacin da Kamalu ke zaune a wurin da take wani irin zafi ne yake ratsa ta, sannu a hankali kuma sai ta riƙa ganin tururuwa na fita daga jikinsa duk wacce ta ƙarasa jikinta sai dai ta ji tana gasa mata cizon da ke ƙoƙarin ɗaye fatarta. Dalilin da ya sa Kamalu na zama ita kuma za ta riƙa zunduma ihun neman agaji. Yana gama cin abinci ya miƙe ya zagaya ta can bayan rumfar bayi ya ci gaba da tafiya har ya isa bakin bishiyar tsamiyar da ke kallon bayan ɗakunan Bayin. Tun bai kai ga zama ba ya ji muryar dattijo Maharazu. "Assalamu alaikuma!" Bai san ya yi rashinsa na kwana biyu ba sai a yanzu da ya ji muryarsa, "Dama kana nan wai ina ka shiga?" Kamalu ya tambayi Maharzu cike da yarinta. "Kada ka bari rauninka ya bayyana a fili ta yadda magauta za su fahimci lagonka har su nemi cin galaba a kanka. Kalli can wurin." Dattijo Maharaz ya furta masa haɗe da nuna masa bayansa. Wani yaro ya gani kusan sa'ansa ne a shekaru kwance a ƙasa sai birgima yake yi yana ɗiban ƙasa yana ci yawu na dalala daga bakinsa. Hankali a tashe ya furta. "Waye wancan kuma me yake yi a wurin nan?" Murmushi Dattijo Maharazu ya yi ya kama hannun Kamalu suka ƙarasa gaban Abubakar sannan ya furta, "Idan har ɗan sarkin Masarutar nan zai kasance haka me kake tsammani a kanka?" A razane Kamalu ya dube shi, "Ka na nufin wannan a masarautar nan yake kuma ɗan sarki ne?" Kafin Dattijo Maharzu ya ba shi amsa Kamalu ya ga matashin ya ɗago yana cizgar gashin kansa, gabansa ne ya faɗi. Jikinsa ya yi matuƙar sanyi, haka kawai yake jin kamar ya taɓa ganin mai yanayin kamanninsa duk da wannan kallo ɗaya za ka yi masa ka fahimci ba shi da lafiya sakamakon yadda surar hallitarsa ta koma. Daga can bayansa ya ji muryar Inna wuro ta ƙaraso tana faɗin. "Kai Kamalu me kake yi a wurin nan da doshin magriba?" Idanun Kamalu suka ciko da ƙwalla ya nuna mata Abubakar ya furta, "Don Allah Inna wuro ki duba wannan wai shi ma ɗan Mai martaba ne ki dubi irin halin da yake ciki." Sororo Inna wuro ta yi tana kallon wurin da yake nunawa babu abin da ta gani, tana shirin yin magana ta sake jin Kamalu ya furta. "Amma Dattijo Maharazu me ya sa Sarki ba ya ba shi kulawa, wacce irin larura gare shi?" Bayan sallar Isha'i Fulani Babba tana zaune saƙo ya iso gare ta wai Mai martaba na gayyatarta cikin turakarsa, ta cika da mamaki matuƙa jiki a sanyaye ta yi wanka ta gyara jikinta haɗe da feshe ko ina da turare sannan ta nufi sashen na shi gabanta na faɗuwa. Banbarakwai take ji wai yau Takawa ne yake son tarawa da ita a turaka, farincikinta ya nunku don idan ba ta manta ba rabonta da Takawa tun da cikin Abubakar, sai kuma mafarkin da take yawan yi yana mu'amala da ita ƙarfi da yaji a cikin mafarkinta. SHU'UMAR MASARAUTA 17 *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* A sanyaye Fulani babba ta ɗaga labulen ɗakin ta same shi kishingiɗe ya ci ado cikin jajayen kayan saki waɗanda aka ratsa cin bakinsu da zaren zaiba, ba ƙaramin kyau ya yi mata ba don rabon da su keɓe kamar haka har ta manta. "Ke zinnariyar mata ce samun kamarki ko an duba dubban mata babu kamarki, wani lokacin idan na zauna sai na dinga gode wa Ubangiji da ya mallaka mini kyakkyawar sura da kyawun halayenki." Fulani babba ta saki murmushi a kunyace. "Kin kasance lantarkin da ke haske birnin zuciyata don Allah ki kasance da ni har ƙarshen rayuwa Fatima." Muryar Takawa ta daki kunnuwanta cikin wata irin murya mai ɗauke da shauƙin so da ƙauna, tare da son nuna tsantsar kewa da begen masoya. "Ban san gaibu ba Fulanina amma ina mai kyautata miki zaton ke 'yar aljannah ce." "Na sani Fulanina ta dabance mai farar zuciya da ladabi da biyaya." "Idan ina kallon sura da kyawun halittarki sai na ga a duk faɗin duniya babu wanda ya kai ni sa'a, sa'ar da nake fatan kasancewa da ita har cikin aljanna. Idan na raɓa gangar jikina a naki ji nake tamkar na dawwama a haka ba tare da zare jikinki ba. Ke 'yar Aljanna ce sarauniya kuma gimbiya a wurina, ki adana waɗannan kalaman duk rintsi ba zan iya rabuwa da ke ba." Lokaci ɗaya ire-iren kalaman da Takawa yake yawan furta mata a shekarun baya suka dawo mata, ta tattaro murmushi tana jin wata irin ƙwarin gwiwa na ratsa ta har ta isa cikin tsakiyar ɗakin. Hannuwa ya buɗe mata yana daga kwance haɗe da sakar mata murmushi, a kunyace ta sunne kanta ƙasa ta ƙarasa jikinsa kusan lokaci ɗaya suka saki ajiyar zuciya. "Me ya sa kike ɗari-ɗari da mijinki ko don na ce zan ƙara aure ne Fulanina?" "Ko kaɗan aurenka bai taɓa ɗaga mini hankali ba, da ace zan samu wannan kulawar ko mata ɗari idan ana yi ka je ka yi babu ruwana." Fulani Babba ta faɗa a zuciyarta. Amma a fili sai ta furta. "Ba haka ba ne Sarkina." Ita kanta sai da ta ji wani iri a kalaman da ta furta masa, ta yi mamakin yadda ta ga Mai martaba yake ba ta kulawa hatta abinci tare suka ci wani abin da ya daɗa sanyaya ranta bai wuce yadda har kawo lokacin fitsarin da ke fita daga jikinta bai fita ba ballantana ya ɓata mata jiki. Daga haka sai hirar ta su ta fara sauya salo, tun Fulani babba na jin nauyi da kunyar mayar masa da martani har ta saki jikinta take sarrafa mijinta cikin kyatatawa. Wani sanyin daɗi da farinciki ne yake ratsa da ta ɗora ƙwayar idonta a kan Takawa da ke yunƙurin mu'amala da ita, ita ma yau jin ta take kamar sauran mata don idan ba ta manta ba rabonta da shi an ɗauki shekaru masu yawan gaske. Wani irin zafi ne ya fara ratsa ƙasanta tamkar an sa kaifaffiyar wuƙa ana yunƙurin fisgo ƙasanta ta ƙarfin tsiya, wata irin ƙara ta ji Takawa ya saki a ɗimauce ya ja da baya hankali a matuƙar tashe. Jinin da ta gani yana tsattsafowa daga jikinsa ne ya sake tarwatsa ragowar ƙwarin gwiwarta. "Ni ba na kishi da ke domin na san na riga da gama da shafinki, domin da ke da babu a wurin Takawa ɗaya kuke." Kalaman Fulani Umaima suka dawo mata ranar da wani saɓani da bai taka kara ya karya ba ya haɗa su. "Ni fa hankalina bai kwanta da wannan kishiyar taki ba an ya kuwa babu sa hannunta a wannan ciwon naki?" Sai a yanzu kalaman Yaya Halima suka sake samun gurbin zama a zuciyarta. Numfashin Mai martaba ya katse mata tunani. "Don Allah ka yi haƙuri! Ban san me ya haifar da hakan ba." Fulani babba ta faɗa jiki a sanyaye, a ɓangare ɗaya kuma wata irin kunya ta mamaye ta. Da kallon tausayi ya bi ta sannan ya furta, "Kada ki damu In shaa Allah ranar Juma'a idan Malam Liman ya dawo zan sa a nema miki magani." Farincikin Fulani babba ya bayyana har a fili, ta share ƙwallah tana sake jin ƙaunar mijinta na taso mata. "Na gode ranka shi daɗe. Allah ya dawwamar mana da zaman lafiya har ƙarshen rayuwarmu." Murmushi ya sakar mata sanna ya yunƙura har lokacin jikinsa bai daina tsatssafar da jini ba, ga wani ɗan zugi-zugi haɗe da raɗaɗi da yake ji. Ƙai tsaye ya wuce banɗaki don ya gyara jikinsa. Da sauri Inna wuro ta janyo hannunsa gabanta na faɗuwa, wato ana murna baƙo ya tafi ashe yana bayan gari. Tun suna Rigar Arɗo suka fahimci irin gane-ganen da yake yi tun yana ƙaramin yaro, ƙirjinta na bugawa ta dubi shi. "Babu abin da nake gani Kamalu don Allah daga yau kada ka sake zuwa wurin na." Kamar zai yi kuka ya bi ta da kallo. "Inna kin ga abin da yake yi." A ɗan tsorace Inna wuro ta waiga wurin da yake nuna mata amma babu abin da ta iya gani. "Don Allah koma waye yake ƙoƙarin taɓa mini ɗa ya yi haƙuri, ku yi haƙuri In shaa Allah ba zai sake zuwa wurinku ba." Inna wuro na gama magana ta ja hannun Kamalu yana ɗan cijewa da sauri Dattijo Maharaz ya ƙarasa wurinsu ya ce. "Ka bi mariƙiyarka don ka yi dace da mariƙa na gari. Amma ina son yau da daddare ka ce musu su baka labarin abin da ya faru a Dajin Wushushe a daidai gefen ƙoramar Ɗinya, a ranar bikin shaɗi." Kai kwai Kamalu ya iya gyaɗa masa sakamaon fisgar hannunsa da Inna wuro take yi har suka ƙarasa cikin sashensu na Bayi. Ganin yanayin yadda su Inna wuro suka shiga ya sa Baffajo ya ƙura mata ido. Duk abin da ya faru Inna wuro ta kwashe ta ba wa Baffajo labari, Baffajo ya kalli Kamalu sannan ya dafa kafaɗarsa. "Kamaludeen!" Baffajo ya kira shi da wani irin yanayi. "Ba tun yau ba jikina ya jima yana ba ni kai na musamman ne sai dai ina tsoron kada miyagun su saka mini kai a gaba. Don Allah ka riƙa takatsantsan, ka ga yanzu kai da 'yar uwarka A'iru ne kaɗai kuka rage mini." Murmushi Kamalu ya yi don a tsammaninsa Baffajo rufe shi zai yi da faɗa, Inna wuro za ta yi magana Kamalu ya dakatar da ita. "Baffajo wai mene ne ya faru a Dajin Wushushe a daidai gefen ƙoramar Ɗinya, ranar bikin shaɗi..." Kallon da ya ga sun wurga masa a tare kusan lokaci ɗaya ne ya katse ƙarshen maganarsa, take tsoro ya mamaye zuciyarsa ya ɗan ja da baya. "Waye ya ce ka yi mana wannan tambayar?" "Ba komai za ka riƙa sanar da su Baffajo ba, idan ka na son na dinga amsa maka tambayarka. Idan sun tambaye ka kawai ka ce musu mafarki ka yi, ka yi mini alƙawari?" Tsawar da Baffajo ya buga wa Kamalu ce ta dawo da shi hayyacinsa a lokacin da ya lula duniyar tunanin wata hira da suka taɓa yi da Dattijo Maharazu. "Baffajo kawai a mafarki ne aka ce na tambaye ku!" "Daga yau idan na sake jin makamanciyar wannan maganar sai ranka ya yi mummunan ɓaci ka ji me na ce?" Kamalu ya amsa wa Baffajo cikin matsanancin tsoro. Hawayen takaici, damuwa da tashin hankali ne ke rige-rigen tsiyayowa daga kwarmin idonta, ta tura kanta cikin ƙafafuwanta kamar ƙaramar yarinya sai da ta yi kuka mai isarta sannan Fulani babba ta furta. "Ya Ubangiji ina godiya bisa wannan jarabta da kake yi mini, Ya Allah ka yaye mini wannan miyagun al'amura da suke bijirowa rayuwata ko na yi mu'amala da mijina kamar kowacce mace." Kuka ne ya ci ƙarfinta ta jima a haka sannan ta faɗa banɗaki ta watsa ruwa ta koma kan gado ta yi lamo kamar mara lafiya. Sai da dare ya tsala sosai kamar sabuwar munafuka Jakadiya ta bi bayan ɗakunan Bayi ta nufi bakin wata bishiyar ɗorawa hannunta ɗaya ɗauke da beran da Boka Shaddas ya ba ta, da sauri-sauri ta hau haƙa rami ta tura beran da ransa cikin ramin ta mayar da ƙasar ta rufe sannan ta taso zuciyar ƙal kamar wacce aka yi wa bushara da Aljanna. A ranar Jakadiya bacci ta yi sosai don har sai da ta kusa makara sallar Asuba, saboda tsananin farinciki. Tun da Fulani Umaima ta zo duniya maganar auren Mai martaba ce abu na biyu da ya yi mummunan ɗaga mata hankali, daga lokacin da Bamaguje ya sanar da ita Fulani Babba na da cikin Abubakar sai wannan maganar. Haka ta yi ta faɗi tashi daga wannan boka zuwa wannan boka sai dai ita kanta tana zuwa ne amma babu wani sauyi ko ci gaba da ake samu daga wurin Mai martaba, sai ana iya kiran ci gaban na mai haƙar rijiya sakamakon wani zaman doya da majar da suka cigaba da yi, cikin tsangwama, kyara da hantara dga wurin Mai martaba. Ganin haka ya sa ta ƙuduri niyyar zuwa wurin Takawa don ta kwantar da kai cikin kissa da kisisina. Wanka ta tsala ta yi kyau sosai sai dai kuma ta ɗan faɗa fuskarta ta yi fayau, bayan Sallar Magriba ta isa Turakar Mai martaba a lokacin ko iso ba ta jira ba. Ƙamshin turarenta ne ya buge shi, a hankali ya ɗago yana kallonta sai kuma ya kawar da kai gefe ya amsa mata sallamar a ciki. "Yanzu a kan ƙasƙantacciyar Baiwa Sailuba Mai marta ya mayar da ni bora, lallai duniya juyi-juyi kwaɗo ya buga tsalle ya faɗa ruwan zafi." Fulani Umaima ta yi maganar a zuciya. Murmushin yaƙe ta aro ta yafa wa fuskarta sannan ta ƙarasa har gaban gadon da yake kwance. "Ni mai laifi a gare ka ce kuma ban farka daga halin da na tsinci kaina a ciki ba sai da na fahimci muhimmancin abin da kake ƙoƙarin aiwatarwa. Don Allah ka yafe mini Sarkina, na gane kuskurena kuma a shirye nake na karɓi duk wani hukunci daga gare ka komai tsaurinsa." Fulani Umaima ta ƙarasa maganar cike da rauni, ƙwallah ta fara gangaro mata ta fara shasshekar kuka mai jan hankali. "Tun da ma can ba mu riƙe ki ba kawai mun ɗaga miki ƙafa ne domin mun lura kina buƙatar haka." Wani ƙululun baƙinciki ya sake mamaye ta ganin yadda yake sha mata ƙamshi. Ta ruƙo hannuwansa har lokacin tana zubar da hawaye ta furta, "Sai nake ganin kamar Mai martaba bai gamsu da tubana ba, ranka shi daɗe za ka iya hukunta ni da duk abin da ka yi niyya matuƙar zai sanyaya zuciyarka. Ban fahimci alkairi ne yake ƙwanƙwaso mana ƙofa game da auren Sailuba ba sai a mafarki da na yi jiya, tabbas Sailuba za ta zame mana tamkar yabanyar da kowanne manomi yake burin samu a gonarsa. Na ga tarun alkairai a game da ita har zuwa Yarima, dalilin da ya sa na fahimci kuskurena tun farko. Amma idan kana buƙatar na baka wuri zan wuce ranka shi daɗe matuƙar hakan zai sanyaya zuciyarka." Tun lokacin da ya ji Fulanin Umaima ta ambaci sunan Sailuba wani farinciki ya mamaye birnin zuciyarsa, tana shirin miƙewa ya kamo hannuwanta ya zaunar da ita kusa da shi. "Mun fahimci kuskurenki, don haka a kiyaye duk wani abu da zai taɓa martabar da mutumcin Sailuba." A ɗan razane ta dube shi jin waɗannan kalaman na Takawa masu kama da ruwan dalma a cikin kunnuwanta, babu yadda ta iya haka ta danne ta ƙaƙalo murmushin ƙarfin hali. Ta yi ƙoƙarin bin Yarima a sha kiɗa duk don ta kai ga cim ma muradinta. Dare ranar daga Fulani har Sarki Abdul'aziz sun gudanar da shi cikin matuƙar farinciki musamman Fulani Umaima ta ga ta mantar da Takawa 'yar togaciyar da ta shiga tsakaninsu. Dalilin da ya sa ta sake sakin jiki aka shiga shagalin bukukun kamar babu komai a ranta. Rana ba ta ƙarya sai dai uwar ɗiya ta ji kunya. Kamar yadda Mai martaba ya faɗa ranar juma'a aka ɗaura auren Khadija da Yarima Safwan, sai kuma Sailuba da Sarki Abdul'aziz. Gidan ya kacame sosai baƙi ta ko'ina ɓarkowa suke suna taya Mai martaba murna. Kafin wani lokaci tuni masu wasan gargajiya da 'yan bori suka fara cin kasuwarsu cikin ƙwarewa da tabbatar da al'adun hausa. Jakadiya wani irin farinciki ta riƙa ji kamar ta zuba ruwa a ƙasa ta sha, haka daga ɓangaren Bayi zuciyoyinsu tas sakamakon wannan ranar ta kasance musu tamkar ranar cin gashin kai. Bayan sallar juma'a aka shirya Khadija cikin shiga ta alfarma da ƙasaita, aka miƙa ta wurin Takawa ta kansa ya riƙe mata hannu bayan ya yi mata doguwar nasiha ya wuce da ita motar da za a wuce da ita Masarautar Gumel. Fulani babba ta yi kuka sosai don ji take kamar an yage mata wata gaɓa daga jikinta, sai 'yan uwanta da suka zo suka dinga tausarta har aka tafi da Khadija. Daga ɓangaren Fulani Umaima 'yan uwanta suma sun zo da yawansu, sai dai ba ta ji da daɗi ba da ta ga Mahaifiyarta ba ta zo ba, sai mahaifinta da yayyanta maza ne kaɗai suka zo ɗaurin aure. Ta so a ce mahaifiyarta ta zo ko ta kawo mata mafitar halin da take ciki amma ta ci alwashin idan aka gama biki komai ya lafa za ta kai ziyara ta musamman wurin mahaifiyarta. A cikin jerin sashen matan Sarki Abdul'aziz aka gyara wa Sailuba nata sashen, ya tsaru sosai ya fita gwanin birgewa. A daren ranar aka shirya Sailuba cikin tsadaddiyar alkyabba baƙa wacce aka yi wa adon fararan duwatsu, sai baza wani irin sihirtaccan ƙamshi take yi kai tsaye aka wuce da ita sashen Mai martaba. Bayan zaman Sailuba babu jimawa ya sa aka kira masa su Fulani Umaima, sai da suka zauna sannan ya haɗa su gabaɗaya ya yi musu nasiha tare da fatan kowanne zai riƙe matsayinsa. Kamar babu abin da ke ran Fulani Umaima haka ta riƙa amsawa tana sakin murmushi har sai da abin ya ba wa Fulani Babba mamaki. Bayan ya gama yi musu faɗa ya sallami su Fulani Babba suka fice, sai dai zuciyoyinsu duk babu daɗi domin shi kishi kumallon mata ne duk yadda ka so danne shi sai ya motsa. Sarki Abdul'aziz ban da murmushi babu abin da yake yi har ya isa wurin da Sailuba ke zaune, a hankali ya ye mata hular alkyabbarta yana sakar mata murmushi. Ɗan sunne kai ƙasa ta yi cike da kissa. "Barka da shigowa Sadaukin Sarakai kuma adalin shugaba!" Ta furta a hankali. "Barkanki dai sarauniyar matan duniya." Ya yi maganar cikin kulawa da nuna tsantsar soyayya ya fara rage kayan jikinsa sannan ya rage mata nata kayan. Sailuba ta saki murmushi a zuciyarta tana mamakin wai yau ita ce a gefen Sarki Abdul'aziz, sarkin da ke mulkar masarautar da kowacce mace za ta so a ce ta haɗa iri da ita. Gasassun kaji da kayan marmari ya riƙa ɗauka da kansa yana ciyar da Sailuba, ita kuwa ganin irin kulawar da yake ba ta ya sa ta sake narkewa cikin kissar da ta sake fizgarsa da jan hankalinsa. Tun da Fulani Umaima ta koma ɗakinta wani abu mai ɗaci ya tokare mata maƙoshi, cikin ƙunan zuciya ta yanke shawarar zubar da makamanta don ta kai wa Bamaguje ziyarar ko zai yi mata magani. A birkice ta ɗauko akwatinta har ta kai hannu za ta ɗauki ƙahon ta busa. "Tun daga yanzu har kin karaya ke kuwa me aka yi da maza, kina ganin idan Bamaguje ya ganki yanzu ba zai yi miki dariya ba. Me kike ci na baka na zuba, idan kin bi a hankali da sannu za ki sa Takawa ya ƙarar da gishirinsa a dahuwar ƙaho." Zuciyarta ta wassafo mata waɗannan kalaman waɗanda suka yi tasiri a zuciyarta. Ajiye ƙahon ta yi ta mayar cikin akwatin ta rufe haɗe da saƙa da warwara a zuciyarta. Guɗar da Jakadiya ta fito tana yi ita ta ƙara jan hankalun ilahirin mutanen da ke cikin masarautar, hannunta riƙe da zanin gadon ta fara shiga lungu da saƙon gidan tana nunawa cike da alfaharin Sailuba takai martabarta har turakar aurenta. Nan da nan aka shiga 'yan tsegungumi da ƙananan maganganu, Fulani Umaima na jin wannan saƙon baƙinciki ya sake lulliɓe ta tare da ɗaukan miyagun alwashi. Lokaci ɗaya ta saki dariyar ƙeta har tana tuntsirawa, don a wani lokacin ura kanta tsoron kanta take yi. Ku taho mu je mu taya Sailuba murkushe daƙwalen kajin amarcin🙊🤭🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️🤣🤣🤣🤣 SHU'UMAR MASARAUTA 18 *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* "Masarutar Bahuswa ita ma na ɗaya daga cikin masarautun yankin ƙasar hausa. Sarakuna da dama sun yi mulki sai dai daga cikin waɗanda suka mulki masaratar nan sun haɗa da jinsin mutane da kuma jinsin aljanu, sai dai akwai ƙalubale, tirka-tirka da gwabzawar faɗa a tsakaninsu kafin birkitattun al'amura su daidaita a samu kyakkyawar fahimtar juna." Kusan lokaci ɗaya muka kalli juna, ƙwaƙwalwata ta famtsama kogin tunanin makomata, sakamakon al'amuran almara da suka kai kawo a cikin rayuwata. "Kenan ni ma aljana ce? Ko kana so ka ce na fito daga cikin jinsin mutane? Ban fahimta ba, ka wayar mini da kai Sarki Hafiz don har yanzu ƙwaƙwalwata cunkushe ta da tarun tunaninnika." Tambayar da na yi wa kaina kenan a cikin zuciyata. "Wannan amsar daga bakin Sarki Hafiz za ki ji ta." Na ji an furta daga gefena na hagu, waigar da zan yi na hangi wani Dattijo da nake ganin tamkar na taɓa ganin fuskarsa a wani wuri. Daga can gefe shi ma ya nemi wuri ya zauna sai da har lokacin mamaki bai kau daga saman fuskata ba, ya yin da shi kuma yake sakar mini murmushi. "Mahaifina shi ne Sarki na biyar daga cikin Sarakunan mutanen da suka mulki masarautar nan, ya yin da Mahaifiyarki ta kasance Sarauniya ta farko wacce mace ke jan ragamar akalar mulki babbar masarauta kamar wannan. Ta samu wannan damar ne ta sanadiyyar mahaifinki wanda shi ne ainihin wanda yake kan karagar amma soyayya da ƙaunar mahafiyarki ta sa ya damƙa mata karagarsa. Mahaifiyarki sunanta Gimbiya Nuwaira yayin da mahaifinki sunan shi Sarki Fawwas..." Kaina na ji ya yi nauyi lokaci ɗaya na shiga ruɗani, don haka na katse shi. "Sarki Hafiz ka na son ka ce ni ma na fito daga cikin jinsin aljanu kenan? Tun da ban ji ka ambaci sunan iyayena a cikin jinsin sarakunan mutanen da suka yi sarauta a gidan nan ba?" Fulani Umaima ta ta gagara ci gaba da karanta littafin sakamakon jin wani azababban ciwo da ya karta wa mararta. Cije baki ta yi tana yarfe hannu ta rufe littafin ruf da ƙyar ta iya mayar da littafin cikin akwatin sabida yadda ta ji naƙuda ta taso mata gadan-gadan, ga wani irin azababban ciwo da yake nuƙurƙusarta. Mutanen Rumzu ba haka suke zaune kara zube ba, sun kasance suna da sarakuna da hadiman masarauta ta yadda suke gudanar da al'amuransu cikin tsari da girmama na gaba da su. Rumzu mutane ne masu daɗin mu'amala sai dai ko kaɗan ba su da haƙuri uwa-uba suna da matuƙar ruƙo a zuci musamman idan har ba su ɗauki fansa a kan wani abu da ya ɓata musu rai ba. Daga cikin waɗannan al'umma sun kasu kashi biyu, akawai waɗanda baka bambamce mazansu da matansu sakamakon ƙwal kwabo da suke yi daga maza har mata, kuma duka haka suke yawo daga su sai fatar da ke ɗaure a ƙugunsu. Idan har ka ga mace ta fara saka fata tana rufe ƙirjinta to an kaita ɗakin mijinta wato an yi mata aure. Akwai kuma waɗanda ko kaɗan ba sa aski gashinsu acukurkuɗe ya danƙare ga datti ga rashin gyara daga maza har matansu haka suke rayuwa. Su irin waɗannan yarinya tana fara girma za ta fara rufe ƙirjinta, amma daga ranar da aka kaita ɗakin miji ta daina saka komai a ƙirjinta. Suna da al'adu waɗanda suka haɗa da al'adun aure, na haihuwa har zuwa al'adun mutuwa da waɗanda suke gudanarwa duk shekara. A lokacin da saurayi ya ga budurwa ya ji yana sonta, zai ɗebi jajayan busuru biyu da baƙaƙen kaji cikin dare ya je bakin bishiyar kukar da suke bautawa ya ajiye su. Zai tuɓe kayansa gabaɗaya ya yi tsirara sannan ya faɗi abin da yake tafe da shi, duk maganganun da zai yi zai faɗa ne idanunsa a rufe. Yana gama faɗar buƙatarsa zai ji wata iska ta mamaye wurin bayan ya ji ta ɗauke sai ya buɗe idonsa, idan har ka ga waɗannan kajin da bunsurun da ka kai suna nan to soyayyarka ba za ta samu karɓuwa ba. Idan kuma ka neme su ka rasa to kai tsaye aure zai tabbata a tsakaninka da yarinyar da kake so. Idan kuma aka tashi auren saurayi da budurwa kafin ayi bikin aure za a haɗa saurayi da amarya a ɗaki guda, mu'amala ta shiga tsakaninsu amma ba haka nan ake kai su ba a kan saka su da gawar mutum wacce aka tsaface wala dga dangin amarya ko dangin angon. Idan kuma babu ɗaya daga ciki za a je fadar Shugabansu akwai wani keɓaɓɓan ɗaki da tsaface ajiyayyun gawarwaki a ɗauki ɗaya a kai musu ita. Ita gawar ita za ta fara shiga cikin ɗakin da ƙafarta, sai ta yi kwanciyar rigingine sannan saurayi da buduwar su ma shiga ɗakin. Da farko za su yanki gashin jikinsu su zuba a kan gawar da ke kwance, sai su tsallake gawar sau uku-uku sannan su koma wuri ɗaya su kwanta. Bayan an tabbatar da komai ya gama gudana a tsakaninsu za a buɗe ƙofar idan har aka ga jini yan fito daga ƙwayar idonta da can ƙasan gawar to wannan saurayi da budurwar sun kai mutumcinsu. Idan aka ga jini a kunnen gawar to saurayin ya taɓa mu'amala da wata macan kafin wannan ma'ana bai kasance saurayi dal ba da bai taɓa aikata komai ba, idan kuma aka ga jini ya tsattsafo a tafin ƙafar gawar to ita ma budurwar ba ta kai budurcinta ba, idan kuma ba a ga jini ba gabaɗaya a jikin gawar to wannan budurwar da saurayin duka ba su kai mutumcinsu ba wato dukkansu sun taɓa wata mu'amalar kafin wannan ranar. Kuma hakan wani zunubi ne da har sai an hukunta duk wanda aka samu matsala daga gare shi kafin a yi musu auren. Kuma ko da an yi auren idan namiji ne yake da wannan matsalar har ƙarshen rayuwarsa zai zame wa matarsa tamka bawa, haka idan macen ce ta rasa budurcinta ita ma za ta zame wa mijinta tamkar baiwa sai yadda ya ga damar sarrafa ta. Inna wuro ta gama duk wasu ayyukan da Fulani Umaima ta saka ta don haka ganin ta kammala ya sa ta rafka sallama daga bakin ƙofar ɗakinta. Shiru ne ya biyo baya hakan ya sa ta sake yin sallama, sai dai can ƙasa-ƙasa ta jiyo muryar Fulani Umaima. Tana son shiga cikin ɗakin amma tsoron kada ta yi laifi ya sa ta haƙura don a yadda kunnuwanta suke jiyo mata kamar Fulani Umaima ba ta da lafiya. "Ranki shi daɗe shin akwai wani abu da kike buƙata?" Inna wuro ta yanke shawarar faɗar haka ko ta ji daga bakinta. "Maza shigo ina son ganinki." Fulani Umaima ta faɗa murya can ciki alamun ta fara galabaita. Jiki na karkarwa Inna wuro ta shigar har uwar ɗakin Fulani Umaima, tana tafe tana kalle-kalle don tun da take ba ta taɓa shiga ciki ba. A zuciyarta tana mamakin irin ruwan dukiyar da aka narka saboda tsadaddun kumbayen da ke ɗakin. "Allah ya taimaki uwar ɗakina ko za a sanar da Takawa halin da kike ciki?" Girgiza kai Fulani ta yi, "Ba buƙatar haka Inna wuro, daga ke babu wanda yasan halin da nake ciki don haka ban ba da umarnin a sanar da kowa ba." Jinjina kai Inna wuro ta yi ta shiga jera wa Fulani Umaima sannu, ita kuwa ban da numfarfashi babu abin da take yi da sumbatu sama-sam. Da kanta ta nuna wa Inna wuro wurin da ta ajiye reza, zare da wata ƙatuwar ledar sugar. Da sauri Inna wuro ta ɗauko ta shimfiɗa, ta taimaka wa Fulani Umaima ta hau kai ta tsugunna. Yuuuu haka ta fara jin jiri na ƙoƙarin ɗaukanta, da sauri ta ruƙo ƙafafuwan Inna wuro sannan ta fara jin wasu irin surutai a saman kanta waɗanda ta gagar fahimtar abin da ake faɗa. Tana daga durƙushe ta ga kamar gilmawar mutum da sauri ta ruƙo Inna wuro ta ce. "Inna wuro kin ga gilmawar wani?" "A gafarce ni uwar gijiyata babu abin da na gani. Sannu Gimbiyar mata In shaa Allahu, Allah zai buɗi ido lafiya." Fulani Umaima ba ta iya amsawa ba sakamakon jin nishi ya taho mata, sai kuma ta ji tamkar an saka farata masu tsini ana fisgar ƙasanta hakan ya sa ta sake riƙe Inna wuro nan take jariri ya faɗo babu jimawa mabiya ta biyo baya. Inna wuro na kai idonta kan jaririn ƙirrr ta ga ya zuba mata ido yana kallonta babu ko ƙiftawa, sai kuma idanunsa na juya mata kamar ana gara ƙwallo, a haka ta ga ya mayar da idonsa kan Fulani Umaima yana hararta ita ma fuskarsa tamkar ba ta jariri ba, lokaci ɗaya Inna wuro ta ji wani irin tsoro ya kamata da sauri ta kawar da kanta gefe. Babu yadda ta iya haka ta sa hannu ta yanke mabiyar ta naɗe ta gyara wurin, sai dai idan ba gizau idonta ya yi mata ba har gani ta yi yanayin surar fuskar jaririn tana rikiɗa daga wannan kammanin zuwa wani, a zabure ta sake kai idonta kansa don yadda ta ji faratan hannuwansa sun karce da ƙarfi har sai da wurin ya yi shati, don haka ta yi saurin kawar da kanta gefe gabanta na matsanancin bugawa. Duk wani aiki da Ungozoma take aiwatarwa Inna wuro ce ta gudanar a cikin daren, kafin wani lokaci Fulani Umaima ta fito shar ita da jaririnta. Tun da Inna wuro ta fita wankin kayan da aka ɓata Fulani Umaima ta ɗauki jaririn ta ƙura masa idanu, fuskarsa faffaɗa ce mai ɗauke da ɗan buɗaɗɗan hanci da manyan idanuwansa ma su ban tsoro. Kuma jarirantakarsa ba ta ɓoye jajayen idanunsa ba, lokaci ɗaya ta ji gabanta ya yi mummunar faɗuwa don babu ta inda jaririn nan ya ɗauko kamannin Sarki Abdul'aziz ko kuma kammaninta. "Kar dai a ce wannan ɗan Boka Shaddas ne?" Fulani Umaima ta faɗa a hankali ƙirjinta na bugawa. Ba ta da amsar tambayarta don haka ta ja bakinta ta tsuke, suna haɗa ido da jaririn sai ta ga tamkar harara yake wurga mata, a ɓangare guda kuma yadda kansa yake suɗal babu ko ɗigon gashi a jiki. Sai da Inna wuro ta gama komai sannan Fulani Umaima ta ba ta umarnin zuwa ta sanar a lungu da saƙon cikin masarautar, har zuwa wurin Jakadiya don ta sanar da Sarki Abdul'aziz. Idan lokacin bikin ya zo mutanen Rumzu kan ɗauki kwanaki biyar suna shagali, kuma kowacce rana da kalar dabbar da za su yanka su yi watanda da ita. Sai dai daga amarya har ango ana gasa musu naman tantabaru kullin, don su ba sa cin naman da 'yan biki za su ci. Ana gobe za su tare sai a kai su bakin bishiyar kukar da suke bautawa su yi tsirara su kwana a haka domin ta saka albarka, a kan sabuwar rayuwar da za su fara gudanarwa. Washegari da sassafe sai duka 'yan garin sun taru a bakin bishiyar don yi wa abar bauta godiya sannan a kai amarya da ango ɗakinsu. Tun daren ranar Jawahir ban da tsala kuka babu abin da take yi, duk yadda aka kai ga rarrashinta abin ya ci tura. Haka Mai gado ta saka ta a gaba ita ma ta fara zubar da ƙwalla don a tsammaninta wani abu ne yake damun Jawahir. Sai kusan doshin asuba sannan ta samu bacci ya yi awon gaba da ita. Ayarin waɗansu baƙaƙen mutane ya gani tafe sun dunfaru sashen Mai martaba hannuwansu ɗauke da miyagun makamai, cikin sanɗa yake biye da su da zarar ya ga za su waigo sai ya yi saurin laɓewa a wani lungun. Yana biye da su har suka shiga ɗakin Mai martaba, ta gefen da yake hangarsu wani jariri ya gani fuskarsa sam ba ta yi kama da ta ainihin jarirai ba. Yana nan tsaye ya ga jaririn ya dira a gaban Takawa. "Ni ne ajalinka wallahi sai na kashe ka na kashe duka mutanen masarautar nan! Sai mun kafa sabuwar da'ira ni da mahaifina domin wannan masarautar ba ta dace da shi ko kai ba. Mahaifiyata Fulani Umaima ce, ita ma ba zan bar ta ba har sai na hallaka domin na tabbata nan gaba tana iya hallaka mahaifina." Yana gama faɗar haka ya bushe da wata irin dariya, daga cikin bakina wani baƙin jini ne ya fara ɗiga. Jin motsin Kamalu ya sa gabaɗaya suka kallo wurin da yake ɓoye, suka dunfaro shi gadan-gadan da niyyar hallaka shi. "Kamalu! Kamalu me yake damunka?" Kalaman Baffajo suka tashe shi daga mummunan mafarkin da yake yi. Ya haɗa gumi sharkaf jikinsa sai karkawa yake, tsoro ƙarara ya bayyana a idonsa. Da sauri Baffajo ya rungume shi a jikinsa ya fara tofa masa addu'a sai da ya ga Kamalu ya dawo cikin nutsuwarsa sannan ya ɗago shi ya ce. "Mafarki ka yi ne Kamalu? Kullin fa ina gaya maka idan za ka kwanta ka ɗauko wannan layar da na baka ka saka ta a ƙasan kanka. Dubi hannunka kamar ka Kamalu a ce ko guru babu a jikinka, an ya kamalu rayuwa za ta tafi haka?" "Baffajo za su kashe Mai martaba, wallahi har mutanen masarautar nan gabaɗaya ni ma gab nake da su kashe ni. Kuma jaririn ya ce mini wai ɗan Fulani Umaima ne, shi ne yake fesar da jini wallahi har kaina ya nufo zai hallaka ni." Ya ƙarasa maganar yana cusa kansa a cikin ƙafafuwansa. A wannan karon jikin Baffajo ba ƙaramin sanyi ya yi ba, fargaba ta dirar masa da jin kamalan Kamalu na ƙarshe. Ya dafa kafaɗarsa. "Ka yi shiru Kamalu kada ka saka mu a matsala, ka daina ambatar sunan iyayen gidanmu idan aka ji kashinmu ya bushe. Babu wata halitta da za ta iya cutar da mu In shaa Allah. Idan Allah ya kai mu gobe zan shiga dawa na haɗo maka turaren miyagu da ƙwanƙwamai ka ji." Kai kawai Kamalu ya iya gyaɗawa amma har lokacin ƙirjinsa bugawa yake. Tun a cikin daren Inna wuro ta fita ta sakin guɗa tana shelar haihuwar Fulani Umaima, kafin wani lokaci gabaɗaya maganar ta karaɗe cikin masarautar. Mai martaba da ya ji maganar ya nuna farincikinsa sai dai babu wani ɗoki da nuna zumuɗin irin wanda ya yi a lokacin da ta haifi Muhsin. A yanzu babba burinsa bai wuce ya ga Allah ya sauki Sailubansa lafiya ba. Bayan Inna wuro ta gama shelar tana komawa wurin Fulani Umaima ta sallame ta tare da yi mata alƙawarin babbar kyauta zuwa wayewar gari. Tun da farar safiya Inna wuro da sauran Bayin Fulani Umaima suka shiga yi mata hidimar ɗora ruwan wanka da abin da ba a rasa ba, Fulani babba ma tun da wuri ta shiga yi mata barka sai dai ita kanta Fulani Umaima a ƙasan zuciyarta kunyar nuna wa mutane jaririn take don gani take kamar wani zai yi mata wata fassarar, ko a gano jaririn ba jinin Takawa ba ne. Tun a ranar da ta haife shi wani abu ya nemi ɗaure mata kai, idan ta fita zuwa banɗaki ko yin wani uzurin, tana dawowa za ta ci karo da ɓoyayyun kayan tsafinta a gefen jaririn. Wani lokacin ma har akwatin da ta ajiye littafin da Bamaguje ya ba ta take ganin a kawo ta tsakiyar ɗakin, idan zuma ta ajiye ko nono da kunu suma haka za ta zo tarar an shanye kusan rabi ko fi ma. Wani lokacin kuma a yi mata faca-faca da shi a ɓata mata ɗaki, tsoro-tsoro ta fara ji don idan take bin jaririn da kallo kuma ƙir haka za ta ga ya kafe ta da ido yana kallo. *Fulani Umaima ta samo daidai da ita.*🤣🤣🤣🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️ SHU'UMAR MASARAUTA 19 *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Ganin tsaiwa da saƙa da warwara ba zai kai ta ba ya sa Fulani Umaima ɗan ƙwanƙwasa ƙofar da ɗan ƙarfi haɗe da ɓoye sihirtacciyar butar a cikin zaninta. "Waye nan?" Ta ji an furta, ana ƙarasowa wurin ƙofar. "Muna buƙatar ganawa da Mai martaba."Cewar Fulani Umaima. Da mamaki Dogarin yake duban Fulani don a lokacin dare ya yi kusan sha biyu ta ɗan gota. "Allah ya taimake ki ranka shi daɗe ya jima da kwanciya..." "Kana nufin ba zan iya ganinsa ba?" Fulani Umaima ta furta a harzuƙe. Babu musu ya turo ƙofar sai da ta shiga ta wurga masa harara sannan ta wuce cikin sashen Mai martaba. Tana shiga soron ƙarshe ta ja ƙofarsa ta datse cikin sanɗa ta wuce ta ƙofar sashen shaƙawatar Sarki Abdul'aziz, duhun daren bai sa Fulani Umaima ta tsorata ba don haka sai da ta yi tafiya mai nisa sannan ta tsugunna a bakin wata bishiya ta fara haƙawa da sauri. Sai da ta tabbatar da ta yi haƙa mai ɗan zurfi sannan ta tura butar ta mayar da ƙasar ta rufe, a fili ta saki murmushin samun nasara tana jin wani farinciki na ratsa ta tamkar wacca aka yi wa kyautar aljanna. Da sauri ta kewaya ta buɗe ɗakin Sarki Abdul'aziz bakinta ɗauke da sallama a lokacin tuni ya jima da yin bacci, sai da ta jima a tsaye tana kallonsa sannan ta bubbuga ƙafarsa. Da mamaki yake kallonta ya yunƙura ya tashi zaune yana shirin yin magana ta riga shi. "Wallahi tsora ta ni ake yi yanzu haka bacci ya gagari idanuna." Mamaki ya bayyana ƙarara a fuskarsa. "Tsoro fa? Me yake tsora ta ki?" "Tafiya nake ji sai kuma na ji an koma!" Ajiyar zuciya ya sauke sannan ya furta. "Shi kenan sai ki kwanta a nan." Yana gama maganar ya matsa mata, a yadda ta lura sam bai ji daɗin kwananta ba. A fakaice Fulani Umaima ta sakar masa harara. "Da ni kake zancan ba dai kana wani rawar ƙafa a kan Fulani Babba ba kai wai mai mata, za mu gauraya ne." Fulani Umaima ta yi maganar a zuciyarta. Rage kayan jikinta ta fara yi sannan ta koma gefen Takawa ta kwanta zuciyarta ƙal saboda tsabar farinciki kasa runtse idanunta ta yi ba ta san lokacin da bacci ya ɗauke ta. "Akwai dalilai da dama da ya sa na ƙauracewa dangina, asalina da tushena na guje su domin ni ban kasance tamkarsu ba, me ya sa kike son kawar da ƙwayar idonki a kan abin da yake daidai? Ke ba kamar sauran mutanen da ke rayuwa a cikin wannan masarautar ba ne hasali ma mutane da dama suna farautar rayuwarki." Shiru Jawahir ta yi tana sauraron matar da tun haɗuwarsu ta furta mata cewar ita mahaifiyarta ce. A hankali ta ga matar ta ƙaraso gabanta ta dafa kafaɗarta sannan ta ci gaba. "Ki je sashen Sarkin cikin masarautarku ki tone abin da matarsa Fulani Umaima ta binne idan ba haka ba Fulani babba za ta mutu, idan kika bari Umaima ta ci gaba da yin nasara a cikin masarautar nan ina mai tabbatar miki sai ta yi nasara a kanki. Sai ta damƙa ruhinta ga hatsabibin boka Bamaguje kuma ki sani matuƙar ruhinki ya je gare shi babu wani taimako da ni ko abin bauta za mu iya yi miki." Tsoro ne ya mamaye zuciya Jawahir, a sanyaye ta furta. "Wallahi tsoro nake ji idan Fulani Umaima ta kama ni kashe ni za ta sa a yi." Take annurin fuskar matar ya ɗauke, ta fara ja da baya a hankali sannan ta daki guntun tsaki. "Tun ranar da na buɗi ido a cikin zuri'ata ban taɓa jin kalmar tsoro ta fito daga bakinsu ba, tabbas Shugaba Zurufu ya yi gaskiya ga irin abin da yake guje wa zuri'armu dangane da auren bare, auren da ba zuri'armu ba." Sai da matar ta tsaya cak fuska a haɗe. "Jawahir!" Ta ambaci sunanta cikin wata irin murya. "Ki gaggauta zuwa ki lalata tsafaffiyar butar da ta binne, ki ɗebi ruwan kogin tsamiya ki kwara a a sashen Fulani babba idan kika bari ta yi nasara a kanta nan gaba tana iya yin galaba a kanki, wannan umarni ne nake ba ki a matsayina na mahaifiyarki." Firgigit Jawahir ta farka daga nnnauyan baccin da ya ɗauke ta mai cike da tarkacan mafarkai kala-kala. A daidai lokacin Mai gado ta shiga ɗakin ta ajiye butar da ta yi alwalar sallar Asuba. "Jawahir tashi ki yi sallah kin san anjima kaɗan za ku tafi sassaƙar dawa." Da wani irin kallo ta bi Mai gado gabanta na faɗuwa, wani irin tsoro na lulluɓe ta. A hankali ta furta. "Inna don Allah wata magana nake son yi miki amma don Allah kada ki buge ni." Rass gaban Mai gado ya faɗi, a hankali ta koma kusa da ita ta zauna. Kasancewar Fulani Babba mai sanyin hali da rashin hatsaniya ya sa ko da aka kawo ta masarautar Huddam ba ta samu matsala da kowa ba, tana matuƙar girmama Mai babban ɗaki don ta ɗauke tamkar mahaifiyarta. Sai da Fulani Asabe ta gama karantar halayen Fulani babba tsaf sannan ta nemi jan ta a jiki don ta haka take son cim ma manufarta, idan ta janyo ta jiki ta dinga bugar cikinta tana jin sirrin Sarki Abdul'aziz daga ƙarshe kuma ta jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya. Fulani babba zuciyarta ɗaya ta aminta da Fulani Asabe amma da yake mahaifiyar Sarki Abdul'aziz ta san halinta sarai sai watarana ta sa aka kira mata ita ɗaki ta nusar da ita halayen da ɗabi'un mutanen cikin gidan don haka dole sai ta yi takatsantsan. Ba ƙaramim daɗi ta ji ba ta sake godiya ga Allah, da Allah ya haɗa ta da mahaifiyar miji ta gari don koda ta san masarautarsu ba ta kai wannan girma ba ta san suma suna fama da kacaniyar makirci da tuggu don haka sai ta iya zama da kowa a ruwan sanyi. Ganin hanyar da Fulani Asabe ta ɗauka ba za ta bille mata sai wata dabarar ta faɗo mata, ta ji daɗi sosai da wannan tunanin ya zo mata a daidai gaɓar da take buƙatar ɗauki. Ƙanwarta Zulai da ke aure a Masarautar Bhahdi ce ta faɗo mata da yake ta san tana da 'yan mata guda biyu, Umaima ita ce babba sai ƙanwarta Zannira, ta na da yayye maza da ƙanne maza. Takanas Fulani Asabe ta kai wa ƙanwarta ziyara don a wannan karon ba za ta aika da saƙo ba. "Zulai aure nake so na ƙulla tsakanin Umaima da Abdul'aziz, amma aure ba na zama dundundun ba." Mahaifiyar Fulani Umaima ta ɗan yi jim. "Ban fahimce ki ba Yaya." "Ina nufin za ki ba ni Umaima na tafi da ita, ni zan yi duk shige da ficen da zan yi wurin malamai da bokaye don ta saye zuciyarsa. Babban burina ya aure ta duk wani kuɗirina sannu a hankali zan dinga zana mata tana aiwatarwa. Ƙarfi da yaji so nake sarautar Masarautar Huddam ta dawo hannun wannan yaron, idan ma mutuwa ce ta dace da Abdul'aziz ni ban damu ba domin kin fi kowa sanin yadda na ƙallafa rai a kan karagar nan, saboda Masarautarmu ta sha bambam da masarautun nahiyar afirka gabaɗaya." Dariya mai sauti Zulai ta saki. "Sai yanzu na fahimci inda kika dosa don na san bakya ƙwanki sai da zakara, ni dama tun da na fara jin kalamanki na san banza ba ta kai zomo kasuwa. Yanzu dai idan komai ya kammala me ye kasonmu?" Fulani Asabe ta bushe da dariyar farinciki tamkar buƙatarta ta gama biya. "Babu abin da za ki buƙata ba zan aiwatar miki ba Zulai, ai ranar biyan buƙata rai ba a bakin komai yake ba." Sai da Mai gado ta aro mayafin jarumta ta yafa wa gangar jikinta sannan ta furta, "Mene ne Jawahir? Gaya mini babu abin da zan yi miki." Jawahir ta ɗan fara murza hannunta a hankali tana jin gabanta na faɗuwa ga wani irin raɗaɗi da tambarin cikinta yake yi mata ta furta. "Inna wannan matar da ta ce ita mahaifiyata yau ma na sake yin mafarki da ita, wai ta ce mini Fulani Umaima ta binne abin da Fulani babba za ta mutu..." Gabaɗaya abin da ya faru ta kwashe ta gaya wa Mai gado, da sauri Mai gado ta sa hannu ta rufe mata baki. Sai da ta tashi ta je ta tura ƙofar ɗakinsu don kar wani ya ji abin da suke faɗa sannan ta koma wurin da Jawahir take zaune. "Ki yi shiru da bakinki kin ji Jawahiruna. Ni kaɗai ce mahaifiyarki ba ki da kowa sai ni kin ji, sharrin sheɗanu ne suke saka ki yin mafarki amma zan sa Malam ya karɓo miki turaren miyagu. Koda wasa kada ki sake ki faɗawa kowa kin ji." Jawahir ta gyaɗa kai a hankali kamar mai nazari sannan ta ce. "Kuma ta ce abin bauta zai yi fushi da ni mai tsanani idan na bari Fulani Umaima ta yi galaba a kaina..." "Kul Jawahir kina son ki jefa mu cikin kogon bala'in da za mu yi tsallen da har abada ba za mu iya fitowa ba?" Jawahir ta girgiza kai. "To kin ga daga yau duk ranar da kika yi mafarki da ita ki ce ke ba ki san wani abun bauta ba kin ji." Jawahir ta amsa sannan ta miƙe har ta je bakin ƙofa ta dawo ta zauna. "Inna wallahi Yaya Habu tausayi yake ba ni saboda da guba a jikinsa." Wannan karon Mai gado ba ta dakatar da ita ba sai ma tambaya da ta wurga mata. "Guba wacce iri Jawahir?" Fulani babba sai da dare ya tsala sosai ta farka sakamakon yadda ta ji wuyanta ya sage mata, a hankali ta tashi har ta je bakin ƙofa ta koma ta sumbaci Abubakar. "Allah ya baka lafiya Abubakar ya nuna mini lokacin da zan ganka ka koma kamar kowa." Ta furta a hankali sannan ta wuce ɗakinta. Tana kwanciya babu jimawa bacci ya yi awon gaba da ita, cikin bacci ta riƙa jin wani abu na yunƙurin fita daga cikin ƙasanta tamkar ɗa yana son fitowa daga ƙasanta. Da sauri ta buɗe idanunta a hankali ta furta. "Yau me nake ji haka a cikin daren nan?." Ta so ace safiya ko rana ce da ta yi turare miyagu ko ta ɗan ji daɗin jikinta. Kwanciya ta sake yi sai dai a wannan karon bacci ya ƙaurace mata, sakamakon yadda take jin duk wata gaɓa ta jikinta kamar ana fusgarta da ƙarfi. A ɓangare ɗaya kuma wani irin zafi ne yake ratsa lungu da saƙon cikinta, babu jimawa kuma ta ji wata irin iska mai daɗi na shiga jikinta wanda hakan ne ya yi sanadiyyar da bacci ya yi awon gaba da ita. Tun asubar fari Fulani Umaima ta so yi wa Sarki Abdul'aziz sallama don ta koma sashenta ta baza kunnuwa ta ji rahoton da zai fito daga ɓangaren Fulani babba da Sailuba, amma gudun kada ya fahimci wani abu ya sa ta haƙura har sai da gari ya waye tangararan. Tana shiga ɗakinta ta samu Basiru ya hargitsa mata ɗaki yana bincike, da mamaki take bin shi da kallo don tun daga rumfa (Falo) har zuwa uwar ɗaki a birkice yake. "Me kake nema da ka hargitsa mini ɗaki?" Kafe ta ya yi da jajayen idanunsa fuska a turɓune, kallon ƙwayar idonsa ya hadda sa mata mummunar faɗuwar gaba. Kammaninsa da na Boka Shaddas suka sake bayyana ƙarara, har sai da ta ji wani kwarjini da shakkunsa ya mamaye ta. "Tambayarka nake me ka ajiye mini da kake birkita mini ɗaki za ka ɗauka?" Fulani Umaima ta sake tambayarsa cikin dakiya. "Wani littafi nake nema?" Ras! Gabanta ya faɗi. "Kai ka ajiye shi?" "Ni da ɗakin mahaifiyata sai na ajiye abu zan ɗauka?" Da mamaki take bin sa da kallo, ba tun yau ba ta lura da tsagerancinsa. Duk da shi kansa Muhsin ba kanwar lasa ba ne wurin rashin kunya amma na Basiru ya dame shi ya shanye, dalilin haka ya sa ko kaɗan ba su cika ga maciji da Takawa ba. Saboda har Takawa Muhammad bai bari ba idan ya so tata masa rashin mutumci. Idan Fulani Umaima ta fara wassafa miyagun ɗabi'unsa a zuciyarta har mamakin ƙanƙantar shekarunsa take yi da hatsabibancinsa. "Fice mini daga ɗaki!" Ta furta fuska a haɗe. "Duk ma inda kika ɓoye shi sai na lalubo shi, saboda dole ne na cika umarnin mai gida. Don haka idan kere na yawo zabo na yawo dole watarana za a haɗu. Ki rubuta ki ajiye ko da arziƙi ko da tsiya sai na mallaka masa littafin nan." Yana gama maganar ya gegare ta ya wuce har yana bangazarta ya fice daga ɗakin. "Duk rintsi kada ki sake wani ya ƙwace littafin nan daga wurinki Umaima." "Ke ba kamar sauran kowa ba ce a wurina don haka na damƙa miki wannan sihirtaccan littafin ki kula da shi." "Ina fatan dai kin yi wa littafin nan kyakkyawar maɓoya?" "Ina sake jan hankalinki kada ki saki jiki da kowa a kan wannan littafin duk kusancinki da mutum koda ɗan cikinki ne!" Ire-iren kalaman da Bamaguje yake furta mata kenan a lokutan baya idan ta ziyarce shi, ajiyar zuciya ta sauke ta shiga kiciniyar gyaran uwar ɗakinta don ba ta barin kowacce Baiwa ta shigar mata ɗaki saboda kayan tsubbace-tsubaccan da ta rataye. Sai da Jawahir ta ɗaga rigarta ta ɗora hannunta saman tambarin cikinta ta yi kasaƙe kamar wacce take sauraron wani abu sannan ta furta, "Tsohuwar guba ce da ta bi ilahirin jiki da ruhinsa, ban san tsahon lokacin da ta ɗauka a jikinsa ba amma ta riga da ta illatar da ruhi da gangar jikinsa." Jawahir ta ɗan ɗago ta kalli Mai gado. "Na san faɗa za ki yi mini Inna amma da na sanar wa Fulani Babba don a nema masa magani." Shiru Mai gado ta yi tana nazari. "Idan kina dakatar da ita za ta daina sanar da ke halin da take ciki." Tsagin zuciyar Mai gado ta gargaɗe ta. Sai da ta sake janyo Jawahir jiki sannan ta furta. "Jawahir duk cikin gidan nan babu wacce nake so nake ƙauna har a raina kamar Fulani babba, to amma ki dubi matsayinmu a cikin gidan nan. Mu ƙasƙantattu ne da ba su da 'yan kansu ballantana galihu, ban da Allah Ya sa Fulani babba ta ja mu a jiki da bautar da za mu dinga yi irin ta su Laure ce. Furta irin waɗannan maganganun matuƙar suka fito sarari ba zai haifar mana da ɗa mai ido ba, Idan kin yi mafarki ko wani tunanin ya zo miki ki same ni a ɗaki ki riƙa gaya mini idan ya so sai mu tattauna ni da mahaifinki." Ganin Mai gado ta bata ƙwarin gwiwa ya sa ta ji daɗi har ta faɗaɗa fara'arta a fili, fita ta yi don ta ɗauro alwala Mai gado ta bi bayanta da kallo cikin jimami da matsananciyar damuwa. Sai da ta tabbatar su Jawahir sun tafi sussuƙar gero sannan ta kira Umaru don su tattauna matsalar da Jawahir take son ɓallo musu. "Malam ba ya ta haihu fa?" "Kamar yaya?" Ya tambaye ta fuska ɗauke da damuwa. "Da alama zancan mahafiyar yarinyar nan na ci gaba da bayyana, idan ba ka manta ba da kanta ta ce mana 'yarta ce za ta bayyana surar jinsi da ta hallitar zuri'arsu bakiɗaya." Duk abin da Jawahir ta faɗa wa Mai gado tas ta kwashe ta gaya masa, shiru ya yi sannan ya furta. "Ki ci gaba da jan ta a jiki kada ki bari ta furta wata maganar da za ta kai ga jawo mana matsala, zan shirya fitar sirri akwai wani Mai magani da na ji Mai martaba ya sa an karɓo wa Fulani magani a wurinsa." Sai da Mai gado ta ji haka sannan ta ɗan saki ranta ta ci gaba da harkokinta. Sai da asuba ta yi sannan Fulani babba ta iya buɗe idonta, ta yunƙura da niyyar tashi lokaci ɗaya ta ji jikinta tamkar an ɗaɗɗaure ta. Motsa ƙafarta take son yi amma sai ta ji ilahirin jikinta ya yi mata nauyi dum! Kamar an danne ta da narkeken dutse, wani abu da ya sake ɗaga hankalinta yadda take jin jikinta tamkar ba nata ba. Tana daga kwance ta fara ƙwalla wa Mai gado kira ita da Baiwa Zainaba amma shiru babu wanda ya amsa mata. Tana nan kwance hawaye ya fara gangaro mata don duk yadda ta so iya motsa jikinta abin ya gagara, sai da gari ya waye tangararan ta fara jiyo gwarancin Abubakar don ta tabbata yunwa yake ji. Babu jimawa ta ji sallamar Baiwa Zainaba, da sauri ta fara jera mata kira. Jin kiran ba na lafiya ba ne ya sa Baiwa Zainab ta faɗa ɗakin da sauri. "Allah ya taimake ki ranki shi daɗe." Take zuciyar Fulani Babba ta karye murya na rawa ta furta, "Shigo Zainab." A hankali Baiwa Zainab ta shiga ɗakin. "Zainab wata ƙaddarar ta sake rikito wa rayuwata, tun asuba idona biyu amma na gagara motsa koda ɗan yatsana ne. Maza je ki kira mini Mai gado ki ce ta zo cikin gaggawa." SHU'UMAR MASARAUTA 20 *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Tun da ya yi wa Baffajo tambayar ƙirjinsa yake bugawa fat fat fat zuciyarsa tamkar za ta hudo ƙirjinsa, fargabarsa ɗaya kada ya ji mummunan labari a kan tushen asali da samuwarsa. "Kamalu da waɗannan hannuwan nawa na tsinto ka a cikin kogon wata ƙatuwar bishiyar kukar da ke cikin ƙasurgumin wani dajin da ke cikin Rigar Arɗo wanda ake kira da Dajin Wushushe da ke gefen ƙoramar Ɗinya, a ranar da ake gudanar da babban bikin shaɗi tun safe na tashi da kasalar jiki ban san dalili ba don har na fasa fita kiwon Shanu sai kawai wata zuciyar ta shawarce ni da na bi bayan su Salele. Cikin ƙudurar Ubangiji bayan na tafi sai wani irin zazzaɓi ya rufe ni, don haka na nemi gefen bishiya na ɗan kishinhiɗa don jikina babu ƙwari. Kamar almara ina zaune sai na fara jin kukan jariri daga gefena, nan take na ciro guruna da layun da ke ƙuguna don a tunanina ko mutanen nan dajin ne suke niyyar buɗe mini idanu da tsakar rana, har na fara haramar yin turare sai idanuwan suka kai kanka kana kwance cikin kogon bishiyar kukar da kallonta kaɗai sai da ya hargitsa mini kwanta. Wata irin juwa na ji tana yunƙurin ɗaukata, idanuwana suka fara yi mini gizo har nake ganin bishiyar tamkar tana tafiya a bisa kanta. Kamar na wuce sai kuma nake jin zuciyata ta yi rauni ba zan iya barinka ba. Idan idanuwana ba gizo suke yi mini ba a lokacin da na fara tunkarar murgujejiyar bishiyar kukar, har gani na yi tamar tana matsawa baya da kanta. A haka na ci gaba da tafiya zuciyata na rawa har na ɗora hannuna a kanka na ɗauko, sai dai abin da ya matuƙar ba ni mamaki bai wuce ganin wani zagayayyan jini a saman kanka ba tamkar wanda aka ɗora hular sarauta. Wani abu da ya sake tsinka mini rai ganin na kai hannuna kanka don na goge jinin kai amma kuma sai na ga tamkar danƙare yake a fatar jikinka, a haka na rungume ka har zuwa gida na kawo wa Innarka kai sai dai muna zuwa gida wannan jinin babu shi babu alamarsa. Ina tunanin hankalina ya kwanta sai kuma muka lura da wani baƙon al'amari a tattare da kai wanda ba mu taɓa ganin halittar ɗan adam da irinsa ba." Lokacin da Mahaifiyar Fulani Umaima ta samu Umaima da buƙatar Fulani Asabe ta zo da ita, tamkar dama tana son abin a ranta don ko a fuska ba ta musa ba. A ranar da Fulani Asabe za ta koma a ranar suka wuce tare da Fulani Umaima. Fulani Umaima tun tasowarta fitsararriyace ga rashin tsoro duk wani abu da za ka yi mata baraza da shi ba zai tsorata ta ba. Uwa-uba kafiya, taurin kai ta taurin zuciya. Tana da matuƙar wayo sosai don lokaci ɗaya ba za ka taɓa gane ainihin halayya da ɗabi'unta ba, tun ba ta kai haka ba ta iya makirci, kissa da kisisina saboda ko a cikin Masarautarsu Mahaifiyarta ba ta jin ko ɗar a game da ita, kuma duk cikin 'ya'yanta ta fi ji da ita. A ranar da ta fara tozali da Sarki Abdul'aziz a ranar kwana ta yi tana ayyana abubuwa da dama a cikin zuciyarta, a yadda zuciyarta ta yi nisan kiwo a kansa ba ta jin za ta iya rabuwa da shi kamar yadda Fulani Asabe ta ce za su yi auren jeka na yi ka. Sannu a hankali sai ta fara shige wa Fulani babba tana yi mata hidimar ɗan aikace-aikace da taya ta hira, da farko daga Mai babban ɗaki har Fulani babba babu wanda ya saki jiki da ita, sai daga baya da suka ga yanayin kyawawan ɗabi'un d Umaima ta nuna musu sai suka sako jiki da ita. Makwan Umaima takwas Fulani Asabe ta ba ta wani farin kwalli ta ce ta saka shi kuma ta tabbatar da sun haɗa ido ita da Sarki Abdul'aziz, daɗi ya lulluɓe Umaima har murnarta ta bayyana a fili. "Ba na son sakarci fa, kada ki ɗauka auren jindaɗi da kwanciyar hankali za ki yi." Da kamar Fulani Umaima ta musa amma sai ta ƙaƙalo murmushi ta furta. "Ba ina yin murmushin saboda wata manufa ba Inna, ina sakin murmushin murna da jin daɗin ganin mulki da sarautar gidan nan sun kusa dawowa tafin hannunmu ne." Fulani Asabe ta saki murmushin farinciki. "Shi ya sa nake ƙaunarki uwar ɗakina." Shiru Fulani Umaima ta yi tana bin Fulani Asabe da kallon ba ki da hankali, don haka ta sake kwantar da kanta har lokacin da Allah ya haɗa fuskarta da Sarki Abdul'aziz. A ranar da ya yi tozali da ita a ranar ne ya yi tattaki har zuwa wurin Mahaifinsa da maganarta. Bai hana shi ba don ganin shi ne shugaba kuma wakilin Masarauta, don haka cikar kamalarsa za ta ƙaru ne idan ya tara iyali sama da ɗaya. A lokacin da Mai babban ɗaki ta samu wannan labarin ranta ba ƙaramin ɓaci ya yi ba, don haka kawai ta ji Umaima ba ta kwanta mata ba, take ta nuna wa Sarki Usman rashin amincewarta amma sai bai ba ta goyon bayan ba. Duk wannan abin da yake faruwa Fulani babba ba ta san wainar da ake toyawa ba, sai dai ta lura da sauye-sauye tsakaninta da Maigidanta. Ya bijiro mata da sababbin halayen da ba ta san da su ba kamar; kyara, hantara, yawan faɗa, saurin fushi da ƙaurace mata, amma gudun tashin hankali a tsakaninsu sai ta riƙa takatsantsan. Amma kuma ta yi mamaki matuƙa da ta ga Umaima ta janye ƙafarta daga shiga sashenta har sai da watarana ta taɓa aika bayinta su gano mata ko lafiya kwana biyu ba ta zo mata ba. Duk da saƙon da Fulani babba ta tura wa Umaima bai sa ta taka ta je ba domin a ganinta ai buƙatar maje hajji sallah, buƙatarta ta riga da ta biya babu sauran wahalar da kai. Lokacin da Mai gado ta ji saƙon kiran Fulani babba da halin da take ciki ba ƙaramin kaɗuwa ta yi ba, zani daban riga daban ko ɗankwali ba ta ɗaura ba ta ɗora mayafinta a kanta ta fice. "Ko dai abin da yarinyar nan ta faɗa gaskiya ne?" Mai gado ta ayyana a zuciyarta. Kamar za ta tashi sama hake take zabga sauri tana shirin gifta ƙofar Fulani Umaima ta ji an furta. "Keee!" Cak Mai gado ta tsaya cikin saranda ta waiga. "Allah ya taimaki ranki shi daɗe." "Ina za ki je?" Fulani Umaima ta tambaya don son jin halin da Fulani babba take ciki. "Tuba nake ranki shi daɗe, Fulani ce ta aika na zo da gaggawa ba ta jin daɗi." Wani sanyi ya ratsa zuciyarta amma sai ta fuske. "Idan kin gama da sashenta ina son ganinki." Rass! Gaban mai gado ya faɗi don ko kaɗan ba ta san wata alaƙa da za ta shiga tsakaninta da Fulani Umaima musamman da ya zama duk cikin Bayi Fulani babba ta fi aminta da ita. "An gama ranki shi daɗe, ki huta lafiya." Mai gado ta furta a sanyaye sannan ta wuce bayan Fulani Umaima ta sallame ta. "A gafarce ni uwar ɗakina idan na yi jinkirin zuwa." Mai gado ta yi magana tana ƙarasawa jikin gadon Fulani babba zuciya a tsinke. A madadin Fulani Babba ta iya tanka mata sai kawai ta fashe da matsanancin kuka, hankali a tashe Mai gado ta matsa gabanta idanunta suka ciko da ƙwalla. "Uwar ɗakina akwai abin da yake damunki ne?" Sai da Fulani babba ta yi kuka mai isarta sannan ta sanar da Mai gado duk abin da yake faruwa, ban da hawaye Mai gado babu abin da take yi, da ƙyar ta iya ɗaga Fulani babba ta jingina da bango ta sauya mata kayan jikinta ta ɗaura mata alwala tana yi tana zubar da ƙwallah. "Ranki shi daɗe mai zai hana a aika da takarda ƙasar Rumm a sanar da Yadikko halin da kike ciki?" Fulani babba ta kalli Mai gado tana son ta girgiza kanta amma ta kasa. "Mai gado... mahaifiyata girma ya kamata, ga Yaya Halima da ke gabanta tana fama da lalurar hauka. Idan na sanar da ita hankalinta zai ƙara tashi." Mai gado ta share ƙwallar idonta tana shirin yin magana Fulani babba ta ci gaba da cewa. "Ban sanki ba, ban san daga inda kika fito ba Mai gado, amma duk cikin masarautar nan da ke kaɗai na aminta." Kuka ya ci ƙarfin Yaya babba, Mai gado ta share mata hawaye duk da ita ma kukan ya gagara tsagaitawa daga ƙwayar idonta. "A halin da nake ciki jikina yana ba ni ajali ya kusanto ni, tawa ta zo ƙarshe. Don Allah ko bayan rayuwata ki kula mini da Abubakar, na san wannan wahalallan alƙawari ne na damƙa miki domin ba ki da ikon kanki wataƙila ma a hana ki shiga al'amuran shi. Amma idan har kin samu dama ki kula mini da shi, na bar shi a hannun Allah da hannunki Mai gado." "Ranki shi daɗe cuta ba mutuwa ba ce, ki daina faɗin haka In shaa Allah za ki samu lafiya." Murmushin yaƙe Fulani ta saki. "Na yi jinya kala-kala Mai gado, na gamu da cutuka mabambam amma wannan ciwon da na wayi gari da shi daban yake da sauran." Lokaci ɗaya wani irin tari ya turnuƙe Fulani babba, ta fara kwara wani irin baƙin aman jini mai wani irin wari. A ruɗe mai gado ta kira Baiwa Zainaba suka fara gyra Fulani babba, a lokacin tuni zuciyar Mai gado ta gama karyewa. Sai bayan wani lokaci Fulani babba ta dawo hayyacinta, Zainaba da Mai gado sai share ƙwalla suke don duk wanda ya ga halin da take ciki sai ya tausaya mata. "Ranki shi daɗe na aika Zainaba wurin Takawa ba ta same shi ba." A wannan karon muryarta ta sake yin ƙasa sosai. "A sanar da Jakadiya idan ya dawo ta sanar da shi halin da muke ciki." Da sauri Baiwa Zainaba ta fita ta samu Jakadiya ta sanar da ita halin da Fulani take ciki. Kamar wacce aka yi wa kyautar Aljanna haka farinciki ya lulluɓe zuciyar Fulani Umaima, ta koma cikin sashenta cikin murna tamkar ta zuba ruwa a ƙasa ta sha. Uwar ɗakinta ta faɗa ta tsinci kanta da ɗauko akwatin da ta adana littafin labarin Hidaya, sai da ta ɗauko ɗaurarriyar fatar da Bamaguje ya bata ta juya a hannunta tana sakin dariyar ƙeta sannan ta mayar ta ɗauko littafin. Sai da ta jingina da bango ta buɗe shafin da ta tsaya sannan ta ci gaba da karantawa. Ban san me ya ba wa Sarki Hafiz dariya a cikin tambayata ba don haka na kafe shi da idanu ina kallo, sai da ya ɗan saita nutsuwarsa ya dube ni yana faɗin. " A tsammanina ko kaɗan bakya daga cikin wani jinsi bayan na bil'adama. A labarin da Kakana ya ba ni wanda shi kansa ya ce kusan labari ne na kunne ya girmi kaka, mahaifiyarki ta kasance 'ya daga wurin sarkin wanzamin garin nan wato Bala wanzam. Su biyu ne 'ya'yansa daga mahaifiyarki sai ɗan uwansa Shamsu, tun tasowar Mahaifiyarki mace ce mai sanyin hali da kyakkyawar mu'amala. Shi kuma mahaifinki ya fito daga zuri'ar Bargi waɗansu mutane ne da ke rayuwa a gaɓar tekunan da ke kewaye da su, waɗannan al'umma al'amuransu na da matuƙar ban mamaki sakamakon ba sa rayuwa a ko ina sai gaɓar teku, kuma duk hunturu ba sa barin wurin. Kuma an yi zargin mahaifinki jika ne ga sarkin ruwan yankin Dahwan, a yadda Kakana ya ba ni labari watarana wani masunci ne ya zo da 'yarsa gaɓar yankin da zuri'ar Mahaifinki suke zaune, sun yi mu'amala da arziƙi da shi yana shiru ruwa da zummar ya yi su, sai kwalakwalensa ya kife da shi. Duk iya ruwa da ƙwarewarsu da kogi ba su iya samo mutumin ba, dalilin haka ya sa mahaifin kakanki ya ɗauki yarinyar da ya bari ya ci gaba da rainonta har ta zama budurwa Kakanki ya aure ta. "Idan na fahimta kenan babu wanda ya asan asalin Kakata kenan?" Na katse Sarki Hafiz daga bayanin da yake yi mini sai dai ko kaɗan kwanyata ta gagara jera kalmominsa a ma'aunin da suka dace. "Mutane da dama sun yi harsashe sai dai har kawo wannan lokacin babu amsa ƙwaƙƙwara kuma mai tushen da za a kafa hujja da ita." Ajiyar zuciya na sauke na sake zuba masa idanu. "A labarin da aka ba ni kakanki tun tasowarsa ya kasance hatsabibi mara tsoro, don an ce waɗansu daga cikin jinsin aljanu har tsoronsa suke ji. A wannan lokacin kuma a kwai ɗan sarkin baƙaƙen aljanu Darri da ya taso cikin taƙadiranci da hatsabibanci kuma ko kaɗan ba sa ga maciji da kakanki, a wannan lokacin sai shi Aljani Dharri ya so auren Kakarki dalili kenan da ya ƙara tsaurara tsattsamar alaƙarsu. Da yake sun buɗe wa kakanki idanu sai ya zamana yana ganinsu muraran har su yi ta sa'insa, daga ƙarshe dai Kakanki ya yi galaba a kanshi don haka sai ya karya ƙadarin Darri, duk hatsabibancinsa sai ya yi laƙwas kuma ya zubar da makamansa. Kwatsam babu zato bayan waɗansu shekaru masu tsayi sai aka wayi gari ɗan autan Dharri ya kamu da matsananciyar soyayya da mahaifiyarki. Da farko mahaifiyarki ba ta san Buhsu ba mutum ba ne, domin idan ya tashi zuwar mata a surarsa ta bil'adam yake zuwa. Sai da ya fahimci soyayyarsa ta yi ƙarfi a zuciyarta sannan ya bayyana mata ainihin zubi da surar hallitarsa. Da yake shi so ƙundunbala yake ya hana ganin laifi ko gezau mahaifiyarki ba ta ji za ta iya rabuwa da shi ba, sai ma soyayyarsa da ta mamaye zuciyarta. Akwai abin da na manta ban sanar da ke ba." Jin kalaman Sarki Hafiz ya sa na ɗago da sauri ina kallonsa, ya jinjina mini sannan haɗe da faɗin. A razane Fulani Umaima ta rufe littafin babu shiri sakamakon jin muryar Jakadiya raɗau a tsakiyar ɗakinta, da sauri ta mayar da littafin ta miƙe ta fito fuska ba yabo ba fallasa. "Umaima wani sabon labari na ji da farar safiyar nan shi ne na zo na ji wanne tuggun kika haɗa wa baiwar Allahr da ba ta ji ba; ba ta gani ba?" A yamutse Fulani Umaima ta dube ta. "Wai dama kura ce za ta ce wa kare maye? To wai ma wane dare ne jemage be gani ba? Zuwa kika yi ki raina mini hankali Jakadiya da za ki kawo mini wannan maganar?" "Fulani na san rashin imaninki sarai, ni kin gan ni na fara tuba ga Ubangiji don zalinci da muka shuka a gidan nan na fara fargaba da tunanin ranar girbarsa." Jakadiya ta yi maganar kamar wacce tsoron Allah ya samu matsuguni a zuciyarta. Shewa Fulani Umaima ta yi sannan ta furta. "Duk ma abin da kika yi tsammani zan iya aikatawa Jakadiya, kin fi kowa sanin wace ce Umaima don haka ƙofa a buɗe take da za ki iya zartar da hisabinki a kaina." Gaban Jakadiya ya faɗi, don wata irin fargaba ce ta dirar mata. Ganin ba ta da abin faɗa ya sa ta fice daga ɗakin kai tsaye da faɗa sashen Fulani Babba. Ƙirjin Kamalu ya ci gaba da bugawa jin labarin da Baffajo yake ba shi, wani irin nauyi kansa ya yi har yaji ƙafafuwansa na yunƙurin bijirewa nauyinsa. Da sauri ya fice daga ɗakin, ya ci gaba da wurga ƙafarsa cikin sauri ba tare da ya san inda yake sa ƙafarsa ba. Can wani ɗan siririn lungu ya bi mai tsananin duhun itace, ya sa mu bakin bishiyar ɗorawar da ke wurin ya zauna. Hannuwa biyu ya sa ya dafe kansa cikin matsananciyar damuwa, tamkar ƙaramin yaro haka ƙwalla ta fara bin idanuwansa zuciyarsa na yi masa ƙuna. "A wannan lokacin da kake ciki sam kuka ba zai fisshe ka ba, kuka da raunin zuciya bai yi daidai da tsarin zubin hallita da ruhinka ba. Ina sake yi maka tuni da kai ba kamar su ba ne, ina ɗora ka a hanya ne saboda aminantakar da ke tsakanina da marigayi Sarki Muhammad Safwan. Ba ni da ikon da zan shiga huruminka domin zuri'ar da ke tare da kai akwai jiƙaƙƙiyar 'yar tsamar da ke tsakaninmu don haka na ke yunƙurin ɗora ka a hanya, idan na nemi na fayyace maka komai zan iya jefa zuri'ata da ta mutanen cikin gidan nan cikin rijiya gaba dubu, da babu rai ɗaya da zai iya tsalle ballantana ya fito. Burinsu su ci gaba da zama tare da kai domin su riƙa cin gajiyarka, amma na tabbata ko ba daɗe ko ba jima akwai lokacin da gaskiya za ta yi halinta. Ina mai haƙurƙurtar da kai mummunan lamarin da zai afka wa rayuwarka babu tsammani, sai dai ina mai shawartarka da ka sanyaya zuciyarka a lokacin da komai zai bayyanar maka." Gama jin kalamansa ya sa Kamalu ya ɗago a sanyaye, ko kaɗan bai fahimci kalamansa ba don haka ya sake sunkuyar da kai haɗe da faɗa wa duniyar tunani. Jakadiya ta matuƙar tsorata da ganin yadda Fulani babba ta koma a cikin kwana ɗaya jal tamkar wacce ta shekara guda tana jinya. "Jakadiya ki dubi Allah ki ce wa Takawa ina buƙatar ganinsa, akwai kalaman sirrin da suke cikin zuciyata da nake son sanar da shi, kalaman da shi kaɗai ya cancanci saninsu don a ganina watarana za su yi masa amfani." Fulani babba ta yi maganar murya can ƙasa idaununta har sun fara shanyewa. "Idan gemun ɗan'uwanka ya kama da wuta maza yi saurin yayyafawa naka ruwa." Jakadiya ta yi maganar a zuciyarta, saboda ganin jikin Fulani babba ba ƙaramin tsoratata ya yi ba. Jiki a sanyaye ta fice kai tsaye ta nufi sashen Takawa a wannan karon tausayin Fulani babba ne ƙarara a zuciyarta. "Allah ya taimaki ubangidana wani muhimmin saƙo ne tafe da ni ranka shi daɗe." Jakadiya ta furta cikin girmamawa. "Muna sauraronki Jakadiya." "Allah ya taimake ka Fulani ta wayi gari cikin matsananciyar jinya har ta kai tana son ganinka domin ta ba ka wasiyya." Take annurin fuskarsa ya ɗauke har sai da Jakadiya ta sha jinin jiminta. "Jakadiya a fice a ba mu wuri muna tattaunawar sirri da manyan baƙi, a je a ce wa Fulani Umaima ta yi duk abin da ta ga ya dace game da magungunan da za a aika mata, idan da hali a gaggauta aikawa sashen ma'ajiyar magunguna idan mun kammala za mu san abin yi." "Ai na san dama biri ya yi kama da mutum, kallo ɗaya na yi wa Fulani na fahimci tsafin Umaima ne ya ci ta, ya zame mini dole na tashi tsaye a kan Sailuba." Jakafiya ta yi maganar a cikin zuciyarta. "Jakadiya muna buƙatar a ba mu wuri, ba ma buƙatar sake ganin kowa a sashenmu." Kalaman Sarki Abdul'aziz suka sauka raɗau a saman kunnuwan Jakadiya, baƙinciki da ya cika ta kai tsaye sai ta koma sashen Fulani babba ta sanarwa da Mai gado saƙon Mai martaba sannan ta wuce sashen Sailuba don hankalinta ba ƙaramin tashi ya yi ba. Wani irin zafi Fulani babba take ji a cikin jikinta tamkar ana ɗana mata rodin da ke cikin wuta, daga ƙafarta zuwa ƙirjinta wani abu ne take jin yana yi mata yawo duk inda ta ji abin ya sauka a jikinta sai dai ta ji tamkar yana yagar fatar jikinta. A galabaice murya can ƙasa ta furta. "Mai gado ki taimaka miki, jikina zafi yake don Allah ki taimaka mini mutuwa zan yi." Mai gado ta goge hawayen idonta, "Ranki shi daɗe ba za ki mutu ba In shaa Allah za ki samu lafiya." Da Baiwa Zainaba ta ɗebo garwashi ta ɗauko wani turaren miyagu, aka fara turarawa a cikin ɗakin. "Mai gado ƙasana zazzagowa yake ki taimaka za su yage mini ƙasana." Fulani ta yi maganar tana sa hannuwa biyu a ƙasanta tana dannewa, wani irin zuuu ta ji saman mamanta. Ta ƙwalla ƙara cikin azaba tana kai hannu ƙirjinta. "Ƙirjina Mai gado, don Allah ki kira mini Takawa ki kawo mini Abubakar zan yi masa kallon ƙarshe." *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Dafa kafaɗarsa Dattijo Maharaz ya yi sannan ya furta. "Kada ka sare!" Kamalu da kwanyarsa ke barazanar tarwatsewa ya furta. "Don Allah ka rabu da ni na ji da abin da yake damuna." Shiru Dattijon ya yi har zuwa ɗan wani lokaci. "Da alama fushin zuciya na iya yin galaba a kanka wanda hakan zai iya kai ka ga turbar danasani. Da sannu, za ka fahimci abin da nake son nusar da kai." Daga haka Dajjito Mahraz sai ya yi gaba abin sa, har ya ɗan yi wa Kamalu nisa sai kuma Kamalu ya ga rashin dacewar abin da ya yi masa, da sauri ya miƙe ya rufa masa baya. Bai san dalili ba amma haka kawai yake jin gabaɗaya wunin ranar jikinsa babu daɗi ga wata irin faɗuwar gaba da ta saka shi a gaba, ilahirin jikinsa a mace yake don haka koda ya ƙarasa wurin Dattijo Maharaz ya ɗan jingina da wata bishiyar darbejiya kansa na wani irin sara masa. Bayan fitar Jakadiya da kansa Sarki Abdul'aziz ya tashi ya ƙara gyara rufin labulen ɗakin, haka kawai ya ji wata irin tsanar Fulani babba ta mamaye zuciyarsa. A ɓangare guda kuma rashin kuzarin da ke tare da shi ya haddasa masa ciwon jiki, bayan sun gama tattaunawa da baƙin wurinsa ya ji ilahirin jikinsa ya mutu ciwon kai ya lulluɓe shi, bayan sun tafi kwanciya ya yi saboda yadda tsagin kansa yake ciwo tamkar zai tarwatse masa. Lokaci-lokaci ƙirjinsa na bugawa bai san dalili ba, yana nan kwance bacci ya yi awon gaba da shi. A ranar da Fulani babba ta samu labarin auren Sarki Abdul'aziz da Umaima ba ƙaramin damuwa ta shiga, take kishin mijinta ya mamaye ta amma gudun kada magautanta su fahimci lagonta ya sa ta nuna tamkar abin bai dame ta ba. Lokacin da aka ɗaura auren Fulani Umaima da Sarki Abdul'aziz a sannan Fulani Babba tana da 'ya ɗaya wato Khadija sai kuma tsohon cikin Sakina, don haka Fulani Umaima tun farko ta shiga da niyyar salwantar da abin da yake cikin Fulani babba. Amma da yake mahaifiyarta ta ɗora ta a turbar zuwa wurin Bamaguje take ya yi mata binciken abin da za ta haifa wato 'ya mace ce, dalilin haka ya sa Fulani Umaima ba ta damu ba take ganin tamkar dama ita ake jira ta zo cikin masarautar ta haifo Yarima mai jiran gado. Hankalin mahaifiyarta da ita kanta bai gama tashi ba sai lokacin da ta shafe sama da watanni ba tare ɓatan wata ba, kamar haɗin baki suna cikin fafutukar neman magani sai Fulani Asabe ta zo mata da maganar da ta nemi girgiza hanjin cikinsu. Ƙuri shugaba Zurufu ya yi wa Fargi da ke hannun mahaifinta sannan ya nuna wani farin kaskon ƙarfe da ke tafarfasa da ruwan zafi, da hannu ya nuna masa kason sannan ya furta. "Ka ajiye ta a nan domin na tsaurara bincike a kanta." Babu musu mahaifinta ya ɗora ta a saman ruwan zafin ta ci gaba da mutsu-mutsu, sannan Shugaba Zurufu ya ɗebo wani jan gari mai haɗe waɗansu gajerun ƙasusuwa ya watsa mata. Wani haske ya gani ya gifta masa, sannu a hankali hasken ya dusashe sai wani zanen farin doki ya bayyana a saman goshinta. Da sauri Shugaba Shaddas ya saka hannu a saman goshin nata domin ya kwashen fararen taurarinta, bai yi tsammani ba ya ji wata irin haniniyar doki a saman kansa. Da sauri ya waiga bai ga komai ba don haka ya sauke ajiyar zuciya a kasalce. "Al'amarinta daban yake, na lura da baƙon lamarin da ke tattare da ita. Akwai ɗaukaka marara gushewa domin sanin kanku ne tsafi ko sihirin da ya shafi dawaki alheri ne. Don haka ina mai yi maka albishiri da karɓar wannan yarinya a matsayin waccan zan horar da horarwata ta musamman, na yi maka alƙwari matuƙar ta samu horon daga gare ni za ta maye gurbina da duk wata gawurtar tsafina. Yanzu ina buƙatar ka ɗauke ta zuwa gaban abin bauta don samun albarka mafi girma daga gare shi." Zuciyar Mahaifin Fargi fes ya karɓe ta ya fice da ita zuwa wurin abin bauta. Kafin wani lokaci tuni labarin karamcin da Shugaba Zurufu ta yi wa Fargi ya watsu, sai girma da mutumcin mahaifinta ya sake lulluɓe idanun al'ummar Rumzu. Suka ci gaba da yi masa fadanci kowa na son nuna kulawa a gare shi, a ɓangare ɗaya kuma Shugaba Zurufu ba ƙaramin mamakin lamarin yarinyar ya yi ba, don haka ya ɓullo da wannan dabarar da rainon ta a hannunsa ko ba komai zai samu damar shiga halwar tsafinsa don ya kwashe tarin arziƙin da ke ɗauke a cikin rayuwarta. Zuciyar Mai gado ta gama karyewa cikin ɗimauta da tashin hankali ta ƙarasa wurin Fulani babba ta rungume ta tana sakin kuka cike da tausayi. A wannan lokacin Fulani babba ta gama galabaita numfashinta ya fara sarƙewa cikin haki sama-sama ta furta. "Don Allah... ki kira mini... Takawa." Da sauri Mai gado ta miƙe jiki na rawa ta fice da niyyar zuwa sashen Takawa, a babban tsakar gida ta haɗu da Fulani Umaima saboda tashin hankali ko lura da ita ba ta yi ba. "Keee! Zo nan." Fulani Umaima ta kira ta, fuska ɗauke da hawaye Maigado ta zube. "Ki mini aikin gafara ranki shi daɗe Fulani na cikin wani hali ta aika na kira mata Takawa cikin gaggawa." Sai da Fulani Umaima ta ɗan waiga hagu da dama sannan ta furta. "Bayan ke waye ya san da wannan maganar?" "Daga ni sai Jakadiya, amma ita tuni ta fice ta mu wuri." Maigado ta yi maganar a gaggauce. "Yau Inna wuro ba ta jin daɗi don haka ki wuce ki gyara mini ɗakina." A firgice Mai gado ta ɗago. "Ranki shi daɗe idan na dawo daga wurin Takawa kenan?" Harara Fulani Umaima ta wurga mata kamar idonta zai faɗo ƙasa. "Maza ki wuce idan ba so kike na zartar miki da mummunan hukunci ba." Mai gado ba ta da zaɓi don haka ta miƙe ta wuce sashen Fulani Umaima tana zubar da ƙwalla. "Mutuwa zan yi don Allah ki kawo mini Abubakar na yi masa kallon ƙarshe." Kalaman Fulani babba suka dawo cikin kwanyarta tamkar a lokacin take furta mata su. Jingina ta yi da bango tana sharce ƙwalla, sannan a gurguje ta ƙarasa aikin tana fitowa ta samu Fulani Umaima a rumfa (Falo) harɗe ƙafa ɗaya kan ɗaya. "Idan kin kammala ina buƙatar tausa ƙafafuwana tsami suke yi." A wannan karon Mai gado amsawa ta yi a hankali don ta fahimci inda Fulani Umaima ta dosa. Sai bayan lokaci mai tsawo sannan Fulani Umaima ta sallami Mai gado, cikin zuciyarta tana yin dariyar ƙeta don ta san haƙarta ta kusa cim ma ruwa. Cikin sauri a ɗan gurguje Mai gado take buga ƙauren Takawa, sakamakon ta yi dace sashen na shi shiru babu Fadawa a ciki. Ta jima a tsaye har tana shirin juyawa ta ji Mai martaba ya buɗe, da sauri ta zube a ƙasa tana haki. "Allah ya taimake ka ya baka yawan rai, Fulani babba na son ganawa da kai..." Tun ba ta rufe ba ki ba ya katse ta a tsawace. "Ba ma son shashanci a matsa daga gabanmu a ba mu wuri idan ba haka ba za mu ɓata muku rai. A ce mata ta yi haƙuri zuwa dare za mu ƙaraso ɗaki mu ji abin da yake damunta." Daga haka ya rufe ƙofar ba tare da ya sake jin ta bakinta ba. Hannuwa biyu ya sa ya dafe kansa yana jin damuwa na mamaye shi. "Shin abin da na ji daga wurinsu Inna wuro ne ya tsaye mini a rai ko mene ne?" Kamalu ya tambayi zuciyarsa. "Ba tun yau na so sanar da kai ɓoyayyun sirrikan da ba ka san da su ba, na jima da fara yi maka hannunka mai sanda amma na lura har yanzu ba ka ankare da ni ba. Kada ka ji ɗaci don sun sanar da kai gaskiyar abin da suka sani, su ba iyayenka ba ne kamar yadda suka sanar da kai. Sai dai ya zama dole a jinjina musu sakamakon namijin ƙoƙarin da suka aiwatar game da rayuwarka..." "Ya aka yi kasan waɗannan kalaman, alhalin daga ni sai su muka tattauna su? Me ya sa a kullin kake neman dulmiya ni cikin kogin tunani? A yanzu haka zuciyata ta yi nisan kiwo wurin zabarin mafitar da za ta dasashen ɗacin da ke cikin zuciyata. Na jima ina ɗora ayar tambaya akanka amma wani tsagin na zuciyata na gargaɗina a kan abin da nake zargi." Kamalu ya yi maganar cikin damuwa. Dattijo Maharaz ya dawo gaban Kamalu yana murmushi, "Na so a ce ka jima da faɗawa kogin tunani akaina, sai dai yanzun ma ba a makara ba, duk zargin da za ka yi ina son ka yi shi a kan zato na alkairi." Shiru Kamalu ya yi bai tanka masa ba yana nazartar kalamansa. "Ka biyo ni zan wuce da kai ta wani sirrintaccan zaure matuƙar ka amince mini a yau zan sanar da kai ainihin wane ne ni da alaƙata da wannan Masarautar." Kamalu kamar ba zai bi shi ba sai zuciyarsa ta ingiza shi suka fara tafiya kai tsaye suka nufi babban sashen Sarki Abdul'aziz ta ɓangaren sashen da yake makwaftaka da su Ciroma da Galadima. Cikin matsananciyar damuwa Maigado ta koma sashen Fulani babba a lokacin Abubakar yana kwance yana yin gwarancinsa, kallonsa ta yi zuciya a karye ta faɗa ɗakin Fulani babba. Daga can gefenta ta tsugunna ta ɗora hannunta a saman na Fulani babba, "Allah ya taimake ki na je Takawa ba ya nan." Ta samu kanta da sauya kalaman saɓanin abin da Mai martaba ya gaya mata. Hawaye ta gani na gangarowa daga idanun Fulani babba, Mai gado ta sunkuyar da kai ƙasa hawaye na zuba. Wani tunani ta yi da sauri ta ƙarasa ta samu Baiwa Zainaba suka shiga ɗakin Abubakar suka fito da shi hannuwansa ɗauke da mari, ɗakin Fulani suka shiga da shi Mai gado ta zaunar da shi a gefen gadon da take kwance. Da ƙwayar idon Fulani babba suka lura da irin kallon da take bin Abubakar da shi hawayen idanunta na sake ƙaruwa. Hannu ya kai saman fuskarta yana jijjigawa yana dariya, take Mai gado da Zainaba suka fashe da wani irin kuka mai cin zuciya. Sororo ya yi ya fara kallonsu bayan wani lokaci ya sake kai hannu kan hannun mahaifiyarsa yana ɗago ta alamar ta tashi. Motsa baki ta fara yi Mai gado ta matsa gabanta da sauri ta kara kunnenta a wurin bakin Fulani babba. "Ga Abubakar nan...don Allah ki kula mini... ki kula mini da shi... Duniya da Lahira... na mallaka miki shi... Mai gado mutuwa zan yi, ƙirjina ciwo yake ki danne mini shi." Cikin kuka Mai gado ta sa hannuwa biyu ta danne ƙirjin Fulani babba. "La'ilaha'ilallahi... Muhammandur... Rasulillah..." Fulani Babba ta furta cikin sarƙewar murya idanunta a kan Abubakar numfashinta ya fara yin sama daga ƙarshe ya ɗauke. "Ranki shi daɗe! Ranki shi daɗe!" Mai gado ta furta a firgice tana jijjiga Fulani babba, a sanyaye Baiwa Zainaba ta ƙarasa ta rufe wa Fulani babba idanu haɗe da jan zani ta rufe mata fuska. Daɓar ta zauna a gefen gado kamar haɗin baki ita da Mai gado suka rushe da wani irin sabon matsanancin kuka. "Mai gado duk ranar da na ga Abubakar ya warke sai na 'yanta ba yi goma, kuma sai na raba dukiyata biyu na bayar da ita sadaka." "Mai gado kin san rannan mafarki na yi wai Abubakar da Yaya Halima sun warke, kin ga dai a cikin mafarki ne amma wallahi kar ki ji farincikin da na ji." "Da Allah ya sa Abubakar lafiyayye wallahi babu abin da zai hana ban haɗa shi aure da Jawahir ba, saboda jin Jawahir nake tamkar 'yar cikina." "Tsakanin ke da Abubakar ban san wanda ya shiga tsakanina da 'yata Jawahir ba, ta shafe kwanaki ban ganta ba an ya Mai gado ba a matsa wa Jawahir da aiki kuwa?" "Wani abu ne yake damuna Mai gado, na san dai da ina raye da ba na raye Allah ne yake kula da Abubakar amma duk ranar da ƙasa ta rufe idona ban san yadda rayuwar Abubakar za ta kaya ba." Mai gado ta sake rushewa da matsanancin kuka sakamakon tuno ire-iren kalaman da Fulani babba take yawan furta mata a duk lokacin da suke zaune suna attaunawa. "Kai wai mene ne yake faruwa kuka cika mana gida da kuka kamar masu zaman makoki..." Kalaman Jakadiya suka katse sakamakon ganin Fulani babba a lulluɓe, babu wanda ya tanka mata don haka ta ƙarasa bakin gadon ta yaye zanin da aka rufe ta, hannu ta kai saman ƙirjinta a razane ta ja da baya. "Mai gado me yake faruwa?" "Babu Fulani babba, Jakadiya mun rasa Fulani wayyo Allahna!" Rass ƙirjin Jakadiya ya buga, ta jingina da bango wata irin zufa na tsattsafo mata. Da sauri ta fice daga ɗakin kai tsaye ta wuce sashen Fulani Umaima. "To Fulani Umaima shi kenan ƙurunƙus! Ta faru da ƙare an yi wa mai dami ɗaya sata. Burinki ya cika Fulani ta bar miki duniyar sauran abin da ta bari sai ki haɗa ki cinye." Jakadiya ta furta wa Fulani Umaima da ke harɗe a kan kujera. Wani sanyi ne ya ratsa zuciyarta shi kenan muradi da burinta zai ka ga ciki, amma a fili sai ta furta. "Jakadiya ya kamata ki iya zarge limzamin harshenki idan ba haka watarana za ki yi ɓarin zancan da zai kai ki ga turnar danasani. Ko Fulani ta so ko kar taso idan lokacin tafiyarta ya yi sai ta je, Allah ya jiƙanta ya gafara sai ki sanarwa Takawa a yi a binne ta kin san jinkirin gawa yana kawo ƙwanƙwamai cikin gida. Haka kawai su dinga firgita mu da tsakar dare, muna kasa fita fitsari." Kasaƙe Jakadiya ta yi tana sake jimanta tsantsar rashin imanin Fulani Umaima. "Wacce irin ƙeƙasasshiyar zuciya gare ki Umaima?" Fulani Umaima ta saki murmushi cike da izza, isa da ƙasaita. Sai da ta zagaye Jakadiya ya kai sau biyar sannan ta furta. "Tambayar da a kullin nake wurga wa zuciyar tawa kenan amma har yau ta gagara nusar da ni alƙibikarta, abu ɗaya na sani dangane da kaina Jakadiya." Sai da ta koma kan kujerarta ta zauna, ta ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya sannan ta ce. "Duk wani abu da nake so nake ƙauna to zai kasance nawa ni kaɗai har abada, ina da matsanancin kishi ba iya a kan mijina ba. Dalilin da ya sa nake kawar da duk wani abu da nake ganin zai zame mini shamaki a gabana, Jakadiya ba zan tsawaita miki ba amma ke kanki kin san Umaima ba kanwar lasa ba ce. Lumbu-lumbu ce wutar ƙaiƙayi idan kin so ki kira ni da suna cinnaka ban san na gida ba. Ki ci gaba da shiri Jakadiya kada ki fasa domin kwanciyar kura ba shi ke nuna yin nasara a kanta ba." Kallo ɗaya za ka yi wa Jakadiya ka fahimci kwanciyar hankali ya yi ƙaura daga jikinta, yayin da tashin hankali ya mamaye gangar jiki da tsokarta. Ganin idan ta ci gaba da tsaiwa tana iya zubewa ƙasa saboda tashin hankali, ya sa ta fice daga ɗakin Fulani Umaima kai tsaye ta wuce Sashen Sailuba. Take wani tunani ya faɗo wa Fulani Umaima da sauri ta fice ta wuce sashen Mai martaba, a gaggauce ta fara bubbuga ƙofar cikin nuna tashin hankali. A tsammanin Takawa Mai gado ce ta sake dawowa don haka ya yi biris da ita. Kusan tun safe suka fara casar gero da sussuka, har kawo yamma abin da yake tsayar da su yin sallah ko cin abinci don haka Jawahir ta gaji liƙis sakamakon ta jima ba ta yi aiki mai yawa kamar na wannan ranar ba. A lokacin da suka fara ɓarar gyaɗa saman cikinta ne ta ji ya yi mata ɗauuuu kamar wacce aka ɗanawa dalma. A gigice ta kai hannu saman wurin da tambarin bishiyar yake wani irin zafi ta ji, har idon kunnenta ba gizo yake yi mata ba ji ta yi tamkar tambarin na fisgar hannunta. A sace ta fice daga wurin ba tare da kowa ya lura ba, can cikin dajin ta ɗan nausa sai da ta waiga hagu da sannan ta ɗaga rigarta. Jawur ta ga wurin ya yi zanen bishiyar ya ƙara fitowa raɗau, wani irin tsoro ya kamata ƙirjinta ya shiga bugawa da sauri. "A matsayina na mahaifiyarki ina mai alhinin sanar da ke daga yanzu a kowanne lokaci ƙofar ƙunci da damuwarki na iya buɗewa, ni na hango miki abin da ba ki hango ba Jawahir amma tun da haka kika zaɓa ga fili nan ga mai doki." A tsorace Jawahir ke kallon matar da ta taɓa gani ta zo mata cikin mafarkinta, sai dai a yanzu ƙiri-ƙiri ta ganta cikin sura da ta ganta a cikin mafarki. Ja da baya ta fara yi tsorace kafin ta yi wani yunƙuri ta ga matar na yin baya-baya har gangar jikinta ya nutse a kikin murgujejiyar bishiyar kukar da ke gabanta ta ɓace mata ɓat. Tsoro ne ya sake mamaye Jawahir da gudu ta falfala cikin tashin hankali ta nufi sashensu na Bayi. Uwar tuwo na ganinta ta fara ƙwala mata kira amma ko waigenta ba ta yi ba, can saman gadon karan Maigado ta faɗa ta janyo zanin gadon ƙirjinta na bugawa jikinta na karkarwa ta lulluɓa. Nan take zazzabin ya lulluɓe mata jiki a ɓangare ɗaya kuma raɗaɗin tambarin cikinta ya haddasa mata rashin kuzari, da ta runtse ido matar take gani a lokacin da take nutsewa cikin jikin bishiyar, wannan ya sake ɗaga mata hankali don ko a mafarki ba ta taɓa ganin haka ba. "Ranka shi daɗe ka buɗe mini yau mun yi babban rashi Fulani Umaima ce ke magana, wayyo Allah Fulani kaico rayuwar duniya zancan banza." Takawa ya ji kalamanta sama-sama, tasowa ya yi ya buɗe ƙofar da sauri Fulani Umaima ta faɗa jikinsa haɗe da fashewa da matsanancin kuka. A ɗan rikice ya dube ta. "Me yake faruwa da Fulani ta shiga cikin firgici haka." "Wato ba ma ta Fulanin da ka ji na ambata kake ba kenan, ni dama ai haka nake so." Fulani Umaina ta yi maganar a zuciyarta. "Ranka shi daɗe Fulani ce babu, Fulani babba ta rasu dai rai ya yi halinsa. Mun rasa Fulani yanzu Jakadiya ke gaya mini mutuwarta." Cak Sarki Abdul'aziz ya yi wani abu na yi masa yaaaammm tun daga tafin ƙafarsa har tsakiyar kansa, ture Fulani Umaima ya yi. "Fulani ba mu san lokacin da muka fara wasa da ku ba! Har rainin ya kai a zo a faɗa mana waɗannan maganganun?" Kalaman Sarki Abdul'aziz suka ratsa ta a lokacin da ya jingina da bango yana jin kansa ya yi masa nauyi kamar zai tarwatse. "Sarkina ka san tun da nake tare da kai ban taɓa yi maka ƙarya ba, yanzu ƙaryar ma sai na rasa wa zan yi wa sai Fulani babba, dama ana yin ƙarya da mutuwa Ranka shi daɗe?" Wani irin sanyi jikin Sarkin Abdul'aziz ya yi, kamar wanda aka zabura ya fita da sauri duk hanyar da ya bi sai dai Bayi su dinga zubewa ƙasa suna kwasar gaisuwa amma ko kallonsu ba ya yi ballanta ya tanka musu. *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* *Daga jiya zuwa yau na ga ƙorafe-ƙorafe ta pc da cikin group, wasu ma na ji sun ce sun daina karantawa sai sun tabbatar da mutuwar Fulani wasu kuma sun tafi hutu to dai duka a yi haƙuri.*😄 *Kamar yadda kuka sani kowanne bawa fa da kalar tashi ƙaddarar, rayuwa ma'auni ce akwai wanda idan ka dubi rayuwarsa za ka Ubangiji ya yalwata shi da dukiya, 'ya'ya, dangi da duk wani abin more rayuwa na farinciki kuma har ƙarshen rayuwarsa, idan da wata matsala ma a ciki ba mai ɗaga hankali ba ce sai ka ga kamar shi ya tsara wa rayuwarsa haka. Akwai kuma wanda za ka ga Allah ya jarabce shi da talauci, rashin lafiyar 'ya'ya jarabta kala-kala, rashin mahalli da sarausu. Wasu kuma ka ga Ubangiji yana haɗa musu duka biyun.* *Salon labarin nan na daban ne don na karanta littafai ba ɗaya ba ba biyu ba da zan ga an zalinci kishiya ko dai wani daga ƙarshe shi wanda aka zalinta ya ga ƙarshen wancen, wannan kusan ya zama gama-gari a cikin labarai ko ni na yi haka a ciki AN YA BAIWA CE. Alhalin a cikin duniyar nan akwai waɗanda za a cuta ƙarshe ma ba su san wanda ya cuce su ɗin ba har su mutu, sai dai su waɗanda suka yi abin daga ƙarshe su tona asirin kansu ko kuma sakayya ta bayyana ƙarara, kai wani lokacin ma sai shari'a a wurin Ubangiji. Akwai mahaukaciyar da na sani asiri aka mata ta haukace ƙarshe mota ce ta bige ta ta mutu a cikin haukan, sai 'ya'yanta aka kwashe, ita kenan sai a ce don me ba ta san wanda ya mata asiri ba kuma ba ta ga ƙarshen mai yin asirin ba? Ina san na nusar da cewa ita duniya ba komai kake nema ka samu, don akwai wacce na sani ta shafe shekaru ba ta taɓa haihuwa ba ta fuskanci ƙalubale daga dangin miji har shi mijin kansa, kwatsam ta samu ciki ba ƙaramin buri ta ci a kan cikin ba ƙarshe a wurin naƙuda ta mutu ita sai a ce don me ba ta ga abin da ta haifa ba? Wallahi Reality akwai wata maƙociyarmu da na sani, mijin ba shi da hali sosai ita matar ta yi wankau, sirfau, har gidajen masu hali take bi tana musu wanki daga baya Allah ya fara yalwata mijin a wannan gaɓar ita kuma Allah ya mata rasuwa, ƙarshe saboda iyali mijin aure ya yi kuma ya zama hamshaƙin mai kuɗi kuɗi sai da 'ya'yanta aka ci kuɗin da amarya, kenan sai a ce ita don me za ta mutu a wannn lokaci? Shin dama idan ka yi haƙuri a kan abu dole ne sai ka ga sakamako? Sam ba haka ba ne, akwai abin da za ka ga sakamakonsa wani abin kuma sai dai Ubangiji ya yi maka tukwici a kan haƙurin da ka yi, tun da dama Ya ce shi yana tare da masu haƙuri. Ita rayuwa sai wani ya rasa wani yake samu, kuma mutuwar wani tashin wani ce. A lokacin da wani zai mutu sai ka ga a lokacin ne shaharar wani take bayyana.* *Masu cewa ya kamata Kamalu ya ji daɗin mahaifiya, su kuma 'ya'yan da suke tasowa a gidan Marayu ba su da kowa ya za su yi da rayuwarsu, shin muna tuna irin yanayin da suke ji a zuciyarsu? Ballantana Kamalu ya samu iyayen goyo na gari, masu ba shi kulawa. Wasu fa mahaifiyarsu na haihuwa take mutuwa kuma su taso cikin tsangwama kenan sai a ce don me?* *Wasu na ganin ana nuna wa Fulani Umaima asirinta na yin tasiri kullin, kun manta duk mai bin bokaye da 'yan tsubbu gani yake a kullin duk abin da ya faru asirinsa ne yake tasiri? Duk fa wanda ya mutu dama lokacinsa ne ya yi sai dai ya kasance da sanadi, abin dariya wasu har cewa suke wai ƙarfin boka fi ƙarfin Allah? Kun manta da hadisin da ke magana akan samuwar bawa tun yana cikin mahaifiyarsa, ana ƙaddara wa Bawa duk abin da zai faru da shi tun yana cikin mahaifiyarsa? Dama can Fulani babba a wannan gaɓar ajalinta yake sai ya kasance da sanadin Umaima, ko ciwo fa wani bai isa ya saka maka ba sai dai idan dama can Allah ya ƙaddari hakan zai faru da kai. Kuma a baya a wurare da dama an nuna asirin nata yana sanyi har Fulani babba ta samu kusanci ga mijinta.* *Kun saka ni rubutu da farar safiya da dogon sharhin da ban shirya ba 😄 ba fa ku kaɗai kuka ji mutuwar Fulani ba ni ma ta dake ni wallahi, to amma kun san an ce wata shari'ar sai a lahira don haka Fulani dai babu ita sai mu ga Umaima za ta samu yadda take so ko akasin haka? Kuma idan muka bar Fulani Babba ta rayu ai Umaima ta ci banza da yawa😄 ƙarshe sai a ce ta nemi yafiyarta kuma Fulani babba ta yafe? Haba ai gara duka su yi nadama a lokacin da nadamar ba za ta yi amfani ba.*🌚 *Yanzu dai a samu wata ta toyo mana wainar sadaka sai wasu su wakilce ni a rarrabawa maƙota, don yanzu haka makaranta zan tafi.*🤭 Tamkar raƙumi da akala haka Kamalu ya ci gaba da bin Datijjo Maharaz sai dai babu wanda yake tankawa wani, suna gab da shiga wani soro mai duhu Kamalu ya ji gabansa ya bada rasa! Har sai da ya sa hannuwa biyu ya dafe ƙirjinsa, tun da ya zo duniya bai taɓa jin faɗuwar gaba irin wannan ba. Runtse idanunsa ya yi yana sauke ajiyar zuciya, Dattijo Maharaz ya matsa kusa da shi ya kamo hannunsa na dama. "Ka yi haƙuri Kamalu! Ina mai ƙara ba ka haƙuri a duk yadda rayuwa za ta zo maka, da duk labarin da za ka ji a nan gaba. Ban so haka ta kasance a tare da kai ba sai dai ka san ita rayuwa abokiyar tagwaitagar ƙaddara ce, ka sa a ranka duk abin da ya faru da kai shi ne mafi alheri. Na so a ce fuskokinku sun sadu da juna koda sau ɗaya ne, amma haka kundin ƙaddararku ya zana muku. Ka yi haƙuri na tabbata lokaci na tafe da sauƙi zai zo a gare ka." Shiru Kamalu ya yi yana sauraron Dattijo Maharaz a tunaninsa sai ya yi tsammanin yana ba shi haƙuri ne silar abin da ya ji daga wurinsu Baffajo. "Babu koma Dattijo Maharaz kuma ina godiya da gudunmawar da kake ba ni. Na amince zan bi ka ne kawai don yayewar damuwar da nake ciki, a baya ban san waɗannan tarin matsalolin ba Dattijo Maharaz." Kamalu ya ƙarasa maganar cikin raunin zuciyata. Ta cikin wannan zauren mai duhu suka shiga a tsammanin Kamalu za su fita ta cikin gida ne, sai kuma ya ga sun ɓilla bakin wani ɗan rami mai ɗauke da taɓo, daga gefe kuma a wata 'yar gajeriyar katanga jikinta ɗauke da sawayen hannuwan mutane. Da mamaki Kamalu ya furta. " Ina ne nan Dattijo Maharaz? Wannan sawayen hannun su waye?" Kamar saukar aradu haka Sarki Abdul'aziz ya dira a cikin ɗakin Fulani Babba, Mai gado ta ɗago ta dube shi take ta ji wani ƙunci da haushinsa sun mamaye ta. Uffan ba ta iya tanka masa ba ta ɗauke kanta gefe. "Ka gafarce ni ranka shi daɗe bisa mummunan al'amarin da ya faɗo mana." Baiwa Zainaba ta faɗa jiki a sanyaye. Bai amsa musu ba yana tsaye ƙwayar idonsa na kan gawar Fulani babba, a hankali ya fara ɗaga ƙafarsa ya isa gaban gawar tata ya tsugunna a gefen gadon. Hannunsa na rawa ya sa ya buɗe yaye zanin fusakarta ya kai kunnensa saitin ƙirjinta. Wani abu ya ji ya danne ƙirjinsa, kamar ƙaramin yaro ya ƙara kansa a gefen ƙirjinta hawaye bibbiyu na zuba. Daga Mai gado har baiwa Zainaba suka sunkuyar da kansu ƙasa suna zubar da ƙwallah, motsin da suka ji a gefensu ne ya sa suka ɗago Fulani Umaima ce a tsaye tana bin ɗakin da kallo. Ganin kukan da Takawa yake yi a jikin gawar Fulani babba ya sa ta taɓe baki cikin takaici, sai da ta ƙarasa gaban gawar sannan ta rushe da wani irin kuka. Yadda Fulani Umaima take kuka har da majina sai ka rantse mutuwar Fulani babba ba ƙaramin dukanta ta yi ba. Jakadiya da Sailuba ne suka shiga sai dai ganin irin kukan da Fulani Umaima take yi ya sa suka yi turus, lokaci ɗaya suka kalli juna hatta Mai gado sai da ta fahimci Fulani Umaima kukan makirci take yi. "Ya Allah ga baiwarka nan Allah ka jiƙanta ka gafarta mata, kaico rayuwa Fatima ta tafi ta bar ni." Takawa ya furta a ɗimauce. "Me ya sa za ki tafi ki bar ni Fatima!" Ya yi maganar a zauce. "Mtsswww, aikin banza!" Fulani Umaima ta faɗa cikin suɓucewar baki don ba ta taɓa tsammanin zancen zucin da take yi zai fito fili ba." A hargitse Mai martaba ya waiga wurinta amma da yake ta san kanta sai ta juya wurin su Mai gado da ke zaune a ƙasa ta furta. "Ku tashi ku fita mana ku bar mutane da abin da yake damunsu." Da sauri su Baiwa Zainaba suka fice jiki na rawa. Tsanarta ta sake mamaye zuciyar Mai gado, ɗauke kansa ya yi don a tunaninsa a kan maganar da ta yi wa su Mai gado ne take yin tsaki. "Allah ya taimaki ɗawisu, Ubangiji ya kwanta makwancin Fulani. Na ce ko za a yi mini izini na fitar da sanarwar wannan babban rashim da aka yi mana?" Kai kawai ya iya gyaɗa mata, Jakadiya ta fice da sauri. Shi kuwa Abubakar yana can gefe a zaune sai bin su yake da kallo ɗaya bayan ɗaya, kamar wanda ya ga sabuwar hallita haka ya tsaya yana kallon Takawa saboda rashin saninsa da bai yi ba, Mai martaba ya rufe Fuskar Fulani sannan ya ƙarasa wurin Abubakar. "A lokacin da mahaifiyarka take raye babban burinta bai wuce ta ga warkewarka ba, ta fuskanci ƙalubalen rayuwa a wurina duk silarka sai dai kuma Ubangiji ya ɗauke ta a gaɓar da kake ci gaba da neman kulawarta. Allah ya gafarta miki Fatima haƙiƙa na yi babban rashin da har abada ba zan manta shi ba, na yafe miki duk abin da kika taɓa yi mini a rayuwa duniya da lahira." Wani haushi ya mamaye zuciyar Sailuba, ita kuwa Fulani Umaima ban da jefa masa harara babu abin da take yi. "Ka gama iyayinka ina nan zaune za ka dawo ka same ni." Ta furta a zuciyarta sannan ta saki murmushi sakamakon kallon gawar Fulani Babba da ta yi, da kuma ta tuna a yanzu magani ɗaya ne ya rage mata ta ƙarasa aiwatarwa wanda za ta cusawa gawar Fulani ɗaurarriar fatar a gabanta sai farinciki ya mamaye ta. Mai gado tana tafe tana kuka saboda tashin hankali duk wanda ya tambaye ta ba ta iya koda furta masa kalma ɗaya, ɗakinta ta faɗa ta zauna a gefe gado nan take ta sake rushewa da sabon kuka mai cin zuciya. A rayuwa bayan mutuwar mahaifanta wannan ce mutuwa ta farko da ta taɓa ta, sun yi wata irin shaƙuwa da Fulani ko kaɗan ba ta nuna mata kyara a matsayinta na shugabarta. Jin kukan da Mai gado take yi ƙi ci ya ƙi cinyewa ya sa Jawahir ta ɗan zuro kanta daga cikin zanin don har lokacin jikinta bai daina karkarwa ba. "Inna... Innaaa me yake faruwa?" Jin yanayin muryar Jawahir ya sa Mai gado ta waiga, sai da ta share hawayenta ta furta. "Me yake damunki Jawahir?" Kamar mai jira sai kawai Jawahir ta fashe da kuka, Mai gado na shirin kawo hannun Jawahir ta ji wani irin zafi zaauu da jikinta ya yi. Da sauri ta yaye zanin a hargitse ta furta. "Ba ki da lafiya ne Jawahir." "Inna wallahi wannan matar ce, tsoro nake ji Inna kar ta kashe ni." Ƙirjin Mai gado ya yi wata irin bugawa da ƙarfi. "Wace ce Jawahir? Ki kwantar da hankalinki In shaa Allah ba za ta yi miki komai ba." "Inna kin ga cikina fa, Allah mutuwa zan yi." Jawahir ta ƙarasa maganar tana buɗewa Mai gado cikinta. Zumbur Mai gado ta miƙe jikinta na karkarwa, tambarin cikinta ne ya daɗa yin wani irin ja a ɗan tsorace Mai gado ta miƙa hannu tana son taɓawa zuciyarta na harbawa. Da ƙyar ta yi ta maza ta ɗora hannunta a jiki wani irin zuuuu ta ji kamar ana fisgar hannunta, ta ja da baya da sauri a tsorace. "Wacce matar kika gani, kuma yaushe Jawahir?" Mai gado ta tambaye ta a firgice. "Inna ina ɓarar gyaɗa kawai na ji cikina yana zafi..." Take ta kwashe duk abin da ya faru ta gaya wa Mai gado. Kamar wacce ruwa ya cinye haka Mai gado ta yi shiru, fargaba, tsoro da tashin hankali suka mamaye ta. "Kada ku damu da sanin zubi da surar halittata, wannan 'yar tawa ita za ta fayyace muku asalin jinsin halittar da na fito." Kalaman mahaifiyar Jawahir suka dawo wa Mai gado cikin kunnenta, da yake zuciyarta a dagule take nan take ta sake fashewa da kuka domin ba ta zaɓin da ya wuce yin kukan. "Inna wallahi tsoro nake ji ta ce abin bauta zai yi fushi da ni." Mai gado ta dafa ta a sayaye. "Kada ki damu Jawahir idan Malam ya shigo zan sanar masa halin da kike ciki, babu abin da zai faru da ke sai alkairi." Mai gado ta furta tana kallon Jawahir. "Inna wallahi Fulani babba ta ce ki daina hana ni shiga wurinta, don Allah ki bari na je kitso zan yi mata." "Daga wurin Fulani babba nake na ci abinci kuma ga alkaki ta ce a kawo miki." "Inna kin ga sabbin kayan da Fulani ta ba ni wannan ma warwaronta ne da yari ta ce na je na sanya ranar juma'a." "Wallahi Inna Fulani tausayi take ba ni idan na ga tana kuka kamar ba matar Takawa ba, Allah da ina da dama sai na kori Fulani Umaima daga gidan nan." Ire-iren kalaman Jawahir na baya suka shiga dawo wa Mai gado, wanda Jawahir take gaya mata game da Fulani babba. Duk da ta san babu abin da suka haɗa da Fulani amma akwai shaƙuwa don haka tausayin Jawahir ya kamata ta san jin mutuwar Fulani babba ba ƙaramin kaɗa ta zai yi ba. "Inna kukan me kike ɗazu." "Ina koka mana game da sabuwar rayuwar da za mu fuskanta nan gaba Jawahir, ina koka mana maraici, kaɗaici da alhinin da za mu shiga. Ta kasance gatanmu a lokacin da ba mu da gata, ta rungume mu hannuwa bibbiyu tamkar ba bayi ƙasƙantattu a wurinta ba." Take gaban Jawahir ya faɗi. "Jawahir mun rasa Fulani Babba Allah ya yi mata rasuwa shi kenan Jawahir..." Kalaman Mai gado suka katse sakamakon kukan da ya ci ƙarfinta. "Ki je sashen Sarkin cikin masarautarku ki tone abin da matarsa ta binne idan ba haka ba, Fulani babba za ta mutu. Idan kika bari Fulani Umaima ta ci gaba da yin nasara a cikin masarautar nan ina mai tabbata miki sai ta yi nasara akanki. Sai ta damƙa ruhinki wurin hatsabibin boka Bamaguje, kuma ki sani idan kika bari rihinki ya je gare shi babu wani taimako da ni ko abin bauta za mu yi miki. Kin ga kenan an ƙarar da gishiri duka a dahuwar ƙaho ba tare da buƙata ta biya ba, na tashi a banza ba tare da cikar muradina ba." Kalaman matar da ta zo mata a mafarki wacce ta gani a ɗazu suka dawo mata, hantar cikinta ta kaɗa zuciyata ta hau dakan lugude tamkar za ta yi tsalle ta hudo ƙirjinta. "Mutuwa fa Inna? Kina nufin Fulani Babba dai tamu ce ta mutu." Salatin da suka ji daga waje da kururuwa ne ya sa Mai gado ta yi saurin fita, wasu daga cikin Bayin tuni suka fara koke-koke da kururuwa wannan ta sa jikinta ya sake yin sanyi don ta fahimci labarin mutuwar ya zo gare su. Waɗannan sawayen hannuwana tsofaffin Sarakunan masarautar da suka yi zamani a masarautar nan ne, wannan ramin taɓon da kake gani tun zamanin mahaifina ya haƙa shi. Dubi can ka gani." Dattijo Maharaz ya nuna wa Kamalu wani farin dutse cikinsa wani mudubi ne mai ɗaukar ido. "Leƙa fuskarka ka gani!" Babu musu Kamalu ya leƙa fuskarsa, a ɗan razane ya ɗago kansa cikin tsoro. Dattijo Maharaz ya saki murmushi, "Kada ka tsorata Sadauki sake leƙa fuskarka hakan ya kasance tamkar sunna ne a cikin masarautar nan ga duk wani mai matuƙar muhimmanci gare ta." Kafin wani lokaci tuni maganar mutuwar Fulani babba ta zaga lungu da saƙon da ke masarautar Huddam, mutane da dama sun jimanta mutuwarta kama daga cikin Bayi Kuyangu, Dogarai Hadimai da duk waɗanda suke rayuwa a cikin masarautar. Duk wanda zai buɗe baki sai dai ya faɗi alkairi da kyawun halinta, a ɓangare guda kuma mutane suka fara jimanta yanayin sabuwar rayuwar da Abubakar zai fuskanta ta maraici a nan gaba. Tun ba a ɗauki lokaci ba Sarki Abdul'aziz ya sa aka rubuta wasiƙa zuwa masaarautar Mahaifan Fulani babba domin a shaida musu da mutuwarta cikin gaggawa, tun daga cikin gari har zuwa sauran ƙasashen da ke maƙota da ƙasar Huddam suka shiga aiko masa da tarin takardun ta'aziya. "Haƙiƙa mun yi babban rashin da har abada ba za mu samun gurbin da zai maye mana shi ba, Allah ya huci zuciyar Mai martaba ya sanya maka dangana. A madadina da na iyalan ƙasa da masarautar Huddam muna mai yi maka ta'aziyar rashin Fulani Babba." Fulani Umaima ta ƙarasa maganar cikin zubar da ƙwalla. Sai da ya share ƙwalla ya dube ta. "Shi kenan fa Fulani ta yi nisa da mu? Umaima kina ganin zan ci gaba da jin daɗin gudanar da al'amuran mulkin ƙasar nan a yanzu." "Idan ba za ka iya ba ai sai ka yi murabus ka damƙawa Yarima Muhsin tun dama a yanzu ya kawo ƙarfi." Ta furta a zuciya tana watsa masa harara a fakaice. "Da taimakon Allah ka haye wannan karagar Sarkina kuma na tabbata da taimakonSa za ka ci gaba da gudanar da al'amuran masarautar nan. Ka yi tawakkali domin Ubangiji da ya ba mu Fulani Shi ne ya buƙace ta a daidai wannan lokacin. A wannan lokacin addu'armu kaɗai Fulani take buƙata Ranka shi daɗe." Ajiyar zuciya ya sauke idanunsa ya runtse da suka yi jawur. "Ina sake alfahari da ke Umaima Allah ya yi miki albarka, ita kuma halinta na gari ya bita." Fulani Umaima ta sunne kai ƙasa sannan ta amsa. "Amma wani hanzari ba gudu ba ranka shi daɗe, na ce mai zai hana idan aka shirya Fulani a dawo da ita sashenka tun da dai kwanan keso za ta yi ina ga sai ya fi don ka samu damar yi mata addu'a cikin nutsuwa, addu'arka na da matuƙar tasiri a gare ta. Ni kaina zan zauna tare da kai don abin da ya yi Fulani shi ya yi ni, kaico rayuwar duniya kaico mutuwa ta yi mana yankan ƙauna." Fulani Umaima ta ƙarasa maganar tana fashewa da matsanancin kuka. Jikin Sarki Abdul'aziz ya yi sanyi, don haka kai tsaye ya amsa a ganinsa zancen da Fulani Umaima ta yi har a zuciyarta ma haka ne. A tsaye yake ya yi tsirara a bakin wata ƙorama wacce take cike da jini, mamaki ne ya matuƙar kama shi sakamakon wayar gari da ya yi ya tsinci kansa a wurin kamar yadda yake yawan ganinsa a mafarki. Waigawa ya yi yana ƙarewa baƙon wurin kallo yana tunanin inda ya taɓa ganinsa a makamancin wurin nan. Yana shirin yin magana yaji an sheƙo masa wani ruwa kamar an ɗaurye namansa sannan aka fara waɗansu irin surutai da ba ya iya gane su, an jima ana abu ɗaya sannan ya ji an sake kwara masa ruwan a jikinsa. Ta cikin ƙoramar jinin ya ga wani mutum ya fito daga ciki hannunsa ɗauke da wata gajeriyar wuƙa, baƙa wuluk sai sheƙi take yi. Mamakinsa ya sake ninkuwa sakamakon ganin matsananciyar kamar da suke yi da mutumin. "Ba kai ba ne shugaba da nake yawan mafarki da shi?" Boka Shadda ya bushe da dariya, "Ba kama ba ce taurarona ni ɗin dai ne." Yawu Basiru ya haɗiya cike da mamaki. "To ya aka yi na gan ni a nan? Wai ma wane ne kai?" Basiru ya yi maganar a zuciyarsa. Bai gama saƙa da warwara ba ya ji mutumin ya fesa masa wani ruwa a fuskarsa, take ya ji wani yanayi ya ratsa shi zuciyarsa ta shiga azalzalarsa, babu zato mutumin ya burma masa wuƙar hannunsa a ƙahon zuciyarsa sai dai ko kaɗan bai ji zafi ba sai ma wani irin sanyi da ya fara ratsa ilahirin jikinsa. Ya waiga cikin sanyin jiki yana kallon boka Shaddas. "Ungo saka rigarka!" Boka Shaddas ya furta yana miƙa masa kayansa, babu musu Basiru ya karɓi kayansa ya fara sawa Shaddas ya furta. "Daga nan maza ka je ɗakin mahaifiyarka ka buɗe akwatin da take ɓoye duk wani sirrinta, za ka ga wani tsafataccan littafi ka kawo mini. Kada ka manta duk abin da za ka yi mini domin nasararmu ce, kai jajirtacce ne kada ka ba ni kunya magajin babban bokan da babu kamarsa a faɗin nahiyar nan." Jin kanbabawar da Boka Shaddas yake yi masa ya sa Basiri sake samun ƙwarin gwiwa bayan wankan tsafin da aka yi masa, cike da ƙarfin zuciya ya fice daga cikin kogon tsafin. Lokacin da ta ji labarin an kai gawar Fulani babba turakar Takawa farinciki ne ya lulluɓe ta, ɗaurarriyar fatar da ke hannunta ta shiga juyawa tana sakin murmushi a hankali. Babban mayafi ta ɗauko ta naɗe jikinta da shi sannan ta lalubo carbin da sai da ta sha wuya kafin ta samo shi, ta soke ƙulalliyar fatar wurinta ta janyo ƙauren ɗakinta ta fito, sannan ta gargaɗi Bayinta da ko da wasa kada wanda ya tura mata ɗaki kai tsaye ta nufi sashen Sarki Abdul'aziz da ƙudurin duk rintsi sai ta aiwatar da mugun ƙudurinta kafin gawar Fulani babba ta bar wannan gidan. Tana fita Basiru ya fito daga bayan katangar da yake ɓoya, ya saki dariyar farinciki mummunar fuskarsa ta sake turɓunewa sannan ya faɗa cikin ɗakin mahaifiyarsa, da niyyar cim ma ƙurinsa da na shugabansa don ya ci alwashin duk rintsi sai ya ɗauko littafin da ke cikin ɗakin kamar yadda Boka Shaddas ya ba shi umarni. SHU'UMAR MASARAUTA 23 *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Kamar kazar da ta tono wuƙa haka Jawahir take tafe a sanyaye jiki babu ƙwari sakamakon yankan ƙaunar da mutuwa ta yi musu kwatsam babi zato babu tsammani, hawaye ne bibbbuyu suke zuba daga idanunta gabanta na ci gaba da faɗuwa ta bi ta hanyar baya zuwa sashen Fulani babba tana jin wani irin ɗaci a zuciyarta. Tun bayan da Mai gado ta sanar da ita mutuwar Fulani babba duk wani tsoro da firgici suka ƙaurace mata, babba tashin hankalinta bai wuce ta isa ta ga gawar Fulani babba ba, duk da ba ta da tabbacin za ta iya kwalli da gawar saboda yadda take jin ta. A zaune yake a kan kujerar gefensa kayan marmari da kayan lambu ne ya zura musu idanu tamkar yana son gano wani abu daga jikinsu, a baya ya ɗauki huɗubar mahaifiyarsa game da kishiyar mahaifiyar tashi amma sannu a hankali da ya fara girma ya sauka daga dokin zugar da huɗubar tsiyar da take yi masa. Ajiyar zuciya ya sauke sannan a hankali ya furta. "Allah ya jiƙanta." Kamar daga sama haka ya fara jin shassheƙar kukanta, karaf idanunsa suka sauka a kanta. Zumbur! Ya miƙe tsaye gabansa na faɗuwa bakinsa na rawa ya furta, "Ke... ke ... ce?" Cak Jawahir ta tsaya cikin kaɗuwa sakamakon ganin Yarima Muhsin a gabanta, a hankali ta fara ja da baya har ta ji bango ya tokare ta. Takowa ya fara yi don ya sake gasgata idanunsa ba gizo suke yi masa ba, ya ɗauki kwana da kwanaki yana zama a wurin ko Allah zai sa ya ganta amma ko mai kama da ita bai taɓa gani ba. Duk taku ɗaya idan ya yi sai ya ji bugun ƙirjinsa ya tsananta, ganin haka ya sa Jawahir ta sake mannewa da bango ta haɗa hannuwanta biyu alamar roƙo ƙirjinta na bugawa ta furta. "Don Allah ka yi haƙuri ranka shi daɗe, wallahi rannan ma tsautsayi ne." Jawahir ta ƙarasa maganar tana runtse idanunta ganin ya ƙarasa kanta gadan-gadan, sautin ajiyar zuciyarsa ta ji a fuskarta tana buɗe idanu ta ga ya yi mata rumfa. "Kin ga ire-iren zargin da ake yi wa su Salame, ko da wasa kada na kuskura na ga kin shige wa wani namiji. 'Yar iska ita ce take mu'amala da maza ko kina son ke ma a dinga kiranki da wannan sunan?" Jawahir ta tuna irin huɗubar da Mai gado ta yi mata watarana. Take jikinta ya ɗauki karkarwa, ta fara yunƙurin ja da baya amma babu zato ta ji ya fisgo hannunta ta faɗo jikinsa. Wani irin zuuuu Yarima Muhsin ya ji saboda azaba bai san lokacin da ya faɗi can gefe ba, wata irin azaba ya ji tana ratsa hannuwansa cike da raɗaɗi kamar ya sa hannuwansa a wuta. Cije baki ya yi yana yarfe hannu bai yi tsammani ba ya ji kukan wata baƙar saniya a bayansa, a hargitse ya ɗago da mamaki yana kallonta don ko a mafarki bai taɓa ganin saniya mai girma da baƙi kamarta ba. Ƙuri ta yi tana kallonsa tamkar wacce take shirin gwabza faɗa, a hankali ya fara ja da baya Saniyar ta fara tunkaro shi har sai da ya dangana da wata bishiya da ke bayansa. Tun lokacin da Jawahir ta ga Yarima Muhsin ya faɗi can gefe ta ɗiba a guje don tseratar da kanta, jikinta na karkarwa ta ƙarasa sashen Fulani babba sai a lokacin ta tsaya ta daidaita nutsuwarta. Ta sauke ajiyar zuciya tana mamakin abin da ya jefar da Yarima Muhsin a ƙasa har ta ji yana zuba ihu, Yariman da duk faɗin masarautar nan babu wanda ake tsoro kamarsa. Wani sabon tsoron ya dirar mata, tana tsoron Allah ya sa ba wani abin ne ya same shi ba. "Ko dai shi ma ɗan iska ne?" Jawahir ta faɗa a zuciyarta, ba ta samu damar ba wa kanta amsa ba kawai ta kutsa kai cikin gidan sakamakon jin sautin kukan 'yan uwan Fulani babba da suka ƙaraso daga masarautarsu. Kalaman Dattijo Maharaz ba su sa Kamalu ya saki jiki sosai ba don haka a ɗarare ya sake zura kansa, ƙurawa cikin farin dutsen idanu ya yi sannu a hankali ya ga fuskarsa na rikiɗa tana sauyawa. Mamaki ya sake mamaye shi, yana shirin ɗagowa ya ga wani farin maciji sol ya kanannaɗe saman kansa a firgice ya ta ƙarƙare ya zunduma ihu cikin tashin hankali. Tsoronsa ya sake ninkuwa sakamakon jin yadda ƙafarsa ta liƙe ƙam da ƙasa, sai da Dajjito Maharaz ya ci dariya ya more sosai sannan ya furta. "Da alama Masarautar Huddam na gabda samun shugaban da zai dinga nishaɗantar da su, wannan macijin da kake gani ba zai bar kanka ba matuƙar ba ka sake sunkuyar da kanka saman dutsen ba." Ganin ba shi da wata mafita ya sa Kamalu ya sunkuya ga namakinsa sai gani ya yi macijin ya warwaro daga kansa ya faɗa ciki. Kamalu na shirin ɗagowa ya ga fuskarsa ta fito dal kansa ɗauke da wani rantsattsan rawani mai matuƙar kyau da ɗaukan idanu. Da mamaki ya kai hannunsa saman kansa yana shafawa, ya sake mayar da kansa saman dutsen yana kallo. "Ka dangwali wancan taɓon da tafin hannuwanka ka shafa a jikin katangar can." Ba musu Kamalu ya sa hannu cikin tabon mai matuƙar danƙo ya manna a jikin katangar kamar yadda ya ga sawayen wasu a wurin. Yana gamawa Dattijo Maharaz ya ja shi suka nufi wata hanya mai ɗauke da waɗansu manyan tukwanen ƙasa, girman kowacce ɗaya za a iya saka mutum a cikinta. A kan tukunya ta ƙarshe suka tsaya Dattijo Maharaz ya furta, "Ɗora hannuwanka akai." Gabaɗaya Kamalu ya ƙosa da wannan abubuwan da yake saka shi, sai dai kuma haka kawai ya ji zuciyarsa ta gagara bijire masa. Yana ɗora hannuwansa ya ji wata irin busar sarewa a saman kansa, da sauri ya waigo Dattijo Maharaz ya sakar masa murmushi, shi kansa bai san dalili ba amma ya ji wani kaso na ɓacin ran da ke zuciyarsa ya kau. Daga haka suka juya har za su tafi daga can bayansu suka ji an furta. "Wane ne kai? Mene ne dalilin zuwanka wurin nan mai tsohon tarihi?" Galadina ya yi maganar yana shan gaban Kamalu. Tun daga ranar da Shugaba ya karɓi ragamar Fargi ya ci gaba da ƙoƙarin sarrafa al'amuran tsafinsa yana ba ta horon da ya dace, sai ya kasance ta taso cikin ƙwarewa da iya sarrafa alƙaluman tsafi da sihiri mutane har mamaki suke yi. A lokacin da ta ka shekara bakwai a duniya a lokacin Shugaba ya sake tsufa don haka koda aikin tsafi aka kawo masa, kusan tare suke aiwatarwa, da yake ta kasance mai kaifin basira har ta fishi gudanar da aiki nan take. Sai ya zamana girmamawar da ake yi wa mahaifinta da Shugaba ta fara karkata zuwa kanta, mahaifinta ko kaɗan bai damu ba sai ma tarin farinciki da yake mamaye shi yake sake tabbatar da a wannan lokacin ne ya san ya samu magajiya. Shi kuwa shugaba Zurrufu a kullin ya buɗi ido ya ga yadda ɗaukakarsa take yin ƙasa sai baƙinciki ya mamaye shi, tsanar Fargi ta sake mamaye zuciyarsa watarana har sai da ya ji tamkar ya hallaka ta. Amma kuma sai ya danne don har yanzu akwai gaɓar da yake son kaiwa domin cikar muradinsa. A lokacin da Fargi ta cika shekara takwas cif a duniya a sannan babu wani irin tsafi, sihiri da siddabarun da ba ta iya ba. Kai tsaye bokaye da 'yan tsubbun da ke wajen gari suke kawo mata aiki don neman taimakonta, kuma duk aikin da ta saka a gaba sai ta yi galaba a kansa. Cikin wannan shekarun na matashiya Fargi sai aka samu sauye-sauye da dama ta ɓangaren tsubbu da ci gaban samuwar kayan tsafe-tsafe, hatta masu zuwa neman taimako wurinsu sun samu ci gaba domin a wannan lokacin ba Bokaye ne kaɗai suke zuwa wurinsu ba daga cikin masu zuwa wurinsu sun haɗa da; Sarakun, masu neman Mulki ko wata ɗaukaka, 'Yan kasuwa da masu bulaguro, Maharba, Mafarauta, Masunta, Mahauta, 'yan bori da Matan aure musamman waɗanda suke da kishiya ko kuma waɗanda za a yi wa kishiya. Sai ya kasnce kawunan mutanen Rumzu ya fara wayewa har sukan gina bukkoki da rumfunan da suke zama suna hutawa, har ma suka fara samar da ƙananan rumfunan kasuwa wasu daga cikinsu sukan fita wajen gari su yo sarin wani abu su kawo cikin dajin nasu su sayarwa. A kuma wannan lokacin sai Fargi ta sake samun horo daga jinsin baƙaƙen aljanun ƙarƙashin ƙasa, bisa yadda za ta dinga sarrafa tsafi da shanu musamman baƙaƙe da jajaye don aiwatar da duk wani ƙulli da take buƙatar ƙullawa. Matsala ɗaya ce ta fara yunƙurin ci wa Fargi tuwo a ƙwarya na rashin samun wadatattun shanun aiki, a lokacin da ta kai ƙorafinta wurin Shugaban baƙaƙen Aljanun Sarki Kadmar. Sun jima suna tattanawa sannan suka tsaida matsayar idan ta amince sai su dinga ban gishiri na baka manda, wato ita ta dinga yi musu yankan duk abin da suke so su kuma za su dinga ba ta duk kalar saniyar da take buƙata a lokacin da za ta yi wani aiki. Zuciyar Fulani Umaima fari tass ta nufi sashen Sarki Abdul'aziz sai dai tana zuwa ta yi tursss sakamakon ganin Takawa da ta yi zaune shi da Mahaifin Fulani Babba sun saka gawarta a gaba suna yi mata addu'a. Ɓacin ranta bai ɓoyu ba har sai da ta bayyana a fili don ko kaɗa ba ta ji labarin Mahaifin Fulani babba zai zo jana'iza ba, tun da tuntuni mahaifiyarta da 'yan uwanta suka iso cikin Masarautar kuma ba tare da shi ba. Tana daga tsaye ƙerere a bakin ƙofa ta furta, "Ranka shi daɗe kuma waye har cikin turakarka? Ina tsammanin mu biyu za mu zauna da ita. "Fulani Umaima ta yi maganar tamkar ba ta gane mahaifin Fulani babba ba. "A yi hattara Fulani. Mai martaba ya ƙaraso yanzu ba da jimawa ba, za ku iya tafiya ku ba mu wuri." Fulani Umaima tamkar za ta fashe da kuka haka ta ji, tashin hankalinta bai wuce ba ta da dabara ɗaya da za ta ce za ta yi don ta samu sararin shiga har ta aiwatar da ƙudurinta. Kamar ba za ta matsa daga wurin ba ta fita tana jan sagaggiyar ƙafarta, zuciyarta a cunkushe ta koma sashenta. Tun daga tsakar gidanta ta fara jin yadda ake wurgi da kaya hakan ba ƙaramin mamaki ya ba ta ba, carko-carko ta ga su Inna wuro sun yi cikin ɓacin rai ta buga musu tsawa. "Uban waye a cikin ɗakin nan da kuka yi carko-carko ba za ku iya wanzar da komai ba?" Inna wuro ce ta yi ƙarfin halin faɗin. "Ranki shi daɗe a gafarce mu, Basiru ne ya shiga ciki kuma ya ba mu umarnin ko da wasa kada mu kuskura mu shiga cikin ɗakin." Rass gabanta ya faɗi, tun ba ta gama jin kalamansu ba ta faɗa cikin ɗakin. Yanayin yadda ta ganshi ba ƙaramin razanata ya yi ba, sak ta ga ya koma mata tamkar boka Shaddas. Cikin zare idanu da rashin tsoro ya dube ta da wata irin kakkaurar murya ya furta. "Ina kika kai littafin nan? Maza ki miƙo mini yanzun nan kar ki ɓata mini lokaci." Haka kawai ta ji toron Basiru ya kamata, don ta ga babu alamar wasa a fuskarsa. Fulani Umaima sai da ta fita can tsakar gida ta kori Bayinta don gudun kada su ji wata ɓaraka tsakaninta da Basiru, a fara yawo da ita a cikin gidan da ƙananan maganganu sannan ta koma ɗakin. "Waye ya aiko ka ɗaukan littafin nan?" "Wannan bai shafe ki ba, abu ɗaya kawai nake so ki damƙa mini shi. Idan kuma ba za ki iya ba ki fita ki bar ni na yi aikin gabana." Cike da faɗuwar gaba take bin sa da kallo, don idan kunnuwanta ba gizo suke mata ji ta yi hatta muryasa ta sauya daga tashi ta ainihi zuwa wata murya marar daɗin sauraro. "Yanzu haka kin dawo daga sashen Takawa ne silar zuwan mahaifin Fulani, kuma jikinki ɗauke yake da gubar da za ki sakawa gawar idan kina son na taimaka miki zan baki layar ɓata da garin kasa uwar bacci a yanzun nan. Za ki shiga cikin ɗakin ki watsa shi nan take za su kwanta nannauyan bacci, sai ki aiwatar da abin da yake gabanki. Amma fa idan kin so, idan ba kya buƙata za ki yi biyu babu domin ko ba yanzu ba na yi rantsuwa da girman Shugaba da horon tsafin da yake ba ni, da kuma sirrin tsafi da sihirinsa ko ba daɗe ko ba jima sai na mallake shi. Gara tun wuri wannan damar kada ta wuce ki." Fulani Umaima kusan mutuwar tsaye ta yi, ruwan mamaki ya mamaye ta; ta yi tsamo a gefe kamar kazar da aka jiƙa da ruwa. "Wai yau Basiru ne a gabana yake furta mini baƙaƙen maganganu? Tabɗijam! Ya zame mini wajibi na tashi tsaye a kan yaron nan. Bamaguje! Ya zame mini dole na je wurin Bamaguje, to amma ta ina za ni wurin Bamaguje bayan kuma ƙahon da nake busawa yana cikin akwatin can, sannan kuma a nan littafin wurin Bamaguje yake." Fulani Umaima ta yi wannan zancan a zuciyarta. Tamkar wanda ya ga abin da yake cikin ranta haka Basiru ya furta mata, "Ungo wannan, ki aiwatar da shi nan take. Idan kin gama da wannan kya tsaya yin shawarar yadda za ki ɓullo wa lamarina, wai tun daga yanzu ne na fara baki tsoro da mamaki? Kada ki yaudari kanki don ni da kike gani garnaƙaƙin dutse ce kowa ja da ni shi zai faɗi." Da mamaki take bin shi da kallo, jikinta na ɗan rawa ta matsa baya. "Waye ya baka wannan abin Basiru? Ya kake yin abu kamar boko ko matsafi? Wane ne Shugaban da kake magana? Basiru duka nawa shekarunka suke?" "Karɓa za ki yi ko tambaya za ki ci gaba da wurgo min?." Ya furta mata a taƙaice. Wannan shi ne ga ƙoshi ga kwanan yunwa, Fulani Umaima ta faɗa kogin tunani, gani take idan ta yi biyu ta tashi a tutar babu don ta matuƙar tsorata da Basiru da sigar da ya ɓullo mata. Babu yadda ta iya don haka ta yi ƙundunbala ta miƙa hannunta, "Zan karɓa amma sai ka fice mini daga ɗaki!" Miƙa mata ƙullin maganin da layar ya yi sannan ya ɗaga kafaɗa cikin halin ko-in-kula ya fice daga ɗakin. Wannan ita ce rana ta farko da Fulani Umaima ta yi dana-sanin haihuwar Basiru a rayuwarta, tun daga yanzu yaron na matuƙar ba ta tsoro musamman yadda yake faɗa mata magana kai tsaye ba tare da shakka ko shayi ba. Sai da ta tabbatar da Basiru ya fita daga sashensa ya koma sashensu sannan ta nannaɗe layar da cusa a jikinta tana jin zuciyarta shar cikin murnar cikar muradinta. Basiru da ke laɓe yana wurga idanu sai da ya ga wucewar mahaifiyarsa sannan ya fito yana sakin shu'umar dariya, yana zuwa ƙofar ɗakinta ya huro iska daga bakinsa take ƙofar ta buɗe ya faɗa cikin ɗakin ya sake turo ta kamar yadda mahaifiyarsa ta yi a baya. Kamar mayunwacin zakin da ke neman abinci ido rufe haka Basiru ya ci gaba da hargitsa ɗakin yana neman littafin wurin Bamaguje, ya ɗan shafe lokaci mai tsaho sannan ya hango tsohuwar akwatin da ke ƙarƙashin gado. Haka kawai ya ji gabansa ya yanke ya faɗi, take ya ɗora zarginsa a kan wannan akwatin. Da sauri ya shiga kiciniyar buɗe ta cikin nasara ya buɗe, idanunsa suka sauka a kan sihirtaccan littafin da Boka Shaddas ya umarce shi da ya kai masa. Hannunsa na rawa ya sa ya ɗauko littafin nan take ya ji wani irin zuuuuu har tsakiyar kansa, tamkar wanda ake fusga haka ya dinga ji da ƙyar ya iya miƙe wa tsaye ya runtse idanunsa ya fara karanta waɗansu kalmomin tsafin da Boka Shaddas ya koyar da shi, nan take ya ɓace daga cikin ɗakin ya sauka cikin tsibirin Boka Shaddas. Suna haɗa idanu suka sakar wa juna murmushin samun nasara, Boka Shaddas ya nuna wa Basiru gefensa sannan ya furta. "Maza zo ka zauna Jarumina,. Tabbas barewa ba za ta yi gudu ɗanta ya rarrafa ba, ba na haufi a kanka gwarzona ko ba na raye ba zan yi kukan rashin magaji na ƙwarai ba." *SHU'UMAR MASARAUTA* *24* *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* "Na ɗauko na ɗora ki a wannan matsayin ne domin a kawar da Abdul'aziz amma sai na lura da tafiyar kunkurin da aikin yake yi a wurinki, me ya sa haka Umama? Me ya sa aka shafe waɗannan watannin babu wani bayani. Ya zame mana wajibi mu kawar da shi cikin 'yan kwanakin nan idan ba haka ba wankin hula zai iya kaimu dare, daga nan kuma komai zai iya faruwa don haka wacce dabara gare ki da kike ganin za mu kawar da shi ba tare da asirinmu ya tonu ba?" Fulani Asabe ta ƙarasa maganar tana zuba wa Umaima ido. A yatsine ta dube ta sannan ta tura baki gaba, "Ni fa gaskiya Inna ba zan ita kashe Takawa ba don gaskiya na fara son shi, kuma su Galadima su haƙura mana dama can Allah ya rubuta ba su da rabo..." Tun ba ta ƙarasa maganar ba Fulani Asabe ta ɗauke ta mari, a fusace ta nuna ta da yatsa. "Har ni za ki faɗawa wannan maganar? To ko Uwarki ba ta isa ta faɗa mini wannan maganar ba ballantana ke! Na san ta hanyar ta zan ɓullo miki idan kin san wata ai ba ki san wata ba." A ƙufule Umaima ta murguɗa baki, "Wallahi tsaf sai na tona, atoh sai na tona asirin kowa ma ya tonu, shi kenan sai a yi biyu babu." Fulani Asabe har ta kai bakin ƙofa ta waigo da sauri, take ta karanci Umaima don haka ta koma ta zauna a kusa da ita. "Ba ki da wayo Umaima, ina son a kashe Abdul'aziz ne domin mu samu wani kaso me tsoka, kina ga fa har yanzu ko ɓatan wata ba ki yi ba. Haka za mu zuba ido waccan yarinyar ta ƙwace gidan? Kin ga idan aka kawar da shi ba sai a ɗaura muku aure da Galadima ba?" Shiru Umaima ta yi kamar mai nazari sannan ta ɗago ta furta, "Na fahimta Inna ni kaina haushin ta nake ji don ma Allah ya sa mata take haifa." Daga haka Fulani Asabe ta fice zuciyarta cunkushe da tunani. "Tabbas na yarda harɓi ga ɗan jaki gado ne, wato ni Umaima za ta nuna wa ita jinin Kilishi ce? Da ni take zancen cikin biyu dole za a yi ɗaya tun da har ta fara zancan tona mini asiri dole na san abin yi a kanta." Tun daga wannan ranar daga Umaima har Fulani Asabe kowa da abin da yake saƙawa a zuciyarsa, a cikin 'yan kwanakin nan ne kuma Allah ya yi wa mahaifiyar Sarki Abdul'aziz rasuwa sakamakon 'yar gajeriyar jinyar da ta yi. Dalilin da ya sa Iyayen Umaima da na Fulani babba suka zo yi wa Sarki Usman da Sarki Abdul'aziz gaisuwa, kuma a wannan zuwan da suka yi ne Umaima ta shaida wa mahaifiyarta yadda suka yi da Fulani Asabe. "Duk da Asabe 'yar uwata ce hakan ba zai hana na kawar da ita idan tana son kawo mini matsala ba. Ki bar mini komai a hannuna, daga yau daga rana mai kamar ta yau ita da 'ya'yanta ba za su sake ɗaga baki a kan sarauta da mulki a cikin gidan nan ba." Mahaifiyar Umaima ta yi maganar cikin cin alwashi. "Fiye da haka na san za ki aikata ranki shi daɗe. Ba don kada na koɗa ki har ki ga kamar zuga ce nake yi miki ba, da sai na ce a kaf faɗin duniyar nan babu wanda ya kai ni sa'ar samun mahaifiya." Murmushi mahaifiyar tata ta saki. "A kan farincikinku zan iya aiwatar da komai domin komai ba komai ba ne a wurina." Basiru ya saki murmushin farincikin jin daɗin yabon da Boka Shaddas ya yi masa, fuskarsa ta sake faɗaɗan ƙaton hancinsa ya sake bajewa yayin da fakekiyar fuskarsa ta ƙara bajewa. "Ni mai biyayya ne a gare ka hatta rayuwar mahaifiyata idan ka na buƙata sai na ɗauko maka ita." Basiru ya faɗa cikin nuna bajinta. Ƙuri Boka Shaddas ya yi yana kallonsa haɗe da nazartar halaye da ɗabi'un yaron. Lokaci ɗaya ya ji ƙirjinsa ya buga don gani yake tamkar yaron ya fi shi bushewar zuciya da rashin imani, amma gudun kada Basiru ya fahimci wani abu ya sa ya sakar masa murmushi sannan ya ɗebi wani ruwa mai yauƙi ya zuba a kan littafin. Lokaci ɗaya littafin ya fara fitar da wani farin hayaƙi sannan ya kai hannu ya buɗe shi, daidai wurin da Fulani Umaima ta tsaya da karatu ya buɗo don haka ya saki shu'umin murmushi ya ɗago ya dubi Basiru. "Tabbas mun taki babbar sa'a domin Mahaifiyarka, ta ci ƙarfin karatun littafin. Da ace mun yi bori da sanyin jiki da tuni wani zancan ake ba wannan ba, sakamakon gab take da kammalawa kuma tana kammalawa za ta kai matuƙar ƙololuwar nasara. Daga haka ta mayarwa da Bamaguje littafinsa, ka ga kenan da mun tashi a tubar babu kuma babu wata amfana da za mu yi." Basiru ya yi wa Boka Shaddas jinjina da hannu. "Ba za ta taɓa yin nasara a kanmu ba." Boka Shaddas ya jinjina kai sannan ya ɗan fara duba shafin da ya ci karo da shi. "Duk da kasancewar zuri'ar mahaifinki sun fito ne daga zuri'ar Bargi su ne suke mulkar yankin nan bakiɗaya, wato kakanninki sune da sarautar masarautar nan. Kuma hakan ba ya hana su yin rayuwarsu ta bakin teku da koguna ba ne, dalilin da ya har suka samu kyakkaywar alaƙa tsakaninsu da jinsin Aljanun cikin ƙarƙashin ruwa waɗanda ake kira da Jinnul-Gawwas. Har ta kai sun buɗe musu su kan gansu suna iyo a cikin ruwa kamar yadda mutane ke shiga su yo su ɗin kifi, a irin wannan lokacin ne idan tsautsayi ya gifta da ajali sai ka ga sun janye mutum can cikin ƙarƙashin ruwa sai sun gama zuƙe jininsa sun ƙwaƙwale wasu hallitu na jikinsa sai su turo shi sama, wannan lamari sai ya fara damun mahaifin Kakanki har ya samu Sarkin Aljanunsu na ruwa suka yi doguwar tattaunawa suka tsayar da matsaya, a kan sun daina cin kowannen bil'adam na wannan yankin sai shekara-shekara, za su ci mutum uku saɓanin a baya da suke cin babu adadi. Ganin hakan ne ya kawo masala shi ya sa mahaifin kakanki ya amince, kuma da yake Sarkin jinnul-gawwas Dattijon ƙwarai ne sai ya tsawatar wa da sauran waɗanda suke ƙasansa ba tare da wani ya karya alƙawarin da aka zartar ba." Sai da na sauke ajiyar zuciya ina mamakin wannan murɗaɗɗan labarin da Sarki Hafiz yake ba ni sannan na furta masa. "Amma wannan labarin da kake ba ni kana ganin zai ɗauki shekara nawa? Kuma ya aka ƙarke tsakanin mahaifiyata da ɗan gidan Aljani Darri? Ya aka yi mahaifina ya yi galaba a kan mahaifiyata har ya tarwatsa soyayyar da ke tsakaninsu wacce ka ce tuni mahaifiyata ta damƙa wa Ɗan autan aljani wuƙa da nama na soyayyarta?" Murmushi Sarki Hafiz ya sakar mini, yayin da Fuskar Fulani Hawwa kulu take a tamke kamar magaribar ɗinya. "Me kike ci na baka na zuba ne Hidaya? Ai duk gaggawar kwarto ya jira mai gida ya gusa kuma duk gaggawar ungozoma ta bari a haife." Murmushi na sakar masa sannan na ji ya ci gaba da cewa. "An sha gwagwarmaya matuƙa tare da baƙin artabu kafin auren mahaifiyarki da mahaifinki, kuma tun lokacin da aka ɗaura auren iyayenki ƙofofin bala'i da na masifa suka fara buɗewa a cikin masarautar nan. Sannan kuma babu takamaiman adadin shekarun da zan iya sanar da ke domin ni kaina Kakana bai sanar da ni ba, abu ɗaya na sani shi kansa Kakana yau kimanin shekararsa ashirin da biyar kenan da mutuwa, kuma labarin auren mahaifiyarki zai iya kai wa tsawon shekaru talatin kenan tun da a bayanta an yi sarakunan da suka shuɗe." A hargitse na dube shi cike da matsanancin mamaki har sai da ya gane mamakina ƙarara a fili, "Me kake shirin sanar da ni Sarki Hafiz? Da bakinka ce iyayena babu wanda ya fito daga cikin jinsin jinnu, amma kuma ya aka yi na kasance mai ƙarancin shekarun da ko sha biyar ban kai ba. Shin ya aka yi haka ta faru? Yanzu haka ina mahaifana? Me ya sa ba sa cikin masarautar nan?" Boka Shaddas ya rufe littafin haɗe da kallon ƙofar kogon tsafinsa, sakamakon jin maganar wata baƙuwarsa da ta kawo masa ziyara. Bai amsa mata ba sai da ya ƙarasa har wurin da kayan tsafinsa suke sannan ya jefa littafin cikin wata ɓaƙar tukunyar ƙasa nan take littafin da tukunyar suka ɓace ɓat. Lokacin da Fulani Umaima ta ƙarasa ƙofar ɗakin Takawa babu abin da yake tashi sai kukan tsintsaye da ƙananan dabbobi, cikin sanɗa ta ɗan bankaɗa labulen ɗakin sannan ta hura maganin hannunta. Komawa ta yi ta tsaya tana kallon abin da zai faru don ba taa yi tsammanin abin da Basiru ya faɗa zai tabbata ba, a hankali ta ga Sarki Abdul'aziz da Mai martaba sun fara hamma babu jimawa kowannensu ya ɓungire bacci ya yi awon gaba da su. Wani uban tsalle Fulani Umaima ta buga cikin farinciki ta faɗa ɗakin, sai da ta rufe ɗakin ruf sannan ta ƙarasa wurin da gawar Fulani babba take kwance sannan ta fara kunce ɗaurin da ke wurin ƙafafuwanta. Kafin wani lokaci tuni ta ware likkafanin cikin farinciki ta ciro wannan ɗaurarriyar fatar wurin Bamaguje ta tura mata a cikin ƙasanta, nan take gawar ta fara wani irin karkarwa sannu a hankali wani baƙin hayaƙi ya fara fita daga jikinta yana bi ta ƙofar yana fita kai tsaye hayaƙin ya wuce sashen Sailuba. Kamar yadda Bamaguje ya gaya mata sai da hayaƙin ya gama fita sannan Fulani Umaima ta mayar da likkafanin ta ɗaure ba tare da ta cire wannan ɗaurarriyar fatar ba. Ta karkaɗe jikinta sannan ta fice daga ɗakin, tana jin ta tamkar ta riga da ta gama da matsalolin gabanta na duniya gabaɗaya. Tun daga tsakar gidanta ta fara cin karo da kayan ɗakinta a warwatse tamkar zaratan jarumai goma ne suka yi dambe a wurin, ƙirjinta ne ya yi wata irin bugawa nan take jikinta ya ɗauki karkarwa tamkar mazari. Kamar kazar da aka tsamo daga ruwa haka Fulani Umaima ta shiga ɗakin jiki a saɓule tana fatan kada Allah ya sa zarginta ya tabbata da take yi a kan Basiru, cak ta tsaya wuri ɗaya tana jin wani irin abu yana mamaye tsarga mata tun daga tafin ƙafarta har zuwa tsakiyar kanta sakamakon hango akwatin ƙarfenta da ta yi a yashe a ƙasa, komai ya tarwatsa da alama babu komai a cikinta. Kamar wace take jin tsoron taɓawa haka ta ƙarasa a ɗarare, ta zauna daɓar irin zaman 'yan bori a ƙasa hawayen da ta rasa na mene ne ya fara bin kuncinta. "Allah wadaran hali irin naka Basiru! Ban san ya zan yi da kai ba wannan wanne irin yaro ne mai taurin kan tsiya." "Ummi me yake faruwa?" Muhsin ya furta daga bakin ƙofa. Jin tambayar Muhsin ya sa ta fashe da kuka tana jin zuciyarta na zafi. Mamaki ne ya kama Muhsin ya bi ɗakin da kallo sannan ya ƙarasa gaban mahaifiyarsa, a sanin halin mahaifiyarsa ya san rasuwar Fulani Babba ba zai ɗaga hankalinta har ta aikata wa ɗakinta haka ba. "Muhsin ƙaninka ya zame mini alaƙaƙai dubi yadda ya yi mini da ɗaki, ni ya raina ni ba zan taɓa yin magana ya saurare ni ba." Ajiya zuciya Muhsin ya sauke sannan ya furta, "Ummi sai dai fa ki yi haƙuri, amma daga ni har 'yar uwata babu mai hali ko ɗabi'a irin na shi. Kin san kowanne yaro da yadda Allah ya halicce shi wataƙila nan gaba zai daina." "Sai yaushe Muhsin? Yaushe kake tunanin Muhsin zai kintsu, rannan fa kamar ya ɗaga hannu ya dake ni." Jin haka ya sa Muhsin ya ɗan taɓe baki. "Ina Ruƙayya?" Ya wurga mata tambaya. "Na haɗa ta da baiwa Inna wuro." Fulani Umaima ta yi maganar tana ruƙo hannun Muhsin. "Muhsin ina jin tsoron ganin girman ƙaninka domin a yanzu ko shekara sha huɗu ba bai yi ba, amma ya gagare ni..." Ihun da Muhsin ya yi ne ya katse ta, ya matsa baya yana yarfe hannu cikin azaba. "Me ya faru Muhsin? Lafiyarka kuwa?" Wani irin kallo yake bin mahaifiyarsa da shi, jiki a sanyaye ya jingina da bango nan take ta ga idanunsa sun ciko da ƙwallah. A tsarace ta kalle shi don ta san abin da zai sa Muhsin ƙwallah ba ƙaramin abu ba ne. "Ummi!" Ya ambata da wani irin yanayi, Fulani Umaima na shirin amsawa ya ci gaba da cewa. "Ta shammaci zuciyata a lokacin da zuciyar tawa ta sakankance a nisan kiwon da za ta yo kalacin abin da za ta ciyar da kanta, ta mamaye gangar jiki da ruhina a lokacin da ban yi zato ba. Kwatsam soyayyarta ta mamaye ni har ta kai komai da kowa na gudurata idan ba tunaninta ba, babu zato soyayyarta ta kewaye duniyata, ta ruhin da nake taƙama da shi. Ruhin da a kullin yawon zabarin nemanta yake ko zai yi tozali da ita domin ya samu sauƙin zugi da raɗaɗin da ke tare da shi, sai da kash! Da alama ban yi dacen ajiye ƙwarya a gurbinta ba, ban santa ba ban san asalinta ba. Ni dai abu ɗaya kawai na sani ina sonta, ina ƙaunarta! Ina jin ta a cikin jiki, zuciya da hantata. Ba na jin zan ci gaba da rayuwa matuƙar babu ita, a duk bugun numfashina yana fita ne tare da kewa, bege da ƙwadayin tozali da ita." Fulani Umaima sakin baki da hanci ta yi cike da mamaki tana kallonsa, lokaci ɗaya kuma tsoro ya kamata don tana gudun kada wata ta asirce mata ɗa don ko akuyarta ba za ta bari a asirce ballantana Yarima guda mai jiran gado. "Wace ce ita?" Fulani Umaima ta tambaye shi a taƙaice. Idanu cike da ƙwallah ya furta, "Ban santa ba! Ban san wace ce ita ba a cikin gidan nan! Ganin da na yi mata na biyu shi ne wannan abin da ya faru da ni." Muhsin ya ƙarasa maganar yana nuna wa mahaifiyarsa hannunsa, ganin yadda hanunsa ya kwaile ya ƙone da wuta ya sa ta miƙe zumbur. "Waye ya yi maka haka?" "Ina tsammanin ba mutum ba ce!" Muhsin ya furta a sanyaye. "A ina take?" Fulani Umaima ta sake wurga masa tambaya, nan take Muhsin ya zayyanewa mahaifiyarsa duk abin da ya taɓa faruwa tsakaninsa da Jawahir, shiru ta yi tana nazari sannan ta sake kai idanunta kan hannuwan Muhsin. "Tashi ka je duk abin da yake faruwa zan kamo bakin zaren, mu bar wa zuwa wayewar gari ka san Mahaifinka a yanzu yana cikin halin jimamin rashin matarsa. Amma mu yi haƙuri zuwa ɗan wani lokaci. Muhsin ya miƙe jiki babu ƙwari har ya zai fita ya hangi wani ƙaramin ƙoƙon kan mage, da mamaki ya tsugunna ya ɗauke yana juyawa. "Me ya kawo wannan abin cikin ɗakin nan?" Rass! Gaban Fulani Umaima ya faɗi. "Za ta iya yuwa ɗan'uwanka ne ya shigo da shi, ba ni nan idan ya dawo zai mini bayanin dalilin da ya sa ya kawo mini shi ɗaki." Fulani Umaima ta yi maganar tana karɓar ƙoƙon kan magen da ke hannunsa wanda Bamaguje ya taɓa ba ta da jima ta saƙalewa a kusurwar ɗakinta. Tun da Muhsin ya fita Fulani Umaima ta saka zaune ta kasa tsaye, damuwa goma da ashirin ta cunkushe zuciyarta. Ta rasa wacce za ta fara magancewa, matsalar Basiru da ke neman gagare mata ko ta littafin da ya ɗauke mata? Ko kuma ta wurin Yarima Muhsin da ta lura ana neman zautar da shi ta ƙarƙashin ƙasa. "Galadima ko Ciroma." Ta furta a fili. "Na tabbata cikinsu akwai mai niyyar salwantar mini da rayuwar Yarima, kuma har abada ba za su yi galaba a kaina ba matuƙar ina da Bamaguje a faɗin duniyar nan." Fulani Umaima ta ƙarasa maganar cikin cin alwashi. Lokacin da Kamalu ya ji tambayar Galadima ya ɗan so ya duburburce, Dattijo Maharaz ya dafa kafaɗarsa ya furta. "Ka ce masa ita karaga tana ga mamallakinta ne ba wanda yake son mallakarta ƙarfi da yaji ba, jinin Marigayi Sarki Muhammad Safwan har abada ba ya buƙatar tilastawa. Mai karaga yana ga abarsa duk rintsi duk wuya, kuma ko ba-daɗe ko ba-jima mai ita zai maye gurbinsa." Kamar yadda Kamalu ya ji haka ya sanarwa da Galadima. Take ya lura da yanayin firgici da tashin hankalin da ya shiga, lokaci ɗaya Galadima ya ji ƙafafuwansa na namenan gagarar ɗaukar nauyin gangar jikinsa. Ganin haka ya sa Dattijo Maharaz ya ja hannun Kamalau suka fice daga cikin soron. "Wane ne shi? Ya aka yi ya san wannan furucin tsohon furucin, ɗan waye shi da zai faɗi wannan maganar mai tasiri ga wanda zai iya baƙuntar karagar Masarauta?" Da sauri Galadima ya bi bayansu amma sama da ƙasa ya nemi Kamalu ya rasa. Dattijo Maharaz da Kamalu suna fita suka ci karo da Baffajo da yake ta bulayin neman Kamalu, da sauri ya damƙi hannunsa suka ɗauki siiririyar hanyar da a ta sada su da sashen bayi. A wannan lokacin Dattijo Maharaz ya so sanar da Kamalu tushen labarinsa da asalinsa, amma sanin firgicin da ke tare da Baffajo dangane da maganar da Kamalu ya ji daga gare su ya sa ya ƙale shi sai bayan wani lokaci, amma ya ci alwashin a haɗuwarsa ta gaba zai feɗe masa biri har wutsiya. Idan ya so duk wacce za a yi sai a yi tsakaninsa da zuri'a da suka yi kane-kane a cikin rayuwar Kamalu. *SHU'UMAR MASARAUTA* *25* *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Kiran sallar asubar farko ne ya farkar da Sarki Abdu'aziz daga nannauyan baccin da ya yi awon gaba da su, haka kawai ya ji jikinsa ya yi masa nauyi da tsami kamar wanda aka yi wa duka. A ɓangare ɗaya yana mamakin yadda bacci ya yi awon gaba da su duk da irin mummunan halin da suke ciki, a hankalin ya miƙe ya fita ya ɗauro alwala yana shigowa ya ga Mai martaba mahaifin Fulani babba ya tashi. Da kanshi ya zuba masa ruwa a buta ya ajiye masa, sannan ya koma gefe ya zauna ya zuba wa gawar Fulani babba idanu da ke kwance babu motsi. "Sarkina watarana fa daga mu biyun nan za mu koma mu uku, daga haka fa sai a gan mu har da jikoki ko?" "Ina matuƙar ƙaunarka Sadaukina, shi ya sa nake addu'ar Allah ya sa na riga ka mutuwa don ba zan iya jure rashinka ba." "Don Allah a duk lokacin da kake gaban gawata ina son ka shaida Wa Ubangiji ni mai biyayyar aure ce kamar yadda kake faɗa, ko roƙa mini yafiyar laifukana ka kuma nema mini salama a cikin makwancina." Lokaci ɗaya kalaman Fulani Babba na tsahon shekarun baya suka dawo masa, a lokacin ba su fi shekara biyu da aure ba don ko Fulani Umaima bai aura ba. "Ke 'yar aljanna ce Fatima! Ke mai biyayyar aure ce Fatima. Allah ya gafarta miki Ubangiji ya ni'imta makwancin da za mu kai ki, amma me ya sa za ki tafi ki bar ni? Me ya sa mutuwarki ta shammace ni..." Kuka ya ci ƙarfin Sarki Abdul'aziz dalilin haka ya gagara ƙarasa kalaman bakinsa, har yanzu gani yake mutuwarta tamkar mafarki ce da yake fatan farkawarsa a kowanne lokaci. Sai a yanzu ne yake tuna irin zaman 'yan marinar da suka dinga yi tsakaninsa da ita yana mamakin musababbin faruwar haka. Wani irin ɗaci ya mamaye zuciyarsa tare da nadama, da-na-sani da kaicon cusgunawar da ya yi mata, babban takaicinsa bai wuce yadda nadamar ta zo masa a lokacin da ba za ta yi masa amfani ba. "Taso mu je masallaci sun shiga Sallah, sai haƙuri Abdul'aziz kuka ba zai dawo mana da Fatima ba." Mahaifin Fulani babba ya yi maganar yana janyo hannun Sarki Abdul'aziz, masallaci suka wuce kowannensu zuciya babu daɗi. "Lafiya kika aika kirana da wannan farar asubar Sailuba? Wallahi ba ƙaramin faɗar mini da gaba kika yi ba, mene ne yake faruwa?" Jakadiya ta yi maganar ƙasa-ƙasa. Kalaman Jakadiya a madadin su sanyaya zuciyarta sai kawai ta fashe da matsanancin kuka, da sauri Jakadiya ta matsa wurin Sailuba tana zama a gefenta wani irin wari ya mamaye hancinta. Da sauri ta ja baya tana ɗan toshe hanci gabanta na tsananin bugawa. "Wani me ye wannan yake wari Sailuba?" Da mamaki Sailuba ke kallon jikinta don ita babu wani da take ji, sai da ta share hawayenta sannan ta furta. "Inna tun daren jiya nake tsula fitsarin kwance ga wani ruwa mai ɗoyi na fita daga ƙasana, ina zuwa banɗaki na yi wanka na ga kwarkwata na faɗowa daga kaina na shiga uku Inna ina tsoron kada irin ciwon Fulani ya same ni." "Jakadiya ni warkice daidai da ƙugun kowacce shegiya, ki rubuta ki ajiye Umaima ba kanwar lasa ba ce kuma ko an ci birnin kura ba a taɓa ba wa ingarman kare dillanci. Wallahi ni Umaima sai na muzanta rayuwarku na maisheku ƙanƙantattun marasa amfani." Take kalaman Fulani Umaima na baya suka dawo cikin kunnuwan Jakadiya, wani irin matsanancin tsoro ya dirar mata. "Fitsari fa Sailuba? Kina nufin fitsarin kwance?" Sailuba ta gyaɗa kai tana share hawaye. "To ai ni yanzu ma wani irin warin jaɓa na ji kina yi, na san wannan ba zai wuce sharrin Umaima ba. Wato dai abin da nake zargi ya tabbata, ta gama da Fulani babba yanzu za ta dawo kanki." Sailuba ta zaro idanu a firgice. "Na rantse da girman Allah, kwarankwatsa dubu da ɗoriya ko zan yi yawo tsirara sai na nuna wa Fulani Umaima ta tsokano tsuliyar autan dodo. Sai na nusar da ita duk girman bishiyar kuka bagaruwa ce babba, ni Jakadiya na yi artabu da waɗanda suka ninke Umaima a fanin hatsabibanci da tsafi na yi galaba. Wallahi-wallahi sai na shammace ta; ta ɓangaren da ba ta taɓa tsammani ba. Sai na cusa mata baƙincikin da har abada ba za manta da shafina ba, kuma sai na ɗanɗana mata azabar da ruwa ko teku bai isa ya sanyaya mata uƙubar da take ciki ba. Ki kwantar da hankalinki Sailuba matuƙar ina numfashi, sai Umaima ta durƙusa da gwiwoyi biyu a gabanki tana neman afuwarki." Yarjejeniyar da Fargi ta ƙulla tsakaninta da baƙaƙen aljanun ita ta sake ba ta damar samun ɗaukaka mafi rinjaye a cikin dajinsu, har ya zama ayyukan tsafi da dama sun koma hannunwanta sai dai idan ta ga aikin ya yi mata sai ta miƙa wa Shugaba Zurufu ya tayata. Wannan ɗaukakar da Fargi ta sake samu sai ta sake ninka ƙiyayyarta da ke cikin zuciyar Shugaba, har ya fara keɓantacciyar shawara da shugabannin aljanu domin su ba shi mafitar da zai hallakar da ita a ruwan sanyi amma hakan bai samu ba. A lokacin da Fargi ta kai shekara goma sha uku ta fara zama budurwa, kyawun sura da na halitta suka bayyanar mata. Baƙa ce ba can sosai ba, sai dai doguwa ce tana da tsayi ba ta da kauri sosai. A wannan lokacin cika da ƙasaitar tsafinta ta tunbatsa don haka samarin cikin zuri'arsu suke shakkar tunkararta da niyyar ƙulla soyayya, sakamakon tsoron kada ta fusata har ta ɗauki mummunan hukunci a kansu. A na cikin wannan yanayin kwatsam Boka Ɗan tani ya kawo Ɗan sarkin ƙasar Bahdi wurin Shugaba a kan ayi masa aikin da za a hallaka yayansa idan ya so ya gaji karagar mahaifinsa. Shugaba Zurufu duk yadda ya so ya buga aikin Sulaiman sai lamarin ya gagare shi sakamakon shi ma Yariman da aka kawo mahaifiyarsa a tsaye take tsayin daka wurin tsubacce-tsubacce, a wani binciken da ya yi ma ya gano shi da kansa ya yi wa mahaifiyar Yariman aikin da Mahaifinsa zai yi murabus ya damƙa masa. Ganin babu nasara ya sa Shugaba ya sallami Sulaiman ba tare da yin nasara ba, a sanyaye ya fito daga kogon dutsen ya hange ta a tsaye a jikin dokinsa tana aiwatar da ɗan tsafe-tsafenta da fuskar dokinsa. Idan ta shafa fuskarsa sai ta koma zuwa da saniya, agwagwa, zaki, kura da duk sauran kayan namun dajin da take buƙata. "Idan aka bar shi da fuskar damisa yau ina na kama?" Sulaiman ya yi maganar cikin zolaya. Waigowa ta yi ta sakar masa murmushi. "Sadaukin namiji ba a san shi da jin tsoro ba. Kai da kake burin zama Sarkin Bahdi dole ka janyo bargon jarumta ka lulluɓawa kanka." Kallon mamaki ya bi ta da shi, ta ɗan matsa daf da shi. "Za ka samu sarautar Masarautar Bahdi indai da yawan numfashi amma kuma sai dai ba ta sigar da kake buƙata ba." A karo na biyu ya sake zuba mata idanu da matsanancin mamaki. Kasancewar duk wasu masukantan Fulani babba sun hallara, gari na ɗan washewa aka fito da gawar Fulani Babba, dubannan mutanen manya da yara ne suka sallaci gawarta sannan aka wuce da ita gidanta na gaskiya. Sarakuna daga ƙasashe da dama ne suka ziyarci Sarki Abdul'aziz domin yi masa ta'aziyyar rashin uwar gidansa, kuma uwar 'ya'yansa. Ilahirin mutane gidan kowanne ka dube shi cikin alhini da jimamin mutuwar Fulani babba yake, Abubakar da ke ɗakinsa sai bin mutane yake da kallo ba tare da ya san abin da yake faruwa ba. Abu ɗaya yake yi kuka idan ya ji yunwa ta dame shi, kuma da ya ga baƙin fuskar ba bai saba gani ba sun shiga ɗakinsa sai ya fara bige-bige yana son cakumo mutum. Mahaifiyar Fulani babba ban da kuka babu abin da take musamman da ta kalli Abubuwar, Su Khadija kowacce ta zo da 'ya'yanta amma kallo ɗaya za ka yi musu ka fahimci suna cikin matsananciyar damuwa. Mahaifiyar Fulani Umaima da 'yan uwanta ba su iso ba sai bayan da aka kai gawar Fulani Umaima, kallo ɗaya mahaifiyarta ta yi mata ta fahimci akwai wata a ƙasa game da mutuwar Fulani babba. "Ba ni labari yadda aka haihu a ragaya don ganin fuskarki kaɗai ya tabbatar mini akwai wata a ƙasa." Mahaifiyarta ta furta bayan sun shige uwar ɗaki da Fulani Umaima. "Aikin Bamaguje ne, kin san ko shugaban sheɗanu haka ya gan shi ya ƙyale." Umaima ta furta. "Ni shaida ce don yanzu haka jiya mahaifinku ya tsayar da ranar da zai yi murabus ya danƙa wa ɗan'uwanki Muhammad." Murmushi Fulani Umaima ta saki sannan ta furta. "Amma fa ina da gagarumar matsalar yanzu dai tun da a cikin kacaniyar mutuwar nan ake zan ziyarci Bamaguje." "Wannan karon ba ke kaɗai za ki ziyarce shi ba domin ni kaina akwai abin da ya fara ci mini tuwo a ƙwarya." Hawaye ne bibbiyu yake zuba a idanun Mai gado da ke gaban gadon da Jawahir take kwance, jikinta ta ɗauki zafi zauuu sai sauke numfashi take sama-sama. Da alama bacci take amma kallo ɗaya idan ka yi mata za ka fahimci a galabaice take, gaban Mai gado na faɗuwa ta kai hannu a hankali ta yaye rigar Jawahir. Dam! Ƙirjinta ya buga da ƙarfi har sai da ta sa hannu biyu ta dafe ƙirjinta, tambarin cikin Jawahir ne ya fito jawur tamkar garwashin wuta. "Kin saɓa umarnina Jawahir! Ina hango abubuwan da ke ba za ki taɓa hango su ba, amma duk da haka hannunka ba zai taɓa rubewa ka yanke ka yar ba. Ba ni hannunki Jawahir." Mahaifiyarta ta furta tana miƙa wa Jawahir hannu. A ɗan tsorace Jawahir ta fara takawa har zuwa gabanta, gabanta na faɗuwa ta miƙa mata hannunta na hagu. Da ƙarfi mahaifiyarta ta fisgi hannunta sannan ta fara tafiya da ita har ta isa bakin bishiyar da Fulani Umaima ta binne butar da Bamaguje ya bata. "Ki haƙo butar nan ji ki je ki ɗebi ruwan rafin tsamiya, ki je sashen Umaima ki zuba asirin jikin Takawa zai wargaje gabaɗaya. Sannan ki ɗauki butar ki damƙawa Kamalu ita ragowar aikin zuri'ar da ke tare da shi za su nusar da shi abin da zai yi a gaba. Kuna da matuƙar tasiri dangane da junanku sai da arashin ruhi ne ke tsaurara tsattsamar alaƙa a tsakaninku." Mahaifiyarta ta ƙarasa ta damƙi wuyan Jawahir da ƙarfin gaske har sai da ta fara wani irin kakari idanunta suka firfito waje numfashinta na yunƙurin ɗaukewa sannan ta sake ta; ta ci gaba da cewa. "Na yi rantsuwa da girman shahara da fifikon tsafin da na fi gabaɗaya zuri'ata matuƙar kika kuskurewa umarnina sai na hallaka ki da tafukan hannuwa, domin ba zan iya jurar a salwantar da rayuwarki ba tare da cikar muradina da na mahaifinki ba." Wani irin kakari Mai gado ta ji Jawahir tana yi numfashin na ƙoƙarin ɗaukewa, tana shirin tashinta Jawahir ta tashi firgigit a galabaice tana sauke ajiyar zuciya idanunta sun firfito. Hannu biyu Jawahir ta sa a wuyanta ta riƙe har lokacin ba ta daina sauke numfashi ba. "Sannu Jawahir jikin ne?" A hankali Jawahir ta girgiza mata kai, "Inna shi kenan Fulani ta mutu?" Jawahir ta yi wa Mai gado tambayar don ta kawar da hankalinta, sai da Mai gado ta share hawaye sannan ta furta. "Jawahir har abada ba zan daina kukan rashin Fulani ba." Jawahir ta miƙe a hankali ta ɗauki mayafinta ta ɗora a kafaɗa. "Ina kuma za ki jawahir ke da zazzaɓi bai gama sauka daga jikinki ba." "Inna yanzu nan zan dawo." Jawahir ta yi maganar tana ficewa daga ɗakin. Tana tafe gabanta na faɗuwa sai raba ido take cikin matsanancin tashin hankali, kallo ɗaya za ka yi mata ka fahimci ba ta cikin nutsuwarta a haka har ta ƙarasa sashen Sarki Abdul'aziz da ke cike da 'yan gaisuwa. Ta bayan sashen shaƙatawarsa ta zagaya a lokacin babu kowa take tsoro ya sake mamaye ta, daga can bakin wata bishiya ta hangi ƙasanta na fitar da hayaƙi. "Ga wurin can, ki yi gaggawar tonewa kada ki ɓata lokaci." Ta ji muryar matar da ta yi mafarki da ita raɗau a cikin kunnuwanta, da sauri ta ƙarasa ta fara tonowa ba ta ɗauki lokaci mai tsayi ba ta tone butar nan take ta ji wani irin yammmm tsigar jikinta na tashi. Kai tsaye rafin tsamiya ta nufa ta ɗebi ruwan ciki tana miƙewa ta ga wurin yana juya mata, runtse idonta ta yi ta ji kamar ana tafiya da ita a saman iska. Tana buɗe idonta ga mamaki ta hange ta a soron sashen Fulani Umaima, a cikin mayafinta ta ɗan ɓoye butar ƙirjinta na bugawa matsanancin tsoro ya mamaye ta. Tana nan tsaye lokaci ɗaya ta ji butar ƙarfen ta fara ɗaukan zafi, tamkar ana neman a kwaci butar haka ta fara ji. Tana son ɗaga ƙafarta don ta shiga tsakar gidan Fulani Umaima amma yadda ake fusgarta na neman gargararta. Sai da ta yi da gaske sannan ta iya shiga cikin sashen, ta fara zubawa. Duk wurin da ta zuba ruwan butar sai dai wani baƙin hayaƙi ya tashi, tana gama zubawa da sauri ta fice daga sashen gabanta na tsananin bugawa. Murmushi ɗauke a saman fuskokinsu suka ƙarasa cikin kogon dutsen Bamaguje, daga can saman dutsen suka hango shi a tsaye riƙe da sandar tsafinsa saboda tsufa ya ranƙwafa sosai jikinsa sai karkarwa yake. Fulani Umaima ta dubi mahaifiyarta tana sakin murmushin don rabon da su kawo wa Bamaguje ziyara a tare a ƙalla an doshi kusan shekara Talatin, Mahaifiyarta ta fara yin gaba ita kuma tana biye da ita. "Tsafi ya ja linzamin dokin shugaba har zuwa ƙarshen rayuwa, ina gwanin wani ga nawa? Ina mai ƙaryata tsafi ya zo ya ga tushen wurin da ake gudanar da gundarin tsafi. Ka daɗe ka yi ƙarko da shekaru irin na dabina Bamagujena, ina ƙananan Bokaye da 'yan tsubbu ga shugabanku. Wa ya isa ya ja da kai yanzu a ga ƙarshen rayuwarsa! Na gaishe ka madogarata mai yaye mini damuwa da share mini hawaye." Mahafiyar Fulani Umaima ta ƙarasa kirarin tana zubewa a gabansa. Fuskarsa a murtuke babu ko ɗigon fara'a ya ɗago ya kafe Fulani Umaima da kallo. Tana shirin yi mata magana ya saka hannu ya ɗauke ta da matsanancin mari, a yadda yake idan ka ga Bamaguje sai ka rantse idan ya mari mutum ba zai yi wani tasiri ko zafi a jiki ba. Azabar marin ta sa Fulani Umaima ta kusa zubewa, kafin ta kai ƙasa ya sake ɗauke ta da wani marin. Hankali a matuƙar tashe Umaima da mahaifiyarta suka kafe Bamaguje da kallo, musamman Umaima da ta san laifin da ta aikata dangane da salwantar da littafin hannunta. Da sandar hannunsa ya nuna Umaima nan take ta tafi shuuuuu har ta dangana da bangon dutsen kogon, ya sake nuna ta da sandar hannunsa rai a ɓace nan take ta ƙame ƙam kamar dutse. A razane Mahaifiyarta ta ƙarasa gabansa cikin kuka ta dafa ƙafafuwansa, bai tanka mata ba sai da ya koma mazauninsa na ainihi sannan ya ɗago ya dube ta rai a ɓace. "Idan na so salwantar da rayuwar Umaima abu ne mai matuƙar sauƙi a wurina, amma tun a wancan karon sai na ɗaga mata ƙafa da ta sa na karya alƙawarin da na ɗauka a kan yarinyar da ta ce za ta kawo mini. Na kawar da kaina ne domin hannunka ba zai taɓa ruɓe ka yanke ba, amma a wannan gaɓar tura ta kai ni bango domin a kan na rasa littafin nan gara na rasa kowa da komai domin shi ne tsanin da zai kai ni ga cin nasarar da na sa a gaba. Don Allah wannan shi ne hukuncin da ya da ce da Umaima, a kan ɗanyan aikin da ta aikata mini. Kuma idan duk bokayan duniya za su haɗu domin su tashe ta ba za su taɓa iyawa ba, har sai na ga damar dawo da ita ainihin surarta. Umaima za ta zauna tamkar dutse a gabana, don haka ki tashi ki ba ni wuri." *SHU'UMAR MASARAUTA* *26* *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Cikin matsanancin mamaki Sulaiman ya dubi Fargi da ke tsaye a gabansa, mamakin kalamanta ya sa ya dube ta ya furta. "Ta wacce hanya kike ganin zan iya mulkar Masarautarmu bayan Shugaba ya nuna mini alamun rashin nasara?" "Sai an gwada a kan san na ƙwarai ɗan samari! Ya kamata ka dinga jarraba sa'arka a wurare mabambamta tun da an ce idan hagu ta ƙi sai a koma dama." Tsoro ya mamaye shi aƙ zuciyarsa yana tsoron kada dai yana gaban matsahiyar da yake jin ana faɗin tsafi da duk wani sihiri ba ya taɓa gagararta. Tamkar Fargi ta hangi abin da yake cikin zuciyarsa ta saki murmushi tana faɗin, "Kada ka tsorata domin zubin surar hallita da tauraronka ba na ragwayen mazaje ba ne. Kamar yadda zuciyarka take kokonta ka shaida mata, kana gaban Fargi 'yar matsafa jikar matsafa mai taƙama da alfarmar tsafi da sihiri." Da sauri Sulaiman ya ɗago ya dube ta, ta sakar masa murmushi sannan ta fara takawa a hankali. Da sauri ya sha gabanta a tsorace murya na rawa ya ce. "Tuba nake Shugaba da fatan dai ban aikata wani zunubin ba?" A karo na biyu ta sakar masa murmshi sai da ta ƙarasa ta kama tafin hannunsa ta ƙura masa, sannan ta dunƙule hannunta ta ɗora a saman hannunsa ta ɗan runtse idonta tana furta ɗalasiman tsafi. Duk yadda Sulaiman ya so ƙwacewa sai ya gagara don haka matsanancin tsoro ya sake mamaye shi, har sai da ya saki fitsari a tsaye saboda tashin hankalin abin da ka je ya zo. "Buɗe hannunka!" Fargi ta furta masa a taƙaice. Da sauri Sulaiman ya buɗe hannu sai ga wani farin rawani ya bayyana a tafin hannunsa, wata zabgegegiyar takobi ta bayyana a ciki da sauri ta taso tamkar za ta tsire idonsa har sai da Sulaiman ya ja da baya. "Ka ƙarasa masarautarku a yanzu haka Waziri da Shamaki na ƙulla yadda za su cutar da mahaifinku, idan ka je ka ɗebo wannan ƙasar ka watsa musu su da kansu za su tona asirin kansu." Fargi ta ƙarasa maganar tana miƙa masa wani ƙullin magani. Jiki na karkarwa Sulaiman ya miƙa hannu ya karɓa, ya shiga zabga mata godiya. Fargi ta sakar masa murmushi sannan ta buga ƙasa da ƙafarta nan take ta ɓace ɓat, ganin haka ya sa ruwan mamaki ya sake mamaye Sulaiman cikin ta'ajibi ya kaɗa linzamin dokinsa ya bar wurin. Duk abin da yake faruwa tsakanin Fargi da Sulaima a kan idanun shugaba, don haka gabansa ya yi mummunar faɗuwa haka kawai yake jin kusancin yaron a gare su babu alheri a ciki. A ƙallah ya shafe shakaru masu yawan gaske amma bai taɓa tsintar kansa a irin wannan yanayin ba, don haka ya sauke ajiyar zuciya ya ƙarasa bakin halwar tsafinsa ya binciki abin da zai faru tsakanin Fargi da Sulaiman a gaba. Hannuwa biyu a saman kanta cikin matsanancin tashin hankali ta faɗa cikin kogon tsafinsa, kuka take har da magina tamkar wacce aka yi wa bushara da wutar Jahannama. Boka Shaddas na zaune a kan wata halitta da ke tsugunne tana lasar wani baƙin jini da ke gabansa, da idanu yake bin Jakadiya har ta ƙarasa gabansa. Yaraf ta zube a ƙasa sannan ta sake fashewa da matsanancin kuka, har lokacin bai tanka mata ba sai ma idanu da yake bin ta da shi har sai da ta ci kukanta ta ƙoshi. "Ya kai babban boka mai yi mini yau ya yi mini gobe, ya Boka Shaddas mai share mini hawaye gani gare ka na zo ka ɗaura mini zanin da Umaima ta kwance mini a bakin kasuwa har jama'ar cikinta sun fara fuskantar rashin kyawun tsiraicin da ke tare da ni..." Tun daga farkon abin da Sailuba ta gaya masa game da halin da take ciki har zuwa ita kanta ɗoyin da ta ji Sailuba na yi ta kwashe ta sanar da shi, ta ƙarashe maganar tana fashewa da matsanancin kuka. Sai da ya lakace jinin da ke gabansa ya sha sannan ya furta. "Bakin alƙalami ya riga da ya bushe Jakadiya! Kin san a kance idan junanka sammako wani a tafe ya kwana, Umaima ta riga da ta cutar da Sailuba da cutar mai matuƙar yawa, tun da har aka binne gawar kishiyarsu bakin alƙalami ya riga da ya bushe, tun kafin ki zo na san abin da ya faru don haka bincikena ya zartar mini Sailuba ba za ta taɓa warkewa ba. Sai dai zan iya taimaka miki na yi miko hanyar Shugaba Zurufu da ke Dajin Bururu ko zai iya shawo kan matsalar ya magance miki ita. Amma ina mai tabbatar miki yadda Umaima ta kassara rayuwar kishiyarta sai ta ninka abin da ta yi shi a kan Sailuba, mafita ɗaya ce ko ki ɗauki fansa ko kuma ki nemi makamin kare kanki." Ajiyar zuciya Jakadiya ta sauke cike da damuwa ta furta, "Duk wacce za a yi a yi Boka Shaddas, ka taimaka mini ni da 'yata Sailuba muna cikin matsanancin tashin hankali." Jakadiya ta ƙarasa maganar tana dafa ƙafar Boka Shaddas. "Matso ki ji abin da zan faɗa miki!" Jiki na rawa Jakadiya ta matsa saitinsa nan take ta ji wani irin ɗoyi ya mamaye ta. Ya jima yana yi mata raɗa a kunne lokaci ɗaya Jakadiya ta bushe da wata irin dariyar ƙeta har da hawaye, ta jima tana abu ɗaya sannan ta furta. "Ka biyani ko ba sisi ubangidana, yadda ka ce haka za a yi a shirye nake ba ka haɗin kai matuƙar a kan Fulani Umaima ne domin ku kifar da jagorancinta." Sai da Boka Shaddas ya ɗauko wani mudubi ya sa a gabansa ya ƙura masa ido sannan ya furta, "Amma da sharaɗi Jakadiya domin a baya ina yi miki aiki ne saboda hannu ya san na gida, a yanzu kuma dole za ki rama wa kura aniyarta." Jakadiya ko kaɗan ba ta damu da abin da Boka Shaddas zai buƙata ba don haka kai tsaye ta furta. "Duk abin da kake buƙata a shirye nake na aiwatar maka da shi duk rintsi duk wahalarsa matuƙar zai biya mini buƙatata." Boka Shaddas ya saki murmushi a karo na biyu sannan ya sake yi wa Jakadiya raɗa a cikin kunne, a hargitse ta ɗago cikin tashin hankali tana kallonsa, ya gyaɗa mata kai cikin halin ko inkula. "Idan har kina buƙatar na yi miki jagora wurin Shugaba kuma na wanke ɓacin ran da Fulani ta dasa miki a zuciya sai kin aiwatar da abin da na sanar da ke, kuma ki san duk yadda za ki yi ki kawo mini duk abin da na buƙata cikin kogon tsafin nan." Nan take Jakadiya ta ji zuciyarta ta bushe ta dubi Boka Shaddas cike da ƙwarin gwiwa. "Na amince Shugaba zan an aiwatar da duk abin da kake buƙata." Boka Shaddas ya yi mata jinjina da hannu sannan ya ɗebo waɗansu garin magani da wata ƙyamurarriyar mage wacce kallo ɗaya za ka yi mata ka fahimci an tsaface ta ya damƙa mata. Jakadiya ta yi masa godiya sosai sanan ta yi masa sallama ta baro Kogon zuciyarta fes. Mahaifiyar Umaima ta tafi da gudu wurin da Umaima ke ƙame tana ambatar sunanta tana taɓa ta, tamkar dutse haka jikin Fulani Umaima ya koma ta ƙandare a wuri ɗaya ko ƙwayar idonta ba ta iya motsawa. Wannan ya sake ɗaga hankalin mahafiyarta don haka ta sake zubawa a guje ta nufi Bamaguje tana gunjin kuka. "Kai taimaka mini Bamaguje ka yi haƙuri duk da ban san laifin da Umaima ta yi maka ba, don Allah kada ka kashe mini ita Bamaguje..." Da sauri ya buga mata tsawa haɗe da katse ta. "Idan kika sake ambatar sunan Allah a wurin nan sai na halaki, taɓaɓɓu kamarmu ba sa ambatar sunan Allah a wurin taɓewa kamar nan." Gyaɗa masa kai ta fara yi har lokacin kuka take ta furta. "Tuba nake Bamaguje tsafi ya shiga lamarinmu, ka dubi girman tsafi Bamaguje ka kada ka kashe mini Umaima. Duk cikin 'ya'yana ita kaɗai na fi ƙauna a zuciyata." Murmushin takaici Bamaguje ya saki sannan ya furta, "Gara ke kina da su da yawa idan kin rasa ta akwai 'yan uwanta. Kin fi kowa sanin Umaima ita kaɗai ce 'yar da na mallaka a duniya kuma bayan ita ba zan sake samun haihuwa ba. Amma hakan ba zai hana na hallaka ta ba idan za ta kawo mini cikas a harkar bokancina, abin da ba ki sani ba hatta mahafina ni na datse numfashinsa na ƙarshe don haka babu wanda ba zan iya kawarwa a faɗin duniyar nan ba." Tsoro ƙarara ya bayyana a fuskar Mahafiyar Umaima, nan take gumi ya shiga keto mata. "Ka da ka mini haka Bamaguje, Umaima duk ba ta san wannan alaƙar da ke tsakaninku ba, ka yi haƙuri kada ka hallaka ta." Bamaguje bai tanka mata ba ya nuna wurin da Umaima ke ƙame ya nuna ta da sanda, take ta zube ƙasa yaraf cikin kururuwa da tashin hankali ta shiga kwalla ihun azaba. Da wata irin murya ya ambaci sunanta mai amsa-amo, nan take Fulani Umaima ta shiga nutsuwarta. A tsorace ta sake ja da baya don ba ƙaramin tsoron Bamaguje ne ya mamaye ta ba, jikinta na karkarwa hawaye na zuba ta matsa ta ci gaba da ja baya. "Ki zo nan! Idan ba haka ba ranki zai yi mummunan ɓaci." Tun bai rufe baki ba ta tafi da sauri ta zube a gabansa. "Ka yi mini rai, tuba nake Bamaguje wallahi ba zan sake..." "Dakata!" Bamaguje ya katse ta rai a matuƙar ɓace, ta sha ganin ɓacin ran Bamaguje da dama amma ba ta taɓa ganin irin ɓacin ransa na wannan ranar ba. "Kalli can." Ya furta mata yana nuna mata sihirtaccan bangon dutsensa. Daga mahaifiyar Umaima har ita rige-rigen kallon wurin suke, nan take hoton Jawahir ya bayyana a dadai lokacin da take ƙwaƙulo butar da Umaima ta binne har zuwa zuba ruwan da ta yi a sashenta. Sai da suka gama gani hoto mai motsin ya ɗauke. "Ba ta san kin binne ba, ba ta ganki a lokacin da kika binne ba hasali ma da ace wani ya ganki a lokacin sa kike gudanar da aiki, daga mutuwar kishiyarki har zuwa ɗoyin jikin Sailuba ba zai taɓa tabbata ba. Wace ce ita? Kuma wa ya sanar da ita wurin da kika binne har da yadda za ta gudanar da makarin aikin?" Bamaguje ya watsa wa Umaima tambayoyi fuska a haɗe. "Wallahi ban santa ba, ban san wa ya sanar da ita ba. Hasali ma ban taɓa saninta a cikin masarautarmu ba, ina tunanin ma ƙila Jakadiya ce za ta turo ta..." "Da ace Jakadiya ta san da wannan ba za ta nemi agajin kowa ba da kanta za ta tone ba tare da wani ya sani ba, kuma yarinyar nan na rayuwa a cikin masarautarku don haka ina buƙatar ki shiga lungu da saƙon masarautar ki kawo mini ita. Ina son sanin wace ce ita? Domin na tabbata banza ba ta kai zomo kasuwa, wannan asirin ba ita aka yi wa ba, ba ta da alaƙa da masarautar nan me zai sa ta tone asirin tun da ba amfani zai yi mata ba." Shiru Fulani Umaima ta yi tana nazari sannan ta furta. "Zan yi duk yadda ka ce Bamaguje." "Kina shashanci ɗanki Basiru ta ɗauke littafina ya kai wa mahaifinsa, ki sani wannan shi ne kuskure na farko da kika tafka a rayuwarki. Kin yi biyu-babu, domin butar da aka tone ita ce jigon mallakar da aka yi wa Sarki Abdul'aziz, kin rasa zuciyarsa kin rasa iko da mallakar da kike masa Umaima. Kin san a yanzu wacce nasara kaɗai ta rage miki?" Da sauri Fulani Umaima ta girgiza kai, nasararki ɗaya an binne kishiyarki da fatar da kika saka mata a ƙasanta wanda hakan zai sa har abada Sailuba ba za ta warke ba, amma bayan wannan ba na jin akwai wata ragowar wata nasara da kike da ita." "Kana nufin a yanzu Takawa zai iya juya mini baya?" Umaima ta tambaya cikin tashin hankali. "Ki rabu da maganar Takawa ki ji da annobar da kika haifo Umaima, kin fi kowa sanin rashin tausayi da ƙarfin zuciyata tun da na jimanta miki haihuwar ɗan bokan da kika yi kin san tsugunne ba ta ƙare miki ba. Basiri sai ya zame miki annobar da za ta nemi gagare miki domin mahafinsa ya jima da tsaface shi. Na san mahaifinsa Shaddas hatsabibin gaske ne kuma akwai wata 'yar jiƙaƙƙiyar tsattsamar alaƙa a tsakaninmu don haka babu wani abu da zan iya yi miki akai, ruwanki ne ki je wurinsa ku sasanta domin ya sakar miki ɗanki, ruwanki ne kuma ki bar masa shi gabaɗaya. Ku tashi ku ba ni wuri, Umaima sai na ji daga gare wato kawo mini yarinyar da za ki yi. Wataƙila na tausaya miki idan akwai wani taimakon da zan iya yi miki." Fulani Umaima har ta buɗe baki za ta yi magana Mahaifiyarta ta dakatar da ita, a sanyaye suka miƙe suka yi masa sallama sannan suka koma cikin masarautar zuciya babu daɗi. Mahaifiyar Umaima faɗa ta yi mata sosai cikin ɓacin rai, Fulani Umaima tana hawaye ta sanar da mhaifiyarta duk abin da ya faru tsakaninta da Basiru. Babban tashin hankalinta bai wuce yadda Bamaguje ya tabbatar mata ta zarginta a kan Basiru ba, don ta jima tana ɗora ayar tambaya a kan shi. "Kamalu shin ka ji zafin maganar da ta suɓuce daga bakinmu har ka nemi ƙaurace mana ne? Allah ya sani ba ni na haife ka ba Kamalu amma yadda nake jin A'iru haka nake jin ka a cikin zuciyata..." Da sauri Kamalu ya katse Baffajo. "Don Allah ka daina haka Baffajo, wallahi ba haka ba ne! Kuma daga yau ba na son ku sake kallona a matsayin wanda ba ku kuka haifa ba, da ku na rayu da ku na buɗe ido don haka ba ni da wasu iyayen bayanku. Na fahimci kowanne ɗan'adam da kalar tashi ƙaddarar Baffajo, wannan ita ce tawa ƙaddarar kuma ina godiya da Allah ya jefa ni hannunku. Wataƙila ma zamana a gabanku shi ne mafi alheri a rayuwata." Cike da jin daɗi Baffajo ya rungume Kamalu sannan suka ƙarasa wurin Inna wuro da ke cikin ɗaki cike da damuwa. Kwanan Mahaifiyarta ɗaya suka tattara suka koma masarautarsu, Fulani Umaima ta shiga cikin matsananciyar damuwa lokaci ɗaya ta fige ta rame waɗanda ba su san halinta ba har gani suke tamkar mutuwar Fulani babba ce ta buge ta. Sai da aka shafe kwana uku cif Fulani Umaima na shige da ficen son ganin ta gano wannan baiwar da Bamaguje ya ba ta umarni a kanta amma ko mai ɓurmushin kamarta ba ta gani. 'Yan uwan Fulani babba na matuƙar ba wa Abubkar kulawar da ta dace, a haka kwanaki suka shuɗe har aka yi addu'ar sadakar bakwai suka tattara gabaɗaya suka koma masarautarsu. Mahaifiyar Fulani babba ta so a ba su Abubakar ta tafi da shi, amma sai Takawa bai amince da hakan ba don a lokacin wata irin soyayyar Abubakar da sauran 'yan uwansa yake ji har cikin ransa. Kuma a wannan lokacin ne Sarki Abdul'aziz ya zartar da umarnin gabaɗaya Bayin Fulani babba na baya za su ci gaba da ba wa Abubakar kulawar da ta dace, Mai gado ba ƙaramin farinciki ta yi da jin haka ba. Don haka ita da Baiwa Zainaba suka ci gaba da ba shi kulawa kamar yadda suka yi wa Mahaifiyarsa alƙawari tun tana raye, kuma da yake ya saba da su sosai babu wata matsala da ake samu daga wurinsa. Duk yadda Muhsin ya so kawar da Jawahir daga zuciyarsa abin ya gagara, a ɓangare ɗaya kuma ga jinyar hannuwansa da yake yi don ma ƙonuwar ta fara warkewa. Ya sha tambayar kansa inda yarinyar take amma duk yadda ya kai ga yin bincike ya gagara gano ta, tun yana mu'amala da 'ya'yan bayi a tunaninsa za su gusar masa da sha'awarta har ya haƙura ya watsar. Idan tunaninta ya yi masa yawa har gani yake ko gamo ya yi da aljana bai sani ba take wahalar da rayuwarsa. A yadda yake jin ƙaunarta gani yake ko aljana ce zai iya zama da ita ko da kuwa zai koma cikin jinsin aljanu da zama. Sai da Sailuba ta gama sauraron Jakadiya ta share hawayenta cikin matsananciyar damuwa ta furta. "Yanzu Inna shi kenan haka zan dawwama cikin wannan warin? Ki duba ki ga irin korar karen da Takawa yake mini." Jakadiya ta ɗan juyar da kai ta tsartar da yawu saboda warin da ya bugo ta sannan ta furta. "Wannan matsalar za ta zo ƙarshe ki bar ɗaga hankalinki Sailubata, babban burina na cika wa Boka Shaddas alƙawarinsa. Yanzu bari mu fara da wannan kuliyar." Jakadiya ta zaro ƙyamusasshiyar Magen da Boka Shaddas ya bata, ta ɗorata a kan wani baƙin jini mai wari nan take Magen ta fara lasa jikinta na kammaninta suka fara rikiɗa suna sauyawa. Sannan ta fara ambatar sunan Fulani Umaima sau uku, tana gama ambatar sunan Fulani Umaima ta sunkuya daidai kan magen da kallon ƙwala-ƙwalan idanunta kan iya tsorata mai kallonta ta furta. "Maza ki dawwama kina ambatar sunan Umaima da muryar tsoratarwa, ki saka mata wasu-wasi a kan muryar marigayya Fulani babba. Maza ki tafi da izinin Boka Shaddas da sirrin tsafinsa." Rufe bakin Jakadiya babu wuya sai magen ta fice a guje ta bi ta saman katanga, kai tsaye ta wuce sashen Fulani Umaima, ta shige ɗakinta da shigarta babu jimawa ta ɓace daga kamar babu ita. Fulani Umaima na zaune ta zuba tagumi kamar a mafarki ta ji muryar Fulani babba tana faɗin, "Umaima kin cutar da ni." A firgice ta ɗago tana waige-waige cikin tashin hankali. *SHU'UMAR MASARAUTA* *27* *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Tun daga ranar da mahaifiyar Fulani Umaima ta sa ƙafarta ta bar masarautar ta duƙufa wurin ganin ta yi duk abin da za ta yi dangane da 'yar uwarta Fulani Asabe. Tun a lokacin ta so Bamaguje ya kashe yayartata amma sai hakan ya gagara sakamakon da ragowar kwanakinta a gaba, dalilin haka ya sa ya yi musu aikin rufin baki ta yadda Fulani Asabe da su Galadima ba za su ƙara maganar mulki ko rabuwar Umaima da Sarki Abdul'aziz ba. A haka rayuwa ta ci gaba da tafiya tsakanin Fulani Umaima da Fulani babba babu wani zama mara daɗi, sai dai tun da Umaima ta auri Takawa kyakkyawar alaƙar da ke tsakaninta da shi ta fara ja baya, don haka ba ta kawo komai a kanta ba tun da a yadda ta lura hatta mahaifinsa ya fara sauya masa ba ita kaɗai ba. Mahaifiyar Sarki Abdul'aziz ta rasu da watanni uku Sarki Usman, Fulani Rabi'atu da Fulani Asabe Allah ya yi musu rasuwa sakamakon hatsarin da ya afka musu a hanyar su ta zuwa gaisuwar mahaifin Fulani Rabi'atu da ke masarautar Nabaldu, wannan mutuwar ba ƙaramin faranta ran Umaima da mahaifiyarta ta yi ba don a yadda ta fahimta Marigayi Sarki Usman yana matuƙar son Fulani babba da 'ya'yanta. Kuma ta lura yana yawan yi wa Sarki Abdul'aziz kutse a cikin sha'anin mulki don haka bayan mutuwarsu ta ci gaba da cin karenta babu babbaka a cikin Masarautar Huddam. Jawahir har ta nufi sashensu na Bayi sai kuma ta yi turus tana tunanin abin yi don haka ta rasa yadda za ta haɗu da Kamalu, dabara ce ta faɗo mata da sauri ta saka ƙaramar butar a cikin mayafinta ta ɗaure ta tamau ta ɗaure mayafin a ƙugunta ta yadda ko ka kalle ta ba lalle ka fahimci da wani abin a jikinta ba. Kai tsaye ta nufi sashen Inna wuro tana ɗan kalle-kalle ko za ta gan shi amma ba ta ga Kamalu ba, don haka ta ƙarasa ɗakin Inna wuro ta same ta ta fito hannunta ɗauke da kayan wankin Kamalu. "Inna sannu da gida! Kamalu ba ya nan ne?" Turus Inna wuro ta yi mamakinta ya bayyana a fili don ta san Jawahir da Kamalu ko kaɗan ba sa jituwa tamkar mage da ɓera, ganin haka ya sa Jawahir ta ɗan sosa kai a kunyace. "Yawwa dama Bala ne ya aiko ni na duba masa shi ko yana nan, shi ya sa na tambaye ki Inna." Inna wuro ta saki murnushi ta ce. "Yawwa ko da na ji, shiga ciki yana ɗaki na ji dai ya ce fita zai yi." Inna wuro ta yi maganar tana wucewa, Jawahir sai da ta tabbatar da Inna wuro ta fita sannan ta kunto butar hannunta ta faɗa ɗakin a lokacin Kamalu ya shirya cikin kayansa na Bayi da alama wani wurin za shi. Ba ta tanka masa ba don haka kai tsaye ta miƙa masa, Kamalu na kai idanunsa kan butar ya ji wani irin yaaaammmmm kamar kiyashi na yi masa yawo a jiki. "Ta mece ce wannan?" "Idan ka karɓa za ka san ko ta mece ce." Jawahir ta furta masa a taƙaice tana bin sa da harara, ba don tana gudun mummunan hukuncin da matar nan ta mafarkinta ta ce za ta yi mata ba me zai kawo ta gaban Kamalu. Sai da ya saki guntun tsaki kamar ba zai karɓa ba sannan ya saka hannun hagu ya karɓa a yatsine. Jawahir tana miƙa masa ta juya ta fice, take jikinsa ya ɗauki karkarwa gumi ya shiga keto masa. Kansa ya ji ya yi masa nauyi dum kamar an ɗora masa dutse, don haka ya tsugunna ya sanya hannuwa biyu ya toshe kunnuwansa. Tamkar wanda ake hajijijiya da shi haka ya ga ɗakin yana juya masa, ya jima a cikin wannan yanayin sannan ya ji tamkar ana fisgarsa don haka ya fice daga cikin ɗakin har lokacin hannunsa ɗauke da butar. "Ka yi gaggawar zuwa ka ɗora ta a saman gidan tururuwar da ke kallon shurin uwar ɗakin Sarki Abdul'aziz." Kamalu ya ji an furta masa a cikin kunnuwansa. Cike da ƙwarin gwiwa ya damke butar, kai tsaye ya wuce sashen Sarki Abdul'aziz. Shugaba Zurufu ya jima a halwar tsafinsa yana bincike game da Sulaiman da Fargi, yayin da ya ci karo da wani ƙaton haske mamaye da duka tauraronsu. Duk yadda ya so gano ainihin mene ne sai ya gagara fahimtar komai, sai dai jikinsa yana ba shi akwai wani sabon al'amari da zai faru a nan gaba wanda yake ji ba zai zame masa alheri ba. "Fargi babu ke babu yi wa yaron nan aiki wannan umarni ne nake ba ki ba shawara ba, don haka kada ki ƙulla wata alaƙa da shi." Shugaba Zurufu ya furta wa Fargi a lokacin da ya kirata. "Saboda me Shugaba? Ina ganin aikinsa ba aiki ne mai wahala ba." Tun da Fargi ta zo duniya wannan ce maganar ja'in'ja ta farko da ta taɓa shiga tsakaninsu, don haka Shugaba Zurufu ya sake kafe ta da idanu yana yana nazartarta. Ganin haka ta sa Fargi ta nemi yafiya a wurinsa sannan ta nuna masa ba za ta sake shiga sabgar Sulaiman ba, amma a ƙasan zuciyarta ba ta jin za ta iya yanke alaƙarta da shi sakamakon baƙon yanayin da ya ratsa zuciyarta. Tun daga wannan ranar sai ya zamana Fargi ta yi takatsantsan wurin gudanar da mu'amala a tsakaninta da Sulaiman, tun suna mu'amala a matsayin zumunci har alaƙarsu ta fara rikiɗewa zuwa soyayya. Kuma duk wannan soyayyar suna gudanar da ita ne a masarautarsu Sulaiman a sirrance ba tare da wani ya sani ba, a duk lokacin da ta so ziyartarsa kai tsaye take rikiɗa zuwa siffar tantabara sai ta sauka a wurin shaƙatawarsa. Shi kuma Sulaiman yana ganinta yake shaidata don haka suka gina soyayyarsu mai ƙarfi ba tare da mutum ɗaya daga cikin zuri'arta sun fahimci haka ba. A duk lokacin da ta tuna babban zunubi ne wani daga cikin zuri'arsu ya ƙulla soyayya da wani jinsin da ba nasu ba, sai hankalinta ya kai matuƙar ƙolokuwar tashi fargabarta bai wuce kaca su kashe ta ita da Sulaiman ba su soke gawarsu a jikin bishiyar abar bauta. Duk da a kan idanunta Jakadiya ta aiwatar da abin da Boka Shaddas ya saka ta amma har lokacin babu walwala a tattare da ita. Duk yadda Jakadiya ta kai ga son lallashinta da ban baki tuni Sailuba ta yi nisan kiwon da ba ta jin kira. "Inna yau ita ce rana ta farko da na yi da-na-sanin aurena da Takawa, don Allah yanzu Inna wacce irin riba muka samu? Tun d aka yi auren nan babu kwanciyar hankali daga wannan sai wannan, tura da kai ni bango gaskiya zan je na nemi takardar saki a wurin Takawa idan ya so na samu Umaima ta karya duk wani kaidi da ta ƙulla mini kin ga na yarda ƙwallon mangwaro dole zan huta da ƙuda..." "Dakata mini sakarya mara sanin kishin kai." Jakadiya ta katse Sailuba a hassale. "Kina son ki zubar mini da ƙima a wurin Umaima ne? Wallahi idan kika aikata wannan ɗanyen rashin hankalin sai na tsine miki albarka, domin da ki watsa mini ƙasa a gaban Umaima gara ki watsa mini a idon duniya." Jin haka ya sa Sailuba ta sake fashewa da matsanancin kuka. Tashin hankalin Fulani Umaima ya sake ninkuwa sakamakon jin motsi a uwar ɗakinta, da sauri ta leƙa ciki amma babu kowa don haka ta koma ta zauna ta rafka uban tagumi. Babban abin da yake sake ci mata tuwo a ƙwarya bai wuce yadda a kullin kusancinta da Takawa yake sake nisanta ba, ta lura tun bayan rasuwar Fulani babba ba ya ta tata da kullin maganarsa tana kan Abubakar. A ɓangare ɗaya kuma ga ƙyama, da hantarar da yake yawan yi mata, ta lura hatta Sailuba da take ɗoyi tana zubar da ruwa mai wari ba ta fuskantar tsangwamar da take fuskanta a wurinsa, sai dai ita ma Sailuban ba wani shirin arziƙi suke yi ba don ta ji labarin ko zuwa sashen Takawa ta daina yi. Ita kanta ganin cin kashin ya yi yawa ya sa ta janye jikinta gefe har lokacin da za ta shawo kan matsalar gabaɗaya. "Me ya sa matsalolina suke rikitowa rayuwata a daidai gaɓar da na ci burin cin duniyata da tsinke tsire, a lokacin baya babban tunanin Fulani babba ce matsalata amma me ya sa bayan na kawar da ita sai matsaloli suke sake kunno mini kai?" "Saboda kowa ya sayi rariya ya san za ta zubda ruwa. Kuma duk wanda ya ce tukunyar wani ba za ta tafasa ba ta shi ko ɗumi ba za ta yi ba, ai tarin masifa da bala'in yanzu kila fara gani Umaima." Jakadiya ta katse Fulani Umaima rai a ɓace. "Wa ya kasa da ke ballantana ki ɗauka, don Allah Jakadiya ki je ki ji da matsalar gabanki. Kada ki yi la'akari da halin da nake ciki don kowa ya biya allonsa wankewa yake." Fulani Umaima ta ƙarasa maganar tana shigewa uwar ɗaki, don yadda zuciyarta take a dagule ba ta jin za ta iya biye wa Jakadiya. Jakadiya ta ja guntun tsaki sannan ta fice daga ɗakin. Tunanin Fulani Umaima kacokan ya tafi a kan yadda za ta kawo wa Bamaguje yarinyar da ya bata umarni, lokaci ɗaya ta saki shu'umin murmushi da wata shawara ta faɗo mata. Da sauri ta fita ta sa aka kira mata Uwar Bayi ta bata umarnin a tattara mata 'Bayi yara da manya domin a faɗarta za ta 'yanta yaran Bayi goma iyayensu biyar. Nan take babu jimawa Uwar Bayi ta tafi sashensu na Bayi ta sanar da saƙon Fulani Umaima, cike da murna Bayin suka fara tururuwa suna taruwa a babban filin harabar masarautar suna jiran fitowar Fulani Umaima kowa a zuciyarsa yana fatan Allah ya sa yana daga cikin masu rabon da za a 'yanta. Ɗaya bayan ɗaya haka Fulani Umaima ta sa aka diga wucewa da Bayi ko za ta yi tozali da ita amma ko mai kama da ita ba ta gani ba, don haka cikin yanke ƙauna ta zaɓi waɗanda suke da rabo a gurguje ta nufi sashenta don a wannan karon ta yanke shawarar zuwa wurin Bamaguje don ta gaji da jegon jakar da take yi babu dare babu rana ba tare da biyan buƙata ba. Tun bayan da Jawahir ta kai wa Kamalu butar hannunta ta wuce sashensu na Bayi haka kawai take jin tamkar ta sauke wani babban nauyin da yake kanta, a lokacin da ta koma Mai gado ba ta nan don haka ta ɗan sha ragowar kokon da ta rage sannan ta koma ta kwanta tana tunanin rayuwa. Duk yadda ta ji Bayin sashensu na tururwar zuwa wurin zaɓen da Fulani Umaima za ta yi haka kawai ta ji ba ta son zuwa, don ba ƙaramin tsanar matar ta yi ba, jin hayaniyar za ta takura mata ya sa ta sake ficewa daga ɗakin kai tsaye ta wuce kogin tsamiya ta zauna tana wasa da ruwa. Tun tana cikin damuwa har damuwar tata ta yaye sakamakon yadda ruwan yake rikiɗe mata yana wani irin tsiri kamar zai rufe ta sai kuma ya tafi da gudu ya sake dawowa, ta jima a bakin ruwan har sai da ta gaji don kanta sannan ta bar wurin. Har za ta koma sashensu na Bayi sai ta yanke shawarar zuwa ta gano halin da Abubakar yake ciki duk da ta san Mai gado ba za ta bar ta shiga wurinsa ba. Tamkar dirar mikiya haka Jawahir ta ci karo da shi a mararrabar ƙofofin da suke tsakanin sashen Fulani Umaima da Fulani babba, yadda ta ga ya yi saranda kamar mutum-mutum ne ya sa ita ma ta daskare cikin faɗuwar gaba. A wannan karon bai matso kusa da ita ba sai ma murmushi ya sakar mata, mamaki ne ƙarara ya bayyana a saman fuskarta. "Barka... da hutawa... ranka shi daɗe." Jawahir ta yi ƙarfin yin maganar muryarta na rawa. "Me ya sa kike jin tsorona?" Yarima Muhsin ya wurga mata tambaya a madadin ya amsa mata. "Amm... dama... dama... haƙuri zan baka..." Tun da ta fara magana ya kafe bakinta da kallo haka kawai ya ji ƙirjinsa na bugawa, sha'awa da soyayyarta na fisgarsa. "Laifin me kika yi mini da za ki ba ni haƙuri?" "Ƙila fa ya manta abin kika yi masa, indai kuwa ya manta ki rufa wa kanki asiri ki yi shiru." Zuciyarta ta raya mata. Tana shirin yin magana ta ji motsin tafiya a bayanta, wani irin turare mara daɗi ya bugi hancinta. Da sauri ta juya karaf idanuwanta suka sauka a kan Fulani Umaima da ke tafe fuska a haɗe Bayinta biyu na biye da ita a baya. "Keee! Ke idanuwana suke gani?" Fulani Umaima ta yi maganar cikin suɓutar baki sakamakon rashin tsammanin ganin Jawahir. Tsoron Jawahir ya ninku a ɓangare ɗaya kuma haushin Fulani Umaima ya turniƙe ta. Tamkar ba za ta gaida Fulani ba haka Jawahir ta zuba mata manyan idanunta, idan ba gizo idanun Fulani Umaima suke yi mata ba har gani ƙwayar idon Jawahir tana rikiɗe mata zuwa wata siffar daban. "Barka da hutawa ranki shi daɗe." Kalaman Jawahir suka daki majiyar sautin Fulani Umaima. Sai da Fulani Umaima ta waiga ta sallami Bayinta sannan ya juya wurin Jawahir tana shirin yin magana Yarima Muhsin ya katse ta. "Ammi dama kin santa ne?" "Ku biyo ni ciki yanzu-yanzu." Fulani Umaima ta furta, tana gama maganar ta shiga cikin gida. Rass! Gaban Jawahir ya faɗi don haka ta ji ba ta aminta da kiran da Fulani Umaima ta yi mata ba, tun da ta san babu wani abu da ya taɓa haɗa su ballanata ta ce ko wani kuskure ta yi mata. "Mu je ciki." Ta riski kalaman Yarima Muhsin cikin tattausan lafazi. Kamar kazar da ƙwai ya fashe wa a ciki haka Jawahir ta shiga sashen Fulani Umaima tana tafe tana ƙarewa sashen kallo, duk taku ɗaya idan ta yi haka take jin bugun ƙirjinta yana tsananta har suka shiga rumfar (Falo) Fulani Umaima. "Ammi ashe ke ma kin santa? Amma na jima ina wahalar da rayuwata." Yarima Muhsin ya yi maganar cike da shauƙin farinciki. "Wace ce ita?" Fulani Umaima ta tambaya shi fuska babu walwa, ta wurga wa Jawahir wani ƙasƙantaccan kallo cike da tsana. "Ita ce farincikin zuciyata da nake kwana nake ta shi da begenta, ita ce ta ja linzamin dokin zuciyata har nake jin babu sauran wata 'ya mace da za ta samu fada a wurina. Ita ɗin ta musamman ce zinariya ce, tauraruwa kuma hasken zuciya. Ammi wannan ita ce yarinyar da na faɗa tarkon ƙaunarta ba tare da na sani ba..." A zabure Fulani Umaima ta miƙe tsaye jikinta na karkarwa ta katse shi. "Wannan yarinyar?" Da wani irin sauri ya ji ƙafarsa na fisgarsa zuwa sashen Sarki Abdul'aziz, amma zuciyarsa na gargaɗin kada ya je ya aikata aikin da kan iya kai shi ga fuskantar mummunan hukunci. Amma kuma ya gagara sanin yadda zai dakatar da yanayin da yake ji don har jin sa yake tamkar yana tafiya a saman iska. A lokacin da ya ƙarasa sashen Sarki Abdul'aziz shiru wurin, da yake da alama babu Dogarawan ƙofa, daga can gefen sashen lambu ya hangi masu hidimar wurin suna gyara ƙananun shukokin da ke wurin dangin su: Karas, ɗata, salak da sauransu. Bai tsaya buga ƙofa ko neman izini ba kai tsaye ya faɗa turakar Sarki Abdul'aziz, a lokacin yana kwance da alama hutawa yake. Ganin Kamalu ya shiga ɗakin ya sa Sarki Abdul'aziz tashi zaune da sauri cike da mamaki. "Waye yake yunƙurin nuna mana rashin ɗa'a zai tako har makwancinmu muna hutawa. Bukar! Bukar!" Sarki Abdul'aziz ya kira shigaban Dogaran da ke kula da sashensa amma shiru babu amsa. Ganin Kamalu ya doshin uwar ɗakinsa ya sa Sarki Abdul'aziz ya rufa masa baya, Kamalu na shiga ɗakin ya ji kansa na juya masa. Taƙama da izzar mulki suka mamaye shi, cikin takun isa da ƙasaita ya tunkari daɗaɗɗan gidan tururuwar da ke kallon shurin cikin ɗaki ya ɗora butar a saman gidan tururwar. Daga gefensa ya ji an furta. "Yau Kamalu ne har cikin zuri'ata? Lallai da alama gaggarumin al'amari zai faru, sai dai ina jimamin da wannan ziyarar ba wurina ka kawo ta ba." Da mamaki Kamalu ya kalli Dattijo Maharaz ya furta. "Dattijo Maharaz kai nake gani." Kafin Dattijo Maharaz ya ba shi amsa Sarki Abdul'aziz ya ƙarasa bakin ƙofar ya furta. "Wane ne kai? Me ya kawo ka har cikin turakarmu kuma me kake yi a wurin nan?" *SHU'UMAR MASARAUTA* *28* *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Boka Shaddas na daga gefe ya zuba wa Basiru ido ganin yadda yake gudanar da alƙaluman tsafi, zuciyarsa ce ta yi fes farin ciki ya mamaye shi don ko a yanzu ya mutu ya san ya bar wa duniya magajinsa. A bakin wata ƙatuwar tukunyar ƙasa yake zaune ya ɗebo wasu turarrika ya zuba sannan ya ci gaba da surutai yana ambatar sunan A'ishatu, Nura, Bala da Nasiru, ta gefensa Boka Shaddas ya zaune ya yi masa jinjina da hannu. "Aikin matar jiya kake yi ne?" Sai da Basiru ya gama jero sunanyen baƙaƙen aljanun da ya tura waɗanda za su yi masa aiki sannan ya furta. "Aikin jiya na riga da na zartar da shi, a yanzu haka ina gudanar da aikin Hansatu wacce ta kawo aikin 'yayan mijinta da ta ce a haukatar da biyu, ɗaya kuma a zaunar da shi ta ƙarshen a saka mata baƙin jini. Shi kuma Uban na mallake mata shi, na tura musu aljani Zurgungu shi zai gama aiwatar da komai. Na yi masa tuwkwicin jinin jariri sabuwar haihuwa da baƙaƙen jakuna, bayan wannan ina tunanin na gama da aikina na yau." Murmushi Boka Shaddas ya yi ya dafa kafaɗar Basiru, "Fiye da haka na san za ka aikata domin ina ji a jikina sai ka fi ni gawurta da shahara a harkar tsafi da sihiri. Amma ba ka tunanin Mahaifiyarka za ta shiga damuwar rashin ganinka har tsawon waɗannan kwanakin ba ka leƙa wurinta ba?" Shiru Basiru ya yi kamar mai nazari sannan ya furta. "Zamana a wurin nan shi ya fi mini alfanu domin tun wankan tsafin da ka yi mini a duk lokacin da na kalle ta sha'awarta mamaye ni take yi, kuma na san ba za ta ba ni dama ba kuma idan na neme ta ta yi yunƙurin hana ni zan iya illatata ko ma na hallakata gabaɗaya. Babban burina ɗaya ne ya rage mini a duniya wanda ba tun yau ba nake mafarkin samu kuma nake haramar yunƙurin cim masa." "Wanne irin buri ne?" Boka Shaddas ya yi saurin tambayarsa. "Masarautar Huddam! Babban burina bai wuce na mallake ta ba ta dawo ƙarƙashin ikona, masarautar da ta gawurta da ƙasaitattun aljanu ita nake so ta rikiɗe zuwa Masarautar Matsafan da babu kamarta a faɗim duniya. Burin Mahaifiyata Muhsin ya gaji Takawa, ni kuma burina ka samu nasarar kammala karanta labarin Hidaya don ka samu nasarar da za ta kai ka gaba har ni ma na mulki nahiya da yankin da nake so." Ƙurrr Boka Shaddas ya yi wa Basiru yana auna kalamansa, bai tanka masa ba ya tashi ya je bakin wani rami ya fara motsa baki. Take littafin ya fara tutsowa daga ƙarƙashin ƙasa ya fito. Da mamaki Yarima Muhsin yake bin Fulani Umaima da kallo ganin yanayin da ta yi maganar. "Ammi wai me yake faruwa..." Tun bai rufe baki ba Fulani Umaima ta ɗauke fuskarsa da mari, tuni Jawahir ta matsa can jikin bango jiki na rawa. "Wai me yake damunki ne Ammi a kan me za ki mare ni don na gaya miki abin da yake cikin raina." Yarima Muhsin ya yi maganar a ƙufule tamkar zai rama marin da mahaifiyarsa ta yi masa. Fulani Umaima ta wurgawa Jawahir mugun kallo tana sake tuno tone butar da ta yi mata, wata irin zuciya ce ta ciyo ta don haka ta yi kukan kura za ta janyo Jawahir ganin haka ya sa Jawahir ta fita da gudu tana kwalla ihu cikin tashin hankali. "Me kike yi ne haka Ammi?" Muhsin ya furta cikin ƙaraji. "Wannan yarinyar annamimiya ce, maƙiyyarmu ce Muhsin ka fita daga harkar yarinyar nan..." "Ki furta mini komai amma ban da kalmar rabuwa don wallahi ko Takawa bai isa ya hana ni aurenta ba, ke kin auri wanda kike so don haka babu ruwanki da rayuwata ni ma ki bar ni na yi sabgar gabana kawai, duk wata damuwa matsalarki ce." Yarima Muhsin ya ƙarasa maganar yana ficewa daga ɗakin ya rufa wa Jawahir baya. "Da ace ka san matsayinsa da ba ka tsaya kana tambayarsa dalilin zuwansa wurin nan ba Sarki Abdul'aziz." Dattijo Maharaz ya yi maganar yana jingina da bango. A razane Sarki Abdul'aziz ya dubi wurin da yake jin muryar da ko a mafarki ya ji ta sai ya tantance ta. "Wane ne kai? Me ya sa kake son yaudarata da muryar Dattijon da nake matuƙar ganin girmansa da mutumtawa?" Murmushi Dattijo Maharaz ya sakar masa sannan ya furta. "Ba yaudara ba ce Sarki Abdul'aziz! Kuma ba gizo ƙwayar idanunka take yi maka ba, kana tare da Dattijo Maharaz, Dattijon da yake matuƙar farinciki da ganin irin girmamawar da zuri'ar aminsa suke masa." A take Sarki Abdul'aziz ya saki baki da hanci cikin tsananin mamaki domin wannan shi ne karo na farko da ya taɓa sanya ƙwayar idonsa a surar Dattijo Maharaz a zahiri duk da ya fito masa a cikin surar mutane, sakamakon tun yana ƙarami sai dai ya ji muryarsa a bakin shurin da ya buɗe ido da ganinsa a turakar mahaifinsa. "Ya aka yi aka haihu a ragaya Dattijo Maharaz? Me ya sa ba ka taɓa bayyana mini kanka ba sai yanzu?" Kafin Dattijo Maharaz ya ba wa Sarki Abdul'aziz amsa suka ji wani irin ƙas ƙas ƙas a daidai wurin da Kamalu ya ajiye butar, wata irin katantanwa ta fara yi sannan wani farin hayaƙi ya fara fita daga cikin gidan tururuwar. Nan take Kamalu ya fara fita daga hayyacinsa, a hankali ya fara takawa don ya ƙarasa kan gidan tururwar, da sauri Dattijo Maharaz ya sha gaban Kamalu hankali a tashe yana faɗin. "Kada ka yi mini haka Furhussam! Kada ka aiwatar da abin da zai zo daga baya ana da-na-sani." Dattijo Maharaz ya furta a ɗan razane. "Ka matsa daga gabana Maharaz, kada ka yi gangancin dawo da borno dawaki. Abin da ya faru ya riga da ya wuce don haka kowa ya yi harkar gabansa." Furhussam da yake magana ta jikin Kamalu ya furta yayin da Dattijo Maharaz ya sha gabansa. "A yarjejeniya da muka taɓa yi babu ɗaukar ɗaya hallita ɗaya daga cikin zuri'ar Masarautar nan." Faɗuwa ƙasa Kamalau ya yi, nan take wani gajeren mutum baƙi wuluk mai fafaɗar fuska, kansa ɗauke da wata hular ƙarfe ruwan zaiba ya ce. "Maharaz ba na tunanin akwai wani mahaluki da ya isa ya sa na gagara zartar da hukuncin da na yi niyya, ba tun yanzu ba ya rayu cikin kulawa da ikonmu. Don me zai sa bayan ya gama aiwatar da abin da muka jima muna buri ba zan ɗauke shi ba?" Gaban Sarki Abdul'aziz ya shiga bugawa. Ya dubi ɓangaren Dattijo Maharaz a ɗan rikice, "Me yake faruwa Dattijo Maharaz? Ina jin tsoron kada wani sabon al'amari ya faru da al'ummar cikin masarautata." "Wannan tsohuwar daɗaɗɗiyar gaba ce Sarki Abdul'aziz, wannan yaron kuma da kake gani makusancinka ne kuma makusancin wannan karagar da kake kai ne. Ban yi niyyar furta wannan maganar ba amma tun da na lura Furhussam bai riƙe alƙwarin da muka ɗauka ba zan fayyace maka komai amma sai yaron nan ya dawo hayyacinsa don na yi masa alƙawarin hakan." Dattjio Maharaz ya ƙarasa maganar yana matsawa gaban Kamalu da ke kwance jikinsa na wata irin karkarwa. "Idan haka ne ba mu kaɗai muka karya alƙawari ba amma tun da haka ne yau ko sama da ƙasa za ta haɗe sai na ɓatar da yaron nan daga cikin masarautar nan." Da sauri Dattijo Maharaz ya ɗago ya dube shi, yana shirin magana Sarki Abdul'aziz ya furta. "Dattijo Maharaz ka fi kowa sanin ni ba ma'abocin son hayaniya da tashin hankali ba ne, don Allah ka lamunce masa ya ɗauki yaron na tun da shi ma yana daga cikin jinsinku na aljanu." Murmushi Dattijo Maharaz ya yi sannan ya kalli Sarki Abdul'aziz da ke cikin matsananciyar damuwa. "Allah sarki Abdul'aziz! Tabbas na yarda rashin sani ya fi dare duhu, duk wannan cizawa da ake yi da ni saboda kai nake yin ta." Da mamaki Sarki Abdul'aziz ya ce. "Saboda ni kuma Dattijo Maharaz?" Dattijo Maharaz ya gyaɗa masa kai cike da ƙarfin gwiwa. "Wannan da kake gani sunansa Sarki Furhussam, ya kasance Sarki kuma Shugaban baƙaƙen aljanun doron ƙasa. Tun a dubban shekarun da suka gabata mun yi zaman maƙotaka da su ga gida ga gida amma bisa yanayin ɗabi'a da mu'amalarmu da ta sha bambam sai ya zamana mun fara zaman doya da manja. Ka san mene ne muhimmiyar gabar da ta gifta a tsakaninmu?" Dattijo Maharaz ya wurga wa Sarki Abdul'aziz tambaya. Girgiza masa kai ya yi sannan ya ci gaba da cewa. "Yara ne suka shiga tsakaninmu, ba iya ku kaɗai ba hatta jinsinmu faɗan yara ya kan yi tasiri har zuwa kan iyayensu idan ba a kai zuciya nesa ba. A dubban shekarun da suka gabata Shugaba Furhussam yana da wata hatsabibiyar yarinya marar jin magana da rashin ganin giraman manya mai suna Hullat, ba zan ɓoye maka ba; ba iya nan ta tsaya ba har 'yan sace-sace da haddasa faɗa tsakanin ma'auratan jinsinku take yi. A lokacin shi kuma ɗana na uku wato Umaru ya tasa sai ya zamana shi mai zafin zuciya ne ba ya ɗaukan raini. Ana cikin haka sai faɗa ya haɗa su har ta kai Umar ya yi mata jina-jina, a lokacin da ƙafata na taka har zuwa wurin Furhussam a kan musamu maslaha na ba shi haƙuri a sasanta yaran, amma fir sai ya ƙi saurarata. In taƙaice maka dai sai ma ya ɗauki gaba da ni ko magana na yi masa ba ya tanka mini, sannu a hankali sai na watsar da lamarinsa da iyalansa. Ashe wannan abin da ya shiga tsakanin Hullat da Umar ita tuni ta faɗa ƙaunarsa har ta taɓa samunsa ta sanar da shi, shi kuma ya yi mata korar kare. Tun daga ranar duk yarinyar da Umar zai gani ya ce yana so ba ta sake kwana a duniyar nan Hullat take hallaka ta, sai da ta kai ta kawo ko ganin Umaru 'yan matan cikin jinsinmu suka yi ba sa tsayawa. Lokaci ɗaya ya zama tamkar mujiya ko kiran sunansa ba a son yi, daga ƙarshe da na yi bincike ma zurfi sai na gano da sa hannun Hullat a ciki. A ranar da na sanar da Umaru a ranar kuma kusan sai da samari goma suka kwanta dama a cikin zuri'ar Furhussam, a ciki kuwa har da yayan Hullat wanda shi ne babban ɗan Sarki Furhussam ɗin. Wannan rashin ne ya harzuƙa Furhussam ya shiga taya 'yarsa kisan zuri'ata, ganin haka ya sa matasan cikinmu suka mara wa Umar ɗan wurina baya aka yi ta ɗauki ba daɗi. Abu kamar wasa ƙaramar magana sai ta zama babba, tun ina ɗaukan faɗan a matsayin na wasa har abu sai da ya kai mu ga gagarumin yaƙi. Bayan da ƙurar yaƙin ta lafa kowannenmu sai da ya rasa wani tsagi daga ɓangarensa, sai Malam Habu limamin cikinmu da shi da Shugaban da ke koyar da su Furhussam na su addinin na bautar ruwa suka haɗu aka tsayar da matsaya cikin maslaha. Shugabanninmu ne suka tsayar da matsayar kowannenmu kada ya kuskura ya shiga sabgar waninmu, ko azabartar da waninmu ko kuma ɗaukan waninmu ba tare da haƙƙinsa ba. Sakamakon mu muna daga cikin jinsin fararen aljanun doron ƙasa, shi kuma Furhussam yana daga cikin jinsin baƙaƙen aljanun doron ƙasa. Daga ƙarshe ma sai suka yi ƙaura daga cikin mu sai dai lokaci-lokaci sukan dawo mahallansu su kwana biyu su ƙara gaba." Ajiyar zuciya Sarki Abdul'azi ya sauke, Dattijo Maharaz ya ci gaba da cewa. "Dubi can Abdul'aziz." Da sauri Takawa ya kalli wurin da Dattijo maharaz yake nuna masa. "Wannan tafkeken gidan tururuwar da kake gani shi ne ainihin muhallinsu, shi ya sa sai a kusa shekara ba ka ga giftawar turuwa ta fito ko ƙwaya ɗaya ba. Idan ban manta ba ka taɓa yi mini ƙorafi a lokacin da turuwa ta addabe ku na ce maka wannan ba hurumina ba ne. Wannan shurin da kake gani shi ne ɓangarena da zuri'ata da muke rayuwa cikin aminci, sai kuma idan mun yi sha'awa ko iyalanmu mata idan za su yi aiki suka fita cikin jinsinku ba tare da ku kuna ganinsu ba. Fulani Umaima ta yunƙura da sauri da niyyar ɗauko ƙahonta don ziyartar Bamaguje, ta ji wani irin ɗauuuu a ƙasanta tamkar zai zazzago, da sauri ta koma ta zauna tana runtse ido cikin azaba. Jin abin na sake tunkuɗo mata ya sa ta kai hannu da sauri nan take ta ci karo da wani mulmulallan abu ya tokare ta tamkar kan ɗa ne zai fito. A galabaice ta fara yarfe gumi ta leƙa don ganin baƙon yanayin masifar da rufto cikin rayuwarta babu tsammani, tashin hankalinta ya nunku sakamakon cin karo da ta yi da wata mulmulalliyar baƙar tsoka ta tokare ta, sannu a hankali wasu baƙaƙen tsutsotsi suka fara faɗowa ɗaya bayan ɗaya. Da rarrafe da jan gwiwa ta fara ja har ta ƙarasa da ƙyar ta iya ɗauko ƙahon ta busa don ƙarasawa wurin Bamaguje ko ya magance mata damuwa da al'amuranta. "Faɗuwa ta yi daidai da zama Umaima! Yanzu nake shirin ɗauko ki sai kuma aka yi katari gaki kin kawo kanki!" Kuka ta fashe masa da shi, a wannan karon duk wata al'ada da take yi ta ziyartarsa ba ta tsaya ta aiwatar ba saboda azaba. "Ka taimaka mini Bamaguje ka dubi halin da nake ciki." "Ki saurara mini Umaima don yanzu haka a kan hanya nake, dama na yi niyyar ɗauko ki ne domin na kai ki dajin Bururu wurin Tsoho kuma Shugaba Zurufu. Shi zai yi mini iso wurin gawurtattun Baƙaƙen al'aljanu domin na samu nasarar dawo da littafina da ke hannun Shaddas, sharaɗi ne ya gindaya mini a kan tilas ne sai na zo da ke domin ke ce mahaifiyar Basiru akwai tambayoyin da zai gudnar miki." Take cikin Fulani Umaima ya ɗuru ruwa, tana shirin yin magana Bamaguje ya dafa kanta nan take suka ɓace, sai ga su a cikin kogon dutsen Shugaba Zurufu da har wannan lokacin shi yake shugabantar Al'ummar mutanen Rumzu. Saboda matsanancin gudun da Jawahir take yi ko kallon gabanta ba ta iya yi, babban burinta bai wuce ta ganta a sashensu na Bayi ba ko don ta ceci kanta. Bayan fitowar Muhsin da sauri ya rufa mata baya, duk inda suka wuce ban da idanu babu abin da ake zura musu wasu kuwa tuni suka fara tsegungumi. Mafi yawa daga cikinsu tsammanin da suke yi Jawahir ta yi wa Muhsin babban laifin don haka yake bin ta zai hukuntata. Kafin wani lokaci tuni Bayi suka ci gaba da kacalcala maganar, masu ƙarfin halin ciki suka rufa wa Muhsin baya don gano ƙwal uwar dakan abin da zai faru. Da matsanancin gudu ta faɗa ɗakinsu kai tsaye kan gado ta haye jikinta ban da karkarwa babu abin da yake yi, a bakin ƙofar ɗakin ya tsaya yana ƙare mata kallo nan take ya ji tausayinta ya kama shi. A hankali ya fara takawa har zuwa bakin gadon, jin motsinsa ya sa Jawahir ta ɗago ƙirjinta na bugawa. Kafe ta ya yi da kallo don sura da ƙirarta ba ƙaramin fisgar hankalinsa suke ba, hannunsa ya kai kan fuskarta yana shirin yin magana ya ji wani irin ɗaaauuu tamkar wutar lantarki ta ja shi. Yarfe hannu ya shiga yi yana kai ƙwayar idonsa ya ga ɗan yatsan da ya taɓa ta ya yi baƙi wuluk. "Ki yi haƙuri a kan abin da mahaifiyata ta yi miki." Muhsin ya furta a sanyaye sannan ya juya ya fice daga ɗakin. "Kamar yadda Maharaz ya sanar da kai sunana Furhussam, ina fatan za ka kasance mai adalci a gare mu bayan sauraron kowanne ɓangaren. Wannan yaron tun a ranar da ya zo duniya rainonsa cakokam ya dawo hannuna da iyalina, idan ban manta ba kusan kimanin shekara ashirin da ɗoriya kenan. Wata rana da doshin asuba wata yarinyar ta dire shi a kujerar da na damƙawa babbar jikata ta wurin 'yata da na fi so a duniya wato Hullat. Tun lokacin da Hullat take da cikin yarinyar na yi mata alƙwarin mallaka mata ragama da shugabancin da na ke kai, kwatsam a daidai gaɓar da na tashi domin a ɗora jaririyar sabuwar haihuwar sai kuma na riski Kamalu a lokacin da yake jariri a kwance ko ɗigon sutura babu ajikinsa. A ƙa'idar masarauta da kujerar mulkin da nake kai ba kowanne jariri ne ake ɗora shi a kujerar ta yi daidai da shi ba sai mai tsananin rabo, sau tari wasu jariran ma ana ɗora su suke mutuwa ko su kamu da matsananciyar jinya. Kuma matuƙar ka hau kanta ka zama jagora mai aiwatar da duk wani hukuncin da ya dace, a lokacin da haka ta faru na ji baƙinciki sosai har sai da na ji tamkar na kashe Jaririn amma sai na fasa, a kan dole na naɗa masa kambu a kansa wanda a zahirin Baffajon da ya tsince shi ya ga zagayayyan jini da tururwa a goshinsa. 'Yata Hullat da kanta ta ba ni shawarar na ɗaura wa Kamalu da Fartuhmu aure, saboda yadda kyakkyawar surarsa ta birge ta don haka take fatan yarta ta aure shi. Ba zan ɓoye maka ba a siffar hallita da ƙira nesa ba kusa ba jinsinku na mutane sun fi mu kyau, dalilin haka yake sa muke auren matayenku da dama don ko ni ina da matan bil'adama sun kai goma. Ta farko na aure ta ne silar rashin wankan tsarkin da ba ta yi yadda ya kamata sakamakon na taɓa wucewa na ji Malam Liman yana yi wa su Dattijo nasiha a kan kyautata wankan jinin al'ada da na haihuwa kai har ma da wankan najasa. Ta biyun na aure ta ne saboda yadda nake ganin tana wanka a banɗaki babu addu'a sai surarta ta matuƙar jan hankalina, kuma har yau ta gagara samun mijin aure kai duk wani haske da taurarinta na dasashe su ko saurayo ba ta yi. Ta ukun kuma na aure ta ne saboda kwanciya baccin dare da take yi babu addu'a kai babu ɗankwali ita kuma na bar ta ta yi auren amma kuma haihuwa ce na ƙi barinta ta yi sai yawan ɓari da nake saka ta. Kasan dalili Abdul'aziz?" Cike zaƙuwa Sarki Abdul'aziz ya furta. "Sai ka faɗa Sarki Furhussam." *SHU'UMAR MASARAUTA* *29* *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Murmushi Basiru ya saki sakamakon gano sirrin yadda mahaifinsa ya ɓoye littafin da yadda ake fito da shi. Sai kuma yadda shi kansa a nan gaba ba zai sha wahalar sace shi a ruwan sanyi ba, Boka Shaddas ya ɗauko littafin ya koma kusa da Basiru ya zauna. "Ina matuƙar ƙaunarka Shaddas babban burina bai wuce na ga ka zama gawurtaccan bokan da har duniya ta tashi ba za a taɓa mantawa da shi ba, zan mallaka maka duka ƙarfin tsafina domin kai kaɗai ne jinina da ke yawo a doron ƙasa." "Na ji daɗin wannan sadaukarwar taka mahaifina Boka Bawa, tukwicin da zan yi maka bai wuce na hallaka ka ba domin amfaninka ya ƙare a wurina. Tun ban kai shekara goma ba nake saka ido don na gano sirrin da zan kwashe duka sirrin tsafinka, amma sai yau hakan ta kasance. Ina yi maka kyakkayawan fata da kwanciya mai kyau a rayuwarka ta barzahu." Kalaman Boka Shaddas da na mahaifinsa na baya suka dawo cikin kunnuwansa tamkar a lokacin suke tattauna su, a gaɓar da mahaifinsa ya mallaka masa ƙarfin tsafinsa shi kuma ya hallaka shi. Shi kansa yana son mallaka wa Basiru halwar tsafinsa amma yana tsoron kada nan take Basirun ya hallaka shi, murmushi ya sakar wa Basiru suna haɗa ido ya furta. "Ban taɓa sanin haka ɗa yake da daɗi ba sai yanzu da na mallake ka, kafin kai na mallaki 'ya'ya biyu amma ban taɓa jin ƙaunarsu kamar kai ba. Basiru ya sakar masa murmushi sannan ya furta. "Da sannu zan ɗauke littafin nan na hallakaka domin na mallaki duk wata ɗaukaka da ke taƙama da ita." Basiru ya raya a zuciyarsa amma a fili sai ya furta. "Ba na ganin amfanin karanta wannan labarin, me zai hana mu je kai tsaye da aiwatar da abin da ya kamata." Basiru ya ƙarasa maganar yana zura wa Mahaifinsa daƙwa-daƙwan idanunsa. "Tabbas har yanzu da sauranka a halwar tsafi Basiru, babban amfaninsa ga duk wanda ya ƙwallafa rai a kansa dole ne ya karanta labarin nan. Kada ka zama mai gaggawa a harkar tsafi da sihiri domin ba zai taɓa haifar maka da ɗa mai ido ba, kada ka nemi shahara da ɗaukaka idan har ba ka zama gwani a harkar ba." Basiru ya sake zuba wa Boka Shaddas na mujiya yana wani nazari daban, Boka Shaddas bai sake magana ba ya buɗo wurin da ya tsaya duk da shi kansa ba daɗin jin karatunsa yake ba, tun da ba daga farko ya fara karantawa ba amma babu yadda ya iya tun da idan ya ce zai karanta daga farko zai matuƙar ɓata lokaci. Sarki Hafiz shiru ya yi yana kallona da alama tambayoyina ne suka yi yunƙurin daskarar da shi, ya ɗan ɗauki lokaci a haka sannan ya furta mini. "Gabaɗaya ban san ta yadda aka haihu a ragaya ba amma idan kika bi ni a sannu zan warware miki zare da abawa, abu ɗaya na sani mahaifiyarki ta sha wuya matuƙa kuma ta galabaita. Soyayya ta yi tasiri a rayuwarta kuma ita ce tsanin da ta kai ta ga halin da ta tsinci kanta a ciki." Ajiyar zuciya na sauke a fili cike da jinjina kai cike da damuwa, haka kawai na ji takaicin Aljanin da ya ƙulla soyayya da mahaifiyata. "Tun ranar da aka ɗaura auren mahaifinki da mahaifiyarki suka fara fuskantar matsaloli ta ɓangarori da dama, domin a labarin da kakana ya bani ya ce shi ɗan autan Darri ne yake saka mahaifiyarki yin abubuwa da dama ba tare da ta sani ba. Kuma tsananin soyayyar da mahaifinki yake yi mata ya sa duk wani cin kashi da mahaifiyarki za ta yi masa ba ya yin fushi ko ya ɗauki mataki. Sun shafe shekaru da dama a cikin zaman doya da manja ba tare da wata kyakkyawar alaƙa a tsakaninsu ba, kuma a wannan lokacin aka naɗa wa mahaifinki saraurar Masarautar nan bayan rasuwar Mahaifinsa. Da yin bikin naɗin Mahaifinki ko wata guda ba a rufa ba ya yi murabus ya damƙa wa mahaifiyarki ragamar mulkin gabaɗaya, a wannan lokacin ne mahaifiyarki ta kafa tarihi domin ita ce mace ta farko da ta fara zama Sarauniya a masarautar nan. A wannan lokacin sai mahaifinki ya samu kan mahaifiyarki har ta ɗan fara ba shi kulawa, dalilin haka ya sa ya sake sakankancewa a soyayyarta. Kwatsan sai aka wayi gari mahaifiyarki ta samu ciki, tun da ta samu ciki yake wahalar da ita ƙarshe sai ɓarinsa ta yi. Kakana ya ba ni labarin tun daga wannan lokacin sai ciki ya ƙi zama a jikin mahaifiyarki, ashe abin da ba a sani ba a bayan fage Ɗan auran Darri ne yake ɓarar da cikin a duk lokacin da ta same shi. Tafiya ta ci gaba da tafiya har mahaifiyarki ta sake komawa 'yar gidan jiya sakamakon ashe a ɓoye ɗan autan Darri ne yake kanainaye ta da daɗaɗan kalamai har ya yi nasara a kanta, kwatsam babu zato sai aka wayi gari Mahaifiyarki ta yi murabus daga kan karagarta ta damƙa masa. A wannan lokacin an ce ran mahaifinki ba ƙaramin ɓaci ya yi ba har sai da ya ƙaurace mata na tsawon makwanni, ita kuma abin da Mahaifiyarki ba ta sani ba ɗan autan Darri yana mata fadanci ne domin ya ƙarɓo wa masoyayiyarsa karagar masarautar nan ne. Kin san wace ce Masoyiyar ɗan autan darri?" Na riski tambayar Sarki Hafiz a tsakar kaina. Yadda Basiru ya yunƙura da sauro zai wafce littafin ne ya sa Boka Shaddas ya yi saurin rufe shi, da mamaki yake bin Basiru da kallo cikin wayancewa ya furta. "Ya kai babban boka mai taƙama da tsafi da sihiri. Ni fa na ƙagauta mu kai ƙarshen labarin nan, don haka nake son karɓa na ƙarasa shi ko ma cim ma abin da muka sa a gaba." Ajiyar zuciya Boka Shaddas ya yi a karo na farko da ya ji ya ɗora zarginsa a kan Basiru, don haka bai tanka masa ba sai da tashi ya ƙarasa can wurin da ya ɗauko littafin ya mayar da shi cikin ƙarƙashin ƙasa, sannan ya koma gefen Basiru ya zauna. Sai da Furhussam ya saki murmushi sannan ya furta, "Saboda ba zan juri ganin tana ba wa 'ya'yan da ba nawa ba kula, don a lokacin kusan haihuwata uku da ita." Jinjina kai Sarki Abdul'aziz ya yi cike da tsananin mamaki. Ya riski Furhussam ya ci gaba da cewa. "Tun yaron nan yana tsumma muke kula da al'amuran rayuwarsa, kai hatta addinin da yake kai ba don son raina yake yi ba sai don babu yadda zan yi ne. A shekarun baya na so na ɗauke hankalinsa zuwa ga addininmu na bautar ruwa, sai Hullat ta gargaɗe ni da na ƙyale shi ya yi addinin da yake so don ko kaɗan ba ta son abin da zai takura wa Kamalu. Cikin haka yake rayuwa kuma duk shekara ina ɗaukarsa na sake gabatar da shi ga zuri'ata a matsayinsa na mamamallakin karaga kuma mijin mafi soyuwar jikata, sai dai nakan jefa masa wasu-wasu har na ya dinga ganin abin kamar ya faru kamar kuma bai faru a gaske ba. Akwai lokaci da dama da matar ubansa take nufarsa da miyagun abubuwa da kaina nake karya shi ko na dakatar da shi, kuma ina mata wannan kawaicin ne saboda kusancina da mahaifinta amma da tuni na hallaka ta. Girmansa da nake gani ne ya sa ko zancan hakan ban taɓa yi masa ba, har dai ta haƙura ta watsar da komai. A yanzu haka zancan da nake yi maka saura watanni uku cif-cif mu yi shagalin bikin tariyarsu, don haka na ci alwashin matuƙar ina raye babu yaron nan babu auren wata hallita bayan jikata. Sannan wannan butar da ya zo ya ajiye ka san ta mece ce?" Tun Furhussam bai ambaci sunan Sarki Abdul'aziz ba ya girgiza masa kai, sannan Furhussam ya ci gaba da cewa. "Wannan sihirtacciyar butar a ƙallah ta shafe sama da shekara dubu biyar, kuma an tono ta ne daga ƙarƙashin ƙasar Rumi da ke fadar Sarki ɓaƙaƙen aljanun ƙarƙashin duwatsu. Haƙiƙa Kamalu ya ɗora ƙwarya a gurbinta, domin alwashi ne ga magabatanmu a kan wannan butar ga duk wanda ya dawo da ita duk abin da ya yi niyya dangane da buƙatar ransa nan take za a zartar masa da ita. Amma na yi mamakin dalilin da ya sa Fargi ba ta aiko ɗiyarta ta zartar da wannan aikin ba." Da mamaki Sarki Abdul'aziz ya furta. "Shin dama wata ce ta turo shi? Wace ce ce ita?" "Ba faɗar labarinta ne ya kawo ni ba Sarki Abdul'aziz, ka bari idan na zartar da abin da yake gabana zan iya feɗe maka biri har wutsiyarsa." Fursussam ya furta cike sa ƙagauta. "Sarki Abdul'aziz ina son ka ƙare wa yaron nan kallo tun daga yatsun ƙafarsa har zuwa tsakiyar kansa." Dattijo Maharaz ya furta yana harɗe hannuwansa biyu a ƙirji. Lokaci na farko kenan da ƙirjin Sarkin Abdul'aziz ya buga a daidai lokacin da ya sauke ƙwayar idonsa a saman yatsun Kamalu da ke ɗauke da cindo irin nasa, ya ci gaba da kallonsa har zuwa saman yatsun hannuwansa da ba su da maraba da na jikinsa. Tarin tunaninnika suka rikito wa kwanyarsa, don haka ya ɗago da mamaki yana shirin wurga wa Dattijo Maharaz tambaya ya katse shi. "Wannan yaron makusancinka ne, magajinka ne kuma shi ɗin jininka ne." Mamakin Sarki Abdul'aziz ya ninku a sanyaye ya ce. "Ban gane ba Dattijo Maharaz." "Ina nufin wannan yaron Kamalu da muke dambarwa a kansa ɗanka ne na cikinka halak-malak, kuma babu ko tantama ko a yanzu zai iya hayewa saman karagarka." Cikin shammata Furhussam ya ɗauki Kamalu ya bigi bangon ɗakin nan take ya ɓace da shi, hankalin Dattijo Maharaz ba ƙaramin tashi ya yi ba. A gaggauce ya dubi Sarki Abdul'aziz ya furta, "Kada ka furta wannan maganar ga kowa har sai na dawo gare ka." Daga haka shi ma Dattijo Maharz ya ɓace daga wurin. Bamaguje shi da Fulani Umaima ba su sauka a ko'ina ba sai a kogon dutsen tsafin Shugaba Zurufu, yana rakaɓe a jikin bango ya tsufa tukuf don har ya fi Bamaguje tsufa nesa ba kusa ba. Kallo ɗaya idan ka yi masa ba za ka taɓa tsammanin zai iya motsi ba ballantaba ya iya aiwatar da wani mugun abu. Ƙurrr ya yi wa Fulani Umaima da ke rakaɓe a gefe tana zare idanu cikin tashin hankali. "A wacce rana kika haifi Basiru?" Shugaba Zurufu ya wurga mata tambaya yana kafe ta da shanyayyun idanunsa. "Wallahi na manta ba zan iya tunawa ba." "Kin haifi asara! Domin kin ɗebo ruwan dafa kanki Umaima. Yanzu dai ina son ki ɗebo mini gashin kansa, ki kuma ki ɗebo mini sawun ƙafarsa. Kuma zan ba ki asirin da zai taimaka miki wanda da za ki kawo mini wannan Yarinyar da ƙafafuwanta har cikin kogon tsafina, domin na yi binciken abin da Bamaguje zai bincika a kanta." Tun bai gama maganar ba gaban Fulani Umaima yake faɗuwa, don yadda take shakkar Basiru ko Takawa ba ta tsoronsa haka. Za ta yi magana ta ji wannan abin ya sake tunkuɗo mata cikin azaba ta zuba ihu tana rirriƙe Bamaguje, a hankali ta ji ya fara lafa mata sai ga wani ruwa tamkar na mugunya yana gangarowa daga ƙasanta. A dudduƙe haka Shugaba Zurufu ya tako a hankali har ya ƙarasa gabanta ya tsugunna, kuka Fulani Umaima ta fashe da shi ta dubi Bamaguje. "Bamaguje ka shiga lamurana ka duba halin da nake ciki." Wannan karon a fili ya nuna tausayinta don haka ya sunkuyar da kansa ƙasa. "Har a kullin ina faɗa miki hannunka ba ya taɓa ruɓewa ka yanke ka wurgar, tun a ranar da kika ziyarce ni na fuskanci matsalarki Umaima. Sai dai kash! Har kawo yau na gagara samun mafitar ciwon da yake tattare da ke, bayan wancan dalilin na littafin labarin Hidaya dama na ci alwashin kawo ki wurin Shugaba domin ya taimaka miki." Shugaba zurufu ya ɗauki wata tsumburarriyar mujiya ya ɗora a ƙasan Fulani Umaima nan take ta fara tsotsa tamkar wacce take cin abinci. "Ka yi alfahari da tsafi da sihiri Bamaguje tabbas za ta warke, da a ce wannan mujiyar ba ta sha gurɓataccan ruwan nan ba da ba za ta taɓa warkewa ba." Daga Bamaguje har Fulani Umaima rige-rigen sauke ajiyar zuciya suka yi, Bamaguje na shirin sake yin magana Shugaba ya katse shi. "Sai dai ba zan aiwatar da aikinta ba har sai na kammala sauran waɗanda muka saka a gaba, yanzu dai ta tabbata ta cika alƙawarin da ta ɗaukar mana na kawo gashin jikin Basiru da yarinyar nan." Da sauri Fulani Umaima ta hau gyaɗa kai sannan Shugaba ya ɗebo tarin magunguna da kayan tsubbace-tsubbace ya damƙa mata haɗe da sallamarsu. Suna isa tsibirin Bamaguje Fulani Umaima ta dube shi cikin damuwa, sannan ta zayyane masa abin da yake tsakanin Yarima Muhsin da Jawahir. Sai da ya yi shiru kamar ba zai amsa ba sannan ya ƙyaƙyace da dariya ya furta. "Kada ki damu da wannan Umaima, ki zuba idanu domin Shugaba Zurufu hatsabibin mutum ne. Tun da kika ji na jinjina wa zalinci da tsantsar mugun aikinsa kin san ba zan yi mana zaɓen tumun dare ba." Jiki a sanyaye Fulani Umaima ta gyaɗa masa kai, ta miƙe cikin hawaye don duk lokacin da wannan naman hallitar ya tunkuɗo mata ji take tamkar ranta zai fita. Fulani Umaima har ta fara tafiya Bamaguje ya ce. "Umaima!" Yanayin yadda ya yi maganar ya sa ta tsaya cak, sannan ta waigo tana share hawaye. "Ina son sanar da ke wata muhimmiyar magana amma ina tunanin ma'aunin da za ki jinginata, amma zan taushi zuciya har zuwa bayan warwarar matsalolin da kike ciki domin ranar wanka ba a ɓoyon cibi." A wannan karon ma sake jinjina kanta ta yi don haka ta ci gaba da tafiya har ta koma cikin masarautar Huddam. Har Yarima Muhsin ya jima da fita Jawahir ba ta iya tashi zaune ba, sai can bayan wani lokaci tana kwance a ƙuryar gado ta ji an ɗaga labulen ɗakin. Uwar soro ce ta saki murmushi sannanta ce. "Jawahiru wato yau kin tsokano wutsiyar ɗan autan dodo ko? Wallahi sai kin yaba wa aya zaƙinta." Daga haka ta fice daga ɗakin tana sakin murmushin mugunta. "Ina tsananin ƙaunarki! Saboda ke farincikina ce." Raɗau kalaman Muhsin suka dawo cikin kwanyarta, take ƙirjinta ya hau dakan lugude. "Ke fa baiwa ce me Yarima ya gani a jikinki da zai ce yana so? An ya ba kunnuwanki ne suke neman yaudararki ba?" Ɗaya daga cikin tsagin zuciyarta ya gargaɗe ta. Tana nan zaune ta ga Mai gado ta faɗo ɗakin kallo ɗaya za ka yi mata ka fahimci tana cikin matsananciyar damuwa. "Wanne laifin kika yi wa Yarima da na ji an ce ya biyo ki har cikin ɗaki? Jawahir wai me ya sa ba kya tunawa da matsayinmu a cikin gidan ne? Mu fa bayi ne ƙasƙantattu a kan me za ki dinga shiga hurumin ɗan masu gida?" Lokaci ɗaya Jawahir ta duburburce don ko karen hauka ne ya cije ta ba za ta taɓa ce wa Innarta Yarima ce wa ya yi yaja sonta. "Inna tsautsayi ne ya sa na bige shi." Jawahir ta furta a sanyaye. "Ki shiga hankalinki Jawahir, kin san dai yadda Yarima yake a cikin gidan nan idan ba haka ba muna zaune za ki kunto mana masifar da za ta nemi ta gagare mu." Da kai Jawahir ta amsa sannan Mai gado ta sake ficewa daga ɗakin. Sarki Abdul'aziz ya shafe sama da minti biyar a tsaye yana juya kalaman Dattijo Maharaz a cikin ransa, a ɓangare ɗaya kuma zuciyarsa na yunƙurin amincewa da abin da kunnuwansa suka ji. "Ta yaya zai zama jininka bayan ba ka taɓa saninsa a cikin 'ya'yanka ba?" "An ya Dattijo Maharaz ba yaudararka yake son yi ba?" "Ɗan mutum a ce ɗanka ne kamar a mafarki, idan ɗanka ne wace ce uwarsa? Kuma a yaushe aka haife shi?" Tarin tambayoyin da Sarki Abdul'azi ya dinga yi wa kansa kenan amma ya gagara samar wa kansa amsoshinsu. Da ƙyar ya iya jan shanyayyun ƙafafuwansa ya koma rumfa (Falo) ya zauna ya rafka uban tagumi. "Yaron nan makusancin Masarautar nan ne, ɗanka ne, jininka ne kuma Magajinka ne." Kalaman Dattijo na baya suka dawo masa raɗau a cikin kunnuwansa. Sallamar da Jakadiya da wasu 'yan matan bayi suka ne ya katse masa tunanin da yake yi, a sanyaye ya ɗago ya dube su hannuwansu ɗauke da manyan tire sai a lokacin ya tuna da shirin tarbar Sarkin Bahdi wato Sarki Sulaiman bn Abdulwahab. "Barka da hutawa ranka shi daɗe ɗawisu mai yawan Ado. Allah ya ja zamanin Mai martaba, sukari ba ka yi farin banza ba bangon zuma kowa ya raɓe ka sai ya lasa." Jakadiya ta yi maganar tana yi masa jinjina da hannu, sannan ta ci gaba da cewa. "Allah ya taimaki Mai martaba ya ƙara wa Sarki lafiya. Sarki Sulaimanu na ƙasar Bahdi ya samu ikon ƙarasowa." Ajiyar zuciya Sarki Abdul'aziz ya sauke a sanyaye ya furta. "Jakadiya a sanar da Shamaki a ba wa Sarki Sulaimanu kulawa kafin mu ƙaraso, me aka zube a gabanmu haka Jakadiya?" Jakadiya da hankalinta ya tafi wani wurin sai a lokacin ta lura da kuskuren da ta tafka, abin motsa bakin da za ta saka Bayi su kai masaukin baƙi sune ta sa suka ɗebo suka kawo sashen Takawa. "Allah ya taimake ka abin saukar ɓaƙi za mu kai sashen Baƙi, shi ne muka biyo don mu sanar da kai isowar Sarki Sulaimanu." Jakadiya ta yi maganar cikin wayancewa. "A ba nu wuri Jakadiya." Sarki Abdul'aziz ya furta a taƙaice. Da sauri suka miƙe gabaɗaya suka fice. Jakadiya na kammala abin da yake gabanta cikin zumuɗi ta wuce sashen Yarima Muhsin don ta cim ma kuɗirinta a kansa. "A iya tsammanina Yarima ya fi ƙarfin kowacce yarinya a ciki da wajen masarautar nan, kaicon wannan rana da na buɗe ido na ga hawaye a idanun Yarima domin wata 'ya mace." A sanyaye Yarima Muhsin ya ɗago yana kallon Jakadiya ya sake sunkuyar da kai ƙasa. "Ka share hawayenka Yariman masarauta, Sarkin gobe da yardar Allah. Ba Jawahir ba ko wacce 'ya kake muradi In shaa Allahu sai ka mallake ta Uban ɗakina." "Jakadiya dama sunanta Jawahir?" Jakadiya ta yi murmunshin yin nasara. "Karɓi wannan fura ce na dama maka ita mai sanyi ka sha ko zuciyarka ta yi sanyi Uban gidana. Sunanta Jawahir kuma sunan Mahaifiyarta Mai gado, yarinyar tamkar 'ya ce a wurina don haka kuwa da kai da kaya ai duka mallakar wuya ne. Ni nan zan wuce maka gaba har gaban Takawa a game da aurenta matuƙar hakan zai faranta maka." A fili Muhsin ya saki murmushin farinciki. Ya miƙa hannu ya karɓi ƙwaryar hannun Jakadiya, ta zauna a gefe suna hira yana sha har ya shanye furar tass. "Ka shanye ƙwayayen abin da za ka haifa Muhsin, ka gafarce ni ba da kai nake yi ba da mahaifiyarka nake yi don haka dalili ne ya sa aikina ya biyo ta kanka. Alƙawarin na ɗauka ko zan tafi tsirara sai na cusa wa Umaima ɓacin rai a zuciyarta, ka yafe ni Muhsin kai da ganin ɗan cikinka sai dai a lahira idan ana haihuwa a can." Jakadiya ta wassafa waɗannan kalaman a zuciyarsa har sai da murmushinta ya bayyana a fili, ta karɓi ƙwaryar wurinsa ta yi masa sallama ta fice zuciyarta fes. *SHU'UMAR MASARAUTA* *30* *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* A lokacin da soyayyar Fargi da Sulaiman ta yi ƙarfi sai ya zama hatta waɗansu sirrikan na alƙaluman tsafi da sihiri Fargi ta fara koya masa, don ma Yarima Sulaiman ya kasance matsoracin gaske shi ya sa ba ya iya gudanar da wani aikin kai tsaye. Fargi ita ta yi tsayuwar tsayin daka ta yi wa Sulaiman aikin da zai gaji karagar mahaifinsa, sai dai tashin farko Mahaifinsa sai da ya ɗaura masa aure da 'ya'yan abokansa biyu sannan aka yi bikin naɗin sarautarsa. A wannan ranar Fargi shiga daji ta yi cikin firgici da tashin hankalin da ba ta taɓa tsammani ba, shi kansa Sulaiman bai taɓa tsammanin haka daga wurin mahaifinsa don sai da ya ji a duniya dama bai taɓa samun karagar mulkin ba a rayuwarsa. "Ban san me ya sa Takawa zai raunata zuciyata ba." Sabon Sarki Sulaiman ya furta a lokacin da ya ratsa cikin ƙungurmin dajin da Fargi ta keɓe kanta a ciki. "Ya aka yi ka san ina wurin nan? Me ka zo za ka yi mini kai da kake da sabbin mata har biy..." Da sauri ya sa hannu a bakinta ya katse ta. "Ke kaɗai ce matata! Da ke zuciyata ta saba kuma har abada da ke za ta rayu. Ban san so ba sai a kanki, ban taɓa ɗanɗanarsa ba sai da kika lasa mini zumarsa. Ke zuciyata ce, zuciyar da a duk bugun numfashi take jerenta hawa da saukar farashin ƙaunarki a zuciyata. Fargiii!" Sulaiman ya furta da wani irin yanayi. A sanyaye ta ɗago ta dube shi nan take idanunta suka sake cikowa da ƙwallah. "Ban taɓa sanin haka soyayyarka ta yi tasiri a zuciyata ba Sulaiman, ina yi maka son da har abada ba na jin akwai hallitar da za ta yi maka kwatankwacinsa. Ina kishinka sai dai a yanzu ka yi mini nisa." Kuka ya ɗan ci ƙarfinta sai da ta yi mai isarta ta ci gaba. "Ka yi mini nisa Sulaiman, nisan da ba na hangen akwai ranar kusantowarsa. Kwatankwacin nisan da sararin samaniya ta yi ƙasa. Yanzu shi kenan ka zama mallakacin wasu soyayyarka ta tashi a banza..." Kukan da ya kwace mata ne ya gayyato haƙoranta suka datse harshenta, ta durƙushe a ƙasa tana fashewa da wani irin matsanancin kuka mai cin zuciya. Da sauri Sulaiman ya ruƙo hannun Fargi ya fara janta har sun fara nisa ta ɗan dakata tana tambayarsa. "Ina za ka kai ni?" "Zan kai ki a ɗaura mana aure a yau ɗin, domin ba zan iya rasa ki ba. Ba zan iya mallaka wa waɗansu kaina ba ke ba, ba zan iya sadaukar da komai nawa ba sai a kanki." Fargi ba ta amsa ba ta ci gaba da bin sa tamkar raƙumi da akala. Sarki Abdul'aziz ya fito fes cikin ƙasaitacciyar alkyabba sai baza ƙamshi yake yi, sai dai ga duk wanda zai yi masa kallon ƙurulla zai fahimci akwai wani abu da yake damunsa a ƙasan ransa. An cika gaban Sarki Sulaiman da kayan ciye-ciye da kayan maƙulashe, da fara'a Sarki Abdul'aziz ya shiga ɗakin saukar baƙin suka shiga gaisawa cikin karamci da mutumta juna. Sarki Abdul'aziz ya girmi Sarki Sulaiman nesa ba kusa ba sai dai kasancewarsa mai sanin ya kamata da girmama na gaba, uwa-uba dattako da sanin mutumci ɗan adam ya sa ta su ta zo ɗaya shi da Sarki Abdul'aziz. Don haka a wannan karon Sarki Abdul'aziz yana zaune takarda ta iso daga ƙasar Bahdi a kan Mai martaba Sarki Sulaiman zai kawo masa ziyara a kan muhimmiyar maganar da za ta kawo shi. "Allah ya taimaki Uba kuma shugaba a gare mu Sarkin Sarakuna Sarki Abdu'aziz." Wata irin izza ce ta sake kanainaye Sarki Abdul'aziz, ya saki murmushin gefen baki. "Da alama Sarki Sulaimanu da tsokana a kalamansa." Sarki Sulaiman ya saki murmushi sannan ya ci gaba da ce wa. "Kuma a haƙiƙanin gaskiya tsokana ba ta cancanci giftawa ta gaban mutanen da suke shirin zama surukai." Sarki Abdul'aziz ya girgiza kai yana dariya don Sarki Sulaimanu mutum ne mai barkwanci. "Ranka shi daɗe magana ta gaskiya neman iri ne ya kawo mu wurinku, idan babu damuwa ina son haɗa aure da ɗan wurinka Yarima Muhsin da 'yar wurina Raihan! Saboda ina kwaɗayin wannan zumuncin namu ya sake ƙarfi har cikin zuri'armu. Amma fa idan babu takura ranka shi daɗe, idan kuma akwai sai mu yi wa fatan kowa Allah ya haɗa shi da rabonsa na alheri." Tun Sarki Sulaiman bai gama maganar ba Sarki Abdul'aziz ya saki murmushin farinciki. "Mun yi murna da waɗannan kalaman naka Mai martaba, kuma mun amince da wannan maganar ko bayan ranmu wannan maganar ba za ta taɓa sauyawa ba. Ba don kada na yi azarɓaɓi ba, da sai na ce wannan auren a ɗaura shi a ranar juma'a mai zuwa." Cikin farinciki Sarki Sulaiman ya amsa wa Sarki Abdul'aziz sannan suka ci gaba da tattaunawa a kan muhimman batutuwa dangane da yadda auren zai kasance. Daga ƙarshe Sarki Sulaiman da Sarki Abdul'aziz suka tsayar da ranar aure makwanni huɗu masu zuwa. Sarki Sulaimanu ya yi wa Sarki Abdul'aziz sallama da shi da Bafadawa da 'yan rakiyarsa suka koma Masarautarsu ta Bahdi cikin matsanancin farinciki. Inna wuro tun da yamma ta ƙarato take saka ran ganin Kamalu amma babu shi babu alamarsa, tun tana tsammanin ko wani aikin ne ya riƙe su har ta fara shiga damuwa. Ganin su Salisu abokan Kamalu sun dawo hakan ya sake firgita ta, musamman da ta tambaye shi Kamalu gabaɗaya suka shaida mata rabonsu da shi tun da safe. A ɗimauce Inna wuro, Baffajo da sauran tsirarun Bayin suka shiga cikin Masarautar suna nemansa amma babu Kamalu babu alamarsa, tun suna ganin abin kamar wasa har aka shafe kwana guda ba tare da an ga Kamalu ko gawarsa ba. Tun a daren ranar zazzaɓi mai zafi ya rufe Inna wuro da Baffajo saboda matsananciyar damuwa da suka shiga, kallo ɗaya za ka yi musu ka fahimci suna cikin matsananciyar damuwa don ko abinci ranar ba su iya ci ba. "Wallahi ni dai na gaji da yin bauta a wurin nan haka kawai wari ya addabe ka, saboda Allah don dai shi Bawa ba shi da gata sai a ce kowanne cin kashi shi zai ɗauka. Hanne dubi wancan zanin na Sailuba ban da ruwan mugunya da tsutsotsi babu komai a ciki." Hanne ta sauke ajiyar zuciya bayan ta gana sauraron Furaira sannan ta furta. "Wallahi gara ke Furaira nesa ba kusa ba, idan kin wanke ai shi kenan sai wani ya sake ɓaci. Ni kina ga kullin ina tare da ita ina aikin kashe mata kwarkwata, ga uban ɗoyin da nake shaƙewa. Wallahi ni kaina na ƙagu na sauya..." Kalaman Hanne suka katse sakamakon hango Jakadiya da ta yi a tsaye. "To tsofaffin munafukai, uban me kuke tattaunawa?" Take suka yi tsilli-tsilli cikin tashin hankali, fargabarsu ɗaya Allah ya sa Jakadiya ba ta ji abin da suke faɗa. "Babu komai Jakadiya hutawa muke." Furaira ta wayance. Jakadiya ƙwafa ta yi sannan ta wuce wurin Sailuba da ke kance a ɗaki ta yashe ƙafafuwa tana shan iska. Ɗoyin da ya daki hancin Jakadiya ne ya sa ta ɗan ja baya da sauri, gabanta ya buga dum! Da matsanancin ƙarfi. Ta zura wa Sailuba idanu cikin tashin hankalin, Sailuba da ke kwance ta bi Jakadiya da jemammun idanunta cikin sare rai da yanke ƙauna. "Sailuba idanuwana ne suke yi mini gizo ko da gaske haka kika sake lalacewa. Yanzu warin da ke fita daga jikinki har ya ta'azzara haka?" Sailuba ba ta tanka wa Jakadiya ba saboda tsananin takaicin da ya cunkushe ta, a duk faɗin duniya gani take babu wanda ya jefa ta a wannan halin sama da mahaifiyarta. "Dama kowa ya sayi rariya ai ya san za ta zubar da ruwa Inna! Kin fi ni sanin wace ce Umaima a kan me za ki tsaya kina tambayata? Na nemar wa kaina mafita amma kin ce ba haka ba kin ga idan na mutu shi kenan kin kowa ya huta. Ita Umaima hankalinta zai kwanta ta mallaki mijinta ita kaɗai, ni kuma na samu salama a rayuwata ke kuma ki huta da yawon neman magani." Sailuba ta ƙarashe maganar ƙwalla na zuba daga idanunta. Tun da sabuwar lalurar nan ta samu Sailuba wannan ce rana ta farko ta kalamanta suka daki zuciyar Jakadiya, wata irin nadama game da auren Sailuba da Takawa ta mamaye ta. A sanyaye ta tsugunna idanunta suka ciko da ƙwallah. "Jakadiya wannan maganin Takawa da kansa ne ya ce ki kawo mini? Amma dai na ji daɗi ko ba komai a wannan karon Takawa ya nuna mini kulawa. Allah ya sa idan na haife cikin nan albarkacinsa ya sa na ci gaba da samun kulawa daga gare shi." Kalaman Fulani babba na baya suka dawo wa Jakadiya raɗau a cikin kunnuwanta, a lokacin da ta kai mata wani garin turare da suka haɗa baki da Fulani Umaima a zuwan Sarki Abdul'aziz ne ya bayar da shi. "Allah ka gafarta wa Fulani babba, Ubangiji ka sa ta yafe mini abin da na aikata mata. Ya Allah kada ka jarabce ni da haƙƙinta a kaina." Jakadiya ta furta zuciya a raunane. "Inna me kalamanki suke nufi? Shin kin taɓa yi wa Fulani babba wani abu ne?" Ajiyar zuciya Jakadiya ta sauke sannan ta furta. "Ba huruminki ba ne Sailuba." "Ba hurumina ba ne amma ai ta silata kike neman yafiyar Ubangiji. Inna me kika aikata ne da abubuwa suka caɓe mana lokaci guda. Ni fa na fara ɗora zargi a kanki don na tabbata ruwa ba ya tsami banza." "Zan shawarci Takawa domin na fantsama nema miki magana, ba zan zura ido na ga kin lalace a banza ba, idan ta kama ma na ɗauke ki na mayar da ke can sashena tun da na lura idan na tsaya kallon ruwa kwaɗo zai iya yi mini ƙafa." Daga haka Jakadiya ta fice daga ɗakin zuciyarta na suya. Ta kowacce fuska abin duniya goma da ashirin ne ya mamaye zuciyar Fulani Umaima, hannuwa bibbiyu ta zauna ta rafka uban tagumi tana tuna irin rayuwar jin daɗi da rashin tarin matsalolin da ta yi a baya. "Ta wacce hanya zan samu damar yankar gashin kan Basiru? An ya Muhsin zai ba ni haɗin kai a kan abin da nake buƙata na kai yarinyar nan wurin Shugaba kuwa?" Fulani Umaima ta watsa wa kanta tambayoyi, murmushin da ya jima bai sauka a saman fuskarta ba ne ya suɓuce mata da ta tuna dabarar da ta faɗo mata game da Muhsin. Ta yunƙura za ta miƙe ta sake jin ƙasanta ya zazzago mata, tsoro ne ya sake kamata don a kullin ƙasanta sake zazzagowa yake yi. "Me ya sa haka? Me ya sa al'amurana suka caɓe lokaci ɗaya?" Daga can bayanta ta ji an furta. "Saboda ni ma ba ki bar ni na zauna lafiya a lokacin da nake raye ba." Raɗau ta ji muryar Fulanu babba a kunnuwanta. Da sauri ta waiga a ɗan tsorace karaf idanunta suka sauka a kan ƙanjamammiyar mage ta zuba mata idanunta masu abin tsoro. Matsanancin tsoro ne ya sake mamaye Fulani Umaima tana shirin guduwa azabar da ke addabarta ta sa ta faɗi ƙasa, tana daga zaune ta fara jan jiki a hankali magen ta ci gaba da tunkaro ta har sai da ta ƙarasa gabanta. "Duk inda za ki je ina biye da ke Umaima!" Magen ta furta sannan ta nutse ƙarƙashin ƙasa ta ɓace daga wurin. Rashin samarwa kai mafita da damuwar da ta cunkushe Fulani Umaima ta sa ta fashe da wani irin kuka mai cin zuciya. Inna wuro ce ta faɗa ɗakin a firgice jin sautin kukan Fulani Umaima. "Allah ya taimaki uwar ɗakina ya ƙara wa Fulani lafiya. Ranki shi daɗe shi daɗe..." Da sauri Fulani Umaima ta katse Inna wuro. "Inna wuro muna buƙatar keɓewa." Inna wuro ta fice da sauri don ita kanta har lokacin tana cikin matsananciyar damuwar rashin ganin Kamalu. Furhussam na ɗaukan Kamalu ya fara zabga matsanancin gudu bai sauke shi a ko ina ba sai a can ƙungurmin dajin Buhdu, a can cikin ƙaton wani farin dutse mai matuƙar ɗaukar idanu. Dajin cike yake da dogayen bishiyoyi a jajjere tamkar wani ne ya dasa su. Sai dai kallo ɗaya idan ka yi take hantar cikinka za ta kaɗa sakamakon yadda suffarsu take da yanayin tsoratarwa. Dutsen a mulmule yake babu ƙofa ko a huda ko kaɗan a jikinsa, sai da ya tsaya a wurin sannan ya ɗora tafin hannunsa a jikin dutsen, nan take ya tsage gida biyu wani ruwa mai garai-garai ya fara ɓulɓulowa daga ciki. Ta cikin ruwan Furhussam ya shiga, yana shiga dutsen ya sake haɗewa ya mulmule. Hallitu ne kala-kala a ciki waɗansu ɗauke suke da siffar tsuntsaye kawunansu ɗauke da ƙaho, waɗansu kuma siffar jikin birrai gare su bayansu ɗauke da jeluna. Duk ta hanyar da Furhussam ya wuce ɗaya bayan ɗaya hallitun suke zubewa ƙasa suna gaida shi cikin wani irin sarƙaƙƙen yare. Tafiya ya ɗanyi ma nisa sannan ya isa tsakiyar babban filin da wata ƙatuwar rijiya a ciki, yana buɗe murfin rijiyar take wani ƙasaitaccen gado ya bayyana. Da kansa ya ɗora Kamalu a kan gadon, daga ɓangaren hagu Hullat ce tafe cikin surar tsuntsu mai ɗan ban tsoro ita da yarta Furtuhmu, sai da suka ƙarasa gaban gadon sannan suka rikiɗe cikin surar bil'adam. Furtuhmu ce ta matsa gefensa cikin shauƙi ta sa hannu ta shafi gefen fuskarsa, a hankali Kamalu ya sauke ajiyar zuciya sannan ya buɗe idanunsa. A hankali yake bin wurin da kallon mamaki, ya ƙura wa Furtuhmu kallo yana jin tamkar ya taɓa sanin fuskarta. "Barka da hutawa." Ta furta masa a taƙaice. Furhussam da ya rikiɗe zuwa siffar da Dattijo Maharaz yake zuwar wa Kamalu ya matsa kusa da shi ya furta. "Kamalu ka farka kenan? Barka da tashi Sadauki." Sai a lokacin Kalamu ya sauke ajiyar zuciya hankalinsa ya kwanta. "Dattijo Maharaz ina ne nan ka kawo ni?" Murmushi ya sakar masa. "Kada ka ɗaga hankalinka Kamalu nan ne wurin da za ku samu 'yancin kanku kai da iyayenka." Rufe bakinsa ke da wuya sai ga waɗansu dattijai sun ƙaraso wurinsa masu ɗauke da siffar Inna wuro, Baffajo da A'iru. Murmushi Kamalu ya sakar musu yana sake jin karamci da ƙaunar Dattijo Maharaz a zuciyarsa. Sarki Abdul'aziz tun da ya kwanta ban da juyi babu abin da yake yi, tunaninnika da dama suka mamaye kwanyarsa yana sake juya kalaman Dattijo Maharaz. Abubuwan da suka faru a ɗakinsa suka ci gaba da dawo masa, a ɓangare ɗaya ga tagwayen larurorin matansa da suka fara ci masa tuwo a ƙwarya. "Idan Dattijo Maharaz ya warware maka zare da abawa ka ƙara aure." Wani tsagin na zuciyarsa ya shawarce shi. "Kada ka yi aure ka dai nema musu magani, ina ganin shi zai fi maka sauƙi tun da kana gani a sakacinka ka rasa matarka kuma uwar 'ya'yanka."Zuciyarsa ta sake shawartarsa. "Don Allah ranka shi daɗe ka nemo mini magani, ni kaɗai na san irin azabar da nake ciki a kullin ji nake ana fisgar ƙasana tamkar zai fito waje." Kalaman Fulani babba suka dawo masa cikin kunnuwansa. "Astagafirullah! Allah ka gafarta wa Fatima Ubangiji ka yafe mini akan sakacin da na yi a kanta." Sarki Abdul'aziz ya furta a fili idanunsa na cikowa da ƙwalla. Duk da ya kasance abokin 'yar tsamarta ne ba ƙaramin jimamin ɓatansa ta yi ba, a ɓangare ɗaya fargabarta ta ninku da ta tuna kusan ta silarta hakan ya faru sai dai ta gagara furta kowa har Mai gado. A duk lokacin da ta keɓe ba ta da aiki sai tunanin halin da yake ciki, wani lokacin har zubar da ƙwalla take yi. Wannan ne karo na farko da Jawahir ta ji ba za ta sake biyewa umarnin matar da ke zuwar mata a mafarki ba koda za ta hallaka. Hatta Mai gado sai da ta fahimci halin damuwar da Jawahir take ciki don haka ta tsare ta da tambaya. "Jawahir wani abu yana damunki ne? Ko mafarki kika sake yi da matar nan?" "Inna ina tunanin halin da Kamalu yake ciki ne! Ko ya mutu ko yana raye Allah ne masani." Jawahir ta ƙarasa maganar kamar za ta yi kuka. "Addu'a ita za mu ci gaba da yi, idan muna nuna karayarmu a fili za mu sake raunata zuciyar Inna wuro don haka kika ga a kullin nake sake ƙarfafar gwiwarta." Lokacin da Muhsin ya gama shan furar wurin Jakadiya tana fita bacci ya yi awon gaba da shi, ya jima yana bacci har bayan sallar Isha'i. Bayan ya tashi ya ɗan ji damuwarsa ta ragu don haka ya wuce ya ɗauro alwala ya gabatar da sallolin da suke kansa, zamansa babu jimawa fuskar Jawahir ta ci gaba da dawo masa a hankali murmushi ya suɓuce masa. Fulani Umaima sai da ta yi wanka ta sake gyara jikinta ta tura ƙaton tsumma ƙasanta domin ya dinga tare ruwan da ke fita daga jikinta, ta rame sosai fuskarta ta yi fayau tamkar wacce ta jima tana jinya. Kai tsaye sashe Muhsin ta nufa a wannan karon ko Baiwa ɗaya ba ta bari ta yi mata rakiya ba, a lokacin da ta je yana zaune zugum cikin damuwa. Da sallama ta shiga sai dai ciki-ciki ya amsa mata ya ɗauke kansa gefe, a kusa da shi ta zauna ta aro murmushin yaƙe ta furta. "Na zo bikon Sarkin gobe." "Hmmm!' Kawai Muhsin ya ce. "A baya na yi maka mummunar Fahimta ne Yarima, a tsammanina Yarima mai jiran gado tamkarka bai dace da auren Baiwa ba. Amma a yanzu da na fahimci irin soyayyar da kake yi mata na amince ɗari bisa ɗari Sarkin gobe, da kaina zan wuce har gaban Takawa domin na yi maka iso a kan neman aurenta." Sai a lokacin Yarima Muhsin ya saki fuskarsa, ya ruƙo hannun mahaifiyarsa cikin farinciki. "Na ji daɗi ƙwarai da kika fahimce ni Ammi! A daren nan kuwa zan yi gaggawar dakatar da Jakadiya tun da kin sauko..." A razane Fulani Umaima ta katse shi. "Wacce Jakadiya? Me za ka dakatar da ita?" *SHU'UMAR MASARAUTA* *31* *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Sarki Sulaiman tare da maƙarrabansa cikin farinciki suka koma masarautarsu, tun bai shiga cikin sashensa ba kai tsaye wata ƙofa ya shiga wacce aka sassaƙa da zallar farin ƙarfe, sai walwali take tana ɗaukan idanu. Kusan ya zame masa al'ada duk fita idan zai yi ko bayan ya dawo daga wani wuri sai ya shiga cikin wannan ƙofar. Babban ɗaki ne da aka ƙawata shi da kayan alatun more rayuwa, a tsakiyar ɗakin an sassaƙa wata ƙatuwar tantamara wacce aka yi mata adon fentin fari da baƙi sai waɗansu duwatsu da aka manna mata a jiki. Sai da ya ƙarasa ya sumbace ta sannan ya fito ya fice kai tsaye ya wuce sashensa, da saukarsa babu jimawa aka haɗa masa ruwan wanka ya shiga ya gaggasa jikinsa sannan ya zura 'yar shararsa ta shan iska ya bayar da umarni Jakadiya ta kira masa matansa gabaɗaya kowacce tare da iyalanta. Sun yi matuƙar mamakin jin kiran da yake yi musu don haka kowacce zuciyarta cike da wasu-wasin dalilin tarasu ta ƙarasa. Sarki Sulaimanu Matansa Uku da 'ya'ya goma cif, yana da 'ya'ya maza huɗu sai 'ya'ya mata guda shida. Uwar gidansa Fulani Habiba tana da 'ya'ya Huɗu, uku mata sai namiji ɗaya. Kuma babbar 'yar Sarki Sulaiman mace ce mai suna Raihanatu. Matarsa ta biyu Fulani Sa'adiyya tan da'yaya mata biyu sai 'ya'ya maza biyu, ita kuma Fulani Zabba'atu tana da 'ya'ya biyu duka mata. "Assalamu alaimum. Muna buƙatar gabaɗayanku ku ba mu hankalanku domin mu sanar da ku abin da yake tafe da mu na alkhari." Sai da ya zayyane musu duk yadda suka yi da Sarki Abdul'aziz sannan ya ci gaba da ce wa, "A yanzu haka ni da Mai martaba mun zartar da lokacin aurensu Raihanatu nan da makwanni huɗu masu zuwa cikin yardar Allah. Ina fatan ke Raihanatu ba za ki watsa mini ƙasa a ido ba." Cikin ladabi Raihanatu ta gyaɗa masa kai, farinciki fal zuciyar mahaifiyarta ya ƙi ɓoyuwa don babu wanda ba zai so ya haɗa zuria'a da masarautar Huddam ba. Sai da suka ɗan taɓa hira a tsakaninsa da iyalansa sannan ya sallame su kowacce ta wuce sashenta. Baƙinciki ne ya mamaye zuciyar Fulani Sa'adiyya don a ganinta Yarima Muhsin da 'yarta Hansatu ya fi dacewa. Dattiji Maharaz sai da ya duba lungu da saƙon cikin dajin amma ko mai kama da jinsin halittar ɗan adam bai gani ba, a galabaice ya zauna a bakin wata bishiya sannan ya faɗa duniyar tunani. "Da wacce shaida zan koma na sanar wa Sarki Abdul'aziz? Shi kenan rayuwar Kamalu za ta koma hannun Furhussan da zuri'arsa?" Dattijo Maharaz ya furta a fili. "Sam ba zai taɓa yuwa ba." Ya yi maganar yana miƙewa tsaye rai a ɓace. "Na ji daɗi har a kullin ƙwarin gwiwarka ne yake rinjayar rauninka, kai mai farar zuciya da jin ƙai ne don haka zan taimaka maka da baiwar da Allah ya hore mini." Dattijo Maharaz ya ji an furta daga bayansa, yana waigawa ya ci karo da Malam Liman. A fili ya bayyana fara'arsa ya ƙarasa wurinsa yana niyyar russunawa ya ɗago shi. "Kada ka damu Maharaz, babu isasshen lokacin da za mu ɗauka. Zan taimaka maka a ƙwato yaron nan domin shi ɗin ba jininmu ba ne kuma ba jinsin mu ba matuƙar aka bar shi a cikinsu an cutar da shi da iyayensa, kuma a kowanne lokaci suna iya sauya masa addini gabaɗaya." Jinjina kai Dattijo Maharaz ya yi sannan ya shiga zabga wa Malam liman godiya bisa karamcin da yake nuna masa da soyayyar addinin musulunci. "Furhussam ya yi amfani da sirrin tsafi da sihiri, mu kuma sai mu karya shi da addu'o'in kariya daga ayoyin Allah. Ka dafa wannan dutsen da bismillah bayan ka yi alwala kuma ka ambata da yaƙini a zuciyarka Ubangiji Shi zai iya aiwatar da komai kuma da taimakonSa za mu samu mu kuɓuto da wannan yaron." Sun fara tafiya mai nisa Fargi ta dakatar da shi tana share hawayenta sannan ta furta. "Idan zuri'arka sun amince na aure ka na san halin zuri'ata har gaban abada ba za su lamunce na aure ka ba Sulaiman, hasali ma a yanzu matuƙar suka ji alaƙar da ke tsakaninmu gabaɗaya hallaka mu za su yi. Haƙuri shi ya kamace mu gwarzona, ina ganin dama can tsafina bai bincika mini daidai ba." "Ba zan iya ba Fargi! Ba zan iya rabuwa da ke ba, idan kin lamunce zan kai ki a ɗaura mana aure a ɓoye idan ya so na dawo da ke cikin danginki kafin mu nemarwa kanmu mafita." Shiru Fargi ta yi tana nazartar kalamansa ganin kamar ba za ta amince ba ya sa ya shiga lallashinta da gaya mata daɗaɗan kalamai har dai Sulaiman ya yi nasara a kanta. Alkyabbar jikinsa ya cire ya rufa mata ya ɗora ta a kan dokinsa sai da suka yi tafiya mai nisa sannan suka fito cikin gari, tsoro ne ƙarara ya mamaye Fargi sakamakon wannan ne karo na farko da ta taɓa tsomo ƙafafuwanta cikin gari ta baro dajin da suke rayuwa. "Ki nutsu Sarauniyata babu abin da zai kama ki, idan kina nuna firgici mutane za su dasa zarginsu a kaina." Sulaiman ya furta mata cikin sigar lallashi bayan ya gama naɗe fuskarsa domin kada a gane shi. Can bayan garinsu ya wuce da ita ya buɗe wani ɗan ƙaramin guda mai ɗaki biyu ya saka ta a ciki sannan ya ce mata yana zuwa. Da fitarsa kai tsaye gidan Waziri ya wuce aminin mahaifinsa, takanas ya ɗauko shi sai da ya kawo shi cikin gidan sannan ya zayyane masa duk abin da yake tafe da shi. Zuciyar Waziri ƙal ya amince da buƙatar Sarki Sulaiman don a ganinsa nan gaba wannan auren da zai yi ba ƙaramin naƙasu da damuwa zai kawo masa a harkar mulki ba tun da babu wanda ya san da auren, idan ya so nan gaba ko hayayyafa ta yi yana iya murje idanunsa ya ce bai san zance ba tun da har Mahaifinsa ya iya tsallake 'yarsa Shafa'atu ya aura wa Sulaiman wasu. A wancan lokacin Sulaiman har sai da ya yi wa Fargi tayin addinin musulunci amma fir ta nuna masa ba ta aminta da shi ba, ko da za ta shiga addinin sai zuwa bayan wani lokaci. Sulaiman bai takura mata ba don haka shi da Waziri suka fice daga gidan, a can wani ƙaramin ƙauye Waziri na da wani amini sunansa Kalidu tare da Sulaiman suka tafi garin Waziri ya zayyane masa komai. Malam Khalidu ya amince zai zo a matsayin waliyyin Fargi shi kuma Waziri ya zo a matsayin waliyyin Sulaiman, suka tara mutane a ƙofar gida aka ɗaura auren Sulaiman da Fargi kamar yadda addinin musulunci ya hukunta. Da ɗan mamaki a fuskar Muhsin yake kallon mahaifiyarsa ganin yadda ta razana lokaci guda. "Ita ta ce mini za ta wuce mini gaba wurin Takawa a kan maganar auren yarinyar." Ajiyar zuciya Fulani Umaima ta sauke a fili tana juya kalamansa a cikin zuciyarta. "Ruwa fa baya taɓa tsami banza ni na san akwai manufar Jakadiya a wannan maganar! To ko ta gano neman yarinyar nake yi ruwa a jallo? Da sannu zan fahimci inda ta dosa, don na yi rantsuwa da ƙarfin ikon Bamaguje Jakadiya ba za ta taɓa kwaye mini baya ba." Fulani Umaima ta wassafa zancan a cikin zuciyarta. Amma a fili sai ta ce. "Me ya sa ka yi mini haka Muhsin? Me ya sa za ka ce Jakadiya ta yi maka iso wurin Takawa, kamar ba ka san tsegungumin cikin gidan nan ba?" "Sai na zauna sai kin amince sannan zan auri wacce nake so? Me ye laifi don Jakadiya ta wuce mini gaba wurin Takawa?" Murmushin yaƙe Fulani Umaima ta ƙirƙiro ta furta. "Ba komai ba ne Yarimana kawai ina gudun ƙananan magangunu, yanzu dai ka tashi ka je ka ce wa Jakadiya mun gama magana da kai." "Tun farko ke ce ba ki so haka ba ai da kin bada kai bori ya hau da haka ba ta faru ba." Muhsin ya furta wa mahaifiyarsa. Fulani Umaima ba ta ce uffan ba ta fice daga ɗakin. Tana komawa ɗakinta ta samu Ruƙayya da sauran Bayinta suna yi mata najanje-najanje, ganin Fulani Umaima ya sa suka miƙe da sauri kowannensu a tsorace don ba sau ɗaya ba ba sau biyu ba ta hana Ruƙayya shiga cikin Bayi a cewarta ba matsayinsu ɗaya ba. Amma ga mamakinsu sai gani suka yi ta wuce ɗaki uffan ba ta ce musu ba. "Baraka don Allah ki ci gaba, kin ga na cire ƙafa ɗaya saura Lami da Fa'iza." A ɗan tsorace Baiwa Baraka ta ci gaba har lokacin hankalinta na kan ƙofar Fulani Umaima. Gyara kanta ta sake yi ta feshe jikinta da turarruka kala-kala ta ko ina ƙamshi ne yake tashi, babban tashin hankalinta bai wuce wannan ruwan mai ɗoyi da yake zubo mata ba. Da wannan tsokar naman da ke zazzagowa. "Yanzu a haka zan tunkari Takawa?" Fulani Umaima ta furta a sanyaye idanu cike da ƙwalla. Ba ta da wani zaɓin da ya wuce wannan don haka ta sake bulbula turare ta wuce sasahen Sarki Abdul'aziz da ita kanta ta manta rabon ta da shiga sashen shi. Da sallama ɗauke a bakinta ta shiga yana zaune da carbi a hannu, a taƙaice ya amsa mata ya ci gaba da jan carbi. Daga can gefe ta rakuɓe tana raba idanu, sai da ya shafa addu'a sannan ya zuba mata ido yana mamakin abin da zugar da ita lokaci guda. Amma kuma wari, ƙarni da turare mai hawa kai da ta sa ne ya sa shi ɗan yamuta fuska, yana shirin magana ta katse shi. "Barka da hutawa Sarkina!" "Barka dai Umaima yau an tuno da mu?" Murmushi ta saki na jin daɗin kalamansa. "Ranka shi daɗe a baya ma gani na yi tamkar ina takura maka tun da wanna larurar ta same ni." Umaima ta faɗa cike da kissa. "Ba mu ƙyama ce ku ba Umaima, muna dai ta fafutukar nema muku magani ne. Yanzu haka akwai masu magunguna har mutum uku da muke jiransu daga yanki daban-daban." Sai da ya gyara zamansa sannan ya ci gaba. "Kin yi sara a kan gaɓa Umaima don yanzu nake shirin aikawa a kira mana ku." Rass gaban Fulani Umaima ya faɗi, tana ɗan fargabar abin da zai sanar da su. "Ina yaron nan Basiru kusan mako guda ban ji hatsaniyarsa ba, Yarima ma yau kwana biyu kenan bai leƙo ni ba." Sarki Abdul'aziz ya furta da 'yar damuwa ɗauke a fuskarsa. "Ranka shi daɗe yanzu haka daga wurin Yarima nake maganarsa ce mata kawo ni, shi kuma Basiru ka san shi da nunkufurci ɗazu dai ya leƙo sashena." Fulani Umaima ta yi maganar tana ɗan sosai kai. Kafe ta ya yi da kallo yana son fahimtar wani abu daga gare ta. Bawa Sammani ya ƙwala wa kira cikin ladabi ya ƙarasa bakin ƙofar ya amsa ya tsaya yana jiran umarnin Takawa. Sarki Abdul'aziz ya ba shi umarnin ya sanar da Jakadiya ta haɗo masa kan iyalansa gabaɗaya har Abubakar yana son tattaunawa da su. "Ranka shi daɗe me ye haɗin tattaunawar da za ka yi da musakin yaron nan Abubakar? Yaron da; da shi da babu duk ɗaya ne..." "Dakata Umaima!" Ba ma son shashancin banza da wofi, yadda Yarima yake a wurinmu haka muke jin Abubukar. Ke kin san ba don Allah ya hallice shi da wannan tawayar ba, da yanzu haka shi ne Yarima mai jiran gado. Idan muka sake jin makamancin shashancin nan daga bakinku ranku zai yi mumman ɓaci." Shiru Fulani Umaima ta yi tana mamakin kalaman da Sarki Abdul'aziz yake gasa mata. "Lallai kura ta yi lafiya." Fulani Umaima ta furta a zuciyarta, baƙinciki ya mamaye ta da ta tuna yadda Takawa ya haɗa matsayin Abubakar da Yarima Muhsin. Cike da ƙwarin gwiwa Dattijo Maharaz ya ƙarasa bakin wata ƙorama ya ɗaura alwala ya tunkarin mulmulallan dutsen bakinsa ɗauke da addu'o'i ya dafa jikinsa. Tamkar yadda ƙwan kaza yake rabewa gida biyu haka dutsen ya rabe gida biyu, haske ya mamaye cikin dutse cikin ƙarfin zuciya Dattijo Maharaz ya kutsa kai har lokacin yana tafe yana karanta addu'ar duk da ta zo bakinsa. Tun farkon shigarsa ya ga yadda hallitun wurin suke bin sa da kallo sai dai uffan babu wanda ya ce mata, a haka ya ci gaba da tafiya har sai da ya kai tsakiyar dutsen daga can nesa ya hango Kamalu ya miƙe d alama wani wurin za shi. "Ina za ka je haka Kamaluna?" Aljanin da ke ɗauke da surar Baffajo ya furta. "Sallah zan yi don ban yi sallar azahar ba." "Na gaya maka ba na son jin zan can sallar nan wai dole ne?" Da mamaki Kamalu yake bin sa da kallo, da sauri Dattijo Maharaz ya ƙarasa yana faɗin. "Kamalu kada ka bari mashirika maƙiyan Allah su yi galaba a kanka, wannan ba Baffajo ba ne." "Ko kaɗan kada ka yarda da shi Kamalu yaudararka zai yi ni ne Baffajo, wancan kuma Dattijo Maharaz ne shi kuma mai yi maka maganar mayaudari ne." Furhussam da ke cikin surar Dattijo Maharaz ya furta yana ƙarasowa a lokacin komai nasu iri ɗaya babu wani abu da zai iya bambamce su. Sororo Kamalu ya yi kansa ya ɗaure, tashin farko tsori ya mamaye Kamalu, murya a sanyaye ya ce. "Dattijo Maharaz me yake faruwa ne?" "Babu abin da yake faruwa Kamalu." Suka furta kusan lokaci ɗaya. e Baƙinciki ya mamaye Dattijo Maharaz ya dubi Furhussam a ƙufule. "Furhussam ba na son tarihi ya sake maimaita kansa don haka a komai nake biyo maka a cikin ruwan sanyi, ka ba ni yaron nan na wuce da shi idan ba haka ba wallahi abin da ya faru a shekarun baya zai sake dawowa." Furhussam ya tamke fuska sannan ya ce. "Kada ka raina mini hankali Furhussam kana nufin yadda ka rikiɗe wa Kamalu ni ma za ka rikiɗe mini?" Kamalu da ya gama shiga ruɗani ya koma ya zauna haɗe da dafe kansa da hannuwansa. Dabara ce ta faɗo wa Dattijo Maharaz don haka ya nuna jikin bangon dutsen nan take sai ga hoton su Baffajo da Inna wuro suna zaune zugum cikin damuwa. "Ka yarda da ni Kamalu waɗannan sune su Baffajo na ainihi har yanzu ba su san halin da kake ciki ba." "Ƙarya yake Yarona ni n Baffajonka." "Kada ka yarda da shi ni ce Inna wuronka mai dama maka fura da yi maka hidima." Masu ɗauke da surar Baffajo da Inna wuro suka yi maganar lokaci ɗaya. Ganin suna neman dagula masa lissafi ya sa Dattijo Maharaz ya nemi taimakon Malam Liman, bayan ya shigo suka haɗa baki suka fara karatun alƙur'ani. Tun aljanun da ke ɗauke da siffar su Baffajo na daurewa har suka fara ihu jikinsu ya fara soyewa, ganin haka ya sa zuciyar Kamalu ta fara aminta da Dattijo Maharaz wanda yake karatu, da gudu ya nufi wurinsa yana sauke ajiyar zuciya wani irin tsoro ya mamaye shi. "Barka da hutawa Malam Liman! Shin me yake faruwa da tsakar rana za ku tako har cikin zuri'armu ku nemi cin zarafinmu bayan wannan daɗɗaɗiyar yarjejeniya ce." Babban malaminsu masanin addininsu na bauta ruwa ya furta a ɗimauce sakamakon kururuwar da ta ɗimauta shi na aljanun da suke ƙonewa. Duk abin da ya faru tun daga farko har ƙarshe Dattijo Maharaz ya zayyane masa, bayan ya gama sauraronsa ya furta. "Yanzu kai Maharaz mene ne alaƙarka da yaron nan bayan shi ba jininka ba ne? Ina ganin wannan yarjejeniyar iya kan zuri'ar kowannenmu ce?" "Yaron nan ya kasance tamkar jini da tsokata, idan ka cire alaƙar da ke tsakanina da kakan-kakansa ko a iya shi kaɗai zan iya tsaya masa. Ballantana idan ba ka manta ba, na taɓa gaya maka Furhussam ya kiyaye hatta bil'adam ɗin da ke rayuwa a tare da mu ne saboda kyakkayawar alaƙarmu." Shiru ne ya ratsa a wurin, daga Fulani Umaima har Sailuba ban da wurga wa junansu harara babu abin da suke yi. "Ina Basiru yake?" Takawa ya tambaya. "Ina jin ya fita ranka shi daɗe." Yarima Muhsin ya faɗa cikin zaƙuwa don a tsammaninsa zancan Jawahir mahaifiyarsa ta yi wa Takawa ne ya sa aka tarasu. Ƙwafa sarki Abudul'aziz ya yi sannan ya buɗe zaman nasu da sallama, bayan sun amsa Sarki Abdul'aziz ya ci gaba da jawabi. "Maƙasudin zaman da na taraku yana da nasaba da kai ne Yarima," Yarima Muhsin ya saki murmushin farinciki. "Ka san dai yanzu kai ba yaro ba ne, sa'aninka har da masu 'ya'ya a duniya. Don haka ni da Sarkin ƙasar Bahdi muka yanke hukuncin haɗa ku aure tare da 'Yarsa Raihana." A razane Yarima Muhsin ya ɗago ya dube shi, "Ranka shi daɗe wai ni za a yi wa aure? Gaskiya ni ina da wacce nake so wai Ammi dama ba ki sanar da shi ba ne yadda muka yi da ke?" Shiru ne ya ratsa, Abubukar da ke jikin Sarki Abdul'aziz ya saki dariya yana nuna Muhsin da ke kumfar baki. "Mu kake furta wa haka Muhsin?" Muhsin ya ɗauke kansa gefe yana ƙananun maganganu. "Wannan ne uzuri na ƙarshe da zan iya yi maka Furhussam, dole ka fuskanci mummunan hukuncu domin idan ba ka manta ba a shari'ar da na yi maka da jikan Malam Idi ce maka na yi idan ka kuma ɗauko mana magana za ka fuskanci hukunci mai tsanani kuma ka amince. Furhussam me ya sa kai da zuri'arka ne kaɗai kuka fita zakka a cikinmu? Ba za mu lamunci wannan isakancin ba, don haka Maharaz ka ɗauki yaron nan ka wuce kuma daga shi har zuri'arsa duk wanda ya kuma shiga gonar yaron nan na ba ku umarnin ku ƙone shi." Farinciki ya lulluɓe Dattijo Maharaz, Malam Liman ya shiga zabga masa godiya sannan Dattiijo Maharaz ya sa hannu ya rufe wa Kamalu idanu nan take suka ɓace sai ga su a ɗakin Sarki Abdul'aziz. A razane duka mutanen cikin ɗakin suka miƙe waɗansu daga ciki har da masu neman wurin ɓuya, shi kansa Sarki Abdul'aziz sai da ya yi ta maza ya iya tsayawa. "Dattijo Maharaz kai ne?" Sarki Abdul'aziz ya furta cikin tsananin farinciki. "Shin ka ba ni dama na ƙaraso cikin iyalanka?" Dattijo Maharaz ya wurga masa tambaya. "Kai da kaya duka mallakar wuya ne Dattijo Maharaz! Na baka wuƙa da nama, ka ƙaraso ka warware mini zare da abawa don tun tafiyarka ka bar ni a cikin duhu." Dattijo Maharaz ya ruƙo hannun Kamalu suka ƙarasa cikin rumfar suka zauna, da idanu su Fulani Umaima suka bi su da kallo. "Ko ba ka faɗa mini ba, na san ka sha gwagwarmaya farin Dattijo mai farar zuciya da dattako!" Sarki Abdul'aziz ya yi maganar cike da girmamawa. "Kusan alhakina ne yin hakan Abdul'aziz, kuma na yi farinciki da na sauke wannan nauyin da yake kaina. Ga ɗanka nan halak-malak na dawo maka da shi, Kamalu ga mahaifinka nan kai ɗan gaban goshi ne, mai gata ne kuma ɗan asali ne kai." Da mamaki Kamalu ya dubi Dattijo Maharaz. "Ni ɗin kuma Dattijo Maharaz? Ka san me kake faɗa kuwa? Ka manta me Baffajo ya furta mini dangane da asalina?" "Akwai tarun tambayoyi a bakina Dattijo Maharaz ban san yadda aka haihu a ragaya ba." Sarki Abdul'aziz ya faɗa a sanyaye. Dattijo Maharaz ya saki murmushi irin nasu na manya sannan ya nuna Fulani Umaima. "Ba za a taɓa jin mutuwar Sarki a bakina ba Abdul'aziz, Umaima ita za ta warware mana zare da abawa domin ita ce ta san yadda aka haihu a ragaya." *SHU'UMAR MASARAUTA* *32* .*Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Bayan ɗaurin auren sabon Sarki Sulaiman da Fargi cikin farinciki ya shiga ɗakin da take zaune a takure wuri ɗaya ta zuba uban tagumi. "A yanzu wannan lokacin ba na damuwa ko ɓacin rai ba ne!" Sulaiman ya furta yana harɗe hannuwansa biyu a ƙirji haɗe da sakin murmushin farinciki. Ɗagowa ta yi ta goge hawayenta a madadin ta yi walwala sai ta sake fashewa da ƙuka, jiki a sanyaye Sulaiman ya ƙarasa wurinta. Ta sunkuyar da kai ƙasa tana murza yatsun hannuwanta. "Na so a ce zamu yi rayuwar farinciki tamkar yadda sauran ma'aurata suke gudanar da rayuwarsu, sai dai kash! Ba lalle mu samu wannan damar ba. Domin ina tsoron ranar da Shugaba ko wani daga cikin dangina zai bankaɗa labulen sirrinmu...." Da sauri ya ƙarasa ya rufe mata baki yana sauke ajiyae zuciya. "A duk lokacin da kika yi wannan furucin ƙirjina yana bugawa, don Allah a duk lokacin da za ki yi tunani ki dinga yi mana na alkairi." Gyaɗa masa kai ta yi sannan ya ajiye mata gasassun 'yan shilan da ya sa aka gasa musu. Sannu a hankali Sulaiman da Fargi suka fara cin 'yan shilan hankali kwance tun tana noƙewa har ta saki jiki suka ci suka ƙoshi, sai da ya ja ta hira sosai don ya kawar mata da duk wani tsoro da fargabar auren nasu da ke cikin zuciyarta sannan ya ce ta shirya don ya mayar da ita. Murmushi ta sakar masa sannan ta haɗa hannuwanta ta tafa su nan take ta rikiɗe zuwa siffar tantabara, a daidai kan kafaɗar Sulaiman ta hau tana kaɗa fukafukanta. Shafata ya fara yi yana murmushi don ya fahimci tun da ta yi nasa haka ba ta buƙatar ya yi mata rakiya. Sai gab da magriba Sulaiman ya koma cikin Masarautarsu a nan ya tarar an kawo masa amarensa biyu, wani irin takaici ne ya kama shi amma da ya tuna a yanzu Fargi ta zama matarsa sai ya ci gaba da walwalarsa har wasu daga cikin dangi suna tsokanarsa wai har ya sauko daga ƙiyayyar auren, saboda da farko ya nuna gabaɗaya ba ya ƙaunar auren haɗin da za a yi masa. Boka Shaddas bayan ya mayar da littafin yana juyowa daga can wurin wannan rijiyar ya ji wata irin kuɗa ta ratsa majiyar sautinsa, ajiyar zuciya ya sauke don tun da ya ji wannan kuɗar ya san akwai wani muhummin taron gaggawar da ake buƙatarsa a fadar Sarkin Aljanun dajin Hubud. Sai da ya ƙarasa wurin Basiru sannan ya furta, "A yanzu haka na samu kiran gaggawa daga wurin madogarar da suke ba ni ƙwarin gwiwa dangane da sirrin tsafi da sihirina, duk wani aiki da ba zai gagare maka ba ka aiwatar da shi don na san kai ɗin gwani ne kuma hatsabibi ne." Wani ƙasaitaccan murmushi Basiru ya saki har sai da gaban Boka Shaddas ya faɗi, don bai san dalili ba haka kawai yake jin zuciyarsa na wasu-wasi a kan Basiru. "Yaushe za ka dawo? Don gaskiya ina da aikin da zan aiwatar a cikin tsakiyar dare kuma ba na jin a nan zan aiwatar da shi." Basiru ya faɗa wa mahaifinsa wannan maganar don ya kawar da tunaninsa daga zarginsa. A fili Boka Shaddas ya faɗaɗa fara'arsa munun fuskarsa ya ƙaru, kalaman Basiru suka yi tasiri a ransa. "Ka yi mini uzuri ba na jin zan shafe sa'a guda." Basiru na gama sauraron mahaifinsa ya wuce can bakin wutar da Boka Shaddas ya tanadar masa wacce yake binciken duk wani abin da ya shafi al'amarinsa na tsafi. Shugaba Zurufu ƙuri ya yi wa Jakadiya da ke gursheƙen kuka, kuma ya yi mamakin ganinta bayan ya san Boka Shaddas ne ya yi mata iso a can kwanakin baya. Yana shirin katse kukan nata ta sake rushewa da kuka tamkar wacce saƙon mutuwar Mahaifyarta ya riske ta. "Ya shugaba mai shugabancin wannan yankin ka taimaka miki ka shiga lamarina, duniya ta yi mini ƙunci yayin da bala'o'i suke rufto wa rayuwata da ta 'yar auta." "Shaddas ya jima yana yaudararki don haka matsawar kika taɓe a wurinsa buƙatarki ba za ta taɓa biya ba." Shugaba Zurufu ya furta wa Jakadiya yana watsa wata jar ƙasa saman allon ƙarfen da ke ƙonewa a kan wuta. "Na jima da fuskantar haka Shugaba don haka na sato ƙafa a yanzu da na kawo ziyara wurinka domin kaine mai share mini hawayena." "Abu ɗaya za ki yi mini matuƙar kina son buƙatarki ta biya, ni nan da kike gani tun da na sa tsafi a gaba nake ganin ci gaba don haka tsafi ba zai taɓa ba ni kunya ba. Yau ina matashiya Fargi da ke nuna za ta iya kara wa da ni, tana in a yanzu? Babu ita tun da na shafe babinta. Jakadiya buƙatarki za ta biya kamar yadda na faɗa miki amma sai kin kawo mini Basiru ɗan Boka Shaddas, kuma sai kin haɗo mini da littafin hannunsa. A yanzu haka zancen da nake yi miki Basiri ya mallaki wannan kundun littafin domin ba ƙaramin hatsabibi ba ne, Duk hatsabibancin mahaifinsa shafar mai ne a kansa. Idan kika cika wannan Umarnin Sailuba za ta warke, zan iya kashe miki Umaima idan kuma sabautata kike buƙata ayi nan take zan zartar da shi." Baki na rawa Jakadiya ta furta, "Shugaba a baya Boka Shaddas ya sha yi mini irin wannan alƙawarin amma ko kaɗan ba ta sauya zani ba..." "Dataka Jakadiya! Shaddas ko ƙafarmu bai kama ba ballantana ki haɗa tsafina da na shi, idan kika kuskura kika sake yi mana wannan furucin za mu shafe ki a doron ƙasa." A razane Jakadiya ta hau girgiza kai, ta zube ƙasa tana ba shi haƙuri sai da ya karɓi tubanta sannan ya damƙa mata magunguna da kayan binne-binnen da za ta yi, ta shiga zabga masa godiya har ta juya za ta tafi Shugaba ya dakatar da ita. "Waccan ziyarar Boka Shaddas ne ya biya miki tukwicin ziyararki, a yanzu kuma dole ki biya wa kanki domin wannan zuwan kanki da kanki ne." Gaban Jakadiya ya faɗi, a sanyaye ta furta. "Mene ne tukwicin ya shugabana?" "Tun da wannan zuwan da kika yi zai zame miki tamkar zuwan farko ne, da farko zan haɗa ki da ɗan autan baƙaƙan aljanun ƙasan ruwa ya yi mu'amala da ke." Da sauri Jakadiya ta ja da baya hannuwa biyu dafe a ƙirjinta cikin tashin hankali ta furta. "Yau ni Salame na shiga uku na lalace! Shugaba ka yi mini rai kada ka yi mini haka wallahi rabona da wannan lamarin har na manta, marigayi Malam Bukar yau shekara Ashirin da biyu kenan." Shugaba Zurufu ya tamke fuska don tuni Jakadiya ta fara tunzura shi, ya nuna ta yatsa yana faɗin. "Kada ki kawo mana wargi yanzun nan na mayar da ke Fanteka ko kumbo. Jakadiya wannan doka ce ga duk wanda ya ziyarce mu a ziyararsa ta farko. Don haka da ki amince da karki amince Aljani Buguzu zai amarce da ke a daren yau, gata ma na yi miki da ban haɗa ki da Bulku ba, domin shi zai iya yin fata-fata da ke." Jakadiya ba ƙaramin firgici ta shiga ba, cikin tashin hankali ta fashe da kuka har da majina tana faɗin. "Ka yi mini rai Shugaba kada ka sa Aljani Buguzu ya turmushe ni wallahi ni ko ɗan autan bunsuru ban taɓa ma'amala da shi ba, idan ka haɗa ni da ɗan aljan ban san ta ina zai fara ba, ka dube ni komai ya ƙare ya tsumbure." Rai a haɗe Shugaba Zurufu ya ce. "Na rantse da gawurtar tsafin da ke cikin dajin nan da muka gada tun iyaye da kakanni idan kika sake magana sai na shafe ki Jakadiya. Ki fice ki ba mu wuri don yanzu haka Buguzu yana can yana amsar horo daga wurin Kabdu." Jakadiya ba ta sake furta koda kalma ɗaya ba, sai kuka da ta saje rushewa da shi ta fice daga cikin tsibirin don rabonta da sharɓar kuka kamar wannan tun mutuwar marigayin mijinta. Tun da Dattijo Maharaz ya fara magana Fulani Umaima ta yi wata irin zabura, cikinta ya yi wata irin murɗa wani irin zazzafan gumi ya fara keto mata. "Me... kake faɗa... ne? Wai ma... waye.. kai?" Fulani Umaima ta yi maganar cikin in'i'na. "Ranka shi daɗe me wannan tsohon yake faɗa ne? An ya ba mahaukaci ba ne..." Tun Muhsin bai gama magana ba Sarki Abdul'aziz ya sauke masa yatsu biyar a fuska. "Idan kuka nemi ku kawo mana rashin ɗa'a ranku zai yi mummunan ɓaci." Ilahirin mutanen da ke wurin jikinsu sanyi ya yi, hatta Abubakar ganin haka sai da ya sa shi ya fashe da kuka yana janye jikinsa daga Sarki Abdul'aziz don gani yake tamkar shi ma zai hukunta shi. A jikin Kamalu ya kwanta, ya saka hannuwa biyu ya riƙe shi yana cusa kansa a jikinsa. "Wannan da kuka gani ba iya kaka na ɗauke shi ba, na ɗauke shi jini da tsokar jikina. Ina matuƙar girmama shi har ban san yadda zan fasalta girma da matsayinsa ba. Ba kai ba ko mahaifiyarka ba ta isa ta furta magana marar daɗi a kansa ba." A wannan karon tuni Fulani Umaima ta yi fuƙai-furƙai, ban da goge gumi babu abin take yi. "Dattijo Maharaz kalamanka na shirin kawo ruɗani a cikin iyalina, ban fahimci abin da kake nufi ba." "A ƙallah na yi zamani da mahaifin kakanka Abdul'aziz, a zubi da tsarina ka san ni ba yaro bane. Ina da zuri'a ina da 'ya'ya da tarin jikoki, idan na furta waɗanan kalaman don na kawo ruɗani ko tashin hankali a tsakaninka da iyalanka shin wacce riba zan ci? Ka na tunanin zan furta maka ƙarya ne Sarki Abdul'aziz?" Kunya ce ta lulluɓe Sarki Abdul'aziz da jin kalaman Dartijo Maharaz, ba tun yau ba ya kan ji ana cewa wasu daga cikin jinsin Aljanu sun iya sharara ƙarya musamman idan suka fahimci mutum yana anfani da abin da suke faɗa. Amma a wannan fannin zai iya bugar ƙirji a ko ina ya tsame Dattijo Maharaz daga cikin waɗanda ake wa kallon maƙaryata. "Ba haka nake nufi ba Dattijo Maharaz, ina fatan za ka yi mini kyakkayawar fahimta farin jakada. Duk magidancin da ya tsinci irin waɗannan kalaman a kan iyalansa dole zai samu shakku da shiga ruɗani Dattijo Maharaz." Murmushi Dattijo Maharaz ya saki sannan ya furta. "Na fahimci kalamanka Sarki Abdul'aziz amma ka san bahaushe yakan ce dole gyaɗa ta yi mai idan ta ƙi ta sha matsa, ka matsa matarka iya bakin ƙoƙarinka na tabbata za ta fito da duk bayanan da kake buƙata. Idan kuma hagu ta ƙi sai a koma dama amma kuma kafin wannan waƙa a bakin mai ita ai tafi daɗin sauraro." Sarki Abdul'azizi juyar da kansa ya yi yana kallon Fulani Umaima da ita kaɗai take ta zabga uban gumi. "Ya aka yi yaron nan ya zama ɗana alhalin ban san da haihuwarsa ba? Wace ce mahaifiyarsa? Kuma ya aka yi ban san da ciki da haihuwarsa ba? Ba yau nake tare da Dattijo Maharaz ba na tabbata ko wanina ba zai yi wa ƙarya ba ballantana ni da zuri'ata." Sarki Abdul'aziz ya yi maganar yana tsare Umaima da idanu. "Ba ni da ɗaya daga cikin amsoshin tambayoyin da kake tuhuma ta a kai. Me ya sa haka Ranka shi daɗe? Me ya sa sai ni za a tuhuma da irin wannan maganganun alhalin ba ni kaɗai ce iyalinka ba?" Fulani Umaima ta yi maganar cikin nuna dakiya da ƙwarin gwiwa. "Umaima!" Sarki Abdul'aziz ta ambata da wata irin muryar da ba su taɓa jin ya yi magana da ita ba saboda tsananin ɓacin rai. "Wane ne yaron nan?" "Ban san shi ba" "Idan ba ki san shi ba ai kin san Boka Bamaguje ko?" Dattijo Maharaz ya wurga mata tambaya. A razane Fulani Umaima ta dubi Dattijo Maharaz a fili cikinta ya ba da sautin ƙuuuu! Har sai da Yarima Muhsin da Sailuba suka bi ta da kallo. Boka Shaddas sai da ya jima da fita sannan Basiru ya miƙe zuciyarsa ƙal ya fara takawa har ya isa bakin ramin da mahaifinsa yake ɓoye littafin, sai da ya gudanar da duk wani abin da mahaifinsa yake yi na tsaface-tsaface kafin ya ɗauko littafin sannan littafin ya fara tutsowa daga ƙasa. Sai da ya gama fitowa ya saka hannu ya ɗauka ya ƙyaƙyace da wata mahaukaciyar dariya, ya jima yana yin mai isarsa sannan ya ɗauki wata farar takarda ya ajiye ta a ƙasa ya sa sandar tsafinsa ya bugi farar takardar nan take takardar ta rikiɗe zuwa surar littafin da ya ɗauke daga cikin wurin. Rungume littafin ya yi a ƙirjinsa babu jimawa ya ji wani abu ɗaaau tamkar ya harbi zuciyarsa, da sauri ya ɗago littafin yana ƙare wa bangon littafin kallo sai ya sake mayar da shi ƙirjinsa ya rungume da hannunsa ɗaya. Har ya je ƙofar fita daga kogon dutsen sai ya hangi wani kurtun giya, ya ɗauko shi ya ɗaga kansa ya ɗaɗɗaka sannan ya fice kai tsaye ya nufi cikin Masarautar Huddam. Jakadiya tun da ta koma ɗakinta ta shiga saƙa da warwarar makomar rayuwarta, a ganinta wannan karon tonen kaza da ke iya kaita ta tono wuƙar yanka kanta ce ya faɗo kanta. Da farko ta karaya sosai, amma da wani tsagin zuciyar tata ya hararo mata irin cin zarafin da za ta yi wa Fulani Umaima kuma Sailubanta ta warke sai wata irin ƙwarin gwiwa ya ratsa ta. Miƙewa ta yi ta ɗauki garin maganin da Shugaba Zurufu ya bata, ta juye shi a cikin ƙwarya ta tuɓe kayanta sai da ta kullo ƙofar ɗakinta sannan ta fara faɗin waɗansu sunaye tana yi tana watsa ruwan ajikinta sannan ta yi turaren sihirin da ya bata. Tana gamawa kuma fargabarta ta koma kan hanyar da ta samu damar ganin Basiru, don ita sai a lokacin ma ta ga wawtarta saboda a ɗebe ta haure sama da kwana biyar ba ta saka shi a cikin idanunta ba. "Ki je sashensa mana!" Tsagin zuciyarta ya ba ta amsa. "Wataƙila ma idan kika samu damar kai masa Basiru yau ya fasa haɗa ki da ɗan autan aljanin da zai turmushe ki." Zuciyarta ta sake raya mata. A gurguje ta saka kayanta ko garin maganin jikinta bai gama bushewa ba ta fice daga ɗakinta, kai tsaye ta wuce sashen Fulani Umaima sakamakon soronsu ɗaya sai dai ɓangaren su Yarima Muhsin daban na Fulani Umaima daban. Tun daga bakin ƙofa Jakadiya ta fara jin waɗansu irin surutan Basiru har sai da tsora ta, leƙawa ta yi ta windo ta hango shi yana birgima duk ya ɓata jikinsa da aman giyar da ya sha, a gefe ɗaya kuma littafin da ya ɗauko yana riƙe a hannunsa na hagu. Da sauri Jakadiya ta faɗa ɗakin jikinta har rawa yake ta tsugunna a gabansa, "Barka da hutawa Saraki!" Jakadiya ta furta don ta ga irin yanayin amsar da zai ba ta. "Ki... tafi ni na... gama da sh... na... ɗauke masa... littafin... tsafi ya... ba ni... dama..." A fili Jakadiya ta saki murmushi ta riƙo hannunsa da ƙarfin gaske sannan furta. "Zuruful-Bukusu Barduku kass." Sai da ta furta haka sau uku sannan suka ɓace daga wurin, suka buɗi ido a cikin kogon dutsen Shugaba zurufu. Da matsanancin mamaki Shugaba Zurufu yake bin Jakadiya da kallo, miƙewa ya yi jiki na makyarkyata ya ƙarasa gaban Basiru sannan ya ɗauke littafin da ke hannunsa. A lokacin da zai ɗauke littafin har sai da Basiru ya ɗago da sauri, Shugaba Zurufu ya hura masa sihirtacciyar iska, take Basiru ya faɗi gefe guda jikinsa ya yi wani irin laushi yana numfashi kaɗan-kaɗan. "Kin cika jajirtacciya Jakadiya, don haka ya zame mini dole na biya miki buƙatarki." Al'amuran da ke faruwa ba ƙaramin dagula wa Kamalu kwanya suka yi ba, tun tasowar shi sam ba shi da son hatsaniya ko tashin hankali don haka ya miƙe tsaye ya furta, "Dattijo Maharaz ni dai zan je wurin Baffajo, ka gafarce Ranka shi daɗe idan har na yi kuskure a kalamaina." Kamalu ya ƙarasa maganar yana russuna wa Sarki Abdul'aziz. Tausayin Kamalu ya kama Dattijo Maharaz, idanunsa suka ciko da ƙwalla sannan ya furta. "Tun da kake ba ka taɓa jin ɗuminsa ba, ba ka taɓa jin gatan da kowanne mai uba yake ji ba musamman da ka kasance asalin mai gata gaba da baya. Don Allah Abdul'aziz ka rungume yaron nan ko ya ji abin da sauran 'ya'ya suke ji." Tun ba rufe baki ba Sarki Abdul'aziz ya riƙo hannunsa, Kamalu sororo ya yi yana jinjina taushin hannun Takawa saɓanin na shi da ya saba da wahala da yake tamkar katako saboda tauri. Mamakinsa ya ninku da ya sake jin Takawa ya rungume shi tsam a jikinsa. "Wai yau nine a tare da Mai martaba ko idanuwana da gangar jikina ne suke yaudarata? Ya Allah idan mafarki nake yi kada ka farkar da ni yanzu domin na ji irin ni'imar da masu mulki suke ji a rayuwarsu." Kamalu ya yi maganar a hankali, a tsammaninsa a cikin zuciyarsa ya yi ta. "Ba mafarki kake yi ba Kamalu, idan kuma kana tantama yanzu ne za ka tabbbatar da haka." Dattaji Maharaz ya furta yana nuna bangon ɗakin Sarki Abdul'aziz. "Ya kai Dattijo Maharaz shin me ye dalilinka na yi mini kutse a lokacin da nake gudanar da aikina a cikin halwar tsafina?" Bamaguje ya yi maganar cike da damuwa. "Ina neman afuwarka Boka Bamaguje bisa shiga haƙƙinka a daidai gaɓar da ba ka tsammace ni ba. Shin ko ka san wannan baiwar Alahr da bawan Allahn nan?" Dattijo Maharaz ya nuna Fulani Umaima da Kamalu. "Wacce irin magana kake yi mini Maharaz? Tambayar wannan a wurina tamkar cin fuska ne da cin zarafina domin Umaima jinina ce 'yata ce ta cikina halak-malak ni ne mahaifinta. Shi kuma wannan yaron ban san shi ba, sai dai zan iya shiga halwar tsafina na bincika tauraronsa..." "Ƙarya kake Bamaguje! Wallahi ƙarya kake ni ba 'yarka ba ce. Wallahi sharri zai yi mini ranka shi daɗe ni ban san shi ba ban ma taɓa ganinsa ba." Murmushin Dattako Dattijo Maharaz ya saki. Lokaci ɗaya fuskar Bamaguje ta murtuke rai a ɓace ya nuna Fulani Umaima ya furta. "A yau ba sai gobe ba na rantse da girman tsafina da sihirin da nake taƙama da shi sai na nuna miki ke ɗin 'yata ce babu wani mahaluki da zai sake yi mini iko da ke." *SHU'UMAR MASARAUTA* *33* *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Jin kalaman Shugaba Zurufu ya sa kan Jakadiya ya sake girma, ta sunyar da kai ƙasa tana sakin murmushin farinciki. A ɓangare ɗaya kuma tana addu'ar Allah ya tsallakar da ita daga mu'amalar da aka ce ɗan autan aljan zai yi da ita. Kamar Shugaba Zurufu ya shiga ranta ya furta mata. "Ban taɓa tsammanin samun biyan buƙatar nan tawa a cikin ruwan sanyi ba, don haka Jakadiya mun ɗauke miki mu'amala da ɗan auta Buguzu. Sannan a daren yau ba sai gobe ba zan fatsama gudanar da aikinki a cikin halwar tsafina." Jakadiya ta sake sunkuyar da kai sannan ta fara zuba masa godiya, wata jar tsoka ya ɗauko ya miƙa mata wacce take ɗigar da wani baƙin jini mai wari. "Ki je ƙarƙashin gidan tururuwa ki binne ta a ciki, bayan kwana biyu ki saurari abin da zai biyo baya." Cikin matsanancin Farinciki Jakadiya ta miƙa hannu za ta karɓa da sauri Shugaba Zurufu ya matsar da hannunsa sai da ya jefa tsokar naman a ciki wata 'yar jakar fatar ya sake miƙa mata. "Kin so ki yi ganganci Jakadiya, da a ce kin taɓa wannan tsokar da duk abin da na yi niyyar ƙulla wa Umaima kanki zai faɗa." A razane Jakadiya ta ja baya, Shugaba Zurufu ya saki murmushi sannan ya Sallame ta. Har ta juya za ta tafi ta dawo da sauri idanunta a kan Basiru ta furta. "Ya kai Shugaba Zurufu shin a ta yaya zan iya mayar da Basiru cikin masarautar Huddam? Ina tsoron kada asirina ya tonu." "Wannan ba aikinki ba ne Jakadiya! Ki bar mini komai a hannuna ni zan aiwatar da komai." Tsoro ne ya mamaye Jakadiya don sai a yanzu wani tunani ya faɗo mata. "Shugaba ina fatan ba za ka hallaka shi ba, domin ina tsoron kada wani abu ya faru da shi ni ma na shiga uku." Jakadiya ta yi maganar a firgice. "Babu abin da zai faru da shi Jakadiya, kuma kada wannan ya dame ki domin zan aika wani aljanin ya rikiɗe zuwa surarsa ta yadda wani ba zai fahimci ba shi ba ne." Sai a lokacin Jakadiya ta sauke ajiyar zuciya sannan ta fice daga kogon dutsen tana jin zuciyart fes tamkar buƙatarta ta gama biya gabaɗaya. Bayan fitar Jakadiya runtse idanu Shugaba Zurufu ya yi ya fara karanta waɗansu ɗalasuman tsafi, ya ɗan jima yana yi nan take kogon dutsen na shi ya rufe ruf sannan ya zaro littafin yana jin wani shauƙi da farinciki ya lulluɓe shi. Saboda yanayin tsufa hannunsa sai karkarwa yake ya saka hannu ya buɗo littafin nan take ya ga a daidai wurin da Boka Shaddas ya tsaya da karatu. Ya saki malalacin murmushi sannan ya furta. "Tabbas ka rage mini aiki da yawa Boka Shaddas." A wannan karon ba Kamalu ba hatta sauran mutanen da ke cikin ɗakin tsananin mamaki ne ya kamasu, Sarki Abdul'aziz ne ya yi ƙarfin halin kallon Boka Bamaguje don mafi yawan su ba ƙaramin tsoro ya ba su ba. A zaune yake jikinsa babu kaya sai ƙugunsa da ke ɗaure da wata fatar damunsa, jikinsa a lulkuɓe da gashi kansa zagaye da furfura har zuwa fuskarsa da ta yi buzu-buzu babu kyawun gani. "Dattijo Maharaz, tarin tunanninka sun yi wa kwanyata jerin gwanon da na gagara kunce koda ƙulli ɗaya ne, kuma lura da hakan bai sa ka fasa rikito mini da waɗansu ƙullin da suke sake dulmiya kwanta cikin taikun tunani ba. Wane ne wannan bokan da nake jin yana alaƙanta kansa da iyalina?" Dattijo Maharaz ya sake nuna Umaima sannan ya ci gaba. "A yadda na ji Bamaguje ya furta shi mahaifinta ne, ka ga ƙarin bayani muna saurare daga wurinsu Sarki Abdul'aziz. Amma kafin mu kai ga wannan shin Boka Bamaguje ko ka gane wannan yaron?" Bamaguje ya ƙura wa Abubakar idanu sannan ya saki wata irin dariya har sai da sauran mutanen suka ɗan tsorata. "Da a ce Umaima ta nuna ƙima da mutumcina a idanun tarin waɗannan mutanen ciki har da Sarki Abdul'aziz, ina ganin da babu abin da zai hana ban lulliɓa mata bargon rufin aziri na wanke ta ba. Amma tun da ta kwaye mini baya ta nemi cin zarafina, babu abin da zai hana ni bankaɗe mata laluben sirrinta kuma daga ƙarshe ko ta ƙi ko ta so na ɗauke ta zuwa kogon tsafina ta dawwama a wurina." Da ace su Sarki Abdul'aziz na ganin yadda zuciyar Fulani Umaima take bugawa da babu abin da zai hana ba su yi tsammanin tarwatsewarta a wannan lokacin ba. "Wannan yaron tun yana cikin mahaifiyarsa ba baƙona ba ne domin daga shi har mahaifiyarsa, na yi rikitattun ayyuka da dama a kansu. Sannan tsafi ya ba ni nasara don a wancan lokacin zan iya yin komai domin farincikin 'yata Umaima, saɓanin yanzu. A taƙaice dai ni ne na yi asirin da ya kasance shagiri-girbau wato marar hankali." Lokaci ɗaya ɗakin ya ɗauki salati ciki har da Yarima Muhsin da Sailuba. Wani irin tuƙuƙin baƙinciki ne ya turnuƙe zuciyar Sarki Abdul'aziz, a sanyaye ya juya ya ƙura wa Fulani Umaima idanu da ta jiƙe sharkaf da gumi idanunta sauka yi tsilli-tsilli kamar shege a rabon gado. "Kada ka aminta da abin da ya faɗa ranka shi daɗe wallahi sharri yake yi mini! Bakinsu ɗaya da Dattijo Maharaz so suke su haɗa mu da kai. Wallahi-tallahi ban san duk abin da yake faɗa ba." "Umaima shi fa shure-shure ba ya taɓa hana mutuwa! Da tun farko kin mutumta ni ba zan kwaye miki baya ba, kuma wannan ba shi ne karo na farko da kike dagula mini lissafi ba. Don haka Maharaz idan ka gama da ni zan sa a ɗauko mini Umaima mu ƙara gaba." "Amma dai ku tsinannu ne Allah ya tsine muku albarka. Allah ya isa tsaninmu da ku..." Kalaman Sarki Abdul'aziz suka katse sakamakon matsanancin kukan da ya ci ƙarfinsa. Jikin Kamalu ba ƙaramin sanyi ya yi ba, Ruƙayya da ke gefe ta ƙarasa wurin Takawa ita ma ta saka kuka. Shiru ɗakin ya yi sai sautin kukan da ke tashin yayin da Fulani Umaima ke gefe tsuru kamar an jiƙa ɓera a buta. "Sarki Abdul'aziz na jima da jin kalmar tsinuwa a kaina, a bakin mahaifiyata na fara jin ta a farkon fara koyon tsafina lokacin da zan haike mata. Ka ga kuwa faɗarka ba za taɓa ɗaɗa ni da ƙasa ba, tambaya ɗaya na yi shin an gama da ni na ɗauke 'yata na yi gaba ko da saura?" Dattijo Maharaz ya jinjina kai don dama ya san dole ranar za ta zo, ranar da Sarki Abdul'aziz zai ji miyagun labaran da za su nemi tarwatsa kwanyarsa. Ya dubi Bamaguje ya furta. "Ba mu gama da ku ba Bamaguje, shin a tunaninka ɗanyan aikin nan da kuka aikata zai tashi a banza ne?" Cikin halin ko in kula Bagauje ya ɗaga kafaɗarsa sannan ya furta. "Zan ci gaba da gudanar da aikina duk abin da ake ciki ina sauraronku, ke kuma Umaima ki saurare ni." "Wallahi kin yi asara duniya da lahira Umaima, yanzu ke ashe dama 'yar boka ce har kike shuka iskancinki son ranki a gidan nan?" Sailuba ta yi maganar tana wurga wa Fulani Umaima harara. Dafa kafaɗar Sarki Abdul'aziz Dattijo Maharaz ya yi ya girgiza masa kai sannan ya ce. "A iya sanina kai ba mai raunin zuciya ba ne Abdul'aziz, kai jajirtaccan namiji ne me ya sa yanzu za ka aro ɗabi'ar raunanan sarakuna ka yafa wa kanka?" "Na tuno Fatima ne Dattijo Maharaz! Na tuna irin wahala da ƙalubalen da ta fuskata a wurina sanadin yaron nan. Na tuna irin ɗawainiya da faɗin-tashin da ta yi a kan ganin ya samu lafiya, da tarin burukan da ta ci a kansa. Me ya sa kake tsammanin ba zan koka a kan wannan ba? Fatima ta fuskanci ƙalibalen da har abada ba zan taɓa manta shi ba Dattijo Maharaz." Jinjina kai Dattijo Maharaz ya yi sannan ya furta. "Duk da na aminta da kalamanka, kuka bai cancanta a gare ka ba, don a yanzu haka kana gaban wanda yake buƙatar lallashinka shi gabaɗaya ma bai santa ba, bai taɓa ganinta ba hasali ko ɗumin da kowanne jariri yake ji na mahaifiya bai sani ba. Ya kake tsammanin shi zai ji a zuciyarsa?" "Wane ne shi? Ban fahimce ka ba Dattijo Maharaz." Daga bangon ɗakinsa Bamaguje ya furta. "Yaron da ke gefenka! Ina nufin Kamalu abokin tagwaitagar Abubakar. Shi ma ɗanka ne, a ƙiyasi da lissafi shi ne babban ɗanka a maza domin shi ne Fulani babba ta fara haihuwa kafin Abubakar, ina nufin tagwaye ne Hasan da Hussaini. Na san za ka yi mamaki Sarki Abdul'aziz amma ba abin mamaki ba ne idan ka yi la'akari da sunana Boka Bamaguje kuma mahaifin matarka, wataƙila ka ƙaryata kalamaina amma shi Maharaz zai iya tabbatar maka idan ma ƙarya nake ko kuma gaskiya nake faɗa maka." Zumbur Kamalu ya miƙe tsaye yana kallon Bamaguje da Dattijo Maharaz bakinsa sai motsi yake amma ya gagara furta koda kalma ɗaya ce. "Zauna Kamalu!" Dattijo Maharaz ya furta a taƙaice, bayan Kamalu ya zauna ya ci gaba da ce wa. "Na fahimci yanayin da kake ciki Kamalu, Sarki Abdul'aziz ka tura yanzun nan aje a kira maka Baiwa Inna wuro da Baffajo a sashen Bayi. Wataƙila ganin iyayen da Kamalu ya saba da su ya sa shi samun nutsuwa har ya fahimci duk abin da ake tattaunawa." Nan take Sarki Abdul'aziz ya aika Yariman Muhsin don ya kira Dogari Ɗan'Sani da ke can bakin ƙofa, da fitar Muhsin babu jimawa sai ga Dogari Ɗan'San ya shigo. Ɗaga lalubensa ke da wuya idanunsa suka sauka a kan Kamalu da ke zaune shiru hawaye na zuba. "A je a sanar da Jakadiya ta yi gaggauta kawo mana Baiwa Inna wuro da Baffajo." Cikin girmamawa ya amsa sannan ya fice daga ɗakin. Shugaba Zurufu na sauke kansa zai fara karatun littafin ya ji giftawar abu a bayansa, ɗan waigawa ya yi amma bai ga komai ba. Daga can ƙarshen bango Fargi ce a tsaye ta harɗe hannuwanta ta zuba masa idanu, Shugaba Zurufu ganin bai ga komai ya sa ya sake mayar da kansa sannan ya buɗe shafin baya na littafin. Ga mamakinsa sai ya ga shafukan baya duk sun shafe, guntun tsaki yaki ya saki ya girgiza kansa a fili ya furta. "Lallai Shaddas ka cika hatsabibi!" Daga daidai wurin da Boka Shaddas ya tsaya a karatu Shugaba Zurufu ya buɗe ya fara karantawa. "Kin san wace ce masoyiyar ɗan autan Darri?" Sarki Hafiz ya sake furzo mini tambayar don ina tsamani ya zaci ban ji tambayarsa da farko ba. Girgiza masa kai na yi sannan na ji ya ci gaba da cewa. "Sarauniya Hazima! Awancan lokacin ita ta sace zuciyarsa, don a yadda aka ba ni labari ɗan autan Darri ya kasance mai son matan tsiya. Kwatsam sai mahaifiyarki ta wayi gari da jin labarin ɗan autan Darri ya damƙa wa Sarauniya Hazima karagar da ta damƙa masa, a yadda kakana ya ba ni labari kuma an yi hakan babu jimawa a tsokane-tsokanensa ya taɓo 'Yar wani malami da ke ƙasar Saudiyya, babu jimawa mahaifin yarinyar ya ƙone shi ƙurmus don an ce an kai ruwa rana da shi a kan ya fita daga jikinta ya ƙi. A wancan lokacin an ce wannaan labarin ya kaɗa mahaifiyarki matuƙa na rashin masoyinta, a ɓangare ɗaya kuma ta faɗa kogin nadamar damƙa masa karagar mulkin da ya bayar da ita zuwa wani gidan. Sarauniya Hazima ta shimfiɗa mulkinta cikin aminci da salama, hakan ne ma ya ɗan rage raɗaɗin da ke cikin zuciyoyin mahaifanki. Kuma tun da wannan karagar ta koma hannun Sarauniya Hazima sai da ta shekara sama da ashirin sannan ta yi murabus ta damƙa wa babban ɗanta mai suna Sarki Bilal. Tun da Sarautar gidanku ta koma gidan Sarauniya Hazima ba ta sake fita ba har zuwa kaina ni Sarki Hafiz da nake ba ki wannan labarin, akwai sarakuna da dama da aka yi a cikin Masarautar nan wasu sun ɗauki shekaru a kan mulki wasu kuma ba su daɗe ba, a cikin kundin tarihi ma na ji an ce akwai sarkin da kwana ɗaya tal ya yi a kan mulkin Allah ya yi masa rasuwa. Kin san dalili?" Na riski tambayarsa. "Ban sani ba Sarki Hafiz." Na amsa masa a taƙaice don na ƙagu ya ƙarƙare labarin da yake ba ni ko na ji ina labarin iyayena da saurn zuri'ata suke. "Saboda yadda masarautar nan ta ɗauki tsafi da muhimmanci domin cim ma manufar duk wani mai neman ƙudurin hayewa sarauta. Ke ba iya gidan nan ba, zan iya bugar ƙirji na ce miki a duk faɗin nahiyar nan babu wata masarauta da ba sa amfani da tsafi da sihiri, sai dai kin san a komai ba duka a ka zama ɗaya ba amma mafi rinjaye a kan doron haka ake." Kalamansa sun matuƙar ba ni mamaki, ina shirin wurga masa tambaya ya katse ni. "Idan har kin fahimci labarin da na ba ki kin ga asalin sarautar gidan nan ta fito daga gidanku ne, sannan ta faɗo hannun zuri'armu. Amma kin san ya aka yi aka san da cewar ke ce za ki dawo ki karɓi kambun sarautarku?" Da sauri na ɗago na furta masa. "Ina sauraronka sai ka faɗa Sarki Hafiz." Takun tafiyar da Shugaba Zurufu ya ji a bayansa ne ya sa ya yi saurin rufe littafin ya rungume shi a ƙirjinsa ya waiga da sauri, a jikin bangon dutsensa ya ga an yi rubutu da ajami cikin manyan baƙi an saka. "FARGI." A fili ya maimaita sunan nan take gabansa ya yanke ya faɗi, da sauri ya ƙarasa bakin ƙatuwar wutar tsafinsa da ke ci balbal sai da ya saki dariyar mugunta sannan ya wurga littafin ciki. Bayan Fargi ta koma cikin dajinsu ware kanta ta yi a cikin bukkarsu ita kaɗai take sakin murmushi, wani irin farinciki take ji a ranta sai dai kuma ta ci alwashin bin duk wata hanya ta toshe ɓarakar da duk wani daga cikin zuri'arsu zai iya kawo mata dangane da alaƙarta da Sarki Sulaiman, musamman Shugaba Zurufu da take ganin take-takensa na nuna mama hassada a duk lamuranta. Ba mahaifianta ba hatta sauran mutanen zuri'ar Rumzu sai da suka fahimci farincikin da take ciki don haka a ranar ta yi shelar yin aikin sihiri da tsafi kyauta ga duk wanda yake da wata matsala, kuma hatta su kansu Aljanun da suke tayata aiki sai da ta gwangwaje su da tukwicin da take yi musu a duk lokacin da za su taya ta aiki. Kwana biyu a tsakani ba ta ga Sulaiman ba; ba ta ji motsinsa ba hakan ya sa ta shiga matsananciyar damuwa a tunaninta yana can wurin amaransa yana shan amarci don haka wani tuƙuƙin haushi da ɓacin rai ya mamaye ta. Tana zaune a bakin wata ƙatuwar bishiyar tsamiya, hawaye ya shiga gangaro mata. Daga samanta ta hangi inuwar mutum tana ɗagowa karaf idanunsu suka haɗu wuri ɗaya. "Me ya sa ake mini asara hawaye?" "Saboda mamallakinsa ya yi watsi da shi." "In ji wa?" "Zuciyata ce ta sanar da ni." Sarki Sulaiman ya saki murmushi. "Zuciyarki ba ta gaya miki gaskiya ba." Juyar da kanta gefe ta yi ya zagaya ya tsugunna a gabanta. "Kwana biyu kin ji ni shiru ko ki tuntuɓi lafiya Fargi." Wani abu ta ji ya soki zuciyarta sai da ta haɗiyi yawu mai ɗaci ta ce. "Saboda ba na son shiga hurumin matanka." Ya fahimci kalamanta cike suke da kishi, sai da ya yi murmushi a fakaice ya ruƙo hannunta. A sanyaye take bin sa da kallo, ta ji ya ce. "Na zo tafiya da matata." Rass! Gabanta ya faɗi, bai jira cewarta ba ya ƙarasa da ita wurin dokinsa, ilahirin jikinta ban da karkarwa babu abin da yake yi. Ya fahimci tsoronta a fili amma sai ya yi tamkar bai son tana yi ba, sai da ta zauna sosai sannan ya hau suka fara tafiya. Sun kusa fita cikin gari Sulaiman ya shafi saman kan dokin da suke kai take suka ɓace, zuciyarsa fes don a yadda mahaifansa suk matsa masa a kan iyalinsa alwashi ya ci ba zai fara sanin kowacce macce a duniya ba sai Fargi domin ita ce zaɓinsa. Bawa Ɗan Sani har ɗaki ya ƙarasa ya sanar da Jakadiya a lokacin ta dawo daga binne tsokar da Shugaba ya ba ta babu jimawa, ko da Bawa Ɗan Sani ya sanar da ita saƙon Takawa ba ta kawo komai a ranta ba, har za ta wuce Bawa Ɗan Sani ya yi ƙasa da murya sannan ya sanar da ita ganin idanunsa biyu ya ga Kamalu a turakar Sarki Abdul'aziz. Jakadiya tana isa ɗakin Inna wuro ta same su suna zaune suna 'yar hira ita da Mai gado da Jawahir, sai da ta sanar da ita saƙon Takawa bayan sun fito Jakadiya ta ɗan tsegunta mata ganin Kamalu da Bawa Ɗan Sani ya ce mata ya yi, amma da sharaɗin idan da gaske ne za ta ba ta tukwici, cikin farinciki Inna wuro ta amince ta leƙa ta gaya wa Mai gado saƙon farincikin da ta ji a wurin Jakadiya, ta yi maganar tana yin ƙasa da murya. Sun nufi hanyar fita daga sashen Bayi suka haɗu da Baffajo a nan suka sanar da shi saƙon Takawa, gabaɗaya suka nifi hanyar sashen Mai martaba ta bayanta Jakadiya ta ji ance. "Jakadiya zan biyo ku." Muryar Basiru ta ji, nan take gabanta ya faɗi da ta tuna Shugaba ya ce mata zai turo aljani a surarsa, amma gudun kada wani ya fahimci lagonta ta wayance da cewar. "Mu je mana ranka shi daɗe Basiru dama ai wurin Takawa za mu je." Jawahir da ke laɓe a bayansu sai da ta ga sun wuce sannan ita ma ta rufa musu baya. Da sallama gabaɗaya suka shiga cikin ɗakin jikin Inna wuro sai rawa yake tana fargabar abin da za su tarar, Jakadiya ta yi turus tana kallon mutanen da ke cikin ɗakin. "Faɗuwa ta yi daidai da zama Maharaz! Ina buƙatar sa bakin Jakadiya akan ƙaryatawar da Umaima take mini dangane da aikin yaron nan da na yi Abubakar." Boka Bamaguje ya yi maganar yana nuna Jakadiya. Jawahir na zuro kanta cikin ɗakin kanta ta ji ya yi wata irin sarawa, juya ta fara ɗaukanta. Wani irin luuu ta ji tamkar ana fisgarta, "Ki buɗe rijiyar uwar ɗakin nan domin wannan aikinki ne. Dalilin haka ya sa tun farko ban ɗago zancanta ba tun da ba hurumina ba ne." Dattijo Maharaz ya furta wa Jawahir. *SHU'UMAR MASARAUTA* *34* *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Tun da suka fara tafiya tsakanin Fargi da Sulaiman babu wanda ya tanka wa ɗaya daga ciki, kallo ɗaya idan ka yi wa Fargi za ka fahimci matsanancin tsoron da take ciki. Har sun kusa fita titi ta waigo a hankali ta furta. "Haka kawai nake jin zuciyata tana bugawa, bugawar da ke alamta mini wataƙila wani al'amari ya faru a cikin zuri'ata." "Saboda me kike tunanin haka bayan kin ɗinke duk wata ɓarakar da Shugaba zai iya gano halin da muke ciki?" Sulaiman ya furta yana ɗan dakatar da dokin da suke kai. "Na fi kowa sanin waye Shugaba Zurufu! Na san bibiya da hatsabibancinsa, jikina yana ba ni zai iya bankaɗa labulen sirrina ko ba yanzu ba, kar fa ka manta ni ce mace ta farko da na auri ɗan wata zuri'ar da ba tawa ba, shi ya sa..." Sarki Sulaiman ya katse ta. "Ni kuma ina ji a jikina babu wani abu da zai faru da mu In shaa Allah." "Me ya sa kake da ƙwarin gwiwa idan ka ambaci abin bautarku?" Ta wurga masa tambay. "Saboda na gasgata Shi a matsayin Ubangijin sammai da ƙassai." Ajiyar zuciya ta sauke ba tare da furta komai ba, sannan ya kaɗa linzamin dokinsa suku fara tafiya. Da fara tafiyarsu babu jimawa sai Fargi ta rikiɗe zuwa surar Tantabara ta ɗane saman kafaɗarsa har suka ƙarasa cikin Masarautarsu. Shigar Sarki Sulaiman tare da tantabarar da ke kafaɗarsa ya sa kallo gabaɗaya ya koma kansa, duk da ya san Fargi ba za ta ba shi kunya ba amma sai da ƙirjinsa ya buga yana tsoron kada a gane abin da yake tare da shi. "Jarumin Sarakai daga ina ka samu kyautar wannan kyakkyawar tantabarar da ke kan kafaɗarka? Ta yi matuƙar birge ni ka san ni da son tsuntsaye." Mahaifiyar Sarki Sulaiman ta furta a lokacin da ya shiga sashenta ya gaishe ta. Cikinsa ne ya karta don lokaci ɗaya ya ji kansa ya kulle, "Amm... dama.. wani abokina ne ya... mini kyautarta ɗazu." Jinjina kai ta yi sannan ta ɗan haɗe fuska babu alamar wasa. "Sulaiman!" Ya ɗago a sanyaye don ya san tatsuniyar gizo ba ta wuce ta ƙoƙi, ya san maganarta ba za ta wuce a kan matansa ba ne. "Yau kwana huɗu da ɗaurin aurenka amma babu wani bayanin farinciki da Jakadiya ta sanar a masarautar nan, kasan dai gabaɗaya idanun masarauta yana kanka ko?" Sai da ya ɗan waiga ya dubi Fargi da ke cikin siffar tantabar, ya ɗan sunkuyar da kai ƙasa yana jin babu daɗi sannan ya ce. "Allah ya taimake ki kin san tun kafin auren nan ba ni da lafiya, yanzu haka ƙafafuwana ne suka riƙe mini shi ne na ɗan zaga bayan gari. Amma In shaa Allahu za a yi abin da ya dace." Amsa masa ta yi sannan ya yi mata sallama ya fice. Kai tsaye turakarsa ya ƙarasa, tun bai ƙarasa shiga ba ya kira Jakadiya ya gargaɗe ta akan baya buƙatar ganawa da kowa har zuwa wayewar gari. Inna wuro na kai idanunta kan Kamalu da sauri ta ƙarasa wurinsa ta riƙo shi idanunta na zubar da ƙwalla, kamar ƙaramin yaro haka ta fara tattaɓa fuskarsa tana duba jikinsa cikin kuka ta furta. "Kamaluna ina ka shiga? Babu dai abin da yake damunka ko yake yi maka ciwo?" Kamalu ya sake lafewa a jikin Inna wuro tamkar wani zai ƙwace shi, ya ɗaga kai yana kallon Baffajo ya ce. "Inna don Allah ki daina kukan nan kowa yana kallonki." Maganar Kamalu ta so ba wa Dattijo Maharaz dariya, jin yadda Kamalu yake maganar a shagwaɓe. "Baffajo bismillah zauna." Sarki Abdul'aziz ya faɗa. Jakadiya na ganin kamar hankulan mutane ba ya kanta ta juya har za ta fita Bamaguje ya katse ta. "Maharaz ka dakatar da Jakadiya za ta ba da shedata." Kallon da Sarki Abdul'aziz ya wurga mata ne ya sa jikinta ya yi sanyi gabanta ya ci gaba da faɗuwa, ta koma tsumu ta zauna. Tun da Jawahir ta leƙo cikin ɗakin Yarima Muhsin ya kasa zaune ya kasa tsaye, wani irin bugu zuciyarsa take yi tamkar za ta yi tsalle ta faɗo daga ƙirjinsa. Idanunta a saman fuskar Kamalu ta sake jingina a jikin ƙofar ɗakin, haka kawai ta tsinci kanta da shiga farincikin da ita kanta ba ta san dalili ba, duk da Kamalu ya kasance abokin faɗanta. Kamalu da har lokacin yake gefen Inna wuro ya ɗago ya wurga mata harara ganin haka ya sa Jawahir ta fara juya idanu tana yi masa fari haɗe da murguɗa baki. "Jawahir!" Dattijo Maharaz ya furta da ɗan ƙarfi, silar haka ya sa ta ɗago da sauri; karaf idanunsu suka haɗu da juna. Ƙuri ta yi tana kallon ƙwayar idonsa wani irin yanayi ya fara ratsa ta, ƙirjinta ya shiga bugu da sauri fat fat fat. Tana shirin juyawa ya dakatar da ita. "Ki ƙarasa ki aiwatar da aikinki." Tun bai rufe bakinsa ba Jawahir ta faɗa cikin ɗakin, tafiyar da ƙafafuwanta suke yi take son dakatarwa amma tamkar wacce ake fusga haka ta ji ana yin gaba da ita. Tamakar kazar da aka jiƙa da ruwan zafi haka Jakadiya ta ƙarasa gefe ta zauna jiki a saluɓe, a madadin aljanin da ke ɗauke da surar Basiru ya koma ɓangaren da Fulani Umaima take sai ya zauna a gefen Jakadiya, suna haɗa ido da Dattijo Maharaz ya yi saurin sunkuyar da kai ƙasa. "Buguzu! Me kake yi a wurin nan?" Dattijo Maharaz ya tambaye shi. Buguzu ya sunkuyar da kai ƙasa sannan ya furta. "An dakatar da matata ya za a yi na tafi." Take cikin Jakadiya ya ɗuru ruwa, fargabarta ta ninku gumi ya ci gaba da keto mata. "Wace ce matar taka?" Dattijo Maharaz ya tambaye shi da sauri don a tsammaninsa Jawahir yake nufi. Buguzu ya ɗago ya nuna Jakadiya ya ci gaba da cewa. "Ga amaryar tawa nan, na ga kun dakatar da ita a hakan ma ɗaga muku ƙafa na yi don akwai babban uzurina da zan aiwatar a daren nan." A razane Jakadiya ta ja baya cikin tashin hankali, har tana faɗawa kan Sailuba ba ta sani ba. "Wallahi ni ba matarka ba ce, ba za ta taɓa saɓuwa ba bindiga a ruwa." "Basiru kana cikin hankalinka kuwa? Jakadiya ce a gabanka idan muka ji makamamciyar wannan maganar ranka zai yi mummunan ɓaci." Sarki Abdul'aziz ya tsawatarwa Buguzu a tsammaninsa Basiru ne. "Wannan fa ba Basiru ba ne Sarki Abdul'aziz! Wannan ɗan autan aljani ne rikiɗa ya yi kamar yadda ni ma na rikiɗe zuwa wannan surar." Inna wuro da Baffajo a tsarace suka dube shi, lokaci ɗaya suka yi firƙai-firƙai da jin kalamansa. "Ɗan autan aljan fa kace Dattijo Maharaz? Basiru fa nake nufi da yake gefen Jakadiya." Mamaki ya sake bayyana a fuskar Sarki Abdul'aziz bayan ya je wa Dattijo Maharaz tambaya. "Ni ma shi nake nufi Sarki Abdul'aziz, amma mu je zuwa mahaukaci ya hau kura za ka tabbatar da zancena." Jawahir na shiga cikin ɗakin ta ji wani irin dum! Tamkar an buga mata guduma a kanta, hannuwa biyu ta sa ta toshe kunnuwanta sai da ta daina jin kuɗar ta cire hannunta. Wata irin ƙara da ƙaraji ta fara ji a wurin rijiyar, a ɓangare ɗaya kuma wani sauti ta ji yana ambatar sunanta sa wata irin murya. A hankali ta ƙarasa bakin rijiyar, ta ɗaga rigarta take tambarin cikinta ya sake fitowa raɗau ya yi jajir, haskensa ya mamaye saman rijiyar tamkar an dasa ƙwan fitila. Hannunta ta kai saman cikinta duk da tana jin ɗumin zafin da ke fita daga cikin tambarin bai sa ta sauke hannunta ba, wata irin ƙara ta sake jin an ƙwallah ta sake kai idonta kan rijiyar da wani baƙin hayaƙi ya fara fitowa. Sauke hannunta ta yi ta sa iya ƙarfinta ta buɗe rijiyar nan take wani irin ƙauri da baƙin hayaƙi ya mamaye ɗakin. Tamkar yadda gajimare yake ƙara haka ilahirin mutanen da ke cikin ɗakin suka fara jin wani irin rugugi, tamkar aradu za ta faɗo musu a tsakar ka. Jawahir ta sauke rigarta sannan ta fito daga ɗakin zuwa rumfa wurin da su Fulani Umaima suke zaune. A wannan karon Fulani Umaima jikinta ya jiƙe sharkaf da gumi, ga wani irin karkarwa da jikinta yake yi saboda matsanancin tsoron ganin yanayin da za ta yi tozali da Baiwa Maimuna. "Wace ce ita Dattijo Maharaz? Me ta aiwatar a ɗakinmu wanda ya sababba wannan rugugin da baƙin al'amura? Shin ko ita ma tana daga cikin zuri'arka ne?" Sarki Abdul'aziz ya yi tambayar a ɗan ruɗe, don lamarin abin da yake faruwa ya daina ba shi mamaki tsoro yake ba shi. "Ko kaɗan ba ta daga cikin zuri'armu Sarki Abdul'aziz, bil'adam ce tamkar kai. Hasali ma wannan yarinyar a shekarin baya mun taɓa tattaunawa a kanta, idan har ba ka manta hirar da muka yi a kan zuri'ar Rumzu da ake shayarwa da Manyan shanu duk ranar juma'a ba." Sarki Abdul'aziz ya mayar da kallonsa wurin Jawahir da ke tsaye a gefe ƙyam, daga bayanta suka fara jin wani irin taku ƙwas kwas kwas tamkar ana taku da takalmi mai tsini. Sautin ba ƙaramin jam hankulan mutanen wurin ya yi ba don haka suka mayar da kallonsu, ita kuwa Jawahir ko motsi ba ta yi ba idanunta sauke a kan Fulani Umaima. Tafe take idanunta a ƙwaƙƙwaƙwale, duk taku ɗaya idan ta yi sai wata irin baƙar ƙura da yana ta faɗo daga jikinta. Kayan jikinta duk sun yi baƙi ga wani irin gashi buzu-buzu da ya lulluɓe ilahirin jikinta. Kallo ɗaya idan ka yi mata ba za ka taɓa tsammanin hallitar bil'adam ba ce sakamakom yadda surar jikinta ta sauya, ganin tana tun karo su ya sa gabaɗaya mutanen rumfar suka miƙe hankali tashe ciki har da ita kanta Fulani Umaima da ta fi kowa shiga tashin hankali. "Shi kenan ƙurunƙus! Ta faru ta ƙare an yi wa mai dami ɗaya sata." Bamaguje ya furta yana tafe hannuwansa haɗe da miƙewa tsaye. Shugaba zurufu ya jima a tsaye yana ƙarewa wutar kallo sannan ya juya da zimmar ya ƙarasa wurin Basiru da ke kwance, a jikin bango ya hangi inuwarta ta yi tsaye riƙe da ƙugu. Ƙuri ya yi yana kallonta sannan ya sauke ajiyar zuwa ya fara tunkarar bangon, kamar yadda yake tunkarar inuwar haka ya lura ita ma inuwar tana tunkaro shi. "Babu wanda ya isa ya aikata mini haka sai ke Fargi! Me kike nema da ni da ba za ki fita daga rayuwata ba?" "Saboda kai ne sila kuma tsanin da ka ɗora ni a doron da neke kai har na dulmiya kogin bakincikin da har duniya ta tashi ba zan taɓa fita daga cikinsa ba. Ka cutar da zuciya da ganagar jikina Shugaba, ka assassa rarrabar zuƙatan da ke cike da shauƙi da begen junansu. Ka azabtar da muradinmu a daidai gaɓar da muke buƙatar kulawar junanmu, ban san sai yaushe za ka goge tabon da ke damɓare a zuciyata ba. Amma ka sani ina mai yi maka kyakkayawan albishir, yadda ka dagula lissafin rayuwarmu daga farinciki zuwa baƙi haka zan dulmiya taka kuma na ƙuntata maka..." "Dakata Fargi! Idan maye ya manta uwar jariri ba za taɓa mantawa ba. Zan sake tunasar da ke bakin rijiya ba wurin wasan makaho ba ne, don haka tun wuri ki kama gabanki idan ba haka ba ranki zai yi mummunan ɓaci." Shugaba Zurufu ya katse ta cikin tsawa jikinsa na karkarwa. "Tun da ka ji makaho ya ce a yi wasan jifa ai kasan ya taki dutse ne Shugaba, har duniya ta tashi matsayinka na shugabana yana nan a idona amma ka sani ni yaɗin mage ce da ba a cinsa a zauna lafiya." Daga haka Shugaba ya ga inuwar Fargi ta ɗauke, gwaruwar ajiyar zuciya ya sauke gabansa na faɗuwa ya juya da niyyar ƙarasawa bakin halwar tsafinsa. Idanunsa suka sauka a kan Basiru da ke kwance tamkar baya numfashi, wani tunani ne ya faɗo masa ya nan take ya kece da wata mahaukaciyar dariya har sa da duka kogon dutsen ya ɗauka gabaɗaya. Can ƙarshen dutsen na shi ya koma ya fuskanci wurin da Basiri yake kwance ya furta, "Zo zo zo." Take tsafinsa ya zuƙo Basiru da ke kwance, zuwa bangon dutsen. Motsa bakinsa Shugaba ya ci gaba da yi Basiru ya ci gaba da zuƙewa cikin jikin dutsen, Basiru na gama shigewa ciki Shugaba Zurufu ya sake kecewa dariya sannan ya furta. "Na gama da babinka Shaddas, ina nan zaune a mazaunina za ka kawo mini kanka, kuma ta hanyarka ne zan cim ma muradina a kanki. Zan taho gare ki Fargi, duk da tsafi ya tabbatar mini da kin mutu amma na yi mamakin sake dawowarki. Zan zo gare ki a wannan karon ba za ki ji ta daɗi ba." Ganin kowa yana neman arcewa Dattijo Maharaz ya miƙe tsaye ya sha gaban Baiwa Maimuna da hallitarta ta rikiɗe zuwa wata siffar, "Tsaya a nan!" "Saboda me za ka dakatar da ni?" "Saboda hallitarki na yunƙurin razana bayin Allah." Dattajo Maharaz ya ba ta amsa. "Ka san irin uƙubar da nake ciki tsawon wanɗannan shekarun? Ka san ƙalubalen da na fuskanta kuwa? Ka san me ake kira duhu da tsanani ko ka san me ake kira da zafin rijiya?" Baiwa Maimuna ta furta ta wata irin murya tamkar za ta fashe da kuka sannan ta ci gaba. "Tun da har ba ka sani ba ka ƙyale ni na zartar da muradin da ke raina, an cutar da ni an zalince ni iya zalinta. An dakusar mini da rayuwa da burinkan da nake shirin cim ma tun a wancan lokacin..." "Ba ke kaɗai aka zalinta ba, an zakinci mutane da dama a wurin nan don haka ki dakata abi komai a sannu." Dattojo Maharaz ya furta mata. Can gefe ta koma ta zauna tana hararar Fulani Umaima, lokaci-lokaci tana yin ƙwafa. Da ƙyar da suɗin goshi Dattojo Maharaz ya shawo kan mutanen cikin ɗakin suka zauna saboda tsoron Baiwa Maimuna, sannan ya dubi Sarki Abdul'aziz ya furta. "A yanzu komai ya kamalla Sarki Abdul'aziz, sai dai na ce maka dabara ta rage wa mai shiga rijiya ya dira ta ka ko ya faɗa da ƙafafuwa. Ina ganin ni zan gusa domin na gama abin da ya dace, nauyi na ɗauka a kaina sai na kare martaba da ƙimar zuri'ar aminina marigayi Muhammad Safwan..." "Amma ta inda aka hau ta nan ake sauka farin jakada, fari mai farar aniya dattijon da sai an bincika dubban al'umma kafin a samu kamarsa. Idan ka gusa a yanzu ni da iyalina ba za mu yafe maka ba Dattijo Maharaz ya kamata ka zauna ka ƙarasa warware mana zare da abawa. " Sarki Abdul'aziz ya katse Dattijo Maharaz. Sai da ya saki murmushi sannan ya furta. "Allah ya gafarta wa Muhammad Safwan! Tabbas jini a duk inda yake jini ne. Ka yi gadon iya furta daɗaɗan kalamai Sarki Abdul'aziz sai dai ko ƙafar aminina ba ka kama ba, zan zauna tamkar yadda ka ce kuma zan yi abin da ya dace amma ba na fatan ka ce na yi maka katsalandan a duk hukuncin da na yanke." Sarki Abdul'aziz ya yi masa jinjina na hannu sannna ya ce. "Gabaɗaya kai da kaya duka mallakar wuya ne tsoho mai ran ƙarfe. Tun daga farkon kogon dutsen Boka Shaddas yake bin ko ina da kallo har ya ƙarasa tsakiyarsa, a tsakiyar kogon dutsen ya tsugunna ya buga ƙasar da tafin hannunsa. Nan take ƙasar wurin ta fara sauya launi sai wurin ya fara rikiɗa tamkar mudubi haka wurin ya fara nuna masa tun daga farkon ɗauke littafin da Basiru ya yi har zuwa ficewarsa da tafiyarsa da Jakadiya wurin Shugaba Zurufu. Wani irin ihu da ƙaraji ya yi ya miƙe a zabure, daƙwa-daƙwan idanunsa suka sake fitowa waje, fuskarsa ta murtuke jikinsa har karkawa yake saboda ɓacin rai. A bakin rijiyar da yake gudanar da tsafinsa ya tsugunna ya rintse idanunsa sannan ya ci gaba da karatan ɗalasiman tsafinsa. Ya jima yana abu ɗaya sannan ya fara surutai cikin matsanancin ɓacin rai. "Na yi rantsuwa da girman tsafi da sihirin da ya zame mini madogara, madogarar da zai ɗora ni a tirbar da babu taɓewa ko da-na-sani. Sai na nuna wa Jakadiya ko an ci birnin kura ba a bawa gawurtaccan kare dillanci, sai na nuna mata ba za ta ci amanata a banza ba sai ta ci ta. Kuma shi ma Basiru sai na hukunta shi da hukunci mai tsanani bayan na fanso gangar jiki da ruhinsa kamar yadda burin Shugaba Zurufu yake." Boka Shaddas yana gama maganar ya haɗe tafukan hannuwansa biyu ya buga da ƙasa, lokaci ɗaya ya ɓace daga wurin. Dattojo Maharaz ya dubi Inna wuro sai da ya sakar mata murmushi ya furta. "An gano iyayen Kamalu." Firgigit Inna wuro da Baffajo suka ɗago suna maimata kalamansa. "Kana nufin Kamaluna an gano iyayensa?" Inna wuro ta sake tambaya murya a sanyaye, gyaɗa mata kai Dattijo Maharaz ya yi a madadin Inna wuro ta nuna farincikinta sai suka ga ta rushe da kuka. Shiru suka yi sai da ta yi mai isarta sannan ta furta. "Ko shi ya sa suka ɗauke mini shi kwana biyu ban sanya shi a idanuna ba? Yanzu raba ni da kai za su Kamalu?" Inna wuro ta ƙarasa maganar tana rushewa da kuka, ta sake ƙanƙame Kamalu kamar wani zai ƙwace shi. "Hai aradun Allah babu mai raba mu da Kamalu, wai ma waye ya gano iyayensa? Ni ban yarda ba kawai so ake a ƙwace mana shi kuma babu wanda ya isa, yaron nan yana tsumma na ɗauke shi da hannuna yanzu katsam rana ɗaya ace an ga iyayensa." Baffajo ya yi maganar yana haɗe fuska. "Duk da sun kasance suna da 'ya'yan da suka haifa sun nuna masa ƙauna tamkar ɗan cikinsu kuma ba su taɓa nuna bambamci a tsakaninsu ba, ni shaida ne a kan kulawa da ƙaunar da suka nuna masa tabbas sun cika jajirtattun iyaye na ƙwarai. "Kalaman Dattijo Maharaz suka ratsa Sarki Abdul'aziz. Farinciki ya mamaye shi bisa yadda ya ga suna nuna masa tsantaar kulawa. "Babu wanda zai raba ku da shi." Sarki Abdul'aziz ya furta fuskarsa ɗauke da murmushi. Da sauri Baffajo ya zube a gabansa, "Allah ya taimake ka ya ƙara maka lafiya, baya goya marayu uban marayu uban marasa gata masu iyaye da gatan ma ka gama musu komai. Mun san kai adali ne don Allah kada ka bari a zalici yaron nan a raba mu da shi." Tun da ya fara maganar Takawa yake murmushi tamkar babu wani tabon ɓacin rai a ransa. "Kai tsaye kana magana da mahaifin Kamalu Baffajo, ina nufin Sarki Abdul'aziz shi ne mahaifin Kamalunku." Ba iya su Inna wuro ba hatta Jakadiya da Jawahir sai da suka razana da jin furucin Dattijo Maharaz, baki na rawa Baffajo ya furta. "Shi ranka shi daɗe shi... shi... ne mahaifin... Kamaluna?" Dattijo Maharaz ya gyaɗa masa kai. "Ina ganin wannan shi zai sake ba wa kowa tabbacin haka." Ya ƙarasa maganar yana nuna jikin bangon ɗakin, gefen wurin da Jakadiya take zaune nan take hoton lokacin da Fulani Babba ta haihu ya fito da shawarar da Jakadiya ta bayar zuwa bayar da Kamalu da Fulani Umaima ta yi a fitar da shi. Sun shagala da kallon abin da ya faru cikin kiɗima, razani da tashin hankali Dattijo Mahazar ya katse, sannan ya dubi Jakadiya. Tun bai yi mata magana ba ta fashe da kuka cike da nadama. "Allah ya isa tsakanina da Umaima, kin cuce ni kin saka ni a halaka." Jakadiya ta furta tana sake rushewa da kuka. Fulani Umaima ta sunkuyar da kai ƙasa ta fara zirarar da ƙwallah murya a sanyaye ta furta. "Tabbas na yarda rana dubu ta ɓarawo ce rana ɗaya ce tak ta me kaya, tun kafin ka aure ni nake cin duniyata da tsinken tsire har kafin lokacin da duniya ta yi mini atishawar kaji, duk abin da ya faru ni ce sila. Da hannuna da gabban jiki tare da taimakon wannan tsinannan mutumin da yake iƙirarin mahaifina ne shi. Na zalinci Fulani na zalince ka ranka shi daɗe." "Ki gama tsinewa Bamaguje ni kuma na tabbatar miki da naki hukunci don na yi rantsuwa na ƙara, sai na shayar da ke ruwan azabar da ko mutuwa kika yi aka ambaci sunana sai kin farfaɗo." Bai Maimuna ta yi maganar cikin wata irin murya mara daɗin sauraro. *SHU'UMAR MASARAUTA* *35* *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Boka Shaddas na ɓacewa daga kogon dutsensa bai sauka a ko ina ba sai a bakin dutsen Shugaba Zurufu, ya jima a tsaye yana ƙarewa dutsen kallo sannan ya shiga ciki a lokacin duhu ya mamaye ko ina, shiru cikin kogon dutsen ya yi babu motsin komai sai sautin tafiyar da Boka Shaddas yake yi. Sai da ya je tsakiyar filin haske ya gauraye cikin dutse. Cak Boka Shaddas ya tsaya ya harɗe hannuwansa a ƙirjinsa, bai yi tsammani ba sai gani ya yi Shugaba Zurufu ya burtso ta ƙarƙashin ƙasa a gabansa har sai da ya ɗan tsorata. Baya ya ja suka fura wurgawa junansu kallo kowa da manufarsa a zuciya, Shugaba Zurufu ya katse shirin da cewa. "Barka da zuwa Boka Shaddas!" Bai amsa ba kuma bai yi alamun zai amsa ba, don haka Shugaba Zurufu ya ci gaba da cewa. "Dama na san ko ba daɗe ko ba jima za ka kawo kanka..." "Ina ɗana yake?" Boka Shaddas ya katse shi rai a ɓace. Sai da Shugaba Zurufu ya koma can kan wani farin dutse ya zauna sannan ya furta. "Yanzu haka yana tare da kai, sai dai ba za ka taɓa tozali da shi ba har sai ka cika sharuɗɗan da zan gindaya maka." "Idan kuma na haƙura da shi fa." Boka Shaddas ya yi maganar yana zuba wa Shugaba manyan idanunsa. Sai da Shugaba ya ɗauki wani garin magani ya watsa a cikin wutar da ke ci a saman cinyarsa sannna ya wara hannuwa alamun rashin damuwa ya ce. "Idan ka haƙura da shi ba ni da damuwa, amma ka sani haƙura da Basiru tamkar ka haƙura da kundun tsafinka ne gabaɗaya. Idan ba ka yarda ba ka koma can kogon dutsenka, ka binciki rijiyar tsafinka za ta ba ka tabbacin abin da nake nufi." Ajiyar zuciya Boka Shaddas ya sauke gabansa na faɗuwa, duk yadda ya so nuna dakiya don kada Shugaba ya fahimci rauninsa abin ya gagara. "Mene ne sharuɗɗan naka?" Boka Shadda ya wurga masa tambaya. Shugaba na jin haka ya miƙe ya ɗauki sandar tsafinsa ya fara tafiya yana zagaye kogon dutsen da ita, sai da ya kammala sannan ya sake komawa mazauninsa na farko ya furta. "Sharaɗina guda ɗaya ne, don haka a yanzu sai da na toshe duk wata ɓarakar da mahaifiyarta za ta ba ni matsala, a baya ta yi yunƙurin binne mana tushenta amma bincikena ya haske mini ita. Sai dai Fargi ta kasance hatsabibiya kuma mai tsananin wayo, ta nesantamu da 'yarta don haka wani daga cikin zuri'armu bai isa ya sarrafata yadda ya dace ba. Dalili kenan da zan tura ta ka kawo mini JAWAHIR, yanzu haka tana can cikin Masarautar Huddam. Idan ka aikata mini haka na yi rantsuwa da girman tsafi da sihirina sai na dawo maka da ɗanka kuma na ninka maka ƙarfin iko da tsafinka." A madadin kalaman Shugaba su faranta ran Boka Shaddas sai ya sake turɓune fuska, "Me ya sa sai ni? Me ya sa duk yawan bokayan da ke faɗin ƙasar nan ba za ka zartar da wannan hukuncin a kansu ba sai ni?" "Saboda sara aka yi a kan gaɓa kuma faɗuwa ta yi daidai da zama." Shugaba ya katse Boka Shaddas, shiru ya yi har lokacin yana bin Shugaba da kallo. "A daidai gaɓar da nake yunwar buƙatarta a wannan lokacin Jakadiyar Masarautar Huddam da ka taɓa kawowa ta kawo mini kanta a kan wata buƙata da take ci mata tuwo a ƙwarya, ganin haka ya sa na jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya. Wato na bata umarnin kawo mini Basiru domin na san kai jajirtacce ne za ka aiwatar mini da abin da nake buƙata, yanzu haka tun kafin ka dawo daga taron da aka gayyace ka na gama magana da Shugaba, ka aiwatar mini da abin da nake buƙatar ni kuma na warware maka zare da abawa." Guntun tsaki Boka Shaddas ya saki sannan ya furta. "Zan koma kogon tsafina domin na nazarci abin da ya kamata, duk hukuncin da na yanke za ka ji daga gare ni." Daga haka Boka Shaddas ya fice daga kogon dutsen ba tare da ya ji abin da Shugaba zai faɗa ba. Kai tsaye halawar tsafinsa ya koma yana jin zuciyarsa na tuƙiƙin ɓacin rai, a ɓangare ɗaya yana ayyana irin mummunan hukuncin da zai yanke wa Jakadiya. Jin kalaman Baiwa Maimuna ya sake kaɗa hantar cikin Fulani Umaima, ta sharce ƙwalla tana sunkuyar da kai ƙasa don haka kawai take jin kunyar mutanen ɗakin. "Yanzu Ammi kina nufin duk abin nan da ake faɗa kin aikata? Wacce irin zuciya gare ki Ammi? Me ya sa za ki biye wa son ranki ki aikata wannan rashin imanin?" Yarima Muhsin ya yi maganar cikin matsanancin ɓacin rai. "Saboda a lokacin shaiɗan ya buga mini gangarsa don haka zuciya ta ingizani har na taka rawa son raina, rawar da ta shammaci ƙafafuwana zuwa faɗawa tekun nadama da da-na sani." Fulani Umaima ta tsahirta saboda yadda ta ji numfashinta na shirin ɗaukewa sakamakon wannan tsokar da ta tokaro ta, sai da zugin ya lafa mata sannan ta ci gaba zayyana duk abin da faru a rayuwarta tun farkon zuwanta cikin Masarautar taba budurwa, har zuwa aurenta da Takawa da rayuwar da suka gudanar ita da Fulani Babba. Ilahirin mutanen wurin jikinsu ba ƙaramin sanyi ya yi ba, ban da hawayen tausayin Fulani Babba babu abin da suke yi. Sailuba ta kalli Jakadiya tana jin wani irin ɗaci a ranta, kunyar Sarki Abdul'aziz ta lulluɓe ta don ba ta san da wanne idon za ta kalle shi da laifin mahaifiyarta ba. "Wannan mata amma ke dai kin cika azzaluma marar imani." Inna wuro ta furta wa Fulani Umaima tana share ƙwallar idonta. Kamalu ya waiga ya sake kallon halin da ɗan uwansa yake ciki, ya tuna irin gwagwarmayar da aka faɗi mahaifiyarsa ta sha sai kawai ya fashe da kuka yana ɗora kansa a kan cinyar Inna Wuro. A sanyaye Jawahir ta zauna tana jin tsanar Fulani Umaima na mamaye ta, ta waiga wurin Kamalu tana bin sa da kallon tausayi. "Ashe dama Inna Wuro ba ita ta haifi Kamalu ba? Kenan a yanzu batsayinmu ɗaya ba shi ba ya tashi daga matsayin Bawa?" Jawahir ta fara watsa wa zuciyarta tambaya. Jakadiya sai da ta share ƙwallar idonta tana shirin neman yafiyar Sarki Abdul'aziz ba ta yi aune ba zuruf ta ji hannun Buguzu a saman rigarta, da sauri ta ɗago za ta yi masa magana ya katse ta haɗe da wurga mata ƙwala-ƙwalan idanunsa. "Kada ki dakatar da ni don na lura abin ba na ƙare ba ne, ni fa ba haka muka yi da Shugaba Zurufu ba. Ya mallaka mini ke har abada kuma tun a farkon dare nake son ɓarje amarci amma sai cikas ake kawo mini." Buguzu yana gama maganar ya sake zura hannunsa, kafin Jakadiya ta yi wani yunƙuri tuni ta ji hannunsa ya murɗe mata mamanta tamkar zai tsinke mata su, dalilin haka ya sa Jakadiya da Buguzu da ke ɗauke da siffar Basiru suka fara kiciniya. "Dakata Buguzu! Kada ka nuna mana rashin ɗa'a. Duk uzurunka ba ka kai waɗannan bayin Allahn ba, don haka wannan rashin girmamawa ne." Dattijo Maharaz ya yi maganar rai a ɓace. Ba don ya so ba Buguzu ya saki Jakadiya, ganin haka ya sa ta yi tsalle daga wurin da koma can gefen Fulani Umaima. Ta sunkuyar da kai ƙasa cike da nadama, "Ka fafarce ni Ranka shi daɗe, wallahi sharrin shaiɗa..." "Ku adana tubanku Jakadiya ba ma buƙata." Sarki Abdul'aziz ya katse Jakadiya murya a kausashe. Ya ɗago ya dubi Fulani Umaima yana jin wani irin ɗaci a ransa, da sauri ta sunkuyar da kai ƙasa gabanta na faɗuwa. "Yanzu wanne irin hukunci kike so na yi miki Umaima?" Shiru ya ratsa ɗakin kowa da abin da yake ayyanawa a ransa. "Don Allah ka yafe mini..." "Hukunci na tambaye ki." Takawa ya sake katse ta. "Duk wani hukunci da za ka aiwatar mini duk azaba da raɗaɗinsa zan iya ɗauka, amma don Allah don girman Allah kada ka tsame ni daga ƙarƙashin inuwarka. Kada ka yanke jajirtacciyar alaƙar da ke tsakaninmu ta auratayya, ba zan iya jure rashinka ba. Allah ya sani kishi da ƙaunarka sune tsanin da suka kai ni ga duk wani mummunan aikin da na aikata ranka shi da..." "Yanzu idan na ce zan ci gaba da zama da ke za ki amince Umaima? An ya kin tuna irin miyagun ayyukan da kika aikata mini? Idan Fulani kishiyarki ce shi wannan yaron ba jinina ba ne?" Shiru Fulani Umaima ta yi ban da hawaye babu abin da yake zarya a saman fuskarta. Sarki Abdul'aziz ya juya wurin Bamaguje sannan ya furta. "Bamaguje kake ko? Ka zo da waɗansu kalamai da suka rikita mini kwanya amma a wannan gaɓar ba zan yanke hukunci ba, don haka za a sake saka mana lokaci domin wannan maganar dole za ta je wurin Mai martaba wato mahaifin Umaima." "Ba gaban Mai martaba ko gaban wa za a je ina nan zaune a tsibirina Sarki Abdul'aziz, ku yi duk wacca za ku kowa ya gama aiwatar da uzurinsa ni dai magana ɗaya na faɗa. Ko ba daɗe ko ba jima sai na ɗauke 'yata zuwa halwar tsafina." Bamaguje ya sake tabbatar wa Sarki Abdul'aziz ƙudurinsa. Kalamansa ba ƙaramin ɗaga hankalin Ruƙayya da Yarima Muhsin suka yi ba, musamman da suka hangi irin mummunan yanayin da Bamaguje yake cikin da ƙasurgumin dajin da yake rayuwa. Babu zato ko tsammani Baiwa Maimuna ta buga tsalle ta dira a kan Fulani Umaima, haƙoranta masu kama da kaifaffun wuƙaƙe ta sa a daidai saman cinyarta ta kafa masa cizo. Ba ta ɗauke bakinta ba sai da ta ciro da tsoƙar cinyar Fulani Umaima. Wata irin ƙara ta ƙwallah cikin matsananciyar azaba, ta faɗi gefe nan take idanunta suka kakkafe numfashinta ya ɗauke. Tamkar biri haka Baiwa Maimuna ta sake miƙewa da niyyar sake kai mata cafke Dattijo Maharaz ya katse ta, da ƙyar ta ji maganarsa ta koma gefe sannan ta mayar da kallonta wurin Boka Bamaguje ta furta. "Ba iya ita ba, kai ma ina tafe gare domin dole na ɗauki fansa a kanka." Taɓe baki Bamaguje ya yi ya furta. "Dama na san ko ba daɗe ko ba jima wannan ranar za ta zo, don haka na shiryawa zuwanta. Ni da kuke ganina ba na taɓa yin ƙwaina sai da zakara don haka a kullin nasara nake yi a rayuwata." Bamaguje ya gyara zamansa sannan ya ci gaba da cewa. "Duka a tsammaninku wannan Baiwa Maimuna ce amma sam ba ita ba ce." Jin kalaman Bamaguje ya sa mutanen ɗakin suka sake zuba masa idanu, cikin matsanancin mamaki. Yarima Muhsin ne ya yayyafa wa Fulani Umaima ruwa ta farko a firgice tana yunƙure ɓuya don tuni ƙwaƙwalwarta ta sake dawo mata da abin da ya faru. Duk wata ɗabi'a da ango yake gabatarwa a daren aurensa ga amaryarsa sai da Sarki Sulaiman ya aiwatarwa Fargi, ya nuna mata kulawa da soyayya sosai sai dai babban tashin hankalin da ya shiga a lokacin da bai san ta yadda zai zanin gadon da Fargi take kai ba. Dabara ce ta faɗo masa ya fita ta ƙofarsa ta baya, ya samu amintaccan Bawansa Faisal ya aika shi ya kira masa Jakadiya a sirrance. Cikin sauri Jakadiya ta ƙarasa tana mamakin kiransa don ta san babu wacce ta shiga turakarsa ballanta a ce wani abu ya gifta da har ake nemanta da wannan safiyar. Tana tura ƙofar ɗakin ta samu Sarki Sulaiman ya rufe ƙofar sannan ya yi mata iso zuwa uwar ɗakinsa, turus Jakadiya ta yi da ganin baƙuwar fuskar da ko a mafarki ba ta taɓa ganinta ba. "Jakadiya don Allah ki taimaka ki ɗauke wannan zanin gadon a sirri ba tare da wani ya gani ko ya ji labari ba, duk wani sauran bayani zan yi miki daga baya." Da sauri Jakadiya ta sake fita ta dawo da ruwan zafi ta haɗa wa Fargi da har lokacin kanta a sunkuye yake saboda kunyar abin da ya gifta tsakaninta da Sarki Sulaiman. Sarki Sulaimanu ya koma rumfa yana jin wani irin farinciki a ransa, sai da Jakadiya ta gama komai sannan Sarki Sulaiman ya sanar da ita alaƙar da ke tsakaninsu da Fargi tun daga farko har ƙarshe. "Amma ba ka ganin nan gaba a samu matsala ranka shi daɗe? Idan aka samu ƙaruwa da yarinyar nan ka na ga Masaraurta za ta karɓi abin da aka zo da shi." Jakadiya ta yi maganar da 'yar damuwa a saman fuskarta. "In shaa Allahu zan yi ƙoƙarin shawo kan abin Jakadiya, don Allah ki taya ni da addu'a kar zuri'arsu su ba ni matsala?" Jakadiya ta amsa masa sannan ta fice tana jinjina girman wawatar da Sarki Sulaiman yake shirin aikatawa. Tun daga wannan ranar a duk lokacin da Sarki Sulaiman yake muradin matarsa zai ɗauke ya kai ta turakarsa bayan wani lokaci ya mayar da ita, hakan ya sa ya ci gaba da zama da matansa ba tare da matsala ba sai dai ba wata kulawa da kirki suke samu daga wurinsa. Bayan auren Fargi da Sulaiman da wata biyar ta fara ciwon kai mai tsanani da yawan zafin jiki, lokaci-lokaci takan fuskanci tashin zuciya da kasala uwa-uba kuma ga yawan bacci. Don ko ayyukan tsafin da take gudanarwa sun ja baya sosai, bayan ɓatan dabon baƙonta na wata ta yi dogon binciken musammababbin ciwukan da take yi a nan ta binciko cikin da take ɗauke da shi na kusan makwanni biyar. Kuma a wannan ranar ne Shugaba ya tirke ta da tuhumar cikin da take ɗauke da shi, wanda ya yi mata shi da musababbin samun cikin shi kansa. Gyaɗa musu kai Bamaguje ya yi sannan ya ci gaba da cewa. "Sunana na asali Nomau kuma sunan mahaifina Mati. Asalinmu 'yan wani daji ne da ake kira Dujji, kuma mu Maguzawa ne gaba da baya domin babu wani addini da muka yarda da shi tun a wancan lokacin har zuwa yanzu. Tun tasowa ta na taso da ganin mahaifina yana gudanar da abin da ya shafi al'amuran tsafi, kuma tun ban yi wayo ba na ji ana ce mini ni ɗan baiwa ne wai na kece duka mutanen dajinmu. Wannan baiwa tawa ta samo asali tun lokacin da aka haife ni, sai ya kasance a lokacin an samu albarkar noman da ba a taɓa samun kamarsa ba kuma har kawo wannan lokacin. Kar dai na ja ku da nisa na ƙware kuma na gawurta a fagen tsafi da sihiri, don ko a yanzu ba na jin akwai shararran bokan da ya isa ya ɗaga miki yatsa ban karya shi ba idan aka cire Shugaba Zurufu. Lokacin da nake da shekara goma sha bakwai a duniya a lokacin ne na hallaka mahaifina ita kuma mahaifiyata na yi mu'amala da ita babu adada dalilin sa'ar da wani hatsabibin aljani ya ba ni kuma mahaɗin shi ne kusantar mahaifiyata." Sai da Bamaguje ya mayar da kallonsa wurin Fulani Umaima da ke cikin galabaita sannan ya ci gaba. "Na shafe sama da shekara Hamsin ina gudanar da mu'amala tsakanina da mahaifiyar Umaima, kuma a cikin mu'amalar da muka yi ne har ta samu cikin Umaima. Da ƙyar mahaifiyarta ta shawo kaina na bar mata ita a hannunta amma da sharaɗin za ta dinga kawo mini ita wurina, don rufin asirinta a wurin Mai martaba, kuma ta nemi alfarmar kada na nuna wa Umaima ni mahaifinta koda ta girma. Kuma hakance ta kasance har ta kai Umaima na zuwa wurina da ƙafarta, Ko ban faɗa wa Umaima ba da ace mai hankali ce za ta fahimci duk wani aiki da nake yi mata ina yi mata ne ba a matsayi boka ba sai a matsayin Mahaifinta. Na jima ina yi mata jurwaye mai kamar wanka amma ba ta ankara ba, kuma ta samu cikina har kusan sau goma sha biyu sai dai tun cikin na ƙarami nake sadaukar da shi ga abin tsafin da yake sake ɗaga darajata a fagen sanin tsafi da sihiri." Kusan lokaci ɗaya mutanen ɗakin suka ɗauki salati, wani irin zafi zuciyar Sarki Abdul'aziz take yi, ya haɗiyi yawu mai ɗaci yana sunkuyar da kansa ƙasa. "Kuma kamar yadda na faɗa ɗazu wannan da kuke gani ba Baiwa Maimuna ba ce, Baiwa Maimuna tun a ranar da na ƙwaƙwale mata idanu ta rasa ranta. Da yake akwai Guzzu wani bawan aljani da yake yi mini hidima wanda ya aikata mini laifi da cin amana, sai na sarrafa ruhinsa zuwa gangar jikin Baiwa Maimuna da na sa, a wannan gaɓar da za ta mutu ne Baiwa Maimuna ta damƙa masa amanar ɗaukar mata fansa a kan Umaima kuma ya ɗaukar mata alƙwarin haka. A lokacin ban wani damu ba don na saka Umaima ta binne rayuwarsa a cikin tsohuwar rijiyar can mai tsohon tarihi. Shi kuma ya ci mini alwashin matuƙar ya bayyana sai ya ɗauki mummunan mataki a kaina da ita Umaima, a taƙaice wannan shi ne tarihina da silar da ta sa Umaima ta zama jini a wurina." Ɗari bisa ɗari ya lura duk sun fahimci kalamansa kuma sun amince. Sarki Abdul'aziz ya miƙe ya fita da kansa ya kira Dogari Ɗan sani, bayan ya shiga ya ba shi umarnin a wuce da su Fulani Umaima sashen horo a sada su da ɗakin duhu. A figice ya dubi Takawa jin kalamasa amma kallon da ya wurga masa ya sa, ya fice da sauri ya kira Bawa Balarabe suna yunƙurin tasa ƙeyar Fulani Umaima Ruƙayya da Yarima Muhsin suka fashe da matsanancin kuka. Tausayin yaran ne ya kama shi amma ba ya jin zai iya yafe wa mahaifiyarsu da ita kanta Jakadiya. "A kai su ɗakin duhu kafin zuwa wayewar gari mu san abin yi." Sarki Abdul'aziz ya furta yana ɗauke kansa gefe. Fulani Umaima ban da ihu da kururuwa babu abin da take yi, cinyarta sai ɗigar da jini take ƙasanta na zirarar da ruwa mai wari, zaraf Buguzu ya maƙalo Jakadiya ana janta shi ma yana biye da ita yana shafo ƙirjinta har aka fice da su gabaɗaya. Dogaran sai kallon Buguzu suke da mamaki duk a tsammaninsu Basiru ne yake yi wa Jakadiya haka. Kamar Kazar da aka tsoma a ruwa haka Sailuba ta raɓe a gefe tana share ƙwalla, Sarki Abdul'aziz ya dubi Dattijo Maharaz. "Allah ya taimaki tsoho mai ran ƙarfe, ina ganin dare ya tsala za mu bari zuwa waywar gari. Amma kafin ka tafi ka roƙar mini iyayen Kamalu su bar mini shi ya kwana a wurina." Murmushi Dattijo Maharaz ya saki, kunya ta kama su Baffajo. "Ranka shi daɗe ai kai da kaya duka mallakar wuya, mun bar maka Kamalu amma gaskiya muma za mu yi kewarsa." Daga haka Dattjjo Maharaz ya sallami Bamaguje har zuwa lokacin da za a kira Mai martaba mahaifin Fulani Umaima, sannan ya musu sallama har ya je bakin ƙofar uwar ɗakin Sarki Abdul'aziz ya juya ya ɗaga wa Kamalu hannu sannan ya ƙarasa bakin Shurim da ke ɗakin nan take ɓace. Aljanin da ke cikin surar Baiwar Maimuna ya miƙe ya yi wa Sarki Abdul'aziz sallama, kai tsaye ya wuce ɗakin da aka wuce da su Fulani Umaima. Cike da al'ajabi su Inna wuro suka russuna suka yi wa Takawa da Kamalu sallama, ta riƙe hannun Jawahir Takawa ya sa Dogarawan ƙofa suka yi musu rakiya har zuwa can sashensu na Bayi. A cikin zuciyar Sarki Abdul'aziz yana cin alwashin wannan ne kwana na ƙarshe da su Baffajo za su sake yi a sashen Bayi. *SHU'UMAR MASARAUTA* *36* *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Duk da Fargi ta san cikin da take ɗauke da shi, sai ta nuna wa Shugaba Zurufu sam ba ta san abin da yake nufi ba. "Shin ka fara zargina ne Shugaba Zurufu?" Tambayar da ta wurga masa kenan don ta ɓatar da hankalinsa. Sai da ya saki murmushi sannan ya furta. "Yaro man kaza! Shin kina ganin za ki iya ɓoye mini halin da kike ciki ne Fargi? Kin san waye ni don haka wannan tambayar ina ganin ba ta da alfanu a gare ni. Shin wane ne mamallakin cikin jikinki?" Gabanta ne ya yi mummunar bugawa ta tattaro mayafin jarumta ta yafa wa kanta, sannan ta furta. "Ba ni da masaniyar abin da kake nufi shugaba." Fargi ta furta tana barin wurin fuska a haɗe. Kaɗa kansa ya yi ya saki murmushin da shi kaɗai ya san manufar yin sa. "Ta yaro kyau take ba ta ƙarko, shi dai ciki ɗan duma ne don haka sannu-sannu ba ta hana zuwa." Hankali a tashe Fargi ta nausa daji sai da ta yi tafiya mai nisa ta ɗan hura huta sannan ta yi wani turare, tana kiran sunayen waɗansu gungun manyan aljanu waɗanda suke taimaka mata a game da 'yan tsaface-tsafacenta. A cikin munanan hallitarsu suka bayyana a gabanta, "Wacce irin damuwa gare ki?" "Shubana Zurufu shi ne matsalata! A yanzu haka ina ɗauke da juna biyu, kuma take-take da yanayinsa na nuna mini yana son bankaɗo laluben sirrina." "Zan yi miki aiki a kansa amma kin san taurin kai irin na Zurufu, don haka za ki yi mana yanka. Ina nufin ki zubar mana da jinin jarirai sababbin haihuwa guda uku, za ki ba mu fararen raƙuma biyu sauran aikin ki bar mana komai a hannunmu." A ɗan tsorace ta dube shi sannan ta ce. "Dole sai ta haka? Haba Aljani Huburu ka san babu asarar rayuka a tattare da ni, ban taɓa kisa ba tun da na wayi gari a halwar tsafin da Shugaba ya horar da ni." Fargi ta furta cike da damuwa. "Dole sai an zartar da haka Fargi, idan kuma ba kya muradi sai mu yi miki fatan sauka lafiya." Ajiyar zuciya Fargi ta sauke sannan ta yi musu sallama. Ta koma gidan mahaifinta. "Fargi akwai abin da yake damunki na ga kwana biyu kin ɗashe, yanayinki ya sauya. Me yake damunki?" Mahaifiyarta ta wurga mata tambaya tana kafe ta da idanu. Shiru Fargi ta yi tamkar ba za ta yi magana ba sannan ta ce. "Kwana biyu ba na jin daɗi ne amma yau na ji ƙwarin jikina." Ta furta tana sunne kai ƙasa. "Ba ni hannunki mu gani." Rass gaban Fargi ya faɗi, ba ta da zaɓi don haka ta miƙa wa mahaifiyarta hannunta. Sai da ta duba tafin hanunta sannan ta saka hannu ta gwale ƙwayar idonta. A ɗimauce ta sake ta tana ja da baya cikin tashin hankali. Ganin haka ya sake firgita Fargi ita ma ta ɗan ja da baya idanunta suka ciko da ƙwalla. Sai da Mahaifiyarta ta rufo ƙofa da windon cikin bukkarsu sannan ta sake jan hannun Fargi suka koma bakin gado suka zauna. "Wa kika buɗewa sirrinki har haka ta faru? Me ya sa za ki yi mana haka Fargi bayan kin san matsayin da kike da shi a garin nan? Shin kin zaɓi ki tashi daga gurbinki na shugaba ki koma bautacciya bayan kin yi aure? cikin waye a jikinki Fargi?" Mahaifiyarta ta wurga mata tambayoyi yayin da Fargi ta sunkuyar da kai tana jin ƙirjinta yana bugawa. Bayan kowa ya watse sai ya rage daga Sarki Abdul'aziz sai Kamalu, Muhsin, Ruƙayya da Yarima Muhsin. Kallon-kallo aka shiga yi tsakanin Muhsin da Kamalu. Abubakar kuwa yana zaune sai bin su yake da kallo. "Allah mun gode maka da ka nuna mana wannan rana mai tattare da farinciki haɗe da ɓacin rai. Ubangiji ka fi mu sanin dalilin da ya sa ka tsara mana wannan al'amari a gare mu, kuma muna roƙon ka ba mu ikon cinye jarrabawar da za ta ci gaba da samunmu mai kyau ko akasin haka." Suka amsa masa da Amin. "Kamalu wannan ɗan uwanka ne sunansa Muhsin, ga ɗayar ƙanwarka nan Raƙayy." "Na jima da sanin Yarima Muhsin ko don rashin mutumcinsa, wannan ce dai ban santa ba." Kamalu ya furta a zuciyarsa. Amma a fili sai ya furta. "Na ji daɗin kasancewata da ku gabaɗaya ranka shi daɗe, har yanzu gani nake tamkar mafarki nake." Murmushi Sarki Abdul'aziz ya yi ya ce. "Haka Allah ya tsara Kamalu babu bawan da ya isa ya kaucewa ƙaddararsa. Kana da yayye mata da ke aure a wasu garuruwan, In shaa Allah zan sa a aika musu da takarda har zuwa dangin mahaifiyarku." Murmushi Kamalu ya saki, haɗe da amsawa Takawa. Sannu a hankali Sarki Abdul'aziz ya dinga jan su Muhsin da hira don ya gusar musu da damuwar da ke ƙunshe cikin zuciyarsu. Jefi-jefi Muhsin yake saka baki daga ƙarshe ya miƙe ya yi musu sallama ya wuce ɗakinsa. Kamalu da su Ruƙayya suka kwana a sashen Sarki Abdul'aziz. Tamkar wasu dabbobi haka aka dinga jan Jakadiya da Fulani Umaima aka wuce da su ɗakin duhu, kamar wasu kayan wanki hakan dogaran suka watsa su ciki sannan suka janyo ƙafar suka datse. Jakadiya ban da kuka da kururuwa babu abin da take yi, ita kuma Fulani Umaima sai ido da take bin su da shi da jinjina darasin rayuwa da mamakin wai yau ita ce Dogarai suke yi wa tsawa. "Allah ya tsine miki Umaima duniya da lahira, wallahi tarraya ta da ke ba ta amfane ni da komai ba." Jakadiya ta yi maganar cikin ɓacin rai. "Wai kina ina ne ba na son na farwa wacce ba halaliyata ba." Buguzu ya furta yana laluben Jakadiya. Tashin hankalinta ne ya ninku suka ci gaba da wasan ɓuya shi da Jakadiya, Fulani Umaima na shirin mayar wa da Jakadiya martani ba ta yi aune ba ta ji wata irin azaba ta ratsa saman kafaɗarta sakamakon cizon da Aljani Guzzu ya kafa mata a kafaɗa. Jini ne ya fara tsartuwa, cikin azaba Fulani Umaima ta kwarara ihu tana neman taimako. Cikin shammata ta sake jin ya sake zuba mata haƙora a gadon bayanta kuma duk wurin da ya sa haƙoransa da naman jikinta yake ɗagowa. Kasancewar ƙarfin mutum da aljan ba ɗaya ba tuni Buguzu ya turmushe Jakadiya ya kafa haƙoransa a saman mamanta ɗaya, tamkar wacce ake zuƙewa jini haka Jakadiya ta dinga jin ana zuƙarta. Duk yadda ta so ta yakice Buguzu sai abin ya gagara, don haka ta shiga kuka har da majina tana neman ɗauki amma ko motsi ba ta ji ba ballantana ta saka ran wani zai shigo ya kawo mata ɗauki. "Ba zan kashe ki ba, sai na gama ɗanɗana miki mummunar azabar da za ta gigita ruhi da gagar jikinki." Aljani Guzzu ya furta wa Fulani Umaima sannan ya ware faratan hannuwansa masu matuƙar kaifi ya shiga karta mata a jiki yana wasa su tamkar yadda ake wasa wuƙaƙe. Fulani Umaima tun tana iya gudun ceton rai har ta galabaita ta faɗi tana jan ciki ƙarshe numfashinta ya ɗauke ta sume a wurin. Tun isar su Inna wuro sashensu na Bayi kyakkyawan labari game da Kamalu ya fara yaɗuwa, take sashen nasu ya kacame da hayaniya aka shiga tattauna maganar kowa yana mamaki da ta'ajibin wannan lamarin. Sai a wannan lokacin kowa ya samu damar furta damuwar da ke cikinsa dangane da Fulani Umaima, Bayi da dama suka shiga bankaɗo miyagun laifukanta da suka sani na zahiri. Suka shiga tattauna ɗumbin haƙurin da Fulani babba ta yi a lokacin da take raye, har zuwa halin da Abubakar yake ciki na ban tausayi. Wannan ya tsinka zuciyar Jawahir da Mai gado suka shiga ɗaki suka sha kukansu, ga dai ranar yabon Fulani babba amma ba ya raye. Sai da suka daidaita nutsuwar suka shiga wurin Inna wuro aka ci gaba da tayata barka. Don ko ba a faɗa musu ba sun san a yanzu su Inna wuro sun yi musu fintinkau don suna da tabbacin Takawa ba zai bar su haka ba, sai ya gwangaje su da tukwici mai girma. Tun a daren wasu suka fara yi mata fadanci da nuna soyayya abin har mamaki ya ba ta don ta san wacce suke kashewa su binne a cikin gidan dama Mai gado ce, Sai da dare ya tsala sosai sannan su Mai gado suka yi wa Inna wuro sallama suka koma nasu ɗakin. Asubar fari Masarautar Huddam ta wayi gari da samun mabambamtan labarai, wasu daga ciki sun samu labarin tun a daren ranar yayin da wasu sai da gari ya waye suka samu labarin abin da ya faru. Kuma tun da asubar Sarki Abdul'aziz ya sa aka rubuta takardu zuwa wurin mahaifan Fulani babba, Fulani Umaima da su Khadija domin a sanar da su abin da yake faruwa. Sarki Abdul'aziz da kansa ya zaɓowa Kamalu kayan 'ya'yan sarakai na alfarma, ya umarce shi da ya sauya na jikinsa don kayan Bayi ba su kamace shi a matsayinsa na ɗan sarki ba. Ba musu Kamalu ya karɓa ya saka a ɓangare ɗaya yana sake tausaya wa rayuwarsu ta Bayi, don har lokacin jinsa yake tamkar bawa domin ya rayu a cikin bautacciyar rayuwa ta 'ya'yan Bayi. "Don Allah ranka shi daɗe idan komai ya lafa a duba rayuwar Bayi da 'ya'yansu." Kamalu ya furta a ɗan ɗarare don har lokacin bai gama sakin jikinsa ba. "In shaa Allahu za mu yadda ka buƙata Kamaluna." Sarki Abdul'aziz ya furta. Lokacin da su Galadima suka samu labari sun matuƙar razana, sai kuma mamaki ya kama su duk da kowa ya san Fulani Umaima ba mai faran-faran da mutane ba ce, amma sun kaɗu da jin miyagun labaran da suke fitowa dangane da ita har zuwa kan mahafiyarsu. Kuma tun da gari ya waye suke sa ran ko Sarki Abdul'aziz zai neme su amma sai suka ji shiru, babu wani aike da suka samu daga fada. Don haka suka shirya shi da Ciroma suka wuce kai tsaye zuwa fadarsa, tamkar babu hassada ko ƙyashi a ransu haka suka shiga taya Sarki Abdul'aziz murna da jimanta masa game da abubuwa biyu da suka faru na farinciki da baƙinciki. Kamar waɗansu sababbin hallitu haka waɗansu daga cikin bayi masu son ganin ƙwaƙwaƙƙwaf suka bi ta hanyar baya suka isa ɗakin duhu suna leƙen Fulani Umaima da Jakadiya. Tsoro ne ya kama su matuƙa da ganin halin da Fulani Umaima take ciki, ilahirin jikinta ya yi kace-kace da jini ta faɗi a gefe sai sauke numfashi take da ƙyar. Ita kuma Jakafiya gaban rigarta a yage ga mamanta ɗaya da ya gutsure wani irin ruwa da jini na zuba. Uwa-uba ga wani irin wari da yake tashi daga cikin ɗakin, don haka suka dinga toshe hancinsu. Sai da manyan Dogaran wurin suka fatattake su sannan kowa ya watse, kafin zuwa yammacin ranar tuni mabambamtan labarai suka dinga zaga ciki da wajen masarautar. Kowa da abin da yake faɗa, wasu su ce Sarki Abdul'aziz ne ya sa ake yi musu wannan horon na azaba, wasu kuma su ce aljanin da suka yi wa Fulani Umaima aiki ne reshe ya juye da mujiya suke dawowa gare ta. Wasu ma har ce wa suke fatalwar Fulani babba ce ta dawo take ɗaukan fansa. Tun safiyar ranar Ruƙayya ta dame shi da son ganin mahaifiyarta, kalaman da suka fara taɓa zuciyarsa yake jin tausayin yaran ya kama shi. Daga ƙarshe ma sai ya sa aka tura ta wurin Mai gado a can sashen Fulani babba domin ta ci gaba da kula da su, wunin da Kamalu ya yi tare da Takawa duk sai ya ji shi a takure don ya saba asubar fari suke fita kowa ya kama aiki gabansa amma tun da gari ya waye sai dai ya ci ya sha su yi hira da Takawa ya kwanta. "Ranka shi daɗe ina son ganin su Inna wuro." Kamalu ya furta yana kallon yanayin Sarki Abdul'aziz. "Mun samar maka Bayin da za su dinga taimaka maka su yi rakiya da duk wani abu da ya shafe ka. Su Inna wuro daban suke a wurinmu don haka za su yi maka rakiya zuwa wurinsu, amma daga yau ba ma son ku dinga yawan fita har sai mun sa an horar da ku ɗabi'u da halayen 'ya'yan sarakuna." Sai da Kamalu ya russuna sannan ya furta. "Ina godiya da wannan karamcin ranka shi daɗe." "Mun sa an fara gina wa su Inna wuro ɗakuna a bayan ɗakunan mahaifiyarka, muna so nan da ɗan wani lokaci mu keɓe su daga sahen Bayi." Sarki Abdul'aziz ya furta wa Kamalu. Farinciki ne ya mamaye shi ya sake zubewa ƙasa ya yi masa godiya, har sarki Abdul'aziz zai sa a kira bayin da za su fara yi masa hidima Kamalu ya ce. "Amma ranka shi daɗe idan babu damuwa zan iya zaɓar bayin da za su yi mini hidima?" Gyaɗa masa kai Takawa ya yi Kamalu ya yi godiya sannan ya faɗi sunan abokansa biyu da tun tasowarsu suke tare, kuma a ganinsa wannan ce hanyar da zai bi domin ya sauƙaƙa musu daga aikin bautar da suke yi suma su huta, tun da shi ma Allah ya 'yanta shi. Kamar waɗanda suka ga baƙuwar hallita haka Bayi suka dinga bin Kamalu da kallo, duk hanyar da ya bi sai dai Bayi su dinga zubewa a ƙasa suna gaishe shi. Shi abin har mamaki yake ba shi, ko da ya shiga ɗakin Inna wuro suna ganinsa suka rungume shi cikin farinciki. Inna wuro ta shiga tattaɓa shi tana ƙare wa kayan jikinsa kallo. "Kamaluna kai ne haka ka fito ka yi kyau?" Baffajo ya faɗa, yana taɓa rantsattsiyar rigar jikin Kamalu. "Baffa wallahi na yi kewarku." Kamar haɗin baki duka suka amsa masa. "Muma mun yi kewarku Kamalu." Jawahir ce ta shiga ɗakin hannunta ɗauke da ƙwaryar furar da Mai gado ta turo ta don ta kawo wa Inna wuro. Turus ta yi tana bin Kamalu da kallo, shi ɗin ma kallo yake bin ta da shi. Karamcin jiya da ta yi wa mahaifinsa ya sa ya fara ganin girma da ƙimarta. Taɓe baki ta yi kamar ba ta gan shi ba, ta miƙa wa Inna wuro furar sannan ta ce. "Inna wuro ga fura Inna ta ce na kawo miki kuma wai ku biyu kaɗai za ku sha." Jawahir ta yi maganar tana satar kallon Kamalu don da ta san yana ɗakin ba za ta yi wahalar dakan fura har ta dama ta kawo kuma ya sha ba. "Inna zan sha fura." Kamalu ya faɗa saboda jin abin da Jawahir ta faɗa. "Malam kar ka sake wallahi ka sha don ban daka fura don wani ƙato ya sha ba..." Daga bayanta Mai gado ta katse ta. "Dama rashin hankalin da kika zo yi kenan ko Jawahir? Kin manta matsayin Kamalu yanzu?" Jin haka ya sa Kamalu ya ɗan sake tsare gida, Jawahir ta ɓata rai baƙincikinta bai wuce a gaban Kamalu Mai gado ta dinga ce mata tana rashin hankali ba. "Wallahi ni kam bai isa ba a wurina, ni kullin a kamalu nake kallonsa tun ba a taɓa sauyawa tuwo suna." Jawahir ta ƙarasa maganar tana ficewa daga ɗakin. Baki sake Mai gado ta bi ta da kallo, sannan ta rufa mata baya don kullin lamarin Jawahir ƙara gaba yake yi sai ta tashi tsaye a kanta. Wani murmushin ƙeta Kamalu ya saki don, ya fahimci hanyar da zai bi ya cusgunawa Jawahir don ya lura rainin da ke tsakaninsu ƙara yawa yake yi. "Ban zaunar da ke domin ki yi mini kuka ba, tambayar ki nake cikin waye a jikin?" Mahaifiyar Fargi ta sake jefa mata tambayar. "Na aikata babban zunubin da ya kasance babban hukunci ne ga duk wanda ya aikata makamancinsa a yankin nan, Inna aure na yi na sirri ba tare da kun sani da. Ki dubi girman tsafi kada ki fallasa wannan sirrin da na sanar da ke, wallahi ban san yadda aka yi na zunduma cikin kogin soyayyarsa ba. Dalilin haka ya sa muka yi aure a ɓoye, kuma ni kaina rannan bincike ya bayyana mini cikin da ke tare da ni." Ilahirin jikin mahaifiyarta rawa yake, ganin haka ya sa zuciyar Fargi ta sake karyewa. "Kuma shi bai kasance jinin zuri'ata ba, hasali ma Sarki ne a wata masarauta da ke nesa da yankin nan, sai dai masarautar ba ɓoyayya ba ce. Don girman tsafi da dogaron da muka yi akansa ki binne wannan sirrin, ke uwa ce za ki fahimci abin da nake faɗa. Ina nan zan ci gaba da binciko yadda zan yi da cikin jikina amma ba zan taɓa lalata shi ko na salwantar da shi ba." "Me ya sa kika aikata haka Fargi bayan kin san zunubi ne yin soyayya da ɗan wata zuri'ar, amma har ta kai ki ga aure?" "Saboda ina son a dakatar da wannan mummunar ɗabi'ar da ke shiga haƙƙin zuƙata, an kashe 'yan mata da dama sanadin haka. Samari da dama sun kashe kawunansu saboda rasa masoyansu da ba sa cikin zuri'ar nan, shin ko kin san Lado, Tine, Wargu, zinne da Damiggu duk sun kashe kansu ne saboda sun san kashe su za a yi matuƙar tsafi ya san suna soyayya da waɗansu da ba sa cikin zuri'armu? Ta yaya za mu samu ci gaba har zuri'armu ta bunƙasa a doron ƙasa, na zaɓi hakan ne ko zan rasa raina a nan gaba ban damu ba matuƙar zai karya wannan alƙadarin da zuri'armu take kai tun iyaye da kakanni. Amma don matsayin da kika ba wa tsafi da sihiri kada ki tona asirina har sai bayan na sauke cikin da nake tare da shi." Ajiyr zuciya mahaifiyarta ta sauke sannan ta furta. "Ba na son na rasa ki Fargi, don haka zan taya ki rufe asirin halin da kike ciki. Amma ina tsoron abin da kaje ya zo a nan gaba." A ranar kwana uku ciff da aika takardun da Sarki Abdul'aziz ya sa aka yi, Mai martaba da mahaifiyar Fulani babba suka yi wa Masarautar Huddam tsinke, ba a gama tarbarsu ba sai ga su Mahaifiyar Fulani Umaima sun ƙaraso. Lokaci ɗaya gidan ya hautsine da baki, Bayi suka shiga hidima da manyan baƙi aka sauke su a babban ɗakin saukar ɓakin Sarki Abdul'aziz, babu jimawa Sakina da Khadija suma suka ƙarasa cikin masarautar. Wasu na ji suna mamakin Ruƙayya 'yar Fulani Umaima ba ta mutu ba, kun manta bayan ta haifi Basiru ta sake samun ciki ta haifi 'ya mace aka saka mata Ruƙayya. Ita waccan Ruƙayyan ai ita take bin Yarima Muhsin wannan kuma ita ce take bin Basiru. *SHU'UMAR MASARAUTA* *37* *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Boka Shaddas ya jima yana kai-kawo a cikin halwar tsafinsa yana bincike game da yadda zai ɗauko Basiru amma ko ɓurɓushin samun mafita bai gani ba. "Tabbas Shugaba Zurufu ya kasance taƙadari kuma hatsabibi amma zan ji da shi, sai na yi masa kwantan ɓaunan da zan shamace shi a lokacin da bai za ta ba." Boka Shaddas ya furta cike da cin alwashi. Waɗansu tarkacan magunguna ya ɗebo ya fara watsawa jikinsa, ya shiga yin turarrika sannan ya zauna a gaban wutar tsafinsa yana tunanin hanyar da za bi don ya isa cikin Masarautar Huddam ya ɗauko Jawahir ɗin da Shugaba ya saka shi ko ya samu damar fanso Basiru da tasirin tsafin da ya dogara da shi. Sai da waɗannan Dattijan sarakunan suka ci suka sha suka huta sannan Sarki Abdul'aziz ya gabatar musu da Kamalu da matsayinsa a wurinsu. Mahaifin Fulani babba har sai da ya zubar da ƙwalla sannan ya rungume Kamalu yana jin ƙaunarsa a ransa, ɗaya bayan ɗaya haka Mai martaba da manyan yayyan Fulani babba suka dinga jan Kamalu har su Khadija suka rungume shi suna kuka, tare ta labarta masa irin halin ƙuncin da mahaifiyarsu ta shiga a lokacin da tana raye, musamman Khadija da ita ta fi sanin sirrin damuwar da ke damun mahaifiyarsu. Sai da wurin ya lafa da hatsaniya sannan Sarki Haruna ya fara magana. "Sarki Abdul'aziz muna zaune takarda ta iso gare mu dangane da 'yata Umaima, na gagara fahimtar saƙon da ke ciki musamman da a ciki ka ce babu buƙatar a sanar da mahaufiyarta abin da yake faruwa." Tun da ya fara magana Fulani Kilishi ta yi zuru gabanta na faɗuwa, don tun da suka zo ba su ji a fitar sunan Umaima ba, kuma ba ta samu damar ƙeɓewa da Muhsin ba ballantana ta ji halin da mahaifiyarsa take ciki. "Allah ya taimake ka ina ganin waƙa a bakin mai ita ta fi daɗin sauraro, ayi mini afuwa zan gabatar da waɗansu mutane domin tattaunawarmu ta samu abin da ake buƙata." Amsa masa ya yi sannan Sarki Abdul'aziz da kansa ya shiga uwar ɗakinsa ya yi magana a daidai shurin Dattijo Maharaz, bayan ya gabatar masa da abin da yake tafe da shi Dattijo Maharaz ya amsa da cewa. "Babu damuwa Sarki Abdul'aziz zan zo gare ku yanzu nan, don haka za ka iya sa wa a kawo ita Umaima domin a yi komai a fili ba tare da kowa ya ga an zalince shi ba." Cike da ladabi Sarki Abdul'aziz ya amsa wa Dattijo Maharaz sannan ya miƙe ya fice, bayan komawarsa ya bada umarnin a je a taho da Jakadiya da Umaima. Sarki Abdul'aziz ya shiga babu jimawa sai ga Dattijo Maharaz sun shiga ɗakin, hannunsa riƙe da Boka Bamaguje suna tafe yana dogara sanda jikinsa na karkarwa. Daga can gefen bangon da ke fuskantar su Mai martaba Haruna suka zauna, suna zama aka shiga da su Fulani Umaima aka watsar da su a gefe tamkar kayan wanki, tun da suka shiga ɗakin ya dum! Saboda wari nan take kowa ya sa gefen rigarsa ya toshe hancinsa. "Wannan tattaunawar ba za ta yiwu a haka ba har sai an tsaface su Sarki Abdul'aziz, shi kansa Bamaguje yana buƙatar kintsawa." Dattijo Maharaz ya furta. "Babu wata kintsawa da zan yi ni wanka bai dame ni ba, shin ka taɓa ganin Boka ko mai sihiri irina cikin tsafta ne? Mu gabatar da abin da yake gabanmu domin a yanzu haka akwai wata tarzomar da ke dumfaro ni, bayan wannan kuma ba ni da wadatacciyar lafiya kai shaida ne Maharaz a lokacin da ka je ka taho da ni." Bamaguje ya furta cike da ƙagauta, ganin Bamaguje na som ba su matsala ya sa Sarki Abdul'aziz ya sa aka fara shiga da turarrukan wuta kala-kala ana sakawa domin samun sauƙin warin da yake addabarsu. Har Bamaguje zai fara magana Takawa ya sa aka kira su Inna wuro don ba ƙaramin girma da mutumci yake ba su ba. Sai da Sarki Abdul'aziz ya gabatar wa Bamaguje mutanen ɗakin sannan ya tsahirta suka zuba masa ido gabaɗaya suna jiran jin daga gare shi. Tun shigar Bamaguje Mahaifiyar Fulani Umaima take ta zabga gumi cikin tashin hankali, kuma yanayin da Fulani Umaima take ciki na sauyawar kammani ya sa babu wanda ya gane ta. "Sarki Abdul'aziz wannan ai karatun baya ne ake son ƙara maimaitawa, me kuke so na ce muku bayan faɗin Umaima ɗiyar cikina ce? Ga Kilishi nan ita shaida ce, tun tana budurwa take ziyartar wurina har bayan aurenta da Sarki Haruna, ita ta sani har yarjejniya muka yi yanzu kuma me ya rage." A zabure Sarki Haruna ya furta. "Me wannan mashirikin yake nufi? Kana nufin Umaima 'yata ita ce 'yar cikinka? Sarki Abdul'aziz Ina Umaiman take ne?" Da hannu Sarki Abdul'aziz ya nuna wurin da Fulani Umaima take kwance, lokaci ɗaya jikinsu ya yi sanyi mamaki halin da take ciki ya kama su. Ganin Mai martaba Sarki Haruna na son nuna gardama ya sa Dattijo Maharza da Bamaguje suka fayyace masa komai tun daga farko har ƙarshe, idanunsa na zubar da ƙwallah ya waiga wurin Fulani Kilishi ya ce. "Shin abin da wannan Bokan ya faɗa haka ne?" Kuka ta fashe da shi cikin nadama ta ce. "Ka gafarce ni ranka shi daɗe wallahi sharrin shaiɗan.." "Sharrin shaiɗan ko? Ki je Kilishi ke da Allah, amma ba zan iya ci gaba da zama da ke ba na sake ki saki uku! Ban san hukunci da Abdul'aziz zai yanke ba amma matuƙar ya sallame ta ke za ki ɗauki 'yarki ki tafi da ita." Murya na rawa hawaye na zuba ya waiga wurin Sarki Abdul'aziz sai da ruƙo hannunsa cikin ƙwalla ya ci gaba da cewa. "Ka gafarce ni Sarki Abdul'aziz bisa duk rashin imanin da Umaima ta aikata, duk hukuncin da ya dace ka ɗauka a kanta kuma idan har akwai wani taimako dangane da hukuncin da za ka yanke a kanta a shirye nake na ba ka gudummawa ɗari bisa ɗari. Zan wuce gida don zuciyata zafi take idan na ci gaba da kallon waɗannan miyagun mutanen zuciyata za ta iya bugawa." Ya ƙarasa maganar yana yunƙurin miƙewa, fadawansa suka kare shi ya tashi har ya fara tafiya ya waigo ya kalli Fulani Kilishi. "Kin ci amanata kin zalince ni ki je ke da Allah, ga mahaifin 'yarki nan idan kin gama idda sai ki aure shi ki ɗora daga inda kuka tsaya." Daga haka ya saka kai fice zuciyarsa na yi masa ɗaci. Fulani Umaima ban da ruwan hawaye babu abin da take yi, wahala ta sa ko magana ta kasa yi. Fulani Kilishi suka ji ta tsuntsire da dariya ta fara fisgar gashin kanta tana kai wa baki. Da sauri Sarki Abdul'aziz ya sa aka fita da ita ya bayar da umarnin da a fice da ita daga cikin masarautar gabaɗaya. Lokacin da Dogarawan suka fita da ita keken dokin su Sarki Haruna ya fito, ganin haka ya sa ta bi keken dokin da gudu tana sheƙa dariya tana ce wa sai ta bi Sarki Haruna. Da Dogaran suka ga ta rage musu aiki sai suka juya suka koma cikin masarautar cike da jimamin abubuwan da yake faruwa. Shiru ɗakin ya ɗauka kowa da abin da yake jimantawa a zuciyarsa, Yarima Muhsin tun da aka shigo da mahaifiyarsa ya kauda kansa gefe yana zubar da ƙwalla. "Duk da ta aikata babban laifi mafi girma ita ɗin uwar 'ya'yanka ce, me ya sa ka sa aka aikata mata wannan mummunan hukuncin? Wannan yaron Kamalu dama can Allah ya ƙaddara wannan ƙaddarar a kansa, yanzu ka ga a silar shi waɗannan bayin Allahn suka shigo cikin masarautar nan. Ka ga kuwa bai da..." A ɗan hanzarce Sarki Abdul'aziz ya katse Mai martaba mahaifin Fulani babba don ji yake zuciyarsa na tafasa. "Ranka shi daɗe kada ku manta ita fa ta raba mu da uwargidanmi kuma uwar 'ya'yanmu, ta raba shaƙuwar tsakanin ɗa da mahaifiyasa, hasali ma ta raba ta da duniyar bakiɗaya." Sarki Abdul'aziz ya ƙarasa maganar muryarsa tana rawa. "Wallahi ko da Umaima ko babu Umaima sai Fatima ta mutu a wannan lokacin, kada ka manta kowanne bawa a rubuce kundin ƙaddararsa yake tun kafin zuwansa duniya, duk wani ciwo da ka ga ya samu Fatima dama can Ubangiji ya ƙaddara mata faruwarsa sai dai ta kasance ita ce sanadinta." Ajiyar zuciya Sarki Abdul'aziz ya sauke ya ɗan haɗiyi yawu mai ɗaci, sannan ya russuna cikin girmamawa ya furta. "Ku gafarce mu ranka shi daɗe idan kalamanmu za su sosa muku rai, amma Allah Ya sani ba za mu iya yafe mata cin kashin da ta aikata wa Fatima ba." Daga haka Sarki Abdul'aziz ya sa aka sake fitar da Jakadiya da Fulani Umaima zuwa ɗakin duhu. Kalaman da Sarki Abdul'aziz ya furta ba ƙaramin faranta zuciyar mahaifiyar Fulani baba da 'yan uwan ya yi ba, Dattijo Maharaz ya dubi Mai martaba ya ce. "Ranka shi daɗe ni kuma wata alfarma na zo nema ban sani ba ko zan iya samu a wurinka?" Gabaɗaya mutanen ɗakin suka tattara hankulansu wurin Dattijo Maharaz, "Ina sauraronka Dattijon arziƙi wacce irin buƙata ce?" "Ina nemar wa Sarki Abdul'aziz arziƙin sake nema masa iri a wurinka, ina nufin ina nema masa auren ɗaya daga cikin 'ya'yanka domin ta maye gurbin Marigayya." Wani daɗi Sarki Abdul'aziz ya ji har cikin ransa, ya ɗan saki murmushi amma shi kansa ya san zai yi wuya mai martaba ya sake aura masa wata 'yar ta sa. "Mun karɓi alfarmarka Dattijo Maharaz, za mu duba a cikin iyalanmu wacce ta fi dace wa da shi. Bayan ita ko akwai wata buƙatar?" Tashinta daga bacci kenan ta ji kanta ya sara mata, ta jima ba ta ji irin haka ba don haka ta ɗan jingina da bango tana murza idanu. Ba ta ga Mai gado a ɗakin ba kuma da ma ta san ba lallai ta ganta na tun da suna can suna hidimar abincin tarbar baƙi, lalubulen ɗakin ta ji yana kaɗawa a hankali ta kai idanunta wurin. A firgice ta miƙe tsaye gabanta na faɗuwa tsoro ya mamaye ta, kamar yadda ta saba ganinta cikin shirgarta ta kullin yau ɗin ma a haka take a tsaye tana sakar mata murmushi. A ɗan tsorace Jawahir ta takure a bango, sai ta ga matar ta shigo cikin ɗakin ta zauna a gefen gadon da take kai. "Me ya sa a kullin ba kya sabo da ni? Me ya sa kika tsoron tozali da ni? Ko kinsan tsoro ba ya daga cikin hali da ɗabi'ata me ya sa muka bambamta da ke a fagen halitta da sura?" Jawahir ta zuba wa matar da a kullin suka haɗu take tunasar da ita cewar ita mahaifiyarta ce. "Ni mahaifiyarki ce ki daina tsora ta da ni." Gyaɗa kanta Jawahir ta yi sannan matar ta ci gaba da cewa. "Ungo wannan riƙe." Ta miƙa mata littafin da ke ɗauke da labarin hidaya, a baya ban ɗauke shi da muhimmanci ba, amma a yanzu da Shugaba yake son shiga gona ta dole zan nuna masa ya yi sake ɗan zaki ya girma. A tsammaninsa ya ƙone littafin gabaɗaya kowa ya rasa, bai sai a lokacin da ya jefa shi wuta abin da bai sani ba a kan hannuna ya ɗora shi ba. Wannan littafin ki adana shi ba na son ko Mai gado ta san da shi, shafi kaɗan ya rage ki kammala karatunsa, idan kin kammala kuma zan sanar da ke abin da za ki gudanar a nan gaba." Ta ci gaba da gaya mata ƙa'idojin littafin da kuma yadda za ta karanta shi. Har ta miƙe za ta fita sannan ta juya ta furta, "Ki tabbatar da kin ɓoye shi yadda wani ba zai samu nasarar ƙwace shi daga wurinki ba." Gyaɗa mata kai kawai Jawahir take sannan ta ɗaga labulen ta fice daga ɗakin. Juya littafin Jawahir ta fata yi tana mamakin dalilin damƙa mata shi, ba don ta gargaɗe ta kada ta sanar da Mai gado ba da ta nuna mata shi. Ta shi ta yi ta bankaɗa ƙarƙashin gadonsu ta tura shi can ƙasan wani ƙullin kayanta sannan ta zauna shiru tana tunanin lokacin da za ta samu ta karanta shi. Murmushi Dattijo Maharaz ya yi ya ce, "Na gode ƙwarai da wannan karamcin da ka nuna mini ranka shi daɗe, kuma a yanzu ba ni da wata buƙata da nake da ita sai dai ko shi Sarki Abdul'aziz idan yana da ta cewa." Wata kunya ta mamaye Sarki Abdul'aziz ya kasa furta komai sai sunkuyar da kai ƙasa da ya yi yana yi wa Mai martaba godiya. Dattijo Maharaz ya dubi wurin da Kamalu yake zaune ya ce. "Wane ne kai? Ita ce tambayar da a kusan kullin muka haɗu da kai Kamalu sai ka wurga mini ita, na sha kawar da hankalinka tun kana ƙarami amma idan ba ka manta ba a baya na yi maka alƙawarin sanar da kai asalina da tushena da ma dangantakar da ke tsakanina da Marigiyin Aminina Sarki Muhammad Safwan." Kamalu ya saki Murmushi sanna ya furta. "Ka daɗe kana ja mini rai don haka ma na haƙura Dattijo Maharaz." Dattijo Maharaz ya ce, "Yanzu sai ka fi jin armashi da daɗin labarin saɓanin lokacin baya da ba lallai ka fahimci abin da nake so ka fahimta ba. Kamar yadda waɗanda suka sani da waɗanda ba su sani ba zan sake sanar da ku, ni dai ba bil'adam ba ne. Na fito ne daga jinsin Jinnu, sai dai kuma ni da iyalaina duka musulmai ne." Damuwar yau da gobe ta sa Fargi ta tunkari Sarki Sulaiman dangane da halin da take ciki na bayyanar cikinta da ƙalubalen da za ta fuskanta. Wannan shi ne ga ƙoshi ga kwanan yunwa, shi a ɓangaren matansa babu wacce take ciki har mahaifiyarsa ta fara ƙorafi, ga ita kuma Fargi da ciki amma babu halin bayyanawa. Lallashinta ya yi sannan ya shiga tunanin mafitar da za su samawar wa kansu. Da farko har shawara ya ba ta akan ko ya ɗauke ta ya samar mata gida ta zauna sai ta ga wannan ba mafita ba ce, don Shugaba na iya binciko halin da take ciki. Watarana tana zaune a ɗakin mahaifiyarta a lokacin cikin jikinta ya shiga wata na huɗu, ya bi jikinta ta yi ƙiba ta murje ta yi kyau. Shugaba ya aiko da kiranta, haka kawai ta ji gabanta na faɗuwa amma gudun kada ya fahimci halin da take ciki ya sa ta shirya ta je wurinsa. "Wannan ne mijin da kika aura, kuma mahaifin abin da yake cikin?" Shugaba ya wurga mata tambaya yana hasko mata hoton Sarki Sulaiman. *SHU'UMAR MASARAUTA* *38* *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Cike da jin daɗin kalaman Dattijo Maharaz mutanen ɗakin suke gyaɗa kawunansu, har ya yunƙura zai ci gaba da magana Bamaguje da ke gefe ya ce. "Zan gusa haka Maharaz tun da na kammala abin da ya kawo ni, kamar yadda na gaya maka a baya lafiya ta fara rauni a gare ni..." Kalaman Bamaguje suka katse sakamakon wata irin cafka da suka ga wannan hallitar mai ɗauke da surar Baiwa Maimuna ta yi masa. A zabure su Mai martaba suka miƙe saboda tashin hankali, Bamaguje ya kwarara wata irin ƙara wace ta sake razana mutanen da ke cikin ɗakin, tamkar ba shi ya yi ta ba. Nan take Bamaguje ya fara yunƙurin amfani da alƙaluman tsafinsa da sihiri amma sai ya gagara aiwatar da koma, a ɓangare ɗaya kuma Guzzu ya ci gaba da kai masa cafka ta ko ina. Da ƙyar Bamaguje ya samu ya bugi ƙasa tare da furta waɗansu kalmomin tsafi nan take suka ɓace gabaɗaya. Ajiyar zuciya gabaɗaya suka sauke Mai martaba na shirin magana Sarki Abdul'aziz ya zayyane masa duk abin da ya faru game da Baiwa Maimuna, a nan suka sake jinjima al'amarin Fulani Umaima da rashin imaninsu ita da Bamaguje. Dattijo Maharaz na daga wurin da yake zaune bayan duk sun koma sun zauna, ya ci gaba da cewa. "Sunana Maharaz bn Muhammad Ishaƙ. Asalinmu mun kasance 'yan ƙasar Misra, sakamakon a can aka haifi magabatanmu wato iyayen kakanninmu kusan kimanin ɗaruruwan shekarun da suka gabata. Ina da matan aure biyu da 'ya'ya goma sha biyar, yayin da maza suka fi yawa a ciki. A yadda na samu labari daga cikin kundun labaran tarihi, asalin wanda ya fara zama a wannan ƙasar kakan-kakana ne mai suna Huzaifa. An ce dalilin barowarsa daga Misra bai wuce auren dole da ake shirya za a yi masa shi da wata 'yar uwarsa ba, silar haka ta sa ya yi nisa da gida ko ya samu farinciki har ya auri wacce yake so. An ce ya shafe sama da shekara saba'in a ƙasar nan ba tare da kowanne jinsi ba har Allah ya haɗa shi da matar aure mai suna Zuwaira, ita kuma ta kasance daga cikin jinsin aljanun ƙarƙashin ƙasa saɓanin mu da muka kasance Jinnul-turabiy. Wannan auratayyar ita ta haddasa zuri'a mai girma, kuma a yadda na ji labari kakan-kakana Huzaifa ya tara iyali mai matuƙar girma sai suka samu baƙuncin Aljani Rabo wanda ya kasance daga jinsin baƙaƙen aljanun doron ƙasa, kuma shi ne asali da tusheh samuwar Shugaba Furhussam wanda muka fafata da shi a baya. Sun ci gaba da rayuwa har kowa ya tara iyalinsa cikin karamci da mutumta juna, na samu labarin cewar a daidai wannan gaɓar sai waɗansu Fulani da buzaye suka yada zango a daidai daular da Huzaifa ya kafa. Rabo har ya so su tashi waɗannan Fulanin waɗanda da alama gudun hijira suka yo suka yada zango a nan sai Huzaifa ya hana shi a yadda aka ce ya nuna masa cewar tun da ba shiga huruminsu suka yi ba gara a ƙyale su. Zaman Fulanin nan da buzaye sai ya zama suma sun kafa na su garin suka naɗa shugabanni har zuwa masu masarautu a cikinsu. Sanu a hankali suka ci gaba da bunƙasa har ya zamana Masarautar Huddam ta fara gawurta, kuma babu wani ƙalubale da suke fuskanta daga wurin jinsin Huzaifa da Rabo tare da iyalansu." Dattijo Maharaz ya dakatar da maganar da yake yi sakamakon ɗaga hannunsa da Kamalu ya yi alamun akwai tambayar da yake son yi. "Shin yaushe ne alaƙa ta shiga tsakanin aljanu da mutanen masarautar nan? Kuma ina neman ƙarin haske game da rafin tsamiya sai kuma..." Kamalu ya yi sauri katse maganarsa. Dattijo Maharaz ya lura da haka don haka ya ce. "Sai kuma me Kamalu? Yi tambayarka kanka tsaye." "Sai kuma Shurin da kake rayuwa a cikinsa wanda yake cikin turakar Mai martaba, yaushe aka kafa shi a wurin?" Dattijo Maharaz ya saki murmushi sannan ya furta. "Ni kaina ban san ranar da aka kafa wannan shurin ba, wannan shurin ya kasance mai tsohon tarihi domin Kakana ya ce mini shi kansa zuwa ya yi ya tarar da shi. Amma an yi mini cikakken bayani game da dalilin wanzuwarsa a wurin." "Muna sauraronka Datijo Maharaz." Sarki Abdul'aziz ya faɗa cike da zaƙuwa. "A wancan lokacin mai tsawo an ba ni labarin cewar Huzaifa shi ya kasance tamkar jagora kuma shugaba har ya kasance sauran al'ummar jinsina sun damƙa masa sarauta, wacce a ita ce take tafe har kawo kaina. Kuma a lokacin da kakana ya karɓi mulki daga hannun mahaifinsa an ce a lokacin ne kuma Marigayi Sarki Sadiƙƙu yake kan mulki cikin masarautar mutanen masarautar Huddam." "Idan na fahimci labarinka Dattijo Maharaz kana nufin wannan masarautar ta huddam ta kasance masarautar da jinsi biyu suke mulkarta? Jinsin fararen aljanu da kuma jinsin bil'adama?" Mai martaba Maifin Fulani Babba ya tambaya. "Tabbas haka ne Ranka shi daɗe, kuma wancan shurin da yake ɗakin Sarki Abdul'aziz a nan muma masarautarmu take, an faɗa mini wannan ya samo asali tun a kan Sarki Saddiƙu jinsinmu suka fara ƙirƙirarsa domin ƙulluwar alaƙa mai ƙarfi a tsakaninsu. Kuma an ce a watarana ne Kakana Sarki Ishaƙ ya samu Sarki Sadiƙƙu a cikin ɗakinsa, Sarki Sadiƙƙu ya tsorata da ganin Kakana amma da ya zauna ya yi masa magana ta fahimta sai suka fahimci juna ya kuma ja shi har uwar ɗaki ya nuna masa asalin wurin da suke rayuwa. Tun daga wannan ranar zumunci mai ƙarfi ya shiga tsakaninsu, don an ce wani lokacin haka kakana zai ziyarce shi su sha hira kuma duk abin da ya ga Sarki Sadiƙƙu zai yi ba daidai ba zai yi masa gyara. Kuma an ce suna matuƙar ba wa juna shawarwari akan abin da ya kamata da harkar masarautunsu, har dai tafiya ta miƙa Sarki Sadiƙƙu ya kwanta dama. An yi sarakuna da dama daga jinsina zuwa naku a cikin masarautar nan har kawo lokacin da muka haɗu da amini marigayi Muhammad Safwan." Idanun Dattijo Maharaz suka ciko da ƙwalla, ya ɗan haɗiyi yawu mai ɗaci sannan ya ci gaba da cewa. Kafe shi da idanu Fargi ta yi tana mamakin yadda aka yi Shugaba ya gano gabaɗaya halin da take ciki, ta furzar da iska mai zafi sannan ta ce. "Ya aka yi kasan da haka?" "Kamar kin manta a gaban wanda kike Fargi?" "Shi ya sa na tambaye ka, don da wani ne ba kai ba sare kanshi zan yi." "Kin manta hukuncin wanda ya aikata abin da kika yi kisa ne a cikin zuri'armu?" Shugana ya wurga mata tambaya. "Ina sane da haka, kuma dalilin hakan ya sa nake son ruguje wannan mummunar ɗabi'a ko al'adar da ba ta da amfani." "Idan na bayyana wa mutanen gari kin san take za su zartar miki da hukunci." A razane Fargi ta dubi Shugaba Zurufu, fuska da muryarsa ko kaɗan babu alamun wasa a ciki. "Idan kika ce da tashin hankali za ki biye masa tabbas za a yi biyu babu, zai sa a kashe ki kuma ki rasa abin cikinki. Tun wuri ki san abin yi tun talatarki ba ta ƙare a raba ba." Zuciyarta ta wassafa mata bayanai. Sai da ta gyara zamanta sannan ta dubi Shugaba Zurufu ta ce. "Me ya sa za ka yi mini haka Shugaba? Ka san dai kai ne mai lullaɓa mini bargon sutura ya kake yunƙurin yaye mini wanda na lulluɓa wa kaina?" "Saboda tun farko kika bijire mini a kansa, ina nufin Sarki Sulaiman." Shugaba Zurufu ya yi maganar zuciyarsa fes don ya lura da samun nasarar da ya yi a kanta. "Yanzu me ye abin yi Shugaba? Ina son mijina kuma ina son abin da yake cikina!" Fargi ta furta tana zuba masa manyan idanunta. "Zan taimaka miki har ki haife abin cikinki ba tare da wani rai mai numfashi ya fahimci halin da kike ciki ba. Na rantse miki da gawurtar tsafina ko mahaifinki ba zai san da cikin jikinki ba ballantana ya san ranar da za ki haife shi." "Ina matuƙar alfahari da kai Shugaba Zurufu..." "Amma da sharaɗi." Shugaba Zurufu ya katse ta. "Wanne sharaɗi ne? Matuƙar zan iya masa na amince zan cika maka shi." "Za ki mallaka kuma ki sadaukar mini da dukkan tsafinki." A zabure Fargi ta miƙe tsaye jikinta na karkarwa, "Kana nufin tsafin da nake rayuwa a doronsa?" Fargi ta jefa masa tambaya a ɗimauce. Gyaɗa mata kai Shugaba ya yi, wani tunani ya faɗo mata ta koma ta zauna murya a sanyaye ta furta. "Kalamanka sun gigita ni Shugaba amma zan yi tunani game da wannan furucin naka! Ina son Tsafina, ina son mijina kuma ina son cikina! Dole zan zaɓi abin da zai fi dacewa da rayuwata." Shugaba Zurufu ya ji daɗin kalaman Fargi, ta yi masa sallama cike da damuwa ta fice daga kogon tsafinsa. Tun a daren ranar Fargi ta nemi Sarki Sulaiman ta sanar da shi halin da take ciki dangane da abin da Shugaba ya ɓullo mata da shi, ya kaɗu matuƙa har sai da ya yi yunƙurin zuwa wurin Shugaba don ya ci masa mutumci amma Fargi ta dakatar da shi don ta san matuƙar ya aikata wannan kuskuren Shugaba sai ya hallaka shi. "Faɗa da aljani babu riba! Ka bar mini komai a hannuna, na san ta yadda zan ɓullowa al'amarin." "Na rantse da girman Allah matuƙar ya taɓa mini mata ko abin da yake cikinta sai na tozarta shi." "Ba na son jin haka daga gare ka gwarzona, kamar yadda na ce ka bar mini komai zan san hanyar da zan ɓullo masa ta ruwan sanyi." Jin shirun Mai gado da ya yi yawa ya sa Jawahir ta diro daga kan gado ta janyo ƙofar ɗakin ta rufe, sannan ta leƙa can ƙarƙashin gadon ta zaro littafin. Haka kawai ta ji gabanta na faɗuwa ta haye can saman gadon ta buɗe shafin baya, ta ga duk ya shafe babu ko ɗigon rubutu a jiki. A hankali ta ci gaba da buɗewa har ta kai shafin da ya fara da rubutu, ta yi jim kamar mai nazari sannan ta ɗago ta ci gaba da karantawa. Sai da Sarki Hafiz ya kurɓi ruwan da ke gabansa sannan na ji ya ci gaba da cewa. "Na ji labarin an ce Kakana ne ya kai ziyara wurin wani babban boka, a binciken da yake yi masa ne ya tabbbatar da cewar Mahaifiyarki na ɗauke da kwantaccan cikinki, kuma matuƙar ya bari aka haife ki duk daren daɗewa sai kin karɓi kambun sarautarku ya dawo hannun zuri'ar mahaifinki. Dalilin da ya sa Kakana ya shiga binciken wurin da Mahaifiyarki take, kuma abin da bai sani ba tuni wani aminin mahaifinki aljani Sadi ya ɓoye mahaifi da mahaifiyarki. Sakamakon tuni ya sanar da su abin da yake faruwa." Jin Sarki Hafiz ya yi shiru ya sa na dube shi, sai kawai na ji muryarsa ta yi rauni ya furta mini. "Ki yi haƙuri da wannan furucin da zan furzo miki." A sanyaye na dube shi ina yunƙurin yin magana na ji ya ci gaba da cewa. "In taƙaice miki labari an ce a ranar da alƙadarin zamanki a cikin mahaifiyarki ya ƙare ita kuma a ranar Allah ya yi mata rasuwa, a yadda na ji labari an ce ko fuskarki ba ta iya gani ba ballantana ta san kalar hallitar da ta haifa. Mutuwar mahaifiyarki ba ƙaramin ɗaga hankalin mahaifinki ta yi ba, an ce sai da ya shafe sama da watanni yana jimamin mutuwarta. Daga lokacin da ta haife ki sai rainonki ya koma wurin mahaifinki da amininsa Aljani Sadi, kuma kin shaƙu matuƙa da mahaifinki kwatsam! Watarana ya wayi gari da ciwon ajali wanda a sanadinsa ne rai ya yi halinsa." A razane na dubi can gefen da nake ganin mutumin da a kullin yake ce mini shi mahaifina ne. Jikina na karkarwa na nuna wurin da yake tsaye yana sakar mini murmushi na furta. "Shi kuma wancan da nake kallo a matsayin mahaifina waye shi?" "Jawahir lafiya kika datse mini ƙofa?" Kalaman Mai gado suka katse Jawahir daga karatun littafin da take yi, da sauri ta rufe littafin ta tura shi can ƙarƙashin gado sannan ta zare sakatar ɗakin. "Inna wallahi sanyi nake ji shi ne na rufe ɗakin, har kin dawo?" Mai gado ta kafe ta da idanu tamkar tana son gano gaskiyar abin da Jawahir ta gaya mata. Kai kawai ta gyaɗa mata sannan ta wuce cikin ɗakin, Boka Shaddas da ke laɓe a bayan ɗakun nan Bayin ya yi ƙwafa yana sake laɓewa don ya ci alwashin a wannan ranar sai ya ɗauke Jawahir ya kai wa Shugaba Zurufu ko ya fanso Basirunsa. "Allah ya gafarta wa aminina." Dattiji Maharar ya furta jiki a sanyaye. Kamalu ya ƙarasa gabansa ya zauna a gefensa, cikin sigar lallashi ya furta. "Tabbas na fahimci abin da kake ji a zuciyarka Dattijo Maharaz, na fahimci haka ne bayan rashin su Inna wuro da na yi a kusa da ni. Addu'a ita za ka bi amininka da ita tun da duk mai rai mammaci." Jinjina kai Dattijo Maharaz ya ci gaba da cewa. "Mahaifina ya ba ni labarin cewar tun ina rarrafe muka haɗu da Sarki Muhammad Safwan a lokacin da mahaifiyarsa take shiga da shi turakar mahaifinsa, wannan abota tamu ta kai har zuwa samartakarmu, duk inda aka ga Sarki Safwan za a ganni a wurin. Hatta wurin zance ni nake yi masa rakiya, don ko ita marigayya da ya aura ba ta taɓa sanin ni ba jinsinku ba ne har sai bayan ɗaurin aurensu. Faɗar irin shaƙuwar da muka yi da Marigayi abin zai ɗauke mu lokaci mai tsayi, amma abu ɗaya na sani ni da shi aminai ne da muke fatan saduwa har ranar gobe ƙiyama." "Ma shaa Allah! Allah ya cika buri Dattijo Maharaz." Mahaifin Fulani Umaima ya furta zuciya a karye. "Ba tun yau ba mahaifina ya sanar da kai tasirinka a cikin masarautar nan, ya sanar da ni bincikensa ya nusar da kai wanzuwarka. Shin ka tuna wurin da na kai ka Kamalu? In da na ce ka ɗauki taɓo ka shafa a bangon wurin?" Da sauri Kamalu ya furta. "Na tuna Dattijo Maharaz." "Duk wanda ya samu sanar aiwatar da duk abin na sa ka aiwatar ana yi masa kyakkyawan zaton kasancewa Shugaba kuma Sarki a Masarautar Huddam, ashe alaƙar da ke tsakaninmu da kai ba ta wuce gurbin da Futhussam yake ƙoƙarin ajiye ka ba. " Dattijo Maharaz ya sake numfasawa sannan ya ci gaba. Dalilin da ya sa ba a shan kowanne irin Nono a masarautar nan ranar juma'a bai wuce wani mummuna saɓani da ya gifta tsakanin wata jikar Rabo da wani Sarki da aka taɓa yi daga cikin jinku ba, wannan faɗan har sai da ta kai ta kawo iyayena sun shiga ciki kuma a ranar aka tattarawa 'yar fulani kayanta aka fitar da ita daga Masarautar nan. To sai dai kafin ta tafi an kai ruwa rana da ita, har sai da ta kafa wannan sharaɗin na haramta shan Nono a ranar juma'a kuma babban kuskuren da Sarki Rufa'i ya aikata da kai tsaye ya amince da buƙatarta. An ce ta ce duk wanda ya sha Nono a ranar shi kenan an rasa shi gabaɗaya. Kuma a yanzu haka wanan 'yar fulani tana can gaɓar kogin Yulwa ta kafa zuri'arta a can, amma duk ranar Juma'a ta kan kawo ziyara gidan nan. Shi kuma rafin tsamiya tsohon rafi ne da tun asalin zuwan kakan-kakana Huzaifa yake, a labarin da aka ba ni an ce shi kansa Huzaifa wannan rafin ya taɓa cinye masa 'ya'ya uku. Sai dai an ce duk tsananin bincikensa bai gano ainihin me yake sababba faruwan hakan ba, amma yau kusan shekara ɗari da ashirin kenan da na ji an ce Babban Malamin jinsinmu Sheik Saifullah da ke ƙasar Madina ya san da wannan tarihi, da musababbin faruwarsa. Kun san komai sai Allah ya nufa, har yau ban taɓa zuwa wurinsa don na jin yadda aka haihu a ragaya ba. Kuma a ƙallah na je na yi umara da aikin Hajji babu adadi. Ban sani ba nan gaba ko zan iya zuwa don na ji yadda za mu magance wannan matsalar. Na gode wa Allah, da Allah ya sa na sauke nauyin da ke kaina na aminina kuma ɗan'uwana Marigayi Safwan. Tun a shekarun baya nake jin ina ma ace aure ya hallata a tsakanin jinsina da jinsinku, da mun ƙulla zumuncin da nake fatan kasancewarsa har gidan Aljanna." Dattijo Maharaz ya ƙarasa maganar a ɗan raunane. Dattijo Maharaz ya miƙe tsaye, sai da ya bi ɗaya bayan ɗaya ya miƙa musu hannu suka yi musabiha sannan ya furta. "Ni a nan zan gusa Sarki Abdul'aziz, Kamalu sai wani lokaci idan Allah ya yarda." Lokaci ɗaya gabaɗaya suka ji babu daɗi, Kamalu ya riƙo hannun Dattijo Maharaz ya yi masa rakiya zuwa bakin ƙofa, waigowar da Kamalu zai yi ya neme shi ya rasa. Mai martaba Mahaifin Fulani babba suma suka yi wa Sarki Abdul'aziz sallama, duk yadda ya so su kwana amma fir suka ƙi amincewa. Ya sa Bayi suka shiga haɗo musu kayan da ya tanadar na tsarabarsu, suka yi musu rakiya Sarki Abdul'aziz yana yi musu alƙawarin kai musu Kamalu idan aka kwana biyu. *SHU'UMAR MASARAUTA* *39* *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* https://chat.whatsapp.com/LAizQA6PofSLoFhQ7XeaQx Assalamu alaikum. Ina kuke masu bukatar kayan kitchen masu kyau da quality.ina masu bukatar bedsheets blankets.ina Kuma masu bukatar takalma da jakunkuna masu kyau.ina masu bukatar latest kayan yara na maxa Dana. mata...albishirnku kukanku ya kare kuji joining group din R&U exclusive kitchen and more..kuga kaya latest masu kyau Wanda ake yayi a farashi mai sauki. Sannan Kuma masu hada lefe bata barku a baya ba.tana hada lefe na gani na fada a farashi daidai da aljihunku Sannan wani abun dadinma masu bukatar kayan kitchen Yana yin adashin gata Wanda zaa baka account number kadinga Tara kudinka aciki iya adadin da kuke da bukata in kagama sai ka siyi abinda kake bukata ba cuta ba cutarwa. R&U exclusive kitchen and more Suna garin kano .sannan suna tura kaya kowanne state afadin kasar nan. Haka kasashen da suke makwabtaka da nageria duk muna tura kaya cikin amincin Allah Duk maineman Karin bayani g number 07034559202 Cikin talatainin dare abin duniya goma da ashirin ne ya haɗe wa Fargi ta kasa kwance ta kasa tsaye. Ayarin tunaninnka suka cunkuso mata har ta fara jin sarewa a zuciyarta, tare da tunanin miƙa wa Shugaba kai bori ya hau. "Matuƙar kika sare tun daga yanzu tabbas za a ci gaba da tafiyar da babu ci gaba a cikinta." Zuciyarta ta shawarce ta. Miƙewa ta yi zaraf ta fice daga cikin bukkarsu a lokacin garin tsi sai kukan tsuntsaye da ƙananan dabbobi da yake tashi. Daga can kogon dutsen Shugaba ta hango wuta na tashi wanda hakan ne ya alamta mata wani aikin siddabarun yake aiwatarwa. Kai tsaye wurin bishiyar bauta ta nufa zuciyarta a karye ta zube bisa gwiwoyinta, ta fashe wani irin matsanancin kuka. "Kin ɓullo da abin da bai cika ɗore ba a cikin zuri'arku shi ya sa al'amura ke yunƙurin ƙwace miki." Daga jikin bishiyar ta ji an furta. "Dalilin haka na kawo kuka gare ki domin ke ce mai yaye mini baƙinciki. Ina fatan yadda na zo a sirrance duka aikin da za a yi mini na sirri ne ba tare da wata hallita ta sani ba." Furgi ta faɗa jikinta a sayaye. "A zubi da surar halitar abin da yake cikinki duk rintsi da tsanani zai zo duniya, sai dai kuma kash! Ƙaddara ta riga fata Fargi, akwai wani al'amari da zai iya giftawa a nan gaba. Za mu taimaka miki amma da shawararin da za ki bi amma kin san dole a yi ban gishiri na ba ka manta." "Ina matuƙar son mijina, cikin jikina da tsafina abin bauta! Shugaba ya gindaya mini wani sharaɗi ni kuma ya mini tsauri ba zan iya sadaukar da tsafina ba." "Ba za ki sadaukar da tsafinki ba! Hasali ma sai dai ki sadaukar da duk wata baiwarki ga abin da ke ɗauke a cikinki, mu kuma mun yi miki alƙawari sai mun kula da abin da za ki haifa ko bayan ba kya raye. Amma idan kin yadda da duk wani sharaɗi da za mu gindya miki?" Damuwar da take ciki ce ta ji ta fara yaye mata, ta sauke ajiyar zuciya ta furta. "A shirye nake na karɓi duk sharaɗin da madogarata za ta gindaya mini." "Idan kika ƙi amincewa Shugaba zai hallaka ki kuma zai hallaka ɗan cikinki da shi kansa mijin naki, matuƙar kika yi masa taurin kai wato kika bari ya fallasa cikin jikinki. Ga shawara ta fako; ko ki sadaukar da abin cikinki a wurin Shugaba, ko ki sadaukar masa da tsafinki ko kuma ke ki sadaukar da kanki domin kuɓutar abin da yake cikin?" "Ban fahimci na sadaukar da kaina ba?" Cikin sauri ta wurga tambaya. "Muna nufin ki haƙurcewa rayuwar gabaɗaya domin wannan ya kasance daga cikin zanen kundin ƙaddararki. Bari na fito fili na miki bayanin yadda za ki fahimta." Take jikin Fargi ya fara karkarwa. "Ƙaddararki ce da abin da za ki haifa, ba za ta rayu da ke ba, ba za ta taso a ƙarƙashin rayuwar tsafi da sihiri ba. Abu ɗaya na sani shi ne Mutuwa! Mutuwar ɗayanku na iya kasancewa bayan haihuwarki. Wannan ya zama dole a gare ku tamkar yadda kowanne mai rai yake numfashi." "Ita dama rayuwar duniya sai wani ya rasa wani yake samu abin bauta! Matuƙar abin da zan haifa zai kasance shi ne silar kuma tsanin da mutanen yankin za su sauka daga kan doron mummunar wannan al'adar, zan amince da duk wani sharaɗi." "Mun haura sararin samaniya mun riski mabambamdan bayanai dangane ita, haihuwarta da rayuwarta babbar nasara ce ba iya wannan yanki ba. Har zuwa yankin da za ta yi rayuwa a cikinsa." Cikin ƙarfin hali da dakiyar zuciya Fargi ta furta. "Na amince halllitar da zan haifa ta yi rayuwa a doron ƙasa." "Amma hakan ba za ta kasance ba sai kin amince da sadaukar da ainihin ruhin da siffarki." Jim Fargi ta yi, lokaci ɗaya idanunta suka ciko da ƙwalla, hawaye bibbiyu ya fara zuba daga kwarmin idanunta. Hannunta ta kai saman cikinta, ta ji yadda ɗan tayin cikinta ke ta wutsil-wutsil. Ta ɗaga kai ta dubi murgujejiyar bishiyar kukar da ke gabanta mai ɗauke da mummunar siffar ban tsoro. "Duka na amince matuƙar 'yata za ta yi duk abin da ka furta mini abin bauta." Fargi ta ƙarasa maganar kuka na cinta. Tun da Sarki Abdul'aziz ya sa aka sake mayar da su Fulani Umaima ɗakin duhu a kullin sau ɗaya ake kai musu ɗan ƙanƙanin abincin da ko yaron goye ba zai ishe shi ba. Cikin wawaso suke cafkar kwanon bai fi su yi loma uku ya ƙare ba. Jakadiya kusan kullin haka za ta ji an zo ƙarfi da yaji ana mu'amala da ita, a ɓangare ɗaya kuma kullin mamanta ɗaya ƙara zaftarewa yake yi yana zagwanyewa. Fulani Umaima kuma duk dare wannan mummunar hallitar ke zuwa ta saka tsinin bakinta mai matsanancin kaifi a wannan tsokar naman da ke zazzagowa daga ƙasanta. Haka take kwana tana ihu tun tana iya zulle-zulle har dai ta sulale ƙasa sumammiya, sanyin asuba idan ya doke ta ne yake farfaɗo da ita. Wannan dalilin ya sa ko harabar wurin ɗakin nasu ka dosa ban da wari da ƙarni babu abin da yake tashi sakamakon yadda ƙasan Fulani Umaima ke fita ruwa mai ɗoyi, ita kuma Jakadiya mamanta ɗaya yake fitar da ruwan mugunya mai wari. A ranar da Muhsin ya je ya gano mahaifiyarsa kai tsaye turakar Sarki Abdul'aziz ya wuce, shi kaɗai ne a zaune yana lissafa kuɗaɗen da suka shigo masa na ribar da aka samu na amfanin gonar da ake sayarwa a sassan yankuna. "Mahaifiyata na buƙatar agaji, tana cikin mawuyacin hali ya kamata Mai martaba ya san abin yi." Ƙuri Sarki Abdul'aziz ya yi masa yana kallonsa sannan ya ce. "Muhsin ba shi da hurumi a kan wannan maganar." A razane Yarima Muhsin ya ɗago sakamkon jin yadda mahaifinsa ya ambaci sunansa kai tsaye, idan ba mantuwa ya yi ba rabon da Takawa ya kira shi da Muhsin zai kai shekara ashirin, "Idan an kammala abin ake yi a bamu wuri muna buƙatar keɓewa." Kamar ba zai miƙe ba haka ya zuba masa idanu yana kallo, jiki a sanyaye Muhsin ya fice daga cikin ɗakin. Tun da haka ta faru daga Ruƙayya har Kamalu da Abubakar Mai gado ce ke kula da al'amuransu, wannan ta sa Jawahir ta fara rage shiga sashen don babu shigar da za ta yi ba tare da wani faɗa ko yamutsi ya shiga tsakinsu ba. Shi kuwa Muhsin dama ko da wasa bai taɓa saka ƙafarsa sashen ba, don har lokacin yana ɗan jin zafin Kalamu don gani yake silarsa ce komai ya tarwatse ya watse musu. Mai martaba tare da 'yan uwan Fulani babba a gajiye tuɓus suka koma gida, kallon fuskokinsu kaɗai zai tabbatar maka da ƙunsassun labaran da suke tafe da su. Sai dai kuma ƙarin wani farinciki tun mai martaba bai shiga cikin gida ba, ya samu kyakkyawan albishiri ɗin samu lafiyar Yaya Halima daga ciwon haukan da take yi shekara da shekaru. Saboda tsabar farinciki Takawa da kansa ya nufi ɗakin da Yaya Halima take zaune, jikinta duk a sanyaye ta bishi da kallo har ya ƙarasa gabanta. "Halimatuna wai da gaske kin samu lafiya?" Hawayen da take maƙalewa suka samu sukunin ɓallewa, ta rushe da matsanancin kuka haɗe da faɗa wa jikinsa."Ranka shi daɗe wai ni ce na yi ciwon hauka? Kai ma ka yarda a baya na yi ciwon hauka?" Ajiyar zuciya ya sauke, ya sa hannuwa biyu ya zaunar da ita sannan ya furta. "Halimatu ba na son rigima, don Allah ina son ki kwanta ki huta zuwa dare zan zauna mu tattauna da ke." Gyaɗa masa kai ta yi ya muƙe ya fice daga ɗakin. Kusan gabaɗaya iyalansa ya tara a babbar rumfarsa suka shiga mayar da abin da ya faru tun daga farko har ƙashe. "Ranka shi daɗe ba ƙaramin mamakin abin da ya faru da yarinyar nan muka yi ba. Baiwa Zahra'u ta kai mata abinci za ta fito kenan ta ji ta ƙwallah wata irin ƙara, ta shiga kururuwa kamar za ta tayar da gidan, da ƙyar muka samu aka rirriƙe ta kawai sai gani muka yi yarinya ta fara wata irin zabura tana karkarwa. Daga nan kawai sai gani muka yi ta yanke jiki ta faɗi, bayan an zuba mata ruwa ta farfaɗo sai gani muka yi tana bin mu ɗaya bayan ɗaya tana kallo. Daga haka ta fara wurgo mana tambayoyi har dai muka fahimci ta dawo hayyacinta." Fulani Sadiƙƙa kishiyar Mahaifiyar Fulani babba ta yi maganr cikin farinciki. Ita ce matar mai martaba ta huɗu. Mai martaba ban da murmushi babu abin da yake, "Tabbas addu'a ba ta faɗuwa ƙasa banza kuma duk abin da ka yi haƙuri za ka ci ribarsa. Allah ya sake shiga tsakanin na gari da mugu." Gabaɗaya suka amsa masa da Amin. Bayan ya sallame su ya bada umarnin a yi gumba, ƙuli-ƙuli da tuwon sadaka domin godiya ga Ubangiji bisa waɗannan abubuwan farinciki da na akacin haka da ya same shi. Sannu a hankali Sarki Abdul'aziz ya sa aka ci gaba da ba wa Kamalu horon yadda 'ya'yan Sarki ke gudanar da al'amaransu, bai sha wata wahala ba tun da dama ya san waɗansu daga ciki al'adun don haka ba a ɗauki lokaci ba ya goge tamkar ba shi ba. Sai dai har wannan lokacin bai fasa hulɗa da sauran abokansa na baya ba waɗanda suka kasance 'ya'yan Bayi. Su Inna wuro tuni suka koma sashen da Sarki Abdul'aziz ya gina musu, ita kanta Mai gado a wannan lokacin Takawa ya ba su umarnin komawa wasu manyan ɗakuna da ke maƙotaka da sashen Fulani babba, sakamakon yadda take ba wa su Abubakar kulawar da ta dace tamkar ita ta haife su. Sai ya zamana ita ma Jawahir ta samu fada a wurin Sarki Abdul'aziz ya ɗauke ta tamkar 'yar cikinsa. Haka kawai wani lokacin idan Mai gado take zuba wa Kamalu idanu tana jin ƙwalla na zuba mata. "Allah sarki rayuwa kenan, Allah ba ya taɓa barin wani don wani ya ji daɗi." "Rayuwa darasi ce! Da ace mahaifiyarku na raye ban san irin farincikin da za ta yi ba, sai ga shi duk wata kulawa da farinciki da kuke samu ƙasa ta turɓuɗe idanunta." "Allah Ya gafarta miki Fulani, ina ma kina raye Takawa yake ba wa iyakinki wannan kulawar da a kullin kike mafarkinta. Na sake aminta da ba kowanne abu ne mai rai yake nema ya samu ba." Ire-iren kalaman da Mai gado idan ta zauna zuciyarta ke saƙa mata, sai dai a hakan ma ba ƙaramin daɗi take ji ba don ba ta taɓa tsammanin bayan rasuwar Fulani za su samu koda arziƙin rabin kulawar daTakawa yake basu a yanzu ba. Kuma da faruwar haka babu jimawa Sarki Abdul'aziz ya rubuta wa Sailuba takardar saki har guda uku, a ranar Sailuba ta ci kuka tamkar ranta zai fita. Babu yadda ta iya haka ta tattara kayanta ta koma ɗakin mahaifiyarta da zama. A wannan lokacin kuma duk lokacin da damuwa ta cunkushe Muhsin ba shi da wurin zama sai harabar wurin da ta raba ɗakunan mahaifiyarsa da sashen da su Jawahir suka koma. Wani lokacin yana cin sa'ar ganinta wani lokacin kuma haka zai ƙaraci zamansa har ya tashi ba tare da ya ga gilmawarta ba. Watarana Kamalu na ɗakinsa ya aiki wani Bawa a kan ya kira masa Jawahir, lokacin da saƙon ya isa kunnenta kamar ba za ta je ba sai kuma Mai gado ta kora ta. Yana zaune a kan tabarmar kaba, ya ga ta yi masa ƙerere a ka. "Lafiya ka aika kirana?" Jawahir ta furta ƙerere daga tsaye. "Ki shiga ki gyara mini ɗaki akwai kayan wankin da na ajiye ki haɗa ki wanke su, idan kin gama ki dawo ki..." "Wallahi ni ba baiwarka ba ce, kai shaida ne ko wankin kayana wani lokacin Inna ke yi mini. Malam idan za ka ware wannan bunguzar rigar jikin naka ka share ɗakinka ka wanke kayanka tun wuri ka ware, yoo Allah na tuba aikin ƙarfi wanne iri ne ba ka iya ba. Lalla samun sararin kuturu gaɗa a cikin rama..." Da sauri Kamalu ya katse ta. "Ba na son sakarci ni kike faɗa wa haka?" Baki sake Jawahir take bin sa da kallo. Ya miƙe tsam ba tare da ya tanka mata ba, sai da ya datse ƙofar shigowa sashensa sannan ya zaro wata murtukekiyar dorina. A tsorace Jawahir ta ja da baya cikin zaro idanu. "Don Allah ka yi haƙuri!" "Kura kenan ga tsoro ga ban tsoro, a haka ta nuna tafi kowa rashin tsoro amma kuma farar kura ce." Kamalu ya faɗa a ransa. "Idan ba ki wuce kin aiwatar da abin da na saka ki ba wallahi sai ranki ya yi mummunan ɓaci." Kamalu ya yi maganar cikin tsare gida. Kamar sabuwar munafuka haka Jawahir ta sunne kai ƙasa ta wuce tana aikin lokaci-lokaci tana yi masa Allah ya isa ƙasa-ƙasa don kar ya ji. "Mai martaba mun tako ne sakamon mun samu labarin duk abin da faru, na daɗi da rashinsa, don haka muka ce ƙafa da ƙafa sai mun ƙaraso. Allah ya kiyaye gaba, Muna taya ku murna matuƙa da bayyanar wannan yaro Kamalu." Sarki Sulaiman ya furta bayan sun gama gaisawa da Sarki Abdul'aziz cikin mutumci da karamci. "Mai martaba Sarki Sulaimanu kuma fa faɗuwa ce ta yi daidai da zama." Sarki Abdul'aziz ya faɗa yana gyara zama. "Ai haka ake so Sarki Abdul'aziz wacce magana ce a bakinka?" "Maganar auren yaran nan, dama a cikin raina nake shirin turo da Shamaki domin ya nemo mana izini a wurinka. Za mu zo gaisuwar iyaye da kawo kuɗin na gani ina so." Fuskar Sarki Sulaiman ta sake faɗaɗa da fara'a." "Muna muraba da wannan maganar Sarki Abdul'aziz Ubangiji ya tabbatar mana da alherinsa." Sarki Sulaimu ya furta sannan suka amsa lokaci ɗaya. Tun Jawahir na noƙewa har ta sake jikinta ganin yadda Kamalu ya tsare gida yake buga mata tsawa, wani abin takaici da ya cika ta bai wuce yadda ya buɗe ƙofar gidan Bayin da ke hidima a sashensa suka dinga shiga suna ganin irin wulaƙancin da yake yi mata ba. Sai da ta gama wanke jinga-jibgan rigunan alkyabbunsa sannan ta koma gefe tana yarfe gumi, tausayi ta ba shi har ransa, ya gintse murmushin da yake cinsa. "Akwai alkaki da nakiya a rumfa idan kin gama." Harara ta wurga masa murya a ciki ta furta. 'Ba na ci." Ɗaga kafaɗa ya yi cikin halin ko in kula ya juya zai shiga ɗaki Bawa Bala ya ƙarasa cikin girmamawa ya zube ƙasa ya furta. "Allah ya taimake ki Takawa yana buƙatar ganinka yanzu." Da kai kawai Kamalu ya amsa wa Bawan ya juya, hanyar fita ya nufa take wasu Bayi maza guda biyu suka rufa masa baya. Hannu ya ɗaga musu da sauri suka koma ya ci gaba da tafiya, ƙwafa Jawahir ta yi tana bin igiyar da ta shanya kayan da kallo wani takaici ya sake lulluɓe. "Da ace ina da iko da tuni na karɓa na fanshe ki masoyiyata." Kalaman Bawa Auwalu ya ratsa ta, ba tun yau Auwalu yake nuna mata soyayya ba amma ko kaɗan ba ta ba shi fuska ba. Harara ta watsa masa ta fice daga gidan, har za ta wuce sashensu wata dabara ta faɗo mata. A fili ta saki murmushin ƙeta don ta ci alwashin Kamalu ba zai ci banza ba a kan mugunta da wulaƙancin da ya yi mata, sai da ta shiga sashensu ta sauya kayan jikinta sannan ta nufi sashen Sarki Abdul'aziz. Bakin Kamalu ɗauke da sallama ya shiga ɗakin saukar baƙin Sarki Abdul'aziz, sai da suka amsa masa sannan ya shiga ciki. A ƙasa ya zube cikin girmamawa ya dubi Sarki Sulaiman ya furta. "Barka da zuwa ranka shi daɗe, da fatan an samu al'ummar Masarautar Huddam lafiya." "Barka dai Sadauki, ya fama da jama'a." Sarki Sulaiman ya furta ya saka hannu a cikin aljihunsa. "Jama'a Alhamdulillah ranka shi daɗe." Waɗansu zobunan azurfa ne guda uku dukkansu duk iri ɗaya, ya miƙa wa Kamalu sannan ya furta. "Ga kyautar azurfa daga gare ni, ga kuma ƙarin alkyabbu ka ɗauki naka da na sirikina sai kuma da abokin tagwaitagarka." Sarki Abdul'aziz ba ƙaramin farinciki ya yi ba. "Muna godiya ranka shi daɗe, Allah ya ƙara wa Sarki lafiya. Ubangiji ya tsare gabansa da bayanka." Cikin jin daɗi Sarki Sulaiman ya amsa da "Amin ." Ya dubi Sarki Sulaiman. "Sarki Sulaimanu me ya sa ba ka gajiya? A ce duk lokacin da za ka ziyarce mu sai ka...?" "Kyauta ce daga mahaifi zuwa wurin 'ya'yansa." Sarki Sulaiman ya katse Sarki Abdul'aziz. "Allah ya ƙara lafiya Sarki mai matuƙar karamci da mutumci." Sarki Sulaiman na shirin amsawa Sallamar Jawahir ta karaɗe dodon kunnuwansu. Ganin takalman Kamalu ya sake tabbatar mata da yana ciki don haka ba ta jira an amsa ba ta faɗa cikin ɗakin. Muryarata har abada ba za ta taɓa zama baƙuwa a wurinsa ba, ko mutuwa ya yi ya dawo ba ya tunanin sautin muryarta zai yi masa gizo ballanta ya mantata. Tun da ya ji muryar Jawahir tsigar jikinta ta yi wani irin yarr, gabansa ya yi mummunar faɗuwa. Wani irin yanayi ya fara ratsa shi, da ƙyar ya ɗan daidaita kansa amma har lokacin ƙwayar idonsa na kan ƙofar, shigar Jawahir cikin ɗakinsa ya kusa haifar masa da dakushewar numfashi na wucin gadi, ya kafe fuskarta da kallo yana mamakin tsananin kamar da fuskarta ta yi masa da matar da har duniya ta tashi ba zai ta taɓa mantawa da ita. Sai da ta zube a gaban Sarki Abdul'aziz ka fashe da kuka. "Ranka shi daɗe ƙararsa na kawo maka wallahi yau ba ƙaramin zalintata ya yi ba." Jawahir ta ƙarasa maganar tana nuna Kamalu, kunyar duniya ta lulluɓe Kamalu. Ya sunkuyar da kai ƙasa, yana jin tamkar ƙasa ta tsage ya shige ciki. "Kamalu me ya haɗa ka da ƙanwarka Jawahir?" Sarki Abdul'aziz ya yi tambayar fuska a haɗe duk da kalaman Jawahir ba ƙaramin dariya suka ba shi ba. Jin sunan Jawahir ya sa gaban Sarki Sulaiman ya ci gaba da faɗuwa, jikinsa ya yi sanyi ya sake zuba mata ido. "Jahawir!" Ya ambata da wani irin yanayi, da sauri Jawahir ta dube shi jin yadda ya furta sunan nata. *SHU'UMAR MASARAUTA* *40* *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Tamkar yadda inuwar mutum ke bibiyar kowacce hallita haka Boka Shaddas yake bibiyar Jawahir domin ya samu nasarar kai ta kogon dutsen Shugaba Zurufu, sai dai a duk lokacin da ya kusance ta wata irin faɗuwar gaba da razani ne suke maye shi. Ya sha ruwan mamaki matuƙa da 'yar ƙanƙanuwar yarinyar take yunƙurin gagare masa, don har lokacin da ta tunkaro sashen Sarki Abdul'aziz yana biye da ita amma ya gagara sarrafa komai a kanta, dalilin da ya sa yake rikiɗa zuwa mabambamtan hallitu don ya yi nasara a kan. Laɓe wa ya yi a jikin wata bishiyar darbejiya, yana jiran fitowarta don ya ci alwashin a wanan karon ba zai bar ta ba. "Ina shakkun nasarar da kake hanga a kanta! Gani nake mahaifiyarta ba ta zuba ido a kanka har ka cutar da ita ba." Boka Shadda ya ji an furta a bayansa yana waigowa ya yi tozali da Dattijo Maharaz. Sai da ya turɓune fuska sannan ya furta. "Me ya sa kace haka? Ko ka manta da nawa hatsabibancin ne?" "Ka manta wace ce mahaifiyarta da zamanin da ta yi? Tun wuri ina mai baka shawara ka haƙura, idan ba haka ba kuwa allura za ta tono garma." Dattijo Maharaz ya furta har zai wuce da sauri Boka Shaddas ya sha gabansa. "Soyayyar ɗana ce ta sa zan yi yunƙurin aikata haka, ko don ba ɗanka aka taɓa ba?" Murmushi Dattijo Maharaz ya yi ya ce. "Kuskuren da Mahaifiyarta ta aikata a baya kenan, Shaddas ka sani shi musulunci daban yake. Kuma a duniya wata hallita ba ta isa ba ta cutar da wata ba har sai Ubangiji ya ƙaddaro haka a cikin kundin ƙaddarorin kowanne bawa. Na ba ka shawara ne a silar zumuncin da ya taɓa giftawa tsakanina da wani kakanka kafin ya rasu wani abin farincikin a hannuna ya karɓi kalmar shahada. Da za ka tuba ka koma ga Allah da ya fiye maka wannan mummunar turbar da kake kai wacce ba za ta dire ka ko ina ba sai a yankin azaba da uƙuba." Daga haka Dattijo Maharaz ya wuce ya ba wa Boka Shaddas hanya. Wani tunani ne ya faɗo wa Boka Shaddas har sai da ya saki murmushi a fili sannan ya wuce kogon tsafinsa. Fargi ta jima a wurin bishiyar kukar da suke bautawa tana kai mata kokenta ba ita ta bar wurin ba sai kusan doshin Asuba, kai tsaye Masarautar Sarki Sulaiman ta wuce a saitin windonsa ta tsaya cikin surar tantabara ta fara kaɗa fuka-fukanta tana kuka. Jin haka ya sa da Sauri Sarki Sulaiman ya ta shi ya fice duk da har lokaci ba a kira assalatu ba. Da hannu ya ɗauki tantabarar ya zagaya ɗakin hutawarsa sai da ya rufe ƙofar sannan Fargi ta yi girgiza ta dawo cikin ainihin surarta. "Yanayinki kaɗai shi ya tabbatar mini akwai wani al'amari da yake faruwa." Shiru ta yi ta sunkuyar da kanta ƙasa tana jin wani abu na yi mata yawo a rai, a hankali ya matsa gabanta ya riko ta tamkar wacce take jira sai kawai ta fashe da matsanancin kuka. "Gabansa ne ya ci gaba da faɗuwa, bai hana ta ba sai da ta yi mai isarta yana shirin yin magana ta furta. "Ina ƙaunarka Sadaukina! Kuma ina ƙaunar abin cikina, ina yi mata so mai tsanani soyayyar da kowacce uwa take yi wa 'yarta. Don Allah ko bayan rayuwata ka kula mini da ita." A razane Sarki Sulaiman ya miƙe tsaye ya furta. "Me kike faɗa haka Fargi? Me yake faruwa da ke ne?" Murmushin ƙarfin hali ta ƙirƙiro ta share hawayenta sannan ta ce. "Sai wani abu ya faru Sarkina? Babu wani abu da ya faru da ni kawai ina tsoron kada nan gaba danginka su ƙi karɓarta a matsayin 'yar cikinka!" Guntun tsaki ya saki haɗe da ajiyar zuciya, sai da ya koma ya zauna sannan ya ce. "Na yi tsammanin wata maganar za ki faɗa, kada ki damu Fargi. 'Ya ta za ta taso cikin kulawar mahaifi da zuri'arsa. Bayan wannan akwai wani abu?" Kai ta girgiza masa tana bin sa da kallon tausayi. Ta miƙa masa wasu wuri guda uku, ta sake miƙa masa wata ƙanƙanuwar jakar fata. Sannan ta ɗauko wata ƙatuwar azurfa ta haɗa masa da su, da mamaki yake bin ta kallo ganin yana buƙatar ƙarin bayani ta ce. "Ka yi mini alƙawarin za ka aiwatar da abin zan gaya maka." "Na amince, ina jinki." "Ka shafa jinin jikinka a jikin kowanne abu da na baka, sai ka ɗauke shi zuwa bakin kowacce irin bishiyar kuka ka haƙa rami mai ɗan zurfi ka binne. Wanne suna kake muradin a sanyawa abin da zan haifa?" Jim Sarki Sulaiman ya yi sannan ya furta. Gudun kada su fahimci yanayin da yake ciki ya sa Sarki Sulaiman ya saki murmushi ya furta, "Suna mai matuƙar muhimmanci da ma'ana!" Daɗi ya mamaye Jawahir, ta dubi Kamalu da ke sunkuye da kai ta yi masa gwalo haɗe da faɗin. "Ka ji dai mai ranka shi daɗe ya ce suna ma ba irin naka ba." A wannan karon gabansa har ya fi na baya faɗuwa, bakinta ya bi da kallo yadda take sarrafa shi tamkar yadda Fargi take magana. "Kada sake shiga harkarta Kamalu, ka bi ka hana yarinya sakat idan ba haka ba ranka zai ɓaci." Sarki Abdul'aziz ya gargaɗi Kamalu. "Allah ya taimake ka wanki fa kawai ta yi mini." Da sauru Sarki Abdul'aziz ya dubi Kamalu, ya sake haɗe fuska ya ce. "Mun soke wannan aikin daga yau, idan kuna buƙatar a yi muku wata hidimar ku nemi Bayi a saka su." Cike da ladabi Kamalu ya amsa yana jin haushin Jawahir a ransa. Sarki Abdul'aziz zai sake yin magana suka ji sallamar Galadima shi da Muhsin. Kallo ɗaya Sarki Abdul'aziz ya yi masa ya fahimci akwai abin da ya kawo shi, ganin Sarki Sulaiman ya sa Galadima ya ɗan haɗe fuska. Sai da suka gaisa sannan Galadima ya furta. "Ranka shi daɗe muhimmiyar magana gare ni, kasan dai ko da ka kasance kai ne Sarki mu kuma yayyanka ne dole mu..." "Galadima a tsumaye mu muna ganawa da Mai martaba, idan muka fito za mu tattauna." Sarki Abdul'aziz ya katse shi cikin hanzari, don ya san maganar da Galadima zai kawo masa ba mai daɗi ba ce. "Ka ga Abdul'aziz wannan maganar ta yi daidai da lokacin yin ta, domin faɗuwa ce ta zo daidai da zama. Ga ka ga Sarki Sulaimanu ga yaron nan Muhsin yanzu me ya rage? Ko ka fi son sai ya tafi idan ya ɗauko magnar ka ce kun riga da kun gama yanke hukunci? To ba za ta saɓu ba, yaron nan ya je ya same ni da magana don haka ni ne gaba da kai dole zan iya yanke hukunci a kan abin da ya kamata." Galadima ya yi maganar cikin haƙiƙancewa don wannan botsarewar da Muhsin ya yi ba ƙaramin daɗi abin ya masa ba, ko ba komai ya samu kafar da zai cusa 'yar wurinsa ga Muhsin tun da ya nuna ba ya son haɗin da mahaifinsa zai yi masa. Kunyar duniya ta lulluɓe Sarki Abdul'aziz, ya sauke gwaron numfashi ya nuna can gefe sannan ya furta. "Bismillah muna sauraronku." Cikin gadara Galadima ya zauna, Yarima Muhsin ya ja ƙafafuwa ya zauna yana sunkuyar da kai ƙasa. "Sarki Sulaimanu ka san dai Abdul'aziz ƙanina ne wurin na biyu, amma da yake bai ɗauke ni da ƙima ba sai da kuka ci kuka cinye a maganar auren yaran nan ba tare da an sanar da mu komai ba..." "Galadima a tafi kai tsaye." Sarki Abdul'aziz ya katse shi rai a ɓace. Sai da Galadima ya yi ƙwafa sannan ya furta, "Yarima ya same ni da maganar ba ya son auren haɗin da ake shirin yi masa, don haka na ga ya dace na zo na soke wannan maganar sai kuma aka yi sara a kan gaɓa tun da kai ma ga ka a zaune Sarki Sulaimanu." Dumm Sarki Abdul'aziz ya ji ƙirjinsa ya buba, tamkar an buga masa guduma. Kunyar Sarki Sulaimanu ta lulluɓe shi. "Mun riga da mun zartar da hukunci Galadima, sanin kanka ne ba ma yin magana biyu." Muhsin ya ɗago a zabure ya dubi Mahaifinsa. "To a yanzu ba sai gobe ba za ka fara! Magana biyu ba, yau ɗin nan za ka fara tun da yaro ya ce ba ya so, kai ma kuma na ga ba auren dole nan aka yi maka..." "Galadima a bamu guri!" Sarki Abdul'aziz ya sake katse shi a fusace. "Ka yi mini afuwa Mai martaba idan kalamaina za su sosa maka rai, ni ne dai mahaifin yarinyar nan kuma ni na tako har nan na nemi arziƙin haɗa wannan alaƙar. Kuma a yanzu ina mai neman alfarmar Sarki Abdul'aziz da a bar yaron nan ya auri wacce yake so, ita kuma 'yar wurina ina nema mata auren Kamalu idan hakan ba zai zama da matsala ba." Sarki Sulaiman ya furta yana zuba maganansa a wurin Sarki Abdul'aziz. A razane Kamalu ya dago jin furucin Sarki Sulaimanu. "Faƙat! Shi kenan, an gama magana yaro ya auri son ransa dama ai matar mutum kabarinsa." Galadima ya furta. A fusace Sarki Abdul'aziz ya ce. "Ba za mu ruguje maganar da muka gina a baya ba..." "Idan har ina da alfarma a wurinka ka yi yadda muka buƙata Sarki Abdul'aziz." Sarki Sulaiman ya katse shi. Rai a ɓace Sarki Abdul'aziz ya ce, "Ka sanar da iyayen yarinyar da kake so su turo magabatansu wurin Galadima ya aiwatar da duk abin da ya dace." Daga Kalamu har Jawahir kusan mutuwar zaune suka yi kowa da abin da yake wassafawa a zuciyarsa, a ɓangare ɗaya tsoron Sarki Abdul'aziz ya mamaye su don tun ranar da asirin Fulani Umaima ya tonu ba su ƙara ganin ɓacin ransa haka ba. "Ni babu wacce nake so sai Jawahir." Rass! Gaban Jawahir ya faɗi, jikinta ya ɗauki karkarwa tamkar mazari. Sarki Abdul'aziz ya ƙura masa idanu sannan ya saki murmushi irin nasu na manya. "Kai Muhsin me kake nufi? Kana nufin duk wannan haƙilon da na yi ya tashi a banza? Na ɗauka za ka ce a haɗa ku da 'yar wurina Ummi?" A wannan karon ba Sarki Abdul'aziz ba har Sarki Sulaiman sai da ya saki murmushi, don gabaɗaya sun fahimci inda Galadima ya dosa. "Ni gaskiya Ummi ba ma tsarar aurena ba ce, Jawahir nake so." Muhsin ya furta har lokacin idanunsa a kan Jawahir da ta sunkuyar da kanta ƙasa. "Jawahir 'yarmu ce sai mun ji ta bakinta tukunna saboda ita ma ba za mu yi mata auren dole ba." Dam! Ƙirjin Muhsin ya buga, nan take hankalinsa ya tashi don ya san ko kaɗan Jawahir ba ta ƙaunarsa. "Kamalu ka ji hukuncin da muka yanke a kanka?" "Eh na ji ranka shi daɗe, Allah ya sa haka ne ya fi zama alheri." Kamalu ya yi maganar murya a sanyaye don wannan maganar ba ƙaramin ɗaga hankalinsa ta yi ba, don dai ba ya san ya watsa wa mahaifinsa ƙasa a ido ne kawai ya amince. "Za ku iya ba mu wuri muna buƙatar tattaunawa da Sarki Sulaimanu, a sanar da Baffajo muna son ganinsa bayan sallar magriba." Tun Sarki Abdul'aziz bai gama magana ba Muhsin ya fice fuuu, da ma shi Galadima tun da ya ji sun raba hanya da Muhsin ya karkaɗe rigarsa ya yi gaba yana masifa da tsine-tsine. Kamalu da Jawahir kamar waɗanda aka zarewa laka a jika suka russuna suka yi godiya suka fice, har Jawahir ta fita Sarki Sulaiman yana bin ta da kallo. Kamalu sauri ya fara yi tamkar zai ta shi sama ya wuce sashensa, yana shiga Bayi suka fara yi masa barka da shigowa ko kallonsu bai yi ba don yadda kansa yake sara masa tamkar zai tsage masa gida biyu. Damuwa ɗauke a fuskar Inna wuro ta shiga ɗakin Kamalu don ta ga lokacin da ya shiga fuska babu walwala, sallama ta yi masa da ƙyar ya iya amsawa yana ganinta ya tashi zaune. A gefensa ta zauna ta zuba masa idanu, a hankali ya fara motsa baki. "Inna Mai martaba ne!" Rass gabanta ya faɗi amma sai ta dake ta furta, "Me yake faruwa?" "Wai aure zai yi mini, amma Inna kada ki gaya wa Baffajo don na ji ya ce zai same shi ya yi masa maganar na san kuma a kanta za su tattauna." Murmushi ne ya bayyana a fuskar Inna wuro. "Kamalu don za a yi maka aure ne ka shiga damuwa? Ba ka san shi ne mutumcinka ba, kai don Allah bari na wuce wallahi har ka tsinkar mini da zuciya na ɗauka wani abu ne. Kai Allah na gode maka Allah ka sa zan ga auren Kamaluna" Inna wuro ta yi maganar ta na ficewa daga ɗakin cikin tsananin farinciki. Jawahir kai tsaye sashensu ta nufa zuciya babu daɗi, can cikin ɗaki ta shige a lokacin Mai gado na ɗakin Abubakar tana koya masa yadda ake tafiya don lokacin ya fara tsaiwa har yana iya miƙewa tsaye ya tsaya ƙyam da ƙafafuwansa, sai dai har lokacin kallo ɗaya za ka yi masa ka fahimci ba shi da cikakkiyar lafiya. Jigum ta yi tana nazari don ta san ko karen hauka ne ya cije ta ba za ta taɓa furta wa Sarki Abdul'aziz ba ta ƙaunar ɗansa ba. Kamar wacce aka tsikara da sauri ta miƙe ta ɗauko littafin labarin Hidaya, kamar marar gaskiya haka ta raɓe daga bayan ƙofa sannan ta buɗo shi ta ci gaba da karantawa. Da mamaki Sarki Hafiz ya dube ni ya dubi wurin da nake kallo ya girgiza mini kai. "Idan har muka ce miki mun ga wata hallita a wurin can to mun yi ƙarya. Babu wanda muke gani, idan kuma ke ƙwayar idonki na gane miki sai dai idan fatalwarsa ce." "Mece ce Fatalwa?" Na wurgawa Sarki Hafiz tambaya. "Fatalwa wata hallita ce da take wakiltar mamaci take tsoratar da mutane ta cikin siffar mamaci, wata kuma ta ci gaba da gudanar da aikin alheri. Ke wata ma har fansa take dawowa ta ɗauka. A taƙaice dai ruhin mutum bayan ya mutu ne yake tashi ya dinga bin waɗanda suka san shi a baya yana tsorata su wasu kuma ba sa tsoratarwa." Jinjina kaina na yi don maganar na ji ta yi mini nauyi aka. "Kuma wannan harsashen gaske ne wanda ya mutu yana fatalwa? Ko kuma dai kawai camfi ne?" Na sake wurga masa tambaya. "Ni dai da idanuna ban taɓa ganin fatalwa ba, na dai ji ana faɗin haka tun iyaye da kakanni. Amma gudun shakku, za ki iya tambayarsa domin muma mu ji daga gare shi." Tun Sarki Hafiz bai ƙarasa kalamansa magana ba na hangi mahaifina ya tunkaro ni, sai da ya ƙaraso gabana ya furta. "Tabbas a kalaman Sarki Hafiz babu ƙarya gabaɗaya ba sa ganina amma yanzu zan buɗe musu idanu." Rufe bakinsa na ga su Fulani Hawwa kulu sun ɗan ja da baya a tsorace. "Kada ku tsorota haƙiƙa ni ba mai cutarwa ba ne " Ya furta musu sannan ya sake harɗe hannuwansa a ƙirji. "Ban so na bayyana ba amma ya zame mini wajibi tun da a yanzu kin haye karagarki, ni ba mahaifinki ba ne. Ni aminin mahaifinki ne wanda ya yi rainonki tare da mahaifinki. Na zaɓi na ci gaba da zuwar miki a siffar mahaifinki ne domin na ɗorar da alƙawarin aminina. Kuma lokaci ya yi da zan mallaka miki takobinki, takobin da burin mutane da dama suke mafarkin mallakarsa. Akwai wata yarinya da za ta zo cikin zamani mai tsawo, matuƙar ta samu sukunin mallakar wannan takobin sai ta gagarewa duk wani hatsabibi da matsafi a nan duniya. Ita kanta yarinyar mahaɗi ce, mahaɗin duk wani silar gawurta da shahara a faɗin duniya. Waɗannan mahaɗan ba za su taɓa tasiri ba har sa sun mallaki wani kundin littafi da zan mallaka miki, kundin da nake fatan za ki zayyane duk labarin rayuwarki tun daga farko har ƙarshe." Murmushi na sakar masa cikin girmamawa na furta. "Tabbas ka kasance amini na gari, ire-irenku sun yi ƙaranci a duniya domin amana ta yi rauni. Amma wani hanzari ba gudu ba, a kwanaki na ji wani matashi yana ce mini ya samu 'yanci a lokacin da nake rufe, shin me hakan yake nufi?" "Yana nufin ya kuɓuta daga ɗaurin da Sarauniya wato ssrauniyar da ta kasance daga zuri'ar Sarki Hafiz, ita ta sa aka yi masa ɗaurin, Boka Tanko ne ya yi mata aikin a waɗansu shekaru da suka wuce." Aminin mahaifina da ke ɗauke da siffar mahaifina ya furta mini. Mun jima muna tattauna waɗansu muhimman maganganu kafin daga bisa, ya ɗauko wannan littafin da na juye tarihin rayuwata a ciki ya damƙa mini. Ya haɗa mini da takobin da ya alƙawarta mini. Daga ƙarshe kuma ya ɗauke ni muka yi tafiya mai nisa sannan ya kai ni bakin wani shuri ya ce na zura takobin da hannuna tare da yankar gefen hannuna na tsartar da jinina a kai, bayan na aiwatar na ga yana kallona. "Ina fatan yadda kika zura takobin nam, wacce za ta tono shi ta kasance tana daga cikin tsatsonki ce." Sam ban fahimci abin da yake nufi ba, daga haka muka baro wurin muka koma cikin masarautarmu. Tun daga wannan ranar sarautar masarautarmu ta dawo hannuna, na ci gaba da kulawa da ɓangaren Bayi hatta wahalar da suke sha a baya sun samu afuwarta. Ban bar Sarki Hafiz haka ba har sai da na ba shi sarautar Wazirin masarauta, tun Fulani Hawwa kulu na nuna ƙyashu da hassadarta a kaina har ta zubar da makamanta. Tafiya ta miƙa sosai har soyayya mai ƙarfi ta shiga tsakanina da Yarima ɗan Sarki Hafiz, kuma hakan ba ƙaramin daɗi ya yi masa ba. Ba a ɗauki lokaci mai tsayi ba aka ɗaura aurenmu muka ci gaba da rayuwa cikin farinciki a farkon auranmu. Jawahir ta ɗago kanta tana sauke ajiyar zuciya a tunaninta ta kai ƙarshen labarin, daga can bangon ƙarshe ta ga wani guntun rubutu daga samansa an rubuta ABIN LURA, cikin rubutun ajami. Jingina ta yi da bango sannan ta ci gaba da karantawa. ABIN LURA Ga duk wanda ya mallaki wannan littafin kuma ya karanta shi, tamkar ya mallaki rabin abin da zai mallaka a nan gaba ne. Babban burina bai wuce jinina kuma ɗan asalina zuri'ata ya mallaki wannan kundin ba. Ina yi wa duk wanda ya kasance mai nasara da fatan alheri. A wannan lokacin da nake yunƙurin kammala rubuta tsakure daga cikin labarina, Hidaya ta san wace ce ita a gaɓar da ba ta taɓa tsammani ba, sanin tarihina ya sa na fahimci ba iya jinsina na bil'adam ne kaɗai suke da karamci ba riƙon amana ba. Haka kuma ba iya jinsina ne kaɗai suke da hatsabibanci gami da shantakewa da dauniya ba. Wannan kundin ya yi kaɗan na zayyane tarihina tun daga farko har ƙarshe, ga tsakuren kaɗan daga abin da ya faru da ni ba zan tona ƙalubalen da ya afkawa rayuwata ba, bayan tara iyalin da muka yi da mijina kuma uban 'ya'yana wanda shi ne mutum na farko da ya fara jefa ni a kogin bala'i, baƙinciki da nadamar kasancewar alaƙar da ta gindaya a tsakaninmu. "Ƙarshe!" Jawahir ta furta bayan ta kai ƙarshen labarin Hidaya, sai dai ba haka ta so ba don ta so jin ƙarshen abin da ya wakana tsakaninta da Ɗan sarki Hafiz wanda ya kasance mijinta. Boka Shaddas ya ɗaga labulen ɗakinsu Jawahir, ya ƙarasa har bayan ƙofar da take tsaye, a tsorace Jawahir ta dube shi yanayin kamanninsa suka sake tsorata. Ihu ta ƙwallah da ƙarfi a daidai lokacin Malam Umaru tare da Bawa Lawandi suka sako kai za su wuce jin ihunta ya sa suka shiga ɗakin da gudu, wata jar hoda ya hura mata take ta yii yunƙurin zubewa ya riƙota da hannunsa ɗaya. Umaru ne ya kai masa duka ta bayansa a tsammaninsa ko ɓata rayuwar Jawahir ɗin zai yi. A fusace Boka Shaddas ya buga masa sandar tsafinsa aka, Bawa Lawandi na shirin futa domin ya yi kururwa neman taimaki shi ma ya buge masa a ka take shi ma ya zube a ƙasa. Ya saɓi Jawahir ya ɗora a kafaɗa yana matsa wata layar da ke ƙungunsa suka ɓace ɓat. A kan wani farin dutse ya kwantar da ita da ke kogon tsafin Shugaba, Shugaba Zurufu ya fara zagaye ta sannan ya fashe da wata mahaukaciyar dariya ƙeta. *SHU'UMAR MASARAUTA* *41* *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Sarki Abdul'aziz shi da Sarki Sulaimanu sun jima suna tattaunawa game da abin da ya shafi sabuwar maganar auren Kamalu da 'yar wurinsa, sannan ya yi masa sallama ya tafi. Sarki Abdul'aziz ba ƙaramin sha tara ta arziƙi ya sa aka haɗa masa ba, fadawansa suka rufa masa baya sannan suka nufi masarautarsu. Sarki Sulaiman ya so kafin ya tafi ya sake tozali da yarinyar da ta tsaye masa a zuciyarsa amma babu yadda ya iya haka ya koma har lokacin ƙwayar idonsa na sake hakaito masa kamanninta. Ko da ya koma kai tsaye wurin sassaƙaƙƙiyar tantabararsa ya nufa, ruwan mamaki ya mamaye shi sakamakon yadda ya ga hawaye bibbiyu na zuba daga idanunta. Hannu ya saka a sanyaye ya ji wani ruwan hawaye mai ɗumi na ci gaba da bin hannunsa, daga gefen fuka-fukin tantabarar ya ga wani sabon rubutu tamkar wanda aka yi da ruwan tawada. "Hallitar da ka yi tozali da ita 'yarka ce!" Ya sake maimata rubutun babu adadi gabansa na faɗuwa. "Ban san me yake faruwa ba, ban san me wannan rubutun yake nufi ba." Daɓar ya zauna a ƙasa tamkar ƙaramin yaro, idanunsa suka fara zubar da ƙwalla, lokaci ɗaya tunanin Fargi da alaƙarsu ta baya ta suka shiga dawo masa. "Na san akwai lokacin da ƙwayar idonka za ta so yin tozali da ni, sai dai zanen ƙaddara ya shata mummunan layin da ya katange gangar jiki da ruhinmu. Abu ɗaya nake so da kai Sadaukina, kada ka manta da ni. Kada ka manta da tsantaar soyayyarka da ke narke cikin sassan jiki da ruhina." Kalaman Fargi na ba ya suka dawo masa raɗau a cikin kunnuwansa tamkar a lokacin take furta masa su. "Na gagara daina kukan rashinki Fargi! Na sha gaya miki kada ki nisance ni amma kika yi ɓatan dabon da har yau nake lalube a ciki duhu. Ya Allah idan Fargi na raye Allah ka bayyana mini ita da abin da yake cikinta." Sarki Sulaiman ya ƙarasa maganar yana zubar da ƙwallah. Jingina kansa ya yi a jikin ginanniyar tantabarar ya faɗa duniyar tunani daga haka baccin gajiya ya yi awon gaba da shi. Ihunta ya fara ji a cikin kogon dutsen da sauri ya faɗa ciki hankali a tashe, daga can nesa ya hangi Fargi na ɗaga masa hannu tana kiransa, ya yunƙura da niyyar ya nufi wurinta ya hangi wata matashiyar budurwa da ta juya bayanta, Shugaba Zurufu na yarfa mata wani ruwan tsafinsa. A hankali ya ga naman jikinta ya fara zagwayenwa, Fargi ta nuna masa wurin cikin ƙaraji tana faɗin. "Ka taimaka wa 'Yarmu Jawahir zai hallaka mana ita..." Firgigit Sarki Sulaiman ya buɗe idonsa daga mummunan mafarkin da yake yi, gabansa ya ci gaba da faɗuwa jikinsa ya ɗauki karkarwa kamar mazari. Miƙewa ya yi tsaye ya nufi hanyar fita ya ji ginin tantabarar nan gabaɗaya ya ruguje, cak ya tsaye cikin firgici yana kallon yadda ginin ya fara wani katantanwa yana rushewa. "Tabbas akwai abin da yake faruwa!" Sarki Sulaiman ya furta a fili sannan ya fice daga cikin ɗakin. Sai da aka kwana biyu Mai martaba Mahaifin Fulani babba ya sa aka kira masa Yaya Halima har cikin turakarsa, tun da ta doso ɗakin ya zuba mata ido yana mamakin wai yau Halimansa ce ta samu lafiya garau kamar ba ita ba. "Barka da hutawa ranka shi daɗe!" Kalaman Yaya Halima suka ratsa majiyar sautinsa. "Barka dai Halimatuna ya sauƙin jiki?" Murmushi ta yi sannan ta ce. "Ni fa ranka shi daɗe babu abin da yake damuna, na ma yi mamaki da aka ce wai na yi cutar hauka har da kurumta." Mai martaba ya miƙa mata hannunsa sannan ya ce. "Me ye wannan?" Baki sake take kallonsa haɗe da dariya ta ce. "Hannunka ne ranka shi daɗe. "To a baya ba kya iya jin abin da nake faɗa ballantana ki ga abin da na nuna miki, Allah na gode maka Ubangiji ya ƙare mu da lafiya. Lokaci ɗaya Halimatu muka wayi gari kin kurumce, kin kuma makance. Tafiya na sake miƙawa sai muka lura da yadda kika fara sauyawa, kwatsam mu ka ga kin fara hauka tuburan. Amma da yake Allah ne mai yadda ya so a sanda ya so, sai ga shi yanzu Allah ya yaye miki." Sai a wannan karon ta gamsu da abin da ake faɗa, da ta ji daga bakin Takawa don ta san shi kaɗai ne ba ya ɓoye mata komai. "Ranka shi daɗe na ji an ce rannan kun je Masarautar Huddam, ka tura wa Fatima takardar samun lafiyar da na yi kuwa?" Take idanunsa suka cicciko da ƙwallah. "Halimatu." Ta ji ya ambaci sunanta da wani irin yanayi. "Fatima tana wurin da ba kowanne irin saƙo ko aike ba ne zai isa gare ta, kin san wanne irin sako za mu iya aika mata a yanzu." Da sauri ta girgiza wa Mai martaba kai. "Ku yi mata addu'a ku yawaita yi mata addu'ar Allah ya yafe mata kura-kurenta. Saboda Allah ya yi wa ƙanwarki rasuwa!" Jin kalaman Mai martaba ya sa ta miƙe a zabure jiki na karkarwa, ya nuna mata wuri sanna ya furta. "Zauna dama muna son magana da ke Halimatu." Kafin ta zauna tuni hawaye ya wanke mata idanu. "Ke musulma ce Halima don haka duk ƙaddarar da ta same ki ki rungume ta hannuwanki biyu, Allah shi ya ba mu Fatima a lokacin da ba mu sani ba kuma Ya karɓe ta a daidai lokacin da yake buƙata." Mai martaba ya furta cikin sigar lallashi. Sai da ta share hawayenta sannan ta furta. "Haka ne ranka shi daɗe. Allah ya gafarta mata, yanzu ina su Khadija wanne halin suke ciki?" Murmushi Mai martaba ya saki ya ce. "Halimatu shekaru fa sun tura, turawar da ta haifar da faruwar abubuwa mabambamta. A yanzu daga Khadija har Sakina kowacce tana ɗakinta da 'ya'yanta, wai ba ki ga Shatu ma ('Yarta) har da 'ya'ya huɗu ba? Lokacin da kika fara rashin lafiyar nan fa ko shekara biyar ba ta rufa a duniya ba. Ga shi matar Sabi'u ma ɗanta ɗaya, ai abubuwa sun tura sosai." Yaya Halima ta jinjina kai cikin mamakin wai ita ce har da jikoki biyar tsakanin babban ɗanta da ƙaramar 'yarta Shatu. "Ranka shi daɗe amma me ya sa har yau Ibrahim bai zo ya ganni ba." A wanna karon ma yanayin mai martaba ya sauya sosai don sai da ya kwantar mata da hankali ya fara yi mata bayani. "Shekararki biyu da fara ciwon da ya same ki Ibrahim bai taɓa gazawa a kanki ba, babu inda bai zaga ba domin ya ga kin samu lafiya amma ba a dace ba. Ni kaina na aika ƙasashe da dama a kullin jiya i'yau, don haka na sa aka kira mini shi na yi masa nasiha a kan zaman da yake yi babu aure, sannan muka sa ya rubuta miki takardar saki. Da ƙyar da suɗin goshi ya rubuta miki saki ɗaya, sai dai a yadda labari ya zo mana har kwanciya jinya ya yi. Bayan ya sawwaƙe miki da wasu wattani ya yi aure ashe ajalinsa a kusa yake don matar da ya aura ma da tsohon ciki ya mutu ya bar ta. Shi ma addu'a za ki masa, domin Ibrahim ya matuƙar nuna miki kulawa." Sai da Yaya Halima ta sha kuka mai isarta sannan Mai martaba ya yi mata bayanin duk abin da ya faruwa a Masarautar Huddam, da kuma hukuncin da ya yanke game da ba wa Sarki Abdul'aziz auren wata 'yar tashi, daga ƙarshe ya tabbatar mata da ita ce wacce ya zaɓar wa Sarki Abdul'aziz tun da ta samu lafiya. Jin kalaman Mahaifinta ba ƙaramin ɗimautata ya yi ba, ganin halin da ta shiga ya sa ya sallame ta a kan ta je ta yi nazari idan an kwana biyu zai sake ji daga gare ta. Daga can gefe Boka Shaddas ya tsaya yana kallon Shugaba Zurufu, yana son tambayarsa matsayin Basiru wani irin tsoro ya mamaye shi. Yana nan tsaye ya ga ya yayyfa wa Jawahir ruwa nan take ta fara motsi a hankali ta fara buɗe idonta, zumbur ta miƙe tsaye tana ƙarewa wurin kallo sannu a hankali komai ya shiga dawo mata. Tsoro ya sake mamaye ta a lokacin da ta yi tozali da Shugaba Zurufu da yake a duke saboda tsufa. "Kamar kumbo kamar kayanta, wannan kama ta yi kama tamkar an tsaga kara ke da mahaifiyarki." Ja da baya Jawahir ta fara yi Shugaba Zurufa yana sake tunkararta. "Na riga da na cika aikinka ina ɗana Basiru yake?" Boka Shaddas ya furta murya babu alamun wasa. Waigowa Shugaba Zurufu ya yi a hankali jikinsa na karkarwa, fuska ɗauke da murmushi ya zuba wa Boka Shaddas idanu har sai da gabansa ya faɗi. Don ya tabbata banza ba ta kai zomo kasuwa wannan murmushin da Shugaba yake yi ba zai tashi a banza ba. "Me kake ci na baka na zuwa Shaddas ai duk gaggawar Ungozoma ta bari a haife." Boka Shaddas ya yi ƙwafa bai tanka masa, Shugaba Zurufu ya fara matsawa gaban Jawahir sannan ya furta. "Ɗaga mini rigarki." Rass gaban Jawahir ya faɗi. "Don Allah waye kai, ku duba girman Allah kada ku cutar da ni." Cak Shugaba Zurufu ya tsaya yana jinjina kai sannan ya furta. "Tabbas ko iya haka Fargi ta bar mu ta kusa yin galaba a kanmu, ta ci alwashin yaɗa zuri'armu abin da ba ta sani ba har addininmu ta so dakushewa." Kafin ya rufe bakinsa ya ga wata tsuntsuwa ta ratso ta jikin bango cikin shammata ta warci littafin labarin Hidaya da tun kwantar da Jawahir a kan farin dutsen ya faɗi a ƙasa. Daga Boka Shaddas har Shugaba Zurufu bin tsuntsuwar suka yi da kallo, da sauri Shugaba ya yunƙura da zummar ya ƙwato shi amma sai ya gagara. Daga can bakin ƙofa wani Dattojo ne tafe da ɗanyan naman bunsuru ɗauke a saman kafaɗarsa, sai da ya ƙarasa gaban Shugaba ya zube yana haki sannan ya furta. "An aiwatar da komai Shugaba shin akwai abin da kake buƙata?" Ganyen da ke ɗaure a jikin dattijon Shugaba ya sunkuya ya goge gumin goshinsa cike da wulaƙanci sannan ya furta. "Babu buƙatar wani abu amma kalli can?" Ya yi maganar yana nuna wurin da Jawahir take tsaye. A gajiye Dattijon ya miƙe yana bin wurin da kallo haɗe da ƙura wa Jawahir ido, lokaci ɗaya jikinsa ya ɗauki karkarwa bakinsa na rawa ya nuna Jawahir yana faɗin. "Faff... Fargi! Ke idanuwana suke gani ko gizo suke yi mini." Cikin yanayin mamaki Jawahir ta bi shi da kallo sam ba ta fahimci abin da suke nufi ba. "Shugaba Fargi ta dawo gare mu." Mahaifin Fargi ya yi maganar cikin tsananin farinciki, hawaye bibbiyu ya fara zuba daga idanunsa. "Na daɗe da fidda rai da sake yin tozali da ke ashe akwai sauran ganawarmu a gaba..." "Wannan ba Fargi ba ce." Kalaman Shugaba Zurufu suka katse Mahaifin Fargi. Shiru ya yi yana ci gaba da kallon Jawahir don da a ce ba laifi ba ne da ya musa kalaman da ya ji Shugaba ya yi. "Wannan jinin Fargi da Sarki Sulaimanu ce, kuma ni na aika aka ɗauko mini ita domin na san mahaifiyarta ba za ta bar ni haka ba. Don haka za ta ci gaba da zama a ƙarƙashin ikona, na sha baƙar wahala kafin na bankaɗo ainihin wurin da ta ɓoye ta. Tabbas Fargi hatsabibiya ce ta ƙarshe, ni kuma na nuna mata duk girman kuka bagaruwa ce babba." Kuka Mahaifin Fargi ya fashe da shi yana jin tausayin rayuwar yarinyar da ba ta san rikiscin da ya wakana a shekaru goma sha shida da suka wuce ba. Ya san ba shi da ta cewa don haka ya ja bakinsa ya yi shiru, saboda tun ranar da Fargi ta bar cikin garin suka koma masa tamkar Bayi shi da mahaifiyarta da 'yan uwanta maza. "Na gaji da gafara sa ban ga ƙaho ba Shugaba ka ba ni ɗana na wuce da shi." Boka Shaddas ya furta a ƙagauce. Shugaba bai tanka masa ba wuce can bangon ɗakin da ya taɓa ɓoye Basiru sannan ya zura hannu ya janyo shi, cikin wata irin tafiyar taƙama da ƙasaita Basiru yake taku ɗaiɗai yana bin mutanen kogon dutsen da kallo har suka ƙarasa wurin mahaifinsa. Hannu Boka Shaddas ya kai zai ruƙo hannun Basiru da sauri ya Basiru ya ɗaga masa hannu. "Dakata! Ni ba ƙaramin yaro ba ne." Ya furta da wata irin ƙatuwar murya. A ɗan tsorace Boka Shaddas ya dube shi sannan ya mayar da kallonsa kan Shugaba. "Na ga sauye-sauye game da Basiru, me ya faru Shugaba Zurufu?" "Guda ka ba ni kuma ni ma guda na damƙa maka ka ga babu kare bin damo!" Shubaba ya furta a taƙaice. "Idan za ka wuce ka zo mu tafi ka da ka ɓata mini lokaci idan ba haka ba zan koma wurin da na fito." Basiru ya furta yana wurga jajayen idanunsa masu kama da sabon borkono. Boka Shaddas ba shi da mafita a dole ya rufa wa Basiru baya har suka fice daga cikin kogon dutsen, zuciyarsa na wasu-wasin sauyin da Basiru ya samu. Tun da Malam Umaru yanke jiki suka faɗi ko kaɗan Bawa Lawandi bai motsa ba, shi kansa Umaru cikin fitar hayyaci yake juya kansa daga kwance ba tare da ya san inda kansa yake ba. Kamar daga sama Mai gado na zagayowa ta hange su a ƙasa, cikin tashin hankali ta ƙwalla ihu ta faɗa kan Umaru tana jijjiga shi haɗe da kiran sunansa. Ganin kukan ba zai kai ta ba ya sa ta fita a guje tana kururuwa neman ɗauki, nan take Bayi suka cika sashenta aka shiga yayyafa musu ruwa sai dai ko kaɗan Lawandi bai motsa ba a nan suka tabbatar da rai ya yi halinsa. Malam Umaru aka ɗauka a ka kai ɗakin Mai gado a lokacin ya daina jujjuya kansa sai dai zuru ya yi yana bin mutane da kallo, duk yadda Mai gado ta so ya yi magana sai dai ya bi ta da kallo. Wannan mummunan yanayin da ya afkar musu ba ƙaramin ƙaɗa mutane ya yi ba, musamman mutuwar Bawa Lawandi da ya kasance mutum mai barkwanci ga kyakkyawar mu'amala da mutane. Duk wannan abin da yake faruwa babu wanda hankalinsa ya kai kan Jawahir, sai bayan da aka sallaci gawar Bawa Lawandi sannan Mai gado ta farga da rashin ganin Jawahir. Wani sabon tashin hankalin ne ya mamaye ta da aka bincika ciki da wajen Masarauta ba tare da anganta ba, hasali ma Ruƙayya ta bada tabbacin ta ga shigarta ɗaki, sai dai ta ce ba ta ga giftawarta ba. Nan take labarin ɓatan Jawahir ya zagaye cikin masarautar sai dai wannan al'amarin ba ƙaramin ɗaga hankulan mutane ya yi ba sakamakon babu baƙon fuska ɗaya da suka yi tozali da shi ballantana a zargi wani abu daga gare shi. Shi kansa Sarki Abdul'aziz ya kaɗu da jin labarin abin da ya faru, a ɓangare ɗaya ya fara tunanin ko saboda Muhsin ya nuna ita yake so shi ya sa ta yi haka, don a lokacin da Muhsin ya yi maganar ya lura da ɓacin rai a saman fuskarta. Tun a daren ranar Sarki Abdul'aziz ya sake baza sojojin masarautar da dogarawa don su ci gaba da binciken ciki da wajen masarauta ko za su gano wani labari. Lokacin da Kamalu ya ji labarin ɓatan Jawahir zuciyarsa tamkar za ta buga shi kaɗai ya dinga zagaye a ɗaki yana sake jin haushin Muhsin ya mamaye shi, don shi ma gani yake duk ta silarsa ce Jawahir ta ɓace. Da zuciya ta ɗebe shi kasa haƙuri ya yi ya wuce ɗakin Muhsin, ko neman izini bai yi ba ya faɗa ɗakin a lokacin ya samu Muhsin zaune ya zuba tagumi da hannuwansa biyu. "Tun wuri tun ba a je ko ina ba ka yi gaggawar janye soyayyarka a kan yarinyar nan domin ba ta ƙaunarka, domin kana ganin yadda kalamansa suka sa aka neme ta sama da ƙasa aka rasa." Kamalu ya furta da tsananin baƙinciki. "Fi ce mini daga ɗaki idan ba haka ba ranka ya yi mummunan ɓaci! Kai ba ka san bala'i ne a gare mu ba? Ka da ka ga ina ɗaga maka ƙafa ka nemi ka shigar mini hanci da ƙudundune, tun da ka bayyana gabaɗaya bala'i da musibu suke afkowa cikin masarautar nan wallahi kai ba ƙaramin annoba ba ne..." Cikin hanzari Kamalu ya katse shi. "Wallahi-wallahi tun kafin gari ya waye ka fito da ita idan ba haka ka fuskanci hukuncin da mahaifiyarka take fuskanta a yanzu." Daga haka Kamalu ya fice daga ɗakin a zuciye. Duk da dare ya fara yi sosai hakan bai hana ganin mutane sun yi carko-carko ba kowa cikin alhini da jimami, Kamalu har zai wuce sashensa Dattijo Maharaz ya faɗo masa da sauri ya nufi sashen Sarki Abdul'aziz, a lokacin da ya shiga ya samu mahaifinsa yana zaune. Sai da suka sake gaisawa sannan ya ɗan sunkuyar da kai ƙasa ya furta. "Dama Ranka shi daɗe wata magana ce gare ni." "Tafi kanka tsaye Kamalu!" "Allah ya taimake ka dama ce wa na yi ko za a ji daga bakin Dattijo Maharaz a kan ɓatan Jawahir, domin na ji daga bakin Dogarawan ƙofa babu wanda ya ga fitarta." Kamalu ya yi magnar yana duban yanayin Sarki Abdul'aziz. "Mun yi wannan tunanin amma sai muke ganin mai zai hana mu bari zuwa wayewar gari, kada mu shiga haƙƙinsa idan yana da wani uzurin." Ba haka Kamalu ya so ba amma sai bai nuna komai ba, ya yi wa mahaifinsa godiya sannan ya fita. Kai tsaye sashensa ya nufa yana shirin buɗe ƙofar shiga ɗakinsa ya ji sallamar Dattijo Maharaz, har a fili Kamalu sai da ya sauke ajiyar zuciya ya faɗaɗa fara'arsa. Sai da ya amsa masa sannan ya buɗe masa ɗakin suka shiga ciki, Kamalu ya buɗe baki zai yi masa bayani Dattijo Maharaz ya dakatar da ni. "Mahaifinka dattijon ƙwarai ne da sanin ya kamata, don haka ban baƙunce shi a wannan lokacin ba kamar yadda ya yi mini uzuri. Duk abin da yake faruwa na san komai Kamalu, kuma ka daina zargin ɗan uwanka Muhsin don ba shi da hannu a ɓatan Jawahir. Sai dai akwai babban hatsari a wannan tafiyar domin karawa ce tsakanin zuri'a biyu, kuma dole wannan tafiya za a yi ta ne da Sarki Sulaimanu." "Sarki Sulaimanu fa? Ko dai kana nufin Mahaifina Dattijo Maharaz?" Boka Shaddas shi da Basiru na isa kogon tsafinsa Basiru ya kafe ahi da idanu har sa gaban Boka Shaddas ya faɗi. "Ba ni hatsabibiyar aska!" Basiru ya furta yana sake kafe mahaifinsa da kallo. "Ya aka yi ka san da ita? Kuma me za ka yi da ita..." Tun bai rufe baki ba Basiru ya ɗauke fuskar Boka Shaddas da hatsabibin mari nan take ƙwayar idonsa na hagu ya faɗo, wata irin azaba ta ratsa shi cikin kiɗima ya kwarara ihu cike da azaba. Babu shiri Boka Shaddas ya turbutsa hannu a cikin ƙarƙashin ƙasa ya zaro wata ƙanƙanwar aska, jikinsa na rawa ya miƙa wa Muhsin don bai manta ba da ita ya hallaka mahaifinsa har lahira. Muhsin yana karɓa bai ko waiwaye shi ba kai tsaye ya nufi Masarautar Huddam. *SHU'UMAR MASARAUTA* *42* *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Tun daga ranar da Fargi ta ziyarci bishiyar da suke bautawa ta fara horar da abin da yake cikinta tare da ba shi duk wata kariya, musamman da ya zaman ta bincika halwar tsafinta ta; ta san mace za ta haifa. A wani lokacin ta kan zauna jigum ta dinga tunanin makomar rayuwar abin da za ta haifa, fargabarta ɗaya kada bayan ta mutu Shugaba ya cutar da abin cikinta, sai zuciyarta ta shawarce ta da ta damƙa ta a hannun mahaifinta ko ta taso cikin kulawar mahaifinta don tana da tabbacin ko bayan ba ta raye zai kula da ita. A ɓangare ɗaya kuma wata zuciyar tata ta ƙi ba ta haɗin kan amincewa da haka. Wannan yanayin da ta tsiro da shi na killace kanta da tsafin da take yi wa cikinta, bai sa ta janye jiki daga wurin Shugaba ba don gudun kada ya zargi shirinta, kuma kusan kullin sai ya tuntɓe ta don ya ji shawarar da ta yanke amma kullin bagarar da shi take tana nuna masa har lokacin nazari take yi, shi kuma babban burinsa bai wuce ta damƙa masa ƙarfin tsafinta ba. Sannu a hankali Mahaifinta da manyan yayyanta suka fahimci yanayin damuwar da take ciki, watarana har sai da mahaifinta ya zaunar da ita ya tambaye ta dalilin da ya sa take keɓe kanta kullin a bukkar da take gudanar da al'amuran tsafinta. Don ta kawar masa da shakku da damuwa sai ta nuna masa wasu manyan ayyuka take gudanarwa, a lokacin da mahaifiyarta ta ji haka ta tausaya mata matuƙa duk ita ma ba ta san abin da Fargi take aiwatarwa ba, amma haka kawai jikinta yake ba ta akwai dalilinta na yin haka don haka watarana ta taɓa samunta a bukkar. A lokacin da mahaifiyarta ta shiga a zaune ta same ta gaban sihirtacciyar wutar da ke gabanta, da sauran tarkacen kayan tsafinta. Wani farin hayaƙi ne yake tashi sai ya je kan allon farin ƙarfen da take tsafi da shi sannan ya dawo ya shige cikinta, duk wani abu da take gudanarwa tana yin sa ne a kan abin da yake cikin jikinta. Shiru Mahaifiyarta ta yi tana kallonta sai da ta ga ta kammala sannan ta furta. "Ko ba za ki sanar da kowa ba ni mahaifiya ce, ki sanar da ni dalilin aiwatar da wannan sabon aikin da kike yi ba dare ba rana. Ko kina tsoron kada na yaye miki labulen sirrinki ne?" Cike da gajiya Fargi ta miƙe ƙafarta ta fara yi mata tsami ta ɗan jingina da bango. "Ko da ba za ta gaje ni game da al'amarun tsafi da sihirina ba, ina katange ta daga kaidin Shugaba da duk wani mai sharri. Na san waye Shugaba da zuri'armu, sanin kanki ne matuƙar wannan cikin ya bayyana a gare su ba za su taɓa ƙyale mu ni da abin cikina ba. Ko na haife ta kin san su da bibiya ba za su bar ta, akwai wani sirri da nake son sanar da ke dangane da yarinyar nan." Fargi ta yi shiru tana bin cikin jikinta da kallo, mahaifiyarta ta sauke ajiyar zuciya ta ce. "Ina sauraronki." "Yarinyar nan ta kasance mahaɗi ce na kowanne matsafi ko gawurtaccan mai sihiri zai so ya mallake ta, babu wani boka da ba zai so ta zame masa tsanin da zai hau da zai kai shi ga tudun shahara da gawurta ba." "Ban taɓa jin irin haka ba, wanne dalili ne zai sa ta zama haka shin kina nufin ba za ta samu sukunin rayuwa ba kenan?" Mahaifiyarta ta wurga mata tambaya. "Saboda taurarin abar bauta sun sauka a kanta, sara na yi a kan gaba a lokacin da na kai kokena gare ta. Ta zubar mata da jinin shanu marasa adadi, akwai muhimman saƙƙonni a kanta, zan labarta miki kaɗan daga ciki idan dare ya tsala." Cikin gamsuwa da maganarta mahaifiyarta ta amsa mata, sannan suka ci gaba da hira. Dattijo Maharaz ya girgiza wa Kamalu kai sannan ya ce. "Sunan Mahaifinka Sarki Abdul'aziz, shi kuma Sarki Sulaimanu ai daban yake." "Amma me ye alaƙar Sarki Sulaimanu da ɓatan Jawahir? Ko dai akwai wani mummuna ala'amari da ya gudanar a kanta. Na rantse da girman Allah, matuƙar aka same shi da hannu a ɓatanta sarautar da yake taƙama da ita ba ta isa ta ba shi kariyar hukuncin da za a yi masa ba. Sai dai duk wani ruguntsumi da zai faru ya faru..." Murmushin Dattijo Maharaz ya katse Kamalu cikin mamaki Kamalu ya bi shi da kallo. "Ina ma za ka bari abin da yake ƙasan zuciyarka ya bayyana a fili, ina ma ba wannan haɗin Sarki Sulaimanu ya zartar ba, da kuwa tabbas haɗin mabambamta zuri'ar nan sun yi daidai. Kwatankwacin yadda ake ɗora ƙwarya a gurbint." Kamalu sam bai fahimci maganar Dattijo Maharaz ba, yana shirin yin magana ya katse shi. "Sarki Sulaiman na tare da wata alfarma ko sirri wanda zai zame muku tamkar fitila da za ta haska muku hanya a cikin duhun dare. Yanzu abin da nake so da kai dai, idan Allah ya kaimu gobe zan samu mahaifinka mu yi magana da shi, kasan ba a shiga dawa haka nan dole sai an yi masa shiri." Jinjina kai Kamalu ya yi ya ji kusan kaso mai yawa na damuwar da yake ciki ta ragu, har Dattijo Maharaz ya miƙe zai tafi Kamalu ya katse shi. "Jikina a sanyaye yake a kan wannan lamarin, ina tsoron kada abin da ya faru da ni ita ma ya kasance a kanta, wallahi ba za ta iya jura ba. Ni na san Jawahir farin sani, cika bakinta da tsiwarta a iya fatar baki ce. Don Allah ka yi wani abu farin jakada idan har za a cutar da ita." Kamalu ya ƙarasa maganar cikin damuwa. "Ba a iya fatar baki waɗannan kalaman naka suke fitowa ba, da alama suna fitowa daga cikin zuciyarka ne. Kusan abin da ya faru da kai ne ya faru da ita, sai dai suna da matuƙar bambamci domin ita gida ta koma, ta koma tsatsonta ne saɓanin kai da babu dangin iya ballantana na baba." A zabure Kamalu ya dafe ƙirji ya ce. "Kana nufin ita ma 'yar cikin jinsinku ce?" Dariya sosai Dattijo Maharaz ya yi sai ya yi mai isarsa ya ce. "Idan hakan ne akwai wata damuwa ne?" "Allah ya sani na aminta da kai Dattijo Maharaz ban taɓa rayawa a raina za ka faɗa mini ba daidai, kuma wannan ɓoyayyan sirri ne da babu wanda ya taɓa jin sa daga gare." Sai da Kamalu ya tattaro jarumta murya a dashe ya ci gaba da cewa. "Tun da na buɗi ido na fara jin wani irin yanayi a game da ita, zuciyata ta jima tana azabtuwa a ƙaunarta sai dai a kullin rashin jituwarmu ta sa ban taɓa gangancin bayyana mata sirrin da ke kwance a cikin raina ba. Dattijo Maharaz na jima da dulmiya kogin ƙauna da soyayyar Jawahir, kogin da ya shallake rijiya gaba dubu a tsananin zurfi da nisa, kuma na yi tsalle babu adadi domin na fito daga ciki har yau ban samu nasara ba. Ko Kalaman Muhsin a kan soyayyarta ba su gigita ni tamkar yadda wannan furucin naka ya ɗimauta duniyata ba, yanzu shi kenan aure ya haramta tsakanin da Jawahir Dattijo Maharaz?" Tausayin Kamalu ya kama shi, ya dafa kafaɗarsa sannan ya ce. "Ita bil'adam ce kamar kai Kamalu, kalamaina sun yi tsauri da ka fahimci abin da nake nufi kai tsaye. Ka bari za mu tattauna idan Allah ya kaimu." A sanyaye Kamalu ya amsa masa sannan suka yi sallama ya fice. Bayan fitar Boka Shaddas Shugaba ya sake kallon wurin da Jawahir ke tsaye tana hawaye ya ce, "Buɗe mini cikinki!" Dire kalamansa ya yi daidai da jin cikinta ya ɗauki raɗaɗi kamar yadda yake yi mata idan tambarin cikinta zai bayyana. Tsoro ya sake mamaye ta, jikinta ya ci gaba da karkarwa ganin ta kai ƙarshen bango ta durƙushe a saman gwiwoyinta ta furta."Don Allah kada ka cutar da ni, ka yi haƙuri idan wani laifin na yi maka." Jin sautin muryar Jawahir ya sake karya zuciyar Mahaifin Fargi. "Zan yi wata doguwar tafiya mai nisan gaske, tafiyar ba a waiwaye ballanta a dawo baya. Don girman tsafi da sihirin da na buɗe ido kuna auwatarwa, iyayena ku yafe mini idan akwai laifin da na yi muku a baya." Kalama Fargi na bawa suka dawo masa cikin kunnuwansa ana gobe za ta yi tafiyar da har kawo wannan ranar ba ta waiwayo su ba tamkar yadda ta faɗa. Goge ƙwallar idonsa ya yi ya fara tunkarar Shugaba yana jin wata irin ƙwarin gwiwa na ratsa shi, don ba ya jin zai yarda ya sake rasa jinin Fargi a karo na biyu. "Biyayya ga Shugaba girmamawa amma ce, amma biyayyar da yankin nan suke yi wa Shugaba ita take ba shi lasisin da yake cin karensa babu babbaka a kanmu. Don natsayin abar bauta mu zama jajjirtattu a kan 'yancinmu, hakan ne zai ɗarsa wa Shugaba shukku a ka cin kashin da yake aiwatar mana." Ya sake tuna kalaman da Fargi ta faɗa masa a ranar da za ta yi bankwana da su. Kafin Mahaifin Fargi ya ƙarasa tuni Shugaba ya isa gaban Fargi, ganin ya tunkaro ta da wani dogon ƙaho ya sa tsoronta ya tsananta har ta faɗi a can gefen. Da ƙarfin tsiya Shugaba ya ɗaga rigarta ya sa ƙahon hannunsa da niyyar zuƙe duk wata kariya da tasirin da tambarin cikinta ke ɗauke da shi. Wani irin jan haske mai kama da harshen wuta ya mamaye fuskarsa, wata irin azaba ta mamaye saman fuskarsa mai ɗauke da raɗaɗi. Tun da ya ga wannan jan hasken ya gifta masa bai sake ganin komai ba sai ma wani irin zafi da yake ji tamkar an watsa masa ruwan barkono, mamaki ne ya kama Jawahir ƙarara haɗe da tsoro. Hannunta ta kai saman cikinta tana mamakin wai yau wuta ce ta fito daga cikin cikinta. Ƙaraji da ihun azabar da Shugaba yake yi ya ratsa cikin kogon dutsen gabaɗaya, har ya fara gayyato tsirarun mutanen da ke maƙotaka da shi. Mahaifin Fargi na ganin haka ya ƙarasa wurin Jawahir yana kukan farinciki. "Tsafi ya albarkaci rayuwarki, saihiri ya ci gaba da baki kariya har abada." "Ni ba matsafiya ba ce, kuma Inna ta ce mini sihiri da tsafi haramun ne ga duk wanda yake yi, idan ya mutu zai dawwama a wutar jahannama." Jawahir ta faɗa tana ɗan ja da baya, duk da shi ta lura ba ya burin cutar da ita amma shi ɗinma ba ta amince da shi. Daga bakin ƙofar shigowa cikin kogon dutsen suka hangi tsirarun mutane na shigowa fuskokinsu ɗauke da yanayin mamaki. Shugaba can gefe ya faɗi har lokaci murza idanu yake kuma fuskarsa babu alamar ƙonuwa ko jin ciwo, hatta idanunsa tangaram suke a buɗe sai dai gabaɗaya baya ganin komai sai duhu. Sai da mutanen suka gama shigowa sannan suka ga Fargi ta ratso ta jikin bangon kogon dutsen, da mamaki suke bin ta da kallo waɗansu da suka san Fargi a baya baki sake suka fara kallon Jawahir suna kallon Fargi da ke tunkaro su. Kai tsaye wurin Shugaba ta isa sai da ta tsugunna ta dafa kafaɗarsa tun ba ta fara magana ba gaban Shugaba ya faɗi. "Ya aka yi tasirin tsafinki ya haure nawa? Tabbas kin yi nasara a kaina Fargi." "Na sha faɗa maka dama mai laya ya kiyayi mai zamani! Ita rana dubu ta ɓarawo ce guda ɗaya ce tak ta me kaya." Tana gama maganar ta watsa masa wani farin garin magani, sannan ta ƙarasa wurin Jawahir da har lokaci tana ƙasa a kwance ta ɗago ta. "Ba tun yau ba, na faɗa miki tsoro ba ya daga cikin ɗabi'a ko halayen zuri'ata. Ki zama mai kare kanki ba sai wani ya kare ki ba." Jawahir ba ta iya furta komai ba, ta ruƙo hannunta suka ƙarasa wurin Mahaifinta. Da hannu ya shafa fuskarta lokaci ɗaya hawaye ya fara bin kumatunta. "Wannan jininka ce, jikarka ce wato 'yar cikin Farginka." Haka kawai Sarki Sulaiman ya ji zuciyarsa duk babu daɗi abin duniya goma da ashirin ya mamaye shi, tunanin Fargi da rayuwarsu ta baya ta shiga dawo masa don haka ko da daddare da ƙyar bacci ya yi awon gaba da shi, hatta iyalansa sai da suka lura da yanayin da yake ciki. Wani irin bacci ya dinga yi mara daɗi cike da mafarkan Fargi masu tsayawa a rai. Tun asuba ba ta yi ba bacci ya ƙaurace masa, don haka ya ci alwashin a wannan ranar sai ya ziyarci Yankin Rumzu sai dai duk abin da zai faru da shi ya faru. Duk da a baya ma yakan badda kama ya je da kayan abinci niƙi-niƙi ya sa a kai wa iyayen Fargi kuma har kawo wannan lokacin bai daina zuwa ba. Ya tashi da niyyar tafiya sai kuma aka wayi gari Mai babban ɗaki babu lafiya, don haka ya haƙurewa zuwa har zuwa washegari idan jikinta ya yi kyau saboda yanayin girma ga shekarun da suka fara cim mata. Mai gado kusan yadda ta ga rana haka ta ƙarasa ganin dare saboda tashin hankalin rashin sanin halin da Jawahir take ciki da matsanancin halin da Malam Umaru yake ciki na jinya, sai dai har gari ya waye babu wani ci gaba a ciwon Malam Umaru, hatta tsarki da alwala ita ta ɗaura masa tana rayawa a ranta wataƙila ko niyya ce ya yi ya gabatar da sallar asuba. Gari na wayewa aka dinga shiga yi mata jaje da dubiyar halin da mijinta yake ciki, hatta Ruƙayya sai da jikinta ya yi sanyi ganin halin da yake ciki da kuma ɓatan Jawahir Don haka Inna wuro ita ta ci gaba da ba su kulawar duk abin da Mai gado ta saba yi musu, Abubakar da ƙyar ya ya yarda ta ba shi abinci don sai da Mai gado ta je ta saka baki sannan ya yarda. Basiru na isa Masarautar Huddam kai tsaye ɗakin duhu wurin da aka rufe su Fulani Umaima ya nufa, wari da ƙarnin da ke tashi a wurin bai hana shi tunkarar ƙofar ba. Da ƙarfi ya doka ƙofar da ƙafarsa ƙofar ta karye cikin takun isa ya shiga ɗakin hannunsa ɗauke da tsafatacciyar askar. Jakadiya da ke zaune a zube kamar kayan wanki cikin tashin hankali ta fara sakin fitsari, duk da jikinta babu ƙwari haka ta fara jan jikinta da ƙyar domin ceton ranta saboda a tsammaninta Basiru kashe su zai yi. Fulani Umaima ta takure a ƙarshen bango ta yi saranda don azabar da take ciki gara mutuwarta da rayuwarta. Har Basiru ya ƙarasa motsin kirki ba ta iya yi ba sai bin sa da take yi da jemammun idanunta, ta rame sosai ta yi wani irin baƙi ga waɗansu ƙananan farare da jajayen tsutsotsi da ke manne a fatar jikinta. Sai da ya tsugunna a gabanta ya girgiza kai yana yamutsa fuska sannan ya furta. "Ki kwantar da hankalinki ba kashe ki zan yi ba, ɗan wani abu zan samu a wurinki wanda zai amfani duniyata. Don ma mahaɗin ya zame mini dole na haɗa da ke saboda tasirinki na kasancewarki a matsayin uwa da babu abin da zai kawo ni wannan ɗakin." "Don Allah kada ka cutar da ni Basiru, don na san nahaifinka ya gama horar da kai al'amuran tsafi da sihiri." Fulani Umaima ta yi maganar murya can ƙasa saboda galabaita. "Kin san an ce kowa ya biya allonsa ya wanke, ba don kin ɓata rawarki da tsalle ba ai da tuni kina can kina cin duniya da tsinken tsire. Yanzu dai tun da kin tsinci talatarki a laraba haƙuri ya zame miki dole, kin ga nan gaba idan aikina ya biyo ta kanki shi kenan." Muhsin na gama maganar ya ture Fulani Umaima a ƙasa, tsafatacciyar askar hannunsa ya sa ya fara reɗar gashin kanta yana zubawa a cikin wani ƙanƙanin ƙoƙon tsafi, sai da ya aske gashin kanta tas sannan ya yanki faratan ƙafafuwanta. Bayan ya gama ya soki cinyarta da askar nan take jini ya fara tsattsafowa ya dinga lakuta da wani farin ƙyalle yana goge jinin. Tun da ya fara gogar jinin jikinta ta fara jin wani irin zuuu kamar ana zuƙe jininta, tana nan zaune hawaye ya wanke mata fuska babu yadda za ta yi, tana gani ya gama ya fice daga ɗakin. Sai ya fice Jakadiya ta samu sukunin sauke ajiyar zuciya, duk da ta san wace ce Fulani Umaima a ƙwarewa wurin mugunta amma ganin yadda siffa da kammainta ya sauya sai da ta bata tausayi, duk da ita ɗinma abar tausayin ce. Sarki Abdul'aziz shiru ya yi bayan ya gama sauraren Dattijo Maharaz, ya dubi Kamalu da lokaci guda ya ga ya zabge sannan ya mayar da kallonsa wurin Dattijo Maharaz. "Yanzu me ye abin yi tsoho mai ran ƙarfe?" "Tafiya ƙasar Sarki Sulaimanu! Don haka ne ma jiya da daddare ban ziyarce ka ba." "Amma kuma mahaifiyarta tana cikin kiɗima bisa abin da ya faru da mai gidanta, kuna ganin za mu iya sanar da ita abin da yake faruwa?" Sarki Abdul'aziz ya tambaya. "Zuwa da Mai gado wannan garin yana da matuƙar muhimmanci, ni na san su waye al'ummar rumzu kuma na san kafiya da taurin kansu." Dattijo Maharaz ya waiga wurin Kamalu sannan ya ci gaba da cewa. "Kamalu ka kula da Malam Umaru sai ka nemi wasu Bayin su taya ka kula da shi." Kamalu bai so haka ba amma kuma mutumci da ƙimar Dattijo Maharaz ya sa ba zai iya musa masa ba. A safiyar wannan ranar Sarki Abdul'aziz da kansa ya sa aka shirya masa keken dokinsa da sauran tantina, mutane sun yi matuƙar mamakin jin tafiyar Takawa a rana tsaka. Tuni aka aikawa da Mai gado game da tafiyar, Kamalu tamkar zai zubar da ƙwalla a lokacin da za su tafi. Sarki Sulaimanu yana cikin turakarsa bayan ya koma daga dubo jikin mahaifiyarsa aka sanar da shi zuwan Sarki Abdul'aziz daga Masarautar Huddam tawagarsa, duk da bai san da zuwansu ba amma nan take ya sa aka shirya musu tarba ta musamman. Ba su ɗauki lokaci mai tsayi ba Sarki Abdul'aziz ya furta. "Sarki Sulaimanu mun zo ne domin ka yi mana wata alfarma." Sarki Sulaimanu fuska ɗauke da mamaki ya furta. "Alfarma kuma Sarki Abdul'aziz? Wacce iri?" Dattijo Maharaz da ke gefe ya yi shiru yana jin tattaunawarsu. "Zuri'ar Rumzu! Zuwa gare su muke son ka yi mana iso..." A zabure Sarki Sulaimanu ya miƙe tsaye jiki na karkarwa. "Ya aka yi ka san da su? Wannan binannan sirri ne da iya mutum biyu ne kaɗai suka da shi. Ya aka yi kasan alaƙata da..." "Ni na sanar da shi haka Sarki Sulaimanu. Kuma mun zo ne domin neman goyon bayanka zuwa cikin waɗannan mutanen domin akwai abu mai matuƙar muhimmamci da za mu aiwatar." Dattijo Maharaz ya katse Sarki Sulaiman. "Ko da babu kowa na fargi a wurin zan je wannan garin ballanta mahaifi da mahaufiyarta suna raye." Sarki Sulaiman ya furta sannan ya sa aka yi musu shiri suka nufi garinsu Fargi. Mai gado tun daga Masarautar Huddam kanta ya kulle, sakamakon babu wani kyakkywan bayani da aka yi mata, ba don Takawa ne a gabanta ba da ta tambayi dalilin gayyato ta da zuwa wannan garin, amma ta san ko karen hauka ne ya cije ta ba ta isa ta wurga masa tambaya ba. Abu ɗaya ne ya tsaye mata a rai jin sunan Fargi don idan ba ta manta ba ta taɓa jin Jawahir ta ce ita ce take yi mata iƙirarin mahaifiyarta ce. *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Ganin ƙofar ɗakin nasu a buɗe hanhai ya sa Jakadiya ta fara jan jiki a hankali ta zo baƙin ƙofar wurin da niyyar ta fita idan ya so ko guduwa sai ta yi tun da dare ya fara yi ba lallai wani ya ganta ba. "Idan kin tafi ina za ki je? Waye zai karɓe ki a wannan yanayin da kike ciki? Ki rufa wa kanki asiri ki koma, zamanki a wannan wurin shi ne suturarki." "Ki gudu kawai, yanzu zama za ki yi azaba ta kashe ki?" Tagwayen shawarwarin suka fara shawagi a zuciyarta. "Kamar ba ki san a cikin gidan da kike ba? Kin manta ke Jakadiya ce labarinki ya gama karaɗe ciki da wajen masarautar nan a kan abin da kika aikata? Ki rufa wa kanki asiri kawai ki koma ciki." Zuciyarta ta sake ba ta shawara. Babu yadda ta iya a hankali ta sake jan jiki ta koma cikin ɗakin, har lokacin Fulani Umaima na wurin da Muhsin ya bar ta tana zubar da hawayen nadama. "Ban san haka duniya take yi wa mutum atishawar kaji ba sai da layinta ya zagayo kaina. Kaicon rayuwar da ba ta da amfani, ni Umaima na cuci kaina." Fulani Umaima ta yi maganar cikin galabaita da tsantsar nadana. Abin duniya ya haɗe wa Sailuba goma da ashirin sakamakon yadda mutane suke ƙyamatarta da wulaƙantata dangane da laifin mahaifiyarta, ko guri ta je tana zama kowa yake darewa sai dai a barta ita kaɗai. Lokaci ɗaya ta fige ta rame ta lalace Uwa-uba cutar kwarkwatar da ke damunta, don ta samu ruwan da ke fita daga ƙansata ya yi sauƙi sosai. Sai a wannan lokacin da ta bambamce tsakanin tsaba da tsakuwa take dana-sanin wulaƙancin da ta dinga yi wa Bayi a baya, sai ga shi Bayin da take hantara take kyara a wannan lokacin sun fita ƙima da mutumci a idanun manyan masarautar da sauran mutanen cikin gidan gabaɗaya. Idan ta yunƙura don ta je ta gano halin da mahaifiyarta take ciki fargaba sai ta mamaye ta, sau ɗaya ta taɓa zuwa ta gano ta ranar ko baccin kirki ba ta iya yi ba saboda damuwa. A wannan ranar ne ta yanke shawarar sake zuwa ta gano halin da Jakadiya take ciki, ta tafi da wani guntun busasshen ƙanzo a leda ta tafi mata da shi don ta san abinci sau ɗaya suke ci a wuni guda. Duk irin dakiyar da ta gayyato wa kanta sai da warin wurin ya addabe ta, don haka ta sa hannu ta toshe hancinta tana jin wani irin amai yana taso mata. Kwamacalar fitsari da tsutsotsin da ke cikin ɗakin ya sa Sailuba ba ta iya shiga ɗakin ba, sai daga bakin ƙofa ta iya wurga wa mahaifiyarta ledar ƙarzon da ko daka shi ba ta yi ba. Kamar kaji haka suka fara kokawa a kan ledar sabida yunwar da ke addabarsu, suna cikin haka ledar ta yage suka ci gaba da ɗibar na ƙasa suna cinyewa. Wani irin kuka ne ya zo wa Sailuba ta juye za ta bar wurin ta hangi wasu ƙaratan Dogarai sun nufo wurin da ƙofa a hannunsu, basu kula ta ba suka fara kiciniyar mayar da ƙofar wurin ganin haka ta sa ta wuce sashensu Bayi zuciyarta a dagule. Gyaɗa kansa Mahaifin Fargi ya yi ya ce mata. "Amma Fargi me ya sa kika yi nisa da mu? Me ya sa kika guje mu? Mun jima muna bulayin nemanki amma ko mai kamarki ba mu taɓa gani ba sai a yau da na yi tozali da yarinyar nan." "Akwai rikitattun labarai da zan bayar game da Fargi, amma sai na kai Jawahir binne littafin labarin Hidaya sannan ta ɗauko sihirtacciyar takobin da ta Hidayan ta binne. Da sauri Jawahir ta fara ja da ba ya ta ce. "Don Allah ki kaini wurin Inna na san tana can cikin damuwa." Jawahir ta furta kamar za ta yi kuma. "Innarki ta taho yankin nan kada ki damu Jawahir." Shiru Jawahir ta yi ba ta amsa ba. Tana nan tsaye mutane suka ci gaba da tuttuɗowa ana shigowa cikin kogon dutsen, kallonsu ta fara yi ɗaya bayan ɗaya tana sakin murmushi sannan ta riƙe hannun Jawahir sosai ta furta musu. "Ku dakace mu zuwa wani ɗan lokaci kaɗan." Daga haka suka ɓace daga wurin ba su tsaya a ko ina ba sai a cikin wata farar sahara, bakin wani koren kogi suka ƙarasa ruwan cikinsa garai-garai kana iya kallo duk abin da yake ciki. Sannu a hankali Fargi ta fara jan Jawahir har cikin ruwan, wani irin sanyi ta ji yana ratsa ilahirin jikinta. A tsamaaninta kogin mai zurfi ne sai dai har suka je tsakiyarsa a yadda yake haka suke tafiya. "A shakaru masu yawa da suka wuce ainihin gurin nan ba teku ba ne, ko lokacin da Hidaya ta binne takobinin babu ruwa a gurin nan. Saka hanunki a nan ki ɗauko takobin nan." Fargi ta yi maganar tana nuna wa Jawahir wani zabgegen farin takobi da ke tsaye cak a cikin gidansa yana walwali da ɗaukan ido. Babu musu Jawahir ta saka hannunta za ta ɗauka ƙam ta ji takobin ya fara fisgarta can ƙasan ruwa, a tsorace ta fara kwarara ihun sai bayan wani lokaci ta ji komai ya lafa sannam ta riƙo takobin hannun nata. "Ungo mayar da littafin nan ciki, jiya na kuɓutar da shi daga hannun Shugaba don na san zai iya ɓatar da shi ko ya ƙone shi domin kowa ya rasa." Kamar mutum mutumi haka Jawahir ta tsaya duk abin da ake saka ta haka take aiwatar da shi, saboda kallo ɗaya za ka yi mata ka fahimci a tsorace take. A hankali ta ƙarasa daidai wurin da ta ciro takobin ta zura littafin, da kansa ta ga yana gangarawa ya shige yana gama shiga ta ji wani abu ya ɗaure mata kai tamkar wacce aka kafa wa hula a kanta har sai da ta kai hannu ta shafa saman goshinta. Luuu ta ji a kanta wata irin juwa na yunƙurin ɗaukanta, tana shirin zubewa ƙasa da sauri Fargi ta riƙo ta tana sakin murmushin. Ruƙo hannunta ta sake yi suka fito daga wannan ruwan sannan ta ja hannunta zuwa bakin wata murgujejejiyar bishiyar kukar da ke maƙota da kogin, jingina ta ta yi a jikinta ta fara motsa bakinta, ta jima a haka sannan ta dafa kafaɗarta nan take suka ɓace daga wurin. A inda suka bar mutane da Mahaifin Fargi a nan suka koma suka same su tsautsaye carko-carko, Shugaba har kawo lokacin yana tsaye baƙinciki ya mamaye zuciyarsa. Jagora ta yi musu zuwa wajen dutsen sakamakon cunkoson mutanen da suka ƙaru a cikin kogon dutse, da hannunta ɗaya ta fara jan Shugaba a ƙasa duk irin ihun da yake yi ba ta kalle shi ba. Kamalu yana cikin Masarautar Huddam yana kula da Malam Umaru amma zuciyars da ruhinsa na wurin Jawahir da halin da take ciki, duk wani abu da Malam Umaru yake buƙata shi yake yi masa daga ƙarshe ma gabaɗaya Bayin da ya kira masu taimaka masa ya sallame su. Har cikin dare Kamalu yana jin shige da ficen da Muhsin yake yi da alamar akwai abin da yake son tambaya amma ganin Kamalu ya sa ya haɗiye abin da yake ransa. Sarki Sulaimanu sai da ya sa aka haɗa musu guzuri da kayan abin da ba a rasa ba sannan Bayi da Sojojin cikin Masarautar suka rufa musu baya, tafiya suka yi mai nisa sannan suka shiga cikin garin Bururu. Kafin su shiga ta cikin ƙofar sai da Sarki Sulaimanu ya isa bakin wata bishiyar kuka da ke gefen ƙofar ya dafa ta da hannunsa na hagu sannan ya furta. "Sulaimanu ba shi kaɗai ba ne tare yake da mabambamtan fuskoki." Sai da ya tsinki ganyen bishiyar kukar ya damƙa musu kowannensu ya riƙe a hannun hagunsu sannan suka shiga cikin garin, tun daga shigarsu cikin garin su Sarki Abdul'aziz suka sha jinin jikinsu kallo ɗaya za ka yi musu ka fahimci a ɗan tsorace suke. "Amma me ye fa'idar yin hakan da ka yi Sarki Sulaimanu?" Sarki Abdul'aziz ya tambaya. "Saboda sun gama tsaface garinsu, tun tasowa ta har zuwa yanzu ban taɓa jin labarin garin da ya yi shuhura a kan aikin tsafi da sihiri tamkar wannan ba. Yin hakan ne zai ba ku damar shi ga cikin garin nan hankali kwance, idan ban yi haka ba akwai matsaltsalun da za su iya biyo baya." Jinjina kai Sarki Abdul'aziz yana mamakin ƙarfin tsafi da sihirin al'ummar Rumzu. Sarki Sulaiman ya sha mamaki da ya ga garin a yaye tamkar babu mutane don sai tsirari daga cikinsu, kuma duk wanda ya gansu haka zai bi su da kallo har sai sun ɓace wa ganinsu sakamkon bambamcin shigar da suke da ita. Tun daga nesa Jawahir ta hango Keken dokin Sarki Abdul'aziz, wani irin farinciki ya lulliɓe ta ta zabure za ta tafi da gudu, Fargi ta damƙe hannunta da ƙarfi. Nan take idanun Jawahur ya ciko da ƙwalla, yadda suka hango cincirindon mutane a hanyar kogon dutsen Shugaba ne ya ja hankalin Sarki Sulaimanu, don da har ya yi niyyar fara zuwa gidansu Fargi domin su ɗan huta idan ya so sai Sarki Abdul'aziz ya gudanar da abin da yake tafe da shi, tun da har kawo lokacin bai san dalilin yin wannan tafiyar ba. Sannu a hankali komai ya shiga dawo masa dangane da alaƙar da ke tsakaninsa da Fargi a lokacin baya. "Sadaukina yanzu fa watarana sai mu zo garin nan mu da 'ya'yanmu idan ka mayar da ni Masarautarku ko?" Kalama Fargi na baya suka shiga dawo masa a lokacin da ba su jima da yin aure ba. Ganin yanayin shigarsu ya sa tun da suka tunkari kogon dutsen mutanen da ke wurin suka shiga darewa suna ba su hanya, Tun da Mai gado ta hango Jawahir ta tafi da gudu cikin kuka ta rungume ta ita ma Jawahir ta saka kukan farinciki, da farko ya yi tsammanin idanunsa gizo suke yi masa amma da ya ƙarasa gabanta a nan ya tabbatar da ƙwayar idonsa ba yaudararsa take yi ba. Jikinsa ne ya ɗauki karkarwa kamar mazari ƙirjinsa ya shiga bugu da ƙarfi zuciyarsa tamkar za ta hudo ƙirjinsa, da hannu ya shiga nuna ta bakinsa na rawa ya furta. "Far... Fargi ke ce ƙwayar idona ke gane mini?" Idanunta suka ciko ƙwalla tsantsar tausayinsa ya mamaye ta, ganin haka ya raunata zuciyar Dattijo Maharaz. Jikinsa shi ma ba ƙaramin sanyi ya yi ba yana fargabar kalaman da za su fito daga bakin Fargi don ya san ba zai taɓa yi wa Sarki Sulaimanu daɗi ba, dangane da tsammanin da yake yi a kan Fargi ce a gabansa. Da ido sauran mutane suka ci gaba da bin su da kallo, Sarki Sulaimanu ya waigo wurin Sarki Abdul'aziz cikin farinciki ya ce. "Ikon Allah ikon gaske, ashe rabon mu gana da Fargi ne ya sa kuka kawo mini wannan gayyatar Sarki Abdul'aziz." Dattijo Maharaz ya yi murmushi sannan ya nuna Jawahir ya furta. "Wannan ita ce silar zuwanmu wurinta, shin har yanzu ba ka gane wace ce ita ba Sarki Sulaimanu?" Ƙurr ya yi Jawahir yana kallonta yana son furta abin da yake cikin zuciyarsa amma tsoron kada ya canka ba daidai ba ya dakatar da shi. "Tun ranr da na fara haɗuwa da ita Fargi nake gani a ƙwayar idon, kuma jikina yana ba ni akwai wata muhimmiyar alaƙar da ke tsakaninsu." Sarki Sulaimanu ya furta cike da shauƙi. "Wannan yarinyar 'yarka ce, jininka ce ta cikinka." Saukar kalaman Dattijo Maharaz suka yi daidai da jin dum! Da Mai gado ta yi tsakar kanta, Sarki Abdul'aziz ya zaro ido cikin tsananin mamaki. "Duk rintsi kada ku furta wannan yarinya ba jininku ba ce, don na san dangina da bibiya ko bayan wasu shekaru na tabbata za su iya bankaɗo labulen sirrin da na binne." Furucin Mahaifiyar Jawahir na baya ya sake dawo wa Mai gado, ta ji wani sabon tashin hankali ya tsarga mata. "Kana nufin wannan 'yar Fargi ce?" Sarki Sulaiman ya tambaya kai tsaye. Dattijo Maharaz ya ba shi amsa. 'Tabbas Biri ya yi kama da mutum, wallahi tun ranar da na fara ganinta a Masarautar Huddam na sha jinin jikina." Sarki Sulaimanu ya ƙarasa maganar yana rungume Jawahir a jikinsa. "Ranka shi daɗe idan Jawahir 'yarsa ce mene ne makomata a wurin Jawahir? A gafarce ni idan da kuskure a kalaman da zan faɗa, amma sam wannan ba shi ne ainihin mahaifinta ba. Mahaifin Jawahir yana gida ba shi da lafiya, ni nan ni ce mahaifiyarta ni na ɗauki cikinta har zuwa haihuwa." A wannan lokacin Sarki Abdul'aziz ya ɗan shiga ruɗani, tabbas a tarihin da ya ji Jawahir na daga cikin zuri'ar Rumzu, kuma a iya saninsa Malam Umaru da Mai gado ne iyayenta. "Me yake shirin faruwa?" Ya furta a fili cikin tsananin mamaki. "Wallahi-wallahi Fargi matata ce ta sunnah, kuma a shekarun baya akwai cikina a jikinta wanda ba na ko tantama wannan 'yata ce. Don Allah Fargi ki sanar da su gaskiya..." "Ka gafarce ni Sarki Sulaimanu bisa abin da zai fito daga bakina." Ta furta tana ɗan sunkuyar da kai ƙasa, jikinsa ne ya ɗauki karkawa ƙirjinsa ya buga tsoron abin da za ta faɗa ya mamaye shi. Wannan shi ne ga ƙoshi ga kwanan yunwa, fargabarsa ba ta wuce kada ya ga samu ya ga rashi ba don ko tantama ba ya yi wannan 'yar cikinsa. "A zahiri na tabbata kowa kallona yake a matsayin Fargi amma ni ba Fargi ba ce." A zabure Sarki Sulaimanu da Mahaifin Fargi suke dube ta jin kalaman da ta furta. "Fargi ta mutu bayan haihuwar 'yarta Jawahir yau kimanin shekara goma sha Shida kenan, na kasance ina amfani da surarta bisa yarjejeniyar da suka ƙulla tsakaninta da abar bauta tun a wani dare da ta taɓa kai wa abar bauta kokenta. Sunana na ainihi Zumjuttu na kasance ɗaya daga cikin jinsin aljanun da ke ɗaukar surar Mammaci suna gudanar da wasu al'amuran na shi na yau da kullum, kafin Fargi ta mutu ta yi wa abar bauta tukwicin da ita kuma ta damƙa mini wannan ragamar a hannuna, domin na kular mata da duk shige da ficen halin da Jawahir take ciki, har zuwa lokacin da za ta yi tozali da mahaifinta. Kuma koda wani mugun abin ake son na aiwatar da zarar an yi mini yanka an zubar da jini domin na dinga razanarwa ina firgitarwa, an riga da an gama biya kuma ba ya juya wa wannan aikin baya, wanda dalilin haka ne za ku ji ana ce wa fatalwar mutum tana tsoratar da mutane. Daga ƙarshe dai na sauke wannan nauyin da kula da Jawahir, sai kuma Abar bauta ta ɗora mini wani nauyin na mallakawa Jawahir hatsabibin littafin da Hidaya ta ba da labarinta a ciki, silar haka na dinga zuwar mata a fili wani lokacin kuma a cikin mafarkinta. Na ci gaba da kai kawo a cikin rayuwarta har zuwa lokacin Jawahir ta mallaki wannan takobin kamar yadda kuke gani." Aljanar da ke magana da surar Fargi ta ƙarasa maganar tana ɗago hannun Jawahir . A razane Dattijo Maharaz ya ɗago yana duban Zumjuttu rai a matuƙar ɓace. "Amma me ya sa sai a wannan lokacin za ku ci amanar abin da ta damƙa muku, me ya sa ba ki fayyace ainihin abin da ya sa kike bibiyarta ba?" Dattijo Maharaz ya yi maganar rai a ɓace. "Saboda a daidai wannan gaɓar muka fi buƙatarta, kana tunanin taurarin abar bauta za su sauka a kanta ba tare da wani dalili ba? Idan ba ka sani ba ka sani waɗannan taurarin sun sauka a kanta tun tana cikin mahaifiyarta, ka ga kuwa ai kai ma ka san banza ba ta kai zomo kasuwa." "Lallai kuwa akwai sauran rina a kaba." Dattijo Maharaz ya furta jiki a sanyaye. Mai gado ta rushe da matsanancin kuka don ba ta taɓa tsammanin wannan rana za ta zo a gare su ba, ganin Dattijo Maharaz da aljanar da ke ɗauke da surar Fargi sun fayyace komai dangane da Jawahir ya sa ta share hawayenta ta fara gaya musu alaƙar da ke tsakaninta da ita, tun daga lokacin da suka tsinci mahaifiyarta a daji tana naƙuda har zuwa mutuwarta da rainon Jawahir har zuwa girmanta. Shugaba da ke durƙushe a ƙasa ya fara lalube da hannunsa sannan ya furta. "Hakika kin yaudare ni Zumjuttu, ashe ke kura ce lulliɓe da fatar akuya ban sani ba? Kin ci amanata na ba ki yarda ashe ke za ki zama silar durƙushewata, a tunanina da guntun binciken da na gudanar a halwar tsafina kullin Fargi nake gani. Don haka kacokam na mayar da hankalina wurin ganin ƙarfi da yaji sai na dakushe ta, ba zan fasa faɗa miki ba ko a haka kika bar ni kin yi nasara a kaina." Haushin Shugaba ya mamaye Sarki Sulaimanu, sai da ya haɗiyi yawu mai ɗaci sannan ya miƙa hannu zai riƙo Jawahiru da sauri Zumjuttu ta janye Jawahir. Dattijo Maharaz ya naɗe hannuwa a ƙirji yana kallon abin da Zumjuttu take yunƙurin aiwatarwa. "A baya ku kuke da iko akan Jawahir amma wannan lokacin sai yadda abar bauta ta yi da ita, matsayinta na yanzu ya sha bambam da na baya. Idan kuna tantama za ku iya sarrafa ta ku gani." Ba Mai gado da Sarki Sulaimanu ba hatta Dattijo Maharaz sai da ya tsora ta da jin kalamanta, don ya san ba ƙananan hatsabibai ba ne. " "Amma me ya sa kuka son cutar da yarinya ƙarama, wacce ba ta san duk abin fa yake faruwa ba." Mahaifin Fargi ya yi maganar yana hawaye, mutanen wurin suka yi tsit kowa yana mamakin abin da yake faruwa. "Saboda Mahaifiyarta ta sadaukar mana da ruhinta da surarta domin kula da abin cikinta, bari na fayyace muku abin da ba ku sani ba hatta gawar mahaifiyarta sai da ta zama mallakinmu ce don haka abar bauta ta nemar wa 'yarta shahara da gawurtar da za ta ci gaba da amfana da ita. A daidai lokacin da ta cika shekara goma sha bakwai kuma za ta zama sadaukarwa ce ba sai na fayyace hukuncin da abar bauta za ta aiwatar a kanta ba. Ko ma dai mene ne Fargi ta tafka babban kuskure a baya, a tsammaninta abar bauta za ta ƙyale ta ne bayan ta auri ɗan wata zuri'ar da ba tata ba? Kwantan ɓauna kawai ta yi mata don haka wannan shi ne hukuncinta a fakaice. Tun da aka kafa ƙasar nan babu wanda ya taɓa aikata mummunan zunubi kamar wanda ta aikata, ka ga kuwa dole ne a tauna tsakuwa don aya ta ji tsoro. Saboda ko mutuwar Fargi ma da tafukan hannuwana na hallakata, na so hallaka 'yarta sai abar bauta ta hana ni domin muna buƙatar rayuwarta." *SHU'UMAR MASARAUTA* *44* *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* Basiru na fita daga Masarautar Huddan kai tsaye wata maƙabarta ya nufa da take bayan garin, ya jima a labe yana dube-dube don kada wani ya gan shi a lokacin da zai shiga cikinta, don sharaɗin aikin ba a yin tsafin ɓata idan za a shiga cikin maƙabarta a gudanar da abin da za a yi, sai dai mutum ya shiga da suffarsa ta ainihi. Ta bayan katanga ya haura sai da ya duba sababbun ƙaburbura sannan ya isa bakin wani sabon kabari, ya saka hannunsa na hagu ya fara ƙwaƙwalarsa da sauri har sai da ya ji ya fara taɓo mamacin da yake ciki, gashin Fulani Umaima ya ɗan damƙa da hannunsa ya zura cikin kabarin sannan ya haɗa da likkafanin gawar, ya zuba ƙasar a cikin sauran gashin Fulani Umaima sannan ya yanki likkafanin ya haɗa, ya ƙarasa mayar da sauran ƙasar wurin cikin kabarin sannan ya miƙe ya fice daga cikin maƙabarta. Kafin ya ƙarasa kogon tsafin mahaifinsa sai da ɗebi ƙasar wani murgujejen shuri sannan ya haɗa da ta gidan tururuwa ya haɗe su gabaɗaya. "Na gama tsorata da lamarin yaron nan Aljani Duggu kuma jikina ya jima yana ba ni Basiru zai iya zama silar ajalina. Shugaba Zurufu ya shammace ni domin ya ci amanar ajiyar da na ba shi, ya sake ƙeƙasar wa yaron nan da zuciya ka taimake ni a bisa taimakon da ka saba yi mini ya kai madogarata." Boka Shaddas ya yi maganar tamkar zai fashe da kuka saboda tashin hankali. "Amma kuma ka kusa ka makara Boka Shaddas! Bakin alƙalamin ya kusa bushewa don Shugaba ya gama horar da zuciyar Basiru, a hatsabibanci da rashin imani ya dame ka ya shanye, sai dai a yanzu ma ba za mu rasa taimakon da za mu yi maka ba." Aljani Duggu ya furta. "Babban taimakon da nake son ka yi mini Aljani Duggu ka kashe mini Basiru, ka kashe mini yaron nan kawai ko hankalina zai kwanta..." Kalaman Boka Shaddas suka katse sakamakon ganin Basiru ya dira cikin kogon dutsen, Murya na rawa ya yi wa Aljani Duggu sallama ya juya wurin Basiru ganin yana sakar masa murmushi. "Basiru har ka dawo?" Boka Shaddas ya yi maganar yana murmushin yaƙe zuciyarsa na bugawa. "Na dawo gawurtaccan Boka mai shinfiɗaɗɗan tarihi." Basiru ya ba shi amsa yana sakin murmushi. "Dalilin da ya sa ka ganni na fita babu shiri saboda wani aiki da na saka a gaba kuma a daren yau ake buƙatar ganin kammaluwarsa, amma yanzu komai ya zo ƙarshe tun da na haɗo duka kayan aikin." "Amma da ka yi magana ai da na sa Aljanun da ke yi mana aiki sun ɗebo maka." Boka Shaddas ya furta murya a sake don ya ga alamar tamkar Basirun bai ji tattaunawar da suke yi shi da Aljani Duggu a lokacin da ya shiga cikin kogon dutse ba. "A yau ba sai gobe ba za ka yi bankwana da duniya, kafin kasa a kashe ni dama tuni ni na ƙuduri aniyar hallaka ka har lahira." Basiru ya yi maganar a zuciyarsa, amma a fili sai ya saki murmushi ya ce. "Rashin dabarar da ban yi ba kenan." Yana gama maganar ya isa bakin wasu ajiyayyun ƙwara gwal da ke tsaye ragowar naman jikinsu yana ci gaba da zagwanyewa, Zama ya yi a gabansa ya fara ciro kayan aikin da ya samo, ya ci gaba da jan mahaifinsa da hira. Tsafatacciyar askar da ke hannunsa a ciro ya soka a tsakiyar maƙogaron ɗaya daga cikin ƙwarangwal ɗin, take jikinsa ya fara wata irin karkarwa, sai da ya ɗauki lokaci a haka sannan ya zaro ta daga jikinsa, ta yi wani irin jawur tana ɗaukan ido. "Irin azababban tsafin da yaron nan yake shirin yi sai fa ta kai maƙura nake yin irinsa, shin har da irinsa dama Shugaba ya koya masa?" Boka Shaddas ya tambayi zuciyarsa ƙirjinsa na bugawa, ya sauke ajiyar zuciya a hankali sannan ya ce. "Basiru wa za ka gudanarwa da aikin nan? Tabbas kowaye zai ɗanɗana azaba mafi girma kuma zai fuskanci bala'i mara yankewa." Murmushi Basiru ya yi sai da ya tsoma askar a cikin wani ruwan tsafi mai kama da manƙuli sannan ya furta. "Mai shirin cim ma buri! Domin ya samu biyan buƙatar da a kullin mafarkinsa kenan." Boka Shaddas ya maimaita kalaman Basiru ba tare da ya fahimci wurin da magaanrsa ta dosa ba. Miƙewa ya yi yana ɗan jujjuya askar ya kwashi ƙasar kabari da sauran kayan da ya haɗo ya zuba a cikin wannan ruwan, ya ɗauka ya fara tafiya a ahankali ruwan na ta zaɓalɓala. Tun da ya fara tafiya gaban Boka Shaddas yake faɗuwa har sai da ya ga Basiru ya wuce wurinsa sannan ya runtse idonsa yana sauke ajiyar zuciya. Cikin Shammata Basiru ya juyo ya kwara masa wannan farin ruwan tsafin a kan Boka Shaddas, matsawa ya yi can gefe ya ga yadda mahaifin nasa ya kwarara ihu cikin azaba. Jikinsa ne ya fara ƙamewa, fatarsa ta fara zagwanyewa ganin haka ya sa Basiru ya ƙarasa wurinsa da wuƙar, ya kai ta goshin Boka Shaddas sannan ya furta. "Ka yi haƙuri da wannan hukuncin da na yanke a kansa domin na jima da mafarkin samun kaina a wannan matsayin da kake kai, mutuwarka ɗaukakata ce don haka ba zan iya ci gaba da hangen ɗaukakata daga nesa ba. Ba iya kai ba, ita ma mahaifiyata akwai aikin da zan sadaukar da ita, ko kuma na aiwatar da wani aikin a kanta, wanda shi ne silar ɗaukakar da zan ci gaba da samu har ƙarshen rayuwata." A galabaice Boka Shaddas ya ɗago ya dubi Basiru hawaye ya fara gangarowa daga ƙandararrun idanunsa da suka fara ƙandarewa. Can jikin ƙwarangwal ɗin da ke tsaye ya nuna ya furta, "Koma can ka dawwama a haka." Tun bai rufe baki ba gangar jikin Boka Shaddas ta ja shi jikin ƙwarangwal ɗin da ke jere waɗanda ba su da adadi. Tsafatacciyar askar hannunsa ya ɗauko ya nufi wurin da mahaifinsa yake tsaye, ya ƙarasa ya soka masa askar a maƙogaronsa. Yana soka masa ita tuni jikinsa ya farar karkarwa naman jikinsa ya fara zagwanyewa yana zuba a ƙasa, sai da ya ga numfashin mahaifinsa ya ɗauke sannan ya zare askar ya mayar da ita wurin da take. Sannu a hankali cikin Fargi ya ci gaba da girma har ya kai watanni tara, a madadin ta ɗan murje ta ciko sai ya zamana wata irin rama take yi saboda tashin hankali. Musamman waɗansu irin munanan mafarkai da take yawan yi a wannan lokacin, ta so sanar da mahaifiyarta halin da take ciki amma gudun tashin hankalinta ya sa ta ja bakinta ta yi shiru. Tun wayewar garin ranar ta tashi da ɗan ciwon baya da mara sama, amma da yake bai yi mata tsanani ba sai take ta gudanar da al'amuranta. Tana nan zaune saƙon kiran Shugaba ya je mata, haka kawai ta ji gabanta na faɗuwa zuciyarta ta fara saƙa mata miyagun zantuka a ranta. Da ƙarfafa gwiwar mahaifiyarta ta samu damar fita ta nufi kogon tsafinsa, kafin ta ƙarasa ta hangi mahaifinta zaune a bakin bishiya da alama hutawa yake. Har za ta gifta shi sai zuciyarta ta fisge ta zuwa wurinsa don haka ta ƙarasa ta zauna a gefensa. "Na tafka maka babban kuskure da laifi mai girma mahaifina. Amma ina mai neman afuwa da yafiyarka don girman tsafi da sihirin da ka gada a wurin mahaifiyarka ka yi haƙuri ka yafe mini." Ta tsinci kanta da furta masa haka, don haka kawai take ji a jikinta wani mummunan al'amari na iya faruwa da ita, sai da ta saka mahaifinta ya yi mata alƙawarin ba zai hukuntata ko azabatar da ita b sannan ta fayyace masa duk abin da yake tsakaninta da Sarki Sulaimanu har zuwa cikin jikinta. "Amma Shugaba ya san da wannan maganar?" Mahaifinta ya wurga mata tambaya zuciyarsa na zafi, ta sanar da shi yadda suka yi da Shugaba Zurufu tun daga farko har ƙarshe har zuwa yarjejeniya da sadaukarwar da ta yi da abar bauta. "Babban kuskuren da kika tafka kenan Fargi, tun kafin na haifi yayyanki ba ma ke ba na san waye Shugaba. Na rantse da matsayin da na ba wa tsafi a matsayin madogarata Shugaba ba zai bar ki haka ba matuƙar ba ki bi abin da yake buƙata ba. Kuskure ne tun farko kika tafka shi, na sha faɗa miki abin da babba ya hango yaro ko ya hau dutsen dala ba zai gano shi ba." "Ka gafarce ni mahaifina." Ta furta cikin kuka da tashin hankalin ganin fushin mahaifinta. "Duk rintsi ni mahaifinki ne Fargi, a tsammanina tun da kina shirin zama mahaifiya ya kamata ki fahimci tasirin soyayyar da ke tsakanin ɗa da mahaifi. Ba zan taɓa juya miki baya ba sai dai ina tsoron abin da Shuga zai iya zartarwa, ina tsoron hukunci da zalincinsa..." "Ya kamata a ce mun dagakatar da tsoron Shugaba daga cikin zuri'armu, Shugaba ba shi ne abin bautarmu ba don haka bai cancanci ya dinga bautar da mu yadda yake so ba." Fargi ta katse mahaifnta. "Ba yanzu ba Fargi! Ba a yanzu nake hango bijire wa Shugaba ba sai dai ko zuwa wasunmu masu zuwa a nan gaba." Cikin rauni mahaifinta ya amsa mata. "Tabbas ba a yanzu ba amma koda ba ragowar numfashi a tare da ruhina, ina fatan jinina ya zama silar wargajewar duk wani tasiri na Shugaba, da wannan mummunar al'adar da aka sa a gaba. Kuma jikina yana ba ni sauyi na gab da zuwa mahaifina, har a ciki zuciya da ruhina ina jin tamkar ni ce wacce zan zartar da wannan sauyin. Don matsayin abar bauta ka maimaita kalaman nan nawa a gaban Shugaba matsawar hakan ya faru a nan gaba." Ta ƙarasa maganar tana miƙewa zuwa kogon tsafin Shugaba Zurufu, da kallo mahaifinta ya bi ta yana maimaita kalaman cikin tsinkewar zuciya. "A yau wa'adin kwanakin da na ɗibar miki suka zo ƙarshe game da maganar da muka taɓa yi da ke a baya. Fargi!" Ta ji Shugaba ya kira ta da wata irin murya, kafin ta amsa ta ji ya ci gaba da cewa. "Kada ki raina mini hankali domin ko mahaifinki a tafin hannuna yake sai yadda na sarrafa shi ba ke ba. Na hangi kusantowar abin cikin zuwa duniya, a yau ba sai wani lokaci ba za ki damƙa mini tasirin tsafinki idan ba haka ba zan yaye miki laluben da kike taƙamar shi ne rufin asirinki. Zan bayyanawa kowa abin da kika aikata kuma sanin kanki ne irin ɗanyane hukuncin da ake zartarwa..." "Tura ta riga da ta kai bangi Shugaba! A baya na yi makauniyar biyayya a gare ka, saɓanin yanzu da na san ciwo da 'yancin kaina. Duk wani hukunci da za ka ɗauka a shirye nake da na fuskance shi matuƙar zai kawo sauyi a rayuwar da zuri'armu take ciki, zan jure duk wata uƙubu daga gare ku kuma zan san duk yadda zan yi domin na tseratar da abin da yake cikina." A razane Shugaba Zurufu ya dube ta, ya sauke ƙwayar idonsa a kan cikin jikinta da ya rairaye ya yi ƙasa, murmushi ya yi mata sannan ya furta. "Ko a yanzu kin nuna mini ke rainona ce Fargi, don haka ni kuma zan nuna miki ba kada kura ke da wuya ba a feɗe ta shi ne aiki." Daga haka Fargi ta fice daga kogon tsafin kai tsaye ta nufi bishiyar abar bauta. Kamalu na lura da yanayin jikin Malam Umaru duk wani abin buƙata shi yake yi masa, amma lokaci sai ya lura da rikicewar jikin nasa duk da ba magana yake iya yi ba, jikinsa ya ji ya ɗauki zafi zau cikin tashin hankali ya sa aka kira masa Waziri da waɗansu manyan hadiman fada don ya san ko ya kira 'yan uwan mahaifinsa su Galadima ba lallai su saurare shi ba. "Baba Waziru jikin Malam Umaru ya yi tsanani ya kake ganin za a yi." Kamalu ya furta cikin damuwa. "A aika yanzu a zo da Malam Sharu mai magani, In shaa Allah zai samu lafiya." Waziru ya ba da umarni. Ba a ɗauki lokaci ba sai ga Malam Sharu mai magani ya ƙaraso rataye da jakar magungunansa na gargajiya. "Zan... sha... ruwa..." Malam Umaru ya furta murya na rawa. Tun da ya kwanta wannan ciwon sai a wannan lokacin ya samu damar yin magana, cikin hanzari Kamalu ya tallafo shi ya ba shi ruwa sai dai kaɗan ya samu ya sha ya ƙware. Sai da tarin ya lafa masa sannan ya furta. "Wani... ne... ya ɗauke mini... Jawahir. Don Allah... Mai gado a sanar da Takawa... a nemo mini ita. Kuma a isar mini wasiyyata... wurinsa idan Jawahir ta... samu miji ya taimaka ya zama waliyinta..." Tari ne ya sake sarƙe shi cikin tarin ya furta. "La'ilaha'ilallah... Muhammadur Rasulilla..." Daga haka harshensa ya sarƙe numfashinsa ya shiga kaiwa da kawowa, kafin daga bisani ya ɗauke gabaɗaya. Cikin kiɗima Kamalu ya fara jijjiga shi yana kiran sunansa, ganin haka ya sa Waziri ya janye Kamalu sannan ya ƙarasa ya rufe masa idanu. Malam Sharu mai magani da sauran mutanen da ke tsaitsaye suka fice jikinsu a sanyaye. Tamkar ƙaramin yaro haka Kamalu ya rushe da matsanancin kuka, don idan aka cire labarin mutuwar mahaifiyarsa da wahalhalun da ta sha wannan mutuwar ita ce mutuwa ta biyu da ta dake shi a duniya. Tun tasowarsa ya taso da bawan Allah mai matuƙar haƙuri, karamci da sanin yakamata. A ɓangare ɗaya kuma Jawahir ta faɗo masa da halin da za su shiga ita da Mai gado idan suka dawo suka samu labarin mutuwarsa. Gama jin kalaman aljana Zumjuttu ya harzuƙa Sarki Sulaiman, wani irin ɗaci yake ji a zuciyarsa nan take jikinsa ya fara karkarwa saboda tashin hankali, a guje ya ƙarasa ya shaƙi wuyan aljana Zumjuttu yana girgiza ta. "Ke annamimiya ce azzaluma maciciya, sai na kashe ki da hannuwana." Da hannu ɗaya ta ture Sarki Sulaimanu har sai da ya kusa kai wa ƙasa, ta saki murmushi tamkar abin da ya yi mata bai yi mata ciwo ba. "Ban san adadin irin waɗannan kalaman naka da na saurara a tsakar kunnuwana ba, don haka ka adana kalamanka idan ba haka ba yanzu kai ma za ka ƙarasa inda Fargi ta tafi. Wai ka san ma dalilin da ya sa abar bauta ba ta bi ta shafinka ba? Saboda ba ka san an haifa maka 'ya ba ballanta ka shiga duniya nemanta. Kuma na tabbata da ta san za ku sadu da juna da tuni kai ma ta hallaka ka don kar ka ba ta matsala." Zumjuttu ta furta cike da gadara. Ilahirin mutanen wurin jikinsu ba ƙaramin sanyi ya yi ba, tsararu daga cikinsu har da masu zubar da hawaye. Mai gado ta dubi Zumjuttu cikin kuka ta ce, "Tabbas biri ya yi kama da mutum domin tun da na zo duniya ban taɓa cin karo da gawar da ta tsaye mini a rai kuma ta ba ni mamaki ba tamkar ta mahaifiyar Jawahir. Don Allah don girman Allah da zatinSa ku ƙyale yarinyar nan tun da kun hallaka mahaifiyarta..." "Mu je ki kai mu wurin abar bautarku mu gana da ita don ina son jin daga bakinta." Dattijo Maharaz ya yi maganar cikin ɓacin rai. Cikin halin ko-in-kula ta amsa masa ta wuce gaba hannunta riƙe da Jawahir da ta yi shiru sai bin mutane take da kallo, don jin abin take tamkar a mafarkinta. Gabaɗaya mutanen da ke gaban kogon dutsen Shugaba Zurufu ne suka rufa wa su Dattijo Maharaz baya, wasu daga cikinsu suna murnanr ganin yadda Abar bauta za ta fusata ta yi musu mummunan hukunci, yayin da wasu suke zumuɗin ganin yadda dambarwar za ta ƙare. "Ku faɗi ku yi sujjada a gaban Abar bauta." Zumjuttu ta furta. "Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kaɗai muke bautawa babu wata hallita ko mahalukin da ya isa ya sa mu yi masa sujjada." Kamar haɗin baki Sarki Abdul'aziz da Dattijo Maharaz suka furta lokaci ɗaya. Wani irin rugugi suka ji tamkar hadari ya haɗo, wasu daga cikin mutanen jin haka ya sa suka arce don gudun kada fushin Abar bauta ya faɗo kansu. "Kun aikata babban zunubi don haka dole na hukunta ku, amma kafin nan me ya kawo ku wurin bautar da ake yi miki."Abar bauta ta faɗa cikin isa da ƙasaita. Dattijo Maharaz ya zayyane duk abin da suka ji daga bakin Zumjuttu, sannan ya ɗora da cewar. "Ki ji tsoron Allah kina hallitar Ubangiji amma kin dulmiyar da Bayin Allahn nan, me ya sa kin san gaskiya amma kika lulluɓe su kike damƙa musu ƙarya?" "Saboda ita ta fi karɓuwa a doron ƙasa, wai ma me ya sa kake son bayyana ainihin wace ce ni a gaban al'ummata?" Suka ji an sake furtawa daga cikin murgujejiyar bishiyar kukar gabansu. Tambayarta har ta so ba wa Dattijo Maharaz dariya, ya ƙarasa gaban bishiyar kukar ya dafa ta sannan ya ce. " Idan babu damuwa zan sa a kira mini waɗansu muhimman bayin Allah domin a kawo ƙarshen komai suma waɗannan mutanen su fara rayuwa irin ta mutane ba ta dabbobi ba." "Kar ka kuskura ka tara mini jama'a idan ba haka ba wallahi sai ranka ya ɓaci, fushina mai tsananj zai sauka a kanka." Dattijo Maharaz bai bi ta kanta ba, ya ambato sunan ɗaya daga cikin 'ya'yansa sannan ya ba shi umarnin gayyato masa Babban Malami, jin haka ya sa Sarki Abdul'aziz ya ce idan babu damuwa a taho da Alaramma wato shugaban limaman garin Huddam. Sai da Dattijo Maharaz ya gargaɗi ɗansa Shu'aibu da ya bi ta sigar da Alaramma zai fahimce shi don kar ya tsora da shi sannan ya sallame shi, yana gargaɗinsa da kada ya ɓata lokaci. Waigawa ya yi wurin mutanen da suka yi tsaye carko-carko ya ce, "Shin kun taɓa jin labarin wani addinin bayan wannan da kuke bautawa." Hayaniya ce ta ɗan kaure wasu sun amsa masa wasu kuma suka nuna ƙalubalantarsa don sun lura yana son wulanƙanta abar bautarsu ne a gabansu. "Da daɗewa na taɓa jin labarin addinin bautar wuta, bautar gumaka, bautar ruwa sai kuma wani addini wai musulunci. Amma shi a wurin masu kawo mana aikin asiri muke jin sa." Wani tsoho ya yi wa Dattijo Maharaz bayani, murmushi ya yi sannan ya furta. "Tabbas Addinin musulunci shi ne addinin gaskiya wanda kowanne bawa idan ya bi shi zai kai shi har cikin aljannah. Wannan abar bautar taku ita kanta hallitar Allah ce, jinsina ce wato jinsin Aljanu. Ko a yanzu idan na so aiwatar da abin da take yi muku nan take zan gudanar muku da shi, tana wasa da hankalanku ne amma ga wanda bai aminta da abin da nake faɗa muku ba ya zuba idanu zai ku ga ikon Allah." Rufe bakin Dattijo Maharaz sai ga Shu'aibu, Alaramma da Babban Malami. Shu'aibu da Babban Malami dukkansu cikin siffar bil'adam suke tamkar mutane ba jinsin aljanu ba. "Barka da zuwa babban Malami, mun taso ka babu shiri a yi mini afuwa dole ce ta sa haka." Dattijo Maharaz ya furta cikin girmamawa. "Assalamu alaikum. Barkanka dai Dattijo Maharaz ai tun da na ji haka na san babban uzuri ne ya haifar da haka, amma ina fatan ba Dela ce ta ɗauko mini wata maganar ba." Babban Malami ya furta yana kallon Abar bauta da har lokacin ba ta bayyana kanta sauran mutanen su ganta ba. Da mamaki Dattijo Maharaz ya ce. "Malam da ma ka santa ne?" Murmushin takaici Malam Liman ya yi ya ce. "Ban yi mamakin jin haka daga bakinka ba Marahaz, domin tun shekaru masu yawa a baya na sallama Dela daga matsayin 'yata. Ka san ɗa ne ka haife shi ba ka haifi halinsa ba." Mamaki ya sake mamaye Dattijo Maharaz da su Sarki Sulaimanu, nan take ya zayyane wa Babban malami duk abin da yake faruwa yana gama sauraronsa ya furta. "Innalillahi Wa'inna'lahir Raji'un! Yanzu Dela hatsabibancinki har ya kai ki dinga haɗa kanki da Ubangiji Dela? Na yi da-na-sanin haihuwarki tir da irinki a doron ƙasa." "Tun da ka sallama ni me ya yi saura Don Allah Baba ka tsame kanka daga cikin maganar nan." Abar bauta ta furta cikin tsiwa. Mamaki ne ya mamaye mutanen wurin wai Abar bautarsu da ta ce musu ita take hallitarsu take ciyar da su ta shayar da su ita ce har take da mahaifi kuma yake tsaye a gabansu. "Tun da har kika shiga hurumin Ubangiji ai sai in da ƙarfina ya ƙare a kanki, ko kaɗan rayuwarki ba ta da amfani, ashe kin san da Ubangiji kika ɗora su a wata hanyar daban. Allah wadaran halinki Dela na san har abada ba za ki sauya halinki ba." Malam Liman ya yi maganar ƙwallah na zuba daga idonsa. Sai da suka ɗaura alwala shi da Alaramma sannan suka fara karanta ayoyin da suke magana akan azaba, nan take ita da muƙarrabanta suka fara ihu da ƙaraji cikin tashin hankali. Tsiraru daga cikin mutanen wurin suka fara yanke jiki suna faɗuwa na su aljanun suna tashi, sun jima suna karatun Alƙur'ani tun suna jin muryoyi daban-daban har sautin ya fara raguwa wanda hakane ne ya tabbatar musu da sun ƙone wasu sai abin da ba a rasa ba. Zumjuttu tun da aka fara karatun ta gudu cikin jin tsananin azaba. Suna nan tsaye carko-carko suka ga wata hallita ta bayyana, tamkar tsuntsu haka take. Kanta akwai manyan ƙaho guda biyu, ta bayanta akwai jela sai ƙafafuwanta kamar na doki idanun uku a fuskarta. Da gudu suka ja da baya har su Sarki Abdul'azia, cikin ɓacin rai Mahaifinta ya ce. "Ki dubi dubban al'ummar nan ina za ki je da hakkinsu, tun wuri ki fito ki sanar da su ke ba Ubangiji ba ce. Ke hallitar Allah ce kuma ko a yanzu zai iya ɗaukar rayuwarki. Ki sanarda su Allah S.W.A. Shi ne Ubangiji sammai da ƙassai, Ubangijin mutum da alja kuma Ubangiji duk wata halitta da ke faɗin duniyar nan." *SHU'UMAR MASARAUTA* *45* *Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin MTN, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.* 🔚🔚🔚🔚🔚🔚 Lokacin da Fargi ta isa wurin abar bauta zubewa ta yi bisa gwiwoyinta ta rushe da matsanancin kuka, sai da ta yi mai isarta sannan ta yi sujjada a gaban bishiyar ta furta. "A kowanne lokaci Shugaba zai iya ɗaukan mummunan mataki a kaina, Abar bauta da ke na dogara ke ce madogarata." "Zan taimaka miki da dukkan taimakon da muka saba yi miki, ki tashi ki koma gida a daren yau ki dawo gare mu domin akwai buƙatun mutane da dama a gabanmu idan muka gama da su za mu ji da na ki." Abar bauta ta furta mata cikin kulawa, sai a lokacin Fargi ta ji ƙwarin gwiwa ta yunƙura za ta tafi, sai dai miƙewar da za ta yi ta ji mararta ta karta mata. A hankali ta fara takawa kafin ta ƙarasa gidansu ta lura da inkiyar da Sarku Sulaimanu yake yi mata idan ya kawo mata ziyara, sai da ta ɗan jingina da bishiyar Tsamiyar da ke gefenta sannan ta furta ɗalasiman tsafinta ta ɓace daga wurin, a inda suka saba haɗuwa ta same shi yana ganinta ya ƙarasa sa sauri ya riƙo hannunta. "Uwar Biyu barka da fitowa." Daidaita nutsuwarta ta yi don kada ya fahimci damuwarta. "Yau ka yi mini kyau Sarkina?" Fargi ta furta tana zuba masa idanu. "Ni kuma kin rame mini yau Fargi me yake damunki?" "Ciwon mara nake sama-sama." Ta furta tana ɗan yamutsa fuska. Da sauri ya ce, 'To ko dai abin ya zo ne?" Rufe idanunta ta yi da sauri cikin jin kunya, ya riƙe hanunta suka ƙarasa wurin dokinsa. Tabarmar kabar da ke saman dokinsa ya ɗauko ya shinfiɗa musu suka zauna suna ci gaba da hira, tun da Sarki Sulaimanu yake zuwa wurin Fargi bai taɓa daɗewa a wurinta kamar na wannan lokacin ba, don har sai da duhun magriba ya yi suna zaune a wurin. Sun yi hira sosai wata hirar ma ba sa dire ta Fargi take ɗauko masa wata. Wata su yi a kan abin da za ta haifa wata kuma a kan yanayin rayuwa, har a game da iyayenta sai da ta sanar da shi don haka duka damuwar da take ciki ta yaye mata. A wannan ranar Sarki Sulaimanu har zai hau dokinsa ya tafi Fargi ta coge wuri ɗaya a kan sai ya yi mata rakiya, wannan ita ce rana ta farko da Sarki Sulaimanu ya taɓa bayyana a zahiri ya yi wa Fargi rakiya har zuwa ƙofar gidansu, duk nutanen da suka wuce sai sun bi su da kallo amma shakkun Fargi ya sa ba wanda ya tanka mata. A ƙofar gida ma sun jima suna hira har sai da Fargi ta gaji don kanta ta sallame shi sannan ya tafi da cewar zai dawo washegari ya sake ganin sauƙin jikin nata. Da kansa ya shigar mata da duk kayayyakin da taho mata da shi gefen bukkarta sannan ya tafi har sai da Fargi ta daina hangensa sannan ta koma cikin gida. Washegari asubar fari suka ji hayaniya da kace-nace a ƙofar gidansu kafin sun yi wani yunƙuri su ka ji an fara kai duka kan kararen da suka zagaye ɗakunan bukkokinsu da shi. "A kashe ta sai an kashe ta tun da ta aikata babban kuskure wannan umarni ne daga wurin Shugaba." "Ba za mu saurarawa maci amanar zuri'armu ba." "A fito mana da Fargi domin ba za ta watsa wa Shugaba ƙasa a ido ba." Ire-iren kalaman da suka dinga ji suna tashi kenan daga bakunan mutane, cikin firgici Mahaifiyar Fargi ta riƙo hannunta ta bayan bukkarsu ta furta. "Maza ku gudu Fargi, ba na son Shugaba ya kashe mini ki, ɓace daga wurin nan Fargi tsafi da sihiri zai dafa miki." Ganin tashin hankalin da mahaifanta ke ciki ya sa ta fara zubar da ƙwallah, ba ta son barinsu cikin tashin hankali don haka ta girgiza kanta tana faɗin. "Ba zan iya barinku ba ban san halin da za ku shiga ba..." "Ki fita ki gudu na ce miki Fargi." Mahaifinta ya katse ta cikin ƙaraji. Duk yadda Fargi ta so sarrafa al'ƙalamin tsafinta domin ta gudu sai ta kasa, don haka ta faɗa ɗaki da sauri ta ɗauki wani sabon ganye ta ɗaure shi katamau a jikinta ta soka wata tsafaffiyar askarta a ƙugu da sauran tarkacanta, ta waiga tana ɗaga wa mahaifanta hannu sannan ta saɗaɗa ta bayan bukkar ta fice, duk da tana jin ciwon baya da marar hakan bai hana ta yin gudu tun ƙarfinta ba, sai da ta ɗan yi nisa sannan mutanen garin suka rushe duk wata bukka da ke gidan a ƙoƙarinsu na ganin sun gano Fargi ƙarfi da yaji, da suka fahimci ta gudu sai Shugaba ya ba su umarni da su rarrabu wuri-wuri ko za su samu nasarar kamo ta. Abu ɗaya ya ba shi mamaki yadda ya gagara sarrafa tsafinsa domin ya gano wurin da take, ya san dai ya dakushe na ta tsafin amma bai san me ya hana na shi ya yi tasiri ba. Abin da Shugaba bai sani ba tun da Abar bauta ta lura yana da niyyar kashe ta, a ranar sai ta dakusar masa da tsafinsa. A galabaice ta faɗi a wani ɗan ƙaramin ƙauye ta ɗebi ruwa ta sha saboda gudun da ta sha, tana nan zaune ta fara jin taku a hankali. Miƙewar da za ta yi ta yi arba da waɗansu matasa biyu daga cikin mutanen garinsu, da sauri suka ƙaraso wurinta ɗaya daga ciki ya kai mata naushi a ciki. Azaba ta sa ta faɗi gefe ta ɗauki wani ganyen bishiya ta hura iskar bakinta ta wurga musu, ganyen na sauka a fuskarsu ta kama da wuta. Wani irin azababban ciwon mara ya da baya ne ya haɗe mata, a daddafe ta iya matsawa daga cikin wannan ƙauyen ta tsallake wani ƙasurgumin dajin da ke gabanta, a lokacin ta da isa ta galabaita sosai don haka ta faɗi a gefan wata bishiyar kuka, da faɗuwarta babu jimawa ta fara jin motsin tafiyar mutane a tsorace ta ɗago don a tunaninta wasu daga cikin mutanen nata ne suka sake cim mata, amma ganin baƙin fuska ya sa ta sake kwantar da kanta ciwo ya sake taso mata gadan-gadan, har zuwa lokacin da Mai gado ta ƙarasa wurinta Malam Umaru ya juya musu baya ta haihu. Cikin ƙanƙanin lokaci mutuwar Malam Umaru ta karaɗe cikin masarautar Huddam, musammam ma Bayi ba ƙaramin kaɗuwa suka yi da jin mutuwarsa ba, kuma har lokacin ba su daina mamakin dalilin kwanciyar Malam Umar jinya da ɓatan Jawahir ba daɗin-daɗawa da suka ji abin da aka ce Malam Unaru ya faɗa kafin Allah ya yi masa rasuwa. Da farko an so a sallace shi a ranar amma kasancewar Magriba ta kawo kai ya sa aka bada shawarar barin gawarsa zuwa wayewar gari, Kamalu , Baffajo da sauran mutanen da suke mutumci da Malam Umaru ne suka ce za ku kwana da shi, domin kowa yaba kyawun halinsa yake da kyakkyawar mu'amalarsa da mutane. Kunyar duniya ce ta mamaye Dela musamamn yadda ta ga mutane suke bin ta da kallon mamaki, wasu daga ciki har sun fara tofa albarkacin bakinsu yayin da wasu har kawo lokacin tsoranta bai gama barin zuciyarsu ba. "Baba me kake so na ce maka bayan ka riga da ka gama tona mini asiri? Duk wannan wulaƙancin da kuka yi mini bai isa ba..." A fusace Babban Malami ya yi kanta ya kai mata duka, Dattijo Maharaz ya ɗan ruƙo hannunsa sanna ya furta. "Ka yi haƙuri Babban Malami ai In shaa Allahu komai ya zo ƙarshe. Idan za ta tuba sai a ƙyale ta ta ci gaba da rayuwarta..." "Ba za ta taɓa tuba ba Maharaz! Na san wace ce Dela 'ya ta ce fa. Ya zama wajibi a ƙone ta kowa ma ya huta." Rufe bakin Babban Malami suka ci gaba da ƙone Dela da ayoyin Ubangiji. ".Na daina na tuba don Allah kada ku hallaka ni." Dela ta furta a galabaice, babu wanda ya saurara mata daga cikinsu har sai da suka ga ta faɗi gefe ɗaya babu numfashi a jikinta. "Alhamdulillah!" Ita ce kalmar da suka furta gabaɗaya, jikin mutanen Rumzu ba ƙaramin sanyi ya yi da ganin abin da ya faru ba. Waɗanda suke gaban Babban Malami lokaci ɗaya suka zube a gabansa ganin haka ya sa sauran da ke bayansu gabaɗaya suka tsugunna alamar sun sallama masa. "A shirye muke da mu bauta maka tun da har muka ga ka kawo ƙarshen Abar bautar da muke bautawa tun iyaye da kakanni, tabbas mun gasgata ita ba abar bauta ba ce tun da har mun fahimci raununta." Tashin hankali ya bayyana ƙarara a fuskar Babban Malami don haka cikin hanzari ya furta. "Ni ba Ubangiji ba ne kamar yadda Dela ba ta kasance Ubangiji ba, ni hallitar Allah ne kuma shi ne ya kawo ƙarshenta saboda ayoyinSa ne muka karanta har muka hallaka ta. Ni da sauran waɗannan bayin Allahn duka Shi muke bautawa, ku sani Dela ta yi wasa da hankalunku ne saboda waɗansu abubuwan almara da take aiwatar muku, shi ya sa har kuka ba ta matsayin da ba ta cancanta ba. Shi jinsin aljani ba kamar mutum ba ne, Allah ya huwace mana baiwar da za mu iya rikiɗa duk wata hallita da muke so, kuma muna iya aiwatar da duk siddabarun da muke so a wurin da addini haɗi da addu'o'i suka yi rauni. Don haka a yanzu ma ba ku makara ba, za ku iya karɓar wannan Addinin ku yi riƙo da shi kuma ya zame muku makamin da za ku yaƙi duk wani hatsabibi ko hatsabiyar da ke doron ƙasa duk makirci da ƙarfin tsafinsa, domin ba su isa su ja da ƙarfin ikon Allah ba. Yanzu idan kuka yi imani da ni watarana na mutu wa za ku riƙa a matsayin abin bauta?" Babban Malami ya wurga musu tambaya, gabaɗaya suka yi shiru don jikinsu ba ƙaramin sanyi ya yi ba ganin haka ya sa ya ci gaba da cewa. " "Ubangiji shi kaɗai ne abin bauta saboda bai haifa ba kuma ba a haife shi ba, Shi kaɗai tal ba shi da abokin tarayya. Annabi Muhammad S.A.W BawanSa ne kuma ManzonSa ne, Ubangiji ba ya mutuwa ba ya tsufa don haka ku ji tsoron Allah ku hau turbar addinin Musulunci." "Muna goyon bayan wannan Addinin kuma a shirye muke mu karɓe shi hannu bibbiyu." Gabɗaya mutanen wurin suka amsa masa. Farincikin su Sarki Sulaiman ya bayyana a fili Dattijo Maharaz zai yi magana suka ga Sarki Sulaimanu ya fara zubar da ƙwallah. "Yanzu shi kenan Fargi ba ta rabauta da samun wannan Addinin ba? Kaico rayuwa ban so haka ba. Na so a ce ta rabauta amma kullin gaya mini take za ta karɓi Addinin Musulunci idan lokaci ya yi Allah ya jiƙanki Fargi." Jin haka ya sa Jawahir ta fara zubar da ƙwallah, Sarki Abdul'aziz ya dafa kafaɗarsa sannan ya ce. "Sarki Sulaimanu ita rayuwa duk yadda ta zo wa Bawa dama can Allah ya ƙaddarar masa ita a haka, tun ran gini tun ran zane. Dama can Allah ya ƙaddari Fargi ba za ta karɓi kalmar Shahada ba, amma kuma wani ikon Allah sai ya zama silar ta ne Al'ummarta za su rabauta da shi, koda Fargi tana raye aka yi haka idan ba ta da rabo ko duniya za ta haɗu a kanta ba za ta karɓi Addinin Musulunci ba. Mu manta da rayuwar baya mu fuskanci ta gaba, ina ganin haka zai fi Sarki Sulaimanu." Rufe Bakin Sarki Abdul'aziz Alaramma ya ɗora da cewa. "Akwai wani jan hankali da zan yi gare ka Sarki Sulaimanu da sauran mutanen wurin nan, duk da a yanzu girma ya kamaka. Ka sani kuskure ne babba yaro ya auri yarinya ba tare da sani ko amincewar iyayenta ba. Wallahi-wallai tun da Allah ya ƙaddari yarinyar nan Jawahir za ta fito tsakanin kai da Fargi da ka sanar da iyayenta babu abin da zai hana faruwar aurenku sai ikon Allah. Sau-tari akwai abin da idanunmu suke rufewa akai wanda ba alkairi ba ne amma idan muka yi haƙuru muka yi addu'a sai kuma mu ga abin ya zo mana ta ruwan sanyi." Ya waiga wurin Mahaifinsu Fargi sannan ya ce. "Babu camfi a addinin Musulunci ko tsubbu, don haka ya zama wajibi ku zubar da duk wasu tsubbace-tsabbace da tsafe-tsafe hatta wannan ɗabi'ar ta hana auren bare dole ku soke ta. Domin kuna ganin irin abin da ya haifar, ga dai yarinya har ta girma shin kun isa dakatar da ƙaddara ne?" Lokacu ɗaya suka ce. "A'a." Alramma da Malam Liman suka ci gaba da yi musu nasiha mai ratsa zuciya daga ƙarshe ya laƙanta musu kalmar Shahada yana faɗa suna maimaitawa. Mahaifi , mahaifiyar Fargi da yayyanta suka rungume Jawahir suna kuka gwanin ban tausayi. Babban Malami ya umarci su Sarki Abdul'aziz da su koma Masarautarsu shi zai koyar da su yadda ake wankan shiga Musulunci da sauran hukunce-hukunce da suka shafi addini. Sarki Sulaimanu kai tsaye ya ce zai tafi da Mahaifan Fargi don idan suka tafi da Jawahir suma ba su yi musu adalci ba, saboda ya lura da tsantsar soyayyar da suke yi wa mahaifiyarta, kafin su kai ga tafiya labari ya iso gare su Shugaba Zurufu ya caƙa wa kansa wuƙa ya mutu har lahira. Mai martaba sai da ya tara duka matansa sannan ya sa aka kira masa Yaya Halima, tun da ta shiga ɗakin gabanta yake faɗuwa don ta san tatsuniyar gizo ba ta wuce ta ƙoƙi ba. Sai da ya yi sallama suka amsa sannan ya dube ta ya ce. "Halimatu ga iyayenku a zaune muna so mu ji hukuncin da kuka yanke?" Idanunta suka ciko da ƙwallah ta ce. "Allah ya taimake ka ba na ƙi maganarka ba ne, amma duk lokacin da na tuna mijin Fatima zan aura sai hankalina ya tashi, ni fa yaya ce a wurin Fatima Sarki Abdul'aziz kuma sirikina ne..." "Gabaɗaya a kalamanki babu hujja Halimatu, ya kamata mu zubar da al'ada mu kama abin da Addini ya zo da shi, babu inda aka ce don ƙanwa ta mutu yaya ba za ta auri mijinta ba, amma idan kuna ganin ba ku aminta ba; ba za mu yi muku dole ba." Mai martaba ya katse ta. "Na amince ranka shi daɗe har cikin raina." Murmushi ya bayyana a saman fuskokinsu. "Allah ya yi muku albarka." Yaya Halima ta amsa da Amin. A wannan ranar Mai martaba ya rubuta wasiƙa ya aika ta Masarautar Huddam wurin Sarki Abdul'aziz, na amincewa da aura masa Yaya Halima a matsayin matar aure. Tafiya suka yi mai nisan gaske har sai da suka kwana a hanya sannan suka ƙarasa, a lokacin da suka isa Masrautar Huddam cikin zumuɗi Mai gado ta nufi sashenta domin sanar da Malam Umaru sabon labarin ban al'ajabin da ya faru a garinsu Fargi, sai dai turus ta yi sakamakon ganin mutane ana yunƙurin fito da makara ɗauke da gawa a ciki. Kamalu na ganinta ya matsa gefe yana zubar da ƙwallah. "Baba ka na ina?" Muryar Jawahir ta karaɗe wurin a lokacin da ta taho da gudu, ita ma turus ta yi tana bin mutane da makara a hannu da kallo. "Kamalu mai ya faru?" Mai gado ta tambaye shi a ruɗe. "Ki yi haƙuri Mai gado, dukkan mai rai mammaci ne dukkanmu can ne ƙarshenmu. Malam Umaru jinya ta ƙare wa'adi ya cika..." "A'a Baffajo ba dai Umaruna ba, Umaru a raye na tafi na bar shi ka bar faɗa mini ya mutu." Mai gado ta katse Baffajo a firgice. Da sauri Jawahir ta tunkari Kamalu, hawaye na zuba ta furta. "Don Allah da gaske ne abin da Baffajo ya faɗa?" Gyaɗa mata kai ya yi jin haka ya sa Jawahir ta rushe da matsanancin kuka. Sai da aka yi wa Mai gado nasihohi da ban baki sannan ta matsa gaban gawar Malam Umaru ta fara yi masa addu'a, ta ɗora hannunta a saman jikinsa kuka ya ci ƙarfinta. "Ina fargabar ranar da zan mutu na bar ku ke da Jawahir Mai gado, don Allah ko ba na raye kada ki yi wa yarinyar nan riƙon sakainar kashi." "Kin san ranar ɗaurin auren Jawahir In shaa Allahu duk wanda zai aure ta ɗinki iri ɗaya zan yi mana ni da shi." "Mai gado me ya kamata mu fara siya na auren yarinyar nan ne?" Ire-iren maganganun Malam Umaru na baya suka dawo mata cikin kunnuwanta. Inna wuro ce ta janye ta sannan aka fitar da gawar. Sarki Abdul'aziz shi kansa ba ƙaramin kaɗuwa ya yi da jin mutuwarsa ba. Shi ya sallaci gawar da su Sarki Sulaiman sannan aka wuce da shi gidansa na gaskiya. Sai da suka yi wanka suka huta suka ci abinci sannan Sarki Sulaiman ya buƙaci tafiya da Jawahir a cewarsa bayan wani lokaci zai dawo da ita, saboda so yake ta san dangi kowa ya santa, da farko Mai gado ta so nuna rashin jin daɗinta hakan ya sa Jawahir ta ƙi amincewa da bin Mahaifinta har sai da Mai gado ta ɗan tsawatar mata. Gabaɗaya suka ɗunguma har mahaifan Fargi suka nufi masarautar Sarki Sulaimanu. Sarki Abdul'aziz da saurah Fadawansa suka yi musu rakiya har bayan gari. Sai dai kafin su tafi Sarki Abdul'aziz ya tabbatar wa da Sarki Sulaimanu Mahaifan Fargi za su ci gaba da zama a cikin Masarautar Huddam gabaɗaya. Saƙon Mai martaba da ya ƙarasa wurin Sarki Abdul'aziz ba ƙaramin faranta masa rai ya yi ba, don haka ya samu Waziri da sauran 'Yan uwan mahaifinsa waɗanda suke raye ya tura su domin su yi duk abin da ya dace. Da yake ya san hannunka ba ya ruɓewa ka yanke ka yar sai da ya sa aka yi wa su Ciroma da Galadima magana, Ciroma ne ya amince da zuwa domim shi tuni ya zubar da makamansa amma Galadima ko kyakkayawar amsa bai bayar ba. Wani abin farinciki suna isa Mai martaba ya sa aka ɗaura auren Sarki Abdul'aziz da Yaya Halima, sannan a wannan ranar masu kawo ta suka nufi Masarautar Huddam. Sarki Abdul'aziz bai yi mamaki ba domin ya san Mai martaba mutum ne mai karamci da dattako, waɗansu sababbin ɗakuna da aka gina aka gyara wa Yaya Halima ta tare a ciki. Nan da nan labarin auren Sarki Abdul'aziz da Yaya Halima ya karaɗe cikin masarautar Huddam, baƙin da suka rako ta Takawa ya sa aka haɗa musu Sha tara ta arziƙi. Da Sailuba ta ji labari tamkar ta haɗi yi zuciya ta mutu saboda baƙinciki, da gayya 'yan matan da manyan matan Bayi suka din ga shiga suna yi mata habaici saboda baƙinciki, sai ta rushe da kukan nadama da da-na-sanin abin da Mahaifiyarta ta ja mata, don ta san har abada taɓon da ta yi musu ba zai taɓa gogewa ba. Kuma a washegarin da aka kawo Yaya Halima ne Sarki Abdul'aziz ya naɗa Inna wuro a matsayin Jakadiyarsa, wannan matsayin sai ya zo musu a bazata daga ita har Baffajo. Takanas suka zube a cikin fadarsa suka shiga zabga masa godiya, shi kansa Kamalu ba ƙaramin daɗin hakan ya ji ba don ya san fiye da haka ma su Inna wuro sun cancanta. Bayan da Sarki Sulaimanu ya gama gabatar da Fargi babu mutum ɗaya da ya amince da kalamansa ciki kuwa har da Mahaifiyarsa, kuma nan take ƙananan maganganu suka fara tashi wasu ma suka fara gulmar Sarki Abdul'aziz ya haifi Shegiya babu aure, takanas ya sa aka kira masa Jakadiya da Waziru waɗanda suka zame masa Shaida, da farko Waziri har zuciyarsa ta fara wassfa masa ya ƙaryata Sarki Sulaimanu amma da ya tuna ƙauyen da suka je da amininsa da ya zama waliyin Fargi, za su iya furta gaskiya nan take ya zayyane gaskiyar abin da ya sani. A hakan ma Mai babban ɗaki ba ta yadda ba sai da ta sa aka tashi waɗansu manyan Fada zuwa garin da Waziru ya ce a nan aka ɗaura aurensu suka yi bincike sannan suka aminta da ita, ya zayyana musu irin kisan zalincin da aka yi wa Fargi da halin da Jawahir ta yi yunƙurin shiga duka a sanadinsa. Nan take Mai babban ɗaki ta gane kuskurensu na ƙin barinsa ya auri zaɓinsa, suka rungumi Jawahir cikin soyayya da kulawa sai dai daga ɓangaren matansa ƙiri-ƙiri suka nuna kishinsu a fili, sai Sarki Sulaimanu da Mai babban ɗaki suka tsawatar musu sannan suka sauko kuke kulawa da ita. Bayan da suka kwana biyu suka huta ne kuma aka fara shiga da Jawahir cikin dangi 'yan uwa da abokan arziƙi, Jawahir har mamaki take yi ganin irin gatan da take samu, a ɓangare ɗaya kuma idan mutuwar Malam Umaru ta faɗo mata sai ta shiga ɗaki ta ci kuka ta more. "Wai ni ma 'Yar Sarki?" Ta wurga wa kanta tambaya tana sakin murmushi, kallon alƙaryar da take ciki take tana jinjina irin wahalhalun da bayi suke sha don jin ta take tamkar a cikin aljanna. "Ranka shi daɗe! Don Allah wata alfarma gar ni." Sarki Sulaimanu ya zuba wa Jawahir ido cikin tsananin soyayya, don jin Jawahir yake ta fi dukkan 'ya'yansa samun fada a zuciyarsa. "Muna sauraronku tafi a kai tsaye Jawahiruna." "Don Allah a dinga kula da rayuwar Bayi da halin da suke ciki, ranka shi daɗe a dinga duba cima da wurin makwancinsu. Na taso cikin ƙangin bauta da Bayi, na san wahala da rashin 'yanci da ke cikin rayuwar Bayi da 'ya'yansu idan da hali a dinga kyautata musu ko da ba za su kai matsayin iyalin Sarki ba. " Jawahir ta sauke numfashi ta ci gaba. "Ba iya Masarautar Huddam ba, a wannan gidan ma na ga irin rayuwar da na fuskanta a baya. Don Allah a tausaya musu domin suma 'ya'ya ne kamar mu." Murmushi Sarki Sulaimanu ya yi jin yadda take zayyana zance tamkar mahaifiyarta. "Tabbas barewa ba za ta yi gudu ɗanta ya yi rarrafe ba. Fargi ba za ta taɓa gogewa daga zuciyarmu ba har sai mun daina numfashi, In shaa Allahu za mu kyautata wa Bayi kamar yadda kuka buƙata, za kuma mu wae musu rana guda a mako domin shaƙata." "Godiya nake ranka shi daɗe." Jawahir ta furta cikin girmamawa. Bayan Wani Lokaci Kamar yadda Sarki Sulaimanu ya alƙawarta bayan da su Jawahir suka samu kwanaki masu yawa, suka shirya da kayan alfarma tare da tsarabar sha tara ta arziƙi suka nufo Masarautar Huddam haɗe da maganar auren su Kamalu. Jawahir na zuwa Sashen Mai gado ta nufa da gudu ta rungume ta sai da ta suka ɗan sha kukansu na rashin Malam Umaru, suka sake jajantawa kansu sannan ta shiga ba ta labarin duk abin da ya faru. Bayin cikin masarautar manya da yara suka shiga tururuwar zuwa ganin Jawahir, nan ta fara ganin kulawa da soyayyar da suke nuna mata. Wasu daga cikinsu har mamakin yadda suke haba-haba da ita take. Ɗakin Abubakar ta shiga ta same shi a zaune, yana ganinta ya sakar mata murnushi alamun ya gane ta, a hankali ya yunƙura ya fara tafiya yana ɗan layi kamar zai faɗi har ya ƙarasa wurin Jawahir. Daɗi ne ya kamata ganin jikin Abubakar ya ƙara kyau don Sarki Abdul'aziz ya dage da nema masa magani sosai, gwaranci ya shiga yi mata tana biye masa suna ciki haka Ruƙayya ta shiga suka ci gaba da hira. Kafin su Sarki Abdul'aziz su zauna tsayar da maganar aurensu Kamalu sai da ya aika aka kira Kamalu, Muhsin da Jawahir. "Ba tun yau ba Jawahiruna na ce ba zan yi miki auren dole ba, don haka na sa a kira ki don na ji ta bakinki shin kina son Muhsin." Dire kalaman Sarki Abdul'aziz suka yi daidai da bugun ƙirjin Kamalu. A razane ya ɗago yana kallonta ta sunkuyar da kai ƙasa idanunta suka ciko da ƙwalla ba tare da ta amsa ba. "Duk yadda kuka yanke daidai ne ranki shi daɗe." Ta ƙarasa maganar hawaye na zuba. "Jawahir a yi magana muna sauraronki ke za ki zauna da shi ba mu ba." Cewar Sarki Abdul'aziz don ya ji daɗin yadda Sarki Sulaimanu ya yi masa kara. "A gafarce ni ranka shi daɗe amma Jawahir ba ta son Muhsin." Kamalu ya furta kai tsaye. Daga Sarki Sulaimanu har Sarki Abdul'aziz idanu suka zuba masa, ya sunkuyar da kai ƙasa ya furta. "Na san Jawahir farin sani ba tun yanzu ba wallahi ba ta son Muhsin..." "Ƙarya kake munafuki." Muhsin ya katse shi a harzuƙe. Murmushi irin na manya Sarki Abdul'aziz ya yi ya ce. "Tsakanin Kamalu da Muhsin wa kike so?" Da sauri Jawahir ta ɗago ta dubi Kamalu, ta yi saurin goge hawayenta ta saki murmushi ta sunkuyar da kai ƙasa. "Kamalu kike so?" Ya sake wurga mata tambaya, da sauri ta gyaɗa kai sannan ta fice daga ɗakin tana dariya. "Za mu aura miki wanda kika so Jawahiruna saboda haka ku tashi ku ba mu wuri." "Dama ni na jima ina ganin bambamci ai, ni na san ba ƙaunata ake yi ba idan ba haka ba ai har mahaifiyata da tuni an fito da ita. Kuma wallahi babu wanda ya iya ya hana ni aurenta." Muhsin ya yi magnanar yana fita daga ɗakin. "Matuƙar muna numfashi za mu aura wa Jawahir zaɓin ranta, duka 'ya'yana ne amma kowa na san nutsuwa da ɗabu'unsa. Amma muna neman alfarmar a ɗaga mana bikin nan zuwa makwanni biyar masu zuwa, sakamkon muna jiran Mai gado saura kwana huɗu ta fita daga Takaba. In shaa Allahu akwai aikin alkairin da za mu zartar a kanta." Sarki Abdul'aziz ya furta yana murmushi. "Ranka shi daɗe da alama kai ma sharce amarcin kake shirin yi, shi ke nan babu damuwa Allah Ya nuna mana." Gabaɗaya suka saka dariya. Takaicin da ya kama Muhsin kai tsaye sashen ɓangaren ɗakin duhu ya nufa, yana tafe yana hawaye ko gabansa ba ya gani duk wurin da ya wuce kallonsa Bayi suke yi. Tsayuwarsa a wurin ƙofar ya ga yadda Mahaifiyarsa ta sake lalacewa, ƙoƙon kanta ya yi waɗansu mula-mulan ƙuraje, da alama duk sun ɗuri ruwa. Basiru ya hanga tsaye a gabanta da wata kaifaffiyar askar, duk yadda Fulani Umaima take yi masa roƙo da magiya bai saurare ta ba. Askar ya miƙa da niyyar ya yanki kunenta Bamaguje ya dira a gabansa, daga fuskarsa har jikinsa a daddauje yake, sai taintsiyar hannun Bamaguje da take a guntule. Kafin Basiru ya yi wani yunƙuri Bamaguje ya ɗauke ta suka ɓace, Fulani Umaima ta shiga ƙwalla ƙarara tana faɗin ya sauke amma ko ta kanta Bamaguje bai bi ba, ganin haka ya harzuƙa Basiru ya kwarara ƙara shi ma ya rufa masa baya, ya ɓace nan take. A ɗimauce Muhsin ya yi cikin gida ya sanar da mahaifinsa halin da ake ciki, Sarki Abdul'aziz shi da Sarki Sulaimanu ne suka je wurin tun a nesa suka dakata saboda wari, ya saka Dogarai suka duba ɗakin sai dai babu Fulani Umaima babu dalilinta, sai Jakadiya da take galabaice cikin dagwalon ƙazanta. Takawa ya bayar da umarnin a fito da Jakadiya a sallame ta daga Masarautar Huddam. Komawarta sashen Mai gado ta ji jikinta ya ɗan ɗauki ɗumi, daga tsakiyar cikinta ta ji ya fara ɗaukan zafi. Tana ɗaga rigarta ta ga tambarin bishiyar abar bauta ya sake bayyana, ta buɗe baki za ta yi magana kenan ta neme shi ta rasa. "Ko dai idanuwana ne suka niyyar yadarata?" Jawahir ta wurga wa kanta tambaya. "Da zarar kin sake ganin wannan tambarin na cikinki, ki tashi ki ɗaura alwala ki fara karatun alƙur'ani, kuma ki sanar da Maharaz ya sanar da ni." Jawahir ta tuno kalam Babban Malami na baya a cikin kunnuwanta. Ajiyar zuciya Nimrah ta sauke bayan ta rufe ƙaton littafin da take karanta wa ƙawayenta su Intisar, wanda a bayansa aka rubuta SHU'UMAR MASARAUTA da babban baƙi. Ta kalli su Nihal da ke gabanta ta furta. "Kun san dalilin da ya sa na fara rubutu har na zama marubuciya da maƙasudin rubuta lattafin nan?" "Amma dai ba kina nufin labarin ya ƙare ba?" Nawwarah ta tambaya tana kwaɓe fuska. "Sai kun ba ni amsar tambayata." Nimrah furta tana rungume ƙaton littafin a ƙirjinta. Cikin haɗin baki suka furta mata. "A'a Sister Nimrah sai kin faɗa." don sun damu su ji daga gare ta. "Ranar da Umma ta ba ni labarin Mahaifiyarta! Saboda labarin cike yake da almara, zalinci ban tausayi da taɓa zuciya." Nihal ta yi sauri faɗin, "Wai kina nufin Jadda dai kakarku ita ce Jawahir ɗin da kika karanta mana labarinta?" Dariya Nimra ta yi ta ce, "Kina mamaki ne?" Lokaci ɗaya suka gyaɗa mata kai. "Ƙwarai kuwa ita ce, don kafin na fara rubutun labarin nan sai da na je na sake jin komai tiryan-tiryan daga bakinta sannan na rubuta shi." "Lallai ashe Jadda ta ga duniya. Amma don Allah da gaske labarin a nan ya ƙare?" Intisar ta tambaya kamar za ta yi kuka. Miƙa mata littafin Nimra ta yi ta ce, "Ga shi nan ki duba idan ƙarya nake miki." Marairaice murya Intisar ta yi ta ce. "Amma bayan tafiyar Fulani Umaima ina Bamaguje ya kai ta? Ya suka ƙarke da Basiru? Kuma wai a ciki wa Jadda take aura Muhsin Ko Kamalu? Ni fa duk tarzomar da aka yi ban ji kin ce Sarki Abdul'aziz ya saki Fulani Umaima ba, kuma wane ne ya gaji Sarki Abdul'aziz? Wai ya aka yi aka kwana a ragaya?" Nimra ta ɗaka mata duka a cinya haɗe da miƙewa tsaye ta ce. "Sannu 'yar Jarida sai ki bari na yi sallar magariba na dawo, kin san dai kullin huɗubar Mai martaba kenan a dinga sallah a farkon lokacinta." Nimrah ta ƙarasa maganar tana ficewa daga ɗakin, Intisar da Nihal har rige-rigen ɗaukar littafin suke yi. Nihal ta sake duba bangon littafin a fili ta furta. "SHU'UMAR MASARAUTA. Labari mai almara da tsaya wa a rai." TAMMAT BI HAMULILLAH Ina matuƙar godiya ga Allah S.W.A da ya ba ni ikon kammala wannan littafi na SHU'UMAR MASARAUTA. Gadiya mai tarin yawa a gare ku masoya waɗanda suka sa kuɗinsu suka sayi littafina wannam ma soyayya ce, ina mai jinjina muku bisa yadda kuka ɗauki kwanaki kuna bibiyar littafin nan Allah ya bar ƙauna. 🥰❤️ Na ce ba🌚 'Ni maYar adam ce wato tara dai nake ban cika goma ba, na tabbata kun ga kurakuran da ba a rasa ba a yafe ni, kuskuren ciki Allah ya yafe mana darasin da ke cikin labarin Allah ya ba mu ikon ɗauka. *DON ALLAH DON GIRMAN ALLAH DA ZATINSA, DON SOYAYYAR DA KUKE WA ANNABI MUHAMMAD S.A.W KADA KU HAƊA MINI DOCUMENT ZAN HAƊA DA KAINA, DON ALLAH BA DON NI BA."*👏🏻👏🏻 Ummou Aslam Bint Adam🌚